*************************⬇********************** ************* Ai Hausa Novels **************** *************************⬆ ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ⬇ ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ⬆ ************************** 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S* _we don't just entertain and educated we tauch the heart of the readers_ #WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM #IG PML WRITERS #https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035 #http://maryamsbello.blogspot.com *AM BACK AGAIN BY THE GRECE OF ALLAH* *Alkhairin dake ciki Allah yasadani dashi, shairin dake ciki Allah ya tsareni dashi* *muje zuwa masoya ana bala'in tare🤝 (UMMU SAFWAN CE*) *1* "Sauri takeyi domin ganin ta k'arasa gida, dan tasan yanzun *kaka* tana can hankalinta a tashe ganin lokacin dawowarta islamiya har ya wuce, kallon agogon hannunta tayi, taga 7:30pm Taja wani dogon ajiyar zuciya had'ida k'ara yin sauri harda d'an gudunta domin ganin sallar isha'i ake neman akira yanzun." taja wani dogon tsaki ta juyawa ta kalli k'awarta Maryam da itama ganin *Afnan* d'in na sauri hankalinta a tashe ya sanyata itama yin saurin." Sannan Tace "Maryam duk kece kika b'ata mana lokaci wurin biyan haddarki, gashi yanzun dare yamana a hanya kuma bayan kinsan kaka ta tsani na kai magariba bana gida, ni yanzun bansan yanda zan cemata ba idan na koma gidan." Maryam tace "kiyi hak'uri Afnan bada son raina muka kai iyanzun bamu koma gidaba, koma meye laifin malam *Nura* ne da ya tsayar damu a cewarsa sai mun iya karatunshi sannan zamu dawo gida." *Afnan* bata kuma tankawa *Maryam* ba, domin batason yawan suruto, magana d'aya biyu takeyi sai tayi shuru, da zarar da cika magana sosai, ko kuma ana yawan yi mata surutu a akai to kanta ciyo yakeyi." Wannan dalilin ne yasanya ko k'awaye bata dasu, k'awarta d'aya ce *Maryam* itama unguwarsu d'aya kuma mak'otane sosai domin gida biyu ne a tsaninsu, Tare suke zuwa makaranta Arabic da Boko." sauri kawai sukeyi ba Wanda ya kuma yiwa d'an uwanshi magana domin *Maryam* tasan halin *Afnan* sarai bata son yawan suruto Karya kwanar da zasuyi, da zata b'ullewa dasu gaban gidansu, saiji sukayi anja burkin mota da k'arfi." A razane suka firgita musamman *Afnan* gaban ne yashiga fad'uwa jikinta na rawa, domin tasan kwanar gidansu mota bata fiya shuguwa ba, ga kuma duhun dare da somayi ba kowa ne mutum ke yawan wucewa ta wurinba." Kashe mata ido akayi da fitilar motar hankalinta ya kuma tashi idonta ta cika da hawaye, taja gefe d'aya ta tsaya tana jiran kowaye ya wuce sannan suma suwuce." Ganin motar tak'i tafiya kuma ankashe masu ido da fitila, Maryam kuma na ganin hakan taja da baya da baya a tsorace ta antaya da gudu ta barta nan." Wani saurayi tagani yafito daga motar da alama a buge yake da giya, sai tangad'i yakeyi yanufota gadan gadan." *Afnan* naganin wurinta ya nufo, a tsora ce, ta k'ank'ame jikinta tadin ja da baya da baya cike da tsoro a fuskarta." Shima biyarta yakeyi yana kallonta yana murmushi." itama kallonsa takeyi domin bata tab'a ganin kalar wannan fuskar tashiba, amma alamu sun nuna cewa d'an sarkine diba da tayi da kalar shigar da yayi da kuma hularshi mai *Tambarin sarautar* masarautar sarki Ahmad Moh"d, Sai kuma alkibbarshi dake rataye a kafad'arshi, " *Bassam* kenan d'an sarki maiji da kud'i da mulki ya taka duk Wanda yakeso a garin yanda yaga dama." nufarta yakeyi da wani kalar murmushi a fuskarshi, domin ganinta yakeyi sak kamar budurwanshi *Basma* wanda suka rabu da ita yanzun a club." Kamota yakeso yayi ya rungume amma besamu sa'ar yin hakanba, sai yashiga fad'in "haba *Basma* yau kuma guduna kikeyi?" Yana nuna kanshi cike da maye." ita kuma tana ja da baya cikin tashin hankali, Tana zubarda hawaye "wannan bala'i daya keso ya tunkarota cikin daren nan, gashi unguwarsu mutune basu cika wucewa ba idan dare yayi hakan." Wannan dalilin ne yasanya *Kaka* bata barinta fita waje, da zarar suntaso daga makarantar islamiya k'arfe shida, to bata barinta Zuwa ko ina sai kuma gobe." "Amma yau gashi kaddara takirata har isha'i tana waje, gata yanzun ta had'u da wannan bala'i a gabanta, "Tasan yanzun wannan mashayin ko kasheta zaiyi ba Wanda zai fito ya taimaketa." Ta kuma fashewa da kuka mai sauti tana addu'a a zuciyarta "Allah yakawo mata d'auki." cigaba tayi da Jada baya shima yana kuma kusan tota, har takawo jikin wani shago dake kulle taja ta tsaya, had'ida runtse idonta tana zubar da hawaye, tana addu'oi." Yana zuwa daf da ita ya kuma ganin takoma mashi *Basma*shi sak,👌🏼 ya kuma sakin wani murmushi irin na mashaya, yarik'o hannunta ya murzashi yace "haba *Basma* baki ganeni bane kike guduna?" Wata gyatsa yasaki mai d'auke da warin giya, da tsami." *Afnan* tayi saurin toshe hancinta, cike da tsoro da kuma b'acin rai, "domin tunda Allah ya halinceta babu namijin da yatab'a rik'a mata hannu sai yau." Bata ankaraba saijinsa tayi ya rungumeta yana fad'in *Basma*yau ni kike toshewa hanci?" Warina kikeji ?" Aikuwa wani k'arfi ya zo mata, cike da b'acin rai ta tureshi daga jikinta tasanya hannu biyu ta kwad'a mashi lafiyayyen mari mai kyau a kuncinshi, wadda sai da ya kusan dawowa hankalinshi, Hakan yayi dai dai dawowar wutar Nepa, *Prince Bassam* rik'e da kunci yayi tsaye tsam, ya kurawa *Afnan* ido ko gyaftawa bayayi kamar wanda ke tunanin wani abun." Bata ankaraba taji muryan *Maryam* tareda mahaifinta Malam *Iro*, Malam *Iro* yace "kinyimin dai dai *Afnan* dakika mari wannan mutumin Wanda besan darajar d'an Adam ba." yanunashi da yatsa👉🏻 Malam *Iro* ya zagayo ta gabanshi ya tsaya." yaci gaba da cewa, "wannan hukuncin da taimaka shine dai dai da kai, Domin kana tak'ama da kai d'an sarki ne, kake taka mutane yanda kaga dama, ka kuma tare 'ya'yan Mutane a hanyan lungu sak'o kana cutar dasu, Dan kana tak'ama da sarauta wadda mahaifinka ba hakan yakeyiba." To kasani mulki ba hauka bane, kuma Allah zai saka mata abunda kayi mata." Yana kawowa nan yaja hannun *Afnan* da *Maryam* suka nufi hanyar gida." *Bassam* dafe da kunci yayi tsaye yana kallonsu d'aya bayan d'aya, har malam *Iro* ya gama zazzaga mashi masifa bai motsa daga inda yakeba." Malam *Iro* yaja hannunta tare da *Maryam* suka tafiyarsu, Tafiya sukeyi yashiga yimata nasiha had'ida bata hak'uri akan abunda yafaru da ita a yanzun." Yashiga kwantar mata hankali, domin a zahirin gskiya *Afnan* tausayi take bashi. Ya kuma ce mata "wannan abun da yafaru karta fad'awa kowa tabarshi iyasu uku da suka sani, har *Kaka* karta fad'a mawa." Nan ta share hawayenta tace "insha Allah *Baba* ba Wanda zanfad'amawa, Sukayi sallama ko wannensu yashiga gida." *Bassam* kuma tsaye yayi yana kallonsu sai da yaga sunshige gida, sannan ya girgiza kai ya cije baki, cike da maye yake tafiya zuwa wurin motarshi yashiga yajata da k'arfi yabar layin 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S* _we don't just entertain and educated we tauch the heart of the readers_ #WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM #IG PML WRITERS #https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035 #http://maryamsbello.blogspot.com *2* " *Afnan* na shiga gida tareda sallama, *Kaka* tayo kanta ta rungumeta tareda ajiyar zuciya mai k'arfi, sannan daga k'arshe tace " *Afnan* ina kika tsaya?" Gaba d'aya kin d'aga min hankali, tund'azun nakasa zaune na kasa tsaye ke kad'ai nake tunani a zuciyata ina Addu'ar Allah yasa ba wani abun yasameki a kan hanya ba." Murmushi *Afnan* tayi had'ida zame jikinta daga jikin *Kaka* sannan tace "tsuhuwa mai ran k'arfe babu abunda yasameni a hanya, kuma lafiya k'alau nake." Abunda yasa muka dad'e malam *Nura* ne ya tsayar damu har sai lokacin da muka iya karatunsa." *Kaka* tayi dariya sannan tace "Kai Allah yayi malam *Nura*Albarka yasa yazamo mijinki har a gudan Aljannah, domin yanda yake kula dake da kuma karatunki inajin dad'i sosai." *Afnan* tasaki wata kalar dariya domin *Kaka* tayabi masoyinta, Cike da murmushi a fuskarta tace. "Kai *Kaka* kinsanfa sainayi karatu sosai nazamo cikakkiyar lauya, domin sai na amso dukiyarmu a hannun azzalumi can, Alhaji *Aminu* sannan kuma daga k'arshe nayi masa hukunci dai dai da abunda ya aikata mana." Idonta ya cika da hawaye, ta rab'a *Kaka* tashige d'aki tashiga zubar da hawaye." *Wacece Afnan*?" Mahaifin *Afnan* Alhaji *Ibrahim Sani* cikakkin bakane ne, a anan cikin garin kano yake da zama, yana kasuwancinsa Nijer zuwa Dubai, idan ya d'auko kaya zai shigo dasu garin kano ya sayar, ko kuma yasara a kano yakai Niger ko Dubai yasayar." Allah yayiwa Alhaji *Ibrahim* rufin asiri dai dai kwarkwado, Wanda ya d'an manyanta amma beyi aureba, ya gina katafaren gida daga shi sai mahaifiyarshi ke zaune cikin gidan, kullum maganar Hajjah mahaifiyarshi itace "yayi aure, Domin itama mahaifiyar tashi rashin yin auren nashi abun yana damunta sosai kullum maganar ta d'ayace "yadaiyi aure." Ya kuma samu mace 'yar gidan mutunci ya aura, amma zaman shi a hakan ba aure be kamata ba." Kwatsam wata rana yaje garin nijer saro kaya yaci karo da wata kyakkyawar mace mai natsuwa da kamala, Anan take yaji tashiga ranshi kuma yashirya zai aureta." anan take yaje yayiwa *Liman* magana akan yanaso abashi auren yarinyar da yagani, Ai kuwa dasa hannun mai *Liman* aka aura masa aure da *Halimatu Sadiya* wato mahaifiyar *Afnan* ba dan Mahaifanta naso ba." Mahaifiyar *Afnan* 'yar asalin Agadas ce, irin buzayayen nan ce na Agadas masu masifar kyau kamar sune suka halicci Kansu, saboda kyau da diri." A can Alhaji *Ibrahim* ya gano *Halimatus Sadiya* ya aurota, yakawota mahaifarshi garin Kano ya ajiyeta gida d'aya da mahaifiyarshi *Hajjah* *Hajjah* najin dad'in zama da *Halima* domin kuwa bata da matsala sai dai rashin jin hausar da batayine, koshi kad'an kad'an zatafara ji." Haka sukaci gaba da zamansu cikin jin dad'i da kwanciyar hankali da walwala, Alhaji *Ibrahim* kuma kasuwanci sa sai bunk'asa yakeyi, domin yanzun Alhmdulillah kud'i sun zauna masa sosai Wanda har ana iya sanya lissafinshi a masu kud'in garin kano." Alhaji *Ibrahim* yana da wani Aboki ko kuma nace babban Amini mai suna Alhaji *Aminu* Wanda yakasance ya bashi amana Sosai, duk wasu harkokishi na kasuwancinshi babu Wanda baya fad'awa Alhaji *Aminu* domin ya yarda dashi, kuma yayi Imani da cewa Alhaji *Aminu* bazai cutar da Shiba." Shi kuma Alhaji *Aminu* a wurinshi ba hakan bane, domin a zuciyarshi babu Wanda ya tsana, yake kuma hassadarshi sama da Alhaji *Ibrahim*." a gabansa zai nuna masa so, sosai a bayan shi kuma yana muna furtanshi, burin shi a d'aya a kullum yaga mutuwar Alhaji *Ibrahim* ko kuma yaganshi ya durk'ushe ya talauce." ___________________________ Haka dai Rayuwa taci gaba da tafiya tsakanin Alhaji *Ibrahim* da matarshi *Halima* rayuwa sukeyi cike da jin dad'i da kulawa, kwatsam tafiya takamashi zuwa Dubai d'auko kaya, a lokacin *Halima* tana d'auke da ciki na tsawon wata tara." Tun lokacin da ya fad'a mata tafiyar taji hankalinta be kwantaba, kullum idan yafita cikin kuka take domin ganin takeyi kamar idan ya tafi bazai dawoba." Idan yaga tana yawan tunani zai dinga kwantar mata da hankali a kan cewa, "tasanfa ba yanzun yafara tafiye tafiyeba kuma da yardar Allah yanda yaje lafiya haka zai dawo lafiya." Haka dai ya dinga kwantar mata da hankali har lokacin tafiyar yazo, Ana gobe zai tafi saida yasaya mata komai na haihuwarta, domin a koda yaushe tana iya haihuwa, Bayan yasaya mata komai kuma yafad'a mata sunan da yakeso a sanyawa abunda ta haifa, "idan mace ce, yana so sanya mata sunan mahaifiyar shi, *Ayshart* adinga kiranta da *Afnan*." idan kuma namiji ne yana son a Sanya mashi suna Abdullah." Kuka tafashe dashi, tana fad'in "Dan Allah Alhaji kadaina fad'in hakan, sai nadinga jin kamar wasiyace kake barmin, "Wlh duk tafiyar da kakeyi bantab'a shiga tashin hankali sama da wannan tafiyarba." Jawota yayi jikinshi yana fad'a mata kalamai masu dad'i da kwantar da Hankali." Ahaka dai har hankalinta ya kwanta tana murmushi har barci yazo yayi awon gaba dasu." Safiya na wayewa yashiga had'a kayanshi tana taimaka mashi, amma zuciyarta a dagule take, Haka tarakoshi b'an garin *Hajjah* domin yayi mata sallama." Bayan sungama sallama da Hajjah tayi masa fatan Alkhairi, anan ne yaciro wani zobe na azurfa mai kyau, a hannunshi yana murmushi ya mik'awa *Hajjah* yace "gashi ki ajiye a wurinki idan yarona ko yarinyar da za'a haifamin yakai shekara 12 ki sanya mata a hannuta, domin kinfini iya ajiya." Ta amshi zuben tana murmushi had'ida yimashi addu'a da Sanya mashi albarka, sukayi sallama gaba d'aya yatafi." Misalin k'arfe hud'u na yamma *Halima* na kwance a kan kujera taji ana sanarwa a gidan redio cewa "jirgin da yatashi zaitafi Dubai misalin k'arfe uku na rana, ansamu labarin yayi had'ari kuma rahoto yabada cewa duk mutanen da keciki babu Wanda yarayu." Batasan lokacin da tasaki wata kalar k'araba ta fad'i k'asa a some." Jin k'ararta da Hajjah tayi yasan yata yin saurin nufo b'angaren nasu domin ganin lafiya meke faruwa?" Da Sauri ta k'araso tana fad'in "lafiya Halima meke faruwa?" kike kuwa hakan?" Dakatawa tayi da tambayar ta, saka makon mugun labarin da taji ana sanarwa a gidan redio." Cikin tashin hankali da k'arfin hali, tayi kan Halima Wanda ke kwance k'asa a some ga tsuhun ciiki a jikinta." Cikin gaggawa takira direba suka tallabeta suka nufi asibiti da ita." Likitici suka dukufa kanta domin bata taimakon gaggawa, Dakyar akasamu ta sauka lafiya ta haifi 'yarta Mace, kyakkywa sak mahaifinta wani b'angare kuma tana kama da mahaifiyarta." Kuka ta fashe dashi, ta kamo hannu Hajjah ta dank'amata jaririyar a hannunta tace " Hajjah "gata ayi mata hud'uba da sunan da mahaifinta ya bar wasiya a nad'a mata, wato *Ayshart* *Afnan* Taci gaba da cewa "Hajjah ga Amanar *Afnan* nan a hannunki, nasan bazaki cutar da itaba, amma idan ta girma kibata labarin cewa mahaifanta na tsanin sonta, Domin nasan nima bazan tashi daga wannan rad'ad'in ciyon da zuciyata takeyi min ba, "Hajjah ki yafemin duk abunda nayi maki." idan kuma mahaifana suka zo amsar gaisuwata kice masu suyafe min." Tana kaiwa nan tadinga kalmar shahada anan take Allah ya k'arb'i abarshi😭 Hajjah taga tashin hankali wanda sai da tayi Neman hawaye amma ta rasa." Fita tayi rungume da Afnan ta kira likita, anan likita ya k'ara sheda mata Da cewa "sai dai hakuri domin *Halima* Allah ya karb'i abarshi." Haka direba ya d'auko gawar *Halima* ya kuma ya d'auko gawar Alhaji *Ibrahim* a kayi masu wanna lokaci d'aya, a kuma mak'abarta d'aya aka rufesu."😭 Bayan mutuwar nahaifan *Afnan* da sati biyu, saiga Alhaji Aminu yazo tareda 'yan sanda, sukayi sallama da *Hajjah* tafito." Tana fitowa taga 'yan sanda a tsaye a k'ofar gida, saida gabanta yafad'i amma ganin tare suke da Alhaji Aminu* sai taji sanyi tayi murmushi hankalinta ya d'an kwanta, domin yanzun Alhaji *Aminu* take gani kamar Alhaji Ibrahim." sai Tace " *Aminu* kaine kuma ka tsaya a waje kamar wani bak'o?" Kashigo daga ciki mana." Be tanka mataba sai dai yaba 'yan sandan umurni dasu shigo." Bayan sun zauna ne, Alhaji *Aminu* ya kalli *Hajjah* yace mata, "* Hajjah* munzo ne domin maganar dukiyar Alhaji Ibrahim, domin tun lokacin da zaiyi tafiya ya barmin wasiya da cewa wad'an nan bayin Allah, suna biyarshi miliyan arba'in, tareda gida uku wad'anda Dama be biya kud'in gidajenba." Sannan kuma "wannan gidan dakuke cikinshi da sauran gidajenshi guda biyu manlakina ne, domin tun kafin yatafi yasayar min kuma nabashi kud'inshi." "Kuma Munduba account d'inshi babu wasu kud'i a ciki illah miliyan shidda, duk ya tattara kud'inshi yatafi dasu Dubai kuma sai ga yanda ta Allah ta kasance dashi." Hajjah dake zaune rungume da Afnan tana barci, tunda Alhaji Aminu ya fara magana take kallonshi domin tasan ba gaskiya ko kad'an a maganarshi, domin duk abunda Ibrahim zaiyi sai yaneme shawararta idan ta amince ya aikata idan kuma bata aminceba bazaiyi aikata shiba duk yanda yakeson abun nan zai barshi." 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S* _we don't just entertain and educated we tauch the heart of the readers_ #WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM #IG PML WRITERS #https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035 #http://maryamsbello.blogspot.com *3* "Kallo *Hajjah* tabishi dashi cike da tuhuma, Sannan tayi k'arfin halin yimashi magana tace " "Amma *Aminu* kabani mamaki a tunanina ko wani kaji labarin zai cutarmu zakayi mana tsaye tsayen daka domin ganin ka karb'ar mana incinmu, Idan kayi dibo da irin haliccin da marigayi *Ibrahim* yayi maka, amma sai gashi abun mamaki kai da kanka za a had'a baki dakai a cucemu, domin a kwace dukiyar marainiyar Allah da k'arfi da yaji." Amma bakomai rayuwace dama duk Wanda kake ganin zai taimakeka wata rana shizai sanyaka a rana." Kuma kasani mutuwa nakan kowa, sai dai idan lokaci bayeba, kaima zatazo kanka, kuma nasan saikayi nadama a lokacin da bata da amfani." Tana kaiwa nan tafashe da kuka ta mik'e tsaye ta goya *Afnan* dake ta barcinta, Ta kuma kallon *Aminu* dake zaune ba abunda ke damunsa ko ajikinshi🤷🏻‍♂ Ta kuma cewa "ina sauran kud'in dasuka rage a account d'in nashi bayan angama biyan kowa bashinsa?" Ya mik'a hannu wurin 'yan sanda aka mik'o mashi wata jakar kud'i miliyan shidda ke cikinta, ya mik'awa *Hajjah* had'ida da cewa "wad'an nan kud'in su kad'ai suka rage a cikin dukiyar Alhaji *Ibrahim*." Tayi saurin d'aga mashi hannu tace "naji na kuma fahimta, Amma sai dai maganar tashi daga gidan nan ayi min hak'uri sai gobe zan had'a kayana sai na natashi." Wani kalar murmushi ya saki Alhaji *Aminu* had'ida sosa gemunshi, sannan yace "bakomai *Hajjah* ai da yau da gobe duk d'aya amma Dan Allah ki tabbatar da gobe zuwa k'arfe hud'u kintashi, domin inada buk'atar ayimin kyarekyare domin anan zandawo da iyalina." Bata tanka mashiba tayi shigewarta d'aki tana zubar da hawaye😭 Domin sai a lokacin ta kuma tabbatar da cewa tabbas Alhaji *Ibrahim* shine gatan ta." Safiya na wayewa tashiga had'a kayansu gaba d'aya, ta goya *Afnan* suka nufi tasha, tashiga mota sai Gombe." Gidan wani k'aninta ta sauka Wanda shi kad'ai ya rage mata a duniya, tayi mashi bayanin duk abunda ke faruwa ya kuma tausaya mata sosai, Anan tabashi kud'i tace "tanaso yasaya mata gida ma dai daici domin ta zauna taci gaba da renon marainiyar da aka barmata Amana." Haka kuwa akayi ansa marmata gida madai daici aka saya mata Wanda yanzun suke zaune a cikinshi, Sauran kud'inda suka rage kuma tadinga kasuwanci tana samun kud'in da zata dinga yiwa *Afnan* buk'atocinta na rayuwa." Haka rayuwa taci gaba da tafiyar masu yau dad'i gobe k'unci, har Allah ya had'asu da wani mak'oci mai mutumci wato malam *Iron* mahaifin *Maryam* kenan." Tun tashin *Afnan* malam *Iro* yaji yana tausayinta kasan cewar yaji labarin mareniya ce bata Uwa batada Uba." Wannan dalilin ne yasa ya d'auki aniyar sai ya taimakawa rayuwarta domin duk Wanda yatai maki wani Allah zai taimakeshi." Ya had'ata tareda *Maryam* 'yarshi yasanyasu makaranta d'aya, Arabic da boko." ________________________________ *Afnan* da *Maryam* Allah ya had'a jininsu sosai Wanda idan d'aya zaici abinnci dole saida d'aya na nan." Tun tashin *Afnan* Allah yayi mata wata baiwa ta iya sarrafa computer domin ko a makaranta da zarar wani injin yasamu wata matsala ko computer cikin ikon Allah da zarar *Afnan* tasanya hannu to zaitashi, wannan dalilin ne yasanya makarantarsu suke alfahari da ita." Tasha samun kyautuntuka akan wannan gyaran da takeyi Wanda yasa malan *Iro* da *Kaka* sukejin dad'i sosai." Akwai wani lokaci a makarantarsu ta *Boko* anshirya bikin yaye d'alibai angayyato manya gari gwamnoni da sanatoci, taro yayi taro akunna jannareto domin kunawa mai girma gwamna famka yaji iska, ana tsaka da dirama jannareton ya tsaya haka kuma duk na'urorin da ake amfani dasu suma suka d'auke." Kowa yashiga mamakin lafiya?" Meke faruwa?" Anan take shugaban makaranta yaba fa umurnin akira mai gyara ya gyara sannan aci gaba da abunda akeyi." Ai kuwa mai gyara uku aka kira amma babu Wanda yayi nasarar gyaran na urar, sai can shugaban makarantar ya tuna da *Afnan* aikuwa da sauri aka shiga cikin d'alibai nemanta, Kasan cewar *Afnan* batason hayaniyar mutane sosai, kuma batason yawan magana shiya sanya ta komawarta cikin aji tayi zamanta tana karatu" Anan shugaban makarantar ya nemota yafad'a mata duk abunda ke faruwa, Murmushi tayi tace "bakomai Malam bara ni nagwada sa'ata, Allah yasa adace." Haka kuwa akayi tana sanya hannunta, tana tab'a wani abu saiga haske ya bayyana komai yatashi lafiya galau yafara aiki." Murna wurin malamai abun ba'a magana, Anan ne gwamna yace "ya d'auki nauyin karatunta har iya rayuwar ta." _______________________________ Haka rayuwa taci gaba da sakancewa *Afnan* kullum sai k'ara girma takeyi halittar jikinta na kuma koma sak mahaifiyarta wani zuben kuma mahaifinta, domin gaba d'ayansu kyawawa ne." Allah ya horewa *Afnan* farin jini Wanda da zarar tafita waje ko zuwa makaranta ne sai maza sunyita bibiyarta. Tun tana kuka *Maryam* na lallashinta har takai ta daina domin idan da sabo yakamata ta saba. Dan dai *Afnan* din ba mai yawan suruto bace, kuma batason damuwa, Namiji d'aya take tsayawa dashi suyi magana wato malam *Nura* koshi tun lokacin da yasamu labarinta ya tausaya mata matuk'a ya kuma d'auki niyar saiya taimaka mata a karatunta." A duk lokacin da taje makarantar Arabic Malam Nura shike mata karatu har sai yaga ta fahimta sosai sannan yake kyaleta, A haka soyayya mai k'arfe ta shiga tsakanin malam Nura da Afnan har sukayiwa kansu Alk'awarin aure.' _____//////////////_________//////_________ A yanzun Tunanin Afnan d'aya ne aduk lokacin da ta zauna shine Allah yacika mata burinta tayi karatu mai zurfi domin takwato dukiyarsu a hannun Azzalumi Alhaji *Aminu* ______________________________ A b'angaren *Bassam* kuma Yana komawa gida a guje yashigar da motarshi a parking space d'in harabar masarautar, dafe da kunci yafito motar, Bayi da kuyangi sai zuwa sukeyi a guje suna zubewa suna kwasar gaisuwa amma baya kulasu." Kai tsaye b'angarenshi yanufa aka bud'e mashi k'ofa yashiga kai tsaye saman wani katafaren gado yafad'a Wanda yaji bargo na more rayuwa." Fad'awa yayi rumda ciki dafe da kunci dai dai inda Afnan ta maareshi, Rufe idonshi yayi yana kuma tunanin fuskar Afnan a lokacin da tad'aga hannu ta kwad'a mashi mari." Wani murmushin mugunta yasaki a lokacin da yatuna da wani tsoho da yayi tsaye gabanshi yana fad'a mashi maganganu wad'anda da alama zaginshi yakeyi." Tashi tsaye yayi domin mayen giyar yasakeshi, amma kuma babu abunda yafi tsaya mashi a rai ilah marin da wata 'yar matsiyata ta kwad'a mashi a fuska." Ya kuma girgiza kai yace "tabbas saina wulak'antaki wulak'anci mai tsanani, Saina ladabtar da wannan tsohon har saiya kai da rayuwarshi amma baya iya more mata." 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S* _we don't just entertain and educated we tauch the heart of the readers_ #WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM #IG PML WRITERS #https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035 #http://maryamsbello.blogspot.com *4* Mik'ewa tsaye yayi a fusace, yanufi b'angaren Maimartaba, Kai tsaya yashiga fada batareda da yajira anbashi iziniba, Domin idan da sabo fadawa masu gadin k'ofar fadar sun saba da halin Prince *Bassam* Kai tsaye yashiga fadar, yatarar da sarki kishingid'e yana diba jarida a hannunshi, ganin shigowar yarima *Bassan* yasan shi ajiye jaridar ya maida hankalinshi wurinshi, *Bassam* tsaye yayi ya hard'e hannuwa had'ida sunkuyar da kansa k'asa alamar baya da niyar magana." Maimarta na ganin hakan ya fahimci cewa rayuwarshi a b'ace take, Amma bazai masa maganaba har sai lokacin da yagaji da tsayuwar da yakeyi ya zauna sannan yafad'i abunda ke tafe dashi." Dan haka shima yabishi da ido yana kallonshi " Ganin Maimartaba baya da niyar tambayarshi abunda ke tafe dashi kamar yanda yasaba a duk lokacin da yaganshi ya shigo fadar, Yasanya shi, d'aga kansa domin suyi ido biyu da shi, Saima gani yayi Maimartaba yaci gaba da karatun jaridarshi." Ransa ya kuma b'aci ya juya hard'e da hannu ya fita." Maimartaba na ganin fitarshi yayi murmushi irin nasu na manya, yace "idan kamatso kaine mai dawowa kayi magana da bakinka." *Bassam* nafita kai tsaye d'akin *Fulani* yashiga domin duk a cikin matan sarki da ita kad'ai yake shiri." Kai tsaye yashiga d'akin *Fulani* batare da sallama ba, ya Tarar da *Fulani* tare da wata mahaukaciya mai suna *Rabi* wadda ta taimaketa ta nema mata magani kuma ba laifi sauk'i ya soma samuwa gareta, *Fulani* Nayi mata tsifar kai." Tana ganin *Bassam* yashigo cikin yanayin b'acin rai, *Fulani* ta b'ata fuska tace "meke damun *Yarima* mai jiran gado,? Waye ya tab'a d'an sarki mai takalmin k'arfe yanzun hukunci ya hau kansa kowaye shi?" *Bassam* yaji dad'in kirarin da *Fulani* tayi masa." ya kuma hard'e hannuwansa sannan yace " *Fulani* meye hukuncin Wanda ya mare d'an sarki?" Sai *Rabi* mahauciya tayi karab, tace " idan mace ce ka aureta kawai karama marinka saika saketa, ta tuntsire da dariya." *Bassam* yaji haushin maganar *Rabi* sosai, Tsawa ya daka mata wadda sai da tayi saurin zabura tare da k'ank'ame jikinta, sannan yanuna mata hanyar waje yace "tashi kifita, mahaukaciya kawai masu hankali na magana kina Sanya masu baki." Da sauri ta mik'e ta fita tana sosar kai." Ya maida kallonshi ga *Fulani* batare da yayi magana ba, alamar ita yake sauraro." *Fulani* tace " duk Wanda k'addara ta aikeshi ya sanya hannu ya mari d'an sarki, to tambas hukunci ne zai hau kanshi mai tsanani, Domin za'a tura fadawa a d'aukoshi ko waye shi, akaishi gidan horo a yimashi horo mai tsanani had'ida azabtarwa mafi muni a gareshi." Murmushin mugunta yayi, had'ida sosa gyamonshi, yace "Nagode *Fulani* sannan yafita daga b'angarenta." ________________________________ *Waye Bassam*?" *Bassam* kenan d'an sarki mai takalmin k'arfe." Shikad'ai ne d'a namiji a wurin sarki *Ahamad Moh'd Gombe* dan haka yake taka kowa yanda yakeso a gari." Mahaifiyar *Bassam* Hajiya *Hadiza* uwar gidan Sarki, Allah yayi mata rasuwa tun a wurin haihuwar *Bassam* wannan dalilin ne yasanya Sarki ya d'auki son duniyar nan ya d'orashi a kan *Bassam* kuma shine d'anshi namiji wadda zai gaji kujerarshi." _______________________________ *Sarki Ahmad Moh'd* shine sarki na bakwai a hawa kujerar sarautar *Gombe* shima ya gaji sarautar ne a wurin mahaifinshi, Sarki *Ahmad* sarkine mai adalci mai taimakon tala kawanshi, tun lokacin da ya hau kujerar sarautar jama'ar gari suke murna da farin ciki domin babu abunda talaka zai nema ya rasa, a yanzun a masarautar *Gombe* Masarautar *Gombe* tana da wasu gundun tarihi mai yawan gaske wanda tun sarki na d'aya da ya sauka akan kujerar mulki, sakamakon ciyo da yasameshi, Shine kad'ai yasan sirrin tafiyar da mulkin masarautar, kuma shi kad'ai yasan kaddarori da dukiyar masarautar take dashi." Kamin ya mutu sai da Ya bar wasiya da cewa "idan ya rasu, duk Wanda zai hau kujerar sarautar mudun idan ba Dan *Allah* zaiyi mulkiba akwai wata manufa a zuciyarshi to tabbas babu wani Abu da zai kuma amfani a cikin masarautar har sai lokacin da akasamu sarkimai adalci sannan masarauta zatadawo dai dai, Ya kuma nuna wani *Tambari sarautar* dake lik'e a cikin fadar masarautar, kamar agogo shiba kuma computer ba, Amma yanaso yayi kama da agogo sai dai yafi agogo girma sosai, Sannan yanuna wasu na'urori masu kama da computer dake ajiye a cikin wani d'aki Wanda ba Wanda ke shiga d'akin sai shi sarkin." yaci gaba da cewa "wad'an nan dakuke gani bayan na mutu idan adalin sarki ya hau kujerata, to sune zasu nuna mashi irin k'undin tsarin mulkin masarautar nan, kuma sune zasu nuna mashi iya dukiyar da masarautar nan ta mallaka da duk wani Abu da yakeso yasani game da sarauta." "Amma kusani duk sarkin da zaiyi mulki in har bada niya zuciya d'aya zaiyi mulkiba toko shekara nawa zaiyi bazasu tab'a amfaniba in har bada zuciya d'aya zaka mulki al'umma ba." Yana kawowa nan yayi shahada ya rasu." Hakan kuwa akayi bayan rasuwar sarki na d'aya, duk sarkin da ya hau kujerar mulki, sai yayi ta Neman *Tambarin sarauta* yatashi domin yasan iya dukiyar da masarauta ta mallaka Dan yasata yayi abunda ya ga dama dasu, amma tambari bazai tashiba." Koda sarki na hud'u ya hau kujerar mulkin, komai sai ya kuma lalacewa domin har gwala gwalai da zinari da a kayiwa fada ado dasu, suna bada haske gwanin ban sha'awa yana hawa kujerarshi komai ya tsaya suka daina bada haske." Kowa mamaki yashigayi, aikuwa hankalin sarki na hud'u ya tashi, yatura fadawa k'asar waje "duk inda mai gyara yake azo mashi dashi ya gyaramashi har *tambarin sarautar* zai biyashi ko nawane." Haka kuwa akayi, ankira masu gyara k'asa k'asa amma babu abunda ya sauya." Anan sarki na hud'u yaba da umurnin duk wani jinin sarautar *Gombe* yana buk'atarshi da ya dinga amfani da photon *Tambarin sarauta* a riga ko a hula, ko agogo?" Bayi da kuyangi kuma bayan rigarsu aka zana masu k'aton photo *Tambarin sarauta* Maza kuma har hular Kansu tana d'auke da photon *Tambarin* Wannan dalilin ne yasanya duk inda akaci karo da photon *Tambarin sarauta* ajikin wani to basai ka tambayaba kasan jinin masarautar *Gombe ne* Tun daga sarki na biyu har zuwa sarki na bakwai *Tambarin sarauta* be kuma tashiba, sai duk Wanda ya hau kujerar mulki saiya d'auko masu gyara domin yagwada sa'a ko zaitashi amma ko alama babu, Har zuwa sarki na bakwai wato sarki *Ahmad moh'd,* mahaifin *Bassam* kenan Wanda shi kwata kwata kujerar sarauta bata gabanshi, asalima ba da son ranshi aka nad'ashi sarautarba sai Dan mutanin gari sun zab'eshi kuma yayi alk'awarin tunda suka zab'eshi shima zai faranta masu kowanensu sai sunyi dariya bazasuyi kuka dashi." *wash hannuna nagaji kuzo muje zuwa masoyana* *ummu safwan CE* 07066214433 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S* _we don't just entertain and educated we tauch the heart of the readers_ #WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM #IG PML WRITERS #https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035 #http://maryamsbello.blogspot.com *5* *Alhaji Ahmad Moh'd* yana da mata hud'u mahaifiyar *Bassam* Itace uwar gida, Sarki na matuk'ar sonta domin tsayuwa da ta a kan gaskiyarta, Sannan ta biyu kuma sunanta Amina sai zainab da kuma Maryam, dukansu babu Wanda Allah yabawa haihuwa, kullum addu'a sukeyi "Allah yabasu ciki su haihu, su kuma haifi d'a namiji domin ya gaji sarautar mahaifinshi." kwatsam saiga Hajiya Hadiza uwar gidan sarki Allah yabata ciki, Lokacin da tasamu ciki, murna a wurin Sarki abun ba'a magana, ya kuma d'auki son dukiyar nan ya d'orashi a kan abunda zata haifa, yin hakan ya kuma sanyawa abokanin zamanta k'iyayyarta da abunda ke cikinta." Hajiya Hadiza macece mai hak'uri da sanin ya kamata, duk abunda za'ayi mata bazata tab'a d'aga kai ta kalli mutum ba bare ta nuna rayuwarta ta b'aci." Irin wad'an nan halayen nata ne, sarki yake masifar sonta." Cikinta ya kai wata tara, likitoci suka tabbatar mata da cewa "d'a miji zata haifa, Ai kuwa Sarki yadinga murna, saboda jin dad'i be iya b'oye farin cikinshi ba, ya dawo gida ya tara matanshi gaba d'ayansu yake shaida masu abunda likita ya fad'a, cewa "Da namiji Hajiya Hadiza zata haifa, dan haka sutayashi da addu'a zai samu magaji." A zahiri sun nuna farin cikinsu, a zuciyarsu kuma babu wanda ya kaisu bak'in ciki musamman ta uku Hajiya Zainab domin duk tafiso bala'i da tungo a gidan." Ta d'auki d'amarar cewa "indai tana da rai da lafiya, Hajiya Hadiza bazata haifi d'a namiji a gidan nan ba." Aikuwa ta tashi tsaye ta dinga shiga bokaye da malamai domin ganin an salwantar da cikin Hajiya Hadiza." Kwatsam wata rana nak'uda ta kama Hajiya Hadiza, hankalin Maimartaba ya tashi sosai, yakira likita cikin gaggawa domin ya taimaketa." Tun 12:am take nak'uda itace bata haihuba sai 12:pm nasha wahala sosai, tana haihuwa tace ga garinku nan ta rasu." Sarki yaji mutuwar uwargidanshi mace mai hak'uri da dantako, kuka yakeyi sosai kamar k'aramin yaro." Haka akayi mata sutura aka kaita gidanta na gaskiya." Hajiya Zainab kuma tayi bak'in cikin mutuwar Hajiya Hadiza ita kad'ai batare da abunda ta haifaba, ta kuma d'auki alwashin mudun tana raye aduniya saita ga bayan *Bassam* a doron k'asa." Haka rayuwar Bassam taci gaba da tafiya a hannun jakadiya itake renonshi take mashi wanka, gaba d'aya dai ita ke d'awainiya dashi." Sannan kuma tunda ta fahimci burin Hajiya Zainab shi taga bayan *Bassam* a koda yaushe sai ta yimashi addu'ar tsari ajikinshi, domin *Bassam* kyakkyawane bafulatani ne, sak mahaifiyarshi ya biyo." Girma yakeyi sai k'ara kyau yakeyi, duk inda ya gifta mutane sai maganar shi akeyi, gashi da saurin sabo, da fasaha, idan yafad'i wata magana saika d'auka fad'a mashi ita akayi, Allah ya horewa *Bassam* saurin fahimtar abu tun yana k'araminshi." Wanda hakan ne yasa ya kuma shiga ran sarki, yanaji dashi sosai." Wanda ita kuma Hajiya Zainab a kullum tana wurin boka neman maganin da zai raba *Bassam* da duniyar gaba d'aya." Ita kuma Hajiya Amina ta zubar da makaman k'iyayyarta ga *Bassam* burinta d'aya ne Allah yabata ciki itama ta haifi nata d'an namiji." Inda itama Hajiya maryam tun lokacin da mahaifiyar *Bassam* ta rasu Allah ya d'ora mata son *Bassam* a rayuwar ta." Gaba d'aya renonshi yadawo a hannunta abunda ke rabasu da *Bassam* barci, domin wurin jakadiya yake kwana." Duk abunda ke faruwa a gidan sarki yana sane dashi, yana kuma lura da duk wani mai kyautatawa *Bassam* da mai musguna mashi, Yana kuma jin dad'in irin yanda Hajiya Maryam ke nuna kulawarta ga *Bassam* kamar itace ta haifeshi, wannan dalilin ne yasanya yabata matsayin marigayiya na *Fulani* Cikin kwana uku aka d'ata a matsayin *Fulani* Nad'inda yafi yiwa Hajiya zainab bak'in ciki arayuwa domin d'aki tashiga tadinga kuka kamar wadda uwarta ta mutu." ________________________________ *Bassam* na kammala secondry a lokacin yanada shekara 16, Maimartaba ya turashi England karatu domin yana lura da Hajiya Zainab a kullum burinta d'aya taga bayan d'anshi tilo d'aya." Tafiyar *Bassam* England karatu da abota da k'awaye yasan yashi ya fara shaye shaye da Neman mata, amma ko mace mako wace yake ma'amala da itaba sai mai aji." Domin *Bassam* akwai aji, ga kuma kud'i, domin maimarta a koda yaushe cikin turo mashi kud'i yake a account d'inshi kuma yamashi gargad'in cewa "karya kuskura yadawo Nigeria har sai ya kammala karatunshi gaba d'aya," Domin a ganin Sarki wannan kariyace yake mashi daga shairin Hajiya Zainab." Shine bedawo gida Nijeria ba saida ya kammala degree d'inshi da masters, sannan Sarki ya bashi umurnin yadawo k'asarshi." A lokacin sai Maimartaba ya gina mashi b'angarenshi ya kuma bashi umurni da cewa "duk wanda be yarda dashiba, to karya bari yashigar mashi b'angare." lokacin da yadawo gida Nigeria *Bassam* ya girma sosai yazama namijin gaske, gashi da gwarjini a fuska da kuma rik'on addini, Domin duk wanda yayi ido biyu dashi sai yaji shayin ya tunkareshi, saboda ba wasa a fuskarshi." Sarki nason *Bassam* sosai domin ya yaba da hankalin shi da kuma tarbiyar shi, Domin a tunanin sarki, *Bassam* ko goro bayaci bare azo ga giya." Wanda shima yake kiyaye duk wata hanya da zai sanya sarki ya fahimci wata b'araka ko rashin tarbiya daga gareshi." sai dai idan dare yayi yaja motar shi yanufi club yasha giyarshi ya holewar shi da 'yan matanshi, sannan yadawo gida babu wanda yasani." Shinefa bayan yadawo daga club d'in a buge yabiyo ta unguwarsu *Afnan* har yaci karo da ita tadawo daga islamiya, cikin maye yaga tayi mashi kama da budurwanshi *Basma* yanemi ya fad'a mata." Wannan kenan." _________________________________ Tafiya yakeyi yana sak'e sak'en a zuciyarshi irin hukuncin da zai d'aukarma *Afnan* tareda wannan tsuhun Wanda yake gani kamar mahaifinta ne, Murmushi mugunta yayi a zuciyar yace " idan nasanya aka d'aukomun wannan tsuhun hukuncin da zanyi mashi sanyawa zanyi a gutsire mashi wannan k'azamin hannun nashi, da yanuna ni dashi." Yana daf da shiga b'angarenshi yaji ana kwala mashi kinashiga nesa, Dajin muryanta ya gane ko wacece, Hajar ce, d'iyar k'aunar Hajiya zainab datake mutuwar sonshi, shi kuma a duniyar nan babu abunda ya tsana kamar Hajiya Zainab da duk wani Abu da yafito daga hannunta, Bai juya ba, be kuma tsayaba, yayi shigewar shi b'angaren shi." Tana zuwa daf da k'ofar b'angaren nashi taja burki ta tsaye, domin tasan duk fad'in gidan babu Wanda yake gigin shigar mashi b'angaren daga Sarki sai *Fulani* sai kuma jakadiya." Bayan wad'an nan babu wanda ya isa yashigar mashi b'angare, koda sarki ne ya aikosu." Dashi garshi d'akin nashi kai tsaye toilet ya fad'a domin yin wanna." shiri yakeyi babu abunda yake gani sai fuskar *Afnan* lokacin da tasanya hannu ta mareshi, Idonsa suka rikid'e sukayi jajir, da Sauri ya d'auki key d'in motarshi yanufi unguwarsu *Afnan* 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S* _we don't just entertain and educated we tauch the heart of the readers_ #WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM #IG PML WRITERS #https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035 #http://maryamsbello.blogspot.com *6* Tafiya sukeyi sai fira sukeyi mai dad'i, *Afnan* tareda masoyinta malam *Nura* Daga makaranta tafito, shine yayo mata rakiya zuwa gida, Domin yanada labarin duk abunda yafaru tsakaninta da prince *Bassam* Kasan cewar yau *Maryam* bataje makarantarba saka makon ciyon kai da take fama dashi." Firar su, sukeyi ta masoya kwanin ban sha'awa duk wanda ya gansu yasan suna cikin farin ciki kuma sona son junansu." Anan ne malam *Nura* ke shaida mata da cewa "da zarar yadawo Madina karatu, gaskiya ya gaji da zama ahaka zaije yayiwa *Kaka* magana a gaggata yin auren su saboda gaskiya yaga nawar su mallaki junansu." *Afnan* dariya tashigayi had'ida rufe fuska cike da jin kunya." Karya kwanan da zasuyi da zata kaisu gida, tafiya sukeyi cike da farin ciki." *Bassam* kuma da tun d'azun ya iso, unguwar, gaba d'aya gidansu *Afnan* ya b'ace masa, Sai dai yasamu wuri yayi parking d'in motarshi a gefen unguwar, yafito sanye da wani bak'in glass a fuskarshi, ya haye kan mota ya zauna cike da b'acin rai, yana kallon duk mai wanda ya wuce d'aya bayan d'aya." A can ya hango *Afnan* tare da malam *Nura* sun karyo kwana." Wani tsalle yayi ya doro kan motar, yanufesu, Gabansu ya tara ya tsaya yana k'are masu kallo d'aya bayan d'aya." *Afnan* na ganinshi sai da gabanta ya fad'i, amma ta dake, ta kalli malam *Nura* tace "ya Sayyadi ka barni daga nan ka koma gida ko." Kallonta malam *Nura* yayi had'ida murmushi, sukayi kamar basu lura da prince a wurin ba, yace "a'a mutafi kawai na k'arasa dake gida Gimbiyata." Rab'a *Bassam*sukayi, har sun d'an gotashi kad'an Saiji tayi anjanye mata hijabi, saida tacire gaba d'aya, yana fad'in ke 'yar matsiyata, ina matsiyacin ubanki yake, yau sai kunyi nadamar abunda kuka aikatawa yarima d'an sarki." Zan nuna maku Ku matsiyata ne, kuma talaka wa, dake da mahaifinki nayi alk'awarin saina azabtar daku, a zaba mai tsanani." Afnan ranta idan yayi dubu ya b'aci idonta ya cika da hawaye batasan lokacin da ta d'aga hannu ta kwad'a mashi mari, a karo na biyu, tana magana tana kuka tana fad'in "kai wane irin dabbane wanda bakasan darajar d'an Adam ba, anfad'a maka mulki hauka ne ko sarauta haukace to kasani Allah yana tare damu." Kallo *Bassam* yabita dashi dafe da kunci, cike da mamaki." Saiji yayi malam *Nura* na fad'in "good *Afnan* kinburgeni, wannan shine hukuncin da ya dace ki d'aukarwa azzalumi irin wannan." Ya duk'a ya d'auko mata hijabinta yabata tasanya, sannan ya kuma kallon *Bassam* yace "idan ka isa, kasanya bindiga ka harbemu mubar duniyar idan katashi." Suka rab'a ta gefenshi sukayi tafiyarsu." *Bassam* tsaye yayi yana kallonsu domin yanzun abun mamaki yake bashi, kallo yabisu dashi beyi mgnaba, har *Malam Nura* ya kaita gida, sukayi sallama ya juyo ya dawo." Ta gaban *Bassam* ya rab'a ya wuce *Bassam* betan kashiba, saida yayi nisa sosai sannan *Bassam* yabishi a baya, saida yaga gidan da yashige sannan ya juyo, Yashiga motarshi da k'arfi ya figeta, ya fita a unguwar ranshi a b'ace." Kai tsaye club ya nufa yasanya akayi masa odar giya, sai d'aga kwalba yakeyi yana shan yewa yana jifa da gwalbar gefe, saijin k'arar fashewar kwalma mutane keji ba halin ayi masa magana, Amma darar ka ganshi kasan a cikin b'acin rai yake." duk abun nan dayakeyi *Basma* na gefe tana kallonshi tana zubar mashi da hawaye domin Allah yajarabeta da masifar sonshi." ganinshi datayi cikin wannan yanayin ne yasan yata bata tunkaroshi ba domin tasan halin *Bassam* sarai mudun yana cikin b'acin rai tanufo shi domin ta lallasheshi, to a ranar zataci dukan tsiya, saita rasa wadda zai taimaketa, gata Kuma Allah ya d'ora mata masifar sonshi kamar ta had'iyeshi takeji." Ganin shi tayi ya kuma d'aukar kwalba ta 5 zai kai bakinshi, tayi saurin zuwa gabanshi da d'an gudunta, ta rik'e mashi hannu idonta cike da hawayen tausayinshi, tace haba " *Bassam* meye hakan kake aikatawa?" Kadiba ga ganifa, kwalba ta biyar kenan kake Neman shanyewa, meyasa kake neman b'ata rayuwarka a wurin giya?" Pls *Bassam* yi hak'uri ajiye kwalbar, tana amsar kwalbar ya mik'e tsaye cikin maye yana kallonta saiji tayi ya d'auketa da mari har sau biyu, Yana fad'in ni zaki Mara?" Waye ke?" Waye ubanki?" A fad'in duniyar nan?" *Kuyi hakuri da wannan*, *ummu safwan* 07066214433 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S* _we don't just entertain and educated we tauch the heart of the readers_ ________________________________ #WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM #IG PML WRITERS #https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035 #http://maryamsbello.blogspot.com 🍔🍔🍔🍔🍔🍔🍔🍔🍔🍔🍔🍔🍔🍔🍔🍔🍔🍔 *Happy Birthday Faty Azland Allah yasanyawa Rayuwarki Albarka, ya k'aro shekaru masu Albarka*🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂 *7* "Tsura mashi ido tayi dafe da kunci tana mai zubar da hawaye, Ganin zai kuma tunkarota alamar zai hauta da duka yasanyata yin saurin ja da baya tana zubar da hawaye." Wurin wasu samari tanufa dake cikin club d'in, suna shek'e ayarsu, Tayi masu magana tace "Dan Allah su taimaka mata, su rik'o mata *prince Bassam* su shigo mata dashi Rom 12 ko nawa ne zata biyasu." Jin kud'i yasa samarin yin wata irin shewa, sukace "angama Baby *Basma* bakida matsala indai wannan ne." Cikin dabara suka rik'o " *Bassam* dayasha giya tayi mashi over suka sanyashi a d'aki had'ida kwantar dashi a kan kado." Kud'i ta d'ebo a jaka Wanda itama kanta bata San ko nawa neba, ta dank'a masu a hannunsu, murna suka shigayi suna k'ara jinjina mata sannan suka fita." Wurin da aka kwantar da *Bassam* tanufa kwance yake yayi d'aid'ai akan gado barci mai nauyi yayi awon gaba dashi, tashiga zage mashi talkamin dake sanye a k'afarshi, ta kuma gyara mashi kwanciya had'ida lullub'eshi da bargo, ta tsura mashi ido tana kallonshi cike da so da k'auna, ita dai a duniyar nan babu abunda takeso sama da *Bassam*." Ahaka tasanyashi a gaba tana kallonshi had'ida shafa gefen fuskarshi har barci b'arawo yayi awon gaba da ita." ________________________________ *Afnan* nashiga gida kai tsaye d'akinta ta nufa, ta fad'a kan katifarta, tashiga rusar kuka, tana tuna irin wulak'ancin da *Bassam* yayi mata yacire mata hijabi a gaban bainar jama'a, me Tatare mashi a rayuwa, meta yimashi? Hasalima bata tab'a ganinshi ba, kuma bata tab'a ganin fuskarshiba amma yakeso yashiga rayuwarta domin ya tuzartata, Dan yaga bata da gata, Ta kuma fashewa da kuka tana fad'in "gatana shine Allah kuma nasan zai taimakeni ya kuma tsaremi ga dukan Wanda keso yaga ya tuzartani." *Kaka* dake tsakar gida tajiyo sautin kukan *Afnan* da sauri tanufo d'akin tana fad'in *Afnan* lafiya meya sameki kike kuka hakan?" *Afnan* tayi saurin goge hawayen fuskarta tace "bakomai *Kaka* kaina ne kiyimun ciyo sosai." Da sauri *kaka* tace "Subahanallahi." tashiga d'akinta ta d'auko mata maganin ciyon kai, had'ida d'ebo mata ruwa tabata tasha, had'ida tufeta da Addu'oi sannan tace "ki d'an kwanta *Afnan* zuwa ajima zakiji ciyon yasakeki kuma kidaina kuka kidinga addu'a saikiji sauki yazo maki." *Afnan* tayi murmushin k'arfin hali tace "na daina *kaka* Allah yak'ara maki tsawon rai da lafiya." Kaka tayi murmushi tace "Amin *Adman* yar gidan *kaka*." ______________________________ Hankalin Marmartaba yatashi matuk'a *Bassam* be kwana a gidaba, duk inda ake tunani yana can, andibashi babu labarin shi, idan aka kira wayarshi a kashe akejinta." Anan take hankalin masarauta yatashi ko ina anbaza fadawa sun tafi nemanshi." Hajiya *Zainab* kuma sai murna takeyi tanajin dad'i tana kuma k'ara addu'ar Allah yasa ya b'ata bacewa ta har abada, dama ko be b'aceba ta k'arb'o wani magani Wanda yau d'in nan zata sanya mashi a abinci da zarar yaci sai dai wani bashi ba." To kuma saigashi an hutar da ita yama b'ace gaba d'aya, Allah yasa kar a ganshi." Agaban maimartaba kuma tafi kowa nuna bak'in cikin rashin ganinshi da ba'ayiba domin har kukan muna furci takeyi." *Fulani* kuma kallonta kawai takeyi domin tasan halin Hajiya *Zainab* sarai macece makira mai tsananin mugunta matuk'a." Farkawar da *Bassam* zaiyi ya Ganshi rungume a jikin *Basma* tana barci, kallo yabita dashi, yana tuna abunda yafaru dashi jiya, Sauri yayi yashafa gefen fuskarshi inda *Afnan* ta mareshi, ranshi ya kuma b'aci, Ya kuma yadiba a gogon hannunshi yaga 8:am ya tuna a nan kenan ya kwana, A hankali ya kwantar da *Basma* domin karta tashi, Ya ayyana a zuciyarshi cewa "duk inda maimartaba yake yasan yanzun hankalinshi na can atashe rashin ganinshi da beyiba." A hankali ya sauko daga kan gadon, yasanya talkaminshi had'ida d'aukar key d'in motarshi yafito yanufi gida." Ta unguwar su *Afnan* yabi aikowa yayi sa'ar tafito tanye da uniform zata makaranta, malam *Nura* na rik'e da jakarta suna tafiya cikin nishad'i Tagabansu yawuce ya fige mota da k'arfi gaba d'aya ya wanke masu jiki da ruwan kwata yayi tafiyarshi." 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S* _we don't just entertain and educated we tauch the heart of the readers_ _____________________________ #WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM #IG PML WRITERS #https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035 #http://maryamsbello.blogspot.com *8* Tsaye *Afnan* tayi tsamo tsamo jik'e da kwata, haka shima malam *Nura* gaba d'aya jikinshi har fuskarshi duk ya b'aci da kwatar, kallon ta kuma bin malam *Nura* dashi cike da tausayin shi domin tasan itace silar janyo mashi wannan wulak'ancin hakan." Idonta cike da hawaye tace "Dan Allah Ya sayyadi kayi hak'uri nasan duk a sanadiyata hakan ta faru da kai." D'aga mata hannu yayi yace "kidaina bani hakuri *Afnan* nasan abunda *Bassam* yake nufi dake, kuma nayi alk'awari indai akankine nafiso narasa Rayuwata wurin kare maki mutuncinki." Ya mik'a mata jakarta littafanta yace "ki koma gida kiyi hak'uri da zuwa makarantar a yau kibari sai gobe kitafi, Ta k'arb'i jakar tana mai zubar da hawaye." A nan sukayi sallama suka rabu da juna kowane daga cikinsu ranshi a b'ace yake musamman *Afnan* da aka wulak'anta mata masoyi da ruwan kwata, Domin ita bata tunanin kanta saboda tasan bata batada gata abunda yafi wannan ma zai iya faruwa da ita." Koda tashiga gida, tsamo tsamo jike da kwata, *Kaka*ta rafka Salati cike da kulawa tace *Afnan* meyafaru hakan naga jikinki duk yajik'e da kwata?" Ta k'ak'aro murmushin dole tace "muna tafiya tareda ya Sayyadi domin ya Samar min abun hawa, saiji nayi na fad'a kwata.* *Kaka* tace "Subahanallahi, to Allah ya tsare gaba wuce kishaga ban d'aki, kicire kayan jikinki sai kiyi wanka, kin arziki da bakiji ciyoba." __________________________________ *Bassam* kuma ranshi ya d'anyi mashi dad'i, domin ko ba komai yasan ya bak'anta masu rayuwa a yanda yagansu cike da farin ciki." Wani dogon nishi yaja adaidai lokacin da zai shigar da motarshi get d'in gidansu, ya tuna da lokacin da *Afnan* take furtawa wannan ustazun saurayin cewa "nagode ya Sayyadi ka barni a nan na iyar da k'arasawa da kaina." Har wani murmushi take masa, shima hakan, wato da ala masoyane kenan kuma alamu yanuna suna tsananin son junansu matuk'a." yayi wani murmushin mugunta, sannan yayi parking d'in motarshi yafito." Babu Wanda yaga shigowarshi domin gaba d'aya hankalin kowa a tashe yake na rashin ganinshi da ba'ayiba, Bebi takan kowaba kai tsaye b'angarenshi yanufa, a cewarshi sai yayi wanka sannan yatafi wurin Maimartaba yasan k'aryar da zai shirya mashi na rashin kwanan da baiyi a gidaba jiya." Kai tsaye d'akinshi yanufa, fadawa da kuyangi masu kula da komai nashi na rayuwa, suna ganinshi cike da murna sunata zubewa k'asa suna kwasar gaisuwa had'ida yimashi kirari." Ba laifi ya d'an saki fuska ya amsa masu sab'anin ya yanda yake masu." Sannan daga k'arshe yaja masu kunne da cewa "kar Wanda yafad'awa sarki cewa yadawo har sai ya kintsa ya huta sannan ya kai kansa fada." Cike da girmama suka amsa da "angama yarima Allah ya taimakeka ya tsare mana lafiyarka." Sannan kowa ya watse yanufi inda yake aikinsa, Ashe tun lokacin da yarima yashigo gida, akan idon Hajiya Zainab, tayi bak'in ciki matuk'a da yadawo batare da ya b'ace b'at ba." tacije Baki tace " tunda kadawo baka b'ataba, ni bari Nazo nak'arasa da kai lafira matsiyacin yaron mai taurin ran tsiya." duk maganun nunkan da nake k'arbowa babu wanda yatab'a yin tasiri a kan wancan tsinanin yaron, bari naje nakwada wannan nagani boko yabani tambacin mudun yaci abincin da aka zubashi a ciki to sai dai wani bashiba." Tamik'e tanufi b'angaren nashi." Dashigar shi d'akinshi, kai tsaye kan makeken gadonshi ya fad'a, yayi ale,ale fuskarshi na kallon silin, babu abunda yake tunani sai hanyoyin da zaibi yaga ya wulak'anta Aljanar yarin can, a yanda yake cewa *Afnan* burinshi ya wulak'antata ya musguna mata yaga ya hanata farin ciki a doron k'asa." Tunawa yayi dayaga yanda Malam *Nura* ya rik'o mata jaka suna tafiya cikin nishad'i ko ba'a fad'aba kasan masoya ne, Sai maganar Maryam mahauciya ta fad'o mashi a rai datace "ka aureta idan karama marinda tayi maka saika saketa." Yaja dogon tsaki yace "No Allah ya tsareni na auri zuri'ar Aljanu, Wata zuciyar kuma tace "aiba sonta kakeyiba, idan ka aureta ka wulak'antata da ita duk wata zuri'arsu, saika saketa ka kuma koresu gaba d'aya a garin, yanda zaka manta da tarihinta a doron k'asa." Ko bayan haka, idan ka aureta ai karabata da masoyinta, yin haka kuma ba k'aramin bak'in ciki bane kadasawa rayuwarsu, ko ba komai kasanyasu cikin k'uncin da bak'in ciki rabuwa da masoyi." Murmushin mugunta yayi yatashi ya fad'a toilet domin yin wanka." Hajiya Zainab kai tsaye tanufi b'angaren *Bassam* Fadawan dake gadin b'angaren nashi, suka bita da kallon tuhuma." ganin da tayi suna mata kallon tuhuma ne, yasan yata, tayi saurin wayan cewa da cewa " *Bassam* ne yanemi tazo domin zasuyi wata magana ne." Suka bata hanya tawuce, shigarta pollon taci karo da me kula da abincinshi d'auke da tiren abin da yabata umurni ta had'a mashi kafin yafito daga wanka." Hajiya Zainab tasanya hannu ta k'arb'i abincin tace "bara nashigar mashi dashi, ina tunanin wanka yakeyi, tamik'a mata tiren abincin itama ba dan ranta yasoba." Sand'a tashigayi ta bud'e k'ofar d'akinshi taji saukar ruwa natashi da alama har yanzun wanka yakeyi be kammala ba." tayi murmushin mugunta, domin hakan yabata damar aiwatar da mugun nufinta gareshi." *Bassam* kuma wanka yakeyi saiji yayi motsi yayi yawa a pallonshi, Yayi saurin watsa ruwan a hankali, yasanya jallabiyarshi yanufi pallon dan ganin meke faruwa?" Tura k'ofar pallon yayi yaci karo da Hajiya Zainab a kan abincinsa, tana kulle wani Abu a Leda a hannuta, tana kuma neman tura ledar a zanenta, d'agowar da zatayi sukayi ido biyu dashi, tayi saurin wayan cewa had'ida fad'in "barka da fitowa Yarima mai jiran gado, jiya kasanyamu a tashin hankalin rashin ganinka baka kwana a gida." Murmushi yayi had'ida cije baki, yasamu kujera ya zauna yana kallonta, sannan yace "yauwa barka dai." Ganin kamar be lura da abunda ta aikata masaba, yasanyata taja wani dogon ajiyar zuciya tace "ga abincinka nan kaci mana nasan kana da buk'atarshi." Ya kuma kallonta yayi wani kalar murmushi na gefen baki, Yace "nagode Hajiya amma da alamar kamar ke kika shiryamin wannan liyafa hakan ko?" Tayi dariya jin dad'i tace " nice mana "Yarima d'an sarki kwaya d'aya tamkar da dubu, ai dole musoka mu kuma tarairayeka." Yace "Nagode Hajiya." Tace "ba damuwa, bara na zuba maka kaci, Bayan ta zuba mashi a plete tace "kaci mana, had'ida tura mashi a gabanshi." Ya kuma kallonta da kyau, yayi murmushi, yace "daina sauri Hajiya ci zanyi yanzun nan kuwa." ya nuna mata kujera a kusa dashi yace "zauna anan idan na kammala cin abincin akwai maganar da nakeso muyi dake." Cike da zak'uwa yayi yaci abincin ya mutu kowa ya huta, yasanya tayi saurin zama a kan kujerar da yanuna mata." Ganin ta zauna ne, sai ya tura mata plete d'in abincin a gabanta, yace "faraci sai nima naci." Cikin fad'uwar gaba tace "A'a Yarima ni a k'oshe nake kaci kawai kai kad'ai a shirya mashi, had'ida k'ara tura mashi plete d'in a gabanshi." Ya canza fuska ya koma mata *Bassam* d'inda tasani Wanda babu wasa a fuskarshi komai yana iya aikata mata a yanzun." Ya kuma tura mata da plete d'in gabanta yace "Hajiya saikin cinye abincin nan gabaki d'aya sannan zakifita a d'akin nan idan ba hakan ba to kasheki zanyi yanzun nan." 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S* _we don't just entertain and educated we tauch the heart of the readers_ _____________________________ #WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM #IG PML WRITERS #https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035 #http://maryamsbello.blogspot.com *9* Mik'ewa tsaye *Hajiya Zainab* tayi cike da tashin hankali a fuskarta, Amma sai ta wayance, ta kalli *Bassam* tace "bud'e idonka da kyau *Bassam* ka diba ka fahimci Wanda ke gabanka, harkake cewa saina cinye abinci ko kuma ka kasheni, Wato kana tunanin zan cutar dakai kenan ko?" Tabbas yau kanuna min cewa banice na tsugunna na haifekaba." Tsawa ya daka mata Wanda batasan lokacin da ta Kai zaune ba, Kallon fuskarshi tayi taga ya canza mata kamannin kamar ba *Bassam* d'in da tasaniba." Yace " *Hajiya Zainab* kinsan bana son yawan surutu, bare gardama, karki kuskura ki kuma bud'e baki kiyumin magana, batare da kincinye abincin da ke gabankiba." Idan ba hakan ba yanzun nan zan kasheki, in kuma kashe banza." Mikewa tsaye yayi ya jawo wata durowa, ya d'auko bindiga, ya saita mata ita saitin fuskarta yace zakici abinci ko sai na aikaki lafira yanzun." Jikin *Hajiya Zainab* ya soma rawa kamar mazari, sai zufa take fitarwa kamar ruwa, Ta shiga yimashi magiya tana fad'in "natuba *Bassam* kayafemin, ka d'auki ko wane irin mataki a kaina, batare da naci abincin nan ba, wlh mudun naci abincin nan mutuwa zanyi, domin guba ce a cikinshi." A razane ya kalleta, yace "guba ce a ciki?" amma kikeso ni naci?" Wato burinki a duniya kiganni na mutu ko? Me natare maki a rayuwa da kikeson ganin bayana tun ina k'aramina?" to yau wasa ta kai k'arshe tsakanina dake, domin idan baki kasheniba ni yanzun ni zankasheki, da kuma abunda kikayi niyar kasheni dashi.' Ya kuma saita bindigar a goshinta yace "zakici abincin ko saina k'arasa dake lafira." Fitsari tasaki, jikinta na rawa, tarik'e mashi k'afa tana kuka tana magiya." D'aga bindigar yayi ya harbi sama, k'arar kukan bindingar ya gauraye gidan sarautar gaba d'aya, *Hajiya Zainab* kuma tayi mutuwar zaune, domin ta d'auka sakar mata ita kayi akai, gaba d'aya tajik'a zanenta da zawo da fitsari sai mulmula takeyi a tsakar d'aki." Tsawa ya daka mata Wanda yasanyata tadawo hankalinta, sai a lokacin ta fahimci cewa ba mutuwa ce tayiba, Yanuna mata kujerar da abincin yake kanta, yace "dawo nan ki zauna, magana ta k'arshe zanyimaki wadda daga gareta bazan kuma yimaki maganaba sai dai ki tsinci kanki a lafira, Tasowa tayi ta zauna a kan kujeran, ya tura mata plete d'in abincin gabanta yace "canyeshi duka, ya koma kan kujera da ke kallonta ya zauna rik'e da bindiga yana kallonta." K'arar bindigar da maimartaba yaji, hankalinshi yatashi yashiga mamaki ina ake harbi a cikin gidanshi, Waye aka kashe a gidanshi." Be gama rufe bakiba sai ganin fadawan yayi wad'anda ke gadin b'angaren yarima sun iso a gid'eme, suka zube a gaban shi, hankalinsu a tashe, suka had'a baki gaba d'aya suka ce, "ranka ya dad'e a kwai matsala a b'angaren *Yarima* domin tun d'azun *Hajiya Zainab* tashiga bata fitoba daga k'arshe sai k'arar tashin bindiga mukaji yana fitowa daga ciki." Hankalin sarki yashi be tsaya suka iyar da maganarba ya mik'e tsaye fadawa suka rufa mashi baya da saurinsu suka nufi b'angaren *Yariman*." Suna gabda shiga sukaci karo da *Fulani* tare da Hajiya Amina suna sauri zasu nufi b'angaren yariman domin sun fahimci k'arar bindigar da sukaji a can yafito, *Fulani* kuma tasan halin yarima da zuciya komai zai iya aikatawa idan ranshi ya b'aci." Babu Wanda yayiwa wani magana gaba d'ayansu suka d'unguma suka shiga b'angaren nashi." *Hajiya Zainab* kuma rik'e da cokalin abinci a hannunta sai cakud'ar abinci takeyi, hannunta sai rawa yakeyi, tanayi tana kallon *Bassam*, Wata hararace ya wurgomata had'ida kuma saita mata bakin bindiga a fuskarta, yasanyata tayi saurin d'ibar abincin zatakai baki kenan sarki yaturo k'ofa tareda mak'arraba sa." Ganin da tayi sarki yashigo yasanyata sakin cokalin abincin tanufi bayan sarki da gudunta ta b'oye, tana fad'in "Ranka ya dad'e ka taimakeni *Bassam* zai kasheni." Gaba d'ayansu toshe hancinsu sukayi sakamakon wani kalar warin zawo da sukaji *Hajiya Zainab* nafitarwa, Sarki yashiga salati yana fad'in lafiya Hajiya Zainab meke faruwa meya kawoki b'angaren *Bassam*?" Wai yaushe ya dawo, a ina ya kwana Daren jiya?" Haka sarki yadinga jefo tambayoyi, amma besamu amsar ko d'ayaba." *Fulani* da saurinta tanufi *Bassam* ta dafa kanshi tace "yarona ina fatan babu abunda yasameka?" Ya girgiza kai alamar babu." domin saboda b'acin rai ko magana baya iyayi." *Hajiya Zainab* dake b'oye a bayan sarki, sai magiya take mashi, sarki ya doka mata tsawa, yace "ya isa *Hajiya Zainab* kiyi min shuru naji magana daga bakin *Bassam* tunda na tambayeki kinkasa fad'amin abunda ke faruwa." *Bassam* zaune a kan kujera ya d'ora k'afa d'aya kan d'aya yana girgiza k'afa rayuwarshi idan tayi dubu to ta b'aci." Sarki na ganinshi cikin wannan yanayin yasan lallai ba k'aramin Abu akayi mashiba, Ya nufeshi had'ida dafa kafad'arshi yace "yi hak'uri *Yarima* kwantar da hankalinka kafad'a min abunda ke faruwa." D'ago kanshi yayi daga sunkuyen dayake, ya kalli maimartaba, idon nan nashi sunyi jajir, Dakyar yabud'e baki yace " babu abunda yafaru Ranka ya dade, illah abun farin ciki da yasamu a gidan nan. Sarki yace "abun farin ciki kuma yarima kamar Yaya?" *Bassam* yace bayan nadawo daga wurin walimar abokina wadda yayi tabud'a wani babban store na kayan masarufi, sai dare yayi mun, a can, kasan cewar kabani umurnin cewa na daina yawo idan dare yayi, shine na yanke shawarar kwana a can da safe idan nadawo nayi maka bayani." Bayan nadawo ne, sainaci karo da Hajiya Zainab tashiryomin kwarya kwayar liyafa ta tarbona domin tace nasanyata a tashin hankalin rashin kwanan da banyi a gidaba." Naji dad'i sosai ranka ya dad'e a tayani godiya a wurin Hajiya Zainab." Fadawa suka dinga cewa "Allah yabiyaki gimbiya Yarima na godiya." Hajiya Zainab ta kumayin tsoru tsoru da ido." *Bassam* yayi murmushin mugunta na gefen Baki, yaci gaba da cewa, "Ranka ya dad'e idan ban mantaba kasha yimin umurni da cewa duk Wanda yabani kyautar abinci ko wanne irine nace yafaraci idan yaci sannan nima sainaci." Sarki yace "tabbas hakane yarima." Yarima ya girgiza kai yace "Ranka ya dad'e kabawa matar ka umurni da tafaracin abincin da takawomin sannan nima sai naci domin yunwa nakeji sosai.' Sarki ya juya ya kalli *Hajiya Zainab* yace " *Hajiya Zainab* zokici abincin nan kiyi ko cokali biyu ne, sannan sai yarima yaci domin yace yunwa yakeji." Kuka tafashe dashi kamar wata k'aramar yarinya tace dan "Allah maimartaba ka rufamin asiri wlh da zarar naci abincin nan mutuwa zanyi saboda akwai guba a cikinsa." Salati kowa yashigayi suka had'a baki gaba d'ayansu sukace guba." kallonta, sarki yayi yace "amma dai Hajiya Zainab kinbani mamaki, ashe dama kina nan da mugun nufinki na sai kinga bayan *Bassam* Yace "todaga yanzun nacireki a cikin jerin matana daga yau Ya juya ya kalli fadawan dake tare dashi yace "ku kamata Ku kaita gidan hukunci a hukunta dai dai da lafinda tayi, idan angama hukun tata, a kaita wancan b'angaren inda ba mutane a cikinshi taci gaba da rayuwarta a can." Ya dafa kan Bassam yace Allah yayi maka albarka insha Allahu Allah zaici gaba da tsaremin kai a duk inda kake." 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S* _we don't just entertain and educated we tauch the heart of the readers_ _____________________________ #WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM #IG PML WRITERS #https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035 #http://maryamsbello.blogspot.com *10* "Sunkuyar da kansa k'asa yayi yace "Amin *Abba*." Sannan *Maimartaba* yabada umurni kowa yayi tafiyarshi yana buk'atar ganawa da *Yarima* Hakan takasance kowa ya watse akabar *Maimartaba* tare da *Yarima*." Sarki ya yatafi kan kujerar dake kallon ta *Bassam* ya zauna had'ida k'ura mashi ido yana kallonshi cike da tausayin d'an nashi." *Bassam* da kanshi ke sunkuye a k'asa, hawayen da yakeso yafitar tun d'azun ganin fadawa yasa ya rik'eso, sai yanzun suke fita a idonshi." Sarki yataso ya rungumeshi yabashi tausayi matuk'a domin rabon da yaga hawayen yarima na zuba, tun lokacin yana k'araminshi. Ko a lokacin ba k'aramin Abu kesanyashi kukaba sai kuma yanzun, tabbas yau anbak'antawa *Yarima* rai." Kuma rungumeshi yayi gam a jikinshi kamar k'aramin yaro, Yashiga cemasa "yi shuru *Yarima* daina kuka duk wani Wanda ke bibiyarka da shairi Allah zai saka maka, kuma Allah zaitoni asirinshi kowayeshi kamar yanda asirin *Hajiya Zainab* ya tuno a yau." *Yarima* ya d'ogo kansa daga jikin maimartaba yace "Abba dama duk Wanda beda mahaifiya hakan rayuwarsa take kasancewa cikin had'ari?" Na lura a gidan nan Abba idan akacire *Fulani* burin kowa shine yaga bayana, yaga bana motsi a doron k'asa, Abba mena taremasu, bani nayi kainaba Allah ya halliceni Pls Abba tunkamin suk'arasa dani lafira, kabani izini nabar garin nan natafiyata England naci gaba da zamana a can, duk lokaci da nabuk'aci ganinka zanzo naganka nakoma." Maimartaba yace "daina fad'in hakan *Bassam* babu inda zakatafi kana kusani dani, bazan tab'a barin ka kuma yin nisadaniba Mafita d'aya ce kayi aure, kanemo yarinyar da kakeso na aura maka ita, zaman da kakeyi a hakan kai kad'ai batareda mataba yana kuma k'ara bawa azzalumai damar da zasu cutar dakai." Ya dafa kafad'arshi yace " *Yarima* ka natsu ka kwantar da hankalinki kanemo matar aure ko 'yar gidan waye a garin nan zan aura maka ita, Kasani kaikad'ai ne d'ana d'aya tilo a duniya, inaso na fara ganin jikokina, inaso nafara d'aukar jikokina tunkafin mutuwa ta d'aukeni na bar duniyar." Idan kuma baka da zab'i nizan zab'a maka matar aure mai mutunci da tarbiya." Shuru *Bassam* yayi yace *Abba* kaine gatana a duniya kuma kaine farin cikina, tunda hakan kake buk'ata na amince zanyi auren kazab'a min matar aure duk Wanda ka amince da ita a rayuwarka." Maimartaba yayi murmushin jin dad'i domin a duniya bbu abunda yakeso sama da *Bassam* gashi da bibiya uwa uba tarbiya, Yadafa kansa yace "nagode *Bassam* Allah yayi maka albarka." *Bassam* yace "Amin *Abba* Maimartaba yatashi yafita cike da farin ciki." D'aki *Bassam* yashiga ya fad'a kan makeken gadonshi, idonshi sama yana kallon silin, babu abunda yake tunani sai yanda rayuwarshi zata kasance idan akayi mashi aure, to wacece Abba zai aura mashi? Haka yadinga tunani, can ya tuna da marin da Afnan tayi mashi, Zumut yayi ya mik'e zaune yashiga shafar fuskarshi inda ta mareshin, ko meyatuna oho tashi yayi zaune da saurinshi ya duru kan gadon had'ida d'aukar key d'in motarshi ya fita da saurinshi." _________________________________ Malam *Nura* tsugunne a gaban kaka yana rok'onta akan ta amince da buk'atarshi, Da cewa "da zarar Afnan ta kammala ssce d'inta a d'aura masu aure, daga baya yayi alk'awari idan tana gidanshi zataci gaba da karatunta har saitace ta gaji." Kaka tayi kyaran murya tace "Nura ba wai nak'i shawararka bane, ni a wurina bakada matsala domin ba tun yanzunba na yaba da hankalinka kuma nabaka Afnan." Amma wani hanzari ba guduba, kajira malam Iro ya dawo daga tafiyar da yayi, saikayi masa maganar domin shine matsayin Mahaifin Afnan a yanxun, kaga daga nan zuwa wata biyar lokacin ta kammala karatun nata, sai ayi aurenku." Gaba d'ayansu murna suka shigayi, sannan Afnan ta mik'e tanufi hanyar waje dama uniform ne a jikinta tanufi hanyar makaranta malm Nura ya rufa mata baya dama shi ke rakiyar ta harta samu abun hawaye sannan ya dawo gida." Sauri ta keyi cike da farin ciki domin kunyar had'a ido takeyi da malam Nura, Shima saurin yakeyi domin yacin mata, da kyar yasamu ya cinmata, yashiga ce mata "Afnan yau kojirana bakyayi nayi rakiyar?" Rufe idonta tayi da hijabi taja wuri d'aya ta tsaya cike da jin kunya, Murmushi yayi yace "Afnan sarkin kunya, Irin wad'an nan halayen naki sune suke k'ara sanya min naji ina sonki, *Afnan* "ina sonki ba zan gaji da furta maki hakan ba, Fatana d'aya Allah yadawo da Baba Iro lafiya yasanya mana ranar aurenmu, Jin kad'an yayi shuru yana kallonta,, idanshi ya cika da hawayen k'auna, yaci gaba da cewa, "Afnan sai nakeji a raina kamar zan rasaki, kuma rasaki a rayuwata kamar rabani da numfashina ne." D'ago kanta tayi, suka had'a ido taji sonshi da k'aunarshi had'ida tausayinshi ya kamata tace "ya sayyadi ka daina furta hakan, zuciyarka ta daina yimaka sak'e sak'en cewa bazaka sameniba, babu Wanda zai rabamu sai munyi aure mun haifi yaranmu kyawawa masu kama dakai." Dariya suka sanya gaba d'ayansu, d'aga kan da zasuyi sukayi ido biyu da *Bassam* gefensu a tsaye duk abunda suke fad'a akan kunnenshi, Sun tsunduma duniyar masoya basuma San yana wurinba." Basu kuma kallonshiba suka jera sukatafi, har sunfara tafiya ya cinmasu ya shiga gabansu ya tsaya, yana dariya had'ida Sosa gemunshi, malam Nura ne yayi k'arfin halin yimashi magana, yace "malam me kake nema damune kakeso kaga kashiga rayuwarmu, me muka tare maka a duniya ne? Be tanka mashiba saima tsurawa *Afnan* ido yayi yana kallonta, da kyar ya bud'i baki yayi magana, yace "kin d'auka zaki mari yarima d'ansarki kuma kiyi tunanin zaki zauna lafiya? Yayi murmushi yace "akwai hukuncin Dana tanadar maku keda duk wata zuri'arku, amma yanzun na rusheshi, ya kalli malam Nura yace zan d'aukar mku wani hukunci daidai daku, Wanda zan hanaku farin ciki da walwala injefa kunci a cikin zuciyoyinku, Ku biyu nan da kai da ita, saina sanyaku kuka da hawayenku." Yana kaiwa nan ya juya yayi tafiyarshi, yabarsu nan cikin tunani daga k'arshe malam Nura yayi k'arfin halin yi mashi magana yace "Allah yafiKa Azzalumi kawai Allah bazai barkaba." Karaf sai a kunnen *Bassam* ya juyo ya kalleshi yayi murmushinsa na gefen baki yayi tafiyarsa." A zahirin gaskiya kalaman malam Nura sun bak'anta mashi rayuwa matuk'a, domin babu Wanda yatab'a jifarshi da zafafan kalamai kamarshi.". Tafiya sukeyi *Afnan* ta kalli malam Nura tace "ya sayyadi niko narasa abunda wannan d'an sarkin yake nufi damu, ya ke kuma bibiyar rayuwarmu, ina ganin alamarshi soyakeyi ya ruguza mana farin cikin rayuwarmu" Malam Nura yayi murmushi yace "kwantar da hankalinki *Afnan* babu abunda zai iya Allah yafishi, Ni dai abinda nakeso dake kiyita addu'a da zarar Baba Iro yadawo nakai sadakinki a d'aura mana aure naganki a gida, daga ranar baZai kuma ganinkiba, suka kalli juna sukayi murmushi." Motarshi yanufa daniyar yatafi, amma yakasa sai tunanin kalaman malam Nura yakeyi, da yace masa Azzalumi, Waibasu San koshi wayebane?" sukeson suci zarafinshi, ya girgiza kai had'ida dukan sitiyari yace "karya ne wlh duk Wanda ya kalleni tun daga shigar kayana zai gane ni jinin saurata ne, musamman idan yayi tozali da *tambarin sarautar* dake gaban hulata." To suwai basu lura da hakan bane, Wata zuciyar tace masa "sun san kai d'an sarkine tsoronka kawai ne basayi." Ya girgiza kai yace zan ganar dasu, inma basu ganeba, yaja motarshi yayi gida." _______________________________ Malam Iro ya dawo daga tafiya, Kai tsaye malam Nura ya tunkareshi da maganar auren *Afnan* malam Iro, ya amince ya kuma yi farin ciki sosai domin batun yanzun ba ya yayaba ta da tarbiyar malam Nura." Bayan kwana biyu malam Nura yaturo magaba tanshi, aka yanka mashi sadaki ya biya, had'ida sanya masu ranar aure, wata hud'u masu Zuwa." Murna a wurin masoyan nan biyu abun ba'a magana." *muje zuwa*👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S* _we don't just entertain and educated we tauch the heart of the readers_ #WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM #IG PML WRITERS #https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035 #http://maryamsbello.blogspot.com *11* Gida *Bassam* yadawo, yashiga sak'e sak'e a zuciyarshi, anan take ya yanke shawarar raba *Afnan* da Malam *Nura*." Domin idan ya rabasu yasan sai sunfi jin ciyon hakan akan a wani hukunci da zaimasu, sannan kuma daga k'arshe zaiyi amfani da wannan damar ya wulak'anta *Afnan* da duk wasu magoya bayanta." Yashiga tunanin to ta wace hanya zaibi domin ganin ya rabasu, rabuwa ta har abada." A can yatuna da maganar *Maryam* mahaukaciya datace "ka aureta idan karama marinka saika saketa." Girgiza kai yayi ya furta a fili yace "tabbas aurenta zanyi na wucin gadi hakan shi zaisanya narabata da farin cikinta masoyinta daga k'arshe na wulak'antata na kuresu gaba d'aya a garin da ita da mahaifanta." , Zunbur ya mik'e tsaye, da saurinshi Kai tsaye fada yanufa wurin *Maimartaba* da sallama yashiga, ya durk'usa k'asa ya gaida Maimartaba, Cike da walwala Sarki ya amsa gaisuwar *Bassam* had'ida k'ure shi da ido yana kallonshi." *Bassam* ya mik'e tsaye yasamu kujera ya zauna had'ida sunkuyar da Kansa k'asa, yana jiran *maimartaba* yai mashi magana sannan yafad'i muk'atarshi." Kallonshi Sarki yayi cike da kulawa sannan yayi murmushi, dan ya fahimci akwai muhimmiyar maganar da yazo da ita, idan kuma be fara yimashi maganaba hakan zai koma da ita bazai furtataba sai dai tayita damunshi a rayuwarshi." Sarki ya kalli *Bassam* cike da kulawa da kuma k'aunar d'an nashi, yace "Allah ya taimakeka sarki maijiran gado meke tafe dakai?" *Bassam* yayi k'asa da kai, sannan yayi gyaran murya yace "Ranka ya dade, game da maganar auren da kace ya kamata nayi, In har baka riga kazab'a min matar da zan auraba, ranka ya dad'e zuwa nayi domin na shaida maka da cewa nasamu matar aure." Murmushin jin dad'i Sarki yayi, yace "Alhamdulillah." *Bassam* naji dad'i sosai da wannan Albishir naka, domin yanzun nakeso natura waziri zuwa masarautar Zamfara wurin sarki Anas, ya kaimashi sakon cewa in har beyiwa 'yarshi Fareeda mijiba nayi maka kamenta domin na yaba da hankalinta da tarbiyarta." To Alhamdulillah tunda kazo da Wanda kakeso naji dad'i matuk'a Allah ya shi maka albarka *Bassam*." 'Yar wane gida ce? Wace unguwa suke?" Kuma waye ubanta?" *Bassam* ya sunkuyar da Kansa k'asa, a zuciyarshi yake cewa, "'yar matsiyatace zuri'ar aljanu, bakowa bane ubanta illah wani gantalanlan tsoho mai yawo da riga d'aya a wuyanshi." A bayyane kuma yace "ranka ya dad'e ba 'yar kowa bace, domin mahaifanta basuda wani k'arfi sosai talakawa ne." Sarki yayi murmushi yace "inason halayenka yarima na taimakon talakan da kakeyi da rashin k'yamatarsu da bakayi." Yimun kwatancin gidansu yanzun nan zantura waziri yazomin da mahaifin yarinya sai a tsaida maganar aurenku." Murmushi *Bassam* yayi Wanda yafi kuka ciyo, yace nagode Abbah." a nan *Bassam* yashiga yiwa *Maimartaba* kwatancen gidansu Afnan." Malam Iro tareda Kaka a zaune a gidan kaka "yana mata bayanin lokacin da yaka mata ayi bikin su Afnan da malam Nura." Sai sallamar yaro sukaji a waje yana fad'in "wai ance idan malam Iro yana nan ana sallama dashi a waje." Da Sauri malam Iro yace "ganinan zuwa, ya tashi tsaye had'ida yiwa kaka sallama ya fita waje yana mamakin Wanda ke nemanshi a wannan lokacin." Fitowar da yayi yaci karo da fadawan sarki tsai tsaye a k'ofar gida, ganin fitowarshi suka nufo inda yake, Gaban malam Iro yashiga fad'uwa a nan yashiga tambayar kanshi meke faruwa?" Tsintar muryansu yayi suna fad'in "Kaine malam iro?" Malam Iro ya had'iye wasu yawo basu Zafi saboda tsoro. Sannan ya kallesu yayi k'arfin halin yin magana yace "Eh nine wani abun ke faruwa?" Suka had'a baki gaba d'ayansu sukace "Sarki yace azo masa dakai." Malam Iro ya razana had'ida zaro ido, yace "da laifin me? Menayi kuma?" D'aya daga cikin fadawan yace "kabari idan katafi can saikayi wannan tambayar." Haka malam Iro yashiga mota suka tafi dashi." Masu zame a ko inaba sai fada a gaban sarki." Sarki yasa aka karrama malam Iro, danganen abinci da abun sha, sai a lokacin hankalin malam iro ya kwanta domin ya fahimci cewa bawani laifi yayiba." Bayan ya kammala cin abincin, sarki ya kalleshi yayi gyaran murya yace "malam iro nasan zakayi mamakin ganinka a gabana, To wannan ba abun mamaki bane, sai alkhairi dakeson shiga tsakanina da kai, da kuma wani taimako danakeso kayi min." Malam iro ya kalleni maimartaba cikin girmamawa yace "ranka ya dad'e wani irin taimako ne wannan nake dashi Wanda har kake nema a wurina.?" Marmartaba yayi murmushi, yace "d'ana yarima *Bassam* yaga 'yarka yanuna yana sonta, in har bakayi mata mijiba ina nemawa d'ana aurenta a wurinka." Malam iro ya sunkuyar da Kansa k'asa yatuna da yanayin da yaga yarima cikin maye haryake tunanin ya aura mashi 'Yarshi Allah ya tsareshi domin 'yarshi mace d'ayace Maryam kuma ya riga da yayi mata miji, d'an uwansa zata aura." Yace "ranka ya dad'e 'yata 'yarkace duk yanda kaso haka za'ayi, amma Allah ya taimakeka 'yata *Maryam* anriga da anyimata baiko da d'an uwanta zata aura." Maimartaba ya kalli malam iro, yace "Maryam kuma?" *Bassam* ba. Maryam yake nufiba *Afnan* yace yanaso." Malam iro ya kuma kallon maimarrtaba yace "Allah sarki *Afnan* yake nufi kenan, Ranka ya dad'e Afnan ba 'yata bace 'yar amanace awurina, domin kuwa marainiyace bata da uwa bata da uba, a hannun kakanta mace take itace gatanta sai kuma ni dake kula dasu, domin ina tausayawa rayuwar yarinyar, Sarki yace "Allah sarki tabbas marainiyace gaba da baya, Allah yabaka ladar taimako malam iro." Malam iro yace "Amin." Amma ranka ya dad'e ita *Afnan* d'in ba'ayi wata d'aya da amsar sadakinta ba domin har ansanya ranar aurenta nanda wata uku basu zuwa." Sarki ya girgiza kai alamar gamsuwa, yace "Allah yasanya Alkhairi yasa ayi damu, malam iro kana iya tafiyarka idan shi *Bassam* d'in yadawo sainayi mashi bayani, duk yanda mukayi dakai." Ya runsunar da kanshi k'asa yace nagode sarki mai adalci ka huta lafiya." ________________________________ Koda malam iro yadawo gida bezame ko inaba sai gidan kaka ya tarar da kaka zaune tsakar gida tareda *Afnan* da malam Nura sai fira sukeyi suna dariya." Anan malam iro yasamu wuri ya zauna yashiga fad'awa kaka wad'anda suka aiko kiranshi fadawane sarki yaturosu sutafi dashi, Gaban Afnan da malam Nura yashiga fad'uwa domin sunsan sunfad'a tarkon yarima d'an sarki, kashe kunne sukayi domin su kuma ji me yasanya aka tafi da malam iro." Malama iro yaci gaba da cewa "wai wannan hatsabibin d'an nan nashi Wanda ya maida giya kamar ruwan pure water waishi yaga *Afnan* yaji yanasonta kuma aurenta zaiyi." Kaka ta washe baki tace Allah sarki ai anriga da anyiwa " *Afnan* miji." *Afnan* tayi saurin mik'ewa tsaya cike da tashin hankali tace "wlh kaka koda maza sunk'are a duniya nasarasa mijin aure babu abunda zaisanyani na aure mashayin giya." Malam Nura kuma dake gefe zaune, idonshi sunfara komawa launin ja, saboda tsanin kishi da jin haushi, mik'ewa tsaye yayi batareda yayiwa kowa maganaba ya fita." Kaka tabishi da kallo had'ida rik'e baki tace ikon Allah🤔 _muje zuwa_ 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S* _we don't just entertain and educated we tauch the heart of the readers_ #WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM #IG PML WRITERS #https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035 #http://maryamsbello.blogspot.com *12* " *Maimartaba* ya aiki *Waziri* domin ya kira mashi Yarima." Waziri Tare da *Yarima* suka nufo fadar *Maimartaba* Anan Sarki yabada umurnin da kowa ya watse a basu wuri zai gana da *Yarima*." Bayan kowa ya fita, Sarki ya kalli *Bassam* da kyau, sannan yace "Yarima inaso ka natsu ka saurareni magana zanyi da kai." Bassam ya kuma gyara zama had'ida sunkuyar da kanshi k'asa." Maimartaba yaci gaba da cewa "Yarinyar da kace mun kanaso zaka aureta, To Nayi magana da Mahaifinta yace mun anriga da anyi mata miji domin har sadakinta an karb'a." "Daga nan yake shaida min cewa Marainiyace, Na kuma tausayawa yarinyar domin marainiyace ba uwa ba uba, a hannun Kakarta mace take zaune ita ke rik'onta." "Wanda kake tsammanin shine mahaifinta Ashe bashi ya haifetaba, mak'ocinsu ne, yana dai kula da itane saboda yana tausayawa rayuwar yarinyar." "Dan haka kajanye maganar aurenta, dakace zakayi, kafita lamarinta gaba d'aya." domin kasani cewa haramun ne, Neman Aure kan Aure." *Bassam* ya d'an runsuna, yace " na fahimta Abbah, amma duk soyayyar da mukeyi da ita bata tab'a nunamin cewa an tsayar mata da mijiba." Abba tana sona nima inasonta sosai amma nayi mamakin jin wannan Maganar daga bakin mahaifinta." "Amma ba komai na hak'ura da ita idan Allah yak'addari rabona ce zan aureta." Maimartaba yace "yawwa Yarima Allah yashimaka Albarka, tashi katafi." Haka Bassam yafito fada yana sak'e sak'e a ranshi, D'akinshi ya nufa yafad'a kan gadonshi yayi rubda ciki yana tunani, Yanzun shi kenan wannan matsiyaciyar yarinya ta mari banza kenan?" Ya kuma mirginawa daga runda cikin da yake zuwa kallon silin, yashiga tunanin, "tun lokacin da tasanya hannu ta mareshi, be kuma samun farin cikiba a rayuwarshi, kullum cikin tunani yake ta yaya, itama zata kasance cikin bak'in ciki da *k'unar Zuci* domin a rayuwarshi babu wanda yatab'a d'aga hannu ya mareshi sai ita, ita d'inma matsiyaciya marasa gata, rik'on tsohowa mai cin goro." Ya girgiza kai yace "ina bazai yiyuba, dolene hukunci ya hau kanta." Da sauri ya duro a kan gado, ya d'auki key d'in motarshi ya fito harabar gidan ya tsaya yana dibe dibe, da alama akwai abunda yake nema." fadawa na ganinshi sukayo kansa suna zubewa k'asa suna kwasar gaisuwa, D'aga masu hannu yayi alamar ya amsa." Sannan ya kuma kallonsu yace "ina fadawan hukunci?" Suka amsa da "gamu ranka ya dad'e Allah ya taimakeka ya tsare mana lafiyarka." Yace "kubiyoni mutafi, akwai inda nakeda buk'atarku." Da saurinsu suka had'a baki sukace "angama Yarima mai jiran gado." Mota uku suka d'auka, gamida motar *Bassam* hud'u kenan." Motar *Bassam* ce gaba sannan ta fadawa na bayanshi, Kai tsaye unguwarsu *Afnan* suka nufa, sukayi sa'a tafito sanye da uniform zata makaranta, malam *Nura* na gefenta d'auke da jakarta suna tafiya suna fira." Burki *Bassam* yayi da k'arfi yaja ya tsaya, yana kallonsu yana murmushi gefen baki." Da gudu fadawa suka fito gaba d'ayansu suka shiga tambayarshi "ko wani Abu ke faruwa?." Murmushin mugunta ya kumayi Sannan ya kallesu, had'ida da nuna masu su *Afnan* yace "kuje Ku kamomin wad'ancan yaran yanunasu da hannu "ku sanyasu a mota ku tafi dasu gidan hukunci a jiyemin su kamin nazo." Cikin girmamawa sukace "angama ranka ya dad'e." *Afnan* da *Nura* dake tafiya basuma lura dasuba, Sai ganin fadawa sukayi tsaitsaye a gabansu sunzagayesu kowane hannunshi d'auke da k'atuwar bulala." D'aya daga cikin fadawan wani k'ato maigirman jiki, ya kalli *Nura* da *Afnan* yace " *Yarima* ne yace azo mashi daku, dan haka kuwuce mutafi." *Afnan* ta kallesu a wulak'ance cikin muryanta mai sanyi tace "wanene *Yarima*?" Wayeshi a garin nan?" " To Kutafi kuce masa bazamu zoba saboda bai isaba." Wani bafade dayaji kalamanta sunyi tsauri dayawa ya hasala da kalaman *Afnan* ya zuciya ya d'aga bulala zai doka mata, *Nura* yashige gabanta ya kareta yana kallonsu d'aya bayan d'aya, yunkuri yayi domin bugawa *Nura* Bulalar saiji yayi a bayansa *Yarima* na magana yana fad'in "karka dakesu, Cewa nayi kutafi dasu gidan hukunci idan kuma suka sanya tsaurin kai ku d'aukesu a kai kusanyasu a mota kutafi dasu." Kallon tsana *Afnan* tabi yarima dashi, zatayi magana kenan, taji malam *Nura* na fad'in karkice komai *Gimbiyata* mubisu mutafi muga iya gudun ruwanshi." Kallo *Bassam* yabi *Nura* dashi yayi murmushin mugunta, Amma kuma Kalmar *Gimbiyata* ta tsaya mashi a rai." 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S* _we don't just entertain and educated we tauch the heart of the readers_ #WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM #IG PML WRITERS #https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035 #http://maryamsbello.blogspot.com *13* *DIDECATED TO AISHA A MOH'D* ( _yayi sake_) Gidan hukunci aka nufa dasu, Aka ajiyesu a cikin wani d'aki marar yalwa." *Bassam* ne ya turo k'ofa yashigo cike da k'asaita, fadawa suntake mashi baya, sai kirari suke zuba mashi." Afanan da Nura Atare suka d'aga kai suka kalleshi, kallon tsana." *Afnan* tace "dan Allah bawan Allah kayi sauri kafad'i buk'atarka da kuma dalilinka na yasanya a satomu aka kawomu wannan kucakin gidan." Ido ya kura mata cike da mamaki da kuma k'arfin hali irin nata naraahin tsoro." murmushi yayi yace "idan kika kuma yin magana saina sanya fadawa sunyi maki bulala goma yanzun nan." *Nura* ne yayi mata alama da tayi shuru karta kuma yin magana, domin yaga fuskar *Bassam* ba wasa a cikinta komai zai iya aikata mata tunda azzalumine." Kujera fadawa suka d'ora mashi ya zauna yana fuskartarsu, sannan yayi murmushi had'ida gyaran murya, ya kuma kallonsu yace "masoyan juna." Kunsan dalilin da yasanya nace a kawo man kunan?" Kallo suka bishi dashi babu Wanda ya tanka mashi." yaci gaba da cewa "saboda inyanke maku farin ciki rayuwarku, kamar yanda wannan mai kama da Aljanun ta yankemin nawa farin cikin lokacin da tasanya wannan mataccin hannun nata ta mareni." Dan haka abunda nake so daku nake kuma baku umurni shine daga yau bakai ba wannan abar, yanuna *Afnan* ta wurga mashi harara🙄 "kema bake ba wannan ustazun dolene Ku rabu, domin na fahimci rabukun da zanyi shine silar yankewar farin cikin rayuwarku gaba d'aya." Be rufe bakiba *Nura* besan lokacin da yace "baka isaba wallahi"babu Wanda ya isa ya rabani da Afnan sai mutuwa kai ko kasheni zakayi wallahi bazan rabu da itaba sai na aureta." Kallo *Bassam* yabishi dashi yana girgiza kai, yace "hattara ustazu ba'a fad'a ina fad'a, Yace "sarkin hukunci." Da gudu sarkin hukunci ya k'araso ya zube k'asa yana fad'in "gani ranka ya dad'e." yanuna malam *Nura* yace afita dashi waje ayi mashi bulala goma, sannan adawo dashi." Haka fadawa suka d'auki *Nura* akayi mashi bulala goma sannan aka dawo dashi." Babu abunda Afnan takeyi sai zubar da hawaye tana ganin yanda ake zalunci k'iri k'iri." Kallo yabi *Afnan* dashi yaga yanda take kuka, yayi murmushi yace "bakiyi kukaba za dai kiyi kukan lokacin da aka d'aura min aure dake." Tayi saurin d'aga kanta sama ta kalleshi cikin muryan kuka tace "Allah ya tsareni na aureka, Dana aureka k'ara Allah ya amshi rayuwata Azzalumi kawai." Yace "aikuwa sai dai ki mutu domin kuwa mutuwarki tafi komai sauki gareki, da irin k'angin bautar da zaki Shiga bayan na aureki." Ya juya ya kalli malam *Nura* yace ko kanada magana?" *Nura* baima kalle inda yakeba bare ya tanka mashi, domin jiyake kamar ya shak'eshi ya mutu yakeji." Dariya Yarima yashigayi yana kallon Nura da Afnan yana nunasu da hannu, yana fad'in "yau ina soyayyar da kukeyi take?" Ya kuma kallon Nura yace karka damu da halin da ka tsinci kanka a cikin masoyiyarka *Gimbiyarka*ce ta daza maka." Kallon *Afnan* Nura yayi da ta had'a kanta da gwaiwa sai faman kuka takeyi, tausayi tabashi matuk'a, shima idonshi ya rik'id'e zuwa launin ja, amma bashida halin lallashinta saboda wannan azzalumin yasanyasu gaba." Kallonsu *Bassam* yakeyi d'aya bayan d'aya, yanayin da ya gansu a ciki yanzun yayi mashi dad'i sai murmushi yakeyi." Fadawa yakira sukazo da sauri, "yanuna malam Nura yace "kud'aukeshi Ku maidashi inda kuka d'aukoshi, Domin ina ganin nadama a fuskarshi, Ita kuma wannan ku barta nan har sai lokacin da naga tayi nadama." Malam *Nura* najin hakan yace "wallahi bazan tafi na bar Afnan wurin Azzalumi irinkaba k'ara ni kacigaba da rik'eni a hannunka ita kasaketa ta koma gida, "Amma bazan tab'a tafiya nabarta a wurinkaba saboda ba imani a zuciyarka komai kana iya aikata mata." Dariya yayi "yacewa fadawa wai mekuke jira dashi ne." D'aukarshi sukayi kamar jariri ko motsi baya iyayi, bare yayi yunk'urin kwacewa, yanaji yana gani yabar *Afnan* aka sanyashi a mota aka tafi dashi." Kuka *Afnan* takeyi sosai saboda b'acin rai,da bak'in ciki gata bata iya yin doguwar magana, sai kallo tabi *Bassam* dashi cike da tsana." Gani yayi tanayi mashi wani kallon rashin kunya ya taso daga inda yake zaune yanufota ya sunkuyar da fuskarshi saiti fuskarta har suna iyajin saukar numfashin junan, Yayi murmushi cikin magana k'asa k'asa yace mata "wannan kallon na meye?" marar kunya." Kinrabu da masoyinki yatafi yabarki ko?, haka zan aureki in rabaku rabuwa ta har Abada." Yawu ta tufa mashi a fuska har cikin bakinshi." Tace "Allah ya tsareni dana aureka." "dana aureka k'ara Allah ya amshi rayuwatah."👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S* _we don't just entertain and educated we tauch the heart of the readers_ #WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM #IG PML WRITERS #https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035 #http://maryamsbello.blogspot.com *14* Idonshi ya rikid'e zl yakoma launin ja, jijiyoyin kanshi suka tashi alamar b'acin rai ya dunkuli hannun shi👊🏻 da niyar ya kaimata duka, Komai ya tuna oho, ya yasauke hannunshi had'ida cije Baki, ya dank'o gashin kansa, sannan yafita d'akin da saurinshin." Fadawa yabawa umurni "duk Wanda yakuskura ya bari tafito to saiya d'aukar mashi mummunan mataki." Suka amsa da "angama ranka ya dad'e Allah ya tsare mana kai." Yashiga motarshi rai a b'ace yajata da k'arfi kamar yatashi sama, Bezame a ko inaba sai Club." ________________________________ Bayan an sauke malam Nura gida, yi yayi kamar yayi hauka idan yatuna Afnan d'inshi nacan a hannun azzumi." Kai tsaye wurin malam Iro ya nufa, cikin tashin hankali ya shaida mashi duk abunda ke faruwa." Hankalin malam Iro yatashi matuk'a dayaji labarin Afnan na can hannun yarima d'an sarki." Wayarshi ya d'auka yakira babban d'anshi Sanusi dake zaune a garin Abuja yafad'a mashi duk abunda yakeyi yazo yanzun yana nemanshi, Sanusi ya amsa da "to Baba gani nan zuwa." Ajiye wayar malam Iro yayi yashiga gidan Kaka yasheda mata abunda Nura yafad'a mashi ya kuma kwantar mata da hankali insha Allahu *Afnan* bazata kwana a hannun Azzalumiba, da zarar Sanusi ya duru garin yau." 11:pm Sanusi ya duro garin gombe baizame ko inaba sai gaban mahaifinshi, a nan malam Iro yashiga zaiyana mashi duk abunda ke faruwa, ya kuma kwatanta mashi fuskar *Yarima* murmushi Sanusi yayi yace "Abbah nagane *Bassam* d'an sarki Ahmad moh'd, wani mashayin giya, Nasanshi kuma tsakanina dashi musan juna farin sani" Sanusi ya mik'e tsaye yace "Baba bari natafi na amso Afnan tunkamin ya cutar da ita domin nasan halin *Bassam* farin sani." Malan Iro yace "kabi a hankali Sanusi domin shiga gidan sarauta akwai had'arin gaske." Kaka dake gefe d'aya babu abunda takeyi sai matsar hawaye, tana tausayawa Afnan da yanzun batasan halin da take cikin saba." Ta kalli Sanusi tace "Allah ya taimakeka yabaka sa'a a kan azzalumi irin *Yarima*." Sanusi yace "Amin Kaka sannan ya fita." Yaransa yayiwa waya, a nan take suka hallara a gabanshi yabasu umurnin "duk inda Bassam yake su binciko masa shi." Anan take suka amsa da "to Oga." Cikin minti talatin sukayo mashi waya da cewa "sunsamu labarin cewa yana Club, anan sukayi mashi kwatancen Club d'in da yake." Da sauri Sanusi yashiga motarsa tare da Bodyguard d'insa suka nufi Club d'in," *Bassam* da ya iso Club d'in rai b'ace, wuri yasamu a kan wani tebur ya zaune, aka shiga jera mashi kwalabin giya irin tasu ta manya mai tsada tare da kofi." Ido rufe yashiga tsiyaya giyar a kofi yana shanyewa, ya d'ora kofi na biyu a kan bakinsa ke da wuya, yaji anzo kusa dashi an tsaya." baiyi saurin d'aga idonshi ya kalli mai tsayuwar ba sai da aka zauna gefenshi, aka buga teburin dake gabansa saida kwalbar giyar da kofin suka girgiza, har a lokacin kansa a k'asa yake ko motsi baiyiba, balle ya nuna yaji tsoro, Ya kuma d'aukar kwalbar giyar ya tsiyaya a kofi, ai kuwa sai Sanusi ya d'auka ya shanye ya ajiye masa kofin." Anan Bassam ya d'aga kai ya kalleshi fuskar nan tashi a b'ace, Duk da jarumta irinta Sanusi sai da ya razana da ganin fuskarsa, har yaso ya gid'eme amma kuma ya dake yayi k'okarin kama kansa, yace "Kai yaro ina k'anwata take, tun safe da tafito zuwa makaranta angaya min lokacin da kazo tareda fadawa ka d'auketa, ina take?" Ina ka kaimin k'anwa?" Ya k'arasa maganarsa cikin d'aga murya." Bassam yayi murmushin gefen baki ya kalleshi cikin rashin tsoro ko far gaba, yace "danine kai da karage d'aga muryarka, Dan bakasan dawa kake maganaba." Sanusi yasha tunkarar mutane daban _daban na kwarai da na tsiya amma bai tab'a had'uwa da mutum mai fuskar damisa irin ta *Bassam* ba." Ai tuni yakira bodyguard d'insa da hannunsa, babu b'ata lokaci suka zagaye inda suke zaune ko wanne naji da bak'i kamar zunubi fuskarsu babu kyan gani." *Bassam* yana ganinsu ya kallesu d'aya bayan d'aya, babu tsoro a tare dashi yayi murmushinsa na gefen Baki, ya d'auki kwalbar giyarsa ya tsiyaya a kofi, Sanusi ya d'auka ya shanye ya ajiye kofin da k'arfi gaban *Bassam* yace "ina k'anwata idan baka fad'a min inda k'anwata takeba komai na iya samunka." Mik'ewa tsaye Bassam yayi, ya kalleshi da jajayen idonshi yace "k'anwarka tana hannuna kuma bazan saketaba yanzun har saina koya mata tarbiya wadda iyayenku basu bata, Idan kuma kacika kai jarumine kazo kabiyoni ka amshi k'aunarka." Bodyguard din dake tsaye bayan Bassam suka dafa kafad'arshi suna fad'in "kai ka iya bakinka Oga ba tsaran wasanka bane." Kamin ya rufe bakinshi Bassam ya rik'e hannun da yadafashi dashi, ya d'agashi ya nanashi da teburin wurin, tuni suka bazu suna k'ok'arin dukan Bassam Wanda jikinsa har rawa yakeyi, saboda dama yana jiran Wanda zai yidashi, haba nan fa suka fara duke duke aka b'ata wurin securities da dama suma jiran hakan sukeyi, aikinsu kenan rabon fad'a sunaji da k'arfi da kyar aka samu aka rabasu. Bassam ya dokesu sosai shi kam be gaji da kokowarba fad'i yakeyi, "Ku kyaleni in dokesu 'yan iska kawai." Yanuna Sanusi yace "kai kasanni na sanka, idan ka isa kazo muje inda ba'a rabamu banza mai k'aton ciki kawai." Sanusi dariya ya kyalkyale da ita, irin wannan bai ban haushi yace "nasan kana da zuciya d'an sarki kayi a hankali dani Kansan kowaye Sanusi gwaska." Kallo Bassam yabishi dashi domin jiyake kamar ya shak'eshi ya mutu yakeji, Shima Sanusi kallon Bassam yakeyi yana sak'e sak'e a ranshi, kome ya tuna oho, yayiwa bodyguard d'inshi alamar "sutafi." Bassam ya koma ya zauna cike da b'acin rai da bak'in ciki, bai tab'a shan sigariba, amma a take ya d'auki kara biyar ya zuk'a ya busar ya lumshi idanunsa, matakin da zai d'aukarwa Afnan yakeyi, saida ya kusan samun awanni uku a zaune sannan yatashi yabar Club d'in." Kai tsaye gida ya nufa, inda yasanya aka ajiye Afnan, kasan cewa yaba da umurni a canza mata d'akin zama D'aya daga cikin d'akunanshi wanda yake hutawa a can aka kaita." Dashigar shi d'akin yaci karo da ita tana sallah, Harara 🙄 ya kaimata cike da tsana, yace "Hmmm." Ya kuma kallonta had'ida mere baki☹ yace "dubeta saikace ta kwarai kullum cikin sallah amma ta munafurci." Ya wuceta yashiga ban d'aki yayi alwala yayi magariba da isha'i a lokaci guda, Ta kalleshi ta yatsine fuska tace a zuciyarta "ko sallah bai tsayawa yayi ya da kyau ga had'a sallah kai wannan mutumin baiyiba, akwai azzalumi wallahi." Koda ya idar da sallah ya tsareta da ido yana kallonta, tanaji a jikinta cewa kallonta akeyi, saiji tayi yace mata, "yar gidan tsohuwa maicin goro, kalli nan photo nane yake nuna mata, photon Kakane da Malam Iro da kuma Yaya Sanusi da kuma photon Maryam." Yace mata na gano cewa keba 'yar kowa bace ba kuma ko maibace bakida gata bakida kowa sai wannan tsohuwar sai Kuma wad'an nan mak'otan naku dasuka taimakawa rayuwarki saboda suna tausayawa rayuwarki." To gaba d'ayanku zan wulak'antaku sai kun gwammace bakuzo duniya ba, ita daga k'arshe nasanya bindiga na harbe kan tsuhuwa ta mutu, su kuma mak'atanku sai sunyi dana sanin saninki da sukayi, "Shi kuma ustaz masoyinki Wanda kuke ikirarin baku iya rabuwa sai mutuwa, to nasa annemo min inda yake kwana, inada matasa da suka shiryu a kan kisa batare da an wahalaba zan basu adireshinsa zasuje su kashe shi a daren yau." "Dan Allah kayi hak'uri ." Afnan tasaki kuka mai sauti had'ida matsowa kusa dashi." "Dan girman Allah kayi hak'uri ka taimakeni kabar min Kakata, ita kad'ai ta ragemin a duniya, kafad'i duk abunda kakeso wallahi zanyi maka." Murmushin mugunta yayi yace "shikenan yimin shuru kiji sharud'd'ana idan kikabi kikayi abunda nakeso to zaki ceci rayuwar kaka da masoyinki." "Gayamin ko mene ne zanyi wallahi zanyi."👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S* _we don't just entertain and educated we tauch the heart of the readers_ #WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM #IG PML WRITERS #https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035 #http://maryamsbello.blogspot.com *15* "Yimun shuru!." Ya daka mata tsawa Wanda saida tayi saurin zabura, had'ida rik'e bakinta." Sannan yace "ki saurareni da kyau inaso kije gida kifad'awa tsohuwa da Iro cewa aure kikeso nan da kwana uku, Kuma ki shaida masu da cewa kinfasa auren malam Nura ni kikeso a aura maki kuma nan da kwana uku." Dafe k'irji tayi cikin tashin hankali tace "aure?" Kuma kai zan aura?" Yace "eh hakan nake buk'ata, kuma idan kika kuskura kika fad'i nina tirsasaki bayin kanki bane, har kika bari kwana ukun suka wuce to a ranar Kakarki da masoyinki zasu bar duniya." Kuka tafashe dashi tana fad'in "wayyo Allah wallahi banason su mutu, naji na Amince zan aikata abunda kace domin na cece rayuwarsu, amma kasani har abada bazan tab'a son kaba." Dariya ya fashe da ita irin ta mugunta nan yace "babu soyayya a tsakaninmu sai dai azaba." Ya mik'a mata dubu biyar yace "ki hau mota." Watsa mashi kud'inshi tayi tace "bana buk'ata bana son kud'inka zanje nayi abunda kasanyani tayi fice warta." Dariya yashigayi yana fad'in "yarinya sai fad'in rai tana magana sanyi_sanyi don tsabagen yaudara." ________________________________ Bayan Malam Nura ya bar gidan malam Iro, kai tsaye gidansu ya nufa cikin tashin hankali, Kai tsaye yafad'a a kan jikin mahaifiyarshi yana kuka, kamar wata mace, kasan cewar shikad'ai ne d'a d'aya tilo a wurin mahaifiyarshi." Hakuri tashiga bashi tana tambayarsa abunda ke faruwa?" Gaya mata yashigayi yana kuka bai k'arasa magana ba numfashinsa yashiga d'aukewa, hankalin mahaifiyarshi yatashi matuk'a da saurita takira mahaifinshi a ka tallabeshi aka sanyashi a mota aka nufi asibiti dashi." ______________________________ Afnan ta isa gida kowa yana mamakin dawowarta domin gaba d'aya zuri'ar gidan malam Iro suna gidan Kaka suna lallashinta domin hankalinta yatashi matuk'a inbanda kuka babu abunda takeyi." Kaka na ganinta ta taso da gudu ta rungumeta tana fad'in Alhmdulillah." Afnan ina fatan baiyi maki illah ba, Kaka ta kuma fashewa da sabon kuka." Afnan ta dafata tace "daina kuka Kaka babu abunda yayi Mani, lafiya galau muka rabu dashi." Gaba d'aya suka had'a baki sukace "Alhmdulillah." Malam Iro yace "to ai bari na bugawa Sanusi waya nace gaki kindawo." Afnan ta kalli malam Iro da Kaka tace "Baba da Kaka inada magana daku, Kaka tace "Afnan bazaki bari kihutaba kici abinci," diba kigani yanda kika fad'a, kikayi dugun wuya, arzikinmu d'aya baiyi maki illah ba, mudai tsakaninmu da wannan yaro sai dai Allah ya isa." Afnan Tayi murmushi tace "Kaka kenan aiba wani aikin wahala nayiba, Malam "Iro yace fad'i maganarki Afnan muna saurarenki." Afnan ta sunkuyar da kanta k'asa idonta yacika da hawaye amma batabari kaka taganeba tace "Baba Kaka ina neman alfarma a wurinku inaso a d'aura min aure nanda kwana uku da yarima d'an sarki domin yanzun shi nakeso ba malam Nura." Tayi maganar cikin d'acin zuciya, amma a fuskartar murmushine da bai kai cikiba." Dole tayi hakan domin tasan Kaka da saurin fahimtar abu, bataso su zargi wani Abu." Kaka tace "Afnan kina da hankali kuwa?" Anya lafiyarki k'alau kuwa?" Keda ko maganar aure bakyaso anayi gabanki meya kawo kice aure kikeso cikin kwana uku?" Malam Iro yace "wannan Abu ya d'aure min kai, to baza'ayi maki aure nan da kwana ukuba, ke ko aure zakiyi cikin kwana uku har abada bazamu had'a zuri'a da mashayin giyaba kuma azzalumini." Kuka ta rushe dashi "wayyo nashiga uku kutaimaka min, Ku aura min shi." Mamaki suka shigayi musammam kaka tunda take da Afnan bata tab'a ganin tashiga wannan halinba sai yau, meke shirin faruwa da ita ne?" Meya sameta?" Afnan ta kalli malam Iro tace "Baba kajanye maganar cewa d'an giyane baza'a aura minshiba, ninaji nagani haka zan aureshi." Kaka ta daka mata tsawa tace "bazai yiwu ba." A za hannun tayi a kai tashiga kuka tana fad'in "wayyo Allah na! Nashiga uku! Kutaima keni Ku aura minshi." Gaba d'aya rik'e baki sukayi suna kallonta cike da tashin hankali, musamman Kaka da tunda take bata tab'a ganin Afnan ta fad'a cikin wannan halinba sai yau, meke shirin faruwa da ita ne ?" Tausayi tashiga bawa Kaka, da tuna da cewa marainiyace ba uba ba uba, ga wannan tashin hankalin da ya tunkarota, Ta durk'usa kusa gareta tashiga bata hak'uri, a kan ta natsu a bi komai a sannu, b'are baki tayi gaba d'aya tana kuka wiwi, tana fad'in Kaka bakison in rayu kenan, kinfison in mutu ki huta." Tun kaka na lallashinta har ta kai da rik'e kafad'arta tana jijjigata, Tana fad'in Afnan lafiya kike kuwa?" To kisani bazamu d'aura maki aure da mashayiba." Malam Iro tsaye yayi yakasa magana domin gaba d'aya abun ya d'aure mashi kai mamaki yakeyi sosai" Mik'ewa tsaye tayi tana kuka takama hanyar barin gidan, Kaka da malam Iro suka had'a baki sukace "Afnan ina zaki?" Kaka nabin bayanta tana kiran sunanta." Ina harta kai tsakar gida, sai cewa takeyi Afnan karki fita, Iro zoka kamomin ita, Bata kai k'ofar gidaba taci karo da Sanusi zai shigo gidan, Saiji yayi kaka na fad'in a ruk'o mata ita." Yasa hannunshi ya rik'e hannunta suka dawo gidan tare." Kuka Afnan takeyi wiwi kukan da takeyi ba wai dan zata rabu da kaka bane, sai ganin tanayiwa Kaka da malam Nura kallon matantu, tana tuna ya zatayi da rayuwarta idan tarasa Kaka, itace gatanta itace bangon jingina warta, bata san kowa ba a danginta sai HKaka itace Wanda idan ta ganta take mantawa da cewa ita marainiyace, Ta gwammace ita ta fara mutuwa kamin ita ta mutu, ta k'ara sakin wani kuka mai sauti." Kaka ta rik'a hannunta ta turata d'akinta ta maida k'ofa ta rufe tana fad'in "kina haukane Afnan?" Daga cikin d'akin Afnan take cewa "lafiya ta k'alau ni aure nakeso ayi min nan da kwana uku da Yarima ko nakashe kaina...."👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S* _we don't just entertain and educated we tauch the heart of the readers_ #WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM #IG PML WRITERS #https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035 #http://maryamsbello.blogspot.com *16* Dukan k'ofa takeyi sosai tana kuka, ita kad'ai tasan abunda take hangowa kanta." hankalin Kaka ya tashi sosai, ta kai zaune tareda rafka tagumi, ta Shiga tunanin yanda Afnan ta taso marainiya gaba da baya, Taso ta auri yaro mai hankali da natsuwa, Wanda zai kula da ita, ya kuma tausaya mata, saboda maraicinta." Sanusi dake tsaye ya sunkuyar da Kansa k'asa shima ranshi ya b'aci matuk'a domin ya fahimci duk abunda ke faruwa." Ajiyar zuciya ya sauke ya kalli mahaifinshi malam Iro yace "Baba ina zuwa bara nadawo." Yafita da saurinshi ransa na tafasa." Kai tsaye Club yanufa domin yasan babu inda Bassam ke zama a dai dai wannan lokacin sai can." Yayi sa'a kuma ya tarar dashi a zaune a inda yasameshi d'azu, gabanshi yaje ya zauna, giyar dake gaban Bassam ita ya d'auka ya sha." Bassam yadibeshi yace "malam kadaina shamin drink." Sanusi ya kalleshi kallon gefen ido yace "kai katurota?" Bassam ya kallashi yace "wakenan?" "Afnan mana." "Wacece kuma hakan." Sanusi ganin yayi yanaso ya raina mashi wayo, yakira waiter yace "kawo min irin tashi barasar." Waiter ya kalleshi yace "Oga mai tsadace ba irin wadda kake saya bace." Yadaka mashi tsawa yace "Kai!! Me ruwanka nace ka kawo min...." Da saurinshi waiter yace "to Oga." Ya fice." Sanusi yaci gaba da kallon Bassam yana mashi kallon tuhuma, yayi shuru yana tunanin wani abu game dashi da Afnan, amma kuma bega alamar wani abunba, sai ma firgitashi da Bassam yayi da mazan takarshi." Haka ya gama shan barasar Shi, saida ya shanye kwalba uku mai tsada, baitab'a sanin gard'in giyaba sai ranar, ashe dai ba giya yake shaba burkutu ce aka gyara ake sayar masu, sai yanzun yasan yasha abu mai gard'i." Ko kamin yagama tunaninshi, ya wai ba Bassam ba alamarsa, haka ya tashi, yanufi gida." Koda yashiga gida maganar d'ayace a kan Afnan, ita fa sai an d'aura mata aure da Yarima d'an sarki nan da kwana uku." Tsawa yada makata yace Ke! Yimana shuru kincika mana kunne da koke koke, shi wanda kikeyi domin shi, yanzun nafito wurinshi cemin yayi baima sankiba." Cikin muryar Kuka Afnan tace "wallah k'arya akeyi yasanni kuma munason junanmu, ni adaina zuwa ana tsireshi kadda ranshi ya b'aci, ni kawai a aura minshi ko nakashe kaina." Shuru kowa yayi yana nazari, domin kowa yarasa abunda zaice." Maryam tashiga d'akin da Afnan take tace "Afnan kina da hankali kuwa, kodai kinfara hauka ne?" Afnan ta jefe Maryam da wani kallo, a zuciyarta kuma tace "kema Maryam kina cikin had'ari indai ba'a aura minshiba." Sannan tace "wato harda ke kallon mahaukaciya kikeyi mun kenan?" To meye haukata a ciki dan nace inason aure?" Tanuni Maryam da hannu had'ida kai mata harara tace "dan Allah malama tashi kifita kibani wuri." Maryam tafito tana zubar da hawayen tausayin k'awar tata." Malam Iro ne yanufi d'akin Afnan d'in, yace "Afnan kiyi shuru daina kuka zamuyi magana dake." Afnan tayi shuru tana kallon Baba." Malam Iro yace "kina dai sonsa kikace ko?" Tayi saurin d'aga kai alamar "eh." Yace "daina kuka kuma ki kwantar da hankalinki za'a aura makishi." Tace "nan da kwana uku nakeso Baba." "Insha Allahu zamu aura maki shi, amma idan kika kwantar da hankalinki kikaci abinci." Kaka tayi karaf tace "toshi malam Nura da kika kawoshi kikace kina sonshi har Kika sanya aka karb'i sadakinshi ya kikeso ayi dashi." Zuciyar Afnan ta narke dataji an ambaci masoyinta taji wani sabon son malam Nura ya dirar mata, amma kuma ta dake, tace "yanzun.bana sonshi a mayar mashi da sadakinshi kawai ya hakura dani." Kaka taja bakinta tayi shuru, Sanusi saboda tausayin Afnan fita yayi domin ya fahimci duk abunda takeyi akwai dalilin da yasanyata take yinshi." A nan sukayi sallama da kaka suka tafi gida Malam Iro kuma a cewarshi gobe zaidawo ya kuma yin magana da Afnan." Washe gari har zuwa magariba ba malam Iro ba labarinshi, aikuwa Afnan tashiga kuka baci basha, ahaka ta kwana cikin tashi hankali ganin saura kwana d'aya kwana kin da Yarima ya d'ibar mata." Kuka takeyi wiwi baji bagani tana cewa Kaka "Ashe dama basona kikeyiba bakya tausayina, sai yanzun na tabbatar da cewa ni marainiyace, domin idan mahaifana suna da rai bazasu hanani abunda nakesoba." Hankalin Kaka yatashi tasanya gyalenta ta nufi gidan malam Iro, Karo taci da malam Iro shama zai nufo gidanta, Anan tashiga gaya mashi abunda Afnan takeyi, batada aiki sai kuka da fad'in maganganu marasa dad'inji, nidai Iro na hakura a aura mata Yarima tunda taji ta Amince tana sonshi." Malam Iro yace "subahanallahi." Abu dai yak'ici yak'i cinyewa, har yanzun batabar maganar Yaron nanba?" "Mutafi gidan naga ita Afnan d'in." Kuka ya tarar tanayi yace "yi shuru Afnan Yarima kikeso ki aura ko?" Tace "Eh Baba lokaci fa yana tafiya wallah mudun ba'a d'aura mana aure gobe ba to saina kashe kaina." Baba "subahallahi." Afnan basai kinkashe kankiba za'a aura makishi, kinada number wayarshi?" Tayi saurin d'aga kai alamar Eh, Baba yace to kirawo shi kice yaturo magabantanshi a d'aura maku aure gobe." Da gudu tanufi d'akinta, katinshi ta d'auko dama ta d'auki d'aya a d'akinshi da burin intabar gidanshi zatayi amfani da number shi, ta had'ashi da hukuma a kamashi, Sai abun ya juya mata." Cikin sauri ta lalubo katin a cikin jakarta, ta d'auki number tasa, tasanya a wayarta, tazo kusa da Kaka ta zauna, tashiga kiran wayar tashi, aka kuma yi sa'a tashiga." Tausayinta ya kama Kaka tashiga share kwallah, domin tasan aure ba k'aramin abu bane, bare aure cikin kwana uku." Ta d'ora wayar a kannenta tana sauraren ringing d'in da wayar keyi." "Hello ta fad'a da sanyin murya, "Ina wuni?" Bassam ya gano itace baidamu da yasan inda tasamo Numbershi ba, yafara yi mata fad'a, "ke kina da kwana d'aya kinyi shuru." meyasa kike nemana?" "Baba ne yace katuro waliyanka." Yayi murmushin mugunta yace to naji, ki tambayar min a ina za'a d'aura aure?" Baba yace "a masallacin malam k'asamu, Masallacin malam k'asamu sanannan wurine kowa ya sanshi a garin nan." Yace "A cikin unguwarku a masallacin malam k'asamu za'a d'aura min aure kike nufi? Ke kifita daga mafarkin da kikeyi." "Dan Allah karufa min asiri kayi hak'uri na shiga uku." A cikin ranshi kukan da takeyi dad'i yakeji yana fad'in ina rashin kunyar taki take?" Sannan yace "shikenan kuje can d'in tunda dama ni burina kenan in aureki zakiga abunda zan yi maki dad'in rayuwa bake bashi." Ta kashe wayar ta kalle Baba da Kaka wad'anda suma ita suke kallo cike da al'ajabi, Tace yace "yau zai turo magaba tanshi." Malam Iro yace to shikenan bari naje gidan Malam k'asimu na shaida mashi yau ko gobe a kwai d'aurin aure a masallaci." 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S* _we don't just entertain and educated we tauch the heart of the readers_ #WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM #IG PML WRITERS #https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035 #http://maryamsbello.blogspot.com *18* *ZAKUJINI KWANA BIYU SHURU BA TYPING TO KUYI HAK'URI FRIENDS HAKAN ZAI FARUNE SANADIYAR HIDIMAR BIKIN AUREN K'AUNATA DA AKAFARA, BANA SABON LOKACIN DA ZANDINGA YIMAKU TYPING AMMA DA MUNK'ARE BIKI KOMAI ZAI ZAMA DAI DAI NAGODE DA K'AUNA MY FRIRNDS* Tafiya akeyi a mota sai jiniya kakeji yana tashi, ita kuma Afnan babu abunda takeyi in banda aikin kuka." gefenta d'aya Jakadiya ce, Sai kuma matan malam Iro su biyu da babban k'awarta Maryam." Kai tsaye cikin gidan sarauta aka nufa da ita, jakadiya ce maiyi masu jagora zuwa b'angaren da aka ta nadar mata, wato b'angaren Bassam." D'akine babban d'aki Wanda yasha gyara da kayan alatu, Maryam tayi mamakin ganin daular da Afnan tashiga, Tashiga fad'i a zuciyarta "haba kai dole tace sai d'an sarki bata son malam Nura, Ashe kud'i ta gani, kai Afnan kinbani, Allah yasa kwad'ayinki kar yazama ajalinki mtsww! Taja wani dogon tsaki da ta tuna da yadda Afnan ta zubar da mutuncinta, saboda kwad'ayin kud'i da mulki, in ba haka ba a ce daga yasaceta ya kawota gidansu, idonta ya ganar mata daula da mulki shikenan kirice kice cikin kwana uku kikeso a aura maki aure dashi." Kinyiwa kanki kin zubar da mutuncinki ga d'a namiji, kin d'aurawa kanki aure cikin kwana uku saboda kwad'ayi☹ Kallo ta kuma bin Afnan dashi tana harararta cike da ban haushe, sannan taci gaba da cewa a zuciyarta, "Sauk'inki d'aya kina da kyau, da kuma shagwab'a mai ban haushi. Kuma na lura da wannan dajjijuwar data amshemu da alama zatayi kirki sosai, Ta kuma mere baki ☹ kai makwad'aici baiji dad'in kansaba." Tasamu wuri ta zauna a pallon ta shiga k'arewa ko ina na pallon kallon tace "shi mijinma ko ganinsa bamuyiba, sai gaton photonshi ne babba kana sallama shi zai yi maka maraba, K'ur zakaga yana kallonka kamar zaiyi magana, Gashi falon mai girma sosai kusan kalar kujeru hud'u a cikinsa, Kowane set an shirya shi gefe daban don tsabar b'arnar kud'i, T.V ta kai guda uku duk a falo d'aya. Hummm! Wani abun in yayi yawa ko kyau baiyi, to a cikinsu wacce zaka kalla? Wacce zaka bari? Ta kuma kallon Afnan dake zaune wuri d'aya ta wurga mata harara🙄 Afnan kuma takasa tsaida idonta wuri d'aya duk da tanayi tana kallon k'asa, Ganin photon Bassam datayi ya kuma sanyata ta tsorata, tana tuna idanunsa na mugunta masu kama da jan gauta, girmansu kad'ai sun isa kaji tsoronshi, Bud'esu da yakeyi yana zazzaresu sai taji tashiga matsanancin tsoronshi da tashin hankali tare da ita..... Maryam tadafa kafad'arta tace "Afnan gaki munkawoki gidan kud'i da mulki nasan yau zakiyi barcin jin dad'i, to kisani kidaiji tsoron Allah domin Allah baya barci, kuma shi zai sakawa Wanda aka zalunta, Malam Nura Allah yabaka lafiya, ya musanya maka da mafi alk'airi." Afnan bata tanka mata ba, sai kuka takeyi a zuciyarta Had'ida lumshi idonta k'iyayyar Yarima na kuma shigarta, da muguntarshi, A ranta sai cewa takeyi "ni mulkinsa ko dukiyarsa ba ita tasa na aureshiba, nasan mutane da dama zasuyita yimun kallon makwad'aiciya zanbiku a hakan amma dakunsa rayuwanka na ceta daga bala'i na wannan azzalumin da keda kike zargina saikinta gode min domin har ke abun yashafa, Domin da ban aureshiba wata k'ila da yanzun kina lahira". Maryam ta kuma kallonta tace "kinsan dai wannan alatun ba'a banzaba." Afnan ta mik'e tayi shigewarta b'an d'aki, Wanda da shigarta tasaki baki tana kallo, a rayuwarta bata tab'a tunanin zataga had'ad'd'an ban d'aki irin wannan ba girmanshi ya kusan girman d'aki, Tasan tunda tashigo wannan gidan k'arshenta mutuwa ce, takirata datuna da kalaman Bassam da yace "zan aureki domin in wulak'antaki zaki shiga k'angin bauta Wanda hatta bayina sai sun tausaya maki." Ta fashe da wani Sabon kuka mai sauti, ta dur k'ushe k'asa a nan tsakar ban d'akin tana k'ara tausayin kanta, Da kuma halin da masoyinta yake cikinsa a yanzun, Kuka takeyi sosai kamar numfashinta zai d'auke." Kwankwasar k'ofar band'akin shi yasa ta daina kukan da takeyi ta mik'e da sauri tana goge hawayenta." Saiji tayi ana fad'in kifito muyi sallama zamu wuce." Da saurinta ta bud'e k'ofa tafito ta rungume Matan malam iro tana kuka tasakesu ta rungume Maryam tasaki wani kuka mai k'arfi, domin ta sadak'ar wata k'ila wannan shine k'arshen ganinsu da tayi, ta kumayi alk'awalin zata dake ta d'auki duk wata wahala da za'a gana mata domin ta ceci rayunka masoyanta da 'yan uwanta." Maryam ta tab'e baki tace "kaji iyayi kukan me kikeyi hakan?" Bayan ke kikasa kanki, Kai duniya akwai abun kallo kala kala dibi yanda take kuka sai kace Wanda aka kawota dan dole, to munsan komai nidai sakeni, muyi tafiyarmu inda mukafi wayo." Haka ta rakasu har bakin k'ofa, tana zubar da hawaye, domin tana ganin kamar ganin k'arshe take yimasu, Ta dafa d'aya daga cikin matan malam Iro, tace "inna kuyafemin, kuma kucewa Kaka ta yafemin iya zaman da mukayi da ita, idan na tab'a b'ata mata rai tayafemin dan Allah." Suna gam da fita falon taji dantijuwar nan mai mutum ci wato jakadiya, tace "ranki ya dad'e ki tsaya daga nan, Ta nuna wata kuyanga tace "ke jibo kiyi masu rakiya zuwa wurin mota." Ta amsa da "to ranki ya dad'e." Haka Afnan ta koma tana kuka tashiga d'akinta, ta zauna a kan makeken gadonta, jikinta duk yayi sanyi, Saiji tayi anturo k'ofa anshigo, jakadiya ce, da masu aiki d'auke da kaya nik'i nik'i kayanta ne da tazo dasu, nan da nan suka fara shiryasu cikin d'akin da ake sanya kayan sawa." Jakadiya ta zauna d'aya daga cikin kujerun d'akin tana duban Afnan tana fara'a." Tace "yarinya meye sunanki?" Afnan tayi gyaran murya ta sauko daga zaman datayi k'asan gado ta zauna kan kafet mai taushi gaske tana magana cikin natsuwa, Sunana Afnan." Masha Allah Jakadiya ta fad'a cikin murya mai walwala." Taci gaba da cewa "nice Jakadiyar Mijinki wato Bassam kuma nice mari kiyarshi tun yana k'arami nake d'awainiya dashi da kula dashi har zuwa yanzun, Allah yasa ke.a zaki tayani tsakaninki da Allah mukula da marayan Allah." Suna cikin magana sai gani sukayi anturo k'ofa anshigo, Fulani ce fuskarta d'auke da farin ciki, tace 'yata sannu da shiguwa sabuwar rayuwa. Idan bazaki damuba inaso insan tarihinki." Anan Afnan tashiga fad'awa Fulani ko ita wacece da sunan mahaifinta da sanadiyar da yasa suka dawo Gombe da zama." Suka tausaya mata gaba d'aya najin cewa marainiya ce gaba da baya." Fulani tace Allah sarki gashi Allah ya had'aki da wasu iyayen, Inaso kizama mai hak'uri da kauda ido da zaman da zamuyi, kisani shi aure ibadane sannu a hankali zaki sanmu muma musanki Banida burin tsangwama maki nima ki d'aukeni kamar uwar da ta haifeki, inaso ki saki jiki kema nan gidanku ne, kiyi yadda zaki yi gidanku kema 'yace a nan...... Ta kalli jakadiya tace "jakadiya cigaba da lurar da ita yanda ake zaman gidan nan, ta juya ta tatafi." Anan jakadiya taci gaba da lurar da Afnan tana fad'amata k'a idodin zaman gidan sarauta." Sannan ta gabatar mata da 'yan aikinta, masu yimata hidima." Talatu 'yar aiki ta matso kusa da ita ta durk'usa tace "ranki ya dad'e sunana Talatu tare da indo itama ta matso ta durk'usa, zamu dinga yimaki hidima duk abunda kikeso mune basu kula dashi, dan haka gamu munmik'a wuyanmu dan yimaki bautar aiki kowanne irine." "Madallah." ta fad'a a ranta, tace kafin in mutu zan d'an samu canjin yanayi Dan haka zan saki raina inyi abunda da raina keso kada in mutu da bak'in ciki biyu ko na b'ata raina ba tsira zanyiba, Dan haka zan sakata in wala in bararraje, aranta take maganar." Indo tace ranki ya dad'e ruwan wanka anshirya." Ta mik'e tsaye suma sukayi saurin mik'ewa, suka isa gareta zasu tab'ata, da saurin gaske ta matsa baya tace mezakuyi?" Ta fad'a cike da tsoro." "Ranki ya dad'e zamu tayaki cire kayan ne." "A'a kubarni kuyi tafiyarku." Tuni yanayin fuskarsu ta sauya suka zube k'asa suna fad'in "ranki ya dad'e kiyi mana rai, Fulani zata b'ata mana." Zaro ido tayi waje a zuciyarya tace "wata sabuwa." "To Ku zauna can inshiga infito." A sanayye sukaje sukayi tsaye gefe guda, tashiga ban d'akin, Turarunkan wanka da bath liguid kala kala wad'anda bata tab'a ganiba, masu bala'in k'amshi, Dama ga Afnan ma abuciyar k'amshi wuri ya d'auke da k'amshi mai dad'i gaske." Ta nutse cikin K'aton bith d'in ta runtse idonta, kai wannan dad'i da suka bani anya..... Anya na gaske ne? K'ila ma gobe zan bar duniya gara ind'anji dad'i ko kad'an ne." 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S* _we don't just entertain and educated we tauch the heart of the readers_ #WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM #IG PML WRITERS #https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035 #http://maryamsbello.blogspot.com *18* *ZAKUJINI KWANA BIYU SHURU BA TYPING TO KUYI HAK'URI FRIENDS HAKAN ZAI FARUNE SANADIYAR HIDIMAR BIKIN AUREN K'AUNATA DA AKAFARA, BANA SABON LOKACIN DA ZANDINGA YIMAKU TYPING AMMA DA MUNK'ARE BIKI KOMAI ZAI ZAMA DAI DAI NAGODE DA K'AUNA MY FRIRNDS* Tafiya akeyi a mota sai jiniya kakeji yana tashi, ita kuma Afnan babu abunda takeyi in banda aikin kuka." gefenta d'aya Jakadiya ce, Sai kuma matan malam Iro su biyu da babban k'awarta Maryam." Kai tsaye cikin gidan sarauta aka nufa da ita, jakadiya ce maiyi masu jagora zuwa b'angaren da aka ta nadar mata, wato b'angaren Bassam." D'akine babban d'aki Wanda yasha gyara da kayan alatu, Maryam tayi mamakin ganin daular da Afnan tashiga, Tashiga fad'i a zuciyarta "haba kai dole tace sai d'an sarki bata son malam Nura, Ashe kud'i ta gani, kai Afnan kinbani, Allah yasa kwad'ayinki kar yazama ajalinki mtsww! Taja wani dogon tsaki da ta tuna da yadda Afnan ta zubar da mutuncinta, saboda kwad'ayin kud'i da mulki, in ba haka ba a ce daga yasaceta ya kawota gidansu, idonta ya ganar mata daula da mulki shikenan kirice kice cikin kwana uku kikeso a aura maki aure dashi." Kinyiwa kanki kin zubar da mutuncinki ga d'a namiji, kin d'aurawa kanki aure cikin kwana uku saboda kwad'ayi☹ Kallo ta kuma bin Afnan dashi tana harararta cike da ban haushe, sannan taci gaba da cewa a zuciyarta, "Sauk'inki d'aya kina da kyau, da kuma shagwab'a mai ban haushi. Kuma na lura da wannan dajjijuwar data amshemu da alama zatayi kirki sosai, Ta kuma mere baki ☹ kai makwad'aici baiji dad'in kansaba." Tasamu wuri ta zauna a pallon ta shiga k'arewa ko ina na pallon kallon tace "shi mijinma ko ganinsa bamuyiba, sai gaton photonshi ne babba kana sallama shi zai yi maka maraba, K'ur zakaga yana kallonka kamar zaiyi magana, Gashi falon mai girma sosai kusan kalar kujeru hud'u a cikinsa, Kowane set an shirya shi gefe daban don tsabar b'arnar kud'i, T.V ta kai guda uku duk a falo d'aya. Hummm! Wani abun in yayi yawa ko kyau baiyi, to a cikinsu wacce zaka kalla? Wacce zaka bari? Ta kuma kallon Afnan dake zaune wuri d'aya ta wurga mata harara🙄 Afnan kuma takasa tsaida idonta wuri d'aya duk da tanayi tana kallon k'asa, Ganin photon Bassam datayi ya kuma sanyata ta tsorata, tana tuna idanunsa na mugunta masu kama da jan gauta, girmansu kad'ai sun isa kaji tsoronshi, Bud'esu da yakeyi yana zazzaresu sai taji tashiga matsanancin tsoronshi da tashin hankali tare da ita..... Maryam tadafa kafad'arta tace "Afnan gaki munkawoki gidan kud'i da mulki nasan yau zakiyi barcin jin dad'i, to kisani kidaiji tsoron Allah domin Allah baya barci, kuma shi zai sakawa Wanda aka zalunta, Malam Nura Allah yabaka lafiya, ya musanya maka da mafi alk'airi." Afnan bata tanka mata ba, sai kuka takeyi a zuciyarta Had'ida lumshi idonta k'iyayyar Yarima na kuma shigarta, da muguntarshi, A ranta sai cewa takeyi "ni mulkinsa ko dukiyarsa ba ita tasa na aureshiba, nasan mutane da dama zasuyita yimun kallon makwad'aiciya zanbiku a hakan amma dakunsa rayuwanka na ceta daga bala'i na wannan azzalumin da keda kike zargina saikinta gode min domin har ke abun yashafa, Domin da ban aureshiba wata k'ila da yanzun kina lahira". Maryam ta kuma kallonta tace "kinsan dai wannan alatun ba'a banzaba." Afnan ta mik'e tayi shigewarta b'an d'aki, Wanda da shigarta tasaki baki tana kallo, a rayuwarta bata tab'a tunanin zataga had'ad'd'an ban d'aki irin wannan ba girmanshi ya kusan girman d'aki, Tasan tunda tashigo wannan gidan k'arshenta mutuwa ce, takirata datuna da kalaman Bassam da yace "zan aureki domin in wulak'antaki zaki shiga k'angin bauta Wanda hatta bayina sai sun tausaya maki." Ta fashe da wani Sabon kuka mai sauti, ta dur k'ushe k'asa a nan tsakar ban d'akin tana k'ara tausayin kanta, Da kuma halin da masoyinta yake cikinsa a yanzun, Kuka takeyi sosai kamar numfashinta zai d'auke." Kwankwasar k'ofar band'akin shi yasa ta daina kukan da takeyi ta mik'e da sauri tana goge hawayenta." Saiji tayi ana fad'in kifito muyi sallama zamu wuce." Da saurinta ta bud'e k'ofa tafito ta rungume Matan malam iro tana kuka tasakesu ta rungume Maryam tasaki wani kuka mai k'arfi, domin ta sadak'ar wata k'ila wannan shine k'arshen ganinsu da tayi, ta kumayi alk'awalin zata dake ta d'auki duk wata wahala da za'a gana mata domin ta ceci rayunka masoyanta da 'yan uwanta." Maryam ta tab'e baki tace "kaji iyayi kukan me kikeyi hakan?" Bayan ke kikasa kanki, Kai duniya akwai abun kallo kala kala dibi yanda take kuka sai kace Wanda aka kawota dan dole, to munsan komai nidai sakeni, muyi tafiyarmu inda mukafi wayo." Haka ta rakasu har bakin k'ofa, tana zubar da hawaye, domin tana ganin kamar ganin k'arshe take yimasu, Ta dafa d'aya daga cikin matan malam Iro, tace "inna kuyafemin, kuma kucewa Kaka ta yafemin iya zaman da mukayi da ita, idan na tab'a b'ata mata rai tayafemin dan Allah." Suna gam da fita falon taji dantijuwar nan mai mutum ci wato jakadiya, tace "ranki ya dad'e ki tsaya daga nan, Ta nuna wata kuyanga tace "ke jibo kiyi masu rakiya zuwa wurin mota." Ta amsa da "to ranki ya dad'e." Haka Afnan ta koma tana kuka tashiga d'akinta, ta zauna a kan makeken gadonta, jikinta duk yayi sanyi, Saiji tayi anturo k'ofa anshigo, jakadiya ce, da masu aiki d'auke da kaya nik'i nik'i kayanta ne da tazo dasu, nan da nan suka fara shiryasu cikin d'akin da ake sanya kayan sawa." Jakadiya ta zauna d'aya daga cikin kujerun d'akin tana duban Afnan tana fara'a." Tace "yarinya meye sunanki?" Afnan tayi gyaran murya ta sauko daga zaman datayi k'asan gado ta zauna kan kafet mai taushi gaske tana magana cikin natsuwa, Sunana Afnan." Masha Allah Jakadiya ta fad'a cikin murya mai walwala." Taci gaba da cewa "nice Jakadiyar Mijinki wato Bassam kuma nice mari kiyarshi tun yana k'arami nake d'awainiya dashi da kula dashi har zuwa yanzun, Allah yasa ke.a zaki tayani tsakaninki da Allah mukula da marayan Allah." Suna cikin magana sai gani sukayi anturo k'ofa anshigo, Fulani ce fuskarta d'auke da farin ciki, tace 'yata sannu da shiguwa sabuwar rayuwa. Idan bazaki damuba inaso insan tarihinki." Anan Afnan tashiga fad'awa Fulani ko ita wacece da sunan mahaifinta da sanadiyar da yasa suka dawo Gombe da zama." Suka tausaya mata gaba d'aya najin cewa marainiya ce gaba da baya." Fulani tace Allah sarki gashi Allah ya had'aki da wasu iyayen, Inaso kizama mai hak'uri da kauda ido da zaman da zamuyi, kisani shi aure ibadane sannu a hankali zaki sanmu muma musanki Banida burin tsangwama maki nima ki d'aukeni kamar uwar da ta haifeki, inaso ki saki jiki kema nan gidanku ne, kiyi yadda zaki yi gidanku kema 'yace a nan...... Ta kalli jakadiya tace "jakadiya cigaba da lurar da ita yanda ake zaman gidan nan, ta juya ta tatafi." Anan jakadiya taci gaba da lurar da Afnan tana fad'amata k'a idodin zaman gidan sarauta." Sannan ta gabatar mata da 'yan aikinta, masu yimata hidima." Talatu 'yar aiki ta matso kusa da ita ta durk'usa tace "ranki ya dad'e sunana Talatu tare da indo itama ta matso ta durk'usa, zamu dinga yimaki hidima duk abunda kikeso mune basu kula dashi, dan haka gamu munmik'a wuyanmu dan yimaki bautar aiki kowanne irine." "Madallah." ta fad'a a ranta, tace kafin in mutu zan d'an samu canjin yanayi Dan haka zan saki raina inyi abunda da raina keso kada in mutu da bak'in ciki biyu ko na b'ata raina ba tsira zanyiba, Dan haka zan sakata in wala in bararraje, aranta take maganar." Indo tace ranki ya dad'e ruwan wanka anshirya." Ta mik'e tsaye suma sukayi saurin mik'ewa, suka isa gareta zasu tab'ata, da saurin gaske ta matsa baya tace mezakuyi?" Ta fad'a cike da tsoro." "Ranki ya dad'e zamu tayaki cire kayan ne." "A'a kubarni kuyi tafiyarku." Tuni yanayin fuskarsu ta sauya suka zube k'asa suna fad'in "ranki ya dad'e kiyi mana rai, Fulani zata b'ata mana." Zaro ido tayi waje a zuciyarya tace "wata sabuwa." "To Ku zauna can inshiga infito." A sanayye sukaje sukayi tsaye gefe guda, tashiga ban d'akin, Turarunkan wanka da bath liguid kala kala wad'anda bata tab'a ganiba, masu bala'in k'amshi, Dama ga Afnan ma abuciyar k'amshi wuri ya d'auke da k'amshi mai dad'i gaske." Ta nutse cikin K'aton bith d'in ta runtse idonta, kai wannan dad'i da suka bani anya..... Anya na gaske ne? K'ila ma gobe zan bar duniya gara ind'anji dad'i ko kad'an ne." 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S* _we don't just entertain and educated we tauch the heart of the readers_ #WWW.PMLWRIT,ERS@GMAIL.COM #IG PML WRITERS #https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035 #http://maryamsbello.blogspot.com *19* *Banda bakinda zan iya Baku hakuri friends a kan rashin ganin typing d'ina kwana biyu, abubuwa sunta faruwa amma komai ya koma dai dai zakujini yanzun akoda yaushe* Hakan ta kammala yin wankan cikin tunani iri iri, Fitowa tayi daga toilet d'in sai k'amshi take zubawa na turarun kan wanka." Da sauri Talatu da indo sukayo kanta suka rirrik'ata suka nufi wurin da aka keb'eshi domin kwalliya, sai kirari suke zuba mata." Zaro ido Afnan tayi waje ganin sunshiga shafe mata jiki da wani kalar manshafawa Wanda bata tab'a ganin irin shiba, zuciyarta kuma tashiga fad'in "dama haka gidan sarauta yake? Ko ko dai ni akeyiwa hakan?" domin lokacin mutuwata ne yaxo?" Haka sukaci gaba da shiryata kwalliya sukayi mata ta d'aukar hankali, nan take ta canza kama kamar ba Afnan bace, sai k'amshi take zubawa." Alkibba suka Sanya mata suka zaunar da ita akan gado, had'ida jera mata kirari, daga k'arshe sukayi mata sallama da cewa yanzun Yarima zaishigo." Gabanta ne ya fad'i, idonta ya cika da hawaye, domin tasan kalar zalunci irin na *Bassam* idon har yashigo tasan bazai bartaba wata kilama yasanya bindiga ya harbeta." Kuka takeyi, da ta tuna da masoyinta Ya Sayyadi, ta kuma fashewa da kuka tana tuna ko a wani irin hali yake yanzun?" Kalmar da mahaifiyarshi ta jefeta da ita a lokacin da za'a d'aukeshi a sanyashi a mota tayita mata yawo a kai, Da take cewa "wlh muddun d'ana ya rasa rayuwarshi a kanki to kisani kema saikin bishi a inda yatafi." Kuka ta kuma fashewa dashi mai sauti, Tana fad'in "kiyi hak'uri Mama, kice kika haifi Malam Nura amma nafiki sonshi, nafikison ya rayu karya mutu, domin shine farin cikina, Nasan mutanen duniya zasuyi min kallon na yaudari Malam Nura, ba hakan bane Allah yasan abunda ke zuciyata, kuka takeyi sosai tana sambatu." Daga k'arshe ta mik'e tsaye ta d'auko wayarta a cikin Jakarta, ta lalubo number Malam Nura, tashiga kiran wayarshi, gata tashiga tana ringing amma ba'a d'aukaba, cigaba tayi da kira tana saraurare har lokacin da za'a d'auka burinta taji muryashi tasan halin da yake ciki koda zata samu sukuni a ranta." ________________________________ Malam Nura kuma tunda aka tallabeshi aka d'orashi a kan gadon asibity be kuma Sanin Inda kanshi yakeba, baci basha sai ruwa kawai ake sanya mashi, Mahaifiyarshi kuma inbanda aikin kuka babu abunda takeyi, tana tsinewa Afnan domin duk itace silar jefa d'anta kwaya d'aya tilo a cikin wannan halin." Ringing d'in da yasanya mata a wayarshi daban ne, Acan cikin kwakwalwarshi yaji sautin kiran wayar Afnan na shugowa, motsa k'afarshi yashigayi had'ida motsa hannunshi, a hankali yake bud'e idonshi, Mama na ganin hakan tayi saurin mik'ewa tsaye ta nufoshi tana hamdala, Da sauri tafita tanufi wurin likita tana shaida mashi ya farka." Wayar taci gaba da ruri k'okarin mik'ewa yakeyi ya d'auki wayar dake a jiye agefen jakar Mama amma ya kasa." Mama CE taturo k'ofa tareda likita tana fad'in ya farka docter zoka dibamin shi wlh shikad'ai gareni a duniya." Malam Nura sai zura hannu yakeyi yana nuni da wayarshi dake ta ringing alamar so yakeyi ya d'auki wayar, kallo ya koma gaba d'aya a wurin wayar, mama tayi saurin zuwa wurin wayar da niyar ta d'auka ta mik'a mashi, sai ganin sunan *Preety* tagani a kan screen d'in wayar a nan take ta fahimci Afnan ce, ta mayar da wayar ta ajiye, Malam Nura na ganin hakan yafara kiran "Mama Afnan ce, Bani na d'auka naji damuwarta, nasan halin da take ciki, Mama Nasan *Bassam* zai cutar da Afnan. Hawaye keta gangaro wa a gefen fuskarshi yana mik'a hannu ya karb'i wayar." Tsawa ta daka masa wanda tasanyashi yaja bakinshi yayi shuru taci gaba da cewa, a hir d'inka Dana kuma jin ka ambashi sunan Afnan a bakinka, Afnan tayi maka Nisan da bazaka tab'a samuntaba har abada, dan hka idan kana cireta a ranka ka cireta idan ba hakan ba zanyi mummunan sab'a maka." Likita duba minshi idan yaji sauk'i a kabamu sallama kai ko be warkeba abamu sallama mu koma gida can yayi jinyar domin na fahimci abunda ke damunshi." Anan likita yashiga dibashi, ba laifi yaji sauk'i aka rubuta masu sallama, suka koma gida zuciyar malam Nura kullam cikin k'unci da tunanin Afnan d'inshi take" ________________________________ Ita kuma Afnan takira wayarshi yayi sau d'ari amma be d'aukaba hankalinta ya kuma tashi tashiga tunanin ko ya Sayyadi ya mutu ne?" Jifa da wayar tayi sai a kan k'afar Bassam wanda shigowarshi kenan bata lura dashi ba, Sai kuka takeyi tana fad'in "nashiga uku ya Sayyadi karka mutu kabarni Wlh inasonka banga amfanin rayuwata ba idan babuka a dorun k'asa." Wani gigitancin mari taji an d'auke mata fuska dashi har sau biyu, dafe kuncinta tayi Had'ida d'a kanta sama tana kallon Wanda ya mareta koba'a fad'aba tasan Bassam ne." Bata sauke idonta daga kallonshi ba taji ya kuma sauke mata wani marin Wanda saida takai kwance." Shi kuma sai huci yakeyi kamar wani zaki." Dafe kunci tayi tana kuka tana kallonshi tana fad'in Allah ya isa azzalumi kawai me namaka?." Murmushin mugunta yayi yanufota da Sauri da niyar ya kaimata duka, tayi saurin mik'ewa tsaye tanufi hanyar fita, K'ok'arin bud'e k'ofa takeyi tajita a kulle alamar ya sanyawa k'ofar key." Tsaye tayi jikin k'ofar ganin yana tunkarota, rufe idonta tayi tana fad'in dan Girman Allah kayi hak'uri,Dan laifi nayi maka bazan sakeba." Matseta yayi a jikin k'ofar har suna iya jin fitar numfashin juna ya sanya k'afarshi mai takalmi ya take mata k'afa ya murza, Wani irin k'ara tasaki dan azaba tana fad'in wayyo Allah na k'afata." Kuma d'aga hannu yayi ya kai mata wani marin a fuska, yace wakike yiwa Allah ya isa? Marar kunya marar tarbiya, duk maganganun da kikeyi a kan kunnena, Bakisan rayuwarki bata da amfaniba sai kin wayi gari kinga nasanya fadawa sun gutsire maki k'afa da hannu, sannan zaki kuma tabbatarwa da cewa bakida amfani a doron k'asa." Ya kuma kai mata mari had'ida kuma murza k'afarta." K'ara tasaki had'ida rufe baki tana kuka, shi kuma sai kallon tsana yake mata, Can tasamu sa'arshi ta rik'a hannunshi ta gantsara mashi cizo, yayi saurin yin baya rik'e da hannu, Tabi ta k'arshin k'afarshi ta fad'a toilet tasanya key, tana fad'in "nace Allah ya isa, Kuma Allah bazai barka ka cutar daniba, azzalumi kawai mashayin giya." K'okari yakeyi ya bud'e k'ofar toilet d'in amma ya kasa, sai diba hannumshi yakeyi inda ta cijeshi wurin yayi jajir abunka da farar fata." Ganin yakasa bud'e toilet d'in kan gado ya fad'a yayi rubda ciki ranshi idan yayi dubu ya b'aci, Mikewa yayi yabud'e prege d'inshi ya d'auko robar ruwan faro mai sanyi yakai bakinshi koda zaiji zuciyarshi zatayi mashi sanyi saboda ta farfasa, Amma INA a banza domin babu abunda kesanyashi yaji yayi saurin mantawa da b'acin rai kamar giya, kuma gashi baya ajiye giya a gida saboda tsaro, gashi dare yayi da zarar yafita maimartaba zaiji tashin motarshi." Hakan yaci gaba da zubawa cikinshi ruwa mai sanyi har b'arci b'arawo yayi awon gaba da shi." Itama Afnan a can cikin toilet d'in, takurewa tayi wuri d'aya tana kuka tana kiran Kaka, har barci ya d'auketa." 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S* _we don't just entertain and educated we tauch the heart of the readers_ #WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM #IG PML WRITERS #https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035 #http://maryamsbello.blogspot.com *20* Kiraye kirayen sallar asuba ne ya tayar dasu Afnan dake makure a toilet, tayi saurin mik'ewa tsaye, had'ida furta addu'ar tashi daga barci a zuciyarta saida tasamu natsuwa sannan ta fahimci a toilet ta kwana jiya, zare zare ido ta shigayi cike da tsoro ganin cewa tabbas a cikin toilet d'in ta kwana." Shima *Bassam* mik'ewa yayi da sauri yanufi toilet domin ya d'auro alwalla yatafi masallaci, Tura k'ofar yayi yajita a rufe, Anan take ya tuna da abunda ya faru jiya, yace "wato a toilet marar kunyar yarinyar nan ta kwana kenan?" Bugun k'ofar yashigayi da karfi, Alwalla takeyi tanajinshi tak'i bud'ewa." tazo wurin wanke k'afarta taji wani irin azabar rad'ad'i a k'afar tata, wurinda Bassam ya takata jiya ne, wurin ya sulb'e yayi ja, idonta ya cika da hawaye tace "Allah shi zaisaka min duk abunda kakeyi mun mugu kawai." Dukan k'ofar yakeyi amma tak'i bud'ewa, ranshi ya b'aci, yace "duk kika kuskura na bud'e toilet d'in nan saina kankaryaki, Ji yayi tace "wlh bazan bud'eba idan kabud'e ka kasheni idan kana iyawa mugu kawai." Girgiza kai yayi cike dajin haushi, ganin zairasa sallah, yayi saurin bud'e k'ofar d'aki yafita da saurinshi yanufi massalaci da niyar idan yatafi can saiyayi arwala abunda betab'a yiba, amma muddun ya dawo saiya kuya mata hankali domin ya fahimci batada tarbiya." Jin alamar fitarshi da tayi yasanyata ta bud'e k'ofar ta lek'a kanta a hankali jikin k'ofar domin ta tabbatar yana nan ko ya fita?" Ganin alamar baya nan yafita." taja wata doguwar ajiyar zuciya, tafito tasanyawa k'ofar key." Sannan ta shimfid'a abar sallah ta tayar da sallah." Bayan ta kammala sallah." zaune take ta d'uko AlKur'ani tana karatu cikin muryarta mai taushi da dad'i." Shi kuma Bassam bayan ya kammala sallah, kai tsaye b'angaren maimartaba ya nufa, domin ya diba ko lafiya yake saboda kullum a tare suke sallah asuba amma yau bai ganshi yafitoba." Kwakwasa k'ofar d'akin maimartaba yashigayi had'ida sallama, Maimartaba najin muryan Bassam yaba shi umurni da yaturo k'ofar yashigo." Kai tsaye ya shiga d'akin had'ida sallama, ya durkusa k'asa ya gaida mahaifin nashi, cike da girmamawa maimartaba ya amsa gaisuwar tashi had'ida tsokanar d'an nashi yana fad'in "ango Mijin amarya kuntashi lafiya lafiya?" Kuma sunkuyar da kanshi k'asa yayi yace "lafiya k'alau Abbah." Hankalina har yasoma tashi rashin ganinka da banyi a masallaciba, nashiga tunani da wasiwasi Alllah yasa dai lafiya kake?" Maimartaba yayi murmushin jin dad'i kulawar da d'ansa yake bashi, Yace "da sauk'i dai Bassam domin daren jiya bansamuyin barci ba sakamakon matsanancin ciyon kai da ya matsamani amma yanzun Alhmdulullah nasamu sauk'i, kammala Sallah ta kenan kashigo." Cike da kulawa Bassam ya kalli Mahaifinshi yace "Sannu Abba bara nakira docter Ahmad yazo yadiba jikin naka." Murmushi maimartaba yayi yace "a'a Bassam kabarshi kawai nasha magani, naji sauki sosai." Hankalin Bassam bai kwantaba saida yaga maimartaba yatashi yayi wanka ya shirya, sannan sukayi breakfast a tare ya tabbatar da cewa babu abunda ke damunshi, sannan suka fito a tare, maimartaba yanufi fada, shi kuma Bassam yanufi nashi b'angarin, saida yakusan kaiwa b'angaren nashi ya tuna da Afnan, cikin ranshi yace ko ita wancan k'azamar ta fito a toilet d'in?" Tana kwance a kan makeken gadonta, barci ne mai dad'i ya figeta saiji tayi ana kwankwasa kofa, a hankali ta bud'e idonta cikin fad'uwar gaba domin A tunaninta shine yadawo, shuru tayi batada alamar tashi ta bud'e k'ofar saida aka d'auki kusan minti goma ana kwankwasa k'ofar amma batada alamar tashi ta bud'e, saida taji murya a waje suna fad'in " wata k'ila Talatu Gimbiya bata tashi daga barciba domin k'ofar a rufe take." Jin muryarsu Talatu ce, tayi saurin durowa daga kan kadon tanufi k'ofar d'akin ta bud'e masu." Ganin anbud'e k'ofar sukayi saurin zubewa k'asa suna kwasar gaisuwa had'ida zuba mata kirari." Kallo tabisu dashi had'ida nuna masu hannu alamar sutashi tsaye." Talatu tayi saurin yin magana tace "ranki ya dad'e anshirya komai akan Dinning table, munzone mushiryaki, domin yau ne zakuyi zagayar gida tareda mai girma Yarima." Gabanta ne ya fad'i jin an ambaci Yarima, amma kuma sai ta dake saboda karsu fahimci wani abu a tare da ita, tace "kuna iya shigowa ta kauce tabasu hanya suka shiga d'akin." Talatu tafad'a toilet domin had'a mata ruwanka_ Indo kuma tashiga gyaran d'aki had'ida goge goge, Tsaye tayi tana kallonsu, sai dai muryar Talatu taji tana fad'in ranki ya dad'e komai ya kammala ke kad'ai ake jira, kishiga kiyi wanka." Kallo tabisu dashi tace nagode Talatu." Suka sunkuyar da kai alamar girmamawa suka ce "ki daina yimana godiya ranki ya dad'e aikinmu dolene muyi maki bauta, Suka fita suka tsaya pallo suna jiran tafito wankan su shiryata." Cikin minti talati ta kammala wanka tafito, sunajin fitowarta suka nufota suka shiga yimata kwalliya." Kwalliya sukayi mata irin ta 'ya'yan sarauta tasha Alkyabba tayi kyau sosai suka take mata baya suka mufi wurin cin abinci da ita." Break fast ne aka shirya mata, abinci ne iri iri aka shirya mata kowane daga ciki saida aka zuzzuba mata shi a plate, Mamaki tashigayi tana fad'i a zuciyarta lallai masu kud'i sunajin dad'insu, Wannan irin daula haka da mulki inama auren soyayya ne aka yimasu?" Inama ace masoyinta ne ya Sayyadi aka aura mata suke cikin wannan daula haka." Nan take zuciyarta ta karye da ta tuna da masoyinta Malam Nura, idonta yacika da hawaye, tayi saurin gogewa saboda karsu talatu su lura da hakan." Abincin tashiga cakud'a tanaci a hankali, sai muryar jakadiya taji tanayiwa su Talatu magana tana fad'in "yauwa Talatu kunshirya ta kenan? Suka runsuna sukace mungama ranki ya dad'e, Sannan tace "ina shi Yarima yake?" Zasuyi magana kenan yak'araso wurin yace "gani Jakadiya." Ta kalleshi taganshi sanye da jallabiya ko wanka beyiba tace "ina katafi ko wanka bakayiba kuma kasan Afnan zataje gaida maimartaba kasan kuma tare zaku tafi." Sai lokacin ya lura da Afnan dake zauna akan dining table tana cin abinci, Harara ya warga mata sai a kan idon Jakadiya, A zuciyarsa kuma yana fad'in wannan Aljanar yarinya tasamu sake diba yanda takecin abinci kamar ba 'yar matsiyataba." Jakadiya tace idan ka gama hararar mutane Yarima saika wuce kaje kayi wanka muna jiranka." Kallon jakadiya yayi yace "wai Jakadiya dole ne sai anjeni wurin maimartaba dani ne? Tabashi amsa da "Eh atare zakuje domin yasanya maku albarka." Be kuma yin magana ba yasanya kai yayi tafiyarshi." Jakadiya ta maida kallonta ga Afnan tace taso kizo nan 'yata." 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S* _we don't just entertain and educated we tauch the heart of the readers_ #WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM #IG PML WRITERS #https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035 #http://maryamsbello.blogspot.com *21* Afnan ta tako a hankali ta zauna a kusa da Jakadiya." Jakadiya tace " ki natsu ki kwantar da hankalinki ki d'auki nan gidan kamar gidanku ne." Kiyi hak'uri da halin mijinki domin kuwa Yarima Baud'and'an hali gareshi, wanda ko Sarki wani lokaci yakan rasa gane kansa." Ki d'aukeni a matsayin Uwa domin tun lokacin da kika shigo gidan nan naji kinshiga raina, kuma nayaba da zab'enki da Yarima yayi a matsayinki na matar aurenshi." domin tun lokacin da Allah ya karb'i ran Mahaifiyar Yarima, nice na reneshi na kula dashi har lokacin da karatu ya rabamu dashi." Amma a kullum addu'ata d'ayace gareshi Allah yabashi mata tagari wadda zata kula da rayuwarshi domin rayuwar Yarima tana cikin hatsari a koda yaushe, kasan cewa shikad'aine d'a d'aya tilo a wurin Maimartaba, gashi kuma maraya." Afnan ta sunkuyar da kanta k'asa tana sauraren jakadiya, a zuciyarta kuma tana fad'in to ni meye nawa a ciki, aiko nima marainiyar ce amma ya rabani da kowa nawa harda masoyina ya d'aukoni ya kawoni wannan gidan, babu abunda yakeyi min sai zaluntana yana dukana." Jakadiya ta katse mata tunani da cewa, yanzun zakuje ku gaida Sarki a tare dashi." Inaso kinatsu da kyau, domin nasan kinada tarbiya." Nan Jakadiya tadinga koya mata yanda zata gaida Sarki had'ida zuba mashi kirari cikin girmamawa." Bassam kuma wanka yakeyi zuciyarshi tunkushe da jin haushi, dole saiya jera tareda Aljanar Yarinyar can suntafi fada, wai halan basusan yanda ya tsaneta bane, kwata kwata bayaso ya bud'e ido ya ganta a kusa dashi bare har su jera a tare su tafi fada a cikin bainar jama'a a nunasu a matsayin aurata." Wani dogon tsaki yaja had'ida fitowa toilet d'in yashiga shiryawa, domin yasan halin jakadiya yanzun tana fara kwankwasa mashi k'ofa, a d'aga mashi hankali a banza, akan wacan abar." Shifa ya lura tun zuwanta gidan nan kowa yafara raja'a akanta musamman Jakadiya wadda ya d'auketa tamkar mahaifiyarshi, Ya lura da yau ko break fast bata damu data tambayeshi ko yayiba sab'anin yanda take mashi a da." Ya lurada kwatakwata hankalinta baya gareshi yana wurin wancan abar." Haka ya kammala shirinsa cikin wata Alkyabba ruwan madara wadda tafito mashi da kyanshi da maxantakarshi na jinin sarauta." Jerawa sukayi a tare suna tafiya fadawa suka take masu baya suna zuba masu kirari suka rakasu har fad'a," Sarki cikin farin ciki da jin dad'i yake kallonsu yana murmushi, gaba d'ayansu suka duka gaban maimartaba, Afnan tabud'a baki a hankali tana magana cikin nutsuwa, gaisuwa take jerowa maimarta." Bassam najin hakan yasan aikin Jakadiya ne, ya tsura mata ido, ita kanta ta lura da irin kallon da yake mata amma bata yarda sukayi ido biyuba dashiba, ta sunkuyar da kanta a k'asa." Sarki yace "masha Allah Tubarakallah." Ka iya zab'e d'an sarki Ashe ni ka gada gurin iya zab'en mata." Yana maganar yana dariya. Fadawa sai kirari suke mata." sarki yace " saiki dage ki haifo mana 'ya'ya maza masu karamci irin na d'ana Bassam." Bassam ya d'auke idonshi daga gareta, a ransa yace "Allah ya tsareni ya kiyayeni ni, aurenta ma danayi kaddara ce, akwai kuma dalili....... Sarki yayi masu hud'ubba su zauna lafiya, sannan daga k'arshe ya basu umurni da sutafi." Tarigashi yunk'urin tashi tayi gaba, ganin hakan Sarki yaja hannun Bassam ya rik'e cikin barkwanci yake kallon Bassam yace "banga alamar kaci amarci daren jiyaba, mekake jira?" Murmushin da baikai cikiba Bassam ya saki yana kallon k'asa." Domin yasan mahaifin nashi da son zolaya da barkwanci." Sarki ya kuma kallon Bassam cikin zolaya yace "ni dai a iya sanina magajin sarki jarumi ne ba ragoba." Kunyace ta cika Bassam yatashi tsam yana dariya yabar fadar, shima sarkin dariya yakeyi." Da sauri take tafiya domin tasamu ta isa b'angaren nasu kamin Bassam ya yafito daga fada, domin tasan idan ta tsaya jiranshi su tafi a tare to kamin sukai ya zalunceta yayi mata illah." Kai tsaye ta isa b'angarensu a kayi sa'a Bata tarar da Jakadiyaba, Bedroom tafad'a kai tsaye ta haye a kan gado ta kwanta tana sauki ajiyar zuciya a hankali." Anan take sai tunani Kaka ya fad'o mata a rai ko a wane irin hali take a yanzun?" Can kuma taji gabanta ya fad'i da tuna da Ya Sayyadi,idonta ya cika da hawaye, wayarta ta laluba a jakarta domin takira gida." Taji bata jitaba, da Sauri tashiga lalubin d'akin har k'ark'ashin gado ko Allah zai sanya tafad'a amma bata gantaba, saima taci karo dawani k'aton kwali da alamar akwai abunda Bassam yake b'oyewa a cikinshi." 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S* _we don't just entertain and educated we tauch the heart of the readers_ #WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM #IG PML WRITERS #https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035 #http://maryamsbello.blogspot.com *22* Jawo kwalin ta shiga yi a hankali, da kyar ta samu ta jawoshi. saboda nauyin da ke gareshi, Da sauri tashiga bud'e wa domin ganin abunda ke ciki." Karo taci da kwalaben giya, cike da kwalin, Zaro ido tayi cike da Mamaki, tashiga fad'in "wato wannan mugun mutumin har a gida yake shan giyar kenan." Dogon tsaki taja, tace "Allah yaraba mu da rashin tarbiya." had'ida tallafar kwalin da kyar saboda nauyin kwalabin dake cikinsa." window tanufa sai da ta fara lek'a kanta, taga ba kowa ga alama mutane basu cika wucewa ta wurin ba, sannan ta kinkimi kwalin tajefa, saijin k'arar fashewar kwalabe kakeji." sannan ta rufe window tana murmushin jin dad'i domin ko ba komai tasan idan ya nemeta be gantaba rayuwarsa saita b'aci, ita kuma zataji dad'i idan ta ganshi a cikin wannan yanayin kodan saboda marin da yayi ta kwad'a mata a daren jiya." ta kai dubanta a k'afarta inda ya taketa ta murgud'a baki tace "Allah ya isa, azzalumi kawai, kuma duk muguntar da zakayi min a sannu zan rama." Ta hayewar ta a kan makeken gadonta barci mai dauyi yayi a won gaba da ita." Tafe yake amma ranshi idan yayi dubu ya b'aci, Zuwan da sukayi fada tare da Afnan, har sarki yake masa zancen jikoki, Allah ya tsareshi da ya had'a zuri'a da wan can marar kunyar, ko mata sunk'are a duniya yanajin ba zai tab'a son wancan abar ba mai sunfar Aljanu." Shifa a duniya babu mace da ya tsana kamar kyakkyawar mace domin a cewarsa, duk macce mai kyau babu abunda ke gareta sai mugunta." Domin yagani a wurin matan maimarta, musamman Hajiya Zainab da yayi laka'ari da dukansu tafisu kyau." Dan haka yake k'arajin tsanar Afnan a ranshi, dan haka burinshi a kullum yaga ya musguna mata, hardai idan ya tuna da hannunta da ta d'aga ta kwad'a mashi mari. A gaban bainar jama'a." B'angarensu ya nufa da saurin shi, domin rayuwar shi ta farfasa takeyi babu abunda ke wanke masa rayuwa yaji sanyi, sai giya." Bebi takan kowa ba, bedroom ya fad'a kai tsaye idonshi rufe bema lura da ita a kwance tana barciba, K'arkashin gado yashiga dibawa amma wa yam, babu abunda ya ajiye da sunan b'oyo, dibe dibe yashiga yi idonshi ya rikid'e ya koma launin ja, yasan babu Wanda zai iya yimashi bincike ya gano inda ya ajiye abarsa sai Afnan domin ya lura idonta a tsaitsaye suke cike da rashin kunya." D'aga rinannun idonshi yayi, Yaci karo da ita kwance akan gado tana barci." Ya matsa kusa da ita cikin zafin rai, yana kallon halittar da Allah yayi mata... Cikin zafin nama yajawo hannunta ya d'aga hannu ya kwad'a mata mari." A firgice ta bud'e idonta tsoro na tashin hankali ya bayyana a fuskarta, tayi k'arfin halin d'aga kai ta kalleshi dafe da kunci idonta cike da hawaye tace Tace "lafiya?" Me namaka?" Kallonta ya kuma yi cike da tsana da jin haushi, yace "OK tambayata ma kikeyi saboda rain in hankali, ya kuma d'aga hannu zai kuma kwad'a mata wani marin ta goce besa metaba." Yashiga cewa ina ajiyar da nayi a k'ark'ashin gado?" Kallonshi tayi tace "wace irin ajiya kuma?" Nuna mata wurin yayi yace "a can na ajiye ina kika kai min kayana?" Kamota yayi ya mikek'ar da ita tsaye ya matseta gam a bango, Yana tambayarta ina takai mashi kayanshi?" Matsar da yayi wa hannunta ne ya sa ta yin hawaye, tare da kai d'ayan hannunta ta rik'e tana fad'in "Wayyo hannuna nashiga uku." Yasaki hannun nata tareda ture ta ta fad'a kan gadon, kuka taci gaba dayi, a hankali tana kuma bashi hak'uri, domin ta ganshi a yanayin da bata tab'a ganinshi ba."👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S* _we don't just entertain and educated we tauch the heart of the readers_ #WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM #IG PML WRITERS #https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035 #http://maryamsbello.blogspot.com *23* "Kifad'a min inda kika kai mun ajiya ta kona b'anb'ala maki hannu." Kuka ta kuma fashewa dashi, tana fad'in ban san in da ka a jiye kayan ka ba, ni ka daina tambaya na." Kuma kusan to ta yayi yana zare idonsa, kamar ya had'iye ta, yakeji saboda jin haushi." Amma hakan bai sa ta daina ce masa ita bata ga kayan sa ba." Fita yayi yana huci, tana ganin ya fita, Ta kalli hannun ta wurin da ya rik'eta, wurin yayi jajir sai masifar zafi yake mata." Wani sabon kuka ta fashe dashi, tana fad'in "wai mutumin nan yasan Allah kuwa?" Muguntarsa ta yi yawa, a kullum burin shi yaga ya illatata, yayi mata tabo ajiki." Cigaba tayi da kuka, Talatu ce ta turo k'ofa tashigo, domin duk abun da ke faruwa a kan idon ta." tazo kawowa Afnan kayan motsa baki, Da Sauri ta koma da baya, Allah yatsare basuyi ido biyu da Bassam ba." Matsota tayi ta durk'ushe k'asa ita ma hawaye sai fita yakeyi a idonta, sai ka ce ita a ka yiwa." Afnan na ganinta tayi saurin mik'ewa tsaye a firgice, Tana fad'in ina yake?" Talatu tace "ya tafi ranki ya dad'e." Afnan ta kuma rushewa da kuka, taci gaba da cewa, Sai ya kashe ni yau d'in nan in huta da wulak'aci da azzabtar da ni da ya keyi." Hannun ta Talatu ta rik'e tana dibawa, tace "ranki ya dad'e wannan shaidar fa?" Kukan ta ya tsanta tace " so yake ya gama b'ata min jiki da tabo, So yake yaga ya in latani sannan ya rabu dani." Mulki hauka ne, ko saura ta hauka ce, Gara ma yasa a kashe ni ta, idon ba hakan ba, zan ganar dashi mulkin macce a kwai banbanci sosai, Domin bazanci gaba da d'aukar wulak'ancinsa ba, sai dai yayi gun duwa gun duwa da naman jikina." _____________________________ Cikin *Kunar Zuci* Bassam ya fita, kai tsaye chilly ya nufa, mashayar giya." Basma yaci karo da ita zai shiga, ita kuma zata fita." Kallon juna suka shigayi, cikin yana yin kuka ta rungume shi." Bassam na ganin hakan ya zanye ta daga jikinshi cikin dabara suka nufi gefe d'aya inda mutane basa wuce wa." Basma ta fad'a a k'irjinshi ta fashe da kuka, tana fad'in "meyasa ka yau dare ni Prince?" Kasan kai kad'ai nake so, kai kad'ai na mallakawa zuciya ta da jikina, amma kai ne mutum na farko da kafara yaudara ta." Banta b'a sanin ko wane d'a namiji ba, sai a kanka, ka shayar da ni zumar soyayyar ka, wadda duk namijin da na tunkara, bayan rashin ka danayi, tamkar 'yar uwata mace nake d'aukar shi." Prince mena maka?" ka yau dare ni?" Kamanta da ni, daga k'arshe sai dai naji labarin auren ka a gari?" Share mata hawaye ya shiga yi, cikin sigar lallashi, yana d'an dukan bayan ta, alamar tayi hak'uri tayi shuru." Sannan tayi shuru ta d'aga kan ta, suka yi ido biyu, sannan ya samu da mar yi mata magana." "Basma ki natsu ki saurare ni, ki kuma fahimce ni da kyau." Auren da kikaji labari nayi, banyi shi ne ba domin na yau dareki, Nayi shi ne domin d'aukar fansa." Sannan kuma na k'unta tawa rayuwar wasu masoya." Har ga Allah bana son matar da kike cewa wai na aure ta, domin kwata kwata bata d'aya daga cikin jerin matan da nake mafarkin aure" Sannan kuma yin aure na bashi ne yan kewar alak'a ta da ke ba." Basma, ke tawa ce ni naki ne, idan Allah ya k'addari ki zama mata ta, zaki zama." share mata wasu 'yan gun tayen hawaye yashiga yi, yana kuma kwantar mata da hankali, A nan take ya mantar da ita b'acin rain dake damun ta." Fira sukeyi mai cike da so da k'auna, mussam Basma, domin Bassam biye mata kawai yakeyi domin ya samu ya rabu da ita lafiya." Domin ko giyar wake yake sha baya jin zai iya auren ta, Macce da suka had'u a Club, yana ma kula tane, saboda yaga tana yi mashi wani mahaukacin so, Amma dan tsabagen muna furci irin na mace, harda wani kuka "wai ya san dai shi kad'ai ta fara kulawa." Koda ya fara ma'amala da ita, tamkar k'ofar text yakejin, haka nan kawai yake biye mata." [3/5, 4:34 PM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S* _we don't just entertain and educated we tauch the heart of the readers_ #WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM #IG PML WRITERS #https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035 #http://maryamsbello.blogspot.com *23* "Kifad'a min inda kika kai mun ajiya ta kona b'anb'ala maki hannu." Kuka ta kuma fashewa dashi, tana fad'in ban san in da ka a jiye kayan ka ba, ni ka daina tambaya na." Kuma kusan to ta yayi yana zare idonsa, kamar ya had'iye ta, yakeji saboda jin haushi." Amma hakan bai sa ta daina ce masa ita bata ga kayan sa ba." Fita yayi yana huci, tana ganin ya fita, Ta kalli hannun ta wurin da ya rik'eta, wurin yayi jajir sai masifar zafi yake mata." Wani sabon kuka ta fashe dashi, tana fad'in "wai mutumin nan yasan Allah kuwa?" Muguntarsa ta yi yawa, a kullum burin shi yaga ya illatata, yayi mata tabo ajiki." Cigaba tayi da kuka, Talatu ce ta turo k'ofa tashigo, domin duk abun da ke faruwa a kan idon ta." tazo kawowa Afnan kayan motsa baki, Da Sauri ta koma da baya, Allah yatsare basuyi ido biyu da Bassam ba." Matsota tayi ta durk'ushe k'asa ita ma hawaye sai fita yakeyi a idonta, sai ka ce ita a ka yiwa." Afnan na ganinta tayi saurin mik'ewa tsaye a firgice, Tana fad'in ina yake?" Talatu tace "ya tafi ranki ya dad'e." Afnan ta kuma rushewa da kuka, taci gaba da cewa, Sai ya kashe ni yau d'in nan in huta da wulak'aci da azzabtar da ni da ya keyi." Hannun ta Talatu ta rik'e tana dibawa, tace "ranki ya dad'e wannan shaidar fa?" Kukan ta ya tsanta tace " so yake ya gama b'ata min jiki da tabo, So yake yaga ya in latani sannan ya rabu dani." Mulki hauka ne, ko saura ta hauka ce, Gara ma yasa a kashe ni ta, idon ba hakan ba, zan ganar dashi mulkin macce a kwai banbanci sosai, Domin bazanci gaba da d'aukar wulak'ancinsa ba, sai dai yayi gun duwa gun duwa da naman jikina." _____________________________ Cikin *Kunar Zuci* Bassam ya fita, kai tsaye chilly ya nufa, mashayar giya." Basma yaci karo da ita zai shiga, ita kuma zata fita." Kallon juna suka shigayi, cikin yana yin kuka ta rungume shi." Bassam na ganin hakan ya zanye ta daga jikinshi cikin dabara suka nufi gefe d'aya inda mutane basa wuce wa." Basma ta fad'a a k'irjinshi ta fashe da kuka, tana fad'in "meyasa ka yau dare ni Prince?" Kasan kai kad'ai nake so, kai kad'ai na mallakawa zuciya ta da jikina, amma kai ne mutum na farko da kafara yaudara ta." Banta b'a sanin ko wane d'a namiji ba, sai a kanka, ka shayar da ni zumar soyayyar ka, wadda duk namijin da na tunkara, bayan rashin ka danayi, tamkar 'yar uwata mace nake d'aukar shi." Prince mena maka?" ka yau dare ni?" Kamanta da ni, daga k'arshe sai dai naji labarin auren ka a gari?" Share mata hawaye ya shiga yi, cikin sigar lallashi, yana d'an dukan bayan ta, alamar tayi hak'uri tayi shuru." Sannan tayi shuru ta d'aga kan ta, suka yi ido biyu, sannan ya samu da mar yi mata magana." "Basma ki natsu ki saurare ni, ki kuma fahimce ni da kyau." Auren da kikaji labari nayi, banyi shi ne ba domin na yau dareki, Nayi shi ne domin d'aukar fansa." Sannan kuma na k'unta tawa rayuwar wasu masoya." Har ga Allah bana son matar da kike cewa wai na aure ta, domin kwata kwata bata d'aya daga cikin jerin matan da nake mafarkin aure" Sannan kuma yin aure na bashi ne yan kewar alak'a ta da ke ba." Basma, ke tawa ce ni naki ne, idan Allah ya k'addari ki zama mata ta, zaki zama." share mata wasu 'yan gun tayen hawaye yashiga yi, yana kuma kwantar mata da hankali, A nan take ya mantar da ita b'acin rain dake damun ta." Fira sukeyi mai cike da so da k'auna, mussam Basma, domin Bassam biye mata kawai yakeyi domin ya samu ya rabu da ita lafiya." Domin ko giyar wake yake sha baya jin zai iya auren ta, Macce da suka had'u a Club, yana ma kula tane, saboda yaga tana yi mashi wani mahaukacin so, Amma dan tsabagen muna furci irin na mace, harda wani kuka "wai ya san dai shi kad'ai ta fara kulawa." Koda ya fara ma'amala da ita, tamkar k'ofar text yakejin, haka nan kawai yake biye mata." [3/5, 4:34 PM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S* _we don't just entertain and educated we tauch the heart of the readers_ #WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM #IG PML WRITERS #https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035 #http://maryamsbello.blogspot.com *24* Haka ya samu da kyar ya lallashi Basma tare da kwatar mata da hankali da cewa idan Allah ya rubuto zasuyi aure tofa zasuyi shi." Bayan Basma ta tafi." ji yayi gaba d'aya komai ya fice mashi a rai, Giyar ma yaji ba ya son sha." Iyar da shigewa yayi cikin chilly d'in, ya sayi barasar da yake gurin baki d'aya irin wadda yake sha." yasa aka jera masa ita a bayan but d'insa." Yashiga mota ya nufi gida da sak'e sak:e a ransa.' " tabbas dole ne ya canza d'aki, Wanda zai dinga ajiye sirrinsa, domin ya fahimci wannan aljanar yarinyar su take tadinga shige masa a hanci." Yana tsayar da mota harabar gidan, fadawa suka taso kansa suna yimashi kirari, Kud'i ya fito dasu 'yan dubu dubu yashiga zubar masu. Yayi hakan ne dan su rabu dashi karsu hango abunda ke but d'inshi." Ai kuwa da gudu suka shiga rugu guwar tsintar kud'in basu kuma bi takan shiba, Kuma matsawa yayi da motar shi kusa garesu, saiti d'aya Window d'akin nashi, Nan yakira wani Amintancen Bafadensa, Wanda ya yarda dashi, ya kuma Amince masa, suka shiga d'aukar barasar ana shigar masa da ita ta bayan k'ofa, ba tare da kowa yasani ba, hankalinsa ya kwanta." _______________________________ Washe gari, sarki da Bassam, suna break fast, domin al'adar sarki ne baya cin abinci da kowa sai da tilon d'ansa ta nan yake jin damuwar d'an nasa." Afnan ce tashigo cikin shiga ta alfarma, ta durk'usa ta gaida sarki cikin girmama wa." Kallo maimartaba yabita dashi cike da jin dad'i ya amsa gaisuwarta." domin tunda ya sanya ido ya ganta a matsayin matar d'ansa, yaji ya yaba da tarbiyar ta da kuma na tsuwarta, Sannan duk ya kalle fuskarta sai yaga tana yi mashi kama da wani babban aminin shi wato Alhaji Ibrahim Wanda yayi rashin sa shekaru da suka wuce", Wanda akoda yaushe idan ya tuna shi zaiji ba dad'i a ransa." saboda ke warshi da ke damunshi." Bassam kuma na kishingid'e gefe d'aya ga fulalluka ya jera yana cin dabino, Ko kallon bata ishisa ba, Sai cewa yake lallai yarinyar tasamu sake, har fada take zuwa gaida maimartaba dan tsabagen muna furci." Can kuma ya d'aga kai sukayi ido biyu da ita, Saiya tuna da lokacin da tad'aga hannu ta mareshi" Tuni haushin ta da takai cinta ya cika mashi zuciya, Nan da nan nishad'insa ya kau, ya juya masu baya." Shi kuma sarki sai fira yake jan Afnan yana yi mata tambayoyi ." Jin haka da Bassam yayi, yaji baya iya zama wurin, Mik'ewa yayi ya bar wurin." sarki kuma ya lura da yanayin sa, ya kuma fahimci tambas akwai abunda ke damunsa, ya kyaleshi bai ce masa ko mai ba." Maimartaba yaci gaba da jan Afnan da fira, domin yanaso ya fahimci wani Abu game da ita." Fitar da yayi daga fada kai tsaye d'akin shi ya nufa Wanda ya koma babu wanda ya isa ya shigesa sai shi kad'ai." Sai da ya fara sanyawa d'akin key sannan, ya bud'e prege ya d'auko kwalbar giyar shi ya shiga sha, domin duk lokacin da yayi tuzali da fuskar Afnan sai ya tuna marin da tayi mashi, zaiji rayuwarshi tana suya, babu abunda yake wanke masa b'acin rai kamar giya." Haka Afnan ta kamalla fira da Maimartaba,daga k'arshe yq bata izini taje ta huta." Tafiya takeyi sai d'in girsa k'afa takeyi inda Bassam ya taka ta har yanzun wurin ciyo yake mata ga kuma hannunta shima da yake mata zugi." gab da zata shiga d'akin barcinta, taci Karo da Jakadiya tare da indo sunfito daga wani d'aki, Jakadiya ta lura da d'in gisa k'afar da takeyi, Ta rik'o hannunta mai ciwon tana kallo, Cikin mamaki, tace Afnan meya sameki a hannu da k'afa? Zuciyar Afnan ta k'arye, a nan take ta fashe da kuka." Jakadiya ta juya ta kalli indo domin tasan suke kula da lafiyar ta, Tace "indo me ya same ta? Tuni indo ta zube k'asa tana inda inda, bata iya cewa ga abunda ya faruba, Domin Bassam ya fi k'arfin a kai k'ararsa, domin sanin halinsa." Afnan ta raunana muryarta tace "Bassam ne !" Jakadiya ta dubeta cike da mamaki, tace "Bassam ya jimaki?" akan me?" Ta kuma fashewa da kuka tace " yana ta tambayata ajiyarsa dan nace bangani ba shine yayi ta buguna." Jakadiya tayi ta lallashinta, taja ta tashigar da ita d'aki tayi ta kwantar mata da hankali, sannan tafito tabata wuri domin ta huta." Jakadiya tarasa gane abunda ke tsakanin Bassam da Afnan." Tayi juyin duniyar nan Afnan tak'i bari ta gano wani Abu a tsakanin su, haka shima Bassam." Dan haka ta d'auki alwashin sai ta yi k'ok'ari ta gano abunda ke tsakaninsu, cikin hikima irin tasu." Zata yi k'ok'arin hana shi dukanta dan kada yajiwa yarinyar mutane ciwo, saboda jikinta baiyi kama da na duka ba." _____________________________ Jin k'arar bud'e k'ofa dayaji yasan yashi yin saurin mik'ewa ya d'auki kwalbar barasarsa ya b'oye a bayan kujera, domin yasan babu Wanda ya isa ya shigo masa d'aki sai jakadiya, Wanda yake jinta tamkar mahaifiyarshi.' Jakadiya ce ta shigo, ya saki murmushin dole. Yace " Anna nemana kikeyi?" Anna shine sunan da yake kiranta dashi tun yana yaro." Ta kalleshi babu wasa a fuskarta, tace "Eh." Sannan taci gaba da cewa wace Ajiya ce kake nema?" Tambayar tazo masa bazata, yarasa abunda zai ce, shuru yayi." Anna ta dibeshi tace "Akan me zaka doki Afnan har kaji mata ciwo?" Jin an ambaci sunan Afnan nan da nan ya b'ata fuska, yace 'ni ban dake taba." "Haka kace?" Afnan CE zatayi maka k'arya?" To shaidar da nagani a k'afarta da kuma hannunta, ta meye?" Shuru yayi yana susar kai." "Haba Bassam akan ajiyarka ta banza, zaka doke matarka har ka jimata ciyo?" Tun kana k'ara minka nasanka da tausayin 'ya mace Bassam meyasa kake son k'untatawa Yarinyar nan ne?" Sunkuyar da kansa yayi yace "kiyi hak'uri bazan sakeba." "Ita dai zaka bawa hak'uri, Tunda aka kawota gidan nan na lura baka damu da itaba, idan kasa k'afa kafita sai kaga dama kake dawowa daga k'arshe ma karaba d'aki da ita." To idan baka kyautatawa matarka ba, ni zanfita daga lamarinka innemi alfarma wurin maimartaba ya canza min wurin zama." Saurin d'aga kai yayi cikin tashin hankali, yayi saurin matsowa kusa da ita, Yace " Haba Anna daina fad'ar hakan don Allah daga yanzun ba zan sake ba wallahi." Fita tayi tace " Allah yasa ka gyara." Tana fita Bassam ya d'auko barasarsa yaci gaba da sha, Yana fad'i a zuciyarsa zai ganar da yarinyar nan shi ba'a kai k'ararsa, lallai ma yarinyar nan saina koya mata hankali." _________________________________ A b'angaren *Malam Nura* kuma........ *Wash hannu na nagaji* [3/5, 4:34 PM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S* _we don't just entertain and educated we tauch the heart of the readers_ #WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM #IG PML WRITERS #https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035 #http://maryamsbello.blogspot.com *25* *Malam Nura* kuma Alhmdulillah, Sauk'i yasa mu, ya kuma san yawa zuciyar shi dan gana." Amma kuma, a kullum cikin tunin Afnan d'in shi yake." Domin a koda yaushe yana sanya ido akan Afnan d'inshi zata dawo gare shi." Domin yasan Afnan shi take so, ba Bassam ba, kuma A kwai babban dalilin da ya sanya ta Amince da Auren Bassam." Dan ya shai dawa kansa cewa, a duniyar nan idan aka cire Kaka to babu wanda Afnan take so sama da shi." Dan haka a kullum yake sanya zuba ido zata dawo gare shi." Dan haka kullum yana gidan *Kaka* Babu abun da ke raba shi da gidan *Kaka* sai barci, sai kuma idan ya tafi wurin aiki." Domin zama gidan *Kaka* yana k'ara d'ebe mashi kewar Afnan, d'in shi, Musammam idan yayi tuzali da d'akin ta, Wanda tayi rayuwa a cikin sa, Sannan kuma *Kaka* bata da firar da take masa sai ta Afnan, wata firar yayi dariya wata kuma yaji wani sabon son ta, da son yasan halin da take ciki a yanzun." *KAKA* Kuma tunda akayi auren Afnan kullum sai maimartaba ya aiko fadawa, da kayan abinci, da cefa ne, da duk wani Abu na kyauta tawa, rayuwarta, da ita da malam Iro." Sannan kuma daga k'arshe yace "a sheda mata, jikan yarta, tana cikin k'oshin lafiya, zai san ya ranar da fadawa zasu zo a d'auke a tafi da ita taga Afnan." Sai a lokacin hankalin Kaka da Malam Iro ya kwanta ganin hidimar da Sarki yake masu da kansa, Hakan ya kuma tabbatar masu da cewa Afnan tana cikin k'oshin lafiya da kwanciyar hankali, Hankalin *Kaka* ya kwanta tasaki jikinta tana cin arziki daga gidan Sarauta." ______________________________ Gida Wanda ya amsa sunan sa, gida ne irin na 'ya 'yan sarauta, kai ko a cikin 'ya'yan sarauta 'ya 'yan gata akeyi wa wannan kalar ginin gidan." Sarki ne ya d'ebi wani babban fili a cikin yan kin cikin gidan sarautar ya sanya aka ginawa d'an sa kwaya d'aya tilo, Yarima kuma sarki mai jiran gado, domin yaci Amarci tare da gimbiya Afnan." Gida ne Wanda Sarki da kansa yake zuwa domin yaga shirin da ake tsarawa a cikin gidan." Tun a waje zaka san an kashi dukiya, saboda masu tsaro ne, da wad'an da zasu kula da Yarima tare da gimbiya, ga sunan birjik, a ko ina kowa na hidimar gabansa." A babban k'ofar da zaka shiga anyi babban gate an buruta sashen *Yarima Bassam Ahmad Moh'd* Daga can gefe d'aya kuma sashen Afnan ne tare da kuyan ginta masuyi mata hidima." Wannan aiki ya yiwa Bassam dad'i, koba komai, nashi b'angare da ban yake, yanda zai ci ka renshi babu babbaka yan da ransa yake so batare da sa ido ba ko kuma ta kura." Afnan kuma ta k'ank'ame Jakadiya sai kuka take yi, domin kuwa Sarki yace" bada Anna za'a koma ba, ita tayi zamanta a tsohon gida, domin ta kula dashi." Anna sai hak'uri take ba Afnan da cewa "ai ba rabuwa sukayi ba, kullum zata dinga zuwa tana diba lafiyar su, kasan cewar Anna ta sanya ido akan su ta fahimci babu jituwa tsaka ninsu, Dan haka ta d'auki d'amarar sai ta sanya jituwa a tsakanin su, cikin hikima da daba ra." Hakan suka tare a sabon gidan, inda gaba d'aya an zuba sabbin ma'aika ta da kuyangi." Bassam na b'an garen shi, ita ma Afnan tana b'an garin ta, Gidan yayi wa, Afnan kyau matuk'a, sai dai matsala d'aya babu kwanciyar hankali." Kwanan su d'aya a gida tajita a takure, gashi gaba d'aya ma'aikan ta da aka zuba Bata wani saba dasu ba." Fitowa tayi domin ta zagaya gidan, ta d'ebewa idon ta kewa." Wani b'angare tagani a can daban, Wanda aka rubuta masa sashen "Yarima Bassam Ahmad moh'd." Get d'in wurin ya k'awatar da ita sosai, sai ta tsinci kanta da son shiga taga yan da b'angaren nasa yake." Tafiya takeyi a hankali har ta isa bakin get d'in taja ta tsaya, domin a tunanin ta babu Wanda yasan ta a cikin basu gadin k'ofar." Saiji tayi d'aya daga cikin su,yace "ranki ya dad'e barka da zuwa, yanzu yan zun nan kuwa yarima yafita." Ajiyar zuciya taja tace " nasani dama akwai abun da zanyi a ciki." Suka bata hanya ta Shige, tun daga hara bar b'angaren Afnan ta fara zuba ido tana kallo, a zuciyarta tana fad'in cab lallai masu kud'i suna abunda suke so." Wata k'ofa tagani a ruf'e, wadda abun da aka rufe k'ofar dashi abun ka tsaya kayi ta kallo ne." Cikin rashin tsoro ta murd'a murfin k'ofar sai gani tayi ta bud'e, Sai da ta fara lek'a k'anta, domin ganin ko dai Bassam na ciki, cewa yayi ace baya nan." Bata hango kowa ba, sannan ta shiga, har da 'yar Sallamarta d'auke a bakinta cikin siririyar muryan ta." Mutuwar tsaye tayi ganin had'uwar falon, tsayawa lissafa abun da ke cikin falon b'ata lokaci ne, domin duk yanda naso na zayyane maku shi masu karatu, bama zan iyaba lol😜 Tafiya kawai take a falon tana kallo, tana fad'in Aljannar duniya, tana jinjinawa Sarki, sai yanzun ta tambatar da maimartaba ba k'ara min so yake yiwa Bassam ba." Wasu k'ofofi ta hango har guda uku da alamar dukan su bedromm ne, sai ta tsinci kanta da son shiga kowa ne daga cikin d'akin domin ganin abun da ke cikinsu." Bedromm na farko ta fara bud'ewa a hankali, ta fara lek'a kanta, ganin bata ga kowa a cikinsa ba, yasa ta kutsa ta shiga kai tsaye." Mamaki ta shiga yi, tabbas an zuba dukiya wurin nan, tunda Allah ya halicce ta, bata tab'a ganin kayan d'aki irin wad'an nan ba." Wani k'aton fridge taga ni a gefe d'aya Wanda yaja han kalinta domin frege d'in ya matuk'ar burge ta." Wurin fridge d'in ta nufa tana kallo, hannun ta tasanya ta bud'e shi domin ganin abunda ke cikinsa." Gabanta ne ya fad'i da taci karo da kwalaben giya Jere rai ras a ciki, Kallo tabisu da shi ta rik'e Baki sannan tace "wato mutumin nan har yanzun bai daina shan giyar nan ba kenan." Cire Alkyabbar jikinta tayi, tashiga kwasar kwalaben giyar tana jefawa ta window sai da ta kwashesu gaba d'aya ta rufe frege d'in sannan ta d'auki Alkyabbatar zata sanya kenan, taji anturo k'ofa anshigo." D'aga kanta da zatayi sukayi ido biyu da Bassam, shima ita yake kallo cike da mamakin abunda ya kawota sashenshi kuma har cikin bedroom d'in shi." Tsaye yayi yana Kallon ta cike da tuhuma, Ita kuma jikinta sai rawa yakeyi, bata San lokacin da tayi jifa da Alkyabbar dake hannun taba, tashiga jada baya baya, cike da tsoro, domin ta San yau k'aryanta ta k'are Bassam kasheta kawai zaiyi ya binne gawar ta babu Wanda yasani, A nan take ta fashe da kuka cikin muryarta ta shagwab'a tashiga fad'in "wayyo *Kaka* ki yafe min yau wa'adin kwanakina ya k'are duniya." Kallonta yaci gaba dayi, sannan a hankali yashiga takowa yana zuwa wurita." Ja da baya tashi gayi tana fad'in "Dan Allah kayi hak'uri tsotsayi ne da k'addara suka kawoni nan, Dan Allah kayi hak'uri." Beyi magana ba sai kuma matso ta yakeyi tana ja da baya, gaba d'aya ta manta da kayan da ke sanye a jikinta, riga da siket ne, na less d'unkin yayi matuk'ar kama jikinta, ya matseta sosai musamman a kan k'irjinta, ga Afnan Allah ya hore mata dukiyar Fulani." [3/5, 4:35 PM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S* _we don't just entertain and educated we tauch the heart of the readers_ #WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM #IG PML WRITERS #https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035 #http://maryamsbello.blogspot.com *26* Saida ta dangane jikin bango, sannan ta tabbatar da ba wata hanyar tsira." sai kuma kusan to ta yakeyi idon shi na kan k'irjinta, da yatafi da hankinshi." Lura tayi da inda yake kallo tayi saurin kallon kanta, sai a lokacin ta tuna da kayan dake sanye a jikinta, gaba d'aya rabin k'irjinta a waje yake Gasu sun cika masha Allah."😎 Hannu biyu tasanya ta rufe inda yake kallon." Ganin ta lura da hakan yayi saurin basarwa, ya matso dab da ita ya had'ata a bango, gaba d'aya suna iya jiyo saukar numfashin junansu, ya kuma had'e fuska babu wasa a fuskarshi." Yace "uban waye ya kawoki sashe na?" Kuka ta fashe dashi tace dan "Allah kayi hak'uri tsotsayine." Tsawa ya daka mata, wadda ta San yata saurin zabura." Yaci gaba da cewa, "wato kinsaba da biyar maza, kinsaba taraiya da wannan ustazun saurayin naki, Ashe Allah a baki fir'auna a zuci, kunsaba tambad'ewar Ku, da lalatarku, Dan haka koda yaushe kuna tare kuna manne da junanku." Shine kin rabu dashi yanzun bakida abokin lalata. Shine kika biyoni har sashena wato kinkawo kanki kenan inyi abunda naga dama dake kenan?" Saboda baki iya hak'uri da dangana idan bakiji d"a namiji a kusa dakeba kuna shek'e ayarku." Wani kuka ta fashe dashi mai sauti tana fad'in Wallah k'arya kake yimin ni ba 'yar iska bace, kuma Allah sai ya saka min k'azafin da kayi min." Mari ya kai mata a kunci, had'ida buge mata Baki, yana "cewa wakike yiwa Allah ya isa?" Idan ba hakan bane meye ya kawoki sashena, so kikeyi a Sosa maki inda yake maki k'aik'ayi, kuma ni Sam bakya cikin jeren matan da nake so bare har nayi sha'awarsu." Amma yau saikin banbance aya da tsakuwa, domin idan kinji ana yiwa wasu matan fyad'e to yanzun a nan shi zan maki", Yanda bazaki tab'a jin sha'awar wani d'a namiji ba, bare har ki dinga bibiyarshi har d'akinsa, domin ya kwanta dake, jarababbiya kawai." Kuka take yi, sosai tana fad'in don girman Allah kayi hak'uri, Wallahi ni ba 'yar iska bace, karka b'ata min rayuwa." K'ok'arin cire rigar jikinsa yake, yana fad'in karya kikeyi, ke ko ba 'yar iska bace, yau sai kin gane ko waye Yarima Bassam wadda har kike iya d'aga wannan matancen hannun naki ki, mareshi." K'okarin zare rigar shi taga yanayi, cikin tashin hankali, wani k'arfi yazo mata, ta cimuimuye shi, da rigarshi, tana k'ok'arin sanya hannunta biyu ta jefa shi a kan gado ta tsere." Kokawa sukeyi, tana k'ok'arin guduwa, sai jinta tayi gaba d'aya sun fad'a a kan makeken gadon." A saman jikinsa ta fad'a, Wanda a dai dai lokacin babu riga a jikin sa." Wata runguma yayi mata wadda sai da ya sauke wata ajiyar zuciya wadda besan yayi taba." K'irjinta ya had'e da gashin k'irjinsa saiji yayi kamar anyi masa shocking." k'ura mata ido yayi cike da sha'awa, besan lokacin da yakai bakinsa cikin bakinta ba, yashiga tsotsa." Kokawar kwace kanta takeyi, domin itama ta tsinci kan ta cikin yanayin da bata tab'a shiga cikinsa ba." Rungumar da yayi mata bata wasa bace, suka kuma mannewa wuri d'aya, hankalin Bassam ya kuma tashi musamman k'amshin da yakeji yana fitowa daga jikinta." Rungumeta yayi da hannu d'aya ya sanya hannu d'aya yafito da Brest d'inta, yashiga wasa dashi." Subahanallahi." hakan kawai yake cewa, domin kuwa Bassam shima ya zama ustazu lol😜 Laushin sa da santsin sa, ga kuma taushi, ya kuma firgita shi, ya fita hayyacinsa, bakinsa ya kai akan Brest d'in ya shiga tsotsa, kamar yaron goye." Dai dai lokacin Afnan tasaki wani Kuka mai sauti Wanda yadawo dashi a hayyacin sa, Da k'arfi ta tureshi daga jikinta, domin ba k'arfi a tare dashi, tayi saurin sankowa daga kan gadon, cike da tsoro da tashin hankali tanufi hanyar fita." Daka mata tsawa yayi, yace "karki kuskura ki fita a hakan." Duk jikinki a waje, ko kin manta akwai maza a wajen, fadawa da bayi?" Koda yake kinsaba Neman mazanki, to wallah mudun kika fita hakan saina matuk'ar sab'a maki." Lol Bassam yaji maza😜 Kallo tabi kanta dashi, sai a lokacin ta ganta kamar a tsirara take, Da sauri ta tafi inda Alkyabbatar take ta d'auka tasanya, ta rufe jikinta, tsura mata ido yayi yakasa d'auke kansa daga kallonta, domin saurin da takeyi domin d'aukar Alkyabbatar gani yake kamar da gangar take girgiza Brest, d'inta, Domin ganinsu yakeyi har wani girgiza sukeyi, tare da mazau nanta, lashe baki yayi, cike da sha'awa, domin Brest suna d'aya daga cikin abunda yafi so a jikin mace, kuma kamar irin na Afnan." Bai ankaraba yana daga kwance sai ganinta yayi a bakin k'ofa tabud'e marfin k'ofar yanda data ga yayi yunk'urin tashi zata fita a guje." Tarik'e k'ugo cike da tsiwa, Tashiga cewa "maye kawai kawani tsireni da ido kana kallona, Nagode wa, Allah da be baka ikon ai watar da mugun nufinka a kaina ba, Kuma duk abunda kayi mun ban yafeba, domin kashiga hurumin da bana kaba." Amma duk da hakan nagode wa, Allah da baka, karyawa Habibina Sahibina wadda a yanzun nasan yana can yana jirana nafita daga wannan k'angin mutafi muyi auren mu, cikin so da k'auna, Mudurcina ba." Sannan kuma kasani duk abunda kayi min ban yafeba." Ransa ya kai k'ololuwar b'aci, musamman da ta ambaci wani wai Sahibinta." Da sauri ya mik'e tsaye yanufota yana fad'in wakike yiwa Allah ya isa?" Ina kamin ya yunk'ura ya tashi, har ta fita a guje kamar filfilwa." Gudun da takeyi, sai ma tabashi dariya." Yaja ya zauna a falo kan kujera, yana murmushi, yana fad'in wannan yarinya ga rashin kunya ga kuma tsoro." Can ya tuna da abunda ya shiga tsakaninsu ji yayi gaba d'aya yana so ya kasance tare da macce, gashi kuma yayi wakansa alk'awari ya daina mu'amala da ko wace mace. To meye mafita?" Dogon tsaki yaja yace "dole ne nayi aure ko dan na kuma ni santa kaina da fad'awa zina." Tsaki yaja ya mik'e tsaye ya nufi bedromm domin babu abunda zai gushe masa da wannan damuwar sai giya." Cikin hanzari ya bud'e frege, sai gani yayi bega komai a cikiba." Girgiza kai ya shiga yi domin idan rayuwar shi tayi dubu to ta b'aci." Wato wannan yarinyar ce ta kwashe masa giya kenan, Wannan dalilin ne yasanyata shigo masa b'angare?" Wai meyasa takeson ta dinga shiga rayuwarsa ne?" Tun lokacin da ya had'u da ita be kuma samun kwanciyar hankaliba har zuwa yanzun, to tabbas yau d'in nan sai ya koya mata hankali, domin ya fahimci bata dashi." A fusa ce yafito yanufi sashinta." Afnan kuma tana fita daga sashin Shi, da gudu, bata koma sashinta ba, Kai tsaye wurin Anna ta nufa." Anna na zaune, sai ganin Afnan tayi ta shigo tana haki." Tashi tayi da sauri ta tareta, tare da zaunar da ita a kan kujera." domin tasan babu wanda zai biyota da gudu hakan sai Bassam." ta zaunar da ita a kan kujera, ta d'ebo ruwa ta bata, tace "ungo karb'i kisha ruwa gimbiya Ki kwantar da hanlinki babu Wanda zai shigo nan yayi maki wani Abun." [3/5, 4:35 PM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S* _we don't just entertain and educated we tauch the heart of the readers_ #WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM #IG PML WRITERS #https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035 #http://maryamsbello.blogspot.com *27* Ruwan ta k'arb'a tashiga sha, Sanyi ruwan ke ratsata taja doguwar ajiyar zuciya." Ta kalli Anna ta fashe da kuka had'ida fad'awa jikinta, tana fad'in Anna dan Allah ki taimake ni ki maida ni gida wurin iyaye na, wallahi Bassam kashe ni zaiyi." Anna tace "nasan za'ayi hakan, ai tunda naga kin shigo a guje nasan Bassam ne ya biyoki." Ki kwantar da hankalinki gimbiya ni nasan matakin da zan d'auka." Bassam kuma kai tsaye ya shiga har cikin bedromm d'inta, yana huci kamar wani zaki, domin muddun tasake ya kama ta, sai ya b'anb'ala mata hannu da k'afa, masu shiga hurumin sa." Ganin be ganta ba cikin bedromm d'in, sai ma karo yaci da photon Malam Nura dana Kaka, a kan gadon ta da alamar idan zatayi barci sutake kallo." Wani abu yaji yana taso masa, a zuciya, da ya kuma sanya ido ya akan pic d'in malam Nura." D'aukar photo nan yayi gaba d'aya ya jefa aljihu, sannan yafito d'akin." Karo yaci da masuyi mata hidima, suna ganinshi sukayi saurin zubewa k'asa suna kwasar gaisuwa." Tsawa ya daka masu had'ida cewa "tana ina?" A nan take suka gane gimbiya yake nema, Had'a baki sukayi gaba d'ayansu suka ce ranka ya dad'e muma ita muke nema." Bai kuma saurarensu ba ya wuce su a fusace, Ya nufi sashen Anna domin yasan babu inda zata tafi sai can." Cikin fushi ya fad'a falon, kai tsaye, hango Afnan yayi kwance a kan cinyar Anna da a lamar lallashin ta takeyi." A bakin k'ofa yaja ya tsaya, saka makon wani kallo da yaga Anna nayi masa, Afnan na ganin shi ta kuma fashewa da kuka ta k'ank'ame Anna tana fad'in Dan Allah Anna ki taimaka min karki bari ya dokeni, wallah kasheni zaiyi." Anna tace " daina wahalar da hawayenki a banza, babu abunda zaiyi maki a yanzun ina wurin." Sosa kai yashiga yi, Anna ta kalleshi tace "Yarima yaushe kazama haka?" Gaba d'aya ka canza, baka tausayin matarka ko kad'an, Tunda akayi aurenku babu abunda kake mata sai dukanta, .metayi maka?" Meta tsare maka?" Dibeka Dan Allah ko kunya bakaji wai kabiyo ta, har gabana kana wani zare ido zaka duketa." Sosa kai yashigayi had'ida sunkuyar da kai yace "Anna baki san b'arnar da tayi min bane." Tace "to tunda bansaniba, "zogata ka kasheta." Ajiyar zuciya ya sauke yace "wallahi Anna duk kece kike kuma sanyawa wannan yarinyar tana renani, yaja ya fita." ____________________________ *FADA* Sarki ne zaune fadawa nayi masa fira, yana dariya." Da gudu wani Bawa ya k'araso a gaban sarki ya zube yana kwasar gaisuwa." Fadawa sukace "sarki ya amsa Bawa." Baiwan ta kuma runsunawa yace "ranka ya dad'e Allah ya taimakeka, muna d'aya daga cikin masuyiwa, Hajiya Zainab hidima a wurin da kasanya aka keb'en ce maka ita, Ranka ya dad'e uwar gijiyata Gimbiya Zainab tana d'auke da tsohon ciki na tsawon wata Tara, wadda haihuwa ko yau ko gobe." Da sauri sarki ya mik'e tsaye *pls kuyi hak'uri da wannan* [3/5, 4:35 PM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S* _we don't just entertain and educated we tauch the heart of the readers_ #WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM #IG PML WRITERS #https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035 #http://maryamsbello.blogspot.com *28* *HAPPY BIRTHDAY SAFWAN ANAS BAWA* *ALLAH ya Albarkaci rayuwarka ya k'aro sheru masu Albarka* 🎂🎂🎂 "Da sauri Sarki ya mik'e tsaye, fadawa suka rufa mashi baya ya nufi b'angaren Hajiya Zainab inda yasa aka keb'e ta." Tana ganin shi tanufo shi da k'aton cikinta, tana kuka ta durk'usa a gaban sa." Kuka takeyi sosai tana fad'in "ranka ya dad'e kayi hak'uri ka yafe min, nasan nayi laifi, laifi mafi muni, wadda a yanzun na gane kuskurena nayi nadama ka yafe min ranka ya dad'e ko dan darajar d'anka dake cikina." Mik'ar da ita tsaye yayi, ya tsura mata ido yana kallon ta tabbas yaga nadama sosai a idon ta." Ya kai dibon shi ga k'aton cikin ta wadda yayi mata girma sosai kwanin ban tausayi ya shiga tunanin, lokacin da yasa akawota nan zuwa yanzun wata nawa kenan?" Domin yana so ya tabbatar da zargin da yakeyi." Wata a jiyar zuciya ya sauke da ya tuna wata bakwai kenan lissafi yabashi, wato koda aka kawota nan tana da ciki wata biyu kenan, Allah mai yanda yaso da bawan sa, Allah gagara gasa." Kallo yabi ta dashi ya kuma d'aure fuska domin yana so ya gane cewa tabbas tayi nadamar abunda ta aikata." Kuma fashewa da kuka tayi, da taga babu alamun yafiya a idon Sarki, tana fad'in " nasan kai maiyafiya ne, sarki ne mai Adalci, na yarda na Amince kajarabani ta kowace hanya domin ganin tabbacin nadamata." Da kyar yayi k'arfin halin yi mata magana saboda tausayin da tabashi, sai da ya saita na tsuwarshi, sannan yace "Hajiya Zainab hak'ik'a ko Allah akayiwa laifi idan bawa ya rok'eshi yana yafe masa bare mu 'ya'yan Annabi Adam." Hak'ik'a ni nayafe maki, saboda dan Allah da kuma darajar abunda ke cikinki, wadda nayi farin ciki da ganin hakan, Tabbas na tabbatar da bawa baya d'ebe rabo da rahamar ubangijinsa." Na dad'e ina Neman haihuwa, har na hak'ura na zurawa sarautar Allah ido, sai gashi yanzun kwatsam banyi tsammani ba, Allah ya azurtani zan samu d'a ko 'ya." Hak'ik'a Hajiya Zainab na yafe maki duk abunda kikayi min, Saura ki nemi yafiya a wurin Bassam." Ya juya ya kalli baiwar da takawo mashi Albishir yace "yake baiwata Albarkaci Albishir d'inda kika kawo min na intaki a cikin 'yan tattatun bayina." Baiwa Saude zubewa tayi k'asa tana kwasar godiya, saboda jin dad'i har da hawaye ke zuba a idonta." Anan sarki ya bada umurnin ya yafewa Hajiya Zainab ta koma cikin matan shi a b'angarenta domin taci gaba da renin cikinta har Allah ya sauketa lafiya." ______________________________ Bassam ya fito daga b'angaren Anna ransa a b'ace, sanadiyar hana shi dukan Afnan da tayi." Karo yaci da maimartaba zai tafi wurin shi mamaki ya shigayi domin daga ganin fuskar sarki kasan yana cike da farin ciki." Cikin murmushin sarauta sarki ya dibi Bassam yace "Yarima dama yanzun wurin ka zan tafi" , Ashe kana b'angaren Anna." haka shima Sarki kece mata yanda Bassam d'in ke cewa." Bassam ya d'an sunkuya alamar girmamawa, yace "ranka ya dad'e da kanka haka, aida ka aiko waziri yakirani ko kuma kayi min waya sai na zo." Sarki yayi d'an murmushi had'ida d'an dukan bayan sa, yace "karka damu Yarima zuwa da kai yafi sak'o." mutafi sashena muyi wata magana mai mahimmaci." Haka Bassam ya biyo maimartaba har cikin palon shi Wanda yasha kayan more rayuwa." Sarki ya kalleshi yana murmushi yace "Yarima Albishirinka." Bassam ya kalli mahaifin nashi, yayi dariya yace "goro fari ranka ya dad'e." Sarki yace "ka kusan samun k'ane ko k'auna a gidan nan." Da sauri Yarima ya k'ara matsowa kusa dashi cike da murna yace "Abba Fulani ke da ciki ko Hajiya Amina?" Sarki ya gyara zaman shi yace " babu ko d'aya a cikinsu, Hajiya Zainab ce keda ciki har na tsawon wata tara." Bassam ka natsu ka saurareni, ka yafewa Hajiya Zainab duk abunda tayi maka domin tayi nadama Dan naga nadama a idonta." Be rufe bakiba Hajiya Zainab ta turo k'ofa tashigo, bakinta d'auke da sallama." A tare suka d'aga kai suka dibe ta kai tsaye wurin Bassam ta nufa ta durk'usa a gaban shi, tashiga bashi hak'uri da cewa ya yafe mata abunda ya faru ta tuba baxata sakeba, ta gane kuskurenta." Kallo yabita dashi cike da mamaki baiyi maganaba domin yasan makircin Hajiya Zainab sarai." Hajiya zainab ta iya k'ulla makirci. Sannan ta iya mulki, saboda ita daga gidan sarauta ta fito. Ta gogu sosai da iya shirya tsarin mulki, Shi yasa kowa a tafin hannunta yake A gidan baki d'aya." Bassam ya tsane ta, saboda bata k'aunar shi bata son ta bud'e ido ta Ganshi yana motsi a doron k'asa." Kuma a sanadinta ya rasa mahaifiyar shi, Anna ke bashi labari," A kan ta ya tsani mata masu kyau a ganinsa duk inda mace mai kyau take to algunguma ce da iya shirya shirri." Ya tsani Mace mai kyau don ya sansu mayaudara ne, shi yasa da Afnan tayi mashi laifi yaji baya iya yafe mata, sai ya aure ta don ya nuna mata kyanta na banza ne shi mace ba ta isa ta wulak'anta shiba ko ta juya shiba." Kallon Hajiya zainab yaci gaba dayi tana bashi hak'uri yana kuma karantar wani sabon makirci Wanda tazo dashi." Sarki ya katse masa tunani da yaji ya dafa shi, Yace "Haba Yarima kazama mai yafiya mana, kayafe mata tunda ta gane kuskurenta tayi nadamar abunda ta aikata maka ko dan darajar k'aninka ko k'auna dake cikinta." Murmushin dole Bassam yayi domin ya fahimci mahaifin nashi yayi amanna da tubanta yace "Abba na yafe mata, Allah ya yafe mana baki d'ayanmu." Ya mik'e ya fita, Hajiya zainab tabishi da kallo tana fad'i a zuciyarta Ashe wannan yaron yana nan da taurin halinshi, lallai aiki ne ke gaba na babba." Kai tsaye sashin sa ya nufa, da tunani kala kala a zuciyar shi, Domin yasan Hajiya Zainab farin sani, bazata fasa abunda dakeyiba Keb'eta da sarki yasa akayi tak'aro wani sabon salon mugunta da sharri, tambas dolene na kiyaye kaina da kuma masu kula dani, domin ta kowa ce hanya tana iya bi domin ta cutar dani." bawansa ya kira, mai mashi hidima Audu ya aike shi chilly ya sawo mashi giya domin Audu shi kad'ai yasan yana shan giya kuma yanzun shike zuwa sayo masa." ____________________________ Hajiya Zainab na ganin yarima yafita, ta d'an zauna a kusa da sarki ta d'an russuna, ta matso hawayen k'arya tace "ranka ya dad'e ina ganin kamar Yarima bai yarda dani ba bai yafe min ba." Sarki yayi saurin kallon ta yace "Haba Hajiya zainab daina kuka hakan karki wahalar da abunda ke cikinki, Yarima ya yafe maki, ganewa ne, bakiyi ba, kin san halin yarima wani lokacin ba'a sanin gaban shi bare bayan shi." Sai a lokacin ta d'anyi murmushi suka d'an tab'a hira domin yanzun sarki ji yake da ita sanadiyar cikin dake tare da ita, sannan daga k'arshe tayi mashi sallama ta tashi, ta fita." Tana komawa sashinta ta sanya a nemo mata Sarkin gida." Shine masanin duk abunda ya kai kawo a cikin gidan." Sarkin gida ya tsugunna yana jero gaisuwa." Ta dakatar dashi da cewa ya isa!! Sarkin gida ba gaisuwa na kiraka kayi minba, Kiranka nayi domin na tambayeka abunda ke tafiya a gidan nan tun lokacin da bana cikin sa har zuwa yanzun." Wane ci gaba Bassam yasamu bayan bana nan." Sarkin gida ya sunkuyar da kai, domin shi kansa tsoron tuggunta yakeyi, lokacin da bata nan sunji dad'i sosai har Addu'a sukeyi Allah yasa daga can karta dawo sai mutuwa." "Yace Ai ranki ya dad'e Maimartaba yaso yaba Yarima kujerar mulkin ya zama Sarki." Dajin hakan ta d'auki ta kalamin da ke kusa da ita ta jefa masa sai a goshinsa tana huci tana fad'in "kada ka kuma fad'in hakan a gabana domin muddun INA motsi babu Wanda ya isa ya zama sarki, sai Yazeed." Abunda ke cikinta take nufi, domin bokayenta sun shaida mata cewa namiji zata haifa anan take ta sanya mashi suna Yazeed." *ikon Allah oh ni 🤔 ummu safwan zanga yanda jariri Wanda baizo duniya ba zai mulki*🤔🤔🤔 [3/5, 4:35 PM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S* _we don't just entertain and educated we tauch the heart of the readers_ #WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM #IG PML WRITERS #https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035 #http://maryamsbello.blogspot.com *29* Sarkin gida ya rik'e .goshinsa da ya kumbura, a ransa kuma cewa yake "Yazeed?" Waye kuma Yazeed?" Kai wannan matar akwai hatsabibiya." Sai jin muryanta yayi tana fad'in Neman sani kakeyi kowaye Yazeed?" To bara na fad'a maka d'an da zan haifawa Sarki yau ko gobe nake nufi." Tuk'ashi!! Abunda bazai tab'a faruwa ba kenan ko a mafarki." A fili kuma yace "Allah ya huci zuciyarki ranki ya dad'e, kin gaji mulki mahaifinki Sarki Kakanki Sarki........" Kai yimin shuru Sarkin gida, kab'ata min jin dad'in yau tashi kabani wuri kanajina." A fad'ace take magana." Mik'ewa yayi yafita yana fad'in Allah ya huce zuciyarki." Jakadiyarta tamatso fuskarta na nuna tsoro, "Ranki ya dad'e kiyi hak'uri Allah ya huci zuciyarki, kowa yasan abunda sarkin gida ya fad'i k'arya ne. Ko labari bai zama bare ya faru." Tsawa ta daka masu, kufita kubani guri, bana son ganin kowa yanzun." Babu b'ata lokaci kowa ya fice daga makeken falonta, Wanda yaji kaya har babu gurin ajiye wani abun." Zuciyarta zafi take yi mata, "sarki sarki shirin da yake yi kenan?" Wato Bassam yakeso ya d'ora a kan mulki, ina Sam bazai yuyuba sai dai kowa ya rasa." Ranta idan yayi dubu ya b'aci, "zan shiga tsakaninka da wannan yaron wata k'ila ajalinsa ne ya dawo dani, yafad'a a fili zan zama sanadinsa kota halin k'ak'ane." ______________________________ Bassam na zaune cikin d'akin shi yasanya Audu yaronshi, mai yi mashi hidima kuma ya mik'a wuya bak'i d'aya gareshi, Shi ne kad'ai yasan Yarima na shan barasa, dan shine ma ajinta tunda ya gane Afnan shigowa take tana kwashewa tana zubarwa." Yana zaune a gefensa yana tsiyaya masa yana sha, shuru babu hira tsakanin su, Audu dama bai damu da surutu ba, saboda tun fil'azal yana da nauyin baki, dan haka rashin maganar ba ta tab'a damunsaba." Ya kwashe komai ya Adana ya shiryawa Bassam ruwan wanka har yayi ya fito, ya zauna bakin gado, Audu zai kashe wuta sai Bassam ya kira sunan, Da sauri ya matso ta tsugunna kansa a k'asa yana sauraron sa." Bassam ya tsura mashi ido sosai, domin yanzun yanayin tsarin tsaro zai canza tunda Hajiya Zainab ta dawo tana iya saye makwad'aici da kud'i masu yawa domin tasamu cikar burinta." Ya kuma kiran sunan shi a karo na biyu, yace "Audu." Ya Amsa cike da girmamawa." Bassam yace "ya ka d'aukeni?" Mene ne matsayina a wurinka?" "Ranka ya dad'e ni a matsayina na mai yi maka hidima, ban wuce bawa mai kawar da lalurorin ubangidansa ba." Yarima ya girgiza kai yace "kasan Amana?" "Eh Ranka ya dad'e." "Kada kaci Amanata domin ganin kud'i ko wani abun duniya." "Zan rik'eka zuciya d'aya kaima ka rik'eni da zuciya d'aya, duk abunda kasani ka barshi tsakanina da kai, Idan kasan bazaka iyaba ka fad'a min tun yanzun karna saki jiki da kai a had'a baki da kai a cutar dani." "Ranka ya dad'e na mik'a wuyana gareka daga Allah sai kai, a hidimomina zanyi k'ok'arin rik'e amanar ka da yardar Allah." Ajiyar zuciya Bassam yayi yace " Madallah sai da safe." "Allah bamu Alheri." Ya fice daga d'akin." ______________________________ Afnan na nan wurin zamanta wurin Anna shagwab'a sai abunda ya k'aru, ga shak'uwa da son junansu dama Afnan ta iya shiga ran mutum farat d'aya, sai wautar da dake sa duk Wanda yake tare da ita dariya." Anna taji labarin dawowar Hajiya zainab ta kira Bassam tashiga shaida masa yayi taka tsantsan da ita sannan kuma ya zama mai kula da duk wani Abu dake tafiya a gidan, kuma ya rik'e Addu'a domin Addu'a ita ce makamin muminice." _____________________________ *Kaka* antare a babban gida Wanda Sarki yasaya mata." Gida ne babban gida mai kayan more rayuwa a cikinsa, gidan b'angare biyu ne b'angare d'aya nata ba'angare d'aya kuma na malam Iro." Sunyi farin ciki sosai kuma suyita sanyawa Auren Afnan Albarka dayi masu fatan zaman lafiya mai d'orewa." Matsalar *Kaka* d'aya ce har yanzun bata sanya Afnan d'inta a idoba." In tana cikin wannan tunanin sai ta tuna da sak'on da Sarki yake mata da cewa "tayi hak'uri Jikanyarta tana cikin k'oshin lafiya, zaisanya rana azo a d'auketa a kaita taganta." Sai ranta yayi mata sanyi tasanyawa rayuwarta dangana." *Malam Nura* kuma tun yana sanya ido Afnan zata dawo gareshi har ya dangana kuma duk ya kira number wayarta a kashe yake jinta." Hakan yasanya wa rayuwar shi dangana, domin yanzun ya fitar da rai akan cewa Afnan zata dawo gareshi, yasan yanzun Afnan tayi masa nisa, sai dai Addu'a dayakeyi akan Allah yakawo masa wadda zata maye masa gurbin Afnan d'inshi." _____________________________ 4:30pm Bassam ne kwance a kan makeken gadonshi sai juyi yakeyi domin buk'ace yake da macce, sha'awa ta dameshi tun yana shan lipton da lomon tsami har ya kai yanzun idan yasha basa masa ganin komai." [3/5, 4:35 PM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S* _we don't just entertain and educated we tauch the heart of the readers_ #WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM #IG PML WRITERS #https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035 #http://maryamsbello.blogspot.com *30* Haka ya dinga murk'ususu, hannu shi dafe akan marar shi sai nishi ya keyi saboda azabar ciyon da yakeji." Da kyar yasamu ciyon ya sake shi, ya d'an samu sassauci, sannan ya tashi ya shiga toilet yayi wanka had'ida d'auro Alwalar Sallar magariba sannan ya fito ya kyamtsa cikin wata da kankiyar shadda milk colour, hular kan shi ita ma Milk colour, Ya d'auko agogon shi mai d'auke da *Tambarin Sarauta* ya d'aura a hannunshi, yayi kyau matuk'a." Kai tsaye b'an garen maimarta ya nufa, domin daga yau hak'urin shi, ya k'are aure yake so ya k'ara." Hajiya zainab na ganin giftawar Bassam yanufi sashin maimartaba, hankalinta ya tashi, domin ganin tayi yak'ara kyau da haiba da cika irinta jarumin maza," "tabbas dole ne, Sarki yace zai sauka a kan kujerar shi yaba Yarima domin ya cancaci ya zama sarki, amma kuma muddun ina raye hakan baza ta tab'a faruwa ba." Da sauri ta koma baya, ta fad'a d'akinta ta d'auko mayafin ta, ta lullub'e jikinta dama kuyanginta suna nan lab'e a guri d'aya jiran umurninta kawai sukeyi." Ta kallesu d'aya bayan d'aya cikin iko da mulki." Tace "kuyi min rakiya sashen Maimartaba." Taga sunyi tsuru tsuru da ido basu da alamar tafiya." Ta daka masu tsawa, tace "me kuke jira?" Kuka kafeni da ido kuna kallona." Gaba d'aya suka zube a gaban ta, suna fad'in "ranki ya dad'e ki gafar cemu maimartaba ya bada lokacin zuwa sashensa daga bayan la'asar zuwa Isha'i, kada Wanda yaje nemansa saboda yana tare da Yarima." Da k'arfi, a fad'ace tace "kuyi min shuru magulmata kawai!" Ta koma cikin palonta hankalinta a tashe, wato bayan bata nan har wani lokaci Maimartaba ya ware na ganawa da Bassam." "To me suke cewa?" wata k'ila shirye shirye sukeyi na yanda za'a d'orashi a kan kujerar sarauta." da k'arfi tace "k'arya ne wallahi abun da bazai tab'a yuyuwa bane in dai ina da rai da lafiya Bassam ba zatab'a zama Sarki ba." ______________________________ Maimartaba da Bassam sunyi nisa wurin hirarsu." Sarki ya fahimci akwai abunda ke damun d'an nashi daga ganin yanayinsa." Amma kuma ya kyaleshi yaci gaba da jansa hira suna dariya." Maimartaba ya kalli Bassam cikin barkwanci yace "waini Yarima sai yaushe zanfara ganin jikokina." Anzo wurin Bassam ya fad'a a ranshi." Ya sunkuyar da kanshi cike da jin kunya sannan yace "Ranka ya dad'e Aure zan k'ara." Sarki yace "iyee da gaske?" Bassam ya kuma sunkuyar da Kansa, yace "Eh Abba ina son in k'ara Aure." Sarki ya kalle shi yayi murmushi yace "lallai yaro kayi gado." Nima kasan a kwaini a kwai son macce." Bassam murmushi yasaki amma baice komai ba." Sarki yace "in kana so zan k'ara maka da kwarkwara biyar." Bassam ya zaro ido😳 yace A'a Abba bari dai na fara auren tukunna." Sarki ya kalli Bassam yace "Kai da Allah can rago halama Anna bata dafa ka ba?" Dan nasan Anna bata wasa da abunda tasan zakaji dad'i gareshi." Kunya ce ta kama Bassam ya shiga sunkuyar da kai k'asa." sarki babu ruwan shi sauk'in kai gareshi da son barkwanci mussam idan suka keb'e da Bassam d'aukar shi yakeyi kamar abokinsa komai yana iya fad'a masa." Sarki ya katse masa tunani yace "Yarima ina son kazama namiji jarumi a gaban kowa." "Kada kazama Wanda zai sanyi a al'ummarsa." Kuma ka kula da irin mutanin da zaka rik'a huld'a dasu, Kasani ita sarauta baki d'ayan ta siyasa ce ta gargajiya, dole kasamu masu adawarka kona tare da kaine." Ka zama mai Sanya ido a ko Ina kake ciki da waje, kada kazama sakake, kuma ka zama mai rik'e sirrinka a cikinka, dan ciki ba anyi shi dan abinci ba, Ka kuma yi taka tsantsan da mutanen da kake hurd'a dasu duk yadda suke tunaninka nuna masu kawuce nan, idan zaka yanke mataki ka nemi shawarar ma'abota sani ba jahilaiba, ka kuma k'ara kula da hak'k'in mutanen da hak'insu ya rataya a wuyanka." Hajiya zainab ta dawo, ba wai ta daina halinta ba ne," Kayi taka tsantsan da ita, da duk wani abu da zata baka kaci, ko menene shi." A tak'aice ka zama mai kula don kuwa ba ita kad'ai bace, Kaza mai kula da Wanda zai kawo maka abinci ko abin Sha, kowaye shi in dai ba yardanden ka ne." "kai ko yardanden kane, ka zama mai kula." domin kud'i suna iya can zawa mutum ra'ayi a nan take ka kiyaye." Bassam ya durk'usa gaban Sarki cike da jin dad'i, yace "Abba nagode kwarai Allah ya k'ara yawancin rai." Sarki ya shafa kansa yace " Amin Allah yayi maka Albarka." Kak'i yarda ka amshi sarauta." "Abba sarauta da da kai ta dace ban San komai ba a kan mulki, ina da saura tukun, ina son in fara koyon tsarin mulki daga gareka." Sarki yaji dad'in kalaman Yarima yayi murmushi irin naso na manya, yace "To shi kenan nagode da tunanin da kayi, Ina so ka mai dani tamkar abokin ka, kada kadamu da abunda zaka fad'a min ko meye shi in har ya shafi rayuwar ka." Am ready to be a father and also a friend." Sosai Bassam yaji dad'in firarsu ta yau da mahaifin nashi daga k'arshe, suka tashi suka nufi masallaci domin yin sallar magariba." _______________________________ Labari ya iske Anna Bassam zaiyi aure, abun ya d'aure mata kai sosai, Ba tace komai ba, don tasan halin sarki, bazai hanashi ba illah ma ya zuga shi zai k'arayi." Don haka ta yanke shawarar ta zura masu ido taga iya gudun ruwansu." _____________________________ 2:20am na k'uda ta kama hajiya zainab sai kuwa takeyi ta hana bayi da kuyangi barci dama sauran mutanen gidan, Fulani kuwa sai hawaye takeyi domin ganin yanda Sarki ya rud'e ya hana kanshi zama lafiya hankalin shi duk ya tashi, baya da lokacin ta, kuma gashi a d'akinta yake." Hankalin mutanen gidan bai kwanta ba sai da hajiya Zainab ta haihu ta haifi d'anta namiji mai kama da ita sak, Murna a wurin sarki abun ba'a magana." Safiya na wayewa sarki ya shiga fad'awa mutane k'asa k'asa shuwa gabanni da yan siyasa." Bassam najin labari baiyi wani murnaba sai dai yace "Allah ya raya mata abunda ta haifa, ya kama gabansa." Satin biki, biki ne akayi na kece raini, manya mutane sun halarta wurin bikin, domin Rabon da ayi taron bikin haihuwa a gidan tun haihuwa Bassam yanzun shekara talatin kenan." Anci ansha an zubar da naira." Tun ana gobe suna Bassam ya tsiri tafiya England dibo takardun sa, domin kaddama ya tsaya ayi bikin yana nan, domin a duniya babu abunda ya tsana sama da hajiya zainab da duk wata zuri'arta." Anyi biki lfy an watse lafiya, hajiya zainab ansamu abun duniya wadda dama shitake nema." Anna da Afnan suna gefe sun zama yan kallo, dama Afnan ba kowa yasanta a gidanba." Fulani da Hajiya Amina, sun nuna farin cikinsu ba laifi, suka duk'ufa da add'a Allah yabasu nasu rabon suma, domin sun san yanzun sai sun danne zuciyarsu da kunnensu da kuma idonsu, domin yanzun hajiya zainab abunda taga dama shi zatayi a gidan tunda taga ta haifi d'a namiji." [3/5, 4:44 PM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S* _we don't just entertain and educated we tauch the heart of the readers_ #WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM #IG PML WRITERS #https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035 #http://maryamsbello.blogspot.com *32* Jikinta ya soma rawa kamar mazari ta had'e hannuta wuri d'aya tana fad'in Dan Allah kayi hak'uri ban san kana wurin ba." Anna ta zuba masu ido tana kallon su, batayi magana." A fusace ya mik'e tsaye, yayo kanta yana wani huci zai daketa, yana fad'in ke mahaukaciyar ina ce?" da bakya ganin gabanki, Ina ko zaki ganni kina tafiya kina girgije girgije." to bari yanzun na saita maki tunaninki tunda baki da hankali." Yayo kanta zai daketa, Anna tace "karka kuskura ka daketa a gabana." Yaja ya tsaya cak yana sauraren Anna." Taci gaba da cewa, tace "kayi hak'uri bata lura bane, amma duk da hak'urin da take baka sai ka daketa?" Sannan kuma meye naka a ciki da tafiyar da takeyi tana girgiza, haka Allah ya hallice ta." Yarima yaushe kazama haka ne?" yanzun kwata kwata baka tausayin macce, musamman Afnan?" Meta tare maka a gidan nan ne?" shin Kasan baka son kabud'e ido ka ganta meyasa ka aureta?" A zuciyarsa yake cewa "domin d'aukar fansa na aureta, yanxun kuma bana son na bud'e idona na dinga ganinta domin yanzun ta zamar min fitina, duk inda naci garo da ita saita tayi min tabo a zuciya, saita b'ak'anta min rayuwa." Anna ta katse masa tunani, tace "zoka fita, na sallame ka, In har kasan domin kadinga takurawa Afnan ko dukan ta zai dinga kawo ka sashin nan to kadinga yin zamanka a sashinka, gaisuwar ma na gode, idon na buk'aci ganinka ni da kaina zanzo, yana d'aya daga cikin aikina." Had'e fuska yayi cikin jin haushi yace "yanzun Anna akan wannan Abar kike korata?" yanuna Afnan da hannu da ta b'oye a bayan Anna sai zarar ido takeyi." Anna tace "niba korarka nayiba, ta nuna masa k'ofa tace "Yarima Allah yabamu Alheri, Bai kuma yin magana ba, yasanya kai yafita, a zuciyarsa ya yana fad'in " ai zan kamata ne a wani wurin sai na koya mata hankali." Anna na ganin Bassam yafita, taja hannun Afnan suka zauna a kan kujera cike da mamaki tace "ya akayi kika gyara wannan agogon?" Kinsan ko shekararsa nawa a jiye an rasa wadda zai iya gyarashi?" Tabbas Afnan ke 'yar baiwa ce, akwai dalilin da yasa kika shigo rayuwar masarautar nan, amma abunda nakeso dake ki ajiye hikimarki da basirarki akwai lokacin da zaki banyanar dasu, dasu mana amfani." domin yanzun a kwai k'alu bale gabanmu." Ta mik'a mata agogon tace ungo tafi ki b'oyeshi inda babu Wanda zai ganshi lokaci na zuwa da zamu fito dashi." ______________________________ Sarki ya Tara matan sa gaba d'ayansu, Tare da manya shedu a kusa dashi, yasa aka kira masa Yarima." Ya d'auko wasu takardu ya mik'awa Yarima, wasu manya Gonakinsa ne Wanda ko wace gona tayi girman rabin gari." yace ya mallakawa Bassam ita kyauta." sakamakon yafito da rusult mai kyau." Godiya aka shiga yiwa sarki, Hajiya zainab dake zaune sai dariyar dole takeyi Wanda tafi kuka cowo." Bassam tashi yayi daga inda yake yaje gaban Sarki ya durk'usa yashiga jero masa godiya." Fadawa sai cewa sukeyi sarki ya Amsa Yarima magajin sarki." Yarima mai jiran gado." Daga nan kowa ya tashi yatafi akabar yarima da sarki suna tattaunawa." ______________________________ Hajiya zainab harda kukan bak'in ciki, bata iya b'oye damuwar taba, sai cizon yatsa takeyi tana kai komo a tsakar d'akinta." Sarkin gida na durk'ushe gefe sai ban hak'uri yake yi yana lallashinta domin yanzun ta saye shi da kud'i yazama na hannun damarta." Cewa takeyi " ni maimartaba zai wulak'anta?" Har da cewa ya ba Bassam gonakinsa guda biyu, hala mutuwa yayi da zai raba gado tun yanzun?" Sarkin gida ya zanyi in wulak'anta Bassam ya zamto ya mutu ko baida amfani?" Sarki gida yayi k'asa da murya yace "ranki ya dad'e a kwai wani mutum da ya fito yanzun aikinsa kamar yankan wuk'a." Hajiya zainab ta tsaya tana kallonshi sannan tace "a ina yake?" Sarkin gida yace "wanzami ne ranki ya dad'e, kinsan suma akwai su akwai lak'ani...." Hajiya zainab tace "ka tabbata ya iya aiki?" "Ranki ya dad'e a gabana sukayi wasa irin Nasu na wanzamai, jaka ce d'auke da kayan aikinsu, Wanzamin ya ajiye yace duk Wanda yakeji da k'arfi yazo ya d'auki jakar." Ranki ya dad'e maza hud'u suka taru amma suka kasa d'aga jakar." Murmushi tasaki na mugunta, tace "me zai iyayi a kan Bassam kasan yana da taurin ran tsiya." Sarkin gida yace Abu mai sauk'i idai zaki iya zube kud'i masu yawa, A dunk'ufar da shi wuri d'aya bai iya tashi inda yake daga nan sai barzahu......." Dariya hajiya Zainab ta kyalkyale da ita, Ta kalli sarkin gida tace "shiyasa duk a cikin dogaraina nakeji da kai." "Sarkin gida inaso ka kasa kunne duk abunda Bassam yake ciki ka tabbatar da kazo kafad'a min." "An gama ranki ya dad'e wadda ta gaji sarauta, babanki sarki kakanki sarki sarauniya maimartaba Ahmad moh'd Allah yaja zamaninki." Ta zaro dumin kud'i ta mik'a masa shi ko sai kirari yake yi yana godiya." _______________________________ Labari ya zowa hajiya zainab cewa Bassam yana so yayi aure." Cikin kinsa da makirci ta nufi sashin maimartaba, anan take cewa Sarki a bata dama ta samowa Bassam matar Aure." Sarki bai hana taba illah ma yanuna jin dad'insa da k'arfafa mata gwaiwa, domin ganinta yakeyi kamar ta fara son Bassam a yanzun." ____________________________ Yarima na zaune a sashinsa cikin lambu yana hutawa." Hajiya zainab tashigo cikin lambun." Yarima na kishingid'e yana shan isa, ga d'awaisu nata shawagi gabansa da bayansa." Ganin hajiya zainab tanufo shi, yasa yayi saurin d'aure fuska, yana cewa me ya kawo ta kuma?." Metake keso?" Kafin ta iso har kuyangunta sun je cikin sauri sun yi mata shin find'a a gefen Bassam." Tana isowa d'auke da d'anta Yazeed, bata b'a lokaci ba ta zauna tana ta fara'a a fuskarta." A ranta kuma ta kaici ne ke damunta irin yanda taga Bassam ya d'aure fuska kamar baitab'a yin dariya ba." Da ita da babu duk d'aya." Ta kuma k'ak'aro murmushin dole tace "Yarima ga k'aninka na kawo maka tunda na lura baka damu da ka ganshi." "Sai nake ganin har yanzun baka ga farta min abunda ya faru a can baya ba?" D'auke kansa yayi, idonsa ya sauka a kan wata barewa dake wasa da 'd'anta." Ajiyar zuciya yayi har har a lokacin bai kalle ta ba." Dogaransa keta mata sannu da zuwa." Sai a lokacin ya d'an saki murmushi ya dube ta da kyau." Duk da manyanta ta shigeta tana da kyau, kyan nata bai dusheba, Ransa kuma yace "dama macce mai kyau had'ari ce dan haka na tsani naga macce kyakkyawa, saboda nasan had'arin da ke tare dasu." Daga sama yaji tace "Yarima naji ance sarki ya baka manyan gonakinsa guda biyu kayi masa godiya kuwa?" Murmushin sa yayi na gefen baki, Sannan ya kalle ta yace "ranki ya dad'e ai ina ganin a gabanki akayi komai ko kin manta ne?" Da alama abun ya tsaya maki a rai." Shuru tayi tana kallon gefenta, saboda jitayi bata iya k'ara kallonsa, domin yana da wani irin Abu a cikin idanunsa dake sashi yin wani irin girma idan ka had'a ido dashi karon farko baka son kasake na biyu." [3/5, 4:44 PM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S* _we don't just entertain and educated we tauch the heart of the readers_ #WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM #IG PML WRITERS #https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035 #http://maryamsbello.blogspot.com *33* Bata kuma had'a ido dashiba, Kuma bata kuma yin magana ba." Mik'ewa tsayi tayi cikin natsuwa, Tana k'ara kallon tsarin ginin sashin Yarima Bassam, Tasan nashi yafi nasu nesa ba kusa ba." Tsarin ginin sa, yafi nasu kyau nesa ba kusa ba." Mts!! Tayi tsaki a zuciyarta tace Yazeed ya ka mata yayi rayuwa a wannan gidan ba kaiba." A zahiri kuma ta k'ak'aro murmushin dole tace "ina maka murnar zama cikakken mutum." zata wuce kenan, Bassam ya kalleta yace "bakinzo muyi maganar aure naba ne?" Ta wangale baki ta dawo ta zauna "tace har naso in mance abunda ya kawoni." Zan turo maka 'yan mata sai ka zab'a, wacce tayi maka." Murmushi yayi na gefen baki yace "A'a kitara min su a can b'angarenki in zab'a a can, ko kin manta me uwa ce." Ta had'iye wani irin miyau da ya zamto mai d'aci a mak'oshinta, Sannnan ta kuma mik'ewa tsaye tana tafiya tana cewa "ba damuwa in dai wannan ne kana iya shigowa gobe da k'arfe hud'u da rabi na yamma." Bai amsa mata ba sai kallon su yakeyi ita da 'yan hidimar ta. A ransa ya ce munafuka Allah ka d'aura ni a kanki." *kuyi hak'uri da wannan* [3/5, 4:45 PM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S* _we don't just entertain and educated we tauch the heart of the readers_ #WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM #IG PML WRITERS #https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035 #http://maryamsbello.blogspot.com *34* *Washe gari* Hajiya zainab ta shirya k'ayataccen biki na musamman. Ta Tara 'yan mata masu kyau da aji." Anyi masu kwalliya anshirya su Yarima kawai ake jira yashigo ya zab'a." Shuru ba Yarima ba labarin sa, Har kusan magariba bai zoba, hajiya zainab tashiga bak'in ciki da jin haushi wulak'anci kunya tata da Yarima yayi mata a idon jama'a, sai cizon d'an yatsanta takeyi, tana safa da marwa a cikin falonta." Wato ita Bassam zaiyiwa haka?" Ta tara mutane amma ya kunyatata yak'i zuwa." Tana cikin tunanin ne sai ga d'an aike daga Yarima, Cewa a shaidawa Hajiya zainab ba zai samu damar zuwa ba yana wurin wasa da doki." Tsawa ta dakawa d'an aiken cike da jin haushi, tace "yi min shuru, tashi kabani wuri kar yanzun na Sanya ayi maka bulala d'ari." Da sauri d'an Aiken yarima yaja 'yan takalminsa yayi fice" Ta kuma Shiga bakin ciki, tana cizon hannun, ta juya ta kalli sarkin gida dake gefenta zaune tace "Bassam har ya isa ya kunya tani?" Sarkin gida yace "ina ya isa kuwa? Tunda a k'ark'ashin ki yake ranki ya dad'e." "Sarkin gida yaza muyi da abunda ka amso wurin boka?" Tunda ko taron baizo ba." Wannan yaro Allah yayi tsinanne wallahi." Sarikin gida ya kuma runsunar da kai k'asa yace "karki damu ranki ya dad'e." A fad'ace tace "ya za'ayi kace karna damu, kasan irin mak'udan kud'in da na kashe wurin amso wannan maganin kuwa?" To kasani kai ne sarkin gida, kai Kasan yanda za'ayi da hanyar da za'abi a b'ata rayuwar Yarima, idan bakiyi k'ok'arin aiwatar da hakan ba, zan d'auki mataki a kanka, zan Sa a fille maka kai." "Tuba nakeyi ranki ya dad'e a gafarce ni, zakiga aikin da zanyi a kansa, kai koda ya bar garin nan sai dai kiji labarin ya mutu mushe ranki ya dad'e a d'an k'ara mana lokaci." "Shi kenan tashi katafi." Ya mik'e ya fita gumi sai zubo masa yakeyi, saboda tsabar tsoro ance za'a cire masa kai." Yace "kai wannan matar hatsabibiyace idan baka ganta a wuta ba ranar lahira to hayak'i ne ya kareta." Bassam kuma ya kishingid'e a sashinsa cike da farin ciki, domin yau yasan ya bak'antawa hajiya zainab kuma kad'an ma tagani, domin duk abunda take shiryawa yana sane dashi kuma Allah ba zai bartaba." Bayan sati biyu da hakan, 'Yan mata ne su biyar hajiya zainab ta zab'o masu kyau ga aji ta shiryasu da kanta, ga abinci kala kala ta shirya, kowacce tayi shiga ta gani ta yabawa, da ka gansu ka San suna da wani matsayi." 'ya'yan ciroma ne da waziri har da d'an iya, hajiya zainab ta kirasu tace "yarima ne yake son yayi aure zai zab'i matar aure daga cikinsu." Kowa nason 'yar sa tazama sarauniya idan Yarima ya amshi mulki." Don haka babu b'ata lokaci aka turosu, yau kwanansu uku sai gyara su akeyi." Da yamma kamar kullum Yarima na kishingid'e cikin garden inda yake shak'a tawa cike da nishad'i d'auke a fuskarsa, iska na kad'awa, can ya hango shigowar 'yan mata, Ya juya ya kalli Audu dake zaune a gefensa, yace "Audu su waye wad'an nan kuma?" Audu yace "ranka ya dad'e sune bak'in dana gaya maka zakayi." Bassam yace "amma baka fad'a min yanzun zasu zoba." Audu yace "haka ne ranka ya dad'e 'ya'yan waziri ne da ciroma da d'an iya suka Zo gaisheka." Murmushi yayi da ya tuna da hajiya zainab ya riga da yasan duk shirinta ne, yana ganin har yanzun bata san halin shiba." Sallama da kirarin da dogarai keyi masa yasa ya daina tunanin da yakeyi, Yana kallon takon ko wacce a cikinsu babu wanda ba tada kyau, ko wacce tasha ado na alfarma ga tsari." Sai da suka ajiye abun da suka kawo inda aka shirya kayan ciye ciye sannan suka zauna a kan kafet mai laushin gaske da aka shinfid'a don zama." Bassam yasaki fuska yace "ina godiya da tsarabarku gareni." Dogarai suka had'a baki sukace Yarima ya amsa gaisuwar 'yan mata adon gari." D'aya bayan d'aya suka fad'i sunayensu da na mahaifinsu." Fuskarsa cike da fara'a yace "nagode da zumunci." Kowacce a cikinsu ta tsura masa ido ta gid'eme domin Yarima ya kai namijin da dole a soshi ga kyau ga kud'i." Minti biyar suka d'auka bayan maganarsa, sannan Yusra d'iyar waziri tace "ran Yarima ya dad'e ance zakayi aure kana Neman mata?" "Haka ne ya fad'a a tak'aice." "Ko zaka zab'a d'aya a cikinmu domin biyan buk'atarka ta aure?" Ya k'ura mata ido fuskarta mai tsawo CE, amma bata da muni." Murmushin da yakeyi a fuskarsa ya kashe mata jiki, taji jitake kamar yace ya zab'eta." Katse mata tunani yayi daya ce " Ku gayawa hajiya zainab ina godiya da tayinta, sai mun had'u zamuyi magana da ita." Suka mik'e rai a b'ace domin ba hakan suka soba, sun so yace "yana son dukansu ko a kwarkwara yana iya ajiyesu." *ikon Allah 'yan mata adon gari kenan🤔* Yace "Audu ka d'auko kud'i kaba ko waccensu, "an gama ranka ya dad'e, Allah ya k'ara taimakawa." Suna wucewa ya tashi ya shiga bedromm d'inshi yacewa Audu "yana so hutu." Shiga yayi ya kwanta rufda ciki a kan gadonsa, yashiga tunin, mahaifiyarshi, yasan da tana da raye hajiya zainab bazata sanyashi a gaba hakan ba, domin ya lura duk a gidan shi kad'ai ta tsana, to meyayi mata?" Bata tausayinsa ko Dan ganin shi marayane baya da uwa." Ransa ya b'aci matuk'a ya mik'e tsaye ya bud'e fredge domin d'auko giyarsa yasha, tunawa yayi da ta k'are, Ya koma kan gadonsa ya kwanta, yashiga tunani, tunawa yayi da Jummai wadda tazamo kuyangarsa tun yana k'arami kamin yatafi England karatu." Mik'ewa yayi tsaye yafito falo, ya shiga kwalawa Audu kira." Da gudu Audu yashigo ya tsugunna gabanshi." Yace "gani ranka ya dad'e." Bassam ya kalli Audu Yace "ina jummai?" Audu yace Allahu Akbar, Allah yayi mata rasuwa shekaru biyu da suka wuce." Bassam ya dafe kai🤦‍♂Ayyah Allah ya jik'anta, ciwo tayi?" Audu yace "Eh sanyi ne ya shigeta." Bassam yace "Allah sarki nasan tanada 'ya ko?" Audu yace "Eh tana da 'ya amma tayi aure." Amma akwai jikanyarta da yanzun tana aiki a nan gidan hajiya zainab." Bassam yace "kaje ka kawo min ita." "To ranka ya dad'e." Rok'on Allah yakeyi Allah yasa bata da kyau, domin yasan kakarta akwai rashin kyau ga kuma bak'i, yasha gaya mata a lokacin da yana yaro ta daina kallonshi, domin tana da manyan idanu kamar su fito waje, ga hancinta a bud'e yake sai a hankali daka ganta kaga irin bayin nan 'yan wahala." Bayan isha'i yasanya Audu yasawo masa barasa, Ya ajiye gabansa, yana sha yana kallon jikar Jummai wadda ta kame jikinta wuri d'aya tana gaida Yarima." Yarima yace wa fadawansa sufita waje, Ya maida kallonsa gareta, yayi sa'a kuwa bata da kyau akwai muni kam, gatanan dai, kamar dutse." a hankali, ya kai idonsa a kan k'irjinta ba laifi tanasu cikanku, sannan tana da haske, duk da dai bata kai kakarta da muniba amma kuma baka isa kace tana da kyauba." Ya kuma kallonta yace "meye sunanki?" Jikinta na rawa tace "Saratu." Da muryarta kamar ganga. Ba yauk'i irin na 'yan mata da suka amsa sunansu irinsu Afnan😜 Yace " Saratu kinaso?" Tambayar ta zama shock a gareta bata amsa masaba, don a ganinta ba taji da kyau ba, k'ila dai Aljanine yayi maganar ba Yarima ba." Ya kuma maimaita maganar, "Saratu kina sona?" Zaki iya aure na." Ajiyar zuciya tayi tana kallonsa, tace "ranka ya dad'e dani kake?" "Basunanki Saratu ba?" Bakinta a sake hancinta a bud'e ta rasa abunda zatace tayi shuru tana murzar hannunta." Audu ya kira, yace "inaso kasame jakadiya ka gaya mata na zab'i Saratu a matsayin mata!" Audu ya dubi Saratu da Sauri ya dubi Yarima yace "Ranka ya dad'e banji da kyau ba." Bassam yace "nace ka gayawa jakadiya ta sanar da maimartaba da Fulani cewa nazab'i Saratu a matsayin matar da zan aura." "Ikon Allah, Audu ya fad'a a bayyane, "ke k'arshen wahalarki tazo, haka Allah al'amarinsa." Yasanya ta gaba yana ta surutunsa, Allah me yin abinda yake so." [3/5, 4:45 PM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S* _we don't just entertain and educated we tauch the heart of the readers_ #WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM #IG PML WRITERS #https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035 #http://maryamsbello.blogspot.com *35* Washe gari labari ya zagaye gari Yarima ya fidda kuyanga a matsayin matar da zai aura." Tabid'jam! A gurin hajiya zainab, guyangar ma wadda tafi tsana a cikin kuyanginta mai wanke mata k'afa." Me Yarima yake son maida ita ne?" Lallai ya d'aukowa kansa wutar dafa kansa." Saratu yake son aure?" Tun jiya da labari ya sameta ta kasa barci, tasanya saratu a gaba, Tana tambayarta abunda tajeyi wurin Yarima har da ya ganta yace yana sonta." Taga ita kanta da am macce bata son had'a ido da saratu idan tana mata gyaran farce, da wankin k'afa saboda tsananin muninta bare Yarima." "Idan Saratu ta burge Yarima to kenan ita hauka kawai takeyi na k'ok'arin samo masa macce first class kenan." Jakadiya kuma ta sanya aka warewa saratu sashi guda, inda za'a gyarata, an kuma sanya lokacin aure nan da wata uku masu zuwa." Sarki kuma abun ya girgiza shi dajin wannan labari, daga baya kuma yashiga jin dad'in d'ansa yayi abunda ba'a tab'a yiba, kuyanga ta zama sarauniya?" Lallai Yarima yazo da nashi tsarin mulkin." Saratu har yanzun gani takeyi kamar mafarki takeyi, domin a mafarki take ganin komai ke faruwa, Har a lokacin da aka wanke ta daga daud'ar da take ciki bata yarda Yarima zai aureta ba." Yau kusan sati d'aya kenan ana koyar da ita yadda zata yi kwalliya da irin shigar tufafin da zata rik'a sanyawa." A can fada kuma sun kasa yadda da zab'in da Yarima yayi, Sarki ya d'aurewa Yarima gindi yace " tunda abunda yakeso ne to kada wanda yasake juya zancen a kyaleshi yayi abunda yake so lokacinsa ne." Ba'a bari kowa yashiga wurin saratu sai jakadiya, A lokacin saratu tasha wanka da kayan k'amshi ana ta cud'ata da dilka." Komai yasamu gyara dole ya canza komai muninsa kuwa, saratu tayi fes fes da ita gwanin sha'awa duk da fuskarta ta d'an canza, fatarta tayi sumul sumul, kusan wata d'aya ana ta gyaranta." Akazo wurin koyar da ita cin abinci, saratu, sannan aka kuyar da ita yanda zata tarbi mijinta, a matsayinta na matar d'an sarki Mamaki tashiga yi kodai barci takeyi?" Kusan watan nin biyu ana Abu d'aya." Da d'an sauyin abinci da take samu da sauyin yanayi yasa saratu tak'arayin kyau har da 'yar k'ibarta tayi." A cikin wata na uku aka d'aura auren Bassam da saratu anyi taron sosai, a gari kowa magana yakeyi, d'an sarki ya aure baiwa, masu kushewa nayi masu yabawa sun yaba, dama ai haka rayuwa take babu abunda zakayi ya zama kayi gwaninta ga mutane." Sashin Yarima aka kawo saratu, An gyara wurin tsaf tsaf, Saratu bata iya runtsu idonta, saboda kada ta farka daga barcin da takeyi." Ga kuyangi irinta sai kai da komo suke mata, suna faman CE mata ranki ya dad'e." Ango Bassam yana tare da mahaifinsa suna hira a can fada kamar yadda suka saba, Maimartaba sai tsokanarsa yakeyi yana fad'in "ango kasha k'amshi saika tashi kaje gun amaryarka na tabbata tana can tana jiranka." Mik'ewa Bassam yayi had'ida yiwa Sarki sai da safe." Bassam ya isa d'aki ya iske Amaryanshi saratu, ko ina a d'akin sai k'amshi yakeyi.' Tanajin ya shigo ta koma k'asa ta zauna takasa ai watar da abunda aka koyar da ita idan mijinta ya shigo." Bassam bai damuba yaje yayi wanka yazo ya zauna a gabanta sai zazzare ido takeyi." Ya kalleta yace "tashi kije kiyi arwala muyi sallah." Bayan sunyi nafila, ya rik'o hannunta zuwa kan gado ya d'ora hannunsa saman kanta yayi addu'a, Sannan yace "kisaki jikinki muyi soyayya ki daina jin tsorona." Tace "to." A ranar Bassam ya karantar da saratu ilimin kwanciya, Saratu har ihu takeyi na dad'i." Bassam ya rufe mata baki saboda kada kuyangi sujita." Itama ba bayaba a wurin kwanciyar su ta farko, Sam Bassam baidamu da rashin samunta da baiyi ba a matsayin budurwaba, saboda yasan kuyanga ce,. Kuma kuyanga komai na iya samunta, don haka bai kyamace taba." Saratu tasha dad'i sai murna takeyi da godewa Allah tasamu miji kamar Bassam." Tanaji ana cewa akwai maza masu iya harka, akan Bassam ta shaida domin duk abunda yakeyi cikin sauk'i da hankali yake yinsa, sai da ya sumar da ita akan dad'i." Tun daga lokacin idan zai shige wurinta, saiba kuyangi da dogarai umurnin suyi nesa dasu, domin yagano Saratu bata iya control d'in jin dad'inta sai tayi ihu da surutai." Amarci sosai suke kurzawa ba k'arya." Hajiya zainab ta fara tunanin abunda ya dace tayi da Saratu, Ta lura da alama yarinyar zasu goga da ita kenan, Tun jiya tatura akira ta amma tak'i zuwa, ya dace ace tana zuwa kullum ta gaidasu a matsayinsu na iyayen Yarima mijinta." Har zuwa yau da tayi sati biyu bata zoba." _____________________________ Jakadiya tashigo da saurinta ta fad'i k'asa a gaban Hajiya zainab tana gaisuwa, tana fad'in "ranki ya dad'e Allah ya ja zamaninki matar Yarima ta iso dan gaidaki." Bata amsa ba, sai dai tayi nuni da hannunta alamar ta shigo." . Saratu ta shigo cikin k'asaita da isa, ta zauna a kan kujera mai kallon ta hajiya zainab." Hajiya zainab ta bita da kallon mamaki tace " Ke! Mekike nufi?" Munzama d'aya kenan?" To k'asa zaki zauna tunda har yanzun ke ak'asa na kike, ke matar yarima ce ba matar sarki ba." Saratu tayi mata wani irin kallon raini tace "Ashe kinsan da haka?" Ta fad'a a gadarance." Sannan saratu ta d'an durk'usa k'asa tayi gaisuwa, Kuyangu sukayi saurin amsa mata, tare da jera mata kirari, suna fad'in " matar Yarima guda d'aya matarsa da ido bay...... "Kai kuyi min shuru dan ubanku, hajiya zainab ta fad'a cikin jin zafi." Saratu ta kalleta cike da mulki, tace "idan baki bari suka k'arasaba bazan sake zuwa gaisheki ba, tunda yana d'aya daga cikin aikinsu." Hajiya zainab tasaki baki tana kallonta, Nan fa kuyangu suka zube suna bawa Saratu hak'uri." Da ka kalli idon hajiya Zainab kasan tashin hankali ya bayyana a tare da ita." Amma sai tayi k'ok'arin kame kanta kar saratu ta fahimci wani abun." Har saratu ta fita kuyangu basu daina ban hak'uri gareta ba." Hajiya zainab na ganin saratu ta fita, ta aika aka kira mata sarkin gida." Sarkin gida jiki na rawa yazo, ya zube a gaban hajiya zainab." Tace "kasan abunda ke faruwa?" Sarkin gida yace " A'a ranki ya dad'e." Hajiya zainab tace "inaso ka b'atawa saratu matsayinta a gidan nan." Sarkin gida yace "ranki ya dad'e metayi?" "Zagina tayi yanzun nan." "Iye ranki ya dad'e, meya dace ayi mata?" "Ina da labarin Yarima jarumine sosai don haka ya dace a sallace ta ya daina jin dad'inta." Kaga tunda naga irin Matan da yakeso, sai mu had'a shi da wata irinta, har wadda tafita lalacewa." Sarkin gida Ya jinjina Kansa." Sarkin gida yace "ranki ya dad'e magana ta kud'ice kinshirya?" Tayi dariyar keta tace " kaje kasamu d'an jumma ku shirya ko nawa ne zai baka a fara aiki daga yau." Yace "angama ranki ya dad'e." Ta kyalkyale da wata kalar dariya, tace "Ni za ki yiwa wulak'anci?" Sainaga bayanki shaid'a niya kawai." [3/5, 4:46 PM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S* _we don't just entertain and educated we tauch the heart of the readers_ #WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM #IG PML WRITERS #https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035 #http://maryamsbello.blogspot.com *36* A kwana atashi ba wuya ga mai yawancin rai, Saratu tasamu kwanciyar hankalin, tayi fes da ita an zama matar manya, babu abunda ke damunta a rayuwa." Halinta d'aya ne dai sai a hankali na wulak'anta bayinta, domin irin wulak'aci da bautar da tasha a wurin hajiya zainab shi take cewa zata rama a wurin kuyanginta, kwata kwata kuyanginta basa jin dad'inta ko kad'an daga ta buge wannan sai ta naushi wancan." Juye takeyi kam a gidan wani wurin hartafi hajiya zainab mulki." Hajiya zainab ta zura mata ido cike da mamaki tana kallon ikon Allah."🤔 Dole taja da baya domin yanzun lokacin ne, Tana gudun kada tayi mata magana tasata jin kunya." ______________________________ Anna na sane da duk abunda ke faruwa a gidan, amma taja bakinta tayi shuru tana zuba ido taga iya gudun ruwansu, Afnan da taji labarin Bassam yayi aure, d'aki tashiga ta rufe kanta tashiga rusar kuka, babu abunda take tunawa sai Kaka da malam Nura." Kwana biyu har da 'yan rama tayi saboda son ganin Kaka da takeyi, kullum duk ta kwanta barci sai tayi mafarkinta." Kullum tunanin ta "wai me Bassam yake nufi da ita ne? Meyasa ya tsaneta?" Meyasa baya maida ita a gaban iyayenta." Saboda kawai mugunta, da tsanar da yayi mata, ta kuma fashewa da wani sabon kuka mai tsuma zuciya." Kwana biyu Anna ta lura da Afnan tashiga damuwa, tashiga k'ok'arin kwantar mata da hankali, tana lallashin ta." Afnan na kwance abun duniya duk ya dameta tun lokacin da taji labarin Bassam yayi aure, bata kuma samun natsuwa ba." Tarasa meyasa ta shiga damuwa." Anna na bedroom d'inta Afnan ta diba taga bata nan, ta kira wani yaro maiyi masu aiki dake zaune a k'ark'ashin Anna, tace ya rakata wurin Yarima." Da yamma ne lik'is Yarima na lambu yana hutawa tare da Saratu, sai hira sukeyi suna dariya." Afnan ce tafe tareda yaro d'an rakiya Sun nufo wurin Yarima." Sabbin fadawa da kuyangin da aka zubawa Yarima basu tsaron lafiyar shi. Suna ganin Afnan ta nufo su, Basu santaba don haka suka tsayar da da ita suka hanata shiga, sai sunje sun nemo izinin shigarta sannan." Kallo tabisu dashi cike da mamaki, Tace "idan kukaje kuce masa sak'o ne daga wurin Anna." Dajin ta ambaci Anna sukayi saurin bata wuri ta wuce saboda sunsan darajar Anna a wurin Yarima." Daga sarki sai Anna sune kawai ke juya Yarima kuma yabi umurninsu a yanda sukeso." A can ta hango Bassam tare da Saratu zauna da alama suna cikin farin ciki, ido ta tsurawa saratu tana kallonta sai da ta kusan tuntsirewa da dariya data hango k'aton bakin saratu ta wangale shi🤣 wai ita nan dariya ta keyiwa miji." Tashiga fad'i a zuciyarta "dama wannan abarce itace Amaryar da ake cewa ya aura?" Tafd'ijam lallai wannan mutumin yayi dacen mata." Hangota yayi tafe zata k'araso wurinsu cikin tafiyarta mai Jan hankali, yayi kamar bai gantaba ya shiga yi mata kallon gefen ido." Lura yayi da inda take kallo Saratu ce ta tsurawa ido, fuskarta na nuna alamar dariya takeso tayi, ta kuma matseta." Yasan ba komai zata yiwa dariya ba illah fuskar saratu." Kuma yasani sarai Afnan bata da kunya sakakkiya ce gata da wautar tsiya, yanzun zata iya kunyata shi a gaban bayinsa." Had'e fuska yayi, yana jiranta ta k'araso yaji meke tafe da ita?" Meta zoyi nan?" Shi har ga Allah idan ba ganinta yayiba mantawa yakeyi da ita." Tana k'ara sowa ta kai gwaiwarta k'asa tana gaida shi, bata kalli inda Saratu take ba." Bassam bai amsa mata gaisuwarta ba, sai ma kallonta da yayi yaji a nan take gabansa ya fad'i da yayi tuzali da k'aramin bakinta, sai da ya lashe leb'onsa na k'asa." Sannan ya saita kansa yace "meya kawoki wurina?" Ya zaki zomin gida batare da kin nemi izinin matar Yarima ba?" Afnan taji wani Abu mai zafi ya tab'ata a k'ok'on zuciyarta, Ta juya ta kuma kallon saratu, Sannan tace "kayi hak'uri na katse maka jin dad'i, kana tare da matarka abar sonka." sannan ta sunkuyar da kanta k'asa tace "Nazo ne Neman izini a wurinka, inaso intafi gida inga iyayena kullum dasu nake kwana dasu nake tashi a raina." Kallonta yayi yace "me kika ce?" "Dan rainin wayyo wato ma baiji abunda nace ba, tafad'a a zuciyar ta." Amma kuma tunda ita ke nema dole ta maimata masa abunda take cewa." Tace "tunda nazo garin nan wata na gama sha d'aya banga kowa nawa ba." Kuma banyi magana da kowa nawa ba, na kuma neme wayata bangan taba, wani b'arawo ya sace ta." Dariya ma taso tabashi wato "shine b'arawo?" Ya dake ya kuma had'e fuska, yace " Baza kijeba." Ta yaya zaki sanya hannuki ki mare yarima d'an sarki sannan kuma kice zaki zauna lafiya?" Wato kinaso kice kin mare banza kenan?" tunda har yanzun banga na nadama akan fuskarki ba, illah koda yaushe da wata sabuwar rashin kunya kike k'ara yimin, domin ganin Anna tana tare maki, har ya kai yanzun Anna bata son ganina idan kina kusa da ita." To yanzun ina Anna?" Kinkawo kanki zanyi maki abunda naga dama kuma babu Wanda ya isa ya hanani." Ya kalli yaron da suke tare da ita, yace "kai tashi kayi tafiyarka, kuma muddun kaji Anna na nemanta ka kuskura kace Kasan inda take saina sanya anyi maka bulala dubu." Da sauri yaron ya tashi yana bawa Yarima hak'uri." Idanun Afnan suka fara komawa launinja, Saratu ta d'ago kanta tace "Ranka ya dad'e wannan kuma wacece?" "Yace "Baiwar ki ce daga yau." Afnan ta d'ago idanunta da suka cika da hawaye, tana kallonsa, Shima d'in ita yake kallo yace "ki zama mai kula da matata banbaki izinin barin harabar gidan nan ba." Ya kira Audu." Audu yazo da saurinsa ya matso" Yace "wannan Yarinyar ta zama d'aya daga cikin kuyangun gidan nan, kada a bari ta bar gidan nan, kuma kar a bari ta zauna ko ina batare da inda Kunyangi ke zama ba, itama tayi bautar gida, irin yanda kuyangi keyi." Ya kalli saratu yace gimbiya ko kina da wani aiki da zatayi maki?" Saratu ta yamutsa fuska kamar kashi🙊 tace "ni babu wani aiki da zatayi min sai dai in zata kula min da wankan tumakina danake dasu." Yarima yace "duk abunda kikeso tayi maki gaya mata." A ranta kuma cewa take "can baya zan turaki, wannan kyan naki kamar Aljana ai sai ki amshe min mijina, tunda Nima a kuyanga ya ganni ya aure ni, kema haka na iya faruwa." Audu ya matso kusa da Afnan yace "tashi mutafi." Suka bar wurin, Yarima na kallonta yana dariya a can k'asan zuciyarsa yana fad'in bazan gyaleki ba har sainaga nadamar abunda kika aikata min a fuskarki." Afnan tafiya kawai sukeyi da Audu amma k'afafunta basu da kwari, A can k'arshen gida aka kaita, aka nuna mata wani d'aki babu laifi sabon guri ne." D'akin tabi da kallo gado ne na k'arfe hawa biyu sama da k'asa da alama akwai mutum a na k'asa, na sama ne nata kenan." zaunawa tayi ta fashe da kuka meyasa Bassam ke son kullum yaga ya wulak'anta mata Rayuwa?" In gaskiya ne ai itama matar sace." Meyasa yake son takura wa rayuwarta bayan ya rabota da iyayenta da masoyinta malam Nura." Kuka tafashe dashi mai sauti😭 *Wayyo Allah Afnan🙆* [3/5, 4:48 PM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S* _we don't just entertain and educated we tauch the heart of the readers_ #WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM #IG PML WRITERS #https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035 #http://maryamsbello.blogspot.com *37* Anna ta diba Afnan sama da k'asa amma bata gantaba." ta tambayi su jummai " ko sunga lokacin da tafita suka ce basu gantaba." Haka tabi kuyangi masu aiki a k'arshinta tana tambayarsu. Amma maganar d'aya ce masu ganta ba kuma basuga lokacin da tafita ba." Anna tayi bak'in cikin guduwar da Afnan tayi, tashiga cikin tashin hankali Wanda sai da ya bayyana a fuskarta." Yaron da yaraketa gidan Yarima yanaji ana cigiyar ta amma yaja bakinsa yayi gum." Bare idan ya tuna da bulalar da Yarima yace zai sanya ayi masa har dubu." Kusan Sati uku kenan Anna ta hana kanta zama lafiya, tasanya cigiyar Afnan domin bata son Basssm _yasan_ abunda ke faruwa Dan haka tabawa kowa umurnin yayi shuru da bakinsa." Afnan tashiga k'uncin rayuwa aiki takeyi ba k'afk'aftawa, daka ne kawai batayi ko shi saboda akwai injinin nik'a a wurin." Kwata kwata Saratu ta sanya a hanata zuwa Sashensu." Haka ta hak'ura ta zauna a cikin kuyangi kullum sai tayiwa tumaki wanka tare da dokin Yarima sannan ta kuma basu abinci." Akwai masu yin wannan aikin maza ne bayi, amma gaba d'aya Saratu ta daka tar dasu, tace "Afnan take so taci gaba da gudanar da aikin." Gaba d'aya yanzun ta daina kwana a d'akin da aka basu sai dai tashiga store ta kwana saboda wadda suke tare ta da ita ta kore ta, kuma ga mazan da take gani a d'akin." Duk Wanda yaga Afnan a wannan lokacin sai tabashi tausayi, saboda bata saba da wahala ba, haka nan take tursasa kanta, tana k'ok'arin ganin tayi aikin da aka sanyata ko yin haka ne, Allah zai amshi Addu'ar ta Bassam yaga tausayinta ya fitar da ita a wannan bak'in gidan, ya mai da ita gaban iyayenta." Tunawa tayi da Kaka sai ta fashe da kuka, tana kallon jikinta da kayan dake sanye a jikinta, irin na kuyangi masu d'auke da photon *Tambarin sarauta* lik'e a gaban rigar." Ta tuna da kayan da tazo dasu a jikinta T.shirt ce da zane sai abaya wadda ta rufe jikinta da ita." Amma saboda zalunci wannan mummunan mai kama da akwa kwa, tasanya aka kwace mata kaya aka bata na kuyangi ta sanya." A kwana a tashi Afnan har tayi wata biyu a gidan, Saratu bata k'aunar ta bud'e ido tayi tozali da ita, sai tayi ta korarta tana fad'in "ke 'yar Aljana matsa baya nace Kada kishigo ciki, koba haka nace maki ba?" Har Afnan ta hak'ura ta daina shiga ciki, duk yanda zatayi ta kaucewa aikin da zaisa taje sashensu shi takeyi." Idan tana yiwa tumakai wanka, zata shiga jero masu wak'ok'i cikin sautin muryarta mai dad'in sauraro, cikin k'ank'anin lokaci duk tumakin dake wurin ta sanya masu suna." Cikin k'ank'anin lokaci suka saba da ita, da zarar sunji sautin wak'arta, zasu zo su zagayeta suna kukan jin dad'in ganin ta." Ta d'ebo abincin su da ruwa taba basu, tashige cikinsu taita kallonsu tana shafarsu, ita kanta bata san tana son dabbobi ba sai yanzun." Dokin Yarima fari ne yana shan wanka a wurin Afnan. Sun saba da ita sosai idan kaji tana fira dasu sai kace da mutum takeyi." Dabba kamar mutum take Hankalin ne kad'ai ya rabasu da mutum, idan zasuyi kashi haka zasu ja jiki sutafi can gefe suyi." Masu gyaran wurin da sunzo sai su kwashe a kai lambu a zuba." A cikin lambun Afnan take samun kayan itace kala kala, taita tsinkowa tana sha, har ya kai tasaba da 'yan lambun sosai, wautar da takeyi masu ita take sanya su dariya." Yanzun ta ba kanta hak'uri ta rage tunanin Kaka sosai, idan taji tunanin yana son zo mata sai tayi saurin kauda shi, taci gaba da ma'a malarta." 'Yan mazan wurin suna ganin girmanta saboda takama kanta, shiyasa ko da wasa babu Wanda yatab'a tun kararta da magar banza." Kwanciyar hankali tasanyawa kanta yaba ta damar cikowa tayi b'ul b'ul da ita kyawonta sai kuma fitowa yakeyi." Wata rana Bassam yashiga wurin dabbobi, kasan cewarsa yana son dabbobi wannan dalilin ne yasan yashi ya ke kiyonsu." A lokacin da yashiga wurin yaga wurin ya canza mashi yayi fes fes dashi ga tumakai yagani tsaf tsaf da su musamman dokinsa a dayake fari har wani haske yakeyi." Mamaki yashigayi, a can k'asan lambu yaji wata murya mai dad'i mai kuma zak'i kamar sarewa tana rera wak'a, Da sauri ya haye kan dokinsa ya gangara zuwa lambun." Haka ya dinga biyar sautin muryar har ya iso gaf da sautin muryar ke fitowa, tsayawa yayi yana sauraren muryar yana lumshi ido, bai tab'a tunanin Afnan bace, lumshe idon da yakeyi sautin muryan na ratsashi ta ko ina." Jin da yayi Wanda ke wak'ar yayi shuru, Ya sanya shi saurin bud'e idonsa yashiga wai ge waige." A can bayanshi kuma inda yafito wurin kiyo a can ya kuma jin wak'ar natashi." Sauka yayi a kan dokinsa yashiga takawa a k'afa a hankali ya dinga bin sautin muryar yana tafiya har ya iso wurin." gabansa ne ya fad'i da yayi tuzali da Afnan tana yiwa tumakai wanka tana wak'a tare da karkad'a k'ugunta, tana watsa masu ruwa a jikinsu, tana kyalkyalar dariya cikin sautinta mai dad'i." Shagala yayi da kallonta yana sauke wani murmushi a fuskarsa Wanda bai San yanayin saba." Ko me yatuna da sauri yaja tsaki ya bar wurin yana mamakin ko mema yasan yashi ya tsaya kallonta." Komawa yayi sashinsa amma kunnuwan sa basu daina jiyo masa sautin muryar Afnan ba, idonsa bai daina hasko masa k'ugunta ba, da take karkad'awa." Tsaki yaja ya mirgina gefen gado yayi tufda ciki, yana tunani." Saratu tashigo d'akin kai tsaye ta fad'a kan jikinsa kamar yanda tasaba, tana fad'in "honey yaushe kashigo?" ina can ina nemanka narasa inda kashiga." Tasanya hannunta a k'irjinsa tashiga shafawa." Saratu akwai jarabarbiya tsiya☹." Tsawa ya daka mata wadda bai tab'a yimata irinta ba, yace "tashi kifita ina muk'atar kad'ai cewa ni kad'ai na hutu." Zaro ido tayi had'ida turo k'aton bakinta alamar shagwab'a, Zata bud'e baki tayi magana yace "karki ce min komai pls tashi kifita." had'ida nuna mata hanyar waje." Mik'ewa tayi jiki ba kwari ta fita, kallo yabita dashi, yana harararta🙄 ya furta a ransa "kai wannan abar akwai muni😂 [3/5, 4:48 PM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S* _we don't just entertain and educated we tauch the heart of the readers_ #WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM #IG PML WRITERS #https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035 #http://maryamsbello.blogspot.com *38* Juyi kawai yakeyi akan gadon sa, amma fuskar Afnan kawai yake gani tare da d'an k'ugunta da take ta faman karkad'awa tana rawa." Dogon tsaki yaja ya kuma juya kwanciyarsa, daga rigingine zuwa rufda ciki yaja wata doguwar ajiyar zuciya tare da fitar da wani kalar numfashi a bakinsa." Can kuma yaja wani dogon tsaki had'ida runtse idonsa, a zuciyarsa yana fad'in " meyasa fuskar yarinyar nan tak'i fita a ido na?" Indai kyau ne tana da kyau, amma kyauwon banza ne domin babu abun ke tare da macce kyakkyawa sai mugunta, da iya sharri." Tunawa yayi da abunda yafaru a tsakaninsu, farkon shigarta sashinsa, lokacin da yaka mata a d'akinsa." Tunawa yayi da Laushin fatar jikinta tareda d'an k'aramin bakinta da yashiga tsotsa kamar sweet." Kuma mirginawa yayi had'ida lashe bakinsa, gaba d'aya Jiyayi tsikar jikinsa natashi kamar anyi mashi shocking." filo ya lalubo ya rungume had'ida sauke numfashi a hankali tare da lumshi idon shi." daga nan har barci b'arawo yayi awon gaba dashi amma Afnan ce a idonsa." *Sarkin gida*a gaban Hajiya zainab durk'u she yana jera mata kirari." Murmushi tabishi dashi alamar ta amsa." domin da zarar taga sarkin gida cikin wannan yanayin tasan ansamo nasara wurin boka." Sarkin gida ya kalli Hajiya Zainab yace "ranki ya dad'e ansamo nasara, ya mik'a mata k'ullin magani k'ulli biyu, yace "wannan aikin nakine ranki ya dad'e domin boka yace "so akeyi ta shanye shi, ya kuma tabbatar min da cewa da zarar ta shanye maganin zata koma Salaf kamar miya ba gishiri." Kinga duk rawar k'afar da Yarima yakeyi a kanta zai daina." Dan na lura da ita a gidan nan so takeyi ta wuce ki a mulki." Hajiya zainab tasaki wata irin dariyar mugunta tace " nagode sarkin gida dan haka nake sonka duk a cikin fadawa na." Ta d'ebo kud'i masu yawa ta mik'a masa tace "wannan nakane." Ya amsa yana godiya had'ida zuba mata kirari sannan ya fita." Saratu ce cikin shiga ta alfarma tafiya takeyi kuyanginta suntake mata baya, ta nufi sashin Hajiya Zainab." Da shigarta ta tarar da hajiya Zainab a zaune a kan kujera tana bawa Yazeed abinci." Batabi takan hajiya zainab ba ta jawo kujera ta zauna cike da mulki da isa, ta d'ora k'afa d'aya kan d'aya ta shiga kallon hajiya zainab tana jefa mata da habaici." Hajiya zainab tashiga ramawa, tace "dibeki ba ciki ba goyo, Allah yasa Yarima ba juya ce ya kwasowa Kansa ba, kamar sauran matan ubansa." Saratu tayi shuru tana nazari domin bata tab'a tunanin haihuwa ba sai yanzun da hajiya zainab tayi mata gori." Ranta ya sosu tashiga tunanin abunda zata cewa hajiya zainab domin ta huce abunda ta furta mata, amma tarasa kalma ko d'aya." Mik'ewa tayi tsaye cike da takaici zata fita." Hajiya zainab ta kalle ta, tace "har kintashi zaki tafiya?" Na aza kinzo ne domin muyi fira." Saratu tayi shuru ta bita da kallo batayi magana ba." Illah ta koma ta zaune." Hajiya zainab ta kuma kallon ta, tayi murmushin cin nasara, tace "Anya saratu baki buk'atar taimakon manya?" Anyi aure kusan shekara d'aya da rabi amma babu ciki?" Jikin saratu yayi sanyi, ta manta da ita maiyin maganar shekararta nawa da yin auren kamin ta haihu?" Ta sunkuyar da kanta k'asa domin maganar hajiya zainab ta fara shigarta, Hajiya zainab ta gano tayi nasara a kan saratu, don haka ta kwatar da Yazeed, ta taso ta matso kusa ga saratu ta saka mata k'ullin magani a cikin tafin hannunta ta rife tana murmushin da bai kai cikiba." Tace "kinsan na d'auki shekaru a gidan nan ban haihuba, amma daga baya dana tashi tsaye da Neman magani bagashi na haihu ba, kuma na haifi d'a namiji." Saratu ta katseta da cewa "eh nasa ni." Hajiya zainab tace "kije kiyi k'ok'arin samun ciki, "wannan maganin dana baki zai taimaka maki ki wuri samun ciki, sannan kuma ki haifi d'a namiji." Saratu taji dad'i cikin murna tace "da gaske?" Hajiya zainab tace "jeki ki kwada mana bari in k'aro miki idan kika fara amfani dashi kada ki tsaya sai kin tabbatar da ciki yashiga jikinki." Saratu taji dad'i sosai tace wa hajiya zainab "kiyi hak'uri da rashin kunyar da nake maki, ranki ya dad'e, idan na tuna da irin wahalar da nasha ne a hannunki sai intajin ba dad'i." Hajiya zainab tace "banga laifinki ba, saratu kada ki damu kanki ai yanzun munzama d'aya, Kisaki jikinki dani zan koya maki abubuwa da yawa wadda zai sanya mijinki ya k'ara gamsuwa dake a b'angaren auratayyah." Murmushin jin dad'i saratu takeyi." Hajiya zainab tace "banaji ance kina ihu ba, idan kina tare da Yarima me yake yine haka da bazaki iya danne jin dad'inki ba har sai kinyita ihu?" Saratu tace "haka aka ce maki?" Hajiya zainab tace oh baki sani bane?" Kunya ta kama saratu, Ta shiga tunanin kwana nan kwata kwata Yarima d'in ya canza mata wurin kwanciya, jiya ma yana kanta yana farawa ya sauka ya tallabe kansa, tayi masa tambayar duniya abun da ke damunsa?" Sai yace mata "babu komai." Haka suka kwana babu abinda ya kuma shiga tsakaninsu, Kuma tasan da ba haka yake ba." Tasan da yana matuk'ar son ya kasance tare da ita." Ajiyar zuciya taja mai k'arfi, ta kalli hajiya zainab tace "zantafi sashina nagode kwarai da kulawarki gareni." Hajiya zainab ta d'auko wani galan na wani nau'in maganin ta mik'a mata tace "wannan zai taimaka maki zaki matse a can k'asa." Saratu taji dad'i sosai kamar hajiya zainab ta gano matsalar ta a bud'e take, batajin kanta gam to koshi yasa Yarima ke nisanta kanshi da ita ?" Hajiya zainab ta dafa kafa d'arta tace "kada kidamu komai zai zama normal." Saratu tace "nagode ranki ya dad'e, nagode kwarai da gaske Ashe ban San kece mai tai makona ba........ Hajiya zainab ta katseta da "kada kidamu na fad'a maki mun zama d'aya." Saratu ta dawo sashinta tasa aka tafasa mata k'ullin maganin da hajiya zainab tabata, Haka ma tsimin gaba d'aya takafa kai ta shanye tayi wurgi da galan d'in tsakar d'aki, kuyangi suka d'auke suka fitar dashi waje." Aka kawo mata na k'ullin shima ta kafa kai ta shanye." Tashiga tunanin ita tasan akwai canji tsakanin ta da mijinta, da har murna yakeyi idan ya ganta, amma yanzun sai tayi tayi masa magana amma bai d'aga ido ya kalleta bare ya amsa mata." Ko d'an zaman da sukeyi a lambu yanzun ya daina gayyatar ta." Ita tarasa abunda ke damunsa kwana biyun nan ko son kallonta bayayi." Can taji ciyo ya tsikareta k'asan mararta, a kwance take ta mik'e zaune, jitayi marar ta tayi mata wani irin juyi na azaba sai da tasaki wata irin k'ara ta azaba." Kuyangu suka shigo Suna cewa " ranki ya dad'e lafiya?" Ganin ta sukayi tafad'i k'asa tana murk'usoso tana juyawa, itama kanta bata san tanayi ba, saboda azaba da take ji." Can sai wani kalar jini ya fara fita bak'ik'irin gudaje gudaje ga wasu irin Abu a ciki kamar dakakken nama haka." Jini sai zuba yakeyi kamar ruwa a famfo can kuma sai ya daina, jakadiya ta shigo tana kallon ikon Allah." "Bari ne ko?" Inji jadiya ta tambaya." "Allah sarki sannu." Saratu ta zaro ido tace "bari fa kika ce dama ina da ciki?" Jakadiya tace "to ya b'are ranki ya dad'e." Saratu ta fashe da kuka tace "yi shuru jakadiya ta aza hannu a kai tace "nashiga uku." Ba'a dad'e ba aka gyara ta tsab aka kwashe komai duk wani ciwo da takeji taji yatafi, sannan jinin da ke zuba ya tsaya tsaf ko d'igo babu." Wannan Abu da mamaki yake🤔 [3/5, 4:53 PM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *Kuyi hak'uri masoya Tambarin sarauta jiya kunji ni shuru gidan biki ta tafi shiyasa bansamu damar yi maku typing ba* *39* A Yanzun Bassam bashi da wurin da yake zama domin shan iska sai wurin kiyon dabbobi, inda yasan yana iya hango duk abunda Afnan takeyi." Yana murmushi wani abun kuma yasanya shi dariya, amma kuma baya barin ta ganshi saboda karta rainashi." Shi dai yasan yana zuwa ne domin yaga dabbobin sa saboda shi ma'a bucin son dabbane." Afnan kuma bata San yanayi ba domin ita har ga Allah har mantawa takeyi dashi a rayuwarta, Ita dai burin ta d'aya ne duk lokacin da tayi sallah take addu'ar Allah ya fitar da ita cikin wannan gidan ta koma gaban mahaifanta." Yau ma hakan taka sance Bassam yayi wanka yasanya wani kaftani mai dogon hannu yayi kyau matuk'a, ya fito yanufi inda yake zama domin nishad'in rayuwarsa." Tafiya yakeyi Audu na biye dashi yana zuba masa kirari." sai da suka zo inda yake zama, anyi masa shinfid'a ta alfarma, kai tsaye yaje ya zauna." Audu ya kalleshi yace "ranka ya dad'e ina da tambaya?" Bassam bai kalli Audu ba yace "ina saurarenka Audu yi tambayar ka." Audu yace "ranka ya dade lafiya kake kuwa a kwanankin nan?" naga tunda aka keb'e wurin kiyon dabbobi a cikin gidan nan baka tab'a zuwa ba." Nayi mamakin ganinka danake yi a nan a koda yaushe, Kuma ranka ya dad'e naga ka maida wajen wurin hutawarka sab'anin lambu da kake zama." Kuma ranka ya dad'e sai naga kamar kana tsurawa wuri d'aya ido kana kallo, kana murmushi a fuskarka." Basaam ya juyo ya kalli Audu Yace "yaushe ka fara sanya min ido a harakokina?" Audu yayi saurin kaiwa k'asa yace "ayi hak'uri ranka ya dad'e tuba nakeyi." Bassam yace "tashi katafi sai na nemeka." Audu ya mik'e yana fad'in "godiya nake ranka ya dad'e a gafar ceni." Bayan tafiyar Audu, Bassam yashiga tunanin maganar da Audu ya fad'a masa, tabbas gaskiya ya fad'a, shima yana mamakin zuwan da yake a nan." Idon safiya ta waye baya samun farin ciki, baya jinsa cikin nishad'i har sai yazo wurin nan yayi tozali da dabbobinsa da kuma mai kula dasu, to meyasa?" Yashiga tambayar kansa." Wata zuciyar tace masa "saboda mai kula dasu ta iya tafiyar da dabbobi yanda ya kamata." Wata zuciyar kuma tace " ba saboda dabbobi kake yazama wurin nan ba saboda kayi tozali da kyakkyawar mace wadda a yanzun da ita kake kwana da ita kake tashi a ranka." Da sauri ya kawar da wannan tunanin yana fad'in "k'arya ne babu wata mace da ta isa a duniya na tsaya b'ata lokaci na nayi tunanin ta , bare wancan abar mai kama da Aljanu." Allah yatsare yaja dogon tsaki." Ya shiga kallon wurin ko zai ganta, amma bai ganta ba, tunda ya zauna wurin yake zuba ido a inda yasan take zama amma bai gantaba." Sai tunanin sa ya canza yashiga tunanin" ko lafiya?" Mai yasa meta wanda har yanzun bata fito ba?" Mik'ewa tsaye yayi yanufi wurin dabbobin ko Allah zai Sa ya ganta, yaji dalilin da yasa bai ganta a dai dai wannan lokacin Dan tabawa dabbobin sa abinci da ruwa." Wurin yanufa bai ganta ba, waige waige yashiga yi, koda zai ganta amma bai gantaba." Lambu ya nufa da sake sake a ransa wanda bai masan yanayi ba, yana fad'in "Allah dai yasa lafiya take." Yayi saurin kauda wannan tunanin ya furta a fili, "wannan bai dameni kuma ba matsala ta bace, ko bata da lafiya sai ta fito ta aiwatar da aikin da ya zamar mata dole." Afnan na lambu taje tsinko mangwaro, tana hango Bassam ya nufo wurin da sauri tashige k'arkashin bayan wani icce ta b'oye." Tana kallonsa, yayi kyau, domin bata tab'a k'are masa kallo ba sai yanzun." Tace "kudibe sa kamar mutumin arziki, amma babu komai a tare dashi sai mugunta, da zalunci da kuma rashin tausayi." Lura tayi dashi sai waige waige yake alamar akwai abunda yake nema, taja dogon tsaki had'ida murgud'a bakin kamar yana ganinta tace "yanzun haka wannan mummunan matar tasa mai kama da agwa_gwa yake nema." Gani tayi ya tunkaro inda take taja jinin jikinta ta b'oye." sai da yazo dai dai inda take yayi tsaye, yaci gaba kallon ko ina yana waige." Kuyangi masu gadin wurin basu lura da shigowarsa ba, suna can zaune a gefe d'aya suna fira." d'aya daga cikinsu ya hango shi, ya nuna wa 'yan uwansa shi." Da gudu suka nufo wurinsa suka zube k'asa suna kwasar gaisuwa, suna fad'in ranka ya dad'e a ga farcemu ayi mana afuwa bamu San kazo ba, Ranka ya dad'e mekake nema?" Rasa amsar da zaibasu yayi, ya kallesu yace "ba komai kuyi tafiyar Ku." Da sauri suka mik'e suka nufi wurin aikin su." Ganin sun wuce, shima ya bar wurin, saboda karsu fahimci wani Abu a tare dashi tafiya yakeyi amma kalle kalle yakeyi koda Allah zaisa ya ganta." Bai ganta ba, yanufi wurin zaman sa yana sake sake a ransa." Afnan na ganin tafiyar sa, ta fito a guje, da mangwaro a hannuta, tanufi wurin dabbobinta ta rera wak'a har da 'yar rawarta." Sallamar da akayi masa ne, ita ce ta katse masa dogon tunanin da yakeyi." "Yasir?" Ya fad'a tare da mik'ewa tsaye." "Daga ina haka?" Ya mik'a masa hannu suka gaisa." Yasir d'an Anna ne ba'a k'asar nan yake da zama ba." suna matuk'ar shiri da Bassam sosai, suka samu wuri suka zauna." Yasir ya kalli Bassam yace "Yarima kenan kana hutawarka kaga yadda kazama kuwa?" Bassam da idonsa na wurin Afnan ko Allah zaisa ya ganta tafito." Bai kalli Yasir ba yace "haba dai ina wani can zawa a haka muna cikin Nigeria." Yasir yayi dariya yace " eh mana sai kace kalar halfcase kalar fatar ka." Bassam ya kauda maganar saboda bayason yawan surutu a wannan lokacin, yace "tun yaushe ka shigo garin?" Yasir yace "tun shekaran jiya." Bassam yace "OK ya iyalinka?" Yasir yace "suna nan lafiya k'alau yana ka iyalin?" Murmushi Bassam yayi ya fad'a a tak'aice yace "kowa lafiya k'alau." Adai dai lokacin da ya hango Afnan a guje tana wak'a tana karkad'a k'ugu tana kuma shan mangwaro, Wani sanyi yajiya a ransa tare da sauke ajiyar zuciya, yana murmushi wadda bai San yana yinsa ba, yana kallon wurin." Sadi d'an daudu Wanda a yanzun shike dafa masa abinci, Ya iso yana rangwad'a kamar wata mace, d'auke da tiren abinci zai kawowa Yasir." D'abi'oin da sadi yakeyi da maganar da yakeyi kamar mace shi yake bawa Yarima dariya, duk lokacin da yakawo masa abinci sai ya zaunar dashi a kusa gareshi yana tsokanar sa domin yayi dariya." Sadi na ajiye tiren abincin a gaban Bassam yace "ranka ya dad'e ga abincin." Bassam ko kallon Sadi baiyiba hankalinsa na wurin Afnan yace "Ajiye nan kayi tafiyarka." Sadi ya ajiye yayi tafiyar sa cike da mamaki yau Yarima ko kallon sa baiyi ba, bare ya tsokane shi." Yasir ya kalleshi yace "Yarima wani d'an daudu aka samu a gidan nan kuma?" Yarima bai kalle shi ba saima murmushi da yaga yanayi a fuskarsa har da 'yar dariyarsa." Yasir yakai idonsa a inda yaga Yarima na kallo yana murmushi." Afnan ce ya hango tana yiwa doki wanka, sauran kuma dabbobi duk sun zagayeta, tana masu wak'a tana 'yar rawar ta mai d'aukar hankali." Yasir ya k'ura mata ido yana kallonta , kyawon ta da yanayin ta ya matuk'ar burgeshi bai San lokacin da yace "wow beautifull girl." Yarima yarinyar can ta matuk'ar murgeni, naji inasonta a shirye nake zan aureta, banda mu da kasan cewarta a matsayin baiwa ba." Wani razanen nen kallo Bassam ya wurga wa Yasir had'ida wata kalar harara,🙄 baiyi masa magana ba, shi kuma yasir bai San yanayiba, gaba d'aya hankalishi ya tafi wurin kallon Afnan." A dai dai lokacin da tayi wani irin juyi tana rawa, d'an kwalin kwanta yacire gashin kanta yazubo har gadon bayanta wani kuma ya rufe mata fuska." Da sauri Yasir ya mik'e tsaye, baiko kalli Yarima ba, yace "Yarima bari natafi tun yanzun na gabatar da kai na tunkafin lokaci ya k'ore." Yana k'ok'arin tafiya Yarima ya rik'o rigarshi ta baya, idon shi ya rik'id'e zuwa launin ja, cike da b'acin rai yace "karka kuskura kaje wlh mudun kayi kuskuren zuwa wurinta saina sanya fadawa sunyi maka bulala dubu." Sannan ya saki rigarsa." Yasir ya kalleshi ido cikin ido yace "a kan me?" Dawani dalili zaka hanani zuwa wurinta bayan baiwa ce, kuma na ganta naji ina sonta, kuma aurenta zanyi, to ko kashe ni zakayi sai na isar da soyayya gare ta." Ya rab'a Yarima ya wuce zai nufi wurin Afnan, Saiji yayi Bassam na kiran "Sarkin hukunci, Sarkin gishiri, sarkin kisa." Da gudu suka zo suka durkusa gaban Bassam kowane sai zarar ido yakeyi fuskarsa babu imani." Bassam ya kallesu cikin *K'unar Zuci* yanuna masu Yasir da yaja yayi tsaye wuri guda yakasa tafiya, Yace mudun wancan ya kuma taka sahu biyu da sunan tafiya ni ninace Ku kamashi Ku kaishi gidan hukunci kuyi masa horo horo mai tsanani." Yasir ya dawo baya yafasa tafiyar yana kallon yarima da yaga nan take ya canza kama kamar wani zaki, yasan halin Bassam sarai komai yana iya sanyawa ayi maka kuma babu Wanda ya isa ya rama ma." Yasir ya rab'a Yarima yafita yayi hanyar waje." Yarima yayi wa fadawa nuni da hannu a kan suyi tafiyarsu, sannan shima yanufi hanyar sashinsa da sak'esak'e a ransa." [3/5, 4:54 PM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *40* *Saratu* ta rasa gane kan mijinta kwata kwata ya juya mata baya." Baya son kusantarta, yanzun gata kuma mai yawan buk'ata." Har gara da yana zuwa ya d'an kwada kusantarta, yanzun kam abun ya lalace ko k'eyarshi bata gani, kuma ya hanata zuwa sashen sa, yace ta d'an dakata da zuwa turaka zai nemeta." Shima Bassam ya rasa dalilin da yasa idan yana tare da Saratu baya jin gamsuwa da ita a ayanzun kuma bayajin dad'in ta kwata kwata sai yaji kamar ya shiga ruwa, Sam baya gamsuwa a kwanciyarsu shima mamaki yakeyi yaushe ta zama haka bai sani ba?" Tunanin yanda zai fara gaya mata halin da take ciki yakeyi Mmki ykeyi ssai, koma abun daga gareshi ne shi baisani ba." A Yau kam ya shirya yana buk'atar matar shi, domin a tunanin sa shi ke da matsalar ba saratu ba, tunda ai ba hakan yasame taba tun farko, Shi dai yasani yana gamsuwa da ita, yanzun ne dai yafara jinta kamar ba komai ya shiga ba , tamkar ya fad'a kwata ga wani irin wari dake fita a tsaka ninsu." Bai San ta inda zai fara gaya mataba, bayason ta gano yana cikin wani haline game da kwanciyarsu." A yau kam ta b'aci yana kanta ya dawo gefe d'aya ya kwanta, yashiga tunanin mai yasa yakejin hakan ne?" Shi dai yasan lafiya k'alau yake, ko dai ita ce bata da lafiya ne?" Ya juya ya kalleta kuka takeyi, ya rik'o hannunta suka zauna suna fuskantar junansu, yashiga lallashinta, Yace "ki daina kuka Saratu abunda ya shafeki nima ya shafeni." Ta kuma fashewa da kuka tace " Rabuwa zakayi dani ranka ya dad'e? Bana son rabuwa da kai." Yarima yace "ki yi shuru bazan rabu da keba, zamu nemi maganani tare domin muyi maganin matsalar." Kintabbata baki sha magani da zai ja maki wannan matsalar ba?" Kinsan fa Ku mata kuna shaye shaye magunguna Dan Ku samu ni'imar da zata gamsar da mazajenku." Da sauri ta d'aga kai tace "eh munayi Allah munayi." Murmushi yayi yace "kada kisha abunda zai b'ataki Dan yanzun kin samu matsala mai makon in gamsu dake sai dai injiki salaf." Ta matso ta rungume shi, warin dake fita a jikinta ya daki hancinsa, yayi saurin m'ik'ewa tsaye yana cewa "bari muyi wanka sai muyi maganar Saratu bazan rabu dakeba." A ransa kuwa, ransa a b'ace yake yana cewa a zuciyarsa waya gaya maki ina iya hak'iri da macce a wannan lokacin dana kejin k'arfi kamar doki, ga kuma maganin tsari da lafiya da nake sha, yanzun ma nake cikin ganiyar sha'awar macce." Ya fad'a toilet Wanka yayi ya fito ya tarar da ita a zaune sai kuka takeyi saboda matsananciyar sha'awa dake damunta, Yarima ya fara lasa mata zuma a baki kuma ya kyaleta." Lallashinta ya shiga yi yana kwantar mata da hankali shiyasa tamu damar da barci ya d'auketa." Ya tsura mata ido yana kallon fuskarta, yace "kai gaskiya Saratu a kwai muni na bak'in kare." Shi dai yasan yana zaune da itane, saboda yasan bazata tab'a zama mai bak'in haliba irin na kyakyawan mata ba, Yana ganin muninta zai hanata mugunta da jin kai, domin ya lura masu kyau akwaisu da jin kai." Me suke tak'ama dashi kyansu?" Shi dai kyan 'ya mace a wurinshi shine k'irjinta da d'uwawu sai kuma tsawo, Tsawon ma d'in ba dole bane, ko guntuwa CE yana sonta in dai a kwai wannan qualities d'in." Sannan kuma yana son mace mai laushin fata, mai laushin jiki, Saratu kan jikinta k'irk'ir kamar na maza, Sannan kuma hannuta nada girma, k'afafunta ma haka sunada girma sai kace nasa. Yana ganin ma tafishi girman k'afa, gasu sambal kamar guduma." Komai girman k'afar da hannun macce kada ta wuce ta namijin da zata aura." Kuma tasamu man hulba ta rik'a shafawa yana maganin fata, idan tana sha a cikin jikinta zata kuma samun lafiya." Dogon tsaki yaja ya kawar da kansa domin shima yashiga cikin yanayin buk'atar mace." Afnan ta had'o masa a rai a yanda ya ganta d'azun tana juya k'ugunta tana rawa." Kai yarinyar ta kai yarinya halitta kamar ita ta halicci kanta, k'irjinta a cike yake fam, Sannan ga diri irin wanda kowane namiji yana iya wasoso a kanta." Tuna wa yayi da yanda yaga Yasir na kallonta, yaji anan take ransa ya b'aci, ya fad'i a fili yace "dole ne nasanya ayi mashi katanga da shigowa gidan nan." Mirginawa yayi daga kwanciyar da yake, domin jinsa yake baya iya barci saboda a buk'ace yake, Wata zuciyar tace kaje kanemi yariyar can mana ai matar kace." "Ina "ina ai saita rainani, kuma saita gane kurenta." A haka dai har barci b'arawo yayi awon gaba dashi." Ko da saratu ta farka daga barci taga babu Yarima babu alamarshi." Hankalinta yayi matuk'ar tashi ta kasa hak'uri tanufi sashin hajiya zainab, Ta shiga fad'a mata abunda ke faruwa." Dariya hajiya zainab tayi irin wannan tasa mun nasara, tace "ai Yarima sai ya gane kurensa bai San ni bace." Sannan ta d'auko wani k'ullin magani ta mik'awa saratu, tana gaya mata yadda zatayi amfani dashi, sai nanata mata takeyi." Tana ce mata "kikula da kanki da kyau Dan yarina akwai shi akwai son mata." Saratu tace "haba?" Hajiya zainab tace "kwarai kuwa aishi yasa nakeson ki mallake shi, tashi kije kisha kamin yashigo gurinki." Saratu tafita tana godiya, hajiya zainab ta ci gaba da dariyarta da tafara yi d'azun, tace "sakarya mahaifarki ta lalace babuke babu yin ciki a gidan nan." _____________________________ Afnan yau ta ari rediyon sadi d'an daudu, da yake suna shiri sosai ahaka zasu zauna suyita hira sai kace k'awaye, Sadi yasha gaya mata tana da kyau." Har shi yake koya mata wasu aikin girki a kicin d'in, sai kuma abinci mai kyau da take samu tana ci daga wurinshi." Yawanci duk abunda Yarima keci shi itama take ci, shiyasa take k'ara yin kyau." Doki take yiwa wanka ta kunna rediyo, tasanya wak'ar Umar m Sharif, sai ta b'uge da yin rawa." A hankali take yin rawar, dai dai da kid'an, Yarima na gefe yana kallonta rawar yau tafi ta kullum burgeshi jiyayi kamar yaje ya rungumeta ya stotse d'an k'aramin bakinsa yakeji." "Sai cewa yakeyi kai wannan yarinyar ta iya komai na rud'a namiji, shi kanshi ya yaba da rawar yau, tun yana kauda ido har yakai yakasa zama ya jingina da bangon dake gurin, yaci gaba da kallonta." Can sai yaga sadi shima yashiga ya jera da ita, yana rankwad'a kamar macce shima yana rawa, suna dariya suna rausayawa a tare." Haushi ya kamashi ta yanda sadi yake jerawa da ita yana rawa, itama ko a jikinta rawarsu sukeyi suna dariya." Tunawa yayi da malam Nura a yanda yake ganin su a tare a koda yaushe sun jera suna tafiya suna firar masoya." Wani Abu yaji yana taso masa Wanda baisan ko meyeba, yashiga fad'i a zuciyar shi, "dama tasaba yawo da maza, tasaba ma'amalarta da maza tun a gidansu, yaja wani dogon tsaki cike da jin haushi ya bar wurin." Kai tsaye fada ya nufa wurin maimartaba, Suka fara fira Bassam yace "ranka ya dad'e "inaso ka gaya min likita macce Wanda ka yarda da ita." Maimartaba yace "matarka nada ciki ne? Bassam yace "bansaniba ranka ya dad"e." Sarki yace "kana nufin har yanzun bata da ciki, to mekake jira?" [3/5, 4:54 PM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *41* Bassam ya sunkuyar da kansa k'asa yace "shi nakeso a duba mata ranka ya dade." Sarki yace "OK ba damuwa akwai likita macce Dana sani ta iya aikinta sosai zan turo maka ita gobe da safe sai ta dubata." Da safe likita tashigo ta shiga duba saratu, Dr tace lafiya lau take babu abunda ke damunta, yarima yashiga mamaki sosai." A daren yace bari ya gwada ya gani ko tamu lafiya, amma sai a hankali Dan abun yafi lalace wa, warin ya k'aru har yafi nada, Sauka yayi a kanta ya shiga tunanin ko an samata hannu ne a gidan nan?" Ya juyo ya kalleta yace "kin tabbata babu Wanda yatab'a wani Abu kikaci ko kika sha?" Ta girgiza kai tace "A'a babu." Bassam yace "ikon Allah kina cikin babban lalura Saratu sai antashi tsaye an nema maki magani." Ya tashi tsam yafita ya barta a nan kwance tana kuka." _____________________________ Afnan ce d'auke da tray na kayan abinci, Wanda Sadi ya kwaso wurin Yarima, hakan Sadi yake mata duk abincin da Yarima yaci ya rage, da zarar ya kwaso kayan to ita yake kawomawa, wani lokacin kuma tun kafin ya kai masa yake d'ebo mata, dan haka kullum sai k'ara cika takeyi tana kuma yin kyau." tafiya takeyi zata nufi wurin abokanenta dabbobi, sam bata san Bassam yazo wurin ba, Karo sukayi gaba d'aya Abincin ya zube masa a jikinsa." Zaro ido yayi yana kallonta, cike da tashin hankali,da takaici duk ya rufeshi, ga shi fararen kaya ne ya saka, duk sunyi manja." Kallonta yayi cikin masifa yace "KE!! ina wasa dake?" Tsaye tayi ta sunkuyar da kanta k'asa cike da tashin hankali, taka sa furta kalma d'aya, jiran hukunci kawai takeyi." Saratu ta iso wurin tana fad'in "Ashe kana nan ranka ya dad'e?" Naje sashinka aka cemin kana nan wurin doki." Bai kalli Saratu ba, Afnan yake kallo data sunkuyar da kanta k'asa, sai zazzaga masifa yakeyi." Tunawa yayi da yanda yake ganinta da Sadi, suna ma'amala kamar macce 'yar uwanta, Da kuma yanda yake ganinta da malam Nura sunjera suna tafiya suna fira, Wani Abu yaji ya taso masa A cikin zuciyarsa , bai san lokacin da yanuna ta da d'an yatsa yace " 👉🏻 ke karuwa kishiga hankalinki bazan d'auki iskanci daga garekiba, dibi yanda kika b'ata min jiki da Abinci, ko kin d'auka nima ina d'aya daga cikin 'yan iskan samarinki?" Afnan ta waro idanunta cike da hawaye ta kalleshi ido cikin ido tace " *NI BA KARUWA BACE*!! kuma duk Wanda ya kuma kirana da karuwa bazan tab'a yafe masa ba, sai Allah yayi mana hisabi a ranar gobe k'iyama." Ya saki dariyar jin haushin kalamanta a gaban fadawansa, yace "ke karuwa ce." Saratu tace eh ke karuwa ce, had'ida galla mata harara." Saratu bata rufe bakinta ba, Afnan ta d'aga hannu ta kwad'a mata lafiyayyen marinta har biyu, a kuncinta." Idanunta yana zubar da hawaye, tace "idan ina magana da shugabanki Wanda ya ajiyeki, kidaina sanya min k'aton bakinki, Sannan ni ba karuwa bace sai dai inkece karuwa." Saratu ta kalleta cike da mamaki da kuma tashin hankali. Tayi kukan kura zatayi cikinta ta doketa." , Bassam ya doka mata tsawa da k'arfi Wanda bata San yana da wannan muryarba yace "karki kuskura ki daketa." Ta zaro ido waje cike da mamaki, batayi magana ba." Bassam yace "ina ruwanki da ita?" Me yasanya bakinki a ciki?" Wato ina magana kinayi?" Ina zartar da hukunci ga bayina kina sanya Baki?" Meya kawoki nan?" Waye ya fad'a maki nazo nan?" Da sauri ta zube k'asa tana bashi hak'uri, Kuyangu sukayi tsaitsaye suna kallo." Ganin haka bai kuma yin magana ba, yajuya yayi tafiyarsa." Sashinsa yanufa Saratu na biye dashi, yana juyo Wa, sukayi ido biyu dashi, ya tsaida ta, yace "koma sashinki ina buk'atar inzama ni kad'ai." A san yaye ta juya ta tafi, tasan hakan sai ya faru." Wai mai yake shirin faruwa da ita ne?" Meke shirin samunta, da har Yarima ya fara fifita baiwa a kanta?" Ya dace taje taga Anna ko ba komai gari d'aya suka fito, kwad'ayine yasa ta sai da kanta gidan sarki" Da jummai kakarta ta rasu, ita da kanta tazo tace tanason tayi aiki a gidan." Hajiya zainab na ganinta tagane ita jinin jummai ce, Da jummai da Anna sune suka rik'e Bassam saboda Allah, suka shiga k'ok'arin tsiratar dashi daga shairin hajiya zainab." Tun daga lokaci Hajiya zainab ta mayar da Saratu mai wanke mata k'afa da gyara mata farce, sai gashi ta zama matar Yarima abunda bata zataba." Bassam sai safa da marwa yakeyi, shi kad'ai a d'aki, Domin bai tab'a jin tausayin Afnan ba sai a yau, Hawaye ya gani kwance a fuskarta, ji yayi kamar yaje ya rungumeta ya lashe mata su." Shima yasan kalmar da ya furta mata ta karuwa, tayi mata nauyi a kai, to amma shi bai san lokacin da ya furta kalmar ba, baisan lokacin da Kalmar ta fito a bakinsa ba." Yashiga tunanin yanzun ko a wani hali take?" Wata zuciyar tace "ai kaima tayi maka rashin kunya a gaban kuyanginka, har da Allah ya isa tayi maka." Kuma ta k'arya taka a gaban kuyangunka." *************************⬇********************** ************* Ai Hausa Novels **************** *************************⬆ ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ⬇ ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ⬆ ************************** Wani zafi yaji yaji a k'irjinsa, yana fad'i a fili, wato ni zata karyata a gaban mutane, Lallai yarinyar can ta d'auko ruwan Dafa kanta zai nuna mata shiba mak'aryaci bane, ita har ta isa yayi mata k'arya akan menene?" Ita wacece ma da za'ayi mata k'arya." Daren ranar har fita yakasa yi, saboda a ganinshi kowa zai kalleshi a matsayin mak'aryaci." Can cikin dare yakasa barci duk abunda ya faru dawo masa yakeyi, ya mik'e tsaye ya d'auko jallabiya ya sanya, had'ida sanya silifas, yafito yanufi inda Sadi yake kwana." Kwankwasa hankali yashiga tashin Sadi, Sadi ya bud'e idonsa ganin Yarima yayi saurin wartsakewa." Yajashi suka fita waje a hankali, Yarima yace kaje Kane momin Yarinyar nan ka kawo min ita sashina yanzun nan." Sadi ya zaro ido ya kalli matattacen agogon dake d'aure a tsintsiyar hannunshi yaga 2:30am yace ranka ya dade wace Yarinya?" Yarima ya kuma had'e fuska yace wannan yarinyar mai son rawa." Sadi yace "Oh Afnan?" Yarima ya mere baki ☹yace " _whatever_ kada kabari kowa ya ganku. Daga nan ka kawo min ita sashena." Sadi yace to angama ranka ya dad'e." Yarima ya juya ya koma, Sadi ya tab'e baki yace "kai Yarima akwai zuciyar banza yarinyar nan tunda yace mata ita karuwa ce, Bai tab'a ganin ta cikin b'acin raiba irin na yau, wuni tayi tana kuka har sai da tabashi tausayi." Store ya isa yana kiranta, wuta ya kunna haske ya gauraye d'akin ya ganta zaune saman buhu tana aikin kuka." Yazo ya zauna gefenta ya shima ya b'ata fuska, yace haba Afnan kidaina kukan mana kanki zaiyi ciyo." Cikin kuka tace "karuwa fa yakira da ita, wallahi tallahi ni ba karuwa bace." Sadi ya b'ata fuska yace "kiyi shuru nima kaina nasan ke bakaruwa bace." Duk kuyangun dake wurin nan suna kasan cewa tare da barori, amma kekika gudu nan, anan kike kwana." Duk inda za'aje Afnan ina shaidarki ke ba karuwa bace." Ta d'an rage kukanta tana kallon fuskar Sadi." Yace " ki yarda dani, ni masoyinki ne, na d'aukeki aminiyata." Afnan tasaki murmushi dole saboda Sadi yana sanyata dariya." Yace "yanzun kizo muje Yarima na kiranki." Ta zaro ido tace "NI?" yace "Eh! Shi yace inzo in kiraki shine Nazo nasameki kina kuka, Tashi muje kinsan Yarima baya da Matsala nasan hak'uri zai baki, yasan bai yi dai dai ba." Allah ko? Ta tambaya." Yace "eh mana taso muje hak'uri zaibaki yana da saukin kai." Tace A"a bazani ba yanada zafi gareni, ban San dalilinsa na tsana taba." Sadi yace "kiyi hak'uri kada ki tsaneshi." Tace "aini na daina tsanarsa yanzun, haushin sa kawai nakeji." "To tashi muje yana jiranmu." Suka mik'e suka nufi sashin Yarima." Suna tafe suna hira Afnan tasaki ranta sai dariya Sadi ke sanyata." Dogarai suka taresu daga bayansu sukaji murya Yarima na fad'in barsu su shigo." Afnan ta fara shiga falon kafin, Sadi har zai shige Bassam ya tareshi da hannu yace koma ka bud'e wayarka zan nemeka." Sadi ya zaro ido zaiyi magana, Bassam ya rufe masa baki da tafin hannunshi tare da turashi waje ya kulle k'ofarsa har da sakata da makulli ya cire makullin ya d'ora a kan tebur." Ya juya yana kallonta ido cikin ido." Ya koma yana kuma kallonta daga sama har k'asa, dirinta abun kallo ne, ya lashe baki😋 kamar maye." Yaje ya zauna yace ki zauna mana." Tayi banza dashi." Ya kuma cewa "kizo ki zauna magana zamuyi nace." Ta durk'ushe nan inda take tsaye tana harararsa." Hararar kyawo yaga ta kuma k'ara mata, yafad'a zuciyarsa "fuskarta mai kyau, gata kuma 'yar k'arama." Murmushi yayi, yace "kince ke ba karuwa bace?" Tace "Eh had'ida murgud'a baki." Yace "to kibani kanki in tabbatar da haka." Tasaki ido da Baki, cikin tsoro, tana mashi d'an kallon nan nata na shagwab'a, Shi kuma sai kallonta yakeyi yanajin tsikar jinsa natashi, domin gaba d'aya ta tafi da imaninsa." [3/5, 4:55 PM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *WELCOME TO THE WORLD OF ISLAM MY LOVELY SON, UBANGIJI ALLAH YA RAYAKA YA KUMA ALBARKACI RAYUWARKA, AKAN TA FARKI NA ADDININ MUSLUNCI* *42* Kallonta yaci gaba dayi, yayi murmushi yace "ya akayi?" Baki iyawa ne?" K'asa tayi da idonta ta marairaice fuska cikin shagwab'a, Tasan abunda yake nufi, ayanzun shekarunta sha tara, a islamiyarsu sunyi karatun saduwa da miji." Ta San hak'in miji a kan matarshi, kuma tasan azabobin da Allah ya tana darwa macce Wanda ke k'aura cewa shinfid'ar mijinta idan ya nemeta." Tasan Bassam mijinta ne, kuma a yanzun batajin k'iyanyarsa ko kad'an a ranta, sai dai ma tadinga jin wani abu game dashi Wanda take gasgatawa kanta." Batayi auni ba ta ganshi durk'ushe a gabanta, ya sanya hannayensa biyu ya tallabo fuskarta ya tsura mata ido kamar yana karantan wani abun a tare da ita." Numfashinsu gaba d'aya yana bugun na junansu. Wani shauk'in son yakeji yana shigarsa dangane da ita, shi kanshi yasan ya dad'e da kamuwa da matsanencin sonta amma yana gasgata hakan. Sai yanzun da dake a gabansa jinsa yakeyi yana iya aikata komai a kan Afnan." Runtse idonta tayi hawaye suka shiga zubowa a idonta, Tana fad'in Dan Allah karka cutar dani, Cikin maganar ta mai cike da shagwab'a da wauta." Hawayen dake zuba a idonta, jinsu yakeyi kamar ana watsa mashi garwashi a jikinshi." Tallabarta yayi ya nufi bedroom da ita, Kan gado ya d'orata tare da cire mata hijabi dake sanye a jikinta, gaba d'aya gashin kanta ya zubo ya rufe mata fuska, baisan lokacin da ya furta a filiba yace. "WOW." Kuma runtse idonta tayi, hawaye suka shiga zubowa. Yasanya hannu ya gyara mata gashin da yarufe mata fuska, Fuskarta ta bayyana tare da d'an k'aramin bakinta, sai motsi yakeyi alamar zatayi magana amma kuma ta kasa." Baisan lokacin da ya kai bakinshi ciki bakin taba yashiga tsotsa, Matse bakinta tayi, tak'i saki." Sai hawaye kawai ke aikin zuba a idonta." Harshinsa yasanya shiga lashe mata hawayen,dake zubowa Yana fad'in pls Afnan don Allah ki daina kukan nan, bana son ganin zubar hawayenki." A shirye nake ki d'auki ko wanne irin hukunci a kaina." Indai hakan zai sanya farin ciki a rayuwarki, Afnan nasan...... *wash hannuna na gaji*😜 *nasan yau sai anyi min zanga zanga* *saboda Anzo wurin* *kuma*...............😜😜😜😜😜😜😜😜😜😜😜 [3/5, 4:55 PM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *WANNAN PAGE D'IN NAKUNE* *UMMU SAFWAN HAUSA NOVEL'S* *AND* *TAMBARIN SARAUTA FRIEND'S* *INAJIN DAD'IN COMMENT D'INKU ALLAH YA BAR K'AUNA INAYINKU IRIN SOSAI D'IN NAN*💋💋 *43* Nasan na horaki ta fanni iri iri, wadda a yanzun kike d'auka ta a matsayin Azzalumi macuci Wanda baidamu da rayuwarki ba." Ya kai durk'ushe a gabanta, Tare da sunkuyar da kanshi k'asa yace "ki yafemun Afnan ki gafarceni ki d'auki ko wanne irin mataki a kaina, in dai hakan zai sanyaki farin ciki a rayuwarki." Afnan a yanzun na kamu da matsanan cin sonki, wadda, idan har na rasaki tamkar na rasa rayuwata ne, basan yanda rayuwata zata kasan ceba." Natuba Afnan Natuba, ki yafemin nasan na kuntatawa rayuwarki." sai hawaye tagani yana zuba akan idanun Yarima." Ido ta kureshi dashi batayi masa magana ba." Shima ita yake kallo, yana jiran tabud'e baki tayi masa magana, Kai ko zaginsa zatayi a wannan lokacin zaiji dad'i a ransa." Tashi yayi ya hau kan gadon, ya jawota a jikinshi ya rungumeta yasaki wata irin ajiyar zuciya." Hannunta biyu ta sanya ta tureshi, daga jikinta, Ta sauka daga kan gadon gaba d'aya." Tsaye tayi tana kallonshi, amma zuciyarta kwata kwata bata yarda da kalaman Shiba, Bata yarda da abunda yake fitowa daga bakinshi ba, yana fad'ane kawai domin ya samu galaba a kanta domin ya cimma wani buri nashi da yake nema a wurinta." Idonta ya cika da waye, bakinta yashiga rawa, Tace "tayaya zaka soni Yarima?" Bayan kasan ni ba kowa bace ba kuma komai bace face marainiya, marar gata 'yar gidan kaka tsuhuwa?" Ko a mafarki ban tab'a tunani zaka soni ba saboda ni ba kowa bace ba kuma komai bace, face baiwarka mai bauta a gareka." Ta fashe da kuka mai sauti, ta matso wurinsa ta durk'ushe k'asa wurin k'afafunshi, tace "nasan kai d'an sarki ne, d'an sarkin ma wadda sarki yafi ji dashi a rayuwarshi kana iya taka duk Wanda kake so ka kuma juya Wanda kake so, tun daga bayi zuwa kuyangu, meyasa ina matsayin Baiwarka zaka biyo min ta sigar soyayya domin ka kuma yiwa rayuwata illah." don Allah Yarima kabarni haka nan kabarni naci gaba da yimaka bauta har zuwa ranar da Allah zai karb'i rayuwata, Ka janye maganar soyayyarka gareni domin nasan bazaka tab'a sona ba, saboda ni ba kowa bace." Runtse idonsa yayi cike da *kunar zuci* yana tunanin ta wace hanya zaibi ya fahimtar da ita, yanda yake jinta a rayuwar shi a yanzu?" Ya kuma tabbatar mata da ya kamu da matsanciyar soyayyar ta wadda babu algunsu ko yaudara a cikinta." Tashi yayi daga kan gadon ya mik'e tsaye yanufeta, sai da ya Dan ganeta a bango sannan yaja ajiyar zuciya wadda yasanya ta tayi saurin rufe idonta." Bakinshi yasanya a cikin kunnenta ya hura mata iska, wadda ya sanya tayi saurin bud'e idonta, saka makon wani abun da taji ya ziyarci tun daga saman kanta har k'afafunta." aka salance ta d'ago idanunta ta kafe shi da su tana kallon shi." Yakira sunan ta cikin wata murya mai taushi, wadda ta kuma sanya ta natsuwa, yace "Afnan ki kalli cikin idona, ki kalli kwayar idona, za kiga tsantsar sonki da k'aunarki a cikin su." Afnan ki yarda dani ki kuma Amince dani,a yanzun nanuna maki irin soyayyar danake maki." Lura yayi da gaba d'aya jikinta ya mutu, ya kai bakinshi cikin bakinta, yashiga tsotsa, sai da suka d'auki minti biyar a hakan, gaba d'aya k'afafunsu suka kasa d'aukarsu, sannan tayi saurin janye bakinta daga bakinsa." Ya kalle ta a lumshe da ido domin ya kai mak'ura, sosai, So yake kawai yajishi a ......kan ta... Domin a buk'ace yake, jiyake mararshi ta fara yimashi ciyo." Yace Afnan kin Amince dani a daren yau na Nuna maki soyayyarki a gareni wadda ba k'arya ba kuma Alkussu a cikinta?" Ya kafeta ta idanunshi." Gaba d'aya kala manshi sun kashe mata jiki, Tasan Bassam mijinta ne, wanda a yanzun idan tace bata sonshi to tayiwa kanta k'arya." Turo baki tayi alamar shagwab'a ta harareshi, tace " ina iya baka kaina tunda kai mijina ne." Murmushi yayi a zuciyarshi yace "Afnan akwai sangarta sainayi fama kenan." Tallabarta yayi yace mutafi nayi maki wanka saboda kinyi datti da yawa, Wutsilniya tashigayi da k'afafunta, tana fad'in "ni bana so da kaina zanyi Har cikin toilet d'in ya kaita ya had'a mata ruwan wanka da turarunkan masu dad'in k'amshi, Ya kai mata kiss a goshi yace, " ina jiranki kiyi sauri ki fito, yaja mata k'ofa ya rufe." Kusan awa d'aya ta d'auka tana wanka, taji dad'in ruwan sosai tashiga tunanin inama ta kasance cikin ruwan nan a koda yaushe." Tunani tashiga yi, tana tambayar kanta "ko tafara son Bassam ne?" A can k'asan zuciyar ta kuma tana fad'in Ko kodai burgeta yakeyi." Kwankwasar k'ofar da taji ne, yasa tayi saurin fitowa daga k'ototon bahon wankan, ta dubi madubi, Taga wankan da tayi ya ishita ba sai tayi kwalliya ba saboda tana da _natural_ _beauty_ a tare da ita." Ta shiga goge gashin kanta da ta wanke, Kayan ta masu datti ta wanke su ta shanya a nan cikin toilet d'in." Ajiyar zuciya tayi sannan ta bud'e toilet d'in ta fito, d'aure da towel Kallo yabita dashi cike da sha'awa da kuma so da k'auna, "beauty kin shanya Yarimanki yana ta jiranki." Sunkuyar da kai tayi cike da kunya, Ganin hakan yace "kinyi Arwala?" Tace "A'a." Yace kije kiyi Alwala, ina jiranki." Bayan tayi Arwala ta fito, ya mik'a mata jallabiyarsa fara sol, Yace tasaka tare da hijabin Saratu da ta ajiye tana sallah da shi." Bayan ta sanya, suka gabatar da sallar da Annabi Muhammad (SAW) ya umurci mu damuyi." Ya juya ya dubeta fuskarta cike take da tsoro, Ya share, ya d'ora hannu akanta yashiga jero addu'o'i " Tunawa tayi da an karantar dasu a islamiya daren farkon mata da miji yana da kyau a yi hakan saboda neman Albarkar Aure da 'ya'ya masu Albarka." Mik'ewa yayi tsaye ya cire rigarshi ya jifar da ita gefe d'aya, Afnan na ganin hakan gabanta yashiga fad'uwa." Ya matso kusa da ita yashiga cire mata hijabin jikinta, ya rage daga ita sai jallabiya." Ya duk'a ya sungumeta sai kan gado, Jikinta yashiga rawa, cikin muryar shi mai taushi yace Afnan ki kwantar da hankalinki ba zan cutar dake ba." Tayi shuru had'ida runtse idonta, yashiga cire mata jallabiyar jikinta, ya barta daga ita sai towel d'aure a k'irjinta." Yashiga k'ok'arin kwance towel d'in ta rik'e." Kallo yabita dashi yace "beauty kiyi hak'uri ki barni na nuna maki zallar soyayyarki a gareni." Ya kai hannunshi ya shiga shafar fatar jikinta, A nan take hankalinshi baki d'aya ya tashi, saboda taushin fatarta da laushinta sai kace auduga, _Ba_ _irin_ _ta_ _saratu_ ba😜 Shafar ta yakeyi ta ko ina tun daga samanta har k'asanta." Jitayi tashiga wata sabuwar duniya, mai cike da abubuwa jin dad'i iri iri, Bata san lokacin da ya cire towel d'in gaba d'aya a jikinta." Dukiyar fulaninta ta bayyana, gata ta cika a tsaitsaye basu langwabeba, hankalinshi ya kai k'ololuwar tashi, bai San lokacin da ya kai bakinshi yashiga tsotsa kamar yaron goye." Gaba d'aya da burcewa yayi saboda gard'i da zak'i na brest d'inta, Sai wasa yake yi dasu yana murza su, idan yasha wannan yasaki yasha wannan, d'aya hannunshi kuma yana wasa d'ayan brest d'in har zuwa k'asanta." Sai da Bassam ya lashe Afnan tun daga samanta har k'asanta, adaren ranar ya koyar da ita wani sabon karatu, ya nuna mata tsantsar soyayyar da baitab'a yiwa ko wacce mace irinta ba." Sannan ya karato addu'ar kwanciya da iya, ya shiga Afnan." Wata razanan niyar k'ara tasaki, saka makon wani azababben zafi da ya ziyar ceta, had'ida k'okarin tureshi a kanta, amma ina Bassam yashiga duniyar da bai tab'a shiga irin taba, baima san tanayi ba." duk da yawace yawacen da yakeyi duniya kala kala, wannan duniyar da yake cikinta a yanzun ta ban banta da kowa ce." Kuka yakeyi Wanda baisan yana yinsa, wani nishi yake fitarwa wanda baisan ta inda yake fitowa ba, sai Albarka yake sanya Afnan had'ida wasu maganganu wad'anda ni kaina *UMMU SAFWAN* bansan abunda yake cewa ba." illah najawo masu k'ofa nafito nabasu wurin." *TO BASSAM ASHA DADI LAFIYA*😋😋 [3/5, 4:57 PM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *44* Afnan tasha wuya sosai, Har ya kai bata iya motsi." Babu abunda Bassam yakeyi sai Abu guda, gaba d'aya ya zauce ya gid'eme, hawaye kawai ke fitarwa a idonshi, sai sambatun jin dad'i yakeyi." bai san halin da Afnan take ciki ba, Sai da yaji bata motsi sannan ya sauka a kanta." Girgizata yashigayi yana kiran sunanta, Amma ina Afnan bata motsi ta suma." cikin tashin hankali ya tallabeta yanufi toilet da ita." Cikin bahon wanka ya sanyata had'ida sakar mata ruwan zafi." Ajiyar zuciya ta sauke, had'ida bud'e idanuwanta a hankali, sakamakon ruwan zafin da taji suna shigarta kota ina tana jin dad'insu." Ido biyu sukayi da Bassam tayi saurin mai da idonta ta rufe, domin a yanzun bata son ganinshi, bata son had'a ido dashi, tasan mugune, baya tausayinta, dama tasan ba sonta yakeyi ba, a koda yaushe burinshi a rayuwa shi ne yayi mata mugunta." Shi kuma Sai sannu yake jera mata, domin yanzun jinta yake kamar k'urjin tsakar kai, Tausayinta yakeji, Baya son ganin zubar hawayenta. Sai sannu yake jera mata amma bata kulashi ba." K'okarin yi mata wanka yakeyi tayi saurin rik'e masa hannu tace "ni zanyi da kaina." Tausayinta ya kuma kama shi, had'ida sonta da k'aunarta dasuketa fisgarshi, yace "Sorry Afnan kiyi hakuri kibarni nayi maki." Girgiza kai tayi alamar bata so, kuma bata bud'e idonta ba." Saboda Tausayin ta da yakeji haka nan ba dan yasoba, Dole ya sashi fitowa daga toilet d'in yabata wuri, tayi wankan." Zaune yayi a kan kujerar dake kusa da toilet d'in yana jiran fitowarta." Wanka takeyi sai kuka takeyi, da kyar tasamu ta kammala wankan, Ta d'auko kayanta wad'anda ta wanke jik'akk'u ta sanya, a jikinta sannan ta fito." Dafe da kai tafito domin matsanancin ciwon da yake mata, saboda taci kuka, har wani zazzab'i takeji, kuma gashi bataci abincin dare ba." Karo taci dashi zaune a kan kujera ya rafka tagumi." Yana ganin fitowar ta, yayi saurin mik'ewa tsaye yana kallonta yace mata "ya hakan?" Shareshi tayi ta rab'ashi ta wuce ta nufi k'ofar da zata kaita Palo." Da sauri ya tareta ya kai hannunsa zai rungumeta, tayi saurin buge masa hannu." Yace "kina nufin da jik'ak'k'un kayan nan zaki zauna?" Bata kalle shiba bata ce masa komai ba, saboda haushinsa takeji, Kauce masa tayi ta wuce." Ya k'ara shan gabanta, cikin zafin nama ya rugumota zuwa jikinsa yace "kina hauka ne?" Zaki fita a tsakar Daren nan?" Ko kuwar kwace jikinta takeyi daga rungumar da yayi mata, tana cewa "ina ruwanka." "Da ruwana dole in kula da lafiyar matata, kina so mura ta kama min ke?" Gashi Asuba na kunno kai sanyi zai yi yawa, zoki kicire jik'ak'k'un kayan nan, ki sanya rigata." Tace "Ni bazan saka ba." Yace "Ashe ko zaki wuni a d'akin nan." Tace "saboda me?" Yace "saboda bakijin magana ta." Hawaye suka soma zubo mata, cikin shagwab'a tace "ni kaina keyi min ciwo." Ya kai hannunsa cike da tausayinta zai tab'a goshinta nan ma ta buge masa hannu." Sangarta ta da shagwab'arta sun fara burgeshi, yanayin maganar ta ne ko?" Ya tambayi kansa." Rik'o hannunta yayi da k'arfi yajawota ta fara tafiya, domin idan ta tsaya a hakan da wad'an nan kayan masu sanyi komai zai iya faruwa da ita." Yace "kije ki cire kayan nan ki sanya jallabiya sai ki sha magani." idan kuma kika kuma bud'e baki kikayi min musu, to saina kuma yimaki abunda nayi maki d'azun." Zaro ido tayi cike da tsoro tace "dan Allah kayi hak'uri, da zafi sosai, wallah idan ka kuma yi kasheni kawai zakayi." Dariya magarta taba shi, yace '"to idon bakison na kuma yi maki, kibi umurni na, kiyi abunda na sanyaki." Ba musu ta wuce shi ta d'auko jallabiyar tashiga toilet ta sanya ta fito." A Bakin gado yayi mata nuni da tazo ta zauna, kusa da shi, ba musu taje ta zauna a d'an nesa dashi, Magani ya d'auko ya k'ak'k'are ya mik'a mata had'ida ruwa yace "ungo ki sha." Marairaice fuska tayi cikin shagwab'a tace "A'a ni yunwa nakeji ba magani ba........" Oh!! Karb'i kisha sai mutafi falo na had'a maki _cornflast_ ki sha ko?' Ba musu ta karb'i maganin ta sha." Taji dad'in hakan a ranta cewa takeyi yau she rabun ta da shan _cornflask_." Rik'ata yayi zasu tafi falo cikin shagwab'a tace, sakeni zan iya tafiya da kaina." Tafiya takeyi a bubbud'e, sai yanzun ya lura da hakan, tausayin ta da sonta ya kuma kama shi, yace "amma kam da na rabu da ke Afnan da na cuci kai cutar da bazan tab'a yafewa kaina ba." Ji kawai tayi an d'auketa kamar jaririya ya nufi falo da ita, ya d'orata a kan kujera, had'ida jera mata sannu." Da sauri ya had'a mata _cornflask_ ya mik'a mata, tana sha ya tsura mata ido yana kallon d'an kara min bakinta, ya yadda take wasa fa cokalin da take shan _cornflask_ d'in." Bakinta mai kyau, d'an k'arami gashi pink shar dashi." Yashiga tunanin ashe mata masu kyau ba duka suka taru suka zama d'aya ba." Ba kowacce mai kyau ba ce ke zama marar kirki, ita mugunta a zuciya take ba'a fuska ba." Ta mik'e tsaye da kyar tace "na gama." Ta katse masa tunanin da yake, ya kalleta yace kinyi wankan tsarki?" Taji kunyar tambayar tashi, ya gano hakan, yace "kalli ogogo ba dad'ewa za'a kira sallar asuba, idan bakiyi ba kije kiyi sai muyi sallah." Ta sunkuyar da kai bata bashi amsaba anan ya gane tayi take nufi." Ya tallabeta yanufi kan gado da ita, gyara mata kwanciya yayi had'ida lullub'eta da bargo, Brest d'inta ya d'an gogeshi k'arjinshi, Wani abu yaji ya taso masa tun daga saman shi, har k'asan shi." cikin dubara ya d'an yaye bargon da ya lullub'eta dashi, Ya tura hannun shi cikin jallabiyarta ya fito da Brest d'in ya sanya bakinshi ya shiga tsotsa yana d'an matsasu cikin wani salo" Saukar ruwan hawayenta yaji a hannunshi yayi saurin barin abunda yakeyi yana cewa "sorry na daina, yi shuru daina kuka." Wuri ya samu a gefenta ya kwanta, gaba d'aya barci yayi awon gaba dasu." Buga k'ofar da akeyi shi ya tayar dasu daga barcin da sukeyi, Bassam ne yayi saurin tashi yanufi wurin k'ofar da sunan bud'ewa." Afnan itama ta farka amma sai tayi likimo kamar barci takeyi." Koda yaje ya bud'e Sadi yagani a tsaye yana rangwad'a kamar wata mace, ganin Yarima ya bud'e k'ofa sai k'ok'arin tusa kansa yakeyi zai wuce cikin d'akin yana kiran "Aminiya." Tura Sadi Waje Bassam yayi had'ida ci masa kwalar riga, ya shak'e wuyan Sa yace "wace ce Aminiyar taka?" Kaifa namijine ba macce ba, to daga yanzun na soke Amintar taku." Da kyar sadi yasamu Yarima ya sakeshi ya zube k'asa yana fad'in ayi hak'uri Yarima bazan sakeba, tafito mutafi." Yarima yace kutafi ina?" bazata je ko inaba, ka fad'awa masu kula da dabbobi su koma a kan aikinsu, Kuma karka kuskura ka fad'awa kowa Afnan na wurina." Sadi ya kalleshi cike da mamaki yace "angama ranka ya dad'e yanda kace haka za'ayi." Afnan najin muryar Sadi tayi saurin saukowa daga kan gadon tanufo bakin k'ofar inda takejin maganarsu , jin hukuncin da yarima ya yanke yasa taja bakinta tayi shuru, batayi maganaba." Sadi bai lura da ita ba, har zai wuce yaji ta kwad'a mai kira tace "Aminiya.' Ya juyo da sauri yana jin dad'in ganinta yace "Naam Aminiya." Ya kuma yi saurin rufe baki, da ya tuna da gargad'in Yarima yayi mashi." Yarima yayi tsaye yana kallonsu, Afnan ta kalli Yarima ta sunkuyar da kai cikin maganarta mai taushi a hankali ta furta, tace wa yarima inaso zanyi magana dashi." Yarima yayi d'an nesa dasu, a nan suka shiga maganarsu a hankali wadda nikaina bansan abunda suke cewa ba." Bayan sun gama ne Sadi ya tafi, itama ta koma d'aki, Bassam ya biyo bayanta." Gabanta yasha ya danganeta a bango ya tsareta da ido, yana huci sannan yace "meye tsakaninki da shi? Me kika fad'a mashi?" Tace "ba komai." Ya kuma kallonta cike da kishi yace kirik'a kama jikinki dashi, shifa namijine ba macce ba ne." Tasa idonta k'asa tana magana k'asa k'asa cikin shagwab'a had'ida turo baki take cewa "meye kuma ruwanka da shi ai a tare ka ganmu." Murmushi yayi domin shagwabarta tana bashi sha'awa da dariya, ya kyaleta yashiga toilet ya d'auro Arwala yafito, yanufi masallaci domin yin sallar Asuba." Afnan na ganin ya fita itama tashiga toilet ta d'auro Arwala tafi to, ta sanya hijabin Saratu, ta shinfid'a sallaya ta tayar da sallah, Bayan ta kammala sallah tayi addu'o'i inta ta shafa, ta mik'e tsaye tanufi hanyar fita." Sai da ta duba ko ina bataga kowa ba, sannan tashiga sauri harda had'awa da d'an gudunta kai tsaye tanufi b'angaren Anna." [3/5, 4:58 PM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *inajin dad'in soyayyarku gareni, da kulawarku gareni masoyana hak'ika ban abunda zan iya furta maku sai dai godiya* *Nagode sosai da nuna k'aunarku gareni* *inajin dad'in kasan cewa daku ako da yaushe, amma idan natuna soyayyarku gareni ta novel ce sai inji d'aci a raina* *domin nasan da zarar kunji ni kwana biyu na daina novel zaku manta dani ku shafe labarina, zaku manta da ummu safwan a rayuwarku*😭😭😭😭😭😭😭😭😭😭 *sai nake tunanin inama zan dawwama ahaka cikin soyayyarku har Abada*😭😭😭😭 *45* Gudu takeyi domin ganin ta isa b'angaren Anna tunkafin Fadawa su fito daga masallaci su dakatar da ita, suhanata shiga." karo taci da Sadi Wanda dama sun shirya hakan shi zai rakata ya zamar mata sheda a wurin Anna, saboda karta zargeta da wani Abu daban." Gaba d'aya suka jera a tare, had'ida gamawa da d'an gudunsu suka shiga b'angaren Anna." Da shigarsu Afnan na gaba Sadi na biye da ita a baya, Mairo da Talatu taci garo dasu suna hidimar gida, suna ganinta, cike da mamaki sukayi saurin zubewa k'asa suna gaida ita." Mamaki Sadi yashi gayi, ganin bayi sun zube k'asa suna kwasar gaisuwa ga Afnan." Mik'ar dasu tsaye tayi ta rungumesu, tace "ina Anna?" Had'a baki sukayi sukace tana ciki?" Gaba d'ayansu suka isa wurin Anna har da Sadi, shi dai mamaki yakeyi biye kawai yake." Anna na zaune tana lazami jin muryar Afnan da tayi takasa ci gaba da Jan carbin, ta mik'e tsaye ta nufo inda takejin hayaniyarsu." Ganin tabbas Afnan ce Anna ta zare ido tare da kiran sunanta "Afnan." Afnan batajira komai ba a guje idonta cike da hawaye ta isa wurin Anna ta rungumeta." Anna ta rungume Afnan a jikinta, tace "ya haka?" ina kika tafi?" Nashiga damuwa mai tsanani Afnan na rashin ganinki." Afnan ta fashe da kuka." Anna na ganin hakan ta kori kowa daga d'akin." tace "kiyi hak'uri Anna nice najawo kai, tsotsayi ya kaini wurin Yarima inaso inje inga Kaka, shine Yarima ya mayar dani baiwa mai aikinshi." Ta kwashe labarin duk abunda ya faru ta gaya mata." Anna Mamaki ta hauyi wato Bassam ya hana Afnan dawowa wurinta, kuma ya kamata yana ta faman cutar da ita?" Tunda yake mata laifi, na yau daban ne, domin ya b'ata mata rai sosai." Lallashin Afnan tashigayi har tayi shuru, tayi kwance a cinyar ta tana ajiyar zuciya." Sadi yayi sallama ya shigo, ya zube k'asa ya dubi Afnan yace "Aminiya kitashi mutafi." "Ina zaku?" Anna tayi tambayar cikin zafi." "Ranki ya dad'e Yarima zai nemeta....." Tayi masa dak'uwa da hannunta tana cewa "kaga naka dakai da Yarima tashi kabani wuri." Sadi ya marereci fuska yace "Ranki ya dad'e idan Yarima ya nemeta bai gantaba kashe ni zaiyi." Anna ta hasala tace "kai tashi ka wuce ka barmin gidana, idan ka kuskura ka gayawa Yarima tana gidan nan nima sai na kasheka." Nan da nan ya rufe bakinsa da hannunsa yace "natuba...." Ya tashi ya fita cike da far gabar abunda zai biyo baya." Bassam na masallaci amma hankalinshi na wurin Afnan d'in shi yana tunaninta." A yanzun jin sonta yakeyi yana bugar masa zuciya, jinsa yake baya iya rayuwa sai da ita." tunani yashiga yi, da ya rabu da ita da ya tabbatar da yayi babbar hasara a rayuwar shi, Domin jinsa yakeyi a duniya babu abunda ya tab'a so kamar Afnan." Gabanshi yashiga fad'uwa bai jira fitowar maimartaba daga masallaciba, kamar yanda suka saba, yataho warshi yana tunanin Afnan d'inshi." Afnan nafita daga sashin yarima, Saratu ta shiga, kai tsaye kan gado ta fad'a ta kwanta a inda Afnan ta tashi, taja bargo ta rufe." Bassam na shigowa cike da d'aukin Afnan, kai tsaye kan gadon ya fad'a, yana fad'in barci kikeyi ne?" Bud'e bargon yayi yashiga had'ida rungumota zuwa jikinshi, wani wari ya daki hanyacinsa Wanda yasa yayi saurin sakinta ya mik'e zaune." Itama tashi zaune tayi ta bud'e k'aton bakinta tayi dariya tace "ido na biyu Yarima na." Ta kuma nufoshi daniyar ta rungume shi, yayi saurin durowa daga kan gadon." *kuyi hak'uri da wannan mura nakeyi kaina ke ciwo*😩 [3/5, 5:18 PM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *46* Da Sauri ya fad'a toilet yana Neman Afnan, amma bai gantaba, ya fito ya Tarar da saratu zaune a gefen gado tana jiranshi domin yau a buk'ace take kwana biyu bai sosa mata ba." Tana ganin ya fito toilet, tacire kayan jikinta, ta koma daga ita sai best da d'an wando, tanufoshi tana wata tafiya kamar wani k'ato," Tsawa ya daka mata Wanda ta sanyata yin saurin tsayawa cak tana kallonshi cike da mamaki." Yace "baki da hankali ne?" meye natub'e kaya daga ganina?" bazaki jira harna tayaba?" To wuce ki sanya kayan ki bana buk'ata yanzun." Sannan kuma A lokacin da kika shigo baki ga kowa ba?" baki ci karo da kowa ba?" Idonta ya cika da hawaye tace "babu Wanda Nagani a hanya da zan shigo." Tausayi tabashi ya matso kusa da ita ya rik'ata." yace "kiyi hak'uri saratu, akwai abunda yashiga gaba na, Ki Koma wurin zamanki da zarar na maganci matsalar zan nemeki kizo turaka." Ta d'aga kai alamar to." A nan ya barta yafita neman Afnan, fadawansa masu gadin k'ofa ya fara tambaya, ko sunga wata farar yarinya mai kyau tafito?" Suka CE basu ganta ba." Da sauri yake tafiya yana kalle kalle ko zai ganta, amma bai gantaba, kai tsaye wurin kiyon dabbobinta ya nufa koda tana can, Sai ma gani yayi masu kula da dabbobin da yasani a da sune suka dawo a kan aikinsu." Tambayar su yayi yace "ina wadda keyin aikin nan?" Sukayi saurin zubewa gabansa sukace "ranka ya dad'e babu gantaba tun jiya, Idan kuma munyi laifi a yi hak'uri Sadi ne yace "kace mudawo bakin aikinmu." Yace "haka ne." A gadarance." Ya tambayesu "ina Sadin yake." Ya ambata a zuciyarsa ai duk inda Afnan ta tafi yasani tunda Aminiyar shi ce.". Nuna mashi wani d'an d'aki sukayi suka ce "ranka ya dad'e yana cikin d'akin can." D'akin ya nufa cike da tashin hankali domin ganin yakeyi yarasa Afnan, kuma rasa Afnan a wurinshi a yanzun wani babban tashin hankali ne, domin itace rayuwarshi bayajin zai iya rayuwa a doron k'asa batare da Afnan ba." A yanzun ya kamu da makahon sonta." Don ya d'and'anni Zak'in zubar ta, wadda baitaba shan irinta ba, ga zak'i ga gard'i." Kai ko a cikin mata Afnan ta daban ce." D'akin Sadi yanufa baiga kowa a cikin saba." Sadi yana hango Yarima tafe, ya tsere, ya b'oye domin yasan za'ayi hakan." Cikin tashin hankali yarima ya nufo masu kiyon dabbobin yana masifa, yana fad'in "na tambaye ku Afnan kunce baku ganta ba." sannan kuma kun nuna min d'aki kun ce min Sadi na ciki, na kuma duba ban Ganshi ba." Zubewa k'asa sukayi Suna bashi hak'uri, suna fad'in "A yi hak'uri ranka ya dad'e tuba mukeyi anan ciki mukaga ya shiga." Bai kulasu ba, illah yaja dogon tsaki yayi tafiyarshi." Mamaki suka shigayi suka kalli junansu suka ce" A gaskiya Yarima ya canza yau akwai abunda keda munshi." D'ayan yace "ni ina ganin kamar a zauce yake, ba'a hankalinshi yake ba. Suka had'a baki suka ce Allah ya kyauta." ************** B'angaren shi yanufa sai safa da marwa yakeyi, baya zaune baya tsaye, ya kasa zama sai yashiga kicin ya fito ya zagaye falon dake gidan kusan falo bakwai bai gajiba, ji yakeyi kamar ya kurma ihu yakeji ." Ina Afnan take?" Ina tatafi?" Yashiga d'aga murya yana fad'in, pls Afnan kidawo gareni, kece rayuwata." A guje Audu yashigo saka makon jin muryar yarima da yayi kamar yana magagganu." Ya runsuna yace ranka ya dad'e gani magana kakeyi?" Tsawa ya daka wa Audu wanda bai tab'a yimasa irinta ba yace "tashi kabani wuri ban kiraka ba." Da Sauri Audu ya mik'e yana fad'in Allah ya huci zuciyar Yarima mai jiran gado." Tunani yashiga yi ina zaiga Afnan?" Wata zuciyar tace kanemi Sadi duk inda Aminiyarshi take yasani." Ya tuna da lokacin da Afnan tace " Yaba su wuri zasuyi magana, To me suke cewa?" Tabbas Sadi yasan inda Afnan take." Kuma gashi yayi ta Neman wayar shi a kashe yake jinta." Misalin k'arfe 5:30pm yafito jiki ba kwari yanufi neman Sadi." Duk yanda Sadi yaso kau cewa Yarima dan karya ganshi yayi shi, domin yasan had'uwarshi dashi ba kyau." Sadi na fitowa yana ganin Yarima ya koma da sauri, Ai kuwa Yarima ya bishi inda yaga ya shiga, B'acewa yayi ya shige cikin store d'in abinci inda Afnan ke zama." Bai tsiraba Dan Yarima ya ga inda ya shiga, Ya bud'e store d'in ya isa gaban Sadi yayi tsaye yana kallonshi." Sadi dake duk'e ya b'oye cikin buhuhunar shinkafa, yasaki baki da ido wuri wuri yana kallon Yarima shima." Da kyar yayi k'arfin halin yi mashi magana, yace " ranka ya dad'e kayi min rai." Cikin k'unar zuci Yarima ke tambayar shi "ina Afnan?" Sadi yace "nima.... ban...sani ba kayi hak'uri." Yarima ya har zuk'a yaciyo kwalar Sadi yace "karya kakeyi muna Fuki kasan inda take, ba aminiyar ka bace?" Sannan maganar me kukayi da ita a jiya?" Sadi ya had'iye miyau masu zafi. Ya turo ido waje yace "Eh haka ne?" Yarima yaga b'ata masa lokaci zaiyi ya yasakeshi, ya sassauta muryanshi yace, Ka kwatar da hankalinka ba abunda zanyi maka ina Afnan?" Sadi yace tana gidan "Anna." Yarima yaji gabansa ya ya fad'i, Ya kalli Sadi yace ya akayi tatafi?" Sadi yace "shima dai bai saniba tace dashi kawai ya tsaya ya rakata." Yarima ya daka mashi tsawa yace "kai! Kai! Mts! Yaja tsaki yace kai soko ne wallahi." Sadi ya tsorata da yanayin da yaga yarima, a yanzun hankalinshi ya kuma tashi, ya fashe da kuka kamar macce yace " ai nafi soko sakarci k'ara min wani dai ranka ya dad'e Dariya ya bawa Yarima yace "kai k'aton banza ka maida kanka macce k'arfi da yaji." Yabaro shi ya fito." Sake sake yakeyi a ransa Yanda za'ayi ya tunkari Anna." Rabonshi da Anna har ya manta, koda ya auri saratu bai fad'a mataba kuma bata sanya shi a ido ba, yasan fushi takeyi dashi, kuma ga wannan laifin da yayi na rik'e Afnan a hannushi yana wahalar da ita." Yasan halin Anna akwai d'aukar zafi, har dai idan aka tab'a mata Afnan." Tunani yashigayi idan yashiga wurin Anna ta ina zai fara?" Wata zuciyar tace kashiga kawai, sai kayi mata bayani, ai Afnan matarka ce. Kuma kai ka auro abarka." Kai tsaye yanufi sashin Anna gabansa na fad'uwa." Anna na zaune a can cikin falon sama suna hira da Afnan, Da sallam ya shiga a hankali jikinsa ba kwari, Ganin Afnan da yayi yaji wani Abu ya daki zuciyarshi ya kafe ta da ido yana kallonta." Da sauri Afnan ta mik'e ta je bayan Anna ta zauna, tare da b'oye fuskarta." Satar kallonshi takeyi dan gani tayi yayi mata wani irin kyau." Tun jiya take tunanin shi. Take tunanin abunda ya faru tsaka nunsu. Ta rufe ido tana jin wani Abu nayi mata yawo a cikin jikinta." Kai tsaye kusa da Anna yaje ya yasamu wuri ya zauna, Ya runsunar da kansa k'asa a alamar girmamawa. Yace " Anna anwuni lafiya." Anna ta shareshi ko kallon shi batayi ba, taci gaba da kallon T.V." Kuma matsowa yayi daf da ita, ya rik'o hannunta yace "Anna nasan nayi laifi kiyi hakuri." Bata tanka mashi ba, kuma bata kalle shiba, domin ya k'ureta da yawa." Sanin halin hushin Anna da yayi, Yasa bai Kuma yin magana ba, illah ya mik'e tsaye, zai tafi, ya kuma kallon Anna yace "tuba nakeyi Anna kiyi hak'uri, zantafi idan kika huce zan dawo." Ya maida kallon shi ga Afnan da tun d'azun take satar kallonshi, K'ura mata ido yayi cike da so da k'auna, D'an k'aramin bakinta yake kallo, ya tuna da Daren jiya." .ji yayi hankalin shi ya tashi, yaji sha'awar ta ta fisgeshi, ya cije leb'on k'asa yafita." Afnan na ganin hakan takasa hak'uri ta tashi tashige dakinta ta rufe kanta." Tunanin Yarima tashigayi duk tabi ta damu da kyaleshin da Anna tayi." Anna naganin ta tamik'e, tabita da kallo had'ida mere baki☹ Tace yaro man kaza, ta k'ara muryar tv taci gaba da kallonta." Bassam kuma kai tsaye fada ya nufa wurin maimartaba." [3/5, 5:21 PM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *47* Ya tarar da maimarta zaune a kan kujerar mulkin sa." tare da wani mutum, a gabansa, daga ganin yanayin yanda sarki yake hira da mutumin zaka gane yana da wani matsayi a wurin shi." Yarima ya shiga fadar da sallama d'auke a bakinshi." Suka d'aga kai gaba d'ayansu suka kalleshi tare da amsa mashi, fuskarsu d'auke da murmushi." Yarima ya samu wuri ya zauna gefen mahaifinshi, ya runsunar da kai ya gaidasu gaba d'ayansu." Suka amsa mashi had'ida Sanya mashi Albarka." Maimartaba yace "yawwa magajin sarki, kwara da Allah ya kawoka. Yanzun nake tunanin na aika fadawa sukiraka, domin kazo ka gaida babban Aminina Wanda duk lokacin da yake zuwa baku tab'a had'uwa da shiba." Yarima ya kuma kallon Aminin mahaifin nashi sai wani bud'ar baki yakeyi, Sam bai kwanta mashi a raiba, daga ganin alamunsa a kwai rashin gaskiya a tare da shi." Maimarta ya maida kallonshi ga Aminin nashi, yace " *Alhaji Aminu* Wannan shine babban d'ana wato Bassam, kamar yanda kasani, sai kuma k'aninsa da ba a dad'e da haifa min shiba, sunan shi Yazeed." Alhaji Aminu yace "Allah sarki Allah yaraya manasu, ya kuma Sanya masu Albarka." Sarki yaji dad'in Addu'ar Alhaji Aminu sosai yace "Amin ya Allah Nagode." Sannan maimartaba ya kuma mai da kallonshi ga Bassam yakira sunanshi yace "Yarima wannan shine d'aya Aminina, wanda muka tashi tare dashi, sunanshi Alhaji Aminu Wanda nasan kanajin sunanshi da labarinshi a bakina." Yana zaune a garin kano inda yake gudanar da kasuwancinsa." Mu Uku ne, muka tashi a tare, kuma muke kasuwancin mu a tare a garin kano, D'aya daga cikinmu Allah yayi mashi rasuwa wato *Alhaji Ibrahim* Wanda yarasu saka makon had'arin jirgin sama a hanyarsa ta zuwa Dubai d'auko kaya." "wadda a kullum idan muka zauna nake baka labarin irin taimakon da yayiwa rayuwata da kuma dukiyata." Yarasu ya bar mata d'aya da "yarsa d'aya da kuma mahaifiyar shi." A yanzun haka Alhaji Aminu shike d'auke da iyalan marigayi, wadda ya d'aukesu gaba d'aya ya kaisu can k'asar waje da zama saboda karatun yar marigayin marainiya Allah." Sarki yace "Alhaji Aminu ina jinjina maka a kan namijin k'ok'arinka na kula da marayun Allah, Sai nakejin ina a garin kano nake da Muntaru mun kuma nunawa wad'an nan bayin Allah gata da kuma d'ebe masu kiwar jigonsu da yarigamu gidan gaskiya." Allah yajik'an Alhaji Ibrahim." Suka amsa gaba d'aya da "Amin." Alhaji Aminu harda zubar da hawaye." Sarki ya kuma kiran sunan Yarima, Yace Yarima ga Alhaji Aminu nan ko bayan bana raye a ci gaba da bashi dubu d'ari biyar duk bayan wata biyu, yana k'arawa domin tallafawa rayuwar Marainiyar Allah." Ni nasan ina kwatantawa ne, domin duk abunda nayiwa zuri'ar Alhaji Ibrahim ninasan ban biyashi d'unbin Alherin da yayi munba." Alhaji Aminu idanunshi na zubar da hawaye yace " godiya sukeyi, Allah ya yatayamu rik'o." Bassam ya kurawa Alhaji Aminu ido yana karanto wani Abu a tare dashi, Wanda shima Alhaji Aminu ya tsorata da kallon da Bassam yake masa, domin wani Abu yake hangowa a cikin idanun Bassam." Bassam yace "insha Allahu Abba yanda ka tsara haka zan aiwatar, Allah ya k'ara maka lafiya." Suka Amsa da Amin, sannan Bassam ya mik'e yace "nabarku lafiya." Ya fita." Yana fita Alhaji Aminu ya kalli maimartaba yace "na yaba da hankali d'an nan namu Bassam, domin kuwa jarumine." Sarki yayi dariya yace " haka nan yake, yarima kenan d'a d'aya tamkar dubu." Bassam na fitowa daga fada ya Tara fadawa masu gadin k'ofar fadar, tun daga k'ofa ta farko har zuwa k'ofa ta biyar." "yana basu umurni yace "kusanya min ido sosai a kan Mutumin da kuka gani yashiga fada yanzun." aduk lokacin da kuka ganshi yazo ku sanya mashi ido tun daga zuwanshi har fitarshi. Idan Nazo sai Ku gaya mun." Suka "Amsa da angama ranka ya dad'e." Yayi tafiyarshi sannan kowa ya koma bakin aikinshi." ***************** Malam Nura kuma a kullum tunanin Afnan yakeyi kuma bai cire tunanin zata dawo gareshi ba." Kullum addu'ar shi d'aya Allah ya dawo mashi da Afnan d'imshi suyi aure har su haifafa." Maryam kuma sai shige mashi takeyi ajiki alamar tana son shi." Shi kuma bata gabanshi kwata kwata." Domin ita tun da ta d'ora idonta a kanshi, tun a makaranta, taji ta kamu da sonshi, jin ya furtawa Afnan kalmar so, ya sanyata hak'ura da kuma dangana gareshi." Amma yanzun tunda kuma Afnan tayi aure, taji soyayyar shi ta dawo mata sabuwa, ta d'auki alk'awarin duk yanda zatayi sai tayi, domin ganin ta shawo kanshi ya manta da Afnan yadawo gareta ya so ta, ya kuma aure ta, suyi rayuwar aure mai cike da soyayya k'auna." *Kaka* kuma babu abunda ta nema ta rasa a rayuwa." da ita da malam iro, Burin kaka d'aya ne a yanzun ta sanya ido, taga Afnan d'inta, Wanda a kullum maimartaba yake yawan aiko mata da sak'on hak'uri cewa "tayi hak'uri zai aiko a zo a d'auketa a kaita wurin jikanyar ta domin ta ganta, ta kwantar da hankinta tana cikin k'oshin lafiya." ******************* Yau satin Afnan d'aya a gidan Anna." Kullum Bassam yana zuwa bawa Anna Hak'uri, amma bata kulashi, sai dai ma ta tashi ta bar mashi wurin." Ji yakeyi kamar ya kurma ihu, yakeji a kan takaici, Babu abunda yafi d'aga mashi hankali irin katangar da tasanya mashi da Afnan kwata kwata bata bari su had'u, bare ya sanya ido gareta ya ganta ko sanyi yaji a ransa." K'arfe goma na safe, ya shirya tsaf cikin k'ananun kaya zunyi mashi kyau sosai, yafito ya nufi wurin Anna domin hak'urin shi ya k'are, yau duk yanda za'ayi sai dai ayi amma matar shi yake buk'ata." Ya shiga babban falon gidan, da sallar shi kamar yanda ya saba." Baija an amsa mashiba, saka makon ba kowa a falon, ajiyar zuciya yayi, yanufi d'akin Afnan." Murd'a k'ofar ya shigayi, yajita a rufe, yaja dogon tsaki. Ya koma wurin window ya d'age labulan window yana lek'enta." Afnan ya gani d'aure da towel da alama wanka ta fito, tana gaban madubi tana tsantsara kwanliya." Kafeta da ido yayi, cike da sha'awa sai had'iyai miyau yakeyi." Gyaran gashin kanta ta shigayi da ya zubo kwance a bayanta." Bayan ta mammala kwanliyar ne, ta tashi daga gaban madubin, ta d'ako bra d'inta ruwan madara ta sanya, ta d'auko bracelet na k'afa da dogo wando peach colour da alama kayan Pakistan take son sanyawa." K'ureta da ido yayi sai lasar Baki yakeyi domin gaba d'aya k'afafunshi sun kusan kasa d'aukar shi, saboda sha'awarta da ta dirar mashi." Audu yaji muryarshi a bayan shi, yasa yayi saurin sakin labulan window, ya zare ido cike da tashin hankali yace "kai meya kawoka nan?" Waya fad'a maka nazo nan?" Tun yau she kake tsaye a nan?" Mekagani a cikin d'akin?" Tabbas Audu kana buk'atar hukunci." Audu ya zube k'asa yace "ranka ya dad'e kayi hak'uri yanzun nazo, kuma banga komai a cikin d'akinba." Baka amsa min tambayata ba nace me ya kawoka nan? Inda mata ke zurga zurga." Ayi min afuwa ranka ya dad'e, na tuba bak'o ne kayi, yana jiranka." Kaje kace bana kusa kowaye yatafi gobe ya dawo." Audu yace "angama ranka ya dad'e kafemin." Audu yafita da gudunsa." Bassam na juyowa sukayi ido biyu da Anna, Ta tsareshi da ido tana kallonshi, tun da yashigo tana zaune a kan kujera lura da ita ne kawai baiyiba, tana kallonshi duk abunda yakeyi." Ya d'an daidaita kanshi ya nufi wurin Anna." Anna da ta had'e fuska tana kallonshi, tace "kaima mekakeyi a nan?" Mekazoyi tun da safe a nan." Kajuya katafi wurin matarka Wanda tafiye maka mu." K'arasowa yayi wurinta ya kai durk'ushe had'ida sunkuyar da kai yace " Anna nayi kuskure kiyi hak'uri, ki yafemin." [3/5, 7:59 PM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *48* Anna ta dubeshi da kyau, tabbas ta hango nadama a cikin idonsa, ya bata tausayi." Tace "ai indai hak'uri ne bakajin wahalar bani shi." Kayi min laifi da yawa, dama d'an Adam butulu ne......" Har aure kayi baka fad'a minba, Sannan ka samu 'yar mutane Afnan kanata azaftar da ita." Ya kuma sunkuyar da kai yace "Anna auren saratu danayi inada dalili, amma kiyi hak'uri ya riga ya faru." Idan ban hak'ura ba ya zanyi Yarima?" Hakan yasamu yayi ta lallashin Anna har ta fara sakar mashi fuska suna fira, sannan daga k'arshe yayi mata sallama yafito cike da murna." Sashinshi ya nufa, da fara'arshi ya tarar da Saratu zaune tana jiranshi, daga ganinshi tayi saurin tasowa ta nufoshi ta rungumeshi tana jera masa sannu da zuwa." Bayabo ba fallasa ya amsa mata had'ida tambayarta ya hidimar gida? Cikin rangwad'a da kissa take amsa mashi, har da wani kashe murya😊." Lura yayi da yanda take wani juya ido tana wani rangwad'a, yasan manufarta, kuma a yau zai daure ya danne hancinsa domin ya faranta mata." Toilet yashiga yayi wanka, had'ida arwala.ya shinfid'a sallaya ya ta yar da sallah." Tana zaune tana kallonshi sai had'iya miyau takeyi saboda jaraba." Bayan ya kammala sallar yayi addu'a had'ida shafawa, ya mik'e tsaye, tayi saurin nufoshi ta rungumeshi, shima rumgumeta yayi wani wari yaji ya doki hancinsa, ya yamutsa fuska, ya daure yace "Baby nayi missing d'inki kwana biyu." Zarcewa sukayi kan gado, ta cire kayan jikinta ta shiga shafa shi ta ko ina." Shima mayar mata yakeyi amma jinsa yakeyi kamar yayi amai saboda azabar warin dake fita a jikinta, Haka ya shiga biya mata buk'atar ta. Sai kuwa takeyi, sai da ya sanya filo ya rufe mata baki." Haka nan yaci gaba da biya mata buk'ata, babu abunda yakeji dangane da ita, saima jinsa yakeyi kamar ya sanya 🍌 a cikin ruwa." Gajiya yayi ya sauka a kanta ya kwanta gefe d'aya." Yana maida numfashi, tunawa yayi da Afnan da irin zumar da ya lasa a daren farkonsu, yayi murmushi yace a zuciyar shi, Afnan ta dabance bazan tab'a rabuwa da keba." Ya juya ya kalli saratu yaga tasaki k'aton baki, tana bacci, A hankali yatashi ya bar mata d'akin, ya koma d'aya d'akin ya kwanta." tunanin Afnan yakeyi har barci ya d'aukeshi." *************** Yau juma'a bayan sundawo daga masallaci tare da maimartaba, Kai tsaye sashin Anna yanufa domin yasan duk ranar juma'a tana shirya lafiyayyen abinci, irin na gargajiya, kuma a tare sukeci." Sallama yayi ya shiga." Anna dake zaune tana cin abinci ta d'an saki fuska ta amsa masa." Ganin ta d'ansaki fuskarta, yabashi kwarin gwaiwar zama kusa gareta yanda yakeyi a da." Yasanya hannu a cikin abincin shima yashiga ci." Anna ta dubeshi tace "ya haka yarima ina matarka ne?" Yace "Anna Dan Allah ki daina maganar wancan abar." Taja bakinta tayi shuru bata kuma maganaba." Dan ta fahimci zancen yakeso tayi masa." Afnan ta fito daga d'akinta cikin shiga ta alfarma, ta sanya turare kusan kala hud'u." Ta fito falo, kuyangi na biye da ita." tundaga nesa kakejin k'amshin turarenta yana tashi, da sauri Yarima ya d'aga kai ya kalleta, yayi saurin kauda idonsa, saboda kadda Anna ta fahimci wani Abu." Tana isowa wuri, k'amshin jikinta gaba d'aya ya dake hancinsa, ya lumshi ido." Ta zauna a kusa da Anna a gefe d'aya, ta kalli Yarima cikin girmamawa tace " barka da warhaka Yarima." Murmushi yasaki yana kallonta sonta na kuma shiga zuciyarsa." Yace "barka." kinyi juma'a lafiya." Bata tanka masa ba, illah tasanya hannu ta tsiyaya lemo a Kofi, tashiga sha." Mamaki yakeyi yanda takyaleshi to me take nufi?" Anna na ganin hakan taji dad'i, saima murmushi tayi irin nasu na manya." Shima basarwa yayi yashiga yiwa Anna hira, yanayi yana kallon Afnan, Anna na lura da hakan ta shareshi." Afnan ta mik'e tsaye tace Anna zanje na kwanta." Anna ta kalleta tace badai bacci zakayi ba?" Tana shagwab'a tana cewa "A gajiye nake Anna." Anna tace "to sai da safe d'iyata ta kaina." Bassam idonsa na k'asa. Yana tunin me Anna take nufi dashi akan Afnan ne?" A yanda yasan Anna da saurin fahimtar abu, Ya kamata ta fahimci cewa ya kamu da son Afnan." Kwatakwata yanzun ya lura Anna bata damu dashiba kamar da." Ta ko san yanda yake buk'atar Afnan kuwa?" Ta ko San yanda yake jin Afnan a ransa kuwa?" Anna na lura da shi tasan a tsuke yake, Tayi kamar bata gane ba, Taci gaba da zuba mashi hira." Shi kuma a lokacin bayajin dad'in hiran tata, Yasha jinin jikinsa yayi shuru yashiga tunanin ta ina zai b'ullowa Anna ta gane gskiyar sa, a yanzun tsakani da Allah yake son Afnan." Tun yana tanka mata a hirar har yakai ynzun daga uhm sai uhm uhm yke cewa." Ganin hakan da tayi kamar ba'a hayyacinsa yake ba yasa tayi saurin mik'ewa tsaye zuwa d'akinta tace "Yarima nima nashiga daga ciki." Ka gaida matar ka." Binta yayi da kallo kamar ya fashe da kuka yakejj." [3/5, 8:10 PM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *49* Mik'ewa yayi a fusace, cikin k'unar zuci, yanufi sashinsa." Da shigarshi, Audu yashiga kwalawa kira, Audu ya fito da gudu ya durk'usa yace "gani ranka ra dad'e." Yace "d'auko min ruwana." Babu b'ata lokaci Audu ya d'auko masa kwalbar giyarsa yashiga zuba masa." K'ofi biyar ya shanye, A daren kusan kasa barci yayi, sai juyi yakeyi a kan lallausan gadonsa." Babu Abunda yake tunani sai Afnan, Daren farkon su yake ta tunawa yana juyi." Tunawa yayi da fatar jikinta ita kanta abun tab'awa ce, Ya tuna da laushin lab'b'anta, haka suke kamar bayan tarwad'a saboda laushinsu." K'amshin bakinta kuma, tamkar k'amshin giginya, ga hak'oranta farare anjerasu tsaf gwanin sha'awa." Ya tuna da lokacin da yaga suna dariya da Sadi a can lambu." Ya mik'e tsaye yace "kai ina bazai yiwu ba." Ya mik'e tsaye ya kuma fesa turare yafito yanufi sashin Anna, a lokacin k'arfe shabiyu da kwata. Na dare" Yasan Anna tayi barci." Dashigar shi babban falon, kai tsaye d'akin Afnan ya nufa da Addu'ar Allah yasa k'ofarta a bud'e take." Ya murd'a a hankali ta kuwa bud'e, ya lek'a a hankali yaga kuyangu sunyi kwace a k'asa su biyu." Suna jin k'arar k'ofa suka mik'e zaune da Sauri suna zarar ido, ya saka hannun a kan lab'b'ansa yana Nuna masu dasuyi shiru." Ya nuna masu a hannu da sufita subar d'akin, a hankali suka fita." Ya lallab'a yashiga d'akin ya isa gefen gado inda Afnan take kwance." Dakaga fuskarta kasan bacci takeyi cike da nishad'i, yashiga tunanin ita batama damu dashiba baccinta takeyi hankalinta a kwance." Kallon ta kawai yakeyi, a hankali ta bud'e idonta kamar wadda aka kira sunanta." Ido biyu sukayi dashi, tsoro ya kamata tayi saurin lunlub'e jikinta tana tunanin abunda ya kawoshi d'akinta." Yayi sauri ya hau gadon ya zauna." Ya lura so take ta gudu, ko dai ta manta dashi mijinta ne? Take k'ok'arin gudunsa." Yace "kina tunanin had'uwa da Allah kuwa Afnan?" Ta kalle shi tace "mekake so?" "Ke! Ya fad'a batare da tunaniba." Tace "Ni?" Yace "Eh." Idanunta suka k'ank'ance ta fara tunanin abinyi." "Ke matata ce inada hak'i a kanki." "Yanzun Kasan da hakan, ni bawani hak'i naka a kaina, katafi kawai wurin wacan matar taka, wadda kafi sonta a kan kowa." "Ke waya fad'a maki hakan?" Ya kuma matsota zai rungumeta, tayi saurin ja baya tace Anna na nan fa?" "Ita ta hana ki kawo kanki gareni?" A'a tafad'a da sauri, kaine baka buk'ata ta burinka akoda yaushe kayi min mugunta, bayan karaboni da iyayena da kuma....." Sai tayi shuru." To Afnan kiyi hak'uri mana duk abunda nayi maki akan kuskureni ne, kibani dama na wanke laifina gareki." Ta girgirza kai tace 'ni dai ka tafi d'akinka, Dan kana tab'ani ihu zan maka, Anna tajika tazo ta rabani da kai." Kawuce kawai katafi sashinka." "Tashi muje tare." Yace da ita." A'a babu inda zantafi a yanzun wannan matar taka k'atuwa tayi min duka." Yaso yayi dariya sai kuma ya kuma had'e rai." Yace "wai ke ba'a gaya maki bane?" Tace "me za'a gaya min?" Bakisan sharud'un aure bane?" Ko bakisan matsayina a wurinki ba?" Ke yadace ki kawo kanki gareni ki nemeni, bani ya dace na nemeki ba." Ta kalle shi tace "Dan kana Yarima d'an sarki?" To Nan ba wurin kiwon dabbobi bane." Ya sassauta murya yace " Pls Afnan ki manta da abunda ya faru daga baya, Nima idan na tuna da irin abubuwan da nayita maki duk sai inji banajin dad'i a raina, kiyafe min." Ya kafeta da ido yana kallon bakinta." Tayi shuru batayi mgnaba yace "tashi mutafi sashina." Ta tuna da darensu na farko irin wahalar da yabata, A ranta tace "kai wannan Abu da ciyo fa, ta ya mutsa fuska." Ta sauka daga kan gadon ta nufi hanyar fita d'akin." Yayi saurin tare gabanta cike da jin haushi, da takaici yanda take wani kad'ashi kamar kwallo, shi kamar shi Yarima. yace "ina zaki tafi?" Kina nufin tafiyarki zakiyi kenan, to idan bakiyi hankaliba zan d'auki mataki a kanki." Ta kalleshi tace "zaka rabu da nine?" Alhmdulillah Allah nagode maka." "Babu rabuwa tsaka nina dake akwai mataki da yawa da zan d'auka akanki." Tak'ura masa ido tana kallonshi batayi magana ba, itama ita yake kallo, ganin bata da niyar magana." Yace "wuce mutafi d'akina umurnine daga yarima, ko hukunci ya hau kanki." Ta sunkuyar da kai tace " tuba nake yarima mutafi." Ya wuce gaba tana bayanshi yana fita ta maida k'ofa ta rufe had'e da sanya sakata." Yana ganin hakan bai kuma bin takanta ba yayi tafiyarshi cike dajin haushi yana cizon leb'e." Yana zuwa d'akinshi ya iske Saratu kwance a kan gadonshi ta sanya wasu kayan barci Wanda duk jikinta a waje yake kamar wqni k'ato." Tsayawa yayi cak a bakin k'ofa, saka makon warin jikinta daya gauraye d'akin." Yashiga kiran sunanta da sauri ta mik'e zaune yace "zoki tafi d'akinki zankiraki idan na shirya." Ta taso tana rangwad'a, Ta wurinshi ta rab'a ta wuce. Yayi saurin rufe hancin sa, sakamakon wani kalar wari wadda yafi nada ya doki hancinsa." Yayi saurin shigewa toilet yana kakarin amai." Idonta yashiga zubar da hawaye, ta fita, A ranar tashiga tashin hankali marar misaltuwa domin talura tanaji tana gani Yarima yana gudunta." Kuyangunta ta tayar daga barci, tace "gaba d'ayanku kuzo ku sinsina." Sukayi tsaye tsuro suna kallonta suna zarar ido. Tsawa ta daka masu tace "cewa nayi kuzo Ku sinsina k'asana koji ko zakuji wari." Suka had'a baki sukace "ranki ya dad'e wari kuma?" A tsawace tace "ku sinsina nace bawai Ku tsaya kuna tambaya taba." Sukayi saurin zubewa k'asa suka shiga sinainarta, sukace "ranki ya dade babu wari sai dai k'amshin turaren wuta mai dad'i nan." Tace "to Ku tashi." tashiga tunanin to meyasa Yarima yake toshe hancinsa da bakinsa yana b'ata fuskarsa yana irin yanayin nan da mutum yaji warin Abu." Idan kuma yana kanta sai yayi ta fama da b'acin rai kamar dole aka sashi." Kwana biyu Saratu ta shiga damuwa, k'aura cewar da Yarima yake mata." Dole macce ta shiga wani hali idan mijinta ya k'aura ce mata." Jakadiya ta lura da Saratu tana cikin damuwa, Ta tuna da Sarki ya turo ta domin ta kula da matar Yarima." Gashi kuma hajiya zainab ta sanyata a gaba, ta hanata sakat kullum saita kirata ta dinga tambayar ta, tana bugun cikinta tana tambayarta abunda ke faruwa tsakanin Yarima da saratu, tun tana nok'e nok'e har ta fara sakin jikinta, tana gaya mata saboda zinare da taba mai girman sosai." Duk tazo bata labarin saratu sai tabata dumin kud'i masu yawa taba jakadiya." Saratu kuma in banda hantara da wulak'anci babu abunda ta iya, ga wulak'anta na k'asa da ita, shekararsu biyu da aurensu da yarima, ta canza kuyangi sunfi d'ari biyu, Ita ta aure yarima dole ta juya duk Wanda takeso, ta wulak'anta Wanda taga dama." Shi yasa komai arzikinka, Da ajinka kace zaka wulak'anta d'an Adam kana tare da asara saboda mutum rahama ne, ka kore kowa kowa na gudunka." Gata da muni sai kace biri ya haifeta, abun nata yayi yawa kenan, ga bak'in hali ga muni." Har gara sarauniya akwai kyan gaske sai dai halin ne itama sai ta saya a kasuwa." **************** Sadi ya maida gidan Anna wurin zuwansa Kullum suna tare da Afnan suna hira suna dariya wadda hakan yana k'ara d'ebewa Afnan kewa." Satin Yarima d'aya baizo gidan Anna ba, ya d'auki zafi da Afnan sosai." Anna takira Afnan take tambayarta lafiya ta daina ganin Yarima kwana biyu ko wani Abu ke faruwa?" Afnan tace itama bata San abunda ke faruwa ba." Anna tashiga CE mata "ki kula da kanki domin nasan halin yarima sarai, Kuma nagane take takensa, kizama macce mai aji sai ki kuma samun matsayi a zuciyar mijinki." Abunda Yarima yayi maki idan na tuna imajin zafinsa, Ki kula da kanki har zuwa lokacin da zai soki soyayya ta gaskiya." Lokacin da zanga nadama a idonsa." [3/5, 8:29 PM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *50* Sati biyu kenan Bassam bai sanya ido ga Afnan ba hak'uri kawai yakeyi yana danne zuciyar shi, Amma ko wanne bugun zuciyarshi Afnan yake tunani." Yau juma'a ya kasa hak'ura, Misalin k'arfe hud'u da rabi, da yamma lik'is, Sadi da Afnan suna cikin lambu a nan b'angaren Anna suna tsintar bangwaro suna dariya." Yarima har zai wuce ya shiga ciki, sai yajiyo hayaniyarsu, ya nufo wurin, cikin sand'a." Sadi ya fara ganinsa yayi masa alama da hannu da yatafi." Sadi ya kama barin hanyar, Afnan tace "Amini ina kuma zaka?" Yace "ina zuwa Aminiya, bari in d'auko miki wani Abu da zamu hau mu tsinko mangwaron." Matsawa tayi wurin iccen mangwaron tashiga tsalle alamar so take ta tsinko." Saiji tayi and'agata sama, sai da ta tsunko d'aya, jin jikin mutum da tayi yasa tafara wutsil wutsil, gaba d'aya sukayi baya suka fad'i k'asa, ta fad'a kansa." A dai dai lokacin kuma ruwan sama ya sauko masu k'arfin gaske. Nan da nan suka fara jik'ewa, ta mik'e da sauri, zata gudu wazata gani Yarima ne a gabanta yana ta mata fara'a." Kasa yin komai tayi, ganin yana gabanta, tana tunanin abunda zatayi." Rik'a hannunta yayi yajata zuwa wani iccen, yana da tsawo sannan a kwai reshe da yawa zai tare masu ruwan " Ya jinginata da iccen yayi mata zube da hannunshi, yanda bata iya matsawa daga gurin." Ido ya kafeta dasu yana kallonta ita kuma duk yanayinta ya canza, duk sai tajita wani iri ga tsikar jikinta dake tashi, saboda hannunshi dake shafar jikinta." Ya furta a hankali yace "sanyi kikeji?" Batayi maganaba sanadiyar matsowa da yayi tanajin iskar numfashinsa a kan fuskarta." Idonta har a lokacin a k'asa suke, shi kuma yana k'ok'arin ya kai bakinshi a kan nata." Ta gano hakan Dan haka saita kame bakinta." Yace "baki son in sumbace ki?" Yayi maganar a cikin kunnenta kamar rad'a." Yin shurunta yabashi damar sanya bakinshi cikin bakinta yana tsotsar lab'b'anta a hankali." Ganin tak'i sakin jikinta yasa yasaki bakinta yaja kunnanta yana kissing a hankali zuwa wuyanta." Ya d'an d'ago ya dubi k'irjinta ta jik'e sharkab da ruwa, Gashi k'irjinta ya bayyana kana iya ganin komai na jikinta." Yarasa abunda zaiyi ga baki d'aya yaji buk'atarta yakeyi, ya dubu dama ya dubi hago babu kowa sai su kad'ai." Yayi mata magana a kunne yace "Afnan pls ki tausaya min yau kizo turaka." Ya kai hannunshi a hankali ya shafa k'irjinta had'ida murza kan Brest d'inda da d'an matsasu, Sabon yanayi ya riski dukkan gab'ob'in jikinta jitayi kamar zatayi yaye ne." Bata tab'a jin hakan ba a tare da ita." Ya sanya harshinsa a kunnenta, yashiga wasa dashi a ciki, Rufe idonta tayi saka makon wani Abu da taji yana mata yawo a jiki." Cikin da sanshiyar murya ya maimaita maganarshi yace "yau kizo turaka please." "To ta fad'a da wata dasan shiyar murya." Yayi murmushi yasan tarkonsa ya kamata." Yasan zataso abun da yayi mata yanzun." Ruwan saman ya tsaya cak ya dubeta yace "kisa d'ankwalinki ki rufe jikinki saboda baki San Wanda zaki had'u dashiba a hanya." Ya rik'a hannunta sai da yakaita a bakin k'ofar babban falo sannan yasaki hannunta." Ai kuwa ta ruga a guje." Tabashi dariya yashiga tunanin yau zasu kasance tare zaiji dad'in sosai, Yanayin jikinta abun sha'awa ne, ya k'ara hamdala da bai rabu da itaba kai da nayi sake......" D'akinta ta fad'a tana maida numfashin gudun da tayi, tana tuna abunda Bassam yayi mata tana murmushi." ************** Bassam yana d'akinsa yayi wanka sai k'amshi yakeyi ya lura Afnan ma'a buciyar son turare ce, Yau zaisha Amarci, Ya dad'e yana muradin macce irin ta, Shagwab'ata ya tuna yayi murmushi Ashe masu kyau suna da halin kwarai, a da ya zargesu amma yanzun ya gane ba duka a ka taru aka zama d'aya ba." Kowa zuciyarshi da ban yanda kowa halittarshi daban." Ajiyar zuciya yayi tare da kallon a gogo, k'arfe sha biyu saura,yaji ana kwankwasa k'ofarsa ta ciki, Da gangan ya bar k'ofarsa a bud'e saboda Afnan ta shigo kai tsaye duk da akwai masu gadi wurin." Da saurin shi ya tashi yanufi k'ofar harda tuntub'e yake yi da kafet d'in dake tsakar d'akin." Bakin k'ofa yanufa jikinsa na rawa ya bud'e k'ofar, Sai ganin fuskar saratu yayi tana wani bud'e baki, Ya kauda idonsa daga gareta ya shiga kallon bayanta, Itama ta juya tana tayashi kallon bayanta." Yafita falon yana ci gaba da kalle kalle, tace "akwai abunda kake nema ranka Ya dad'e?" "Oh A'a ba komai ya b'ata fuskarsa yace "kije d'akinki zan nemeki, ina aiki......." "Ranka ya dad'e kwananka goma sha biyar yau rabonka dani......" "Nace kije d'akinki zan nemeki, ya fice a fusace zuwa d'akin barcinsa, ya rufe gub! Kakeji." Ta gano akwai matsala babban ta tsaya tana kallon k'ofar tana hawaye, kusan minti ashirin tayi a tsaye tana kallon k'ofar ya zatayi can ta juya ta fita." Yanajin fitarta daga falon shima ya fito, baiji dad'in yanda ta kasance tsakaninsu ba yana ganin bai kyauta mata ba." To amma idan ma wata goma yayi saita jirashi ya nemeta meya kawota?" Turare ya d'auko yana fesawa saboda warin da tabari." Zaiyi magana da malam Sanusi a dubata k'ila jifa akayi mata." Wasu mutane suna da sakaci basu Neman kariyar da zata karesu daga shairin muguntar d'an Adam." Ance kana iya koyon shairin dan ka kare kanka amma kazama mai yin komai Dan Allah." Ya dace ko addu'ar safe da Allah ya tanadar yayi Alk'awarin kare bawansa mudage muyi Allah mai hikimane." Babu abunda zakayi a duniyar nan da babu addu'arsa ko ta wane yare kayi Allah najinka kuma zai kareka, idan har kayi imani dashi, koda wani mugun abu zai sameka zai zo maka cikin sauk'i." Shuru ba Afnan ba labarinta, Yarima ya kasa zama sai safa da marwa yake tsakanin falo zuwa d'aki, yarasa abunda keyi masa dad'i, Ya tattara ya haye kan gado, yaso ya tafi sashin Anna sai kuma ya duba agogo k'arfe biyu da rabi, baya son a fara tunanin wani Abu a kansa, Dan haka yayi zaune kan kujera ya d'auko giyarshi yana sha yana kallon TV." Da kyar yasamu safiya ta waye, masa." Misalin k'arfe goma na safe yanufi fada wurin maimartaba da damuwa a fuskarsa." Maimartaba nada bak'i dole ya sallamesu, Ganin yarima ya shigo kuma ya lura yana da damuwa a rayuwarsa baya son ganin Bassam cikin damuwa." Ya matso ya zauna kusa dashi yace magajin sarki ya akayi ne?" Ya d'anyi shuru sannan daga k'arshe yace "Anna ce ta rik'e min matata." Sarki yace "bangane matar da kake nufiba?" Bassam yace "matata ta farko Afnan." Sarki yace "yanzun kana buk'atar ta kenan?" Yarima ya sunkuyar da kai, Sarki yace "ina ita d'aya matar taka?" Yarima yace "ina ganin kamar ansamata hannu, kasanar da jakadiya a nema mata magani." Yarima yace "ranka ya dad'e tashi muje Anna tabani matata." Sarki yace "A'a bari muyi salla mana sai mutafi, zomuje muci abinci suka jera suka nufi wurin cin abinci ga kuyangu sai zagaye sukeyi." Suka baje gaban abinci da aka shirya masu, maimartaba ya kalli Yarima yace "shiyasa nace ka had'a da kwarkwaraye." Bassam yayi dariya sarki Ahmad Mohammad shima yayi dariya." Sarki yace "shikenan tunda bakaso, Amma fa kabani mamaki da ka zab'o wannan abar a matsayin mata, bayan kana da tsaleliyar mace." Ka koyi gadona kuwa Yarima? saboda ni akwaini a kwai son macce kyakkyawa." [3/5, 8:32 PM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *Pls Dan Allah basu biyata prv suna Neman natura masu novel daga farko Dan Allah su daina saboda na riga da nayi nisa* *51* Bayan Sallar la'asar iskan yamma na bugawa a hankali, sarki da Yarima suka jera suna hira gwanin ban sha'awa suka nufi wurin Anna." Fadawa suka ruga suka fad'awa Anna cewa ga sarki nan tafe da kansa ba aikeba." Anna ta mik'e daga kan kujera ta shirya, dama kuma a shirye take, ta zauna a kan kafet." Sarki ya shigo tare da fadawa sai kirari suke mata, yayi masu nuni da su dakata a waje, Sannan yashiga sashin Anna." Kai tsaye kan kujera ya zauna, shima Yarima ya zauna a k'asa gefen Anna." Anna tashiga gaida sarki had'ida jera masa kirari, sarki ya d'aga hannu yana murmushi a lamar ya amsa." Sannan yayi gyaran murya yace "Anna meya had'aki da d'an naki?" Ayi hak'uri a bashi matarsa." Anna ta dubi Bassam daya sunkuyar da kai, a ranta tace "wato k'arata ya kai wurin maimartaba kenan." Tace "ran sarki dad'e ban hanashi matarsa ba, kasan yarinya ce k'arama idan za'a kaita gidan shi ya dace a gyara t....." Sarki ya girgiza kai yace "gaskiya ne Anna." Anna ta dubi Bassam daya kasa had'a ido da ita, tace "ina rok'on Yarima yabamu nan da watanni goma za'a kawo masa ita." Bassam yayi saurin d'aga kansa ya kalli maimartaba. Sukayi ido biyu, sarki yasan manufar sa." Dan Bassam ji yake kamar yayi ihu." Sarki yace "Anna ayi hak'uri a tausayawa d'an naki, wata goma sunyi yawa, a barshi a wata biyu." Bassam yayi sauri ya kalli mahaifinshi, shima kallonsa yake, sukayiwa junansu murmushi, yaji dad'in taimakon da sarki yayi masa, Yafara godiya." Sarki yace "za'ayi k'aya tancen taro ana gobe zata tare saboda mutane su shaida ta." Dad'i yak'ara kama bassam sai murmushi yakeyi." Anna tace "to ranka ya dad'e yanda kazartar haka za'ayi, sai a tara mutane kenan." Sarki yayi murmushi yace "Anna nima baza bari naga Amaryar ba?" Murmushi Anna tayi tace ranka ya dad'e Angama inkana buk'atar ganin d'iyar taka." Sarki yace "ba damuwa a ci gaba da gyarata zamu had'u ranar biki." *********** Labari ya Iske hajiya zainab cewa Yarima aure zaiyi, Kuma matar sace a cikin gidan nan take zaune." Hankalin hajiya zainab yatashi tace "ina bazai yiwoba, sai dai ta kashe Yarima da matar tasa ta huta, ita wannan bala'i ya isheta a kan Yarima ta hana kanta zama lafiya to anzo k'arshe kashe shi kawai yakamata ayi kowa ya huta." Ta aika aka kira mata sarkin gida." Sarkin gida yazo da gudunsa ya zube a gabanta sai huci takeyi tana burzar da iska mai zafi a bakinta." Sarkin gida yashiga ce mata "Allah huci zuciyarki ranki ya dad'e, ki kwantar da hankalinki in dai inada rai da lafiya, bazaki tab'a zama cikin k'unciba." Sannan ta d'an saki fuskarta, ta kalle shi tace "Sarkin gida ka kosan abunda naji kuwa dan gane da Yarima?" Sarkin gida yace "ban katsi numfashinki ba ranki ya dad'e, nasan lbrin Aurensa kikaji zaiyi To ba aure zaiyiba ya dad'e dayi dan matarsa ce ta fari ta dad'e a gidan nan, Hajiya zainab ta mik'e tsaye tace "yaushe hakan tafaru ban saniba?" Tabbas saina d'auki mummunan mataki ga bassam, Ni d'in nan saina ga bayan Bassam kamar yanda naga bayan uwarsa, inyi da uwarshi yace Zaiyi dani?" Sarkin gidan ya jinjina kai yana cewa a ransa kin d'aukowa kanki babban aiki, saboda mungwada yi mashi sammu, amma abun ya gagaremu." Saboda yayi nisa a neman tsari, babu yanda banyi ba amma an kasa yin komai a kansa, shi yasa ko ido kuka had'a sai hanjin cikinka ya motsa Dan gani zakayi damusa kake kallo, Anya ba'a bashi naman zaki yaciba?" A fili kuwa yace "ranki ya dad'e zamuyi k'ok'arin cimma burinmu, ki kwantar da hankalinki ki d'auka cewa Yarima da matarsa dukansu kamar sun bar duniya ne." Ki natsu kisaki kud'i aiki kamar anyi angama ne idan har boka wanzam nada numfashi a doron k'asa, Tace "sarkin gida sanin kanka ne, kud'i batsalata bane indai buk'atata zata biya musamman a kan tsinanan yaron can Bassam, mai taurin ran tsiya." Yace ranki yadad'e zamuyi k'ok'arin cimma burinmu, Allah yaja zamaninki matar da babu irinta a gidan sarki kekad'ai kike juya gidan sarki yanda kikeso." Da alama kirarin da sarkin gida yake mata yana ratsata, ga sanyin AC sai lumshi ido takeyi tana murmushi." Kai jama'a mulki da dad'i da kuma b'ata, Allah yasa mu dace, Amin." Saratu tafito domin tasha iska, saboda a kwanakin nan a cikin d'aki take yini bata fitowa Dan kar a zargi wani Abu tsakaninta da yarima." Ta gifta ta wurin kuyangunta basu lura da itaba, sai gulmar ta sukeyi irin bak'in halinta d'aya daga cikinsu tace "ai ance ma wai aure zaiyi." Tsayawa tayi daga tafiyar da takeyi, taji gabanta na fad'uwa, ta kallesu tace "wa zaiyi aure?" Baki d'ayansu suka juyo, suna ganin itace suka fara inda inda, Tasaka hannayenta a k'ugunta tace "tambayarku nakeyi?" Sukayi tsuru tsuru hankalinsu a tashe." Ta kira d'aya daga cikinsu da alama tafi yimata d'awainiya, kuma ita tafi samun alherinta ko dan sunyi kama ne?" Haka dai kuyangun suke fad'i." Tace "inno." "Naam ranki ya dad'e." Muryarta har rawa takeyi." "Zo nan." Ta matso ta tsugunna hankalinta duk a tashe yake." Tace "ki gaya min abunda kuke fad'i, kinsan ke tawa ce muna d'asawa, ki fad'a min inci masu mutumci tunda su magulmata ne, ki fidda kanki inba hakaba zansa a zaneku duk kuduka." "Ranki ya dad'e muntuba, baki d'ayansu suka zube k'asa, "Ina jinki tana kallon bakin Inno." Inno tace "cikin murya mai nuna tsoro "Dama..munji..ance..uhmm." "Ki gaya min mana! Ta fad'a cikin tsawa da takaicin b'ata mata lokaci da takeyi, "Ance Yarima zaiyi aure." Tayi saurin zabura tace "iyee!! Ta fad'a cike da razana." Ubanwaye yace zaiyi aure?" Wato gulmar da kukeyi kenan munafukai kawai har dake inno?" Inno ta kuma shiga tashin hankali tace "A'a ranki ya dad'e nima Nazo wucewa naji suna fad'i, kiyi hak'uri ranki ya dad'e kiyi hak'uri." Saratu na nishi sama sama cike da bak'in ciki, tace Dan uwarku gulma ta kawoku a gidan nan?" Kuma da kuke cewa Yarima zaiyi aure uwarku zai aura?" Hak'uri dai suka bata, bata kulasuba ta wuce tanufi d'akinta, inno tabi bayanta." "Ranki ya dad'e Allah ya huci zuciyarki. Allah yabaki miji na kwarai daga ke ba wata har duniya ta nad'e." "Ranki ya dad'e Allah yabaki 'ya'ya masu arziki dasuka gaji sarauta." Tsawar da saratu ta dakawa inno shiyasa taja bakinta tayi shuru, had'ida cewa ranki ya dad'e lafiya?" Tuba nakeyi." "Lafiya k'alau ta rik'o hannu inno abunda bata tab'ayi ba, Idonta cike da hawaye tace "inno inaso ki taimaka min kizama ta hannun dama na, kizama mai kula dani duk da nasan baki sona." "Haba ranki ya dad'e wace ni, nace bana sonki duk a gidan nan ke kad'aice baki zageniba, Duk sashin da na zauna sai an zageni an hantareni ana cemin sai muni kamar zunubi." Ajiyar zuciya saratu tayi tana duban fuskar inno tace "ni kaina ina maki wannan kallon ina godewa Allah da irin tawa fuskar, A gaskiya inno ina da sauk'i a kanki, shi yasa nake k'aunar ganinki a kusa dani saboda nasan ko makaho ya shafa yasan nafiki kyau." Amma Dan Allah inno bari in tambayeki, nasan ana zagina ko a ce sai muni ga bak'in hali? Inno tace "waya isa ranki ya dad'e?" Babu Wanda ya isa ni ban ma tab'a sanin kina da rashin kyauba sai yanzun da kika fad'a." *lol saratu kina bani dariya*🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣 [3/5, 8:40 PM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *52* Saratu ta dakawa inno tsawa tace "ya isa Inno!! Inno ta zamura ta kama kanta "Ke 'yar garin nan ce?" Inno tace "eh ranki ya dad'e, Mahaifiyata baiwace tayiwa sarki hidima, saboda haka ta auri mahaifina a matsayinsu na bayi. Shine mu muka amshesu su suna gida basa aiki, sarki ya basu gida a bayan fadarsa." Saratu ta k'ura mata ido tana kallonta tana tuna tata rayuwar." Tana tuna lokacin da take zuwa wurin kakarta jummai, tana samo mata naman rago, da soyayyen kaji, Saboda kwad'ayin naman yasa ta fara sha'awar zama gidan sarki, jummai tak'i yarda da zamanta a gidan Sai data ta rasu sannan ta kwaso kayanta tazo gidan sarkin." Ta iske ana ta hidimar gyaran naman tasanya hannunta anatayi da ita, Haka aka gama gyaran naman nan baki d'aya aka soyeshi wani kuma akayi farfesu dashi, wani kuma gasawa akayi ga kamshi na tashi ko ina amma aka hatana ko tsinke d'aya." Tashiga tunanin mutum yayi aiki amma a hanashi ko d'aya wannan cin zalun yayi yawa." Ai sai tafara tunanin d'auka tunda ba'ada niyar bata, Sai da taga babu kowa kusa." ta kai hannu ta ta d'auki tsokar nama d'aya zata kai a baki kenan, sai ga manya manya masu aikin kicin d'in suka cafke hannunta." Suna tambayarta "ke daga ina?" Ta fara zubar da hawaye." "Kinsan hukuncin b'arawo a gidan nan kuwa?" A'a ta fad'a cikin tashin hankali." "Hannunsu ake yankewa iya nan ta rik'e wuyan hannun saratu mai satar naman." Ai sai saratu ta fara ihu tana fad'in "nashiga uku Dan Allah kuyi hak'uri, aka jawota waje aka jefar kamar kayan wanki, Babu tausayi suka hau kanta suka shiga yimata dukan tsiya harda fasa mata hanci." Kuka takeyi tana cewa "Dan Allah kuyi hak'uri ni jikar jummai ce." Suka tsayar da dukanta jin ta ambaci ita jikar jummai ce, Suka had'a baki sukace kikace ke jikar jummai ce. Ai ya kamata hajiya zainab ta ganki." Suka sanya ta a gaba suka nufi wurin hajiya zainab da ita." Saratu taji dad'i a ranta, yau gata ga hajiya zainab, Kullum tana burin ganinta kusa da hajiya zainab, saboda kayan sanyawarta gwala gwalaine, suna burgeta duk tasan ita bazata sakasuba amma ganin ta kusa dasu zaisanya ta farin ciki." Hajiya zainab ta ya motsa fuska tace "meye wannan?" Kuyangunta suka zube k'asa sukace "ranki ya dad'e wannan jikar jummai ce musan zata amfaneki sosai... "Ranki ya dad'e zatayi aiki sosai bakiga yanayin halittartaba?" Hajiya zainab ta kalle saratu tace wannan ai bata da babbanci da k'aramin doki, Kujaye min ita fuskarta ce banason gani." "Ranki ya dad'e jikar jummai ce zakiso kirama....." "Oh nagane yar gari, to yayi kyau kin kyauta, shiyasa kinfi kowa a cikin..." Ta kalli saratu tace "cin zarafin da kakarki tayi min sai na ramashi a kanki, Dibi idanki sai kace mujiya." "Ai na mujiya ma yafi nata kyau, ranki ya dad'e." "Hajiya zainab tace "kai yarinyar nan Allah yayi maki muni, ko da yake baki yarba kakarki kika biyo, tashi kitafi waje sai nayi tunanin abunda zakiyi min." Daga k'arshe dai ita ke kula da wankin k'afafun hajiya Zainab da yankar mata farce." Musamman har makaranta aka sata ta koyon _manicure_ da _pedicure_ kunsan wata goma tayi sannan ta iya." Hajiya zainab zata d'ora k'afafunta a bayan saratu kamar ta d'orasu a kan tebur, saratu zata duk'a hannunta a k'asa idan ta kuskura ta motsa tasa a zaneta saboda wahala wani lokacin har kashi take saki, kuma a hanata abinci, ba kuma damar ta gudu." Sai gashi cikin shekara hud'u ta aure d'an sarki mai suffar larabawa, duk da muninta da ake kira." Inno ta katse mata tunani da tace "ranki ya dad'e da bazaki damuba, akwai wata magana danake son yi dake." Saratu tace "zoki zauna ki fad'a min ai yanzun munzama d'aya." "To ranki ya dad'e dad'i ya kama inno, tana zaune a k'asa ita kuma tana kan kujerar mulkinta." "Ina saurarenki inno." "Cewa nayi dama akwai wata mata da nasani tana zuwa fada gun wasa da Aljanu..." Saratu ta zaro ido😳tace " ina saurarenki." "Da zaki yarda inkawo maki ita tayi maki binciken abunda ke faruwa ranki ya dad'e." "Bin cike kuma?" "Eh." "Aini ban yarda da bincike ba." "Amma bakison sanin abunda maigirma Yarima yasonyin ne?." "Banaso inno bari wannan zancen Yarima bazaiyi aure yanzun ba." "Ai aure an d'aura ranki ya dad'e sai dai hak'uri." "Iyee!! Ta mik'e tsaye ba shiri." A ina kikaji?" Inno tace "ranki ya dad'e ki dai k'ara tunani a kai na barki lafiya." ************* Bayan kwana uku, Bassam na son ganin Afnan kamar yayi hauka, amma Anna ta hanashi idan yatafi sashin nasu har yagaji da zamanshi bazai sanya Afnan a ido ba, abun yana damunsa matuk'a." Afnan kuma da Anna tabata labarin a sanya ranar ko mawarta gidan yarima nan da wata biyu masu zuwa, kuka ta tsirawa Anna tana fad'a mata irin wahalar da yayi ta gana mata." "Anna tace "Ada kenan amma banda yanzun domin a halin yanzun na lura da Yarima babu wacce yake so sama dake, Ina ganin soyayyarki mai tsanani a cikin idon yarima wadda ida ya rasaki komai zai iya faruwa dashi." Afnan kiyi kiyi hak'uri ki sanya soyayyar Yarima a ranki, na tabbata da kindace da mijin, Yarima bazai tab'a cutar dake ba a yanzu, Kisani ke marainiya ce shima marayane Ku rungumi junanku Ku kula da junanku cikin so da k'auna." Babu abunda Afnan takeyi sai zubar da hawaye, magagganun Anna nayi mata yawo a kai." *********** Yarima duk Abun duniya ya dameshi yanaji yana gani dashi da matar shi Amma Anna tayi masu katan gar k'arfe, Ya yanke shawarar tafiya England bazai dawoba sai ana saura sati d'aya ko mawar Afnan gidansa." Haka kuwa akayi yafad'awa maimartaba maganar tafiyarsa England yace "yana so yaje ya dubo wasu takardunsa. Sarki ya Amince. Bassam yaji dad'i sosai. Washe gari ya hau jirgi yayi tafiyar sa batare da kowa yasani ba a gidan, harda saratu." ************** Alhaji Aminu a gaban maimartaba suna fira, suna dariya, gaba d'aya sarki ya bashi amana ya yarda dashi jiyakeyi komai yana iya fad'a mashi domin babban Amininshi ne na Amana." Tun farkon shigowar Alhaji Aminu fadawa sukayiwa, Yarima waya suga shaida masa gashi nan yazo." Yarima yace "kusanya ido akansa sosai karku bari ya lura da hakan daga gareku." Suka ce angama ranka ya dad'e." *************** Saratu ta duba sama da k'asa, Gabas da yamma bata ga mijinta ba, duk Wanda ta tambaya a cikin fadawansa sai dai suce mata basu San inda yatafiba, yau sati d'aya kenan." Abun ya dameta har ya kai bata iya cin abinci, har tafara ramewa." yau kuma ta yanke shawarar tafiya fada Domin ta sanar da maimartaba abunda ke faruwa, wata k'ila yasan inda yarima ya tafi ya fad'amata ko zata samu natsuwa a ranta." Tana Gafda da shiga fada, yayi dai dai da fitowar Alhaji Aminu, sukaci karo da juna." Kallon kallon suka shiga yiwa juna cike da mamaki, Alhaji Aminu yarik'e baki yace "Sarah baby Ashe kina duniyar nan, me kuma ya kawoki gidan sarauta?" Hannu ta d'ora a bakinta da alamar yayi shuru." ta duba gabanta da bayanta bata ga kowa ba, tayi masa nuni da yazo sutafi, sai suyi maganar." Kai tsaye d'akinta ta nufa dashi, shi kuma sai sakin baki yakeyi yana dariya." A kan makeken gadonta tayi masa nuni da yaje ya zauna." Sai da ya gama k'arewa d'akin kallo cike da mamaki yaje ya zauna, da tambayoyi d'auke a bakinsa." Yace " sarah baby ya akayi hakan?" Meya kawoki gidan sarauta?" Kina nan da kwad'ayinki Ashe baki daina ba." Kai amma fa kinyi kyau, har naji kintayar min da kwad'ayinki na shekara da shekaru." Dariya ta saki mai Sauti, tace Alhaji Aminu kenan kana nan da jarabarka baka daina ba, kaima?" To bari na amsa maka tambayoyinka kamin muje wata duniyar domin nima kaina nayi missing d'inka tun rabuwata da kai a kano ba'a tab'ayi min sau takwas ba, amma nasan yau zan sha dad'i." *ikon Allah*🤔🤔🤔 [3/5, 8:50 PM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *53* Na farko dai ni 'yar cikin gidan nan ce, Yarima nake aure d'an sarki, wanda sarki keji dashi, kamar k'urjin tsakar kai." Alhaji Aminu ya zaro ido waje, cike da mamaki yace "yanzun kece matar wannan yaron mai suffar damisa, Amma dai nayi mamaki saratu. To mezaiyi dake?" Ta zaro ido waje cike da tsiwa tace "Alhaji Aminu ka iya bakinka karka manta akan gadona kake." Yayi saurin rufe bakinsa had'ida da mik'ewa tsaye yace "saratu nayi nan, dan karya dawo ya tarar dani nan nasan hukuncina a wurin sa kasheni kawai zaiyi." Saratu tasaki dariya tace "matsoraci to ai ina ganin baya k'asar gaba d'aya yau sati d'aya kenan da tafiyarsa." Dariya Alhaji Aminu yayi yace "tsoro gaskiya ne, musamman a wurin wannan yaron a duk lokacin da mukayi ido biyu dashi sai gabana ya fad'i bansan daliliba." Saratu tace "dalili saboda ka sanyawa rayuwarka tsoransa, kuma yarima mutum ne kamar kowa." Nan tashiga cire kayan jikinta sai da ta koma ziddir sanna ta nufo Alhaji Aminu dake zaune yana kallonta sai had'iyar miyau yakeyi." Tashiga cire masa kaya da kanta, sai da ta tub'eshi ta mayar dashi ziddir zannan ta haiye kansa." Anan suka shiga shafar juna suna luddun junansu sannan Alhaji Aminu ya mirginata ya haye kanta, ya saita 🍌 ya sanya mata." wani irin ihu, tasaki yayi saurin kwad'a mata mari a fuska, had'ida rufe mata baki, da filo yaci gaba da aikinsa." Ranar dai sai da sukayi sau takwas. da zarar ya sauka ya huta ya kuma k'ara komawa, daga k'arshe Alhaji Aminu a nan ya kwana suna abu guda." Tun daga lokacin da zarar taji jarabarta zata yiwa Alhaji Aminu waya yazo daga b'oye, su shige d'akinta suyita aikata masha." ************** Yau Bassam ya dawo Nigeria, da murnarsa domin kuwa saura sati d'aya Afnan tazama mallakinsa." Sai yanda yayi da abarsa ba tare da sa'idon Anna ba." Kishingid'e yake a tsakar falonsa ga tum tum baje a ko ina masu laushi da dad'in k'amshi, ga inibi yana ci yana kuma kallon jarida yana karatu." Yaji shigowar da akayi bai damu da ya kalli mai shigowar ba ya San saratu ce, Warin da ya bugi hancinsa shi yasa ya d'ago ya dubeta." Fuskarta cike da fara'a ta zube a gabansa tana gaisuwa shima yana d'an sakin fuska ya amsa mata a ransa yana cewa "ina ma Afnan d'ita CE...." "Ranka ya dad'e ya gajiyar hanya?" "Alhmdulillah." Ta zauna ta tsora masa ido tana kallonsa ita dai tana mutuwar son yarima, komai tana iya aikatawa akan yarima." Tace "ranka ya dad'e kayi min kyau sosai." Dariya mai sauti yayi yace "kema kinyi kyau sosai matar yarima." Murmushin jin dad'i tayi, tace "nagode." Bai kuma kallonta ba yace "jakadiya tayi maki maganar da ya dace kuyi?" Tana masa kallon rashin fahimtar abunda yake nufi." Ajiyar zuciya yayi ya mik'e zaune ya gyara zamansa sosai yace "akwai lalurar dake damunki kuma ba laifinki bane, ki dage da shan maganin tsarin da nace a nema maki." Dama abunda ke ranta kenan, yarima ya sosa mata inda ke mata k'aik'ayi, hawaye ta shiga xubarwa, tasan hakan zai faru tunda taga Bassam ya k'aura CE mata lokaci guda." Yarima yace "kiyi tunanin abunda aka baki saboda abunda ke damunki sammu ne, k'ila sha kikayi." Kallon da tayi masa ya gano ta tuna wani abun, sai tak'ara fashewa da kuka sasai." Tace "tabbas hajiya zainab tabani magani tace "zai taimaka min insamu ciki da wuri." A take b'acin rai yashige shi, tsanar hajiya zainab ta k'aru tare dashi, Ya zaiyi da matar nan wai?" Yana sane da duk abunda take aikatawa a gidan nan, yana raga mata ne saboda mahaifinshi, Yasan idan ya rabasu bai kyauta ba." Maimartaba ya manyata yana buk'atar hutu yanxun dole ya kula dashi baya son sashi b'acin rai kwata kwata baya son ya rasa shi, yana sonshi fiye da komai, Ba zai biye mata ba suka kasheshi, saboda shi kad'ai ya rage masa shine gatansa." Wannan dalilin ne yasa yake ragawa hajiya zainab duk abunda takeyi yakeyin kamar baisaniba." Ya kalli saratu yace "waya baki shawarar zuwa wurin hajiya zainab?" Ke kinsan babu Wanda take k'i kamar ke, balle yanzun da kike aure na, abun ya zama goma gareki." Meyasa baki gaya min kina son haihuwa ba?" Sai in nemo likita a duba mu gaba d'aya." Kukanta ya k'aru tace "dama shiyasa kake son k'ara aure saboda lalura ta?" Ya dubeta da kyau yace "saratu ina da aure a kaina tun kafin in aureki...." Ta zaro ido😳 cike da mamaki, Na b'oyeta ne a gidan nan ban bayyanata ba saboda wasu dalillai." Sannan itace wannan yarinyar mai kyau danace maki ita baiwa ce." "Naam ta fad'a da sauri, abun ne taji kamar ba da kyau ba." Ya maimaita mata "Afnan itace yarinyar danake aure kuma nace tazama baiwarki." Ta d'ora hannu a kai tace "nashiga uku🙆 Yace "saboda me?" "Saboda tafini kyau ranka ya dad'e." "Ashe tasan batada kyau,😊?" Da tafi ki kyau kuma na zab'oki da kaina na aureki." Ai bata San lokacin da tasaki ajiyar zuciya ba, duk dad'i ya kamata duk sai tajita _on top of the world_ "Anyi haka ranka ya dad'e kaine ka nemoni." Ya lura da farin cikin dake tare da ita, Yace "kiyiwa jakadiya magana kiji abunda zata ce, na fad'a mata ta bincika abunda ake ciki." Ta washe k'aton bakin gaba d'aya. Ta kafeshi da ido tana kallon fuskarsa wadda ta cika da gashi a gyare take gemunsa bak'i ne wulak, gashi sunyi kwance kamar abunda ruwa ya tab'a, haka na kansa gashi a kwance kamar yasa hula, da ace shi mace ne da sai yayi yawan gashi." Ajiyar zuciya yayi ya katse mata tunaninta yace "ki kiyaye abubuwan da ke faruwa ki k'aucewa hajiya zainab tana iya yi maki komai saboda ni." Tace "insha Allahu ranka ya dad'e." **************** A Daren ranar saratu batayi barci ba tunani ta shigayi, tana sak'awa tana kwance, "Anya zata zauna ta dinga ganin Afnan a matsayin uwargida?" Wato duk nisantata da takeyi kada yarima ya ganta a banza tayi shi." Meye dalilin da yasa ya b'oye matar sa, bai bayyata ba, sai yanzun yake son fito da ita? Kodai yanaso yabata wani matsayi ne, a gaban jama'a Ita yana ganin munin yayi mata yawa bazai iya nuna ta a gaban jama'a ba." Wata k'ila dana sanin aurenta yakeyi a yanzun." Tunanin mafita kawai takeyi, Ya dace a ce yanzun tana d'auke da cikin yarima, kada Aljanar yarinyar can tazo tafara haifawa yarima 'ya'ya maza ita tana zaune." Washe gari ta aika aka kira mata inno, ta zauna a gefenta." Ta kalli inno tace "matar nan da kikayimin magana kin tabbata bata da alak'a da hajiya zainab?" "Eh ranki ya dad'e, matar bata shiri da Hajiya zainab kwata kwata." "To shi kenan babu damuwa kije kizo min da ita yanzun." "To ranki ya dad'e an gama." Saratu tayi shuru tana sauraren wani abu mai kama da Almara, wai an b'ata mata mahaifa." Hawaye masu d'umi suka Shiga ambaliya a fuskarta." Bokanya jibo tace "a kwai lokacin da kika shiga cikin wani yanayi na azababben ciyon ciki da kuma zubar da jini cikin k'ank'anin lokaci ciwo ya d'auke." "Tabbas anyi haka tana gama shan maganin da hajiya zainab ta bata ne abun ya faru." Kuka tasaki wiwi har da buga hannunta a kan kujerar mulkinta." "Hajiya zainab ta d'auke mata jin dad'in rayuwa kenan, ta b'ata mata ma haifa, kuma tayi mata asiri bata iya zuwa kusa da mijinta, ashe yau dararta tayi?" Tayi Alk'awarin d'aukar fansa, ta lura a duniyar nan babu Wanda takeso kamar Yazeed, Zatayi sanadinsa sai tasan zafin yau darar da tayi Mata." Ta dubi jabo tace "kina iya kisa?" "Kisa ranki ya dad'e?" Wannan ba aiki na bane sai dai na tura masa da sammu." Zai zamo dashi da babu duk d'aya?" Inno tace "haka ne ranki ya dad'e ki yarda a dasa mata bak'in cikin da baya gushewa har ta mutu tanaji tana gani amma ba yarda zatayi." Kukan da saratu takeyi ta daina." Tace shikenan yanzun takaini ta baro yarinyar can ita zata haifi 'ya'ya bandani." "Ranki ya dad'e ki kwantar da hankalinki, ai kema ramawa zakiyi, mulki ya gaji haka, dole sai an zubar da jini sannan sai an d'auki mataki kwankwara sai ancima buri." Saratu tace duk abunda mukeyi a tsaka ninmu ya zama sirri." "Angama ranki ya dade." Jibo yanZun warin da suka saka min ya za'ayi dashi?" Ganin tulu tayi jibo ta d'auko. Tsoro ya kama saratu." Jibo tace "asirin da sukayi maki ne, ranki ya dad'e cikin rijiya suka jefashi, Za'a zuba ruwa a cikin tulun nan ki mayar dashi ruwan shanki insha Allah zaki warke." Ganin hakan sai ta wangale baki, cike da jin dad'i." Saratu tace "zaki iya damk'a min yarima a hannuna sai yanda nayi dashi." Jibo tayi shuru ta kasa magana, saboda abun da kamar wuya." Tace ranki ya dad'e bari mu gama da aikin da kika ce a fara a kan Yazeed d'an hajiya zainab." Haka ne taji dad'i a ranta, Bata da wani buri a yanzun sai ganin bayan hajiya zainab, tunda tayi mata lahani ta rasa mahaifar da zata haifawa yarima d'a Wanda zai gaji sarauta a gaba." Ta fad'i da k'arfi tace hajiya zainab bakisan ko wacece saratu ba sai kinyi nadamar abunda kika aikata min." ****************** Saratu ke tafiya cike da k'asaita zata nufi sashin hajiya Zainab, Alhaji Aminu ya kira wayarta yake CE mata "ya yaji shuru kwana biyu bata nemeshi ba, kuma bayan ta d'and'ana masa." Cewa tayi "Alhaji Aminu ka d'an saurara min kwana biyu domin kuwa yanzun yarima ya dawo, Koni kaina ina kewarka da yawa, yanzun haka wayar da mukeyi da kai duk ka d'aga min hankali najini cikin wani yanayi wanda a yanzun haka duk najik'e pant d'ina." Alhaji Aminu yasaki wata dariya ta yaudara har da wani Jan iska a bakinsa a kunnenta, kamar Wanda yaci yaji, sai gaba d'aya hankalin saratu ya tashi sai da tanemi wuri ta zauna kusan minti Biyar ta samu natsuwa sannan ta mik'e taci gaba da tafiya ta nufi wurin hajiya zainab." Kai tsaye tashiga d'akin hajiya zainab batare da sallama ba. Ta Tarar da hajiya zainab zaune a kan kujerar mulkinta, Kai tsaye gefen kujerar da hajiya zainab take zaune ta tafi ta zauna. Tare da d'ora k'afa d'aya kan d'aya." Saratu ta gaida hajiya zainab, Cike da mamaki hajiya zainab ke kallonta, tashiga tunanin wata k'ila tasamu lafiyar jikinta Dan haka take d'agawa da lafiyarta." Kenan ta gano ita tayi mata asiri kenan?" Hajiya zainab tacewa saratu "lafiya." Saratu tace "lafiya ta wuce haka mekike son gani?" Maganar ta bata haushi, amma tace mata "har yanzun cikin baisamu ba?" Saratu tayi murmushin ta kaici tace "ai ciki lokaci gareshi." Hajiya zainab tace "naji ance yarima aure zaiyi?" Murmushi saratu ya kau ranta ya kuma b'aci tace " ta dubi hajiya zainab cikin ido tace "tazo mana ai yanada damar yin haka tunda har kwarori yana iya ajiyewa, Kuma ni bazan juya masu mahaifa ba Dan karsu haihu da yarima." Hajiya zainab ta har zuk'a tace "magana zaki fad'a min?" Na d'auka kinxo ne Dan musan shirin da zamuyiwa kishiyarki Dan naji ance kyaunta tamkar...." Ki kwantar da hankali in taimakeki." [3/5, 9:33 PM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *54* Dariyar da saratu keyi ne, shi ya dakatar da hajiya zainab da zancan ta." "Kina nufin wurinki zan nemi taimako?" Lallai ma kuwa to kicanza tunani, Auren yarima kuma da auren sa ya aure ni ko baki da labari ne hajiya zainab?" Hakan ya nemoni bani na nemoshi ba, ya aure ni saboda da so da k'aunar da yake Mani." Mik'ewar da hajiya zainab tayi shiyasa Saratu tayi shuru tana hararar ta." Itama saratu ta mik'e tsaye sukayi gaba da gaba, saratu tace " har kingaji da jin maganata, to ni zan wuce, Maganata ta k'arshe dake itace ki kula da *zuciyarki*." Sannan saratu ta fito a fusace." Hajiya zainab ranta yayi bak'ik'irin kamar bak'in leda. Tashiga tunanin kalaman da saratu ta fad'a mata. Bare kalmarta ta k'arshe *kikula da zuciyar ki* me take nufi zatayi?" Da sauri tasa aka kira mata sarkin gida. Yashigo da sauri ya zube." "Ranki ya dad'e gani." Saratu tazo sashin nan yanzun, tayi min wulak'anci har da yimin gatse!! wai in kula da zuciyata. Me take nufi da hakan?" "Ranki ya dad'e ba komai so take ta gaya maki kifita a harkarta, saboda ranki zaita b'aci da irin matsayin da zaita k'arayi." "Oh shi yasa naganta cikin k'asaita ga komai warwas, lallai ina ganin ta fara samun lafiya." "Zan tarwatsa ta, zan ganar da ita ni ba abunkiyar yinta bace, Yarinya k'arama ta neme gasa min gyad'a a hannu." Me ya kamata inyi yanzun?" Dawa take ma'amala yanzun Dan na lura tasan komai a kanmu, naga tafara ji da kanta, inason musguna mata...." "Ranki ya dad'e ki natsu. Da kyau kadda saratu ta tayar maki da hankali ita d'in banza." Yau d'in nan ba sai ankwana ba muna iya sanyawa tabar duniyar gaba d'aya." Hajiya zainab ranta yayi fari tasaki dariya mai sauti." **************** Anna tashigo da k'ofi a hannunta, ta mik'awa Afnan tace ongo karb'i ki shanye." Afnan ta k'arb'a tana turo baki, alamar shagwab'a ta shanye, Anna ta kuma zube wani garin magani cikin k'ofi ta d'auko Zuma da Lipton ta zuba ruwan zafi, ta girgije ta kuma mik'a mata, Shanye wannan yanzun." Ta k'arb'a ta rik'e tak'i kaiwa bakinta. "Anna ki barni yau in huta dan Allah." "Hutu." Inkikaga kin huta to sainaga an kaiki kinsamu ciki." Afnan ta turo baki tace a ranta "ni Anna ba wannan ya dameniba yarima baya sona." Anna tace "sha mana tawan, kinsan inaji dake Afnan ina maki sha'awar yarima." nan da nan taji son yarima da k'aunar shi tare da ita, batasan lokacin da tafara sonshi ba." Ta tuna da ranar farko da tafara ganinshi. Bata tab'a jin tsoro wani mutum ba sai a kanshi." Afnan na kusa da Anna gyarata akeyi kullum saita sha maganin tsari irin Wanda take bawa yarima. Duk muguntar mutum sai dai ya buga ya barsu." Afnan kullum tunanin Bassam takeyi, tun lokacin da aka sanya masu rana bata sake ganinsa ba har yanzun da yarage saura sati d'aya a kaita." Tana yawan tunawa da irin salon soyayyarsa, Lokacin da yasamesu lambu ita da sadi." Sadi na yawan tambayarta wai meye tsakaninsu da yarima, sai dai tayi masa dariya tace bakomai." Tayi murmushi da ta tuna lokacin da ta fad'awa Sadi zata tare a gidan yarima a matsayin matar sa." Yayi fushi sosai, yace "ke dai Aminiya fushi nakeyi dake, Duk tsawon lokacin da muke tare kink'i fad'a min yarima mijinki ne, Yanda naga yarima yana shige maki nayi tunanin sonki yakeyi har nafara jimaki dad'i. Ashe mijinki ne gaba d'aya." Tace "yi hak'uri Amini labarin yana da tsayi. Kabari sai mungama hidiba zan gaya maka komai." Sai a lokacin yayi dariya yace "na hakura Aminiya, ya shirye shiryen biki kinsan gobe ne za'ayi dinner *Ranar dinner* an shirya a lokacin Bassam kasa b'oye farin cikinsa yayi, duk Wanda yaganshi yasan yana cikin farin ciki Wanda ba'a tab'a ganinsa a fuskarshi ba." Abokanan shi da sukayi karatu a England duk sun hallara duk wani aboki nashi ko wani Amininsa ya gaiyatosa domin su shaida Afnan a matsayin matarshi." Haka maimartaba, ya gayyato yan uwa da abokanan arziki." Amarya Afnan ansha gyara sai wani shege takeyi, kusan wata d'aya ana gyarata. Sai da Anna tace "kar ayi mata halawa saboda yanayin fatar ta." Taci ado cikin wani material pink and blue, doguwar riga, sai wani gyalli yake fitarwa, gaba d'aya jikinta gwala gwalai ne aka yimata ado dasu." Duk Wanda yaga Afnan a wannan lokacin bazai ganeta ba. Saboda tayi kyau har ta gaji." Anna sai yaba kyaun 'yarta takeyi tana zuba mata kirari." Bassam shima ya shirya tare da abokanansa yasanya wata dakakkiyar shidda blue ya sanya hula pink da takalmi da agogo, Kuzo kuga bassam yanda yayi kyau kunsan dama kyakkyawa ne." A cikin gidan sarautar maimartaba ya shirya masu dinner, kowa ya hallara Amarya da Ango kawai ake jira." A can na hango Bassam rungume da Afnan suna k'arasowa, gaba d'aya kallon ya koma kansu. Yan jarida da yan sa ido kowa sai d'aukarsu photo akeyi." Wurin zamansu suka nufa na Alfarma suka zauna, ko wannensu zuciyarshi cike da farin ciki. Maimartaba dake zaune gefe d'aya akan kujerarsa ta mulki tare da abokanansa sarakuna, kowa sai yaba zab'en yarima yakeyi, maimartaba yaji dad'i sosai." Hajiya zainab bata tab'a ganin Afnan ba amma dai tanajin labarin irin kyawonta, Sai yanzun da tayi ido biyu da ita, sai da gabanta ya fad'i saboda yanda take hasashenta ba haka ta gantaba." Wani bak'in ciki ya taso mata, Ta mik'e da sauri ta bar wurin domin bazata kuma k'ara kallontaba, Tabbas akwai Jan aiki gabanta, Idan tayi wasa wannan matar yarima sai ta amshe mata kujerar ta ta sarauniya a gidan nan." Tashiga kwad'awa sarkin gida kira." ********* Saratu kuma babu abunda takeyi sai aikin kuka, Inno na kusa da ita tana bata hak'uri, Inno tace "ranki ya dad'e kitashi ki shirya ki d'au kwanliya nasan babu abunda matar yarima zata nuna maki." Haka kuwa akayi saratu ta shirya takira mai kwalliya tayi mata, tare da yan rakiyarta suka nufi wurin dinner." Tana zuwa wurin tayi ido biyu da yarima da Afnan zaune fuskokinsu cike da farin ciki suna kallon wasan gishiri da maimartaba yasanya aka shirya kamin a fara gudanar da dinner din." Saratu na ganin Afnan batasan lokacin da hawaye ya fara zuba a idontaba Juyowar da Bassam zaiyi sukayi ido biyu da ita, ta juya da sauri ta bar wurin idonta sai zubar hawaye sukeyi." Afnan ta lura da inda yake kallo taji kishi ya kamata, Ta rik'o hannunshi ta matse da karfi, sai da yad'an runtse idonsa, yana kallonta, cikin magana kasa kasa yace menayi kuma?" Bata kulashi ba saima hararasa data warga masa, wadda ta k'ara mata kyau." Yayi murmushi, yace "ayi hak'uri amarya yarima tuba nakeyi idan laifi nayi." Bata kulashi ba, ta kawar da kanta gefe." Yasan kishine ke damunta, saima yaji dad'i a zuciyarsa yace " a she tana sona." Anci Ansha an zubar da naira biki na d'angata." Yarima bassam A can na hango yan group din ummu safwan hausa novels Dana Tambarin sarauta friends Sai wasar baki sukeyi suna so suje suyi sulfie da Afnan amma fadawa sun hanasu k'arasawa wurin, Nida ke kusa da Afnan ina d'auko rahoto sai gwalo nake masu😜 A can na hangosu sunyi group wuri d'aya asanya shinkafa a tsakiya da naman kaji saici sukeyi suna dariya. Su ooo da ooo d'an kwalin kansu da gyalen jikinsu duk sun cire basu saniba." 🤣🤣🤣🤣🤣 [3/6, 8:11 AM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *55* Amarya Afnan gobe dai za'a kaita gidan Bassam gyara kam tashashi a wurin Anna." Maimartaba yaturo a kira masa Anna, Bata b'ata lokaci ba ta isa wurin maimartaba." Yana fada zaune tare da manyan bak'insa. Yana ganin tafowar Anna ya mik'e yanufi wani babban falo." Anna na ganin hakan tabi bayanshi domin tasan zancanda zasuyi ba k'arami bane, kuma yana da muhimmaci." Ta zube tana gaida sarki, ya saki fara'a sosai." Sannan yace "ina d'an naki?" Tace "yana lafiya ranka ya dad'e." "Kinsanfa yarima nakine zurfin ciki yake min bansan gabansa ba ban kuma san bayansa ba." Natsuwar sa da hankalinsa a kullum ina maki godiya domin kece kika d'ora shi a kan tarbiya mai kyau." Babu abunda zan saka maki dashi Anna sai dai intayi maki godiya da addu'ar har zuwa ranar da zanbar duniya." "Nadamu kwarai da rashin haihuwar da baiyi ba har yanzun." Matarsa tayi shekaru biyu amma yanzun shuru bata haihuba." Yarinyar nan Afnan ta kwanta min a rai kamar yadda naga kema ta kwanta maki." Tun lokacin da aka kawota a gidan nan ina sane dashi ya banzartar da ita baya kulata, bansan manufarsa akantaba, bana so yaje ya cutar da ita, Na lura yarinyar nan tana da wauta sosai Ina Neman Alfarma a wurinki. Ki taimaka da taimakon da kika saba kibita can sashinta Ku zauna har ta saba da gurin." Kuma kisamin ido da abubuwan da ke faruwa saboda take taken hajiya zainab ya fara bani tsoro." Anna dai shuru tayi duk halayyar Bassam da ya zayyana mata itama abun na damunta, Amma hakan da ya yanke yayi mata dad'i, saboda ita ma tana son sanin abunda ake ciki." Zatayi k'ok'arin Kare Afnan daga shairin hajiya zainab, tana jin haushinta yanzun kuma lokaci yayi da zata dakatar da ita daga mugun nufinta, Shiyasa ta duk'ufa wurin bawa Afnan maganin kariya Wanda take bawa yarima." Sun rabu da sarki a kan zasuyi abun cikin sirri dama jiran hakan Anna takeyi tashiga fadar sarki da hujja maik'arfi." ***************** Yarima ya kira sadi yace "ya gaya masa matar da yake so ya aura." Rufe idonsa🙈 yayi wai yaji kunya Bassam yaja dogon tsaki "mts!! Ka gani bana son sakarci, ka fad'a min gobe zan sa a d'aura maku Ku dukanku, ko ba ka so?" Ya rik'e hannayensa wuri d'aya tare da nuna murna da ya bayyana a fuskarsa. Yace "ranka ya dad'e mairo da talatu sunake so." Yarima yace " kuyangun Afnan?" "Eh ranka ya dad'e." "To angama gobe zasu zama naka, sai dai inaso ka shirya yanda zasu rik'a zuwa wurin Afnan kullum." "Angama ranka ya dad'e godiya nakeyi." Yarima yace "kadai canza hali mata ba'a sake masu fuska sai su neme hallakaka." A'a nikam wasa zamu rik'a yi muna rawadasu, ina zan iya rayuwa ina had'e sai kace su ba mutane bane." Bassam yaja dogon tsaki yace shikenan matsalata da kai baka ganewa." Abunda nakeso da kai karka yarda ka mayar da sashin Afnan daddalin hirarka, idan hira kakeso kazo muyi, Dan bazan dauki iskancinka ba." "Dariya Sadi yayi yace "ai kagama mai wuyar tunda kabani abunda nakeso." *Washe gari anshirya k'ayataccen biki tarewar Afnan gidan yarima a ranar kowa ya tabbatar yanzun yarima yayi auren kyau, Ansan manya da auren mata masu kyau, Musamman ake shiga gari neman zuri'a masu kyau, domin. A zo a bawa sarki labari aje kuma a auresu." Amma abun mmki Dan sarki ya auri macce mai suffar biri🐒 Talatu da mairo an d'aura masu aure da Sadi, kowa yana cikin murna da farin ciki." Anshirya Afnan cikin lace ne ko material ne baza gane ba. Purple ne da peach ta sha kwallita mai kyau. Ita kanta data ganta a madubi sai da taji tsoro, saboda bata gane kantaba." Kyanta yayi yawa." Anna sai nasiha take mata na yanda zata zauna a gidan mijinta lafiya. Taci gaba da nuna mata yanda zata tarbi yarima idan yashigo da bincin sa da duk wani abu da tasan hak'k'ine a kan mata tayiwa mijinta, mussam yarima da bakasanin gaban sa bare bayansa." Kuka takeyi sosai ta rik'e Anna, Anna tace ki daina kuka Afnan zan sameki a can domin a tare zamu zauna." Babu abunda yake damun Afnan sai kishin saratu, idan ta tuna da yanda taga yarima a wurin dinner ya tsurawa saratu ido, sai ta dinga jin wani zafi a ranta." Cikin wannan tsananin damuwar ne aka d'auki Afnan aka kaita sashin yarima." Gabaki d'aya taga ancanza alatun tsarin wurin. Can k'urya aka kaita aka zaunar da ita kan kilishin da ke shimfid'e k'asa ga tuntu zube a gurin masu laushi, kamshi kawai ke tashi." Taji lokacin da Anna tace "wai ina yarima?" Aka ce yana tare da saratu.' Ta d'aga murya tace "agaya masa Amarya ta iso." Wani bak'in kishi da haushi yarima ya kama Afnan." Duk k'ok'arinta da tayi Dan kada tayi kuka abun ya gagara hawaye suka zubo mata sharrr a kan fuskarta. Babu Wanda yagani saboda jikinta a yafe yake babu Inda ake ganin fatarta." [3/6, 8:19 AM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *56* Yarima a d'akin saratu, sai lallashin ta yakeyi, yana nuna mata da cewa ta kwatar da hankalinta bazai tab'a wulak'an tataba." Babu abunda takeyi sai aikin kuka." Tana kuma marairacewa a jikinsa, Wanda jinginawar da tayi a jikinsa, jinshi yakeyi kamar an d'ora masa wani k'aton dutse jiki." Ganin bata da niyar hak'ura yasan yashi zame jikinsa daga gareta. Ya mik'e tsaye, yace mata sai da safe, idan kingama kukan kiyi Addu'a ki kwanta, bai kuma bi takantaba yayi fitowar shi." Karo yaci da bayi wad'anda Anna ta aikosu kirashi." Sukayi saurin zubewa k'asa, suna fad'a mashi sak'on Anna." Murmushi yayi yace "ina Anna take?" Suka had'a baki sukace tana tare da gimbiya ranka ya dad'e." Bai kuma yin magana ba ya wuce su a ransa yana fad'in "Anna da ita za'ayi zaman d'akin kenan tunda ankawo 'yarta, saboda dan kar na cuceta." Ya kuma yin murmushi yace "Anna bakisan yanda nakejin Afnan a raina bane, da bazaki tab'a tunanin zan cutar da itaba." Afnan kuma batasan lokacin da kowa ya watseba, Jin gurin tayi shiru ta yaye rufin da akayi mata, ta mik'e tsaye. taci gaba da k'arewa d'akin kallon ganin komai ya canza mata." Hotunansu dana yarima take kallo d'aya bayan d'aya, duk da a lokacin biki akayi su." Can ta hango wani hoton a d'an k'aramin frame daga gani mahaifiyar Bassam ce." Ta kai hannunta ta shafe hoton tare da d'auka ta rik'e a hannunta, suna kama da mahaifiyarsa, taji ina ma tana raye?" Aida tazama _complete_ amma yanxun ita bata da uwa shi bai da ita, su dukansu duk marayune." Sun san zafin rashin uwa su biyu, Hawaye masu d'umi suka zubo mata, Jin motsin mutum a bayanta yasa ta firgita har hoton ya fad'i daga hannunta tas! Kakeji." Tayi saurin d'aga kanta taga yarima ne ya shigo." Da sauri ya isa gabanta tana tsugunne tana kwasar kwaba da ta fashe, hankalinta duk ya tashi cewa takeyi "dan Allah kayi hak'uri, nayi maka banna Dan Allah kayi hak'uri." Rik'o hannunta yayi da taji ciwo har jini ke fita, har ya fara d'iga k'asa." Ganin jinin a hannunta yasa ta rik'e hannunta ta fashe da kuka." Tana fad'in "wayyo hannuna, cikin sigar shagwab'a da tsoro." Cikin tashin hankali yarima yayo kanta yana fad'in ingani hannun yana k'ok'arin kama hannunta." Tayi saurin yin baya tace "ni karabu dani." Yayi saurin nufarta tana ja baya tana fad'in "ba sai ga ganiba zai warke ba sai kasa min maganiba." Anan ya gano tsoron magani takeyi, Yayi saurin nufarta ya rungumeta ya kamo hannun yana dibawa, Yana sanye da shadda ruwan madara tasha aiki, gaba d'aya gaban rigar duk ya b'aci da jini." Ai saita k'ara sakin kuka, ta runtse idonta." Cikin kuka da shagwab'a take tambayarsa, tace "ciwon babba ne?" Ya kalleta cike da burgewa yace "Tambaya ta kikeyi?" Ta kuma fashewa da kuka tace "wayyo na shiga uku, nidai kabarni naje wurin Anna tabani magani." Ta kwace daga jikinsa ta mik'i hanyar barin d'akin a zuciyarsa yake cewa "wautar Afnan da yawa take." Kafin ta kai k'ofa ya rik'o hannunta, ya kuma rik'o ya tsanta mai ciwo yana kallo yana yuyawa." Yace "kin cika samaka kanki tsoro, bawani ciwo bane amma jini ya fito." Kwalbar ra tsireki ne shi yasa jinin ke fita amma bawani ciwo a gurin." duba kigani yanda duk kika b'ata min jiki da jini." Yasanya auduga ya goge mata jinin Dama tana cike da jin haushinsa har a lokacin bata manta da abunda yayi mata ba a gurin dinner, da kuma yanzun." Ta fisge hannunta ta wuce zata fita." Yana daga inda yake tsaye yace "kin mance abunda Anna ta umurce ki?" Tayi tsaye tare da zaro ido, Anna ta fad'o mata a rai. Ta tuna da tarbar da akace tayiwa yarima idan ya shigo." Cike da wauta ta furta "Au!" Ta fad'a a fili." Da sauri ta koma inda aka zaunar da ita, ta kuma gyara Alkyabbarta ta lullub'e jikinta baki d'aya." Bassam dariya ta cikasa amma ya dake ya zauna kan kujerar nan da akekira ( _lazy chair_) yana kallonta, Can yaga ta mik'e tsaye ta tako zuwa wurinshi. Kallonta kawai yakeyi, sai da ta kawo gabansa ta kai k'asa." Bata dubisheba ta sanya hannunta ta fara cire masa takalmi." Ta mik'e tsaye taje ta d'auko ruba mai fad'i ta zuba ruwan d'umi. A cikinta dama komai shirye yake." Ta isa gabanshi, bai b'ata lokaci ba ya tsoma k'afafunsa cikin ruwan." Ta d'auko tiren da aka jera tawul da kuma ruwan kumfa mai shegen k'amshi, ta d'ebo d'an kad'an tashiga wanke masa k'afa dashi." Bassam lumshi idonsa yayi yanajin dad'in hakan, tanayin komai cikin natsuwa, Bayan ta kama ta saka tawul tana gogewa a hankali." Sannan ta lalubi irin silifas d'in nan mai taushi ta sanya masa sannan ta kwashe komai ta kai toilet." Da tadawo ta isa bakin gado, dama akwai wata na'ura mai saukar da k'amshin turare ta kunna, gaba d'aya d'akin ya d'auki k'amshi, dad'i yacika bassam zuciyarsa tayi masa sanyi ya kuma yiwa Allah godiya da ya azurtashi da mata kamar Afnan." Yana kallonta tayi duk abunda aka koyar da ita, Sannan ta d'auko madara da dabino tana cire kwallon tana bashi yana ci. Nan da nan yake had'iye dabinon yana mik'a mata hannu tana kuma bashi,wani Har a lokacin bata huceba, tana dai yin abunda Anna ta sanyata kawai ne, Dan kadda Anna taga laifinta." Mik'ewa tsaye yayi, itama ta mik'e tsaye ta sunkuyar da kanta k'asa tashiga cire masa botir d'in rigarsa." Rasa yanda zatayi, ta cire masa rigar tayi, ta sauke hannunta k'asa, kanta a sunkuye, takasa had'a dashi." Bata ankaraba har ya cire rigar daga shi sai d'an gajeren wando." Hannunsa da yakai ya cire mata Alkyabbarta shi yasa hankalinta ya dawo gareta." Idonta ta d'aga ta dubeshi tana ganin shi da gajeren wando, gaba d'aya jikinsa duk gashi ne, kota ina yayi kwance luf luf a kyakkyawar fatarsa fara tas kwanin ban sha'awa." Gabanta ya fad'i tayi saurin sunkuyar da kanta k'asa." Tunawa tayi da Anna datace "kada ta hana yarima Abunda yakeso da ita. D'aukarta yayi cak yanufi kan gado da ita, Rufe idanuwanta tayi takasa had'a ido dashi, gabanta sai fad'uwa yakeyi duk a tsorace take." Shima ganin ta tsorata da ganinshi hakan, Bayason abunda zai d'aga mata hankali, yafison yabita a sannu cikin kwanciyar hankali, ya karantar da ita, salon soyayyarsa, mai rikitarwa." ya ajiyeta, a kan gadon had'ida gyara mata kwanciya, ya mik'e yanufi wadruf ya Ciro kayan barcinsa ya sanya." Yadawo ya zauna a gefen gado. Ya kira sunanta a hankali cikin murya mai taushi." Ta bud'e idonta a hankali ta dubeshi, ganin yasanya kaya a jikinsa, Yasa taja doguwar ajiyar zuciya, had'ida bud'e idanunta gaba d'aya." Yace "beauty tsorona kikeyi ne?" Ki daina tsorona ninaki ne, Ni masoyinki ne ki yarda dani bazan tab'a cutar dake ba, wadda nayi a baya ina Neman yafiyarki." Kibani dama a yau na goge kuskurena dana yita aikata maki." Shuru tayi batayi maganaba, ganin hakan da yayi." Yasaki fuskarshi sosai, Ya tsuguna ya tallabota daga kwancen ya zaunar da ita yace "bani labarin abunda Anna ta koyar dake." Bata tsaya wata wata ba, ta gyara zamanta, duk abunda tayi masa shi ta zayyane masa, da takai inda zata cire masa kaya sai ta fara inda inda." Duk sai takasa idawa, ta k'arasa da cewa "Anna tace idan INA haila kada inkwanta kusa da kai." "Naam!!!!!!!". Ya fad'a da sauri." Bai San lokacin da yace "kina nufin Al'ada kikeyi?." *pls Dan Allah kuyi hak'uri na jina kwana biyu wasu abubuwa ne suka shiga gabana, amma nakusan kammala maku novel din insha Allahu* [3/6, 8:22 AM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *57* Taji kunyar tambayar tashi, Ta rufe fuskarta tace A'a jiya nayi wanka." Wata Ajiyar zuciya ya sauke mai sanyi a ransa yace Alhamdulillah." Mik'ewa tsaye yayi ya d'auko mata rigar barci, fara sol mai bakin lesi, ya mik'a mata yace "ungo karb'i kisanya, idan kuma kika kuskura, kika bud'e baki kikayi min gardama, to babu Wanda zai hana nasanya maki ita da kaina." Da sauri ta Karb'i rigar tana kallonta ta kuma ta d'an saci kallon fuskarsa ta ga alamar da gaske yakeyi." ta Mik'e tsaye jiki ba kwari tanufi toilet domin ta sanya." Rigar tayi mata kyau kuma ta karb'i jikinta, amma sai dai duk ilahirin jikinta a bud'e yake mussam k'irjinta." Kunyar fitowa taji, tayi tsayenta a cikin toilet d'in." Ganin ta d'auki kusan minti goma bata fitoba, Yasa yayi gyaran murya yace "ko nashigo in d'aukokine?" Tanajin hakan batasan lokacin da tabud'e k'ofa ta fitoba, domin tasan halin shi zai iya." Yana ganin fitowarta ya kura mata ido yana kallonta, ya kasa d'auke ido daga gareta." Tasowa yayi ya tareta ya rungumeta, yanufi kan gado da ita." Bai san lokacin da ya kai bakinsa cikin bakinta ba." Taso yin gam da bakinta kamar yadda ta saba, jin ya kai hannunsa a cikin rigar barcinta, ya cafko Brest d'inta, Tayi saurian gantsarewa, Tayi saurin sakin bakinta ba shiri." Yana tsotsar bakinta tamkar an aikoshi, laushin jikinta yasa yayi saurin tub'e mata rigar jikinta gaba d'aya." Cikin muryarta mai sanyi tace "meyasa kakeyi mun haka ne?" Yace "baki so?" Tayi shuru batayi maganaba." Ya tallabeta zuwa tsakiyar gado." Robar Zuma ya d'auko ya zuba a saman Brest d'inta, yashiga lashe zumar yana tsotsar kan brest d'inta, d'aya hannunshi kuma yana cikin pant d'inta yana wasa dashi." Wani numfashi Afnan take fitarwa, wadda batasan tana yinsaba." Shima Bassam hakan, Tun daga k'asanta har zuwa Samanta, Bassam yayi amfani da Zuma sai da ya lashe Afnan tas, wadda bata San abunda yakeyi ba gaba d'aya yarima ya kasheta da zazzafar soyayyar shi." Babu abunda Bassam yafiso yake d'auke masa hankali irin Brest musamman na Afnan, haka ya kamasu yayi ta tsotsa yana shafarsu yana murza saman kan." Sai da ya tabbatar da ya zautar da Afnan ya mantar da ita a duniyar da take sannan ya karanto addu'ar saduwa da iyali, ya saita🍌. Yashiga, ya fara aiki." Gaba d'aya kunnuwansa suka d'auke daga ji." Idanuwansa suka rufe daga gani." Wani jijjiga yakeyi yana wani sambatu, idanunsa na zubar da hawayen dad'i." Gaba d'aya ya jik'ewa Afnan fuska da hawaye, wadda bai San yana fitar dasuba, Sai nishi yakeyi mai had'e da kuwa." Sai sanya mata Albarka yakeyi." Sai da ya d'auki lokaci mai tsawo, sannan ya samu biyan buk'atarsa wadda bai tab'a samun kansa cikin natsuwa kamar hakan ba." Gefe d'aya ya kwanta yana maida numfashi, ya jawo Afnan ya rungume yana shafar gashin kanta, had'ida sakar mata kiss ta ko ina." Yashiga fad'in "nagode Afnan hak'ik'a ke ta dabance a cikin mata." Dana rabu dake dana tafka babban Asarar da bazan tab'a yafewa kainaba." Pls Afnan ki manta da komai, ki zubar da komai kisoni ki k'auna ceni. Kamar yanda nake sonki Mu shinfid'a sabuwar rayuwa. Mushiga wata sabuwar duniya ta masoya." Nayi maki Alk'awarin duk yanda kikeso na zama zan zama, in har zaki soni." Idonta ya cika da hawayen jin dad'i, hak'ik'a kalaman Yarima sunyi mata dad'i sosai, kuma ta yarda ta amince a yanzun yarima yana mata soyayya irinta uwa da d'anta." Tabbas yarima abun so ne, ga kowace macce kuma jarumi ne." Hawayen fuskarta ya kuma k'aruwa da ta tuna da ba ita kad'ai bace gareshi, ba ita kad'ai bace ta d'and'ani wannan zumar soyayyar tasa ba." WaNi Zafin saratu da kishinta taji ya k'aru a ranta, ta kuma d'auki d'amarar duk yanda zatayi sai tayi domin ganin yarima ya zama nata mallakinta, ita kad'ai batare da kowa ba." Ganin sai zubar da hawaye takeyi, bata bud'e baki tayi magana ba." Ya tsura mata ido yana kallonta, a nan take ya karanto tsantsar k'aunarsa a tare da ita." Kuma rungumeta yayi gam a jikinsa, ya tallabota ya d'orata a kan jikinsa. Yana murmushin farin ciki, da jin dad'i, fatar jikinsu ta manne da juna, dama ba kaya a jikinsu _skin_ _to_ _skin_ harshe ya Sanya yashiga lashe mata hawayen dake zuba a fuskarta, Cikin murya mai taushi yace "beauty daina kuka, in dai kina dani, a duniya bazaki tab'a kokawa ba, Ni nakine ke tawace bazan tab'a had'a sonki da nawata ba, keta daban ce, beauty komai naki mai kyaune da kuma d'and'ano." Wani sanyi taji ya saukar mata a cikin zuciyarta." Ganin hakan da yayi yasanya baki ya cafko Brest d'inta yashiga tsotsa yana wasa dashi, birkice ta yayi ya hau kanta. Yasanya ya tsanshi cikin pant d'inta, yashiga wasa da hq d'inta. Wadda Afnan ji tayi kamar ta suma dan dad'i. Sannan ya gyara ya saita🍌 yashige akaro na biyu." Wani sinadarin dad'i ya kuma durarwa basaam wadda kuka yakeyi mai sauti baisan yanayi ba." A Daren ranar sun nisha d'antar da junansu sun farantawa junansu, Bassam ya jigatar da Afnan, har sai da tafara bashi tausayi sannan ya kyaleta haka nan." Rungume da jikinsa ta kwanta, barci mai nauyi yayi awon gaba dasu." Saratu na d'akinta takasa barci sai safa da marwa takeyi, a tsakar d'aki, jitayi bata iya juriya ta bud'e k'ofa ta fito cikin Daren ta nufo d'akin yarima." Tana kawowa k'ofar d'akin ta dingajin saukar numfashinsa da kuwarsa yana kukan dad'i." Da gudu tayi baya tajuya tana kuka tanufi d'akinta, Abunda taji yaci gaba da yimata yawo a kunne, Tana tunanin ita yarima bai tab'a yimata irin wannan kuwarba, bai tab'ayi mata kukan dad'i ba." Asalima idan yana kanta, yanayi yana yak'unar fuskar kamar wadda aka sanyashi dole." Shin hakan yana nufin bata da dad'i ne?" Ko kuma muradinta ne bayayi?" Ta bud'e k'aton bakinta tasaki kuka mai sauti, tana fad'in Allah ka kawo mani agaji mijina zai juya min baya." Kiraye kirayen sallar asuba ne ya tayarda su daga barcin da sukeyi." A hankali ya sauketa daga Jikinsa Dan karta tashi, kamar wata yarinyar goye." *oh ni Ummu safwan naga abun mamaki*🤔 Toilet yashiga yayi wanka ya d'auro arwala ya fito da tawul d'aure a k'ugunsa." Sannan yanufo wurin Afnan a hankali yake hura mata iska a kunnenta, Ta bud'e idonta a hankali da murmushi d'auke a fuskarta." Yace "Beauty atashi ayi sallah, a ruk'a mana Allah yasa a cikin daren nan munsamu 'yan biyu." Murmushi tayi ta rufe fuskarta, Saman gadon ya hau, Zanen gadon yasanya ya rufe mata jikinta, Sannan ya d'auketa kamar jaririya yanufi hanyar toilet da ita." Wanda yayi dai dai da shigowar saratu d'akin. Kasan cewar tana da key d'in d'akin a hannunta." Bassam yayi mamakin ganinta a yanzun a dai dai wannan lokacin shi har ga Allah yama manta da ita, Kuma gashi d'auke da Afnan a hannunshi." Afnan na ganin Saratu tsaye a bakin k'ofa tana kallonsu, ta lank'ama hannunta a saman wuyan yarima, Ya sunkuyo da kansa dai dai bakinta, ta turo bakinta ta cafke bakinsa suka shiga tsotsar bakin junansu. tana d'auke dashi." Yi yayi kamar bai baisan saratu tashigo d'akinba." A cikin salon soyayyarsu ya nufi toilet da ita." Saratu jitayi kamar ta kurma ihu, tunda take da Bassam bai tab'a d'aukarta ba, bai tab'a rungurmar taba, kiss ma baya d'aukar dogon lokaci yana mata shi, Tabbas tasan zamanta a gidan nan ya kusan k'arewa." Bassam yayi Afnan wanka ya wanke ta tas sannan yace tayi wankan tsarki, tayi Arwala tafito, shi ya tafi masallaci, Amma kuma taza cikin shiri domin da yadawo zasuci gaba da abun jiya." Zaro ido tayi tace "wlh nafa gaji da yawa fa." Dariya yayi yace zaki murmuje ne idan nadawo, ya fita yana dariya had'ida rufo mata k'ofa." Bayan ta kammala yin wankan ta fito. Tasanya kayanta da hijabin sallah ta shinfid'a abar sallah ta yar da sallah." Tana kammalawa a nan saman sallayar barci yayi awon gaba da ita." Sai da akayi raka'a d'aya sannan Bassam ya shiga masallacin, Raka'a d'aya yasamu." Maimartaba yana lura dashi a ransa yace "abunda Bassam bai tab'ayi ba." Bayan an kammala sallar ne, yarima da sarki sunjero suna tafiya kamar yanda suka saba." Sarkin ya kalli Bassam yace "Ango Ango, Bassam yayi dariya ya sunkuyar da kai cike da jin kunya." Sarki yace "lallai yau naga canji kuma na tabbata." Kai Allah dai ya biya Anna." Sarki ya lalubo wani k'ullin magani a aljahunsa, Ya mik'awa Bassam yace "ga nawa gudun muwar kasha da ruwa, Zakazo kabani labari da kanka." Koda yake dai zurfin cikinka yayi yawa." Nasha fad'a maka kad'aukeni tamkar abokinka, amma miskilancinka baya barinka" Murmushi kawai Bassam yake mai cike da jin kunya." Zai takawa sarki zuwa d'akinsa kamar yanda yasaba a koda yaushe idan suka fito daga masallaci Sarki yace A'a yi tafiyarka wurin Amaryarka barni na k'arasa da kaina." Bassam yace "to Abba a kwana lafiya." Sarki yayi dariya. Ganin ya dakatar dashi daga rakiyarsa ko musu baiyi masa ba." Ya kalli bassam da har yayi nisa da tafiya yace "a daibi a sannu." [3/6, 9:13 AM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *58* Ya juyo ya kalli maimartaba yayi murmushi, A ransa yace "Abba ko kunyata bayaji, kwata kwata bayajin nauyin yi mun irin wad'an nan magagganun." Kai tsaye d'akinshi ya nufa, da sallamarsa a hankali d'auke a bakinsa." Turus yayi ya tsaya ganin Afnan kwance a saman sallaya tana barci." K'arasowa yayi ya tsuguna gabanta, ya kura mata ido yana kallon kyakkyawar fuskarta, yanajin kansa cikin wani yanayi, Dawani sabon sonta yana durar mashi a zuciyarshi." Tausayi tabashi domin yasan tasha wahala a Daren jiya, tayi juriya, sosai." Tallabarta yayi a hankali ya d'orata a kan gado had'ida gyara mata kwanciya, yajawo bargo ya rufeta ya juya ya bar d'akin." D'akin saratu ya nufa, Ya tarar da ita kwace a kan gadonta tayi rufda ciki, Jin shigowar sa, yasa tayi saurin rufe idonta, kamar wadda ke barci." K'arasowa yayi kusa da ita, ya kalli fuskarta. Gani yayi ta kuma yimasa muni, Ya k'ak'aro murmushin dole, yakira sunanta yace "saratu nasan ba barci kikeyi ba, ganina yasa kika rufe idonki.' Ina Neman Alfarma da kitashi zaune muyi magana." Hawayen da take b'oyewa ne dan karya gani sune suka shiga ambaliya a fuskarta." Gefen gadon yaje ya zauna. Wani wari ya daki, hancinsa, amma kuma ya dake, cikin k'arfin hali ya d'agota ya zaunar da ita." Yace "saratu ki daina sanyawa rayuwarki damuwa, kisani kema matata ce saboda ina sonki na aureki." Ki kwantar da hankinki ki daina kuka. Karkije ki janyowa kanki wani ciwo, kisani dake da Afnan duk d'aya na d'aukeko dukanku mata nane." Sai a lokacin ta d'ago jajayen idonta ta kalleshi." Cikin muryar kuka tace "duk d'aya ka d'aukemu kace dani da ita?" Amma bakatab'a Shiga yanayin da naji kashiga a daren jiyaba idan muna tare da kai." Ranka ya dad'e kuwa fa naji kanayi kana wasu irin magagganu, Ta kuma fashewa da kuka mai sauti." Taci gaba dacewa Baka tab'a d'aukata ba da sunan ka kaini toilet tunda ka aureni." Wannan shine kake kira da duk d'aya ka d'aukemu?" Mamaki yashigayi yana tambayar kansa " to wane sabon yanayi ne yashiga?" Har da kuwa yakeyi?" Shi dai yasan kwata kwata baya cikin hankalinsa a wannan lokacin, bai baima san ko a wace duniya yakeba." Kai Afnan ta dabance ta haihu." Amma sai ya shiga Lallashinta yana bata hak'uri, yace "ki daina shiga d'akina in har bani na nemekiba, Bana son kinayi min lab'e idan ina tare da iyalina, Kamar yadda idan ina tare dake bana son wani yazo yadinga yi mana lab'e." Ya mik'a mata hannu yace tashi ki d'auko min extra key d'ina dake hannunki." Ba musu ta tashi ta d'auko masa ta mik'a masa, Ya karb'a yasanya a aljihu yafito d'akin." yanufi d'akin Anna." ****************** Afnan na farkawa da salati a bakinta, kuyangu tagani, zagaye da ita shi ya tabbatar mata da safiya ta waye, kunya duk ta isheta, tace masu "Ina Anna?" "Suka had'a baki sukace "tana falo ranki ya dad'e ita ta turomu Dan mu taimaka maki." Babu b'ata lokaci komai an kimtsashi tsam tamkar babu abunda ya faru." Tashi tayi, tashiga toilet tayi wanka ta kuma gyara jikinta sannan ta nufi d'akin Anna." Tana Shiga da sallamarta a hankali, Anna ta amsa mata, sai wani sunkuyar da kai takeyi tana jin kunyar Anna." Anna ta lura da hakan saita shareta Dan ta lura nauyinta takeji." Yunwa ke damunta kai tsaye ta wuce wurin abincin gasu anjerasu kala kala." Tana kaiwa wurin taga yarima zaune gefe yana cin abincin shima, yana ganinta ya sakar mata murmushi yace Angel antashi lafiya?" Juyawa tayi taga Anna na cikin d'akin, tayi saurin juyawa zata komawa, Yakira sunanta yace "Afnan!!" Ta tsaya cak, yace "ina zakije bayan nasan abinci zakici kina tare da jin yunwa." Ta turo bakinta,cikin shagwab'a D'aya daga cikin d'abi'un Afnan kenan." Tasowa yayi daga inda yake yanufota, da gudu tabar wurin, abun dariya ya bashi, yanda Kasan taga zaki." Dama yasanta batajin wuyar gudu.' Wurin Anna ta isa sai faman b'ata fuska takeyi. Anna tace "lafiya d'iyata?" Ta turo baki tace "Yunwa nakeji." Anna tace "naga daga d'akin cin abinci kika fito." Tace "yana ciki." Anna bata kuma yin maganaba, Dan tasan kwanan zan cen. sai dai tayi tab'i da hannunta kuyanga ta matso ta zube k'asa." Anna tace "lissafo duk abunda ke cikin kicin d'in Wanda kuka dafa." Babu b'ata lokaci tashiga lissafowa." Anna ta kalli Afnan tace "mezaki ci?" A dai dai lokacin yarima yashigo falon.' Anna ta kuma cewa, "kifad'i abunda kikeso kici da kaina zanshiga kicin d'in." Ganin yarima tsaye gabansu, yasanya hannayensa a Aljihu yak'ureta da ido yana kallo, yana wani murmushi wadda ita kad'ai tasan manufarsa, duk sai taji bata iya magana, Ta mik'e tsaye tabar wurin." Anna tayi murmushi tace "Afnan ho! Duk halinta a Tara Yake bai cika goma ba." Yarima yabita da kallo. Yace "Anna Niko nasan da hakan." abani break d'inta na kai mata. Nasan yunwa takeji sosai zan ciyar da ita da kaina." Anna ta kalleshi batayi magana ba. Tace ranta "'ya'yan zamani basa da kunya, Ta tashi tashiga kicin ta had'o masa breakfast ta mik'a masa ya amsa yace "mungode Anna Allah ya bar manake." Sukayi dariya gaba d'ayansu,." *************** Hajiya zainab abun duniya duk ya dameta, Komai ya jakule mata." Aikinma da sarkin gida ke amso mata akan yarima da duk wani masoyinsa zasu bar duniya Aikin kwata kwata bayaci kashin kud'i kawai takeyi." D'anta Yazeed kuma wadda takeji dashi kamar k'urjin tsakar kai, a yanzun shekararsa hud'u, a duniya, Daren jiya da suka tashi daga barci suntsinci Kansu cikin wani Sabon yanayi na tashin hankali, domin Yazeed ya tashi cikin mawuyacin hali, Kamar wadda Aljanu suka shafa, Kansa ya karkace idonshi ya juye, babu abunda ke fita a bakinsa sai miyau." Da gudu tafito d'akin maimartaba ta nufa a lokacin yana tareda Fulani, cikin tashin hankali take fad'a masa halinda yazeed yake ciki yanxun." Da sauri maimartaba ya mik'e tsaye, suka nufi wurin Yazeed, d'in Gashi kwance amma baya iya aikata komai, Likita maimartaba yakira a waya, cikin minti goma sai ga likita ya iso da saurinsa, aka shiga diba yazeed likita bai fahimci abunda ke damunsa ba sai dai ya yak'ara masa ruwa, had'ida yi masa allurar barci." Yace "insha Allah da zarar ya farka daga barcin komai zai zama normal." Anan take labari ya zagaye gidan sarauta cewa "Yazeed baida lafiya ciwon hauka yakamashi" Saratu na zaune a falonta gefenta kuyangunta ne, na hannun damarta, wad'anda take shiri dasu, da inno da ladidi, Ladidi take Cewa "ranki ya dad'e kina da labarin abunda yasamu Yazeed a Daren jiya kuwa?" Saratu tayi murmushi abunda take jira taji kenan." Tace meya sami yazeed d'in?" Ladidi tace "ance a daren jiya ciwon hauka yatashi dashi baya iya komai." Saratu tayi saurin kallon inno sukayi dariya, Tace "inno aje azomin da jibo, domin nayi mata babbar kyauta dan yau burina ya cika akan hajiya zainab, tasanyani a k'uncin rashin haihuwa, nayi Alk'awari tunda ta hanani na haifi d'ana jinina a gidan nan, itama baxata tab'a moruwar d'antaba, baxai tab'a yi mata amfaniba, kuma daga k'arshe nasanya a kasheshi, kowa ya rasa." *********** Malam Nura kuma soyayya tayi k'arfi tsakaninsa da Maryam, har anyi baiko ansanya ranar aurensu wata biyu masu zuwa.' A yanxun ya hak'ura da Afnan yasanyawa zuciyarsa da rayuwarshi dangana, yako yawa zuciyarsa son maryam." Wadda a yanzun soyayya sukeyi kamar su canye junansu." Kaka itace uwar Amarya kuma itace uwar Ango, shirye shirye biki kawai akeyi." [3/6, 9:31 AM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *59* Bayan sallar isha'i Bassam yana zaune a kusa da maimartaba, suna hira, Yana shaidawa maimartaba cewa "yanaso yatafi England wurin bikin abokinsa kuma tare da Afnan yake son zuwa." Sarki yayi murmushi yace "kayi tunani mai kyau kuwa, Allah ya nuna mana lokacin sai Ku fara shiri tun yanzun." Bassam yace "to Abba nagode Allah yak'ara girma, sukayi sallama yafito, hankalinshi gaba d'aya yana wurin Afnan, yasan tana wurin Anna yanzun." Dan haka kai tsaye yanufi d'akin Anna, ya tarar dasu a zaune a falo Afnan sai fira take zubawa Anna tana shagwab'a Anna na biye mata." Afnan na ganinshi taja bakinta tayi shuru tak'asa iyar da maganar da takeyi." Ta sunkuyar da kai cike da jin kunyarsa." Wuri yasamu ya zauna a kan kujera, had'ida gaida Anna." Idonsa akan Afnan, a kullum ganinta yakeyi tafi jiya kyau, Wata irin sha'awarta yaji ta fisgeshi yayi saurin runtse idonsa, had'ida sakin ajiyar zuciya." Yayi shuru yarasa abunyi, duk abunsa baya iya cewa Afnan ta tashi sutafi d'aki, a gaban Anna." Anna ta katse masa tunani tace "Yarima akwai abunda kake so ne?" Idonsa a kan Afnan yace A'a dama nazone ayi firar dani, amma naga shagwab'ab'iyar 'yar nan taki, ta hana ki kulani." Anna tace "ni ko sai naga kamar a gajiye kake, hala yau kunsha aiki?" A gajiye ko dai sha'awar 'yarki?" Ya fad'a a zuciyarshi, dama zaki sallameta muwuce d'aki yanzun." A fili kuma yace " bari intashi inje in d'an huta, ya fad'a gad'ida mik'ewa tsaye a wahalce." Anna ta kalli Afnan tace "tashi kije ki ciyar da mijinki kiji mai yake buk'ata daga k'arshe kuma ki tayashi hira, sai da safe." Tayi rau rau da ido ya cika da hawaye, ta tuna wahalar da tasha a daren jiya." Gaba d'aya jikinta duk ciwo yake mata, tana k'ok'arin shareware ne saboda kar a samata ido da yawa." Hawaye suka cika idonta, Anna tabita da kallo tasan sai anyi fama da Afnan, saboda jikinta baya son wahala." Ta lura da shaidar hannun Bassam a damtsenta, wata k'ila yanuna mata k'arfi, baiyi mata a sannu ba." Bata son nuna mata tasan abunda ke faruwa tsakaninsu, ta Shiga lallashinta cike da Jan hankali irin nasu na manya." A sanyaye ta mik'e zuwa gurin k'ofar fita sai kuma ta tsaya tace "Anna." "Naam d'iyata." "idan zai takura min nadawo wurinki?" Murmushi Anna tayi tace "Eh mana kizo." Itama murmushin tayi tafita a d'akin gaba d'aya." Anna abun yabata dariya ya za'ayi ya barta tafito daya sameta ai shikenan, Allah ya amsa masu addu'a tasamu ciki shine burinsu." Kai tsaye ta bud'e k'ofar d'akin, yana zaune akan kujera da jallabiya sanye a jikinsa, da alama bai dad'e da fitowa daga wanka ba." Ya d'aga idonsa ya dubeta, ajiyar zuciya yasaki, ya bud'e hannunsa alamar tazo gareshi, yana fad'in oyoyo Angel." Murmushi tayi taje kusa dashi ta zauna ya rungumeta had'ida sauke ajiyar zuciya, ya kai bakinsa a kunnenta yace Angel luv u." Sonki zai kasheni." Ta turo baki tace Anna cewa tayi Nazo natayaka hira, karkayi mun komai." Yayi dariya yace "OK to muyi hira bani labarin." Ta tafa hannunra ta fara, yana kallonta, tana k'ok'arin kauda idonta." Da tagama tace _your turn_",kaima kabani labarinka, ya mik'e tsaye kamar wadda aka mitsala mashi allura." Itama ta mik'e tsaye da sauri ko kafin ya waigo, har ta kai bakin k'ofa, Yace tsaya mana Angel ina zaki?" "Ba mungama hiraba." Ai kince inbaki labari nima ko?" Tace "Eh." shine na mik'e tsaye in gyara." Toni ta bud'e k'ofa ta fita da gudu sai d'akin Anna." Anna na kwance har tafa bacci taji shigowarta, Kuyangu suna cewa "lafiya ranki ya dad'e?" Tayi banza dasu. Ta isa kan gadon Anna tana k'ok'arin hawa bisa." Anna tayi saurin tashi zaune tace "ke meye haka?" "Anna kikace in gudo idan yari.... Ta katseta da tashi ki koma wurin mijinki." Ni bazan kwana dakeba." "Ke wai bada ke nake ba?" Ta turo baki tace "wlh ni yana bani wahala." "Kash!!"🤦‍♀ Anna ta fad'a, "fita ki koma nace Afnan kina so inyi fushi dake ko?" A'ah." Ta fad'a tana girgiza kanta." "To tashi kitafi wurin mijinki, bakisan mala'ikun rahama na tsine makiba, ko malam bai fad'a maki ba?" Idan baki zuwa shinfid'ar mijinki Allah zaiyi fushi dake." Idonta ya cika da hawaye tace "nidai Anna kice mashi yayi hak'uri...." "Wai baxaki wuce ba." Ta kira kuyangu tace "kurakata." Ta fara zubar da hawaye tare da kama hanya duk hankalinta a tashe yake, Sosai Anna ta tausaya mata, dole sai tayi hak'uri tasan Bassam ba sauk'i ne dashi ba, shima dai ya rik'a yimata a hankali mana." Yana tsakar d'aki sai yawo yake shidai Afnan so take takasheshi da sonta da kuma sha'awarta ta huta." Shin meye laifinsa dan ya nuna yana sonta yana kuma son kasancewa da ita?" Yanaji ana kwankwasa k'ofa, ya isa ya bud'e da sauri yana addu'ar Allah yasa itace." Ai kuwa ita d'ince ya isa ya ruk'o hannunta, yanajin yanda jikinta yayi sanyi, ya karanci tsoro daga fuskarta." A bakin gadonsa yajata suka zauna, ya kalleta yace "me Anna tace maki?" Shuru tayi bata bashi amsa ba." Bai jira amsartaba ya fara aikin nashi dama a buk'ace yake, bata iya hanashi ba tasan bata iyawa tunda ya Riga da yasameta." Ita abunda yake damunta dashi sai yayi ta yimata da k'arfi, sai tayi tagani kamar baya a hayyacinsa, ko yaya ne sai yaji mata rauni, shin hakan zasu cigaba?" Kusan sati suka samu tare da yarima, baya d'aga mata k'afa, kuma baya binta da sauk'i." Abun mamaki Afnan duk tafara ramewa saboda Sam batada sukuni, yarima yana matsa mata sosai, ko motsi taji saita firgita saboda jarabar yarima nadamunta." Anna na lura da hakan, suna zaune da yamma ta kalli Afnan tace "naga kin rage kuzari kuma kid'an fad'a." Babu numfasawa Afnan tace "yarima ne." Anna tace "hak'uri xakiyi aure kenan." Idonta yacika da hawaye tace "kullum sai ya tab'ani wlh akwai wahala, baya sona, ta fashe da kuka." Anna tace "waya gaya maki?" "Ni nasani baya sona saratu kawai yakeso, ita yana yimata a hankali." Anna tayi shuru tana naxarinta ta gano kishi ne k'arara a tare da ita, Ashe dama tana sonshi haka?" Suna cikin maganar sai gashi ya shigo, tana ganinshi ta tashi sum sum tabar wurin, ya bita da kallo yasan hakan na iya faruwa amma shi meye nashi take gudunsa, ita matarshi abar sonshi dole tayi hak'uri da shi." Anna ta fara sa ido sosai a kan irin abincin da Afnan ke ciki, saboda k'azabar yarima gareta idan bata kula ba zata lalace da yawa." Tunda duk ta Dami kanta tsoro da rashin sabo da ta d'orawa kanta shi ke sata rama." Dama idan namiji mai yawan buk'ata ne ya had'u da maccen da bata damu da jima'i ba, farko dole ta fuskanci wannan matsalar." Ya dace macce ta dinga laka'ari da ire iren abincin da zata rik'a ci Dan samun kuzari da wadataccen lafiya." Idan ba haka ba saita fita hayyacinta. Duk ta lalace saboda tunani da damuwar da zata d'orawa kanta." Akwai hanyoyi daban daban da zata rik'a kwantarwa da mijinta hankali, Dole tayi tunani tasan yanda zata gamsar da mijinta kobata jima'i ba, Sannan tayi hak'uri da jajircewa Dan bashi kanta idan ba haka ba akwai matsala kuwa." Bassam ya zama abun gudu ga Afnan, ta gaji da fitinarshi ita tarasa dalilin da yasa har yanxun bata sababa, Shin ita kad'ai keda wannan matsar?" Ta lura da ma aurata suna tsananin son sukasance tare da junansu amma ita dai kam ba hakaba ne." Ta tsani yashigo da rana ko yamma ko dare ya nemeta, ita kam tagaji idan dare yayi ko barcin kwarai bata samu, ba dole ta lalace ba." Snn wuni idan yashigo sai yace sai ya nace sai yayi shin su kad'ai ne a gidan?" Baya laka'ari da mutanen dake xagaye da su?" Kullum tana cikin wanka gashinta yana da tsowo sosai ga cika gata bata son kitso. Kullum a jik'e yake tana zama ana gyara mata shi, kenan ita bata da aiki sai wanka kowa sai yasan abunda suke ciki. Dama gashi bayajin kunyar uban kowa a yanzun duk inda take sai ya nemota tun a can zai shiga kissing dinta har suzo d'aki, Ba wai bata son yarima bane A'a tana son abunta jarabarce tashi a kanta tayi mata yawa." Shima yarima yasan a kullum yana canzawa bai San haka yakeba sai da ya auri saratu yayi dace da itama irinsa ce harma tafishi shiyasa bai gano yana da yawan sha'awa ba sosai." A kan Afanan ya gano shi mabuk'a cine, to ya yake danne sha'awarsa a da?" Duk da dai yasan barasa na mantar dashi abubuwa da yawa." Oho🤷‍♂ yanzun lokacinsa ne gara ya amfana ma kansa farin ciki tunda Allah yabashi wadda yafiso a rayuwarshi." ************** Anna a gaban maimartaba, tana gaya masa ya dace ya rage bawa yarima maganin da yake bashi na jaraba." Abin dariya ya bashi maimartaba yace "ni bana bashi maganin jaraba, halinsa ne, aishi magani yafi k'arfi da irin halin mutum, Dan haka Anna karki shafa min wannan laifin." Tace "ranka ya dad'e to wani irin magani kake bashi?" "Wannan kuma ba ruwanki tsakanina dashi ne." Anna tace "ranka ya dad'e kiransa zanyi nayi masa magana yarinya duk ta kod'e ta ya mutse saboda fitinarsa." Jiya harda kukanta, Allah ya taimakeka mezai hana kayi dubara ka lurar dashi fitinarsa gareta tana hanashi sukuni." "Bakince zakiyi masa ba?" A'a ranka ya dad'e kai yakamata kayi masa tunda maganarku ce." Naga a da ba haka yakeba, Maimartaba yayi dariya mai sauti yace "Anna karfa kitakura masa kibarshi yayi lokacinsa ne yanzun yakejin k'arfi." Dole Anna ta samuma Afnan maganin k'arin lafiya da kuzari h _honey telly capsole_ dan samun ingantacciyar lafiya." Kuma tana cin abinci mai kyau kullum zata bata maganin d'aya tasha sannan hankin Anna ya kwanta." ************** Maimartaba da yarima suna hira cike da nishad'i, sarki ya kalli Bassam yace "yarima ina maka sha'awar kwarkwara." Murmushi Bassam yayi tare da sa idonsa k'asa yasan Anna ta gaya mashi halinsa ga Afnan." Shin meye ruwanta wai? "Ranka ya dad'e zanyi kwarkwara amma ba yanzun ba." Akwai kwarkwarori yan shekara goma sha uku wad'anda basu San namiji ba jiya aka kawosu idan kanaso kawo maka su." Bassam yayi murmushi a ransa yace "a duniyar nan babu macce da takai min Afnan, Afnan itace rayuwata Afnan ta dabance a cikin mata babu tamkarta kota ina." A zahiri kuma yace Abbar abarsu kawai idan natashi buk'ata zanyi maka magana." Sarki yayi murmushi yace har yanzun bakason tara mata, Mata biyu sun isheka?" A lokacin da nake kamarka matan da na ajiye sunyi ashirin." Da Sauri ya dubeshi tare da sakin baki, Sarki yayi dariya yace "naga ka kai salati Bassam, amma kana nok'e nok'e." Kana da damar yin hakan akwai mata masu aji da suka shahara wurin kwanciya da namiji, musamman danjin dad'in namiji akayi." Anshirya komai ko yanzun kake son ganinsu zaka gansu." Bassam ya nisa yace "ranka ya dad'e a gaskiya nafi 'ya'ya daga matana kawai, Kasan 'ya'ya suna d'aukar hali na usulinsu. Nafi son 'ya'yana sufito daga uwa ta gari, Jin dad'in tara zuri'a da maccen da baka San asulintaba akwai matsala." Tabbas maganarka gaskiya ce, amma kuma ana iya tsaida masu da haihuwa, shiyasa kagani banada 'ya'ya a kwarkwarori." Bassam ya kuma nisawa yace "Abba a dai barsu zan naima zuwa nan gaba." Hajiya zainab ta katse masu hira da shigo a gigice cikin tashin hankali." [3/6, 9:33 AM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *60* Takai gurfane a gaban Sarki idonta yana mai zubar da hawaye tace "ranka ya dad'e ka taimaka min Yazeed ya farka ya kuma yashiga cikin wani sabon yanayi, ka taimaka min mukaishi asibiti." Maimartaba ya mik'e tsaye da sauri, ya kalli yarima dake zaune yace "tashi mutafi yarima." Sai a lokacin hajiya zainab ta lura da yarima zaune a wurin, ido biyu sukayi sai da taji gabanta ya yanke ya fad'i." Yarima ya mik'e tsaye yabi bayan mahaifin nashi suka nufi sashin hajiya zainab." Yanayin da sukaga yazeed cikinsa abun ya firgita su, musamman maimartaba yace hajiya zainab wai meke faruwa da wannan yaron ne?" Meyasa meshi? Yarima kuma yana gefe baiyi magana ba, a zuciyarsa yana fad'in "kad'an kikagani, tunda a zuciyarki mugunta kika sanya a gaba, babu Allah a cikinta." Maimartaba bai rufe bakiba, sarkin gida yashigo da gudunsa, Ganin maimartaba yasa yaja ya tsaya wuri d'aya had'ida zubewa k'asa yana gaisuwa." Maimartaba ya cika da mamaki yabi sarkin gida da ido, yace "sarkin gida a d'akin hajiya zainab batare da neman ixiniba?" Ya dokawa sarkin gida tsawa yace "waye ya baka izinin shigowa har cikin nan." Lallai yau zansanya a hukunta ka." Jikinsa na rawa zaiyi magana, hajiya zainab tayi karaf tace "ranka ya dad'e nice na aika akira munshi, ba laifinsa bane nice nabashi izinin shigowa Sai a lokacin Bassam yayi gyaran murya yayi magana yace "Abba kabarshi kawai akan yanda tace, mu fuskanci abunda ke gabanmu." Maimartaba ya maida kallonsa ga Bassam yace "yanzun d'aukarshi za'ayi akaishi asibiti kenan a dubashi likitici su fahimci abunda ke damunsa?" Bassam ya girgiza kai yace "A'a Abba ciwon Yazeed bana asibity bane, adai nema masa maganin gargajiya." Sarki yace, "to meye mafita yarima?" Hajiya zainab babu abunda takeyi sai zafgawa yarima harara idan taga zasu had'a ido sai ta waske ta k'ak'aro murmushin dole." Duk abunda takeyi yarima na kallonta ta gefen idonsa." Yace "Abba ninasan wani mai bada magani, irin wannan ciwon da yazeed yakeyi, Kuma hajiya zainab tasan shi, Sarkin gida ma yasanshi." Da hajiya zainab da sarkin gida, suka kashe kunne suna sauraron Bassam." Bassam ya kalli hajiya zainab yace "kicewa sarki gida ya d'aukeshi ya kaishi wurin wanzam." kinsan yafi kowa sanin yana aiki sosai aikinsa kamar yankan wuk'a." Zaro ido sukayi waje a tare, duk da sanyin Ac dake d'akin bai hana hajiya zainab fitar da zufaba, A ranta take cewa "wannan yaron akwai abunda yake nufi damu a gidan nan, Kar dai ace duk abunda mukeyi yana sane dashi." Maimartaba yace "Alhmdulillah Abu yazo gidan sauk'i kenan hajiya zainab sai ya d'aukeshi a had'ashi da fadawa sutafi a kaishi, Allah yabaka lafiya yazeed," Bakinsu na rawa suka amsa da Amin." Bassam ya kuma kallon sarkin gida, dayaketa zarar ido kamar wadda yayi k'arya, sai zufa yake fitarwa yace "nayi magana bakace komai ba, Ko ka manta wanzam d'in danake nufi ne? nafad'a maka shi dala dala, yanda zaku fahimta." Sarkin gida yace Allah ya taimakeka ya k'ara maka lafiya mungane shi, ba sai ka fad'eshi ba." Bassam yayi murmushin mugunta yace "yawwa tunda kaganeshi a can zaka kaishi, Ya kalli maimartaba yace Abba mutafi kawai, sun fahimceni, zasu maganci matsalar." Sarki yabiyo bassam suka fito yana Sanya mashi Albarka, suka rabu da juna kowa ya nufi sashinsa." Hajiya zainab na ganin fitarsu, ta sauke ajiyar zuciya. Ta had'e rai ta kalli sarkin gida tace "sarkin gida ina zarginka da ballasa sirrinmu a wurin yarima." Sarkin gida, ya kai gabanta ya gurfana yace "wlh tallahi bantab'a ballasa sirrinki ga kowa ba, ki yarda dani." Na dad'e ina fad'a maki halin yarima wanda baki saniba ranki ya dad'e." Zaki nefa, wlh har yafi zaki bala'i, Ni ina ganin kamar da Aljanu yake yawo masu d'auko masa rahoto." Hajiya zainab ta mik'e tsaye ranta b'ace "tace idan shi zakine to ni damisa ce, bada Aljanu yake yawoba ko da ifirito sarkin Aljanun, yake yawo na rantse da Allah sai naga bayan shi." Kuma muje zuwa dani dashi, har da Aljanar matarsa, ita kuma abunda nayiwa saratu sai na lunka mata biyunshi." Sarkin gida yace "ranki ya dad'e kibi komai a sannu kar muje wurin Neman gira murasa ido kisani komai lokaci gareshi." Ta daka masa tsawa tace "yi mun shuru!! Lokacina bazai tab'a wucewa ba a cikin gidan nan nagaji saurata gaba da baya, don haka dole ne najuya gidan nan da abunda ke cikinsa, yanda naga dama." Sarkin gida ya had'iye miyau masu zafi a mak'oshinsa shi dai yasan abunda yake hangowa a wurin yarima." Yace "haka ne Allah ya huci zuciyar sarauniya." Yayi mata sallama ya fita, kwata kwata ya manta da abunda ya kawoshi wurinta." *************** Afnan na wurin Anna kwance yau batajin dad'in jikinta. Anna tabata magani tasha dakyar tasamu zazzab'in ya lafa tasamu damar yin barci." Farkawar da zatayi, taji a duniya babu abunda takeso sai k'amshin turaren Bassam." Mik'ewa zaune tayi, Anna tace "d'iyata kintashi?" To ya jikin naki?" Tace naji sauk'i Anna, Bara na shiga daga ciki nayi wanka sainayi sallah." Anna tace "to afito lafiya." Cikin tafiyarta mai cike da natsuwa, ta isa d'akin nasu, Ta tarar da bassam kwance akan gado yayi rufda ciki da Alama ya jima da dawowa." K'amshin turaren jikinta yajiya ya tabbatarwa kansa itace, Ya tashi zaune had'ida bud'e hannayensa alamar tazo gareshi." Da sauri ta isa wurinshi ya maida hannunsa ya rufe, ya rungumeta, dama tanaso tashak'i k'amshin turaren jikinsa." Tana rungume dashi tayi lamo a jikinsa tana shak'ar daddad'an k'amshin jikinsa, tana lumshi idonta, Shi kuma sai kissing d'inta yakeyi a wuya a kuma baki da kuncinta, yana Neman cire mata riga yasha Brest Idonta ya sauka akan kwalbar giyar dake gefen gado ajiye da alamar yanzun ya k'are shanta." Ta yunk'a ta kwace jikinta daga jikinsa, a dai lokacin da ya fara fita daga hayyacinsa, yana Neman zuge mata zif d'in rigarta." Tashiga ja da baya idonta na zubar da hawaye, Nufota yayi yana fad'in Angel meke faruwa?" Pls karki gujeni a dai dai wannan lokacin, Mena maki?" Me kike so?" Angel kina Azaftar dani da soyayyarki, shin har yanzun baki yafe min abunda nayi maki ba?" Kizama mai yafiya gareni, nayi maki Alk'awarin duk yanda kikeso ki ganni na zama zan zama in har zaki daina guduna." Sai a lokacin hawayen fuskarta suka tsaya cak, ta tsureshi da ido, ta tabbatar da abunda yake fad'i da gaske yakeyi har cikin zuciyarsa yake fitowa." Yabata tausayi sosai, taje kusa dashi ta zauna." Yabita da ido yana kallonta. Yace "Angel kin Amince dani bazaki k'ara gudunaba?" Ta d'aga kanta alamar "Eh." Tace "Amma da sharad'in bazaka kuma shan wannan abarba ta nuna masa kwalbar giya." Ya tsurawa kwalbar giyar ido yana kallonta, yana tuna lokacin da yafara shanta tun yana England makaranta, Dama bak'in ciki da b'acin rai yake sanyashi ya shata." Mudun ta Amince dashi ta tarairayeshi ta nuna masa so a gaban kowa babu abunda zai kuma yi da giya." Ya kalleta yace Angel nayi maki Alk'awari daga yau daga yanzun bazan k'arashan barasaba, in dai hakan zai sanyaki farin ciki." Batasan lokacin da ta rungumeshi ba, tashiga aika masa da kiss kota ina." Shima yashiga mayar mata dama a buk'ace yake, nan da nan ya cire mata kayan jikinta, shima ya cire nashi, ya haye kanta yashiga aikin nashi." Ba laifi Afnan tayi dauriya, wadda bassam da kansa sai da yayi mamakinta." Bayan sun gama, bassam yaji dad'i sosai ya kuma samu gamsuwa, yaji wani sabon sonta da k'aunarta sun k'aru a zuciyarsa, Ya jawota ya rungumeta, yace nagode maki Angel hak'ik'a ke Alherice a rayuwata." Kinsan Albishir d'in da zan maki?" Ta rufe fuskarta had'ida girgiza kai alamar "A'a." Yace "gobe ki shirya zankaiki wurin kaka da kaina, Ki ganota. Dolene a jijjinawa Kaka tareda yimata babban kyauta, Allah ya biyata yasa ta gama da duniya lafiya." Sann kuma Albishir na biyu. Nayi maki _passport_ zamuje England kihuta." Afnan taji dad'i ta kuma rungumeshi tace "Nagode my prince, Allah ya barmu tare." Daren yau sunfarantawa junansu sunji yarda junansu dad'i Wanda Afnan dauriya ce kawai takeyi, Dan ta jigata sosai." Haka sukayi barci cikin farin ciki Afnan ta matsu safiya ta waye mata." **************** Shiri sukeyi Bassam cikin dakakkiyar shadda ruwan Zuma ya sanya hula itama ruwan Zuma da ogogon gwal sanye a hannunshi yayi kyau matuk'a." Itama Afnan taci ado da gwala gwalai tasanya super English Atamfa tayi mata kyau, ta d'auko Alkyabbarta ruwan zuma ta sanya, sunyi kyau matuk'a, Basaam yace "Angel kinganki kuwa kinyi kyau, inajin kishin kadda wani ya gane min ke a haka." Tayi murmushi tace "ai kafini kyau prince, Ta kawar da maganar da cewa "amma ya kamata muje muyiwa Anna sallama." Haka suka jera suka fito gwananin ban sha'awa." Suka shiga d'akin Anna sukayi mata sallama, Ta dubesu kwanin ban sha'awa, tayi masu Addu'ar dawowa lafiya, had'ida bawa Afnan turamin Atamfofi takaiwa Anna saura kuma ta rabawa yan uwa da abokanan arzik'i." Ta d'ur k'usa k'asa tashiga godiya ga Anna, Anna ta mik'ar da ita tsaye tace "ki daina yimin godiya Afnan a rayuwata babu abunda bazan makiba." Kicewa Kaka ina gaida ita saina zo." Haka suka fito d'akin Anna cike da murna, suka nufi wurin maimartaba, tsakanin sashin su Dana maimartaba akwai 'yar tafiya, Suna tafiya suna hira cike da nishad'i." Saratu sukaci karo da ita tafito wani lungu sai waige waige takeyi kamar bara gaskiya." Wuri d'aya taja ta tsaya ganin yarima ya tsaya yana kallonta cike da tuhuma, Har ga Allah ya manta da ita, idan ba ganinta yayiba, Kuma duk lokacin da ya ganta saiya tsinci kansa cikin yanayin rashin yarda da ita. itama ta daina bibiyarshi kamar yanda tasaba." Cike da tuhuma yake kallonta yace "daga INA kika fito a nan?" Ta dake tace "ranka ya dad'e nafito ne domin nasha iska." Ya kafeta da ido yana karanto rashin gskya a tare da ita." Afnan nan gefe tana kallonsu kishi duk yacika mata zuciya, jitakeyi kamar ta fashe." Inda yaga tafito nan ya maida idonsa yana kallo, Wani mutum ya hango ya juya baya yana tafiya, Ko a mafarki yaga mutumin yasan kowaye, shi, Alhaji Aminu ne, ko dayake bayansa kad'ai yagani." Yayi murmushin nan nashi na gefen baki yace "wancan fa? Waye shi? Daga INA yafito?" Ta juya ta kalli wurinda yake nufi, hango Alhaji Aminu da tayi shiyasa gabanta ya fad'i, Amma dayake 'yar duniya ce, Ta dake tace "ranka ya dad'e ni banga kowaba, bayan wancan mutumin dake tafiya." kuma a rayuwata bantab'a ganin halitta irin tashiba sai yanzun da ka nuna minshi." Ya kuma yin murmushi yace "karki damu kishiga ciki, Fita zanyi da Angel idan muka dawo, inaso zanyi mgna dake." Bata bashi amsa ba, tarab'ashi ta wuce cike da jin zafinshi, yana nuna fifiko a tsakaninsu da wancan Aljanar." [3/6, 9:47 AM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *61* _hmm mutum ba'a iya masa, halin mutum sai shi_ _ina ganin fa rubuta littafin nan ba wani yasanya niba, nice naga dama na sanya kaina, labarina a rubuce yake nariga da natsara abuna. To meyasa akeson ayimin haka ne?_ _pls dan Allah kurabu dani kubarni naci gaba a yanda natsara labari_ _idan kuma kinka inda baiyi dai da yanda kikesoba, to ki kyara a ranki."_ _ko kuma ki rubuta naki_ _labarin, amma idan aka nemi a takemin duga dugai to gskya za'a samu Matsala danifa, saboda bana da hak'urin da juriya ina gani aneme shige min a hanci_ _afa kiyayeni ehe_😎 Ya juya kalli Afnan dake tsaye nesa dasu dan gudun karta jiyowa kunnenta abunda zai b'ata mata rayuwa, Yaga taci magani. Ta had'e fuska ba fara'a a tare da ita, ya k'araso wurinta ya rik'a hannuta had'ida d'an matsashi kad'an yace "Angel meye abun had'e rai kuma?" Bata tanka mashiba illah ma ta fisge hannunta, ta shige gaba, Murmushi yayi yabita a baya, yanajin dad'i a ransa saboda ya hango kishinsa k'arara a idonta." Gabda zasu shiga fada, taja ta tsaya ya cimmata suka jera gaba d'aya fadawa na ganinsu suka take masu baya had'ida zuba masu kirari." A gaban maimartaba suka zube, suna gaisuwa." Cikin jin dad'i da murmushi d'auke a fuskar sarki yake amsa gaisuwarsu Tareda sanya masu Albarka." Kallon Afnan sarki yakeyi yana anyanawa a zuciyarshi yana fad'i "ikon Allah, Allah mai yanda yaso, a duniya ana kama, Da ace 'yar Alhaji ibrahim na k'asar nan, da babu wanda zai Hana ya rik'e Afnan yace itace." Saboda suna matuk'ar kama da Amininsa har dariyarsu iri d'aya da d'an murmushin da Alhaji Ibrahim yakeyi idan suka je wurin da yakejin kunya, Sak irinshi Afnan takeyi, Allah mai yanda yaso, aduniya ana kama." Bassam ya katse masa tunani yace "Abba zamutafi gidan kaka yanzun kayi mana Addu'a, sannan kuma na shirya komai gobe zamu wuce England, jirgin k'arfe 8:am zamubi." Maimartaba yace Allah ya tsareku ya kareku a duk inda kuke ya kuma duban Afnan yace "d'iyata a dawo lafiya." Suka fito tare da fadawa wad'anda zasuyi masu rakiya." Motoci hud'u aka cika da fadawa masu rakiya gamida motar su yarima biyar kenan." Motarsu Afnan ce tsakiya sannan gabansu da bayansu duk motocin fadawa ne, sai jiniya ake masu." Isarda sukayi k'ofar gidansu kaka cike yake da mutanen d'auren Auren malam Nura da Maryam." Jin jiniyar da sukayi ne yasa kowa ya raja'a ya maida hankalinshi wurin kallon motocin, ganin *tambarin sarauta* lik'e a kowace mota ya tabbatar masu da yayan gidan sarauta ne." Malam Nura dake tsaye tareda abokanansa yana ganin motocin gidan sarauta sai da gabansa ya yanke ya fad'i." Tsayawar motarsu yarima fadawa suka fito da gudu suka nufi motarsu, suka zagayo wurin yarima suka bud'e mashi yafito cike da k'asaita, Zasu zagaya subud'ewa Afnan yarima yad'a masu hannu dasu dakata." Sukayi saurin jada baya, Da kanshi ya zagaya mazauninta ya bud'e mata k'ofa ta fito, Rumgumeta yayi a jikinsa batare da yadamu da taron mutanen dake wurin ba." Ya kara bakinshi a kunnenta yace "muddun kikayi k'ok'arin kwace kanki gareni, bazan kuma kawoki kiga Kaka ba." Aikuwa Afnan najin haka ta kuma lafewa a jikinsa, ta tura kanta a k'irjinshi tana shak'ar k'amshin turaren shi." Aikuwa kallo yadawo kansu kowa sai mamaki sukeyi wasunsu na fad'in "waccan kuwa Afnan ce?" Wasu nakiran "eh itace amma gskya ta canza kama kamar ba itaba." wani yace "aidama Afnan matar manyace. Karanbani ne kawai yakai malam Nura soyayya da ita." Malam Nura dake tsaye gefe d'aya sanye da manya kaya abokanansa sun zagayeshi, Yana ganin fitowar Afnan rungume da yarima sai da Idonshi yacika da hawaye, yayi saurin maidasu." Ido biyu Bassam yayi da malam Nura yasakar mashi murmushi ya kuma rungume Afnan d'inshi kamar wadda za'a kwacewa ita, suka shiga gidan." Afnan batayi mamakin sabon gidan da kaka da malam iro suke cikinsaba, dama tanajin labarinsu a wurin Anna. Wadda ita kuma Anna maimartaba yake gaya mata komai." Tana rungume dashi suka shiga gidan, ganin taron mutane cike da gidan yasa gabanta fad'uwa tayi saurin kwace jikinta daga gareshi." Ta kutsa cikin taron mutanen tana kiran "Kaka!!" Kaka dake falonta zaune tareda abokanan Maryam suna barkwanci tajiyo sautin muryar Afnan tana kiranta, Da sauri ta zabura ta mik'e tsaye tace "muryar wa nakeji kamar ta Afnan dina." Afnan ta rugo da gudu ta rungume Kaka tana sauke ajiyar zuciya, Kaka tace "oyoyo Afnan suka kai zaune cike da murna." Maryam da abokananta mutuwar tsaye sukayi da suga yanda Afnan ta canxa masu." Kasa yimata magana sukayi saboda mamaki." Sallamar da Bassam yayi ya shigo, ita yasanya kowa ya watse yabar d'akin." Bassam ya kai gurfane gaban kaka yana gaida ita, Kaka rungume da Afnan tana murmushi cike da jin dad'i take amsa mashi, had'ida cewa "Bassam anshigo d'aurin auren?" Munga abun Arziki Allah yabiya yasaka maka da Alheri yabaku zuri'a tagari." Afnan tasaki baki tana mamaki, "Auren waye akeyi?" Shin dama yana zuwa gidan kaka ne baitab'a fad'a mata ba?" Ya katse mata tunani da cewa "kaka bari naje wurin d'aurin auren can, nasan yanzun hakan ni ake jira ga sadakin nan a wurina." Kaka ta zaro ido tace "yarima abun ba'a gajiya harda sadakin kaine zaka biya?" "Anfa gode Allah yabaku wad'anda zasuyi maku kuma." Yace "Amin had'ida kallon Afnan yayi murmushi ya tashi ya fita." Afnan na ganin fitarshi. Tace "kaka ni duk abun ya d'aure min kai shin wai auren waye akeyi a gidan nan?" Dama yarima yana zuwa gidan nan ne?" Kaka tayi dariya tace "ai Yarima yazama d'an gidan nan kwana ne kad'ai ne bayayi a gidan nan, duk matakin da kikaga mun taka to aikin yarima ne a yanzun danida malam iro babu abunda zamu iya cewa Yarima sai Allah yayi mashi Albarka ya bashi zuri'a ta kwarai." Sannan mutanen da kikagani a waje yau ake d'auren auren malam Nura da Maryam, Wanda Bassam ne ya d'auki nauyin komai har sadaki da kuma gidan da zasu zauna." Allah sarki Ya Sayyadi, ta furta a fili. Tace "kaka naso naga Ya Sayyadi naga yanda ya koma, nabashi hak'uri abunda ya faru." Kaka tace "karki damu malam Nura ya dad'e da yafemaki, dama Allah baiyi kece matarsa ba." Fira sukeyi mai cike da farin ciki da yaushe rabo." Afnan ta zama abar kwatance a cikin mutane kowa sai nunata yakeyi." An d'aura auren malam Nura da Maryam akan sadaki dubu d'ari wadda Bassam ne yabiya mashi." Anyi shagulgular biki, an kai Amarya d'akinta. Wadda Afnan bata damu da hakan ba, ta d'auki soyayyar malam Nura da cewa dama a da k'uriciya ce, bata San ko meye soba, Sai akan prince d'inta ta gane menene so menene kuma k'auna." Malam Nura kuma dole yasanyawa rayuwarshi dangana da hak'uri domin Afnan ta riga da tayi masa nisa." Haka aka kammala komai yarima ya d'auko Afnan suka nufo gida, sai wani had'e fuska takeyi, na rabuwa da Kaka,shi kuma a tunaninshi saboda malam Nura takeyi." Dan haka bai kulata ba, saima yaji duk haushinta yakeji." Haka suka dawo gida babu wanda ya kula d'an uwansa, Kai tsaye yanufi d'akin saratu yashiga, had'ida turo k'ofa da k'arfi." Wani haushi da bak'in ciki had'ida kishi taji ya kamata, idonta ya cika da hawaye, ta nufi d'akin Anna tana kuka." [3/6, 10:04 AM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *62* Kai tsaye jikin Anna ta fad'a ta fashe da kuka zuciyarta na k'una." Anna tashiga tambayarta "Afnan lafiya? Meya faru?" Ina shi yariman yake?" Kuka takeyi ba amsa, Anna taja bakinta tayi shuru, Tare da kwantar da ita akan cinyarta tana bubbugar bayanta, sai da tasamu natsuwa sannan tayi shuru sai ajiyar zuciya takeyi." Snn Anna tace "ina yarima?" Cikin murya k'asa k'asa tace "yana d'akin saratu." Anna tayi shuru Dan ta fahimci harda kishi ke d'awainiya da ita, Tace "Afnan kidinga hak'uri da halin yarima, Ya kamata ace kin rubuta littafin halinsa. Tunda kinfi kowa sanin waye yarima Amma kike zama kina wahalar da kanki akansa." ********* A kwance ya tarar da Saratu tayi d'ai d'ai a kan gado." takashe murya sai waya takeyi tana dariya, tana sanye da wata riga Wanda da ita wa babu duk d'aya, Gaba d'aya tsaraicinta a bayyane yake, kamar k'ato, Jikin ta ba fasali, babu kyan gani." Dogon tsaki y yaja ya doka mata tsawa. "Ke meye haka wai?" Da Allah malama tashi ki Sanya kayanki magana zanyi dake." Dawa kik'e waya ne wai?" Ke wai ma dakike zama tsirara haka kina tsammanin ba Wanda zaishigo ya ganki ne?" Mik'ewa zaune tayi, tajawo hijabi ta sanya, tana turo k'aton bakinta, wai shagwab'a takeyi☹ Cikin magana k'asa k'asa alamar shagwab'a tace "toni zafi nakeji, idan nasanya manyan kaya jinakeyi sunayi min nauyi a jiki." Tsawa ya daka mata "da Allah malama kibud'e baki kiyimin magana. Kina wani turo baki Banajin Abunda kike fad'a." Duk'arda kanta k'asa tayi, bata kuma yin maganaba duk inda ranta yake ya b'aci." Bai damu da yanayin da yaga ta sauyaba, yace "Gobe tafiya zanyi England tare da Angel zantafi wata biyu zanyi na dawo, Idan nadawo raba kwana a zantsaninku." idan zan koma sai na tafi dake." yanxun dame dame kike buk'ata?" Murmushin tayi dan ko a jikinta bataji zafiba, wata damace tasamu wadda zataji dad'in holewarta da Alhaji Aminu yanda takeso suci karensu ba babbaka." "Bana buk'atar komai ranka ya dad'e, Allah yakaiku lafiya ya kuma dawo daku lafiya, "Amin." Yace a tak'aici, sannan ya tura hannunsa a Aljihu ya ciro chark ya rubuta mata dubu d'ari biyar ya mik'a mata yace "gasu ki rik'e a hannunki." Ta amsa tana godiya, Bai kulataba yafito duk rayuwarsa a dagule take." Afnan dake kwance akan cinyar Anna jikinta ya d'auki zafi, zazzab'i ne yake son rufeta, Anna ta d'auko magani taba, Dan a kwanakin nan tana lura da ita bata wani cin abinci sosai sai tace adafa mata iNdomie, itace abincinta, Anna ta furta a ranta "Allah yasa zargina ya yazama gaskiya da nafi kowa murna da farin ciki." Ganin tayi barci Anna, ta gyara mata kwanciya a kan kujera ta mik'e tashiga ciki." Bassam a d'akinshi sai zuba ido yakeyi yaga Afnan ta shigo, amma shuru kakeji har k'arfe tara baiga tashigoba , yayi tsammanin Anna zata turota amma shuru kakeji." Tashi yayi yashiga shirya kayansu da Kansa, wad'anda zasuyi tafiyar dasu, har da kayanta duk ya shirya mata wad'anda yake buk'atar yaga tayi amfani dasu a can." Har ya kammala shirya kayan a cikin akwati, a lokacin 11pm bata shigoba. Yashiga mamakin ko lafiya,? yasan dai koda fushi take dashi, Anna bazata barta ta kwana a can ba saita turo masa ita." Jallabiyarsa ya d'auko ya sanya ya fito yanufi d'akin Anna." Tura k'ofar yayi yashiga, yaci karo da Afnan kwance a kan doguwar kujera, tana barci, kuyangunta zagaye da ita Suna mata fifita, duk da sayen Ac dake d'akin." Suna ganinshi sukayi saurin mik'ewa tsaye zasu bar wurin. Ya dakatar dasu yake "tambayarsu meya sameta?" Suka had'a baki, "ranka ya dad'e batajin dad'in jikinta zazzab'i yake damunta." "Ina Anna?" Ta shiga daga ciki yanxun." Amma kuma tabata magani tasha." "OK kuyi tafiyarku, idan tafito kuce mata nace sai da safe." Sukace to ranka ya dad'e." Ya d'uk'a ya d'auki Afnan kamar jaririya yanufi d'akinshi da ita, Afnan batasan abunda akeyiba saboda barcin yaci k'arfinta." Saman gado ya d'orata, yashiga rage mata kayan jikinta, ya barta daga ita sai best da wando, yaja bargo ya rufeta Ji yayi jikinta yayi zafi sosai, ya dafe kansa🤦‍♂ Yasanya hannunsa yashiga gyara mata gashin kanta da yazubo ya rufe mata fuskarka, cikin tausayi yace "Am sorry Angel duk laifina ne, Kiyi hak'uri nayi Alk'awarin bazan kuma b'ata makiba duk abunda kikeso shi zanyi maki in dai zai sanyaki farin ciki." Ya bud'e bargon yashiga ya jawota jikinshi ya rungumeta yana shafa bayanta." Har barci ya d'aukeshi." Asubar fari Afnan ta farka ta ganta rungume a jikinshi kamar zai maida ita ciki, ta yunk'ura zata tashi, Ya farka da Addu'a a bakinsa, yace "Angel kintashi?" Ya jikin naki?" Ya kai hannunsa a wuyanta, yaji jikin nata babu zafi yace "Alhmdulillah." Tashi mutafi na taimaka maki kiyi Arwala kiyi sallah." Murmushi tayi tace "zan iya da kaina." Ta rik'a hannunshi biyu, had'ida sunkuyar da kanta k'asa idonta ya cika da hawaye, "Idan laifi nayi maka kake fushi dani, kayi hak'uri bazan sakeba Pls karka juya min baya kaine farin cikina, Idan ka juya min baya bansan yanda rayuwata zata kasan ceba." Tausayi tabashi bai san lokacin da yajawota jikinsa ba, yasan harshinsa yashiga lashe mata hawayen dake zuba a idonta, Yace "Daina kuka Angel ninakine ke tawa ce, kisanya a ranki prince bazai tab'a juya maki bayaba, bazai tab'a daina sonki ba." Na fahimceki na yarda da soyayyarki gareni, kinajin zafi da haushin rabuwa da Kaka ne. Nayi maki Alk'awari da zarar mundawo England zanje na d'auko kaka ta dawo kusa damu mu zauna tare da ita, Domin farin cikinki." K'ank'ame shi tayi, tana dariyar farin ciki, "Nagode prince Allah yabarmu tare." "Babu godiya a tsakaninmu komai zan iya maki idan har zai sanyaki farin ciki mai d'orewa." Tashi mutafi muyi Arwala muyi sallah." Hakan suka mik'e rungume da juna suka shiga toilet sukayi Arwala cike da farin ciki da k'aunar juna, suka fito, shi yanufi masallaci ita kuma ta shinfid'a sallaya ta tayar da Sallah." Bayan sun kammala sallar ne yarima yashigo sukayi wanka suka fara shirin tafiya jirgin k'arfe 8 zasubi." Maimartaba da kansa ya tafo sashin yarima tare da fadawa suka jera domin suyi masu rakiya. Anna sai Addu'a take masu, Saratu kuma na kan gado tayi d'ai d'ai tasaki k'aton bakinta sai barci takeyi." Har mota maimartaba ya rakasu sai da yaga tashin motarsu yana d'aga masu hannu had'ida yi masu Addu'a har suka tafi." Duk abunda akeyi a kan idon hajiya zainab tana ganin tafiyarsu tayi dariya da shewa tace "sai dai wasu ba kuba, kunyi tafiyar da bazaku dawoba sai lahira." Saratu na farkawa daga barci ta duba agogo k'arfe sha biyu na rana, Ta Tabbatar da cewa tuni yarima sun dad'e da tafiya, ta duro daga kan gadon, tashiga kwalawa ma'aikatanta kira, gaba d'aya suka hallara falo, suna jiran umurninta." Ta dubesu d'aya bayan d'aya tace "kuna da labarin yarima yayi tafiya?" "Suka had'a baki "Eh ranki ya dad'e." "To ina buk'atar kowa yaje ya huta nadakatar da aikinku a sashin nan har sai lokacin da yarima yadawo domin ina buk'atar Hutu." Shuru sukayi ba amsa suka Shiga mamaki a ransu, abunda ba'a tab'a yiba a gidan nan." "Kunyi shuru Baku bani amsaba, idan kuka nemi kuyimin gardama zansanya a hukunta ku." "Kiyi hak'uri ranki ya dad'e tuba muk'eyi yanda kikace haka za'ayi." Suka tashi suka fita kowa da abunda yake sak'awa a ransa." Tana ganin fitarsu tayiwa Alhaji Aminu waya, da cewa yataho yarima ya tafi." Dariya yayi yace "gani nan a bakin k'ofa kice yau zamuji dad'i kenan." Bata sauke wayarta a kunnenta ba, Ya turo k'ofa yashigo, Tayo Kansa ta lank'ameshi ta turashi a kan gado, ta haye kansa, kamar wadda taga nama." Shima Alhaji Aminu ba kanwar lasaba ne, Ya sauketa a jikinshi ya mik'e tsaye ya cire kayan jikinshi ya koma zindir, Itama ya cire mata kayan jikinta." Ya nufeta ya haye kanta yana wasa da ita, sai bud'e k'aton bakinta takeyi alamar tanajin dad'i, daga nan ya saita🍌 yashige yashiga aiki, Sai kuwa takeyi, a ranar Abu d'aya suka shigayi yayi raund 12 amma bataji ta gamsuba, shima dayake ba gajiya yakeyiba yashiga suburbud'arta." *England* Garine mai sanyi da ni'ima." Kai tsaye yarima gidansa ya nufa, wanda babu kowa a cikinsa sai masu gadi da masu kula da tsaftar gidan." Gida ne madaidaici Wanda anxuba kayan more rayuwa a cikinsa." Gidan ya burge Afnan da yanayin garin sai murmushi takeyi alamar farin ciki." Yarima na ganin haka ya d'auketa cak yanufi bidromm da ita, yana fad'in Angel da alama yanayin garin nan ya maki dad'i Muje kibani tuk'uicina." Ya tallabeta a hankali yake tafiya da ita bakinshi cikin bakinta, yana kissing d'inta, idonshi ya fara sauya launi, saboda buk'atuwa, bai zame ko INA da itaba sai a kan gado." A hankali yake cire mata rigar jikinta har a lokacin bakinshi yana cikin bakinta, Sannan ya gangaro zuwa Brest d'inta." Gani yayi sunyi mashi girma da laushi har wani shek'e sukeyi, Yasanya hannu yana shafarsu cikin wata siga mai rik'itarwa, daga nan ya sanya harshensa yashiga wasa da kan Brest d'in, yana juyashi da harshi yana d'an tsotsawa yana saki yana kuma k'ara loliyashi, cikin salon rikitarwa." Afnan sai lumshe ido takeyi, A hankali ya kai hannunshi ya cire mata pant d'inta, ya shiga wasa da HQ d'inta, yana sanya hannu yana fitarwa, wata irin k'ara tasaki tajin dad'i, sannan ya haye kanta yashiga aikin nasa." Ya jigatar da ita ya kuma wahalar da ita, Sai da tabashi tausayi sannan ya saurara mata, Ya kwanta gefe d'aya yana sauke numfashi, Ya tallabota ya d'urata a kan cikinsa, ya kwantar da ita a kan k'irjinsa, Brest d'inta ya had'e da k'irjinshi ya manne, wuri d'aya, yanajin taushi da santsi. Ya lumshe idonshi hawayen dad'i suka shiga zuba a idonshi, ya shiga shafa bayanta yana fad'in luv u Angel, tareda hura mata iska a kunne." "Ke ta dabance a cikin mata, komai naki daban yake, komai naki mai kyau ne, da kuma d'and'ano." Kisama ranki yarima bazai tab'a rabuwa dakeba domin kece rayuwar yarima da jin dad'insa." Itama hawaye takeyi tanajin dad'in kalaman yarima gareta." Wata irin yunwa takeji, cikinta har wani ciwo taji yafayi mata. Ta d'aga kanta ta dubeshi tace "Prince yunwa nakeji." a hankali ya sauketa daga jikinshi, ya mik'e tsaye yashiga toilet yayo wanka yafito sanye da jallabiya yace "mekikeso kici? Ta marairaici fuska cikin shagwab'a tace indomie." Yace "Angama Angel, yanzun za'a dafa maki, yafita da saurin shi." Tana ganin ya fita ta lallab'a ta tashi tana d'an cije baki, saka makon zafin da takeji a can k'asanta, Ita dai batasan ko yaushe zata saba da wannan abunba, Prince yacika mugunta da yawa sai yayita yimata da k'arfi." Toilet tashiga ta tsuguna tana fitsari wani zafi taji ta a gabanta tayi saurin mik'ewa tsaye da sauri idonta yashiga zubar da hawaye. ruwan zafi ta zuba ta zauna a cikinsu, sannan ta farajin sauki." Haka nan ta lallab'a tayi wanka tafito." [3/6, 10:18 AM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *63* K'ananun kaya tasanya wando da riga, sunkama jikinta kuma sunyi mata kyau, Taja gashinta a tsakiyar kanta ta d'aureshi da ribon, Tafito falo tana jiran indomie domin yuwa takeji sosai ji takeyi kamar tayi amai." Bassam na kicin ya tsare kuku sai masifa yake masa, yana fad'in "dahuwar indomie kamar nasanyaka ka dafa min tuwo, Tabbas hannunka ya farayin sanyi, ya kamata na canzaka." Kuku sai hak'uri yake bawa yarima, da kyar yasamu ya gama dafuwar indomie ya xuba a plete, yarima ya d'auko ya fito." A falo ya tarar da ita zaune a kan kujera ya dubeta yayi murmushi yace Angel kinfito, Taso ga indomie kici." Yanufeta da plete d'in a hannunsa, Warin indomie ya daki hancinta, taji ba irinta take buk'ataba, tashiga yunk'urin amai." Amai takeyi ba sauki jitakeyi kamar ta amayar da hanjin cikinta, gaba d'aya duk ta b'atawa yarima jiki da mai." Rud'ewa yayi hankalinshi ya tashi sai fad'in yakeyi "Angel meyasa meki meke damunki?" Rik'ata yayi da sunan yanufi toilet da ita sai gani yayi ta zube k'asa a some." Bai San lokacin da yabitaba yana girgizarta yana kiran sunanta cikin tashin hankali." Ruwa ya d'auko a cup ya yayyafa mata, sannan taja doguwar Ajiyar zuciya, tana sauke numfashi a hankali." Wayarsa ya d'auka ya kira abokinsa Kalil, yace yakawo masa mota yanzun da sauri wife d'inshi zai kai asibity.' Ba'ayi minti goma ma Kalil yazo Bassam ya d'auki Afnan yasanya mota kalil yaja suka nufi babban Asibityn England." Likito da suka tarbesu da gaggawa aka Shiga duba Afnan.' Wanda Bassam babu abunda yakeyi sai safa da marwa, kalil yake kwantar masa da hankali." Likitoci sunyi mata aune aune anyi mata awon fitsari da jini, sun tabbatar da tana d'auke da ciki na tsawon wata biyu." Likita yana bud'e k'ofa ya fito, Bassam yayo kansa yana tambayarsa, "docter meya sameta?" Meke damunta?" Ta farfad'o ne?" Likita yace "kwantar da hankalinka, ta farka kuma munyi mata kwaje kwaje mungano matarka tana d'auke da ciki na tsawon wata biyu." Wani irin ihu Bassam ya kurma ya duk'a ya d'auki likitan yashiga juyashi a cikin asibitin, likita sai naiman agaji yakeyi yanaso ya kwace kansa a wurin Bassam da kyar yasamu ya saukeshi, da gudu likita ya bar wurin.". Yana saukeshi Yayo wurin kalil yana dariya yana murna wadda kalil bai tab'a ganin dariya Bassam hakan ba." D'aukar kalil yake nemanyi, kalil yaja baya had'ida nad'e hannunsa yace "wlh duk ka d'aukeni sai na suka maka k'ulli.👊 Naga alamar sukakeyi ka zare lokaci d'aya." Suka sanya dariya gaba d'ayansu Bassam yace " ba doleba na kusan zama Abba." A nan kalil yake masa murna Allah ya inganta." Kai tsaye yanufi wurin Afnan d'in dake kwance tana barci anyi mata alurar barci." Gefenta Bassam ya zauna ya tsura mata ido yana kallonta cike da so, yana murmushi." Wayarsa ya d'auka yakira maimartaba yake mashi Albishir , sarki yayi murna sosai wanda hakan ya kasa b'oyuwa a fuskarshi." Yace "da zarar ta farka taji sauki sudawo gida, idan ta kuma murmujewa saisu koma idan suna buk'atar hakan." Sarki ya aika aka kira masa Anna yayi mata Arbishir abunda yarima ya fad'a masa, Anna taji dad'i kuma tayi murna sosai tareda Addu'ar Allah ya sauketa lafiya." ************ Sarkin gida a gaban hajiya zainab kurfane yace "ranki ya dad'e matar yarima saratu, duk ta sallami ma'aika tanta daga sashinta narasa dalili." Hajiya zainab tayi murmushi tace "samun wuri abunda ba'a tabayi a gidan nan ba." Kaje mata cikin siyasa da dubara irin taka kaji meye dalilinta metake shukawa a sashin nata, da batason ganin mutane a cikinsa." Sarkin gida yace angama ranki ya dad'e." Saratu da Alhaji Aminu suna kwance suna farantawa junansu rai, daga sama sukaji ana kwankwasa masu d'aki." Ai tuni suka sauka akan gado zuna rige rigen saka kaya hankalinsu a tashe yake." Alhaji Aminu ya b'oye toilet saratu ta zauna a kan kujera tace waye?" Ya shigo." Sarkin gida yashiga da sallama ya durk'usa gabanta." Had'a ido da ita yayi yashiga karantar wani Abu a tare da ita, yace "ranki ya dad'e nashigo ne mu gaisa ya gida?" "Lafiya galau tace had'ida had'e fuska tace karka kuma yimun hakan idan INA barci bana son a tadani, wannan dalilin yasa na sallami ma aikatana saboda ina da buk'atar hutu." "Kiyi hakuri ranki ya dad'e tuba nakeyi sai anjima ki huta lafiya ya tashi ya fita." Fitarsa ke da wuya Alhaji Aminu ya fito ya cirewa saratu kamfensa a kanta, Ta xare ido rud'ewa da sukayi yasa ta d'ora k'aramin wandonsa a kanta." Ta dube Alhaji Aminu tace "inaga ya gane ko?" Ya fahimci kamfen namijine akaina ko?" Yace "inaga bai ganeba." Tace "idan ya gane munshiga uku... Yace "bai ganeba nagaya maki." Tace "ina tsoron asirinmu ya Tonu, kasan hukuncinmu idan ankamamu?" Yaca "A'a." Tace "kashemu za'ayi." "Kisa?" Nima kasheni za'ayi?" "Eh mana batare mukayi ba." Ina matsayin matar d'an sarki kuma a kamani ina zina." Ta d'aure fuska ganin hankalin Alhaji Aminu ya tashi, tace "kana nufin ba sona kakeyiba, Meye a ciki Dan mun mutu saboda son da mukeyiwa junanmu." Ya had'iye miyau yace "gara dai nafita tunkafin asirimun ya tonu, sarki fa Aminina ne." Tace "bazaka fitaba Dan bangaji da kaiba idan kuma kayi yunkurin fita kud'inda na baka sai ka dawomin da abuna." Shuru yayi yana tunanin bak'uddan kud'in da take bashi, idan ta karb'e ai yayi asara." Amma kuma wake son zama da irin saratu, koba Dan muninta ba tanada rashin ni'ima, gata da k'arfi tamkar doki." Shin ya yarima yakeyi da ita ne?" idan suna jima'i gata bata gajiya duk jarabarsa saita k'ureshi sai yayi da gaske take kyaleshi." Bai ankaraba yaji ta jawoshi ta jefashi kan gado." **************** Bayan awa biyu Afnan ta farka, bud'e idonta ke da wuya sai akan Bassam, yasakar mata murmushi, itama ta sakar masa, yayo kanta ya d'an dafa cikinta yace Angel na kusan zama baba, kin kusan haifa min 'ya'ya masu kama dake." Murmushi tayi had'ida rufe idonta, tace "nidai ka kaini wurin Anna." Yace karki damu tun da kinji sauki gobe goben nan zamu koma gida, idan kika murmuje sai mu dawo tunda na lura da yanayin garin yayi maki." Jirgin k'arfe hud'u suka shigo suka dawo gida Nigeria, ba Wanda yasan da dawowarsu sai sarki, Dan haka ya tura da motoci aka d'aukosu." Suna shiga gidan, kai tsaye Afnan wurin Anna ta nufa, Anna na ganinta tashiga murna, Ta turo baki tace Anna yunwa nakeji, kidafa min indomie irin wadda kike dafa min da kuma farfesun kifi." Anna tace Angama d'iyata, yanzun nan zakici indomie." Bassam na ganin tashige d'akin Anna ya dubeta yayi murmushi had'ida girgiza kai yanufi nashi d'akin, Ganin baiga kowa na shawagiba, ya shiga tambayar kansa "ko lafiya meke faruwa? Ba kuyangu ba bayi?" Ya fasa shiga d'akinsa yanufi wurin saratu domin ya tambayeta ko lafiya?" Yana tunkarar d'akinta ya farajin sautin kuwarta, Gabansa ya yanke ya fad'i k'afafunshi suka kusan kasa d'aukarsa yana Addu'ar Allah yasa mafarki yakeyi abunda ya juyowa kunnensa." Bamafarki bane sautin kuwarta ne, kuma da Alama tare take da wani namijin suna aikata zina." Kai tsaye yanufi d'akin had'ida murd'a k'ofar." K'ofar ta bud'e, a hankali ya fara tura kansa gabansa na fad'uwa, Mai zai gani saratu ce tsirara haihuwa uwarta, Alhaji Aminu nata rabama mata aiki sai kuwa takeyi, cikinsu ba wanda yasan a bud'e d'akin Kansa yaji ya fara sara mashi yashiga fad'in innalillahi wa'innailaihirraji'un." Ya jawo k'ofar a hankali ya rufesu, da Sauri ya nufi d'akinsa ya d'auko makulli da kwad'o ya rufesu, duk basu San abunda akeyiba." [3/6, 10:22 AM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *64* Jinginewa yayi a bakin k'ofar d'akin inda har zun yana jiyo kuwa da santin saratu." Idonshi yashiga zubar da hawaye kuka yakeyi kamar macce." A hankali ya bar wurin ya dinga tafiya kamar wanda kwai ya macewa a ciki, Kai tsaye fada yanufa wurin maimartaba." Sarki na ganinshi cikin wannan yanayin yasan ba lafiya, ya bada umurnin a watse zaiyi magana da yarima." A nan take kowa ya watse, Bassam na ganin hakan yaje da sauri ya fad'a jikin maimartaba yasaki kuka mai sauti." Hankalin maimartaba ya tashi ya tallaboshi ya dubi idon yarima yaga tabbas kuka yakeyi, Ya cikin tashin hankalin yace "yarima ke kuka?" Magajin sarki maike faruwa?" Rabonda naga hawayenka tun kana yaro. Ko a lokacin ba k'aramin Abu kesanya ka kuka ba." Ya rik'oshi ya zaunan dashi yace "daina kuka sassauwa zuciyarka kafad'a min meya faru." Cikin k'arfin hali yace "Abba matata ta sunna da kwarto a kan gadona, Wanda muke raya sunnar manzun Allah (SAW) Sauri sarki ya mik'e tsaye yace "kwarto a gidan na?" Kuma matar magajin sarki?" Yarima tashi mutafi, na rantse da Allah kowace CE ko wanene sai hukunci ya hau kansa tunda suka sanya zubar hawaye a idonka." Suka mik'e suka fito sarki yace "gaba d'aya fadawansa da kuyangunsa su biyo bayansu." Haka suka jera suka nufi sashin yarima." Hajiya zainab na hango tawagar sarki yanufi sashin yarima, kuma ta hango yarima a tare dashi. Tace "tabbas ba lafiya to meke faruwa?" Me kuma ya dawo da yarima daga tafiyar da yayi bai mutuba." Tace "bari naje naji abunda ke faruwa Dan naga alamar ba lafiya ba." Da saurinta ta nufi wurin." Afnan tafito d'akin Anna da plete d'in Indomie a hannunta, tan fad'in " Anna bari natafi wurin my prince muci atare nasan yana tare da jin yunwa." Anna ta mere baki tace "kudai kukasani, kunata faman canzawa junanku suna, shiyace maki wai Angel ke kuma ko Prince ☹ yarage naku." Afnan ta fito tana dariya, tana cewa "Anna yaushe kika fara sa'ido kuma." Fitowar da zatayi taci karo da tawagar fadawa da kuyangu da kuma sarki gaba d'aya da Prince, abunda bata tab'a ganiba tun zuwanta gidan." Acan kuma ta hango hajiya zainab tafe tareda sarkin gida suna sauri harda d'an had'awa da gudunsu." Mamaki tashigayi tana tambayar kanta lafiya?" Komawa tayi da baya, Tashige d'akin Anna, "Anna tace me kuma ya dawo dake?' "Anna INA ganin gidan nan ba lafiya Dan naga tawagar fadawa tareda maimartaba sun nufi sashin saratu." Anna tace "subahanallahi to meke faruwa. Zo sanya Alkyabbarki mutafi mugani." Haka suka jera Anna na gaba Afnan na baya suka nufi sashin Saratu." A can wurin Kaka kuma Daren jiya babu abunda take mafarki sai Afnan, wayewar safiyar yau, tashirya tayiwa malam iro sallama tare da matansa tace "gidansu Afnan zataje daren jiya tayita mafarkinta ta gaji da ana Sanya mata rana za'azo a d'auketa a kaita ta ganota, to yau kam ta shirya tafiya zatayi." Malam iro yayi mata rakiya zuwa bakin titi tasamu abun hawa, tanufi gidan, sarautar." bata sha wahalaba wurin shiga gidan kasan cewa fadawan dake gadin bakin k'ofar duk sun santa wani lokacin maimartaba yana aikasu wurinta su kai mata Sak'o, wannan dalilin yasa sukasan kowacece ita da yanda take a gidan." Sai girmamata akeyi ana zuba mata kirari, sannan d'aya daga cikin fadawan yayi mata rakiya har gafda sashin yarima ya juyo ita kuma ta shiga." Maimartaba yana zuwa gafda da bakin k'ofar yaji kuwa na tashi alamar santin dad'i akeyi, yarima ya runtse idonsa, Maimartaba ya mik'awa yarima hannu yace "bani makullin d'akin, Yajuya ya kalli a yarin fadawa yace dana bud'e d'akin kowa ya biyoni ya shigo, karaf sai a kunnen Kaka da zuwanta kenan tace ko lafiya?" Yashiga k'ok'arin bud'e d'akin yana bud'ewa ko ya fara shiga sannan yarima sai hajiya zainab da Anna da Afnan, Sannan gaba d'aya a yarin fadawa da kuyangu suka shiga Kaka ta biyo bayansu." Saratu kwance tsirara Alhaji Aminu tsirara ya na kanta, sai ganin mutane sukayi mak'il zagaye dasu." Tirk'ashiii!!!! Alhaji Aminu ya sauka kanta, tashiga turashi k'asa sai da ya fad'o daga kan gadon." Sarki ya daki gaba cikin tashin hankali yace "Alhaji Aminu da matar d'ana yarima?" Aminina a kan shinfid'ar d'ana yana cimasa Amana?" Kaico duniya." A tare suka jawo zanen gado suka rufe jikinsu. Fuskokinsu cike da tashin hankali." Afnan tanajin sarki yace Alhaji Aminu ta kuma dubeshi da kyau, ta tabbatar da tabbas shine azzalumin da tadad'e tana Neman Allah ya cika mata burinta a kanshi." Ta matso kusa gareshi idonta yana zubar da hawaye, tace "Allah ya kamaka azzalumi ba yaudari basik'i Wanda bai d'auki zalunci a cin amana a bakin komaiba." Ta juya ta kalli maimartaba ta d'an russuna, tace "ranka ya dad'e wannan azzalumin Wanda make kira da Amininka shine yaci Amanarmu ya ha incemu ya kwace dukiyar mahaifina yace dukiyarsa ce sannan daga k'arshe ya kwace gidan da muke ciki ya koromu garin kano mukadawo gombe da zama." Ina ma Kaka zata ganka a cikin wannan halin da tayi a lawadai da rayuwa irin ta." Bassam ya jawota ya rungumeta yana bubbugar bayanta alamar tayi shuru." Dakyar kaka tasamu ta kutso cikin taron mutanen dake k'ofar d'aki sunyi cincirindo." Tana shigowa taci garo da Alhaji Aminu tace "dama mai hali baya fasa halinshi, duk inda Azzalimi yake k'arshinsa jin kunya." Tad'aga kai sukayi ido biyu da Sarki. Tace Alhaji Ahmad!! Yace Mama!! Dama Afnan 'yar gidan Alhaji Aminu ce?" Ya kuma juya ya kalli Alhaji Aminu yace "tabbas kacika babban macuci maciye Amana." Kaci Amanata kaci Amanar d'ana kaci Amanar marainiyar Allah wadda kake k'arya da ita kana amsa kud'i a hannununa, sannan kuma kaci Amanar kanka, Dan wlh na rantse da Allah sai na hukuntaka hukunci mai tsanani, dakai da wannan mummunar abar." Babu abunda idon saratu da Alhaji Aminu yake fitarwa sai hawayen nadama." Ya dubi Saratu yace d'an Adma butulu. Kina matsayin baiwa kinsamu yanci d'an sarki ya aureki har kike iya cin Amanarsa." Dama makircin da kike k'ullawa kenan tun yarima yana da rai kenan, Jikin saratu sai karkarwa yakeyi kamar mai jin zazzab'i, idanunta sunyi jajir sun k'ank'ance, "ranka ya dad'e kayi min rai don girman Allah na tuba." Bai kulata ba ya dubi Alhaji Aminu yace "Tun yaushe kuke tare?" Ya kasa magana ya had'a hannayensa guda biyu yana rok'on gafara" Sarki yace "bakaji tambayata ba?" D'aya daga cikin fadawan yada masa tsawa yace bakiji tambayar sarki ba, maciye Amana." Jikinsa na rawa yace "najiya, mun dad'e tare da ita, budurwa tace tun a kano, Na d'auki kusan shekara biyar bangantaba sai lokacin da nakawo maka ziyara naci karo da ita a nan gidan, nayi mmki da tace Yarima take aure saboda saratu tsohuwar yar barikice tsohuwar karuwace, tasan dad'in d'iya maza." Marinda yarima ya kwad'a mashi shiyasanyashi yaja bakinshi yayi shuru." Hajiya zainab ta matso kusa da Saratu ta zungureta tace "ni dama tunda wannan Abar tashigo gidan nan naji ban natso da itaba, naji na tsaneta Nayi mamakin da yarima yaganeta yaji yana sonta har ya aure, ta kai mata mari tace munafuka kawai yau k'aryarki ta k'are." Sai a lokacin Yarima yayi gyaran murya yayi magana yana rungume da Afnan, ya dubi Fadawa yace " tallabesu haka kufitar mun dasu acan gaban fada, Ku ajiye munso tsakar fili, Kucewa sarkin hukunci yafara yimasu bulala dubu dubu tare da hukunci mai tsananani kafin safiya ta waye a zartar masu da hukunci dai dai laifinsu, kuma akar a basu kaya susa a barsu haka." Sukace Angama ranka ya dad'e, suka tallabesu suka sanyasu gaba cikin zanen gado d'aya suna tafiya fadawa na tsine masu Albarka." ******************** Kafin safiya ta waye sarki ya tura fadawa garin kano gaba d'aya aka tattaro dukiyar Alhaji Amin a ka kawo masa." Daren ranar labari ya gauraye gidan sarautar ankama matar yarima da kwarto tana cin Amanar sa." Yarima ya sanya shela gobe da safe misalin k'arfe "8:am kowa ya hallara gaban fada za'a zartar masu da hukunci." Ba wanda ya runtsa yayi barci daga sarki har yarima. Mussam Afnan da taketa kukan dad'i tana tsakiyar Anna da Kaka zaune suna hira, kaka tana bawa Anna labarin irin cin Amanar da Alhaji Aminu yayi masu." Safiya na wayewa misalin k'arfe 8:am kowa ya hallara gaban fada, kuyangu da bayi kai duk wani mai aiki a cikin gidan sai da ya hallara, gasu tsakar fili kowa yana kallonsu." Sarki ya fito ya tare da yarima ya tsaya, yayi kyaran murya, ya fara magana." " Aminu a bisa cuta da cin Amana daka aikata min, ka daffareni kud'ad'e a wad'anda nake baka kana cewa kana taimakawa iyalan Alhaji Aminu bisa k'arya kakeyi. To ni nayafe maka." Amma dukiyar marainiya bazata tab'a yafe maka ba, Jiya kafin safiya ta waye, matura garin kano an d'auko min duk wani Abu da nasan Alhaji Ibrahim ya mallaka a zo min dashi, Dan haka za a bawa marainiya hak'inta gadon mahaifinta Wanda ya mutu ya bar mata kasa k'asa ka danne saboda kana Azzalumi." yanuna masa wata jaka yace "wannan itace kaddarar Afnan, ya kira Afnan da Kaka ya mik'a mata gaban mutane, Afnan ta runsuna ta karb'a tana godiya had'ida zubar da hawaye." Sarki ya dubi yarima yace sauran "hukunci na hannunka magajin sarki." Yarima ya matso ya dubi fuskar Saratu cikin tsana da bak'in ciki, ya kuma d'aga kai ya dubi bayinta da kuyangunta yace Ku matso kusa duk Wanda yasan wannan mummunar ta tab'a cin amanarsa ko zaluntarsa ni nace kuyi mata dukan tsiya har sai kunrama, Ku had'a harda wancan muna fukin." Aikuwa suka hausu da duka, baji bagani, saida suka fitar masu da jini sannan yarima yayi gyaran murya yace "Kugyalesu haka. Ya dubi jakadiya yace " "Jakadiya d'auko masu kayan bayi jibasu su sanya." Aka d'auko masu, suka tub'e gaban bainar jama'a suka sanya." Yarima yace "sarkin hukunci ya matso yace "Naam ranka ya dad'e." Yace ku d'aukesu kubar garin nan dasu Ku kaisu can cikin daji Inda ake zuwa kama bayi, Akamasu atafi dasu can wata masarautar suyi aikin baita, su wulak'anta su zama abum tausayi." Ya kuma kallon Saratu ya matso kusa da ita ya sauke mata bari biyu masu kyau yace na sakeki saki uku Kada Allah ya kuma had'ani da mummunar fuskarki." Yace kud'aukesu kutafi dasu Ku wurgar dasu can na daina ganinsu." Haka aka d'aukesu aka wurgasu cikin motar d'aukar dabbobi aka tafi dasu." Bye bye Sarah Baby😂😂😂😂😂 [3/6, 10:26 AM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *64* Jinginewa yayi a bakin k'ofar d'akin inda har a lokacin yana jiyo sautin kuwa da santin saratu." Idonshi yashiga zubar da hawaye, kuka yakeyi kamar macce." A hankali ya bar wurin ya dinga tafiya kamar wanda kwai ya macewa a ciki, Kai tsaye fada yanufa wurin maimartaba." Sarki na ganinshi cikin wannan yanayin yasan ba lafiya ba akwai abnda ke damunsa, Ya bada umurnin kowa ya watse zaiyi magana da yarima." A nan take kowa ya watse, Bassam na ganin hakan yaje da sauri ya fad'a jikin maimartaba yasaki kuka mai sauti." Hankalin maimartaba ya tashi ya tallaboshi ya dubi idon yarima yaga tabbas kuka yakeyi, cikin tashin hankali yace "yarima ke kuka?" Magajin sarki maike faruwa?" Rabonda naga hawayenka tun lokacin da kana yaro. Ko a lokacin ba k'aramin Abu kesanya ka kuka ba." Ya rik'oshi ya zaunan dashi yace "daina kuka sassautawa zuciyarka kafad'a min meke faruwa" Cikin k'arfin hali yace "Abba matata ta sunna da kwarto a kan gadona, Wanda muke raya sunnar manzun Allah (SAW) Da Sauri sarki ya mik'e tsaye yace "kwarto a gidan na?" Kuma matar magajin sarki?" na rantse da Allah kowace CE ko wanene sai hukunci ya hau kansa tunda suka sanya zubar hawaye a idonka." Suka mik'e suka fito sarki yace "gaba d'aya fadawansa da kuyangunsa su biyo bayansu." Haka suka jera suka nufi sashin yarima." Hajiya zainab na hango tawagar sarki yanufi sashin yarima, kuma ta hango yarima a tare dashi. Tace "tabbas ba lafiya to meke faruwa?" Me kuma ya dawo da yarima daga tafiyar da yayi bai mutuba." Tace "bari naje naji abunda ke faruwa Dan naga alamar ba lafiya ba." Da saurinta ta nufi wurin." Afnan tafito d'akin Anna da plete d'in Indomie a hannunta, tana fad'in " Anna bari natafi wurin my prince muci tare nasan yana tare da jin yunwa." Anna ta mere baki tace "kudai kukasani, kunata faman canzawa junanku suna, shiyace wai Angel ke kuma ko Prince ☹ yarage naku." Afnan ta fito tana dariya, tana cewa "Anna yaushe kika fara sa'ido kuma." Fitowar da zatayi taci karo da tawagar fadawa da kuyangu da kuma sarki gaba d'aya da Prince, abunda bata tab'a ganiba tunda tazo gidan nan Acan kuma ta hango hajiya zainab tafe tareda sarkin gida suna sauri harda d'an had'awa da gudunsu." Mamaki tashigayi tana tambayar kanta lafiya?" Komawa tayi da baya, Tashiga d'akin Anna, "Anna tace me kuma ya dawo dake?' "Anna INA ganin gidan nan ba lafiya Dan naga tawagar fadawa tareda maimartaba sun nufi sashin saratu." Anna tace "subahanallahi to meke faruwa. Zo sanya Alkyabbarki mutafi mugani." Haka suka jera Anna na gaba Afnan na baya suka nufi sashin Saratu." A can wurin Kaka kuma Daren jiya babu abunda take mafarki sai Afnan, wayewar safiyar yau, tashirya tayiwa malam iro sallama tare da matansa tace "gidansu Afnan zataje daren jiya tayita mafarkinta ta gaji da ana Sanya mata rana za'azo a d'auketa a kaita, to yau kam ta shirya tafiya zatayi." Malam iro yayi mata rakiya zuwa bakin titi tasamu abun hawa, tanufi gidan, sarautar." bata sha wahalaba wurin shiga gidan kasan cewa fadawan dake gadin bakin k'ofar duk sun santa wani lokacin maimartaba yana aikensu wurinta su kai mata Sak'o, wannan dalilin yasa suka san kowacece ita da yanda take a gidan." Sai girmamata akeyi ana zuba mata kirari, sannan d'aya daga cikin fadawan yayi mata rakiya har gafda sashin yarima ya juyo ita kuma ta shiga." Maimartaba yana zuwa gafda da bakin k'ofar yaji kuwa na tashi alamar santin dad'i akeyi, yarima ya runtse idonsa, Maimartaba ya mik'awa yarima hannu yace "bani makullin d'akin, Yajuya ya kalli a yarin fadawa yace " dana bud'e d'akin kowa ya biyoni ya shigo, karaf sai a kunnen Kaka da zuwanta kenan tace ko lafiya?" Yashiga k'ok'arin bud'e d'akin yana bud'ewa ya fara shiga sannan yarima sai hajiya zainab da Anna da Afnan, Sannan gaba d'aya a yarin fadawa da kuyangu suka shiga Kaka ta biyo bayansu." Saratu kwance tsirara Alhaji Aminu tsirara ya na kanta, sai_ ganin mutane sukayi mak'il zagaye dasu." Tirk'ashiii!!!! Alhaji Aminu ya sauka kanta, tashiga turashi k'asa sai da ya fad'o daga kan gadon." Sarki ya doki gaba cikin tashin hankali yace "Alhaji Aminu da matar d'ana yarima?" Aminina a kan shinfid'ar d'ana yana cimasa Amana?" Kaico duniya." A tare suka jawo zanen gado suka rufe jikinsu. Fuskokinsu cike da tashin hankali." Afnan tanajin sarki yace Alhaji Aminu ta kuma duban shi da kyau, ta tabbatar da tabbas shine azzalumin da tadad'e tana Neman Allah ya cika mata burinta a kanshi." Ta matso kusa gareshi idonta yana zubar da hawaye, tace "Allah ya kamaka azzalumi ma yaudari basik'i Wanda bai d'auki zalunci da cin amana a bakin komaiba." Ta juya ta kalli maimartaba ta d'an russuna, tace "ranka ya dad'e wannan azzalumin Wanda kake kira da Amininka shine yaci Amanarmu ya ha incemu ya kwace dukiyar mahaifina yace dukiyarsa ce sannan daga k'arshe ya kwace mana gidan da muke ciki ya koromu garin kano mukadawo gombe da zama." Ina ma Kaka zata ganka a cikin wannan halin da tayi alawaddai da rayuwa irin ta." Bassam ya jawota ya rungumeta yana bubbugar bayanta alamar tayi shuru." Dakyar kaka tasamu ta kutso cikin taron mutanen dake k'ofar d'aki sunyi cincirindo." Tana shigowa taci karo da Alhaji Aminu tace "dama mai hali baya fasa halinshi, duk inda Azzalumi yake k'arshinsa jin kunya." Tad'aga kai sukayi ido biyu da Sarki. Tace Alhaji Ahmad!! Yace Mama!! Dama Afnan 'yar gidan Alhaji Aminu ce?" Ya kuma juyawa ya kalli Alhaji Aminu yace "tabbas kacika babban macuci maciye Amana." Kaci Amanata kaci Amanar d'ana kaci Amanar Aminta ka kuma ci Amanar marainiyar Allah wadda kake k'arya da ita kana amsa kud'i a hannununa, sannan kuma kaci Amanar kanka, Dan wlh na rantse da Allah sai na hukuntaka hukunci mai tsanani, dakai da wannan mummunar abar." Babu abunda idon saratu da Alhaji Aminu yake fitarwa sai hawayen nadama." Ya dubi Saratu yace d'an Adma butulu. Kina matsayin baiwa kinsamu yanci d'an sarki ya aureki har kike iya cin Amanarsa." Dama makircin da kike k'ullawa kenan tun yarima yana da rai kenan, Jikin saratu sai karkarwa yakeyi kamar mai jin zazzab'i, idanunta sunyi jajir sun k'ank'ance, "ranka ya dad'e kayi min rai don girman Allah na tuba." Bai kulata ba ya dubi Alhaji Aminu yace "Tun yaushe kuke tare?" Ya kasa magana ya had'a hannayensa guda biyu yana rok'on gafara" Sarki yace "bakaji tambayata ba?" D'aya daga cikin fadawan yadaka masa tsawa yace bakaji tambayar sarki ba, maciye Amana." Jikinsa na rawa yace "najiya, mun dad'e tare da ita, budurwa tace tun a kano, Na d'auki kusan shekara biyar bangantaba sai lokacin da nakawo maka ziyara naci karo da ita a nan gidan, nayi mmki da tace Yarima take aure saboda saratu tsohuwar yar barikice tsohuwar karuwace, tasan dad'in d'iya maza." Marinda yarima ya kwad'a mashi shiyasanyashi yaja bakinshi yayi shuru." Hajiya zainab ta matso kusa da dad'inSaratu ta zungureta tace "ni dama tunda wannan Abar tashigo gidan nan naji ban natso da itaba, naji na tsaneta Nayi mamakin da yarima yaganeta yaji yana sonta har ya aure, ta kai mata mari tace munafuka kawai yau k'aryarki ta k'are." Sai a lokacin Yarima yayi gyaran murya yayi magana yana rungume da Afnan, ya dubi Fadawa yace " tallabesu kufitar mun dasu acan gaban fada, Ku ajiye munso tsakar fili, Kucewa sarkin hukunci yafara yimasu bulala dubu dubu tare da hukunci mai tsananani kafin safiya ta waye a zartar masu da hukunci dai dai laifinsu, kuma a basu kaya susa a barsu haka." Sukace Angama ranka ya dad'e, suka tallabesu suka sanyasu gaba cikin zanen gado d'aya suna tafiya fadawa na tsine masu Albarka." ******************** Kafin safiya ta waye sarki ya tura fadawa garin kano gaba d'aya aka tattaro dukiyar Alhaji Aminu a ka kawo masa." Daren ranar labari ya gauraye gidan sarautar ankama matar yarima da kwarto tana cin Amanar sa." Yarima ya sanya shela gobe da safe misalin k'arfe "8:am kowa ya hallara gaban fada za'a zartar masu da hukunci." Ba wanda ya runtsa yayi barci daga sarki har yarima. Mussam Afnan da taketa kukan dad'i tana tsakiyar Anna da Kaka zaune suna hira, kaka tana bawa Anna labarin irin cin Amanar da Alhaji Aminu yayi masu." Safiya na wayewa misalin k'arfe 8:am kowa ya hallara gaban fada, kuyangu da bayi kai duk wani mai aiki a cikin gidan sai da ya hallara, gasu tsakar fili kowa yana kallonsu." Sarki ya fito tare da yarima ya tsaya, yayi kyaran murya, ya fara magana." " Aminu a bisa cuta da cin Amana daka aikata min, ka daffareni kud'ad'e da dama wad'anda nake baka kana cewa kana taimakawa iyalan Alhaji Ibrahim bisa k'arya kakeyi. To ni nayafe maka." Amma dukiyar marainiya baza'a tab'a yafe maka ba, Jiya kafin safiya ta waye, natura garin kano an d'auko min duk wani Abu da nasan Alhaji Ibrahim ya mallaka a zo min dashi, Dan haka za a bawa marainiya hak'inta gadon mahaifinta Wanda ya mutu ya bar mata kasa k'afa ka danne saboda kana Azzalumi." yanuna masa wata jaka yace "wannan itace kaddarar Afnan, ya kira Afnan da Kaka ya mik'a mata gaban mutane, Afnan ta runsuna ta karb'a tana godiya had'ida zubar da hawaye." Sarki ya dubi yarima yace sauran "hukunci kuma ya na hannunka magajin sarki." Yarima ya matso ya dubi fuskar Saratu cikin tsana da bak'in ciki, ya kuma d'aga kai ya dubi bayinta da kuyangunta yace Ku matso kusa duk Wanda yasan wannan mummunar ta tab'a cin amanarsa ko zaluntarsa ni nace kuyi mata dukan tsiya har sai kunrama abunda tayi maku , Ku had'a harda wancan muna fukin." Aikuwa suka hausu da duka, baji bagani, saida suka fitar masu da jini sannan yarima yayi gyaran murya yace "Kugyalesu haka. Ya dubi jakadiya yace " "Jakadiya d'auko masu kayan bayi kibasu su sanya." Aka d'auko masu, suka tub'e gaban bainar jama'a suka sanya." Yarima yace "sarkin hukunci ya matso yace "Naam ranka ya dad'e." Yace ku d'aukesu kubar garin nan dasu Ku kaisu can cikin daji Inda ake zuwa kama bayi, Akamasu atafi dasu can wata masarautar suyi aikin bauta, su wulak'anta su zama abun tausayi." Ya kuma kallon Saratu ya matso kusa da ita ya sauke mata bari biyu masu kyau yace na sakeki saki uku Kada Allah ya kuma had'ani da mummunar fuskarki ko a lahira." Yace kud'aukesu kutafi dasu Ku wurgar dasu can na daina ganinsu." Haka aka d'aukesu aka wurgasu cikin motar d'aukar dabbobi aka tafi dasu." Bye bye Sarah Baby😂😂😂😂😂 [3/6, 10:35 AM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *65* Ana tafiya dasu kowa ya watse ya kama gabansa suna la'antarsu tareda tsine masu Albarka." Fada maimartaba ya nufa, yayi wa yarima magana da Afnan da Kaka yace "su biyoshi yanaso zaiyi magana dasu." Fada sarki a kan kujerar mulkinsa, Gaba d'aya suna k'asa sun zauna had'ida sunkuyar da kansu." Yayi murmushi yace "Mama kiyi hak'uri na banzar da rayuwarku, Ban rik'e Amana da Aminta dake tsakanina da babban Aminina Alhaji Ibrahim ba." Nayi sakaci dana bar rayuwarku cikin garari kuna ta wahala a wurin wancan Azzalumin." Kuyafe min, daga yau k'arshen wahalarku da k'unci yazo k'arshe, Ku d'auka cewa Alhaji Ibrahim ya mutu, kuma ya dawo." Kaka tace "mungode Ranka ya dad'e, ko hakan kabarmu burinmu ya cika, munga k'arshen Azzalumi." Kuma burin 'yarka Afnan ya cika domin a duniya bata da wani buri illah ta kwato dukiyarta a hannun Azzalumi Alhaji Aminu." Ya dubi Afnan yace "matso nan 'yata ta matso kusa dashi tana murmushi. Yace tun lokacin da nasanya idona akanki nakeji a jikina cewa ke jinin Aminina ce, Amma Wancan Azzalumin yake kawar min da tunanin hakan, sai nake d'auka wata k'ila kamace kukayi dashi." Ya dubi zoben hannunta ya dubi zoben hannunshi iri d'aya danashi, yayi murmushi yace "Allahu Akbar, wannan zuben dake hannuki 'yata lokacin da mukatafi aikin Hajji da Alhaji ibrahim muka sayeshi a tare." Lokacin ya d'auki Alk'awarin cewa da zarar yayi aure ya haihu, to duk abunda aka Haifa masa sai ya sanya wannan Zuben a hannunshi." Kaka ta matso hawaye tace "tabbas anyi hakan, lokacin da zaiyi tafiya dubai kamar yasan ba zai dawoba, ya iskoni har cikin d'akina ya ciro Zoben yabani yace "mama gashi ki ajiye min a wurinki nasan kinfini iya ajiya, idan aka haifa min "ya Mace ko namiji, a sanya masa a hannunshi, akuma shaida mashi cewa babanshi yana sonshi." Afnan ta fashe da kuka tana fad'in "Abba nima ina sonka Allah ya jik'anka ya haskaka ma kwancinka." Suka Amsa da "Amin." Bassam ya dawo kusa gareta ya kamata ya kwantar da ita a kafad'arsa yana d'an bubbugar bayanta alamar tayi shuru." Sarki da Kaka suka bisu da Kallo suna murmushi." Sarki yakira sunan Yarima, Yace "yarima ga Amana nabaka ta k'aunarka kuma 'yar uwarka, Ka Kula da ita kabata farin ciki Wanda zaisanya nayi Alfahari daku." Yarima ya runsunar da kai yace to Abba na karb'i Amanarka in Allah ya yarda Afnan bazata tab'a kokawa ba." "Allah yayi maku Albarka, sarki ya fad'a." Suka amsa da "Amin." Sarki yace "sai maganar dukiyar Afnan, wannan jakar dana bata takardune na kamfanonin Da takardun gidaje da filaye, dakuma chark na kud'i kusan biliyan hamsin da uku, to ya kuke ganin za'ayi?" Kaka tace "duk hukuncin da kayanke ranka ya dad'e duk d'aya." Sarki ya dubi Afnan yace "'yata zab'i na wurinki ki fad'I duk abunda kikeso ko kike da buri da zakiyi da dukiyar ki." Afnan ta sunkuyar da kai tace "Abba burina na farko shine na taimaki marayu marasa k'arfi. Na ginawa mahaifana masallaci da makarantu, Allah ya kai lada a cikin kabarinsu." Sannan daga k'arshe sauran kud'in a bawa yarima, shi yasan abunda ya dace yayi min dasu, da duk wani Abu nawa." Kaka tace "tabbas kinkawo shawara mai kyau Allah yajik'an wad'anda suka rasu." Sarki yace "Yarima Allah yabaka ikon kula da dukiyar marainiy." Suka amsa da "Amin gaba d"ayansu." Sannan kaka ta mik'e tayi masu sallama zata koma gida." Afnan da yarima suka shiga yimata magiya a kan tayi zamanta kusa dasu, tace "bazata zaunaba." Suka dube sarki a kan ya tayasu rok'onta akan ta zauna." Zai magana kenan yaji tace "zan zauna amma ba yanzun ba, sai kin haihu." Suka sanya dariya sukace "to Kaka Allah yanuna mana." Anan sukayi sallama sarki ya Sanya aka kaita gida aka kuma cika ta da kayan more rayuwa." ************** Tun a wannan ranar Afnan tazama 'yar gaban goshin Sarki, baya son ganin b'acin ranta." Wanda hakan yana yiwa hajiya zainab bak'in ciki, tanaji tana gani Afnan zata amshe mata tauraruwa a gidan. Duk inda kashiga bayi da kuyangu sai hirar Alherin Afnan kawai akeyi." Gaba d'aya labarin Saratu yashafe a gidan kowa ya kama hidimar gabansa." Wata sabuwar soyayya ce ta kuma shiga tsakanin prince da Angel, wanda sai tarairayarta yakeyi, Da Zarar sunfara wasanni taga zai zarcewa zuwa wurin boos saitayi mashi dubara ta gudu tayi wurin Anna." Shi kuma abun yana damunsa gashi mtum ne mai yawan buk'ata." [3/6, 10:37 AM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *67* Hakan yaci gaba da yimata, da zarar taci kifi sai labari ya canza salo." Kusan sau hud'u kenan, Afnan ta rasa gane abunda ke damunta." Meyasa ta dainajin zafin abunda yarima yake mata, Kuma abun mmki ita ke nemanshi da kanta?" Bata mance duk abunda yake shiga a tsakaninsu mai yameta ne?" Ta tsinci kanta da jin kunyarsa saboda irin abubuwan da take yi mashi da kanta." Shima ya lura da hakan, amma Bai damu ba saboda yasan da a hayyacinta take da bazai sameta hakan ba." Baya gajiya da kasancewa da ita akoda yaushi saboda komai nata mai kyau ne da d'and'ano, Wuri d'aya yake tausaya mata saboda bata barcin dare, ko kad'an shiyasa yake kyaleta da rana." Idan suka Shiga bayan sallar isha'i babu wani Abu da sukeyi sai ba Kansu dad'i, Lallai yanzun suke amarci mai dad'i." Cikin kwana goma Afnan ta fara tunanin ko akwai abunda ake mata nabawa yarima kanta a sauk'ak'e?" A Daren yau kam cewa tayi bazataci komaiba A can wurin Anna taci abincinta ta k'oshi. Yarima ya gano yau akwai rigima kenan tunda tak'icin komai, Amma kuma sai ya shareta." Sukaita kallo har tafara hamma, taji batajin yanayin da takeji,tayi mmki Mik'ewa tsaye tayi ta wuce d'akin barcinsu, ta kwanta." Yarima yabi bayanta, yasan yau zaisha jinini kenan da raki, kuma bazai hak'uraba Dan ya shiryama yau." Haka ya bita yayita lallab'ata, har yasamu ya biya buk'atarsa cikin kwanciyar hankali, dajin dad'i." ba laifi, tafara sabawa Dan har tafara zomasa da wani sabon karatu wanda ya dad'e yana mamakinta." Zaman lafiya da kwanciyar hankali yaci gaba da wanxuwa a tsakaninsu suna son junansu suna tarairayar junansu, a gaban kowa suna iya nunawa junansu kulawa Da so da k'auna." Cikin Afnan Kuma sai girma yakeyi, Yayi mata kyau ta kuma cika tayi k'iba masha Allah." yanzun tashiga watan haihuwarta Wanda ake sanya mata haihuwa ko yau ko gobe, Tattali a wurin yarima da maimartaba da Anna abun ba'a magana." ***************** Da yamma yana kishingid'e a gadina, Anna tabata _juice_ tace ki tabbatar da yarima ya shashi akwai abunda nasaka mashi a ciki." "Na minene Anna?" Yasoni ni kad'ai?" "Jeki ki kaimashi Dan Allah na tsarine, Ta kama hanya tana tafiya, duk inda ta gifta kuyangu sai sannu ake mata saboda girman cikinta." Fuskarshi cike da fara'a ya hangota ya mik'e ya tarota ya rungumeta yasanyata a jikinshi yana mata sannu." Murmushi tayi tace " barka da hutawa my Prince." Cikinta ya shafa, "barka da zuwa my son, had'ida kaiwa cikin kiss, gaba d'aya sukayi dariya." Ta tsiyaya mashi _juice_ d'in a cup, ya tsaya yana kallonta yana kallon _juice_ d'in." Yace " _juice_ ne haka?" Tasaki fuska sosai ta k'ara matsowa kusa dashi, ta d'auki _cup_ d'in zuwa bakinsa, ya amshi kofin ya rik'e." Rashin gaskiya ya bayyana a tare da ita duk ta sukurkurce, Batun yauba ta lura idan ta kawo mashi _juice_ haka yakeyi sai ya dad'e yana kallon kofin kafin sai ya d'auka ya sha." Ya maida kofin ya ajiye, ya dubeta "Angel!!! Ya kira sunanta da murya mai taushi, "me kika saka a cikin _juice_ d'in nan?" Ta d'an zaro idonta daka kalleta zaka gano a tsorace take, idonsa a kanta ya rik'o hannunta, sai rawa yakeyi." "Ina saurarenki, ba wannan ne na farko ba, Waya baki shawarar sa min Abu a cikin _juice_ ?" "Uhm ban San komaiba." "Baxaki gaya minba?" Akwai abunda nake maki Wanda bakiso?" Kike so in daina?" A'a babu." Ta fad'a a sanyaye. "Meyasa to?" Tarasa abunda zata ce masa, tayi shuru." "Kiyi magana mana." Ya d'auki kofin zai kai bakinsa tace "kada kasha akwai......tayi shuru kuma." "Kina so ki mallakeni ne?" Tasaki baki tana kallonshi." "Bari insha ki mallakeni Angel." Tayi shuru tasa kanta k'asa, Ya shanye juice d'in ya ajiye kofin." Kallonshi takeyi, tace "ya akayi kasani?" Kema baki bani amsa ba, Dan haka nima bazan baki amsaba." "Anna ta koya maki?" Da sauri tace A'a ba ita bace." "Ina kika samu?" Ta matso kusa dashi sosai suna iya jin saukar numfashin juna, tace "inasonka baxan iya abunda zan zaluncekaba, ko kuma na cutar da kai. Ka yarda dani." "Nasani ai bance baki sonaba." To ka yarda banyi komaiba, yayi murmushin gefen baki yace "na yarda dake Angel bazaki cutar daniba." A ranta tace "sai nagayama Anna kada ak'ara sawa." A zahiri kuma hira sukeyi cike da nishad'i, al'amarin yarima yana bawa Afnan mamaki sai kace gaba nai akayi?" Ko dai akwai mai zuwa yana gaya masa?" Anna tana bata labarin Bassam tabbas ba k'aramin shiri akayi masaba sai yau ta tabbatar da hakan." Hira sukeyi suna dariya yana bata labarin d'anta da zata haifa sai kace ya Ganshi da idonshi." gajiya tayi da zaman ta mik'e tsaye had'ida shagwab'e fuska, ta kalleshi my Prince zanje na kwanta na huta." Mik'ewa tsaye shima yayi "mutafi na kwantar dake." Murmushi sukayi suka nufi hanyar sashinsa." Afnan ce gaba yana biye da ita a baya yana kulata da gefenta da bayanta." Tana kaiwa k'ofar d'akin tajita ta taka wani Abu mai sulb'i tana k'ok'arin karta fad'in ina sai jinta tayi ta fad'i, Ta saki wata irin k'arar wahala." Da gudu yayo kanta ya tallabeta jini kawai ke mata zuba. Cikin tashin hankalin yashiga kiran sunanta yana girgizata amma ina bata motsi." Ganin wurgawar mutum yayi da sauri, bin wurin yayi da ido yana kallo tabbas akwai abunda aka zuba a wurin domin Afnan ta taka ta fad'i." Haka yayi dai dai da zuwan maimartaba tare da Anna." Cikin tashin hankali Sarki ya kira fadawa sukazo da mota aka d'auketa tare da Anna aka nufi asibity da ita domin ceto rayuwarta." Gaba d'aya jikin bassam ya b'aci da jini. Amma bai damu da hakanba, hankalinshi a tashe yake." Maimartaba yashiga kwantar mashi da hankali, yana tambayarshi ya akayi hakan ta faru?" Murmushi Bassam ya k'ak'aro yace "munfito kenan ina ganin nakuda ce taka mata tafad'i" Sarki yace "Allah ya sauketa lafiya, kaje ka can za kayan jikinka. sai ka k'arasa asibitin ko dayake Anna na wurin tare da waziri da fadawa." Yana ganin sarki ya tafi, yanufi inda yaga giftawar mutum a lokacin da Afnan ta fad'i." Wata baiwa ya hango sai kugudu takeyi tanufi sashin hajiya zainab." Kai tsaye yanufi sashin hajiya zainab d'in zuciyarshi tana ta farfasa." Baiwar tsugunne a gaban hajiya zainab tana fad'in "ranki ya dad'e nagama komai, a gaban idona ta taka tafad'i yanzun hakan an nufi asibity da ita jini na bata zuba, ai ranki ya dad'e ina ganin da ita da abunda ke cikinta bazasu rayuba." Dariya hajiya zainab tasaki mai sauti, tace kwananki ya k'are "yar Aljanar yarinya, waya gaya maki ana karawa dani." Sai a kunnen Bassam da yashigo a fusace, duk abunda ake fad'i a kan kunnensa." Wani huci yakeyi kamar wani zaki. Yasanya hannu ya damk'o gashin baiwar yajashi da k'arfi, tasaki wata irin k'arar wahala harda sakin fitsari." Idonshi ya rik'ed'e zuwa launinja ya koma damisa, Hajiya zainab datayi ido biyu dashi Sai da gabanta ya fad'i jikinta yasoma rawa." Yace "duk abunda kuke k'ullawa naji kuma nagani." Yanuna hajiya zainab da hannu yace "wallahi tallahi muddun Afnan ko abunda ke cikinta ya suka rasa rayuwarsu, narantse da Allah kema saikin bar duniyar nan, ni zan kasheki da hannuna." In kuma gashe wannan d'an naki." In kashe duk wata zuri'a taku wadda kike Alfahari da ita." Dan haka ki kwana da shirin barin duniya kema." Yajawo gashin kan baiwar yafito da ita yana janta a k'asa sai kuwa takeyi tana bashi hak'uri." Yakira sarkin hukunci yace "ayi mata horo mai tsanani kafin yadawo asibity ya zartar mata da hukunci da kansa, Yashiga mota yajata da k'arfi yanufi asibity." Hankalin hajiya zainab ya kai k'ololuwa wurin tashi bata zaune bata tsaye ta aika akira mata sarkin gida, yacewa d'an aikin yace baya nan." Tabbas tasan duk abunda Bassam yafad'i saiya aikatashi, ta d'ora hannu akai tace "wayyo Allah nashiga uku. Allah ka kawomin d'auki banaso na mutu yanzun, kuma bana son yazeed ya mutu shine farin cikina a nan duniya." [3/6, 10:39 AM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *68* A guje ya nufi asibity, baya kallon gabansa, kai tsaye d'akin haihuwar ya nufa yana k'ok'arin shiga." Anna da Waziri suka rik'oshi suka zaunar dashi, suna lallashinsa da ban hakuri." Wanda yayi dai dai da zuwan kaka wurin itama fuskarta cikin tashin hankali, ganin Bassam yafita shiga tashin hankalin yasa ta koma bashi hak'uri tana kwantar mashi da zuciya." Likita ne ya bud'e k'ofa ya fito yana fad'in ina mutanen Afnan?" Da Sauri suka mik'e suka nufeshi, Bassam ya rik'e likita yana girgizashi yana fad'in "gani nine mijinta meyasa meta?" Ta haihu ne?" Likita yace "kwantar da hankalinka Yarima sakeni na fad'a maka." Anna ta jayeshi daga jikin likita tace ka natsu mana yarima, kabar likita yayi bayaninsa musan halin da take ciki a yanzun Afnan Addu'a kawai take buk'ata. Likita muna saurarenka." Likita ya d'an ja baya d'an ya had'iye miyau. Ya kalli Yarima yasaki murnushi yace "ina tayaka murna matarka ta haihu ta haifi 'yan biyu, duk suna cikin k'oshin lafiya, sai dai ita, a yanzun tana cikin mawuyacin hali domin tana buk'atar jini sakamakon tayi zubar jini da yawa." Alhmdulillah kaka da Anna suka ce, yarima kuma yace likita mutafi a d'ebi jini na asaka mata." Haka akayi aka d'ebi jinin sa aka sanyawa Afnan wanda take kwance bata san Inda kanta yakeba." Addu'a kawai yarima yake mata yana tufa mata, kotakan 'ya'yan baibiba, d'aya yana rungume da kaka d'aya kuma yana rungume da Anna." Suna zaune a waje dukansu sai addu'ar samun lafiya sukeyiwa Afnan." Ko wannensu da carbi a hannushi yana salati." Likita ya turo k'ofa yashigo ya dubi yarima yace "kayi hak'uri nan da awa biyu zata farfad'o kafita daga waje kabata wuri zuwa anjima kad'an sai ka dawo. A lokacin ta farka." Ko kallon likitan baiyi ba, yaci gaba da Addu'ar da yakeyi yana tofa mata." Likita naganin hakan bai kuma yi mashi maganaba yaja k'afarshi ya fita." Awa biyu na bugawa Afnan ta bud'e idonta sai a kan yarima, murmushi ya sakar mata itama ta mayar mashi, Da sauri ya fita yanufi wurin kiran likita." Tare sukazo tare dashi, yashiga dibata yana aunata, ya tabbatar da tasamu lafiya sai dai rashin k'arfin jiki saka makon wahalar da tasha." Baza'a sallametaba yanzuba sai zuwa gobe a lokacin ta kuma samun sauki." Sai a lokacin hankalin yarima ya kwanta, yashiga yiwa likita godiya." Likita yayi murmushi ya fita." Yana ganin fitar likitan ya tashi tsaye ya haye kan gadon ya jawota jikinshi yashiga sakar mata kiss ta ko ina, yana fad'in " Nagode Angel kinkawo farin ciki a rayuwata, da kuma rayuwar maimartaba, kin haifamana kyawawan 'ya'ya masu kama dake sak. Sannu Angel ya kuma rungomota yasanya Bakinshi cikin bakinta yashiga tsotsa, jin k'arar bud'e k'ofar ne yasa yayi saurin durowa daga kan gadon yana d'an sosar kai." Anna ce da kaka suka shigo, Anna ta kai mashi harara tace " nasan za'ayi hakan, wuce kafita kaje gida ka canza kayan jikinka, baka lura da yanda suka lalace bane?" Sai a lokacin ya lura da jinin da ya b'ata masa kaya, ya juya ya kalli Afnan dake zaune a kan gado itama shi take kallo tana murmushi, yasakar mata murmushi had'ida kashe mata ido d'aya." Maimartaba ne da kanshi ba aikeba ya turo k'ofa yashigo, fadawa na biye dashi." Daka kalli fuskarsa Kasan yana cike da farin ciki, Kai tsaye bakin gadon Afnan ya nufa yayi mata sannu da jiki, sannan aka d'ora mashi kujera ya zauna aka mik'a mashi jariran, ya karb'a farin cikinshi ya kasa b'oyuwa a fuskarshi sai murmushi yakeyi yana kallon yaran, wanda shima bassam dake tsaye kusa dashi ya tsurawa yaran ido cike da so da k'auna mussam 'yar macen daya lura tana kama da Afnan sak, shi kuma d'an namijin koba a fad'aba dashi yake kama." Maimartaba yayi masu kiran sallah tare da hud'uba yasanya masu suna, Yasanyawa namijin sunan babban Amininshi wato Alhaji Ibrahim mahaifin Afnan kenan, macen kuma yasanya mata Halimatun Sadiya, sunan mahaifiyar Afnan kenan." Yafad'i sunan da yasan masu, kowa yashiga murna kaka harda kuka tayi haka itama Afnan." Bassam yaja dogon numfashi yadubi jariran yace " Ubangiji Allah ya rayaku Amir da Amira yasanyawa rayuwarku Albarka, Gaba d'aya d'akin suka amsa da Amin, kowa yaji dad'in sunan da aka sanyawa yaran har wanda Bassam yakirasu dashi Amir da Amira." Sai a lokacin aka mik'awa Afnan su ta karb'rsu cike daso da k'auna take kallonsu idonta na tsiyayar da hawayen farin ciki." *************** Labari ya game gidan sarautar Afnan ta haihu ta haifawa yarima 'yan biyu. Kuma dukansu suna cikin k'oshin lafiya." Ajiyar zuciya hajiya zainab ta sauke, Domin tasan ta kub'uta daga hukuncin da yarima yace zai d'auka a kanta idan d'aya daga cikisun ya rasa ransa." Wani bak'in ciki da jin haushi taji yataso mata ya tokareta a wuya, jin Afnan ta haifi 'yan biyu, Ta kai zaune, ta dubi d'anta yazeed kwance cikin mawuyacin hali. Washi wa babu duk d'aya, idonta yana zubar da hawaye." Ta mik'e tsaye kamar wata zautanciya, tace "na rantse da Allah indai ina numfashi a doron k'asa Bassam da zuri'arshi bazasu hau kujerar mulkiba." Sai dai kowa ya rasa, domin zankasheshi in kashe zuri'arshi in kashe maimartaba, sannan daga k'arshe ni da kaina na haye kujerar mulkin, inyi yanda naga dama in juya kowa yanda nakeso, in kwashi dukiya in yi abunda nakeso da ita." TaSaki wata irin dariya ta samun nasara." ************** Alhmdulillah Afnan sauk'i yasamu, sundawo gida, A b'angaren Anna aka ajiyeta, tana samun kula sosai tsakanin kaka da Anna wanda a yanzun kaka tadawo gidan da zama, idan Afnan tayi Arba'in zata koma gida a cewarta." Barka ake zuwa yiwa maimartaba da Bassam k'asa k'asa garigari." Kowa a gidan cike yake da murna da farin ciki, amma banda hajiya zainab." Ranar suna bikine na 'ya'yan gata jikoki a wurin Sarki Ahmad mohd, Kuzo kukaga taron jama'a a cikin gidan sarautar." Matan sarakuna da matan shuwagabannin k'asa, matan gwamnoni kai duk wasu masu fad'a aji sun hallara a wurin bikin Amir da Amira." Duk wanda kagani fuskarshi cike take da murna da farin ciki, Afnan da Bassam sunci ado na burgewa sunsan ya wata dakankiyar shadda ruwan zuma har wani mai take fitarwa tana shek'e, daka gansu ka dubi fuskarsu kasan suna cike da farin ciki, sai d'aukarsu hoto akeyi." Yan jarida da yan gulma duk ba'a barsu a bayaba, kowa k'ok'arin yake ya d'aukesu photo yaji dad'in ya d'awa a duniya." To nima dai ina gefe d'aya zaune, da birona da takardata a hannuna sai d'aukar rahoto nakeyi, d'aya gefena kuma jama'ar groups dina ne _Ummu safwan and tambarin sarauta_ sai kwasar gara sukeyi, Matsalata d'aya dasu a nan sukafi maida hankali, wurin dannar gara, musamman su o'o da o'a nidai ban fad'i sunaba😜 A can na hango ta wakagar yan group din Aisha A moh'd, wai wai ba laifi sun d'auki wanka, amma abun mamaki kular shinkafa suke hange suna had'iyar miyau." Tare da lashe baki😋 Karku damu bikin Amir da Amira ne 'ya'yan gata zakuci shinkafa har sai kunbarta😜 Nima dai nayi nan, saboda nikaina yunwar nakeji, mukwashi gara lafiya😜😜😜😜😜😜😂😂😂😂😂 [3/6, 10:42 AM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *69* Sarkin gida gurgane a gaban hajiya zainab yana sauke numfashi da sauri da sauri kamar wanda yayi gudu." "Ranki ya dad'e wannan karon kam da kyar nasha a wurin boka na hayi." Ya ciro k'ullin magani ya mik'a mata Yace wannan yace kitafasashi da ruwan zafi, kibawa Yazeed yasha da zarar yashanyeshi kiyi mashi turare yace tabbas zai warke, domin ya gano sammu ne akayi mashi." Wannan kuma yace idan dare yayi, misalin k'arfe biyu da rabi na dare, idan kika tabbatar da kowa ya kwanta, zakiyi ziddir kicire kayan jikinki gaba d'aya, ki zuba maganin a kaskon wuta, kifito waje tsakar fili. Ki kikira sunan yarima sau uku da Afnan da maimartaba, da duk wanda kikeso kiga baya motsi a doron k'asa ki kira sunanshi sau uku." Amma da sharad'i yace "kada kijuya, kada kiyi magana bayan kin ambaci sunan su." Idan kika sab'awa umurninshi yace daga ni harke muna cikin matsala da tashin hankali." Allah ya taimakeki Allah yabaki kujerar mulkin nan a ranar komai namune, muyi yanda mukeso dashi." Wata dariya tasaki mai sauti, ta buga k'afarta k'asa tace "lallai ashe kwanan yarima da duk wani magoya bayanshi ya k'are." "Sarkin gida kasanyawa rayuwarka cewa da zarar na hau kujerar sarauta, nayi maka Alk'awarin zinari dubu, gwala gwalai dubu, duk wata zuri'a taka nayi maka Alk'awarin sai na kaisu aikin hajjin bana, Sannan kuma zan baka kujerar waziri na." Sarki gida yace " godiya nake ranki ya dad'e Allah ya tayaki rik'o, Aini yanzun hakan na hangoki a kan kujerar sarautar." "Amma ranki ya dad'e ki kula da kyau da yanda zakiyi aiki da maganin dan gudun samun matsala daga ni harke." "Kar kadamu sarkin gida aina fahimce ka, insha Allahu baza'a samu matsalaba." Ta mik'a mashi rafar kud'i "ga wannan tukuicinka ne kafara rik'awa." Yasanya hannu biyu ya amsa tare da bud'e baki yana dariya cike da jindad'i yatashi ya fita." Da fitarshi takira kuyangunta ta mik'a masu maganin tace "ina bugatar a tafasa min wannan maganin da ruwa zafi a kawo min shi yanzun, Dasauri suka karb'a suka nufi kicin domin ai watar da aikin da tasanyasu." Cikin minti goma suka kawo mata tafasasshin maganin har wani kumfa yake fitarwa, A hakan ta Tayar da Yazeed zaune tashiga d'ura mashi maganin yana sha, sai da ya shanyeshi tas sannan ta ajiye copin maganin tana murmushin samun nasara." Minti biyar da kammala bawa yazeed magani ya fara wani kalar zawo tsanwa shar mai mugun wari." Da gudu ta bar d'akin tana toshi hancinta saboda azabanbin wurin kashin, D'aya d'akinta ta bud'e ta shiga, ta shiga kiran masuyi mata hidima "tabasu umurnin su kula da Yazeed." *2:30am* Hajiya zainab ziddir haihuwar uwarta tafito waje, tsakar fili, da kaskon wuta a hannunta hayaki na tashi, fuskarta ba tausayi ba imani. Yarima shine mutum na farko da tafara kira har sau uku sannan ta fara kiran maimartaba." Jitayi anrik'e mata k'afa tayi saurin juyawa domin ganin ko waye, Yazeed tagani a gefenta tsaye rik'e da k'afarta yana fad'in "mama mekikeyi a nan ba kaya a jikinki?" Murna da jin dad'i ya kamata tace "yazeed ka warke kai Allah nagode maka, Wuce ka koma d'aki ganinan zuwa yanzun." Tunawa tayi da sarkin gida yace "ba'a magana tayi saurin rufe bakinta tana fad'in "wai na manta ance ba'a magana to amma kuma ai murna ce nayi." Taci gaba da turarenta takira sarki takira Afnan da yaranta, harda Anna, duk sunshiga a cikin matattu." Tana kammalawa tasaki wata irin dariya da shewa gaba d'aya filin wurin sai da ya amsa, Hakan yajawo hankalin bayi masu gadin wurin suka firfito da fitulu a hannunsu suna fad'in "waye ne?." Keta kowa hajiya zainab tayi ta yanka da gudu tabi hanya tsirara tana fisgar gashin gabanta." Dafa mata baya sukayi suna fad'in hajiya zainab ce fa." Amma ina tab'ace masu, Basu gantaba kasancewar gidan babban gida ne, wanda baya misaltuwa." Jin hayaniyar mutane gidan kowa ya farka, yasa maimartaba fitowa yana tambayar lafiya meke faruwa?" Anan aka shiga fad'a mashi abunda ya faru, Cikin tashin hankali ya dokawa bayi tsawa yace "me kuke jira da bazaku shiga lungu da Sak'o na gidan nan kunemotaba?" Ai bairufe bakinsaba gaba d'aya kowa ya watse a wurin, suka rarrabu ko wannensu da fitila a hannunshi suka Shiga nemanta." Tashin hankali sarki ya shigeshi na haukacewa hajiya zainab, wanda damuwar tasanyashi zubar da hawayensa, barcin da bai kwantaba kenan yashiga jera salloli, yana Addu'ar Allah ya bayyanata." Har safiya ta waye ba a gantaba, sai dai akaji labarin sarkin gida ya rasu, saka makon wasu k'uraje dasuka fito masa cikin dare kafin Safiya ta waye yarasu." Hankalin Sarki ya kuma tashi ya d'aga waya yakira Bassam da baisan abunda ke faruwaba, yana can b'angaren Anna yana wasa da 'yan biyunsa yana dariya." Ganin kiran maimartaba yasa ya mik'awa Kaka su, Ya d'aga wayar had'ida mik'ewa tsaye yanufi hanyar waje." Sarki yace "yarima duk Inda kake kayi Sauri kazo ina kiranka domin gidan nan ba lafiya." Da sauri Bassam ya fita yana fad'in "Abba lafiya meke faruwa?" Sarki ya katse wayar, Da sauri Bassam yanufi sashin maimartaba." Sarki yashiga gaya masa abunda ke faruwa harda b'atan hajiya zainab a daren jiya harda mutuwar da sarkin gida yayi yanzun da safen nan." Wannan labarin ya girgixa yarima sosai, duk da dai yasan mugun abunso ne ya koma masu." Ya dubi sarki yace "Abba toshi yazeed awane hali yake yanxun?" Sarki ya mik'e tsaye yace "mutafi munganshi musan halin da yake ciki." Yazeed kwance cikin zawo mai wari, gaba d'aya jikinshi wasu manyan k'uraje sun fito mashi, shigowar maimartaba da yarima ransa na fita." Runtse idonsa Sarki yayi yaja da baya yafita d'akin ya jingine da bango ya yana sauke numfashi a hankali." Yana fad'in "meke faruwa a gidan nan ne bansaniba?" Hajiya zainab ta haukace ba'a gantaba, Sarkin gida ya mutu jiya, Yanzun kuma d'ana yazeed shima ya mutu yau." Yarima meke faruwa ne?" Ya fad'a cikin d'aga murya, alamar tashin hankalin!!!!!!! Yarima ya matso kusa dashi ya dafashi, yace "Abba karka d'aga hankalinka, har wani ciwo yashigeka." Ka natsu ka kwantar da hankalinka, ka fahimci ko wacece hajiya zainab da irin mugun halinta da yanda take gudanar da rayuwarta." Abba nasan kafi kowa sanin ko wacece ita, tunda kai kake cewa muyi hattara da sharrinta,da muguntarta." Idan kayi la'kari da hakan, zaka fahimci cewa Allah ne ya mayar mata da muguntarta da mugun nufinta ya koma a kanta." Sarkin gida kuma dama na hannun damarta ne duk abunda take k'ullawa da kwancewa a gidan nan tare sukeyinsa." Ka kwantar da hankalinka Abba karka sanyawa rayuwarka tunani. Gudun kar wani ciwo ya shigeka kasani kaine gatana, kai kad'ai nake dashi a duniyar nan." Muyi Addu'a duk inda tashiga Allah ya bayyanar da ita." Fadawa aka kira akayiwa sarkin gida sutura tare da yazeed aka kaisu ma kwancinsu." Wasa wasa kusan sati biyu kenan ba labarin hajiya zainab gaba d'aya anduba cikin gidan ba'a gantaba, Gaba d'aya gidan ba mai fad'ar mata alheri sai sharrinta, ma aikatanta bbu abunda suke furta mata sai tsinuwa suna fad'in Allah yasa kar a ganta." Tun sarki yana damuwa, har ya kai ya hak'ura sai dai a duk lokacin da yayi sallah yana addu'a Allah ya bayyanata, koda gawarta ce a gani." ************** Ayau Afnan take cika kwana arba'in da haihuwa." Gyarane tashashi a wurin Anna da kaka, tayi kyau har ta gaji, Amir da Amira kuma suma sun girma sunyi k'iba idan ka gansu sai ka d'auka 'yan wata bakwai ne." Shiryata akeyi sosai domin yaune zata koma turaka." Inda shima yarima cike yake da murna da jin dad'i, yau zai kasance tare da abun sonshi Afnan." Indai hak'uri yayi hak'uri, yau kwanansa arba'in batare da macce ba, sai dai idan dare yayi yayita matse matse akan gado mararshi tana yimashi ciwo." Idan kuma ya tunkari wurin matarshi Anna ta koroshi tana cemasa baya da hak'uri to shi kuma meye rashin hak'urinshi a ciki, tunda dai matarshi ce." Shiri yakeyi sosai ya shiga toilet yayi wanka ya feshi jikinshi da turare ya sanya kayan barci ya haye kan gado ya kwanta Afnan kawai yake jira." Da sallama ta shogo tareda kuyangu d'auke da Amir da Amira da suka dad'e da yin barci." Karb'arsu tayi ta kwantar dasu ko wanne a kan gadonsa, tayi sallama da kuyangu suka tafi." Juyawar da zatayi tashiga brdrom yarima taci karo dashi tsaye a bayanta." Rugumeta yayi yashiga aika mata da kiss ta ko ina yana fad'in _missing you Angel_ A hankali yajata zuwa gado yashiga nuna mata yanda yayi _missing_ d'inta." A yau ya kuma tabbatar da Angel d'inshi ta dabance ko a cikin mata, Jinta yayi ta canza mashi dama haka macce take canzawa idan ta haihu?" Sai yanzun ya kuma tabbatar da ni'imar da Allah yayiwa Afnan ta dabance, hannu ya d'aga sama yna godiya ga Allah da ya Azurtashi da macce kamar Afnan." Itama A wurinta hakan ke faruwa, domin bata tab'ajin dad'in da tajiya irin na yauba." Tabbas da gaskiyar Anna datake cewa Afnan " kinatsu ki saurareni yau zaki koma wurin mijinki Inaso kisaki jikinki ki nunawa mijiki soyayya domin zakijiki kinshiga cikin wata sabuwar rayuwa mai cike da jin dad'i." Sai yanzun ta tabbatar da abunda Anna take nufi, Rungume prince tayi tasanya bakinta a cikin nashi, Anan suka shiga bawa junansu dad'i. Ko wannensu sai nishin dad'i yakeyi suna zubarda hawayen k'auna." [3/6, 11:21 AM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *70* Wata biyu kenan ba hajiya zainab ba labarinta, Sarki ya yanke shawarar d'ora Afnan a kan kujerarta a matsayin sarauniya." Inda Fulani da hajiya Amina suka farajin haushi domin a tsamma ninsu d'aya daga cikinsu za'a d'ora akan kujerar." Bassam yaji dad'i sosai ya nuna farin cikinsa a fili." Da murnansa ya nufi wurin Afnan, ya tarar da ita akan gado tana sanyawa Amir da Amira Pampas." Rungumeta yayi ta bayanta ya sakar mata kiss a kunci had'ida d'aukar Amira da aka shirya mata yana wasa da ita tana dariya." Itama murmushin takeyi ta k'ure da ido da alamar yana cike da farin ciki." Tace "my Prince sannu da shigowa, amma daga ganin fuskarka akwai magana a bakinka." Murmushin fuskarshi ya kuma yawaita, yace Albishirinki Angel." "Goro fari." Ta fad'a itama tana murmushi." "Sarki ya yanke shawarar d'oraki a matsayin sarauniya." Zaro ido tayi waje, cike da mmki, tace "Anya my prince zan iya shugabancin nan kuwa?" Dibo da yanda hajiya zainab take juya gidan nan tana fafatawa da kuyangu, Sannan duk wani shige da ficen abincin gidan nan d'anye ko dafaffe a k'ark'ashinta yake." My Prince bansan ko maiba a kan mulki, tayaya zan shugabanci mutanan gidan nan?" Ido yabita dasu yana kallon d'an k'aramin bakinta dake magana cikin natsuwa da girmamawa, Ya matso daf da ita yanda suke iyajin saukar numfashin junansu, Ya rungumota cikin murya k'asa k'asa yace "Angel zaki iya mulkin gidan nan, karki manta da Anna na kusa dake anna zata nuna maki yanda zaki tafiyar da mulkinki cikin amana da gaskiya." Tunawa tayi da Anna na kusa, yasa hankalinta ya kwanta ta sauke ajiyar zuciya tace "Allah ya tayani rik'o." "Amin Angel, yace had'ida shafa cikinta, Anya Angel ba ajiyata a cikin nan domin na fara ganin alamu." Turo baki tayi alamar shagwab'a "A'a nidai ba yanzunba ya zanyi dasu Amira?" Murmushi ya kuma saki '"su Amira basuda Matsala, nifa nafison naga anata cika mun gida da 'ya'ya, kasan cewar in kad'aine a wurin maimartaba." Batayi maganaba illah tashi da tayi tabar mashi wurin tashiga sauya kayan jikinta." "Yawwa kiyi saurin ki shirya mutafi fada sarki nason ganinki." Hakan ta shirya tsaf tasanya lesi ruwan madara, ta d'ora Alkyabbar ta, itama ruwan madara, ta d'auki Amira ta sab'ata a kafad'a, Shima ya d'auki Amir suka jera suka fita suna tafiya suna hira gwanin ban sha'awa, suka nufi fada." A gaban maimartaba suka runsuna suna gaisuwa." Yana murmushi yana kallonsu cike da burgewa, Yake Amsa gaisuwarsu, ya tara hannu ya karb'i jikokinsa da sukafi soyuwa a ransa. Yana masu wasa suna dariya kasancewar sunsaba dashi kullum a wurinshi suke yini idan ya fito daga fada." Ya dubi Afnan yace "Afnan yarima ya fad'a maki matsayinda zaki hau a gidan nan, na yarda dake na yarda da tarbiyarki wannan dalilin yasa nazab'eki a matsayin sarauniyar masarautar nan." Allah yatayaki rik'o yabaki ikon rik'e gaskiya da Amana." Suka Amsa da Amin gaba d'ayansu." Afnan ta tsurawa *Tambarin sarautar* ido data Ganshi a jiye wuri d'aya anzagayeshi da kyale kyale gwanin burgewa da alama yana da mahimmaci a masarautar saka makon yanda take ganin bayi da kuyanku da duk wasu masu dangataka a masarautar take ganinshi lik'e a jikinsu." Bata mantaba ta tab'a tambayar Sadi da cewa wai meye amfanin mannawa mutane wannan tambarin a bayan rigarsu ko a saman hularsu." Idon kuma motar masarautar ce zata ganta lik'e da tambarin." Sadi yace Tab Aminiya akwai tambaya kamar 'yar jarida, To Nima dai yanda kike ganin tambarin nan haka nake ganinsa, bansan dalilin dayasa masarautar nan suke girmama tambarin nan ba Amma kuma ina ganin shine k'undin tarihin sarautar nan sannu a hankali zamu san komai." To sai yanzun gata kusa da tambarin, kuma tana Neman sanin ko meye shi." Ta kalli maimartaba da shima ita yake kallo tace "Abba inada tambaya." Yarima ya d'ago kai ya dubeta, ta dubishi ta sakar mashi murmushi, "Abba na dad'e ina tambaya akan wannan tambarin narasa Wanda zaibani amsa, Abba Dan Allah wannan tambarin nameye?" Me akeyi dashi?" Meyasa duk wani mutum wanda ke rayuwa a gidan nan ko wanda keda dangartaka a masarautar nan sai na gashin lik'e da wannan tambarin?" Sarki yayi murmushi yace 'yata kinyi tambaya mai kyau, wadda koda baki tambayaba nayi Alk'awarin zankiraku tareda yarima nabaku labarin *tambarin* nan." Wannan shine *Tambarin sarautar* masarautar nan, duk wani k'undun tarihi na masarautar nan yana cikinsa, da iya adadin dokiyar da masarautar nan ta mallaka." Sarki na d'aya yabar wasiya da cewa bazai tab'a amfanuwaba har sai sarki mai adalci ya hau kujerar mulkin garin nan Bayan mutuwar sarki na d'aya sarki bakwai ya hau kujerar mulkin garin nan nine na takwas amma abun mmki maimakon ya gyaro sai dai ya kuma lalacewa saboda ba gaskiya a cikin zuciyoyin wasu sarakunan, har zuwa yanzun a kaina munkasa gyarashi, Wanda ni bashine a gabanaba domin bantab'a dogaro da dukiyar sarautaba, wannan dalilin yasa tunda na hau kujerar mulki bantab'a kiran wani mai kyara dasunan ya gyarashi ba, Sab'anin sauran sarakunan da suka gabata burinsu d'aya ne da zarar sun hau kujerar mulkin su gyara wannan tambarin domin su san adadin abunda masarauta takeda shi, su kwashi dukiya suyi abunda sukesu da ita." K'asa k'asa jahohi jahohi, sunta kiran wanda zai gyara, masu shi." Amma abun mmki da zarar antab'ashi da sunan gyara sai wani Abu a cikin fadar nan ya kuma d'aukewa ya daina aiki." Wannan dalilin yasa bandamu dashiba, mulkina nasanya a gaba, babban burina a rayuwarta talaka yaji dad'i, Babban burina shine in kyautatawa talakawa in faranta masu in yaye masu damuwa da kuncin rayuwarsu." Wannan dalilin yasa kike ganin kowa a cikin gidan nan da *tambarin sarauta* like a bayansa." Afnan ta nisa tace "Abba zan iya gyarashi." Yarima yayi saurin juyowa ya dubeta cikin mmki yace "tayaya?" Bayan kinji Abba yace "babu k'asar da ba'a d'auko mai gyaraba da sunan ya gyarashi amma ya kasa." Saike?" Mekika sani?" A fannin gyara?" Tayi murmushi tace "ni zan iya gyarashi, yarima yayi murmushi yace Angel ina ganin kamar baki fahimci bayanin da Abba yayi ba da kyau." "Na fahimta sai dai idan Kaine baka fahimceni da kyauba." Maimarba yayi gyaran murya yace "Ku saurara, "Afnan bazaki iya kyara tambarin sarautar nan ba, kibarshi kawai a yanda kika ganshi idan Allah yayi kafin nasauka a kan kujerar mulki zai gyaru Alhmdulillah idan kuma Allah yayi bazai gyaruba shikenan duk wanda ya hau ya gyaru a lokacinsa ina mashi Addu'ar Allah ya tayashi rik'o." Suka amsa da "Amin gaba d'ayansu sukayi mashi sallama suka fito." A Daren ranar Afnan kasa barci tayi sai tunanin *tambarin sarauta* takeyi, itafa zata iya gyarashi. Ta gyara abunda yafishi girma da had'arin gaske bare wancan tambarin." Koda dai ance sai lokacin sarki mai adalci xai gyaru. Amma ai Abba yana da adalci ga tausayin talakawanshi, tun kafin ta sanya rayuwar zata shigo gidan sarautar takejin labarin irin tausayi da karamcin irin na sarki Ahmad moh'd." Juyawa tayi ta dubi yarima taga barcinsa yakeyi." Agogo ta duba taga k'arfe uku na dare, A hankali ta sauka daga kan gadon ta d'auko hijabin sallarta ta sanya a kan kayan barcinta kasan cewar riga da dogon wando ne masu yalwar fad'i, Ta lallab'a a hankali cikin sand'a ta fita d'akin had'ida jan kofa." Kai tsaye fada ta nufa, tayi sa'a da gaba d'aya masu gad'in fadar duk barci sukeyi, Kai tsaye wurin tambarin sarauta ta nufa, Ido ta tsora mashi tana tunanin ta ina zata fara." Wuri tasamu ta zauna ta bud'eshi gaba d'aya tashiga gyarawa, Tana cikin gyaran taga gaba d'aya wasu manyan kwaya kwai na kwala kwalai da suka bar aiki a masarautar sunkawo haske, tsoro abun yabata, amma hakan baisa ta daina gyaranba taci gaba." Wasu kwaya kwayi tagani wad'anda ke ajiye wuri d'aya suma sunkawo haske sunfara aiki." Sai wani jiniyar kuka da tambarin yake fitarwa wanda duk wanda ke rayuwa a cikin gidan saida yaji jiniyar." Fadawa dake gadin wurin suka mik'e tsaye da takobi a hannunsu ganin hasken da basu tab'a ganin shiba yasa sukaja wuri d'aya suka toge suna zarar idanu. Gaba d'aya haske ya haske masu fuska Sarki a can cikin barcinsa yaga haske ya kashe masa ido, da sauri ya tashi zaune, yashiga mamaki ganin ba hasken NEPA bane wasu na"urori ne da tunda ya hau kujerar mulk yaga basa aiki sai yanxun." Sautin jiniyar wani Abu yakeji yana tashi, a cikin gidan, da sauri ya sanya jallabiyarsa ya fito waje cike da mamaki da tashin hankali." Gaba d'aya gidan ya haskake da gaske kuma ba hasken wutar NEPA bane." Karo yaci da Bassam shima ya nufo wurinshi Gaba d'aya fada suka nufa domin sun fahimci a can komai ke faruwa." Duk ilahirin jama'ar gidan gaba d'aya sun d'unguma suna bakin fada tsaitsaye anrasa Wadda zaishiga cikin fadar." Zuwan sarki da Bassam wurin, kallo ya koma kansu, kai tsaye suka tunkari fadar gadan gadan babu fargaba a tare dasu." Shigarsu fadar yayi daidai da kammala gyaran *tambarin sarautar* da Afnan Takeyi [3/6, 11:23 AM] Ummu Safwan WS P1: 👑 *TAMBARIN SARAUTA*🤴 👑. 🤴 👑 *NA* *UMMU SAFWAN* ( Farida Bashir) *71* 🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚 Wuri d'aya suka ja suka tsaya suna kallonta cike da mamaki, Murnace a fuskar sarki ko farin ciki?" Wani murmushi yake fitarwa yana kallon Afnan. Yana kuma kallon fada da nan take koma kamar ba itaba." Da sauri Bassam yanufeta ya rungumeta, Cikin da farin ciki da jin dad'i yarasa abunda zai cemata sai dariya' yake yana shafa bayanta, A hankali ta janye jikinta ta nufi wurin maimartaba ta durk'usa k'asa tace "Abba kayi hak'uri, idan hakan da nayi nab'ata maka." Kallon ya bita dashi ya kasa yin magana saboda farin ciki dake tare dashi." Nuni yayi mata da ta mik'e tsaye, yace "nagode maki Afnan hak'ik'a ke Alheri ce a rayuwarmu. Ya juya ya kalli yarima da yaje wurin tambarin sarautar yanason yatab'a yanajin tsoro kuma." Mutanen dake waje ganin sarki da yarima sunshiga basu fitoba. Yasa sukayi ayari gaba d'ayansu suka shigo cikin fadar." Abunda kowa ya ganewa idonsa yasa suka shiga mmki, tambarin sarauta ne ya gyaru.?" Murna sukeyi suna kuwa, Suna jin dad'i." Sarki ya dakatar dasu yace "kowa yaje ya kwanta sai da safe za'ayi magana." Ya dubi yarima dake rungume da Afnan yace "kutafi sashinku sai gobe zamuyi magana, ku kwanta da shirin gobe za'a gabatar da Afnan a matsayin sarauniya a gaban kowa ya shaidata." Hakan kowa ya kwanta cike da farin ciki a ransa." Anna tayi murna sosai taji dad'i ta kumajin ta k'ara son Afnan a ranta, Hakan itama kaka taji dad'i sosai Anan tashiga bawa Anna labarin irin baiwar da Allah yayiwa Afnan tun tana k'ara marta." B'angaren Bassam shima hakan domin rungume yake da ita jiyakeyi kamar ya maida ta cikinsa, saboda murnar dafarin ciki." Bakinsa ya Sanya a kunnenta yashiga yi mata rad'a yana fad'in? Tabbas Afnan ke Alherice ga rayuwar Bassam, kuma farin ciki ce a cikin wannan masarautar." Soyayyar Afnan ta kuma lunkuwa a cikin zuciyar Bassam." Angel kinbani mamaki, Ashe ke 'yar baiwace, kece jin dad'inmu da annashawarmu." Nayi maki Alk'awarin yanda kika wanzar da farin ciki a rayuwarmu, data mahaifina da kuma masarautar nan gaba d'aya baxaki tab'a kokawa." Nayi Alk'awarin zanjiyar dake dad'i in kuna sanyaki farin ciki, mai d'orewa tare dake da duk wata zuri'a taku." Kuma matseta yayi a jikinsa, ya shiga aika Mata da sak'onninsa masu wuyar misaltuwa." *9:am* Sun shirya tsam sunyi kwalliyarsu irin ta 'ya'yan sarauta, manyan Alkyabba ne s suka Sanya wad'anda sun karb'esu gaba d'aya sunyi kyau wanda baya misaltuwa." Fitowa sukayi suka nufi wurin taron gabatarda Afnan a matsayin Sarauniya." Duk mutanen cikin gidan sun hallara har matan sarki Fulani da Hajiya Amina, Da Anna da Kaka, suna gefe d'aya na musamman a zaune." K'arasowar Afnan da yarima sukayi wurin kowa ya hau kallonsu gwanin burgewa." Wurinda aka tana darmasu domin su, zauna, a can suka nufa suka zauna." Sarki da kansa, ya mik'e tsaye fuskarshi cike da annashawa yana murmushim farin ciki. Sannan ya fara jawabi." Yanuna Afnan yace "ayanzun itace sarauniyar gidan nan, duk wani Aiki da kukasan hajiya zainab na aiwayarwa a gidan nan, ya dawo a kan Afnan." Kuyi mata biyayya kamar yanda kukeyiwa hajiya zainab biyayya." Yin hakan shi zai sanya naji dad'i na kuma k'ara Alfahari daku a cikin masarautar nan." Afnan takawo canji da d'aukaka a masarautar nan, na rantse da Allah da macce na hawa kujerar sarauta dana sauka na d'ora Afnan akai." Bassam ya fara tab'awa sannan gaba d'aya kowa ya d'auki tab'awa." Kaka da Anna Dan murna harda hawayen farin ciki suke fitarwa." Anan aka shiga bikin nad'in Afnan a matsayin sarauniya, kid'e kid'e akeyi da bushe bushe, ana zuba mata kirari." *A gurguje* Gimbiya Afnan mulki takeyi cikin kwanciyar hankali da Adalci, Wani lokacin gani takeyi kamar abun yanaso yafi k'arfinta, da taimakon bassam da Anna, komai ke tafiya dai dai yanda ya kamata. Tafiya takeyi cike da k'asaita kuyangu na bayanta suna zuba mata kirari, gani tayi anwuce da kayan abinci b'angarin fulani." Sashin su fulanin ta nufa, wurin da ake dafa masu abinci da kayan motsa baki taja ta tsaya." Mamaki ya cikata ganin irin abincin da suke amfani dashi a rana d'aya." Ya isa ya wadatar da mutum a shin a rana d'aya." A dadin kud'insa a abincin talata mutum d'ari zai iya ciyar da gidansa da kud'in." Ta dakatar da masu aiki a b'angaren, ta umurcesu da cikin kashi uku, a surage kashi biyu sudinga yimasu amfani da kashi d'aya." Suka amsa da angama ranki ya dad'e." Sashinsu ta koma ta tarar da yarima zaune cikin yaranshi yana wasa dasu suna dariya." Kusa dashi taje ta zauna, yajawota a jikinsa, yana fad'in "sannu da aiki sarauniya." Sarki da mutanen gidan nan suna Alfahari dake." Murmushi tayi "ina godiya my prince. Ta kuma nisawa. Yarima yace "meke faruwa sarauniya." "Nasan Fulani zasuga laifina. ni kuma idan akan gaskiya ne bana shakkan hakan." Tayaya abincin da suke amfani dashi rana d'aya ya isa ya wadatar talata d'ari tare da iyalinsa." Tayaya zamu zab'i rayuwar jin dad'i talaka yana cikin k'unci na talauci." Nayi Alk'awarin duk wanda naga zaishiga cikin dukiyar talakawa, domin jin dad'insa saina dakatar dashi." Prince ya rungumeta yana aika mata da kiss ta ko ina." "Allah ya tayaki rik'o sarauniya nima ina bayanki." Sarki yace a fad'amaki kishirya gobe zamuje masarautar zamfara bikin sunan jikan da aka haifawa sarkin zamfara." Domin sarakuna da matan sarakuna zasu hallara a wurin. Za'a nunaki a cikin taron sakuna kece macce d'aya tamkar da dubu, kice kika samu nasarar gyara *tambarin sarauta* a gaban sarakuna maimartaba zai baki kyautar ban girma da d'aukaka." Tayi murna sosai wanda hakan yasa ta k'ank'ameshi tana godiya." Tace my prince tashi mutafi karakani store na shirya duk wani Abu da za'ayi amfani dashi gobe." Hakan suka shirya suna tafiya suna hira gwanin ban sha'awa da burgewa." Suna gafda shiga store d'in, sukaci karo da bayi tsaitsaye a k'ofar wurin suna zarar ido." Yarima ya fara tambayarsu "lfy meke faruwa?" Dukansu suka zube k'asa "ranka ya dad'e motsi mukeji a saman sili,mun d'auka kusani, amma wannan motsin yafi k'arfin na kusa." Kai tsaye Afnan tashiga yarima yayo saurin jawota yadawo da ita baya, ya wuce gaba bayi suka rufa mashi baya." Wata k'ofa ce k'arama wadda zata sadaka har cikin silin. ya d'ora tsani ya hau , yanufi cikin silin." Wazai gani hajiya zainab, Gaba d'aya tafita hayyacinta wannan kyawon nata ya dusashe. Gashin kanta ya gutsere, sai nishi takeyi sama sama alamar mura tayi mata muguwar kamu." Saukowa yayi yaba bayi umurni su hau su fito da ita." Bayan anfito da ita gata kwance tsirara, Afnan tabawa bayi mata umurni da sud'auko sutura su Sanya mata." Bayan ansanya mata sutura, yarima ya d'aga waya ya kira maimartaba, Da sauri maimartaba yazo." Yana ganinta cikin wannan halin saida gabanshi ya fad'i ya tausaya mata matuk'a." Gani sukayi ta mik'e zaune idonta yana zubar da hawaye, Anan tabud'e baki tashiga tonawa kanta asiri duk irin mugun abunda tayita shukawa." Ta dubi yarima "yarima ka yafe min, Maimartaba ka gafarceni, Afnan kema ki yafe min." Tana kaiwa nan tafara shakkuwa, ranta ya fita." Duk wanda ke wurin sai da idonshi ya cika da hawayen tausayinta." Anan take akayi mata wanka akayi mata sittura. Aka kaita gidanta na gaskiya." *hajiya zainab Allah ya yafe maki* ************** Zamfara, Masarautar zamfara masarautace mai cike da Adalci da daraja d'an Adam." Bikine akeyi na jikan sarkin zamfara jika na uku." Kowa ya hallara sai wad'anda ba'a rasaba." Afnan da Bassam sunk'araso cikin shiga ta Alfarma suna rik'e da 'ya'yansu gwanin burgewa." Wanda shi maimartaba ya dad'e da zuwa tare da Fulani." Tafiya sukeyi wanda zata sadasu da fadar masarautar." Wasu bayi sukagani su biyu macce da namiji, and'ora masu manyan itace suna tafiya ana tsula masu bulala sai kuwa sukeyi saboda azaba." Sautin Kuwaarsu yaja hankalin yarima da Afnan suka juya, Wazasu gani saratu da Alhaji Aminu, duk sunfita hanyacinsu cikin k'angin bauta." Saratu nayin ido biyu da yarima da Afnan da yaransu masu sunfar larabawa, Kukanta ya tsanta tana kallonsu ba damar tayi masu magana." Yarima yakuma kallonsu ya mere Baki, Afnan kuma ta tausaya mata matuk'a amma ba yanda zatayi mata Tana gani aka tasa k'eyarsu suna tafiya ana zafga masu bulala." *karshen Azzalumi da maci Amana baikyau. Allah yasa mufi k'arfin zuciyarmu* Alhmdulillah anyi biki lfy ank'are lfy, Inda Afnan tasamu kyaututtuka a wurin sarakuna da matayensu." Sundawo gida cike da murna da farinciki." Alhmdulillah duk wani farin cikin rayuwa Afnan tasameshi." Amir da Amira sunada shekara uku Afnan ta kuma haihuwar wasu 'yan biyu, inda sukaci sunan maimartaba da sunan mahaifiyar Bassam, Ahmad da Maryam, Amma Waleed da Waleeda ake kiransu." Ranar sunan walid da walida abun ba'a magana, Domin murna a wurin maimartaba kuzo kugani, shi dai babu abunda zaicewa Afnan sai godiya domin takawo farin ciki a masarautar shi ga kuma 'ya'ya da yafiso a rayuwarashi tana ta haifa mashi biyu biyu. Alhmdulillah kawai zaice sai dai ya godewa Allah." Malam Nura sun zo tareda matarsa Maryam da d'ansu Sadig." Wata sabuwar Amintace tashiga tsakanin Bassam da malam Nura, wanda yin hakan bak'aramin farin ciki yasanya Kaka ba." _ALHAMDULILLAH anan nakawo k'arshen littafina tambarin sarauta, kuskuren dake ciki Allah kayafemin, Alherin dake ciki Allah kasadani dashi, nagode masoyana sai kunjini a sabon littafina na gaba_ _zanyi missing d'inku masoyana bye bye bye🤚🏻🤚🏻😭_ *************************⬇********************** ************* Ai Hausa Novels **************** *************************⬆ ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ⬇ ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ⬆ **************************