*************************⬇********************** ************* Ai Hausa Novels **************** *************************⬆ ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ⬇ ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ⬆ ************************* 💗💗💗💗💗💗 YANCINKI 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 *NA* *AYSHA A BAGUDO* DEDICATED TO MRS ADAM (YAR MUTAN KAGARA) PAGE 1 to 5 ......Mota ce kiran honda accord ke sharara gudu akan titin ilupeju dake kan Express din mushi road ,yayinda wata mata ke zaune abayan motar, sanye cikin wasu had'add'un kananan kaya ,wando jeans da Riga pinky, kanta kwance da gashin attachement har gadon bayanta wanda ya sha gyara. "wata yarinya wace bazata wuce kimanin shekara tara zuwa goma ba, ke kwance a saman cinyar wannan matar ,tana fidda numfashi sama sama tamkar me cutar asma . kuka sosai wannan matar take hannuta rike da gorar ruwan roba tana shafawa yarinyar a fuskarta, saboda numfashinta dake barazanar d'aukewa daga gangar jikinta . Cike da matsanancin tashin hankali wannan matar tace "Dan Allah malam ka taka motar nan sosai," kayi sauri dan Allah mu samu mu isa asibiti nan da wuri ,tun kafin wani abu yasamu yarinyar nan nashiga uku takarasa maganar tana sake yayyafawa yarinyar ruwa ,direban yace "Baiwar Allah gudu fa nakeyi sosai ... ganin numfashin yarinya yayi kasa sosai fiyye da d'azu al'amunta numfashinta na daf da tsayawa ,yasa wannan matar sake yin magana a matukar firgice. "Dan Allah malam k'ak'ara sauri kar kabari yarinyar mutane ta mutu a hannuna, dan Allah dan Annabi ka k'ara gudu idan yarinyar nan ta mutu zan shiga tashin hankali mara misaltuwa .... A tsawace direban yace " what are you saying? "do you want me to be involved in a car accident because of you ? "da kikewa wa mutane zancen banza... "Wayyo Allah nashiga uku "wannan wani irin maseefa ne haka, ke kokari samuna? "me zancewa iyayen yarinyar nan ? " me zance yasamu 'yarsu? "Dan Allah malam, ba dan halina ba saboda Allah kayi hakuri kayi sauri.. " see I have already gotten to my speend limit, how much did you me? "da kike kokarin na kashe kaina akan matsalarku ya ja tsaki tare da meida hankalinsa da natsuwarsa kan tukinsa ... Numfashin yarinyar sai sake yin kasa yakeyi gabadaya idanunta sun gama birkicewa yasa matar tace "oh my goodness God have mercy on me "malam ,kindly speend up plz ! Direban yace " I can't speend more than this in this area. cikin zafin rai yacigaba da magana "Oh my God which kind of people boarded my car this morning . "sai da zuciyata ta gargad'eni akan d'aukarku da zanyi, amman naki bin umarninta "me yasa na d'aukeki da irin me wannan ciwon alhalin ban makance ba ? "gasky daga yau zan dinga lura da irin mutane da zan dinga d'auka most especial irinki, ko dayake na yi mark din face dinki bama zan sake wautar d'aukarki a motata ba. Gabadaya matar nan tagama firgicewa ta rud'e iya rud'ewa sai gumi ne ke keto mata ta koina a gabadaya ilahirin jikinta, banda sambatu babu abinda take ", wayyo Allah hummm ...am..am "malam Dan Allah karkaji haushina kayi hakuri ka duba halin da yarinyar nan take ciki ,kayi gudu ko dan gudun abinda zai sameta.. "Dan Allah matar nan karki dameni , ki shafamin lafiya mana "ina kan yin iyakacin bakin kokarina ,I can't kill my self for you.. fly kikeson nayi akan titi ko me ? inji cewar direban . Muryarta cike da matsanancin kuka tace" bance ka kashe kanka ba, ko kazama tsuntsu akan titi ba ,but at least ka duba yanayin da karamar yarinyar nan take ciki " karkayi silar shigata maseefa da tashin hankali ,na gaya maka idan wani abu yasamu yarinyar nan karshena yazo, domin zan rasa aikina akanta " kaga kalli ga wani traffic can gabanmu .. "Eh nagani me za'a yi da trafic? " idan kakaraso gurin ka karya hannunka na hagu . "Na karya hannuna hagu kuma ya tambayeta a wulakance? Tace "Eh . shi kuma sanin da yayiwa hanyar bata da kyau, yasa yaki bin hanyar hagu kamar yadda tace yasoma kokarin bin dama. tasaka wani irin firgitaccen kara "Ina kuma kake kokarin bi ? " kai da nace maka kabi hannunka na hagu . "Wayyo Allah ni dai yau nashiga uka nashiga motar wahala , kana bukatar kabi hannunka na hagu ba dama ba .. " wai me ke damunki ne wannan matar ? "baki da ido da hankali ne ko me ? " bakiga hanyar bata da kyau bane dazaki dinga min ihu akai ,wallahi idan kika dameni zan saukeku anan ku nemi wata motar. " ni dai Dan Allah ka koma Kabi hannunka na hagu idan baso kake kayi silar rasa rayuka guda biyu ba alokacin daya acikin motarka ba.. " yaya kike son nayi I have told you this road is not good yayi maganar a zafafe .. ihu da masefa take masa ganin yaki sauraronta sai tuki yake hankali kwance, cikin kankanin lokacin taga ya bullo wata hanya wanda yayi daidai da hospital din, take ta sauke wata irin naunayen ajiyar zuciya "yauwa a she dai kasan abinda kake, ga hospital din da zamu shiga can mun iso ta nuna masa da hannunta "ai na d'auka wawa ne kai bakasan hanya ba shiyasa kaji ina ta maka maseefa "kayi sauri tunda mun karaso plz . "Dan Allah karki dameni da shirmenki din banza da wofi ,ba gashi kokarin danake yi ba kenan, yayi maganar tare da sanya hancin motarsa Cikin harabar hospital. matar tace "Ni dai ban nemi jin wani dogon turanci daga gareka ba, ka..ka daidaita tsayuwar motar kawai ,gama daidai tsayuwar motar keda wuya ta bud'e murfin motar da sauri tana ihun kiran"doctor!nurse! "Dan Allah malam taimaka ka fito ka d'aukar min yarinyar nan.. dareban yace " Dan Allah gani nan fitowa karki dameni," ko ni ne ubanta? yayinda ita kuma tashiga ihun kiran doctor da nurse jikinta na wani irin kirma ta zame Kan yarinyar dake kwance saman cinyarta, ta kwantar a kujera tasoma yunkurin fitowa tana kiran" hhh uhmm tana 'barin jikin fitowa da yarinyar ,a daidai lokacin da shima direban ya fito daga mazauninsa har ya bud'e bayan motar yace " kinga Dan matsa na taimaka miki ,da sauri jikinta na kyarma tabar jikin motar tayi baya . Direban yashiga kokarin fito da yarinyar yana kai hannunsa jikin yarinyar yaji yanayinnta ya sauya tayi nauyi sosai,yayi saurin cewa " ai sai matso ki d'auketa kin wani tsaya kamar wata dolowa kina kallon mutane . jikinta na rawa ta matso tasoma kokarin janyo hannayen yarinyar amman ta k'asa sai kyarma take tana kuka. "ki fito daita man kin wani tsaya kina rawar jiki ko ba yarki bace? Cikin rawar murya tace "zan d'auketa tana sake kai hannuta amman tsoron ganin yanayin yarinyar yasa ta kasa d'aukarta, ta matsa baya da sauri "shikenan abinda nake gudu ne ke shirin faruwa dani. direban ya dubeta a matukar firgice "naga alamun kina son sakani cikin tashin hankali ba? " ,ki d'auketa daga cikin motata ki sallameni na kara gaba neman abincina, " kayi hakuri abinda nake kokarin yi kenan sai dai bazan iya d'aukarta ba tayi nauyi sosai . Wani tunani direban yayi kar fa ya tsaya sanya yarinyar tazo ta mace masa acikin mota yashiga uku,wannan tunanin dayayi yasa ya tattara gbdy karfinsa yasoma janyo hannunwan yarinyar ya fito da rabin gangar jikinta yayin kafafunta ke cikin motar "oya kamata mu fito daita . fito da yarinyar keda wuya, ta dinga yin wasu abubuwa tamkar macijiya yayinda matar nan sai ihu take tana kuka tana kiran sunan yarinyar "NASREEN dan Allah ki rufa min asiri karki mutu "domin idan wani abu yasameki madam bazata barni a raye ba, kuka take sosai tana biye da bayan direban "look at how she curling like a snake may God have mercy inji cewar direban . gudu gudu sauri sauri suka iso bakin kofar shiga cikin reception " kin damu mutane da ihu ki matso ki bude min kofa mana . da sauri takaraso jikin kofar ta bud'e masa kofar suka shiga nurse naganinsu suka yi hanzarin karasowa garesu ,tare da amsar NASREEN a hannun direba, kai tsaye d'akin babban likita suka nufa daita ,suka kwantar daita akan gadon likita dake zaune yana dudduba wasu file dake gabansa,likita ya mike da sauri yana gyara zaman farin medical glass dinsa, ya isa gadon da NASREEN take kwance yasoma kokarin bata taimakon gaugauwa . ******** Tsaye take cike da kamewa da natsuwa a tsakiyar maza ,wanda a kalla zasu kai guda goma zagaye daita sai mata guda biyar ,wad'an da ke karkashin ikonta , acikin conference room. kowanensu sanye yake cikin shigar black suit , yayinda ita kuma take sanye cikin wata had'ad'd'iyar doguwar rigar abaya baka har kasa ,wace akayiwa adon da green stone ajikinta tun daga zaren har duwasu, tayi rolling kanta da mayafin abayar wanda ya fidda ainihin sahihin Shep din fuskarta da sirrin kyawunta. black hill Shoe ne sanye a kafafunta ,yayinda tsintsiyar hannuta yake d'aure da farin agogon diamond me matukar kyau da d'aukar hankali. wani irin sihirtaccen kamshi na musamman jikinta ke fitarwa ,wanda ke sanya duk wanda ya shaki kamshin yaji yasamu wata natsuwar ta daban a zuciyarsa. "me'ad kenan diya ga alhaji idris takai dake karkashin hukumar jahar kano ,alhaji idris takai hamshakin me kudi ne wanda ya rike mukamai daban daban agidan custom har zuwa yanzu dayake matsayin controller k'asa gabadaya . me'ad kyakkyawa ce ajikin farko ta bugawa ajarida ,mace ce first class me tsananin kyau da kyauwun sura wace ta tattara duk wani abinda cikakken d'a nmj me jini ajika yake bukata daga diya mace. "fara ce sol ko tabo daya babu ajikinta sannan doguwa ce sosai mara kiba, sai dai takasance irin matan nan ne masu shape din cokacola, wato daga samanta tana da cikar halitta qirji na dukiyar fulanin, yayinda cikinta ke shafe tamkar bata sakawa cikinta komai, daga k'asanta kad'an tana da wani irin Hip's na ban mamaki me tsayawa arai ,tana da doguwar fuska da hanci kamar yadda tsarin jikinta yake, sannan tana da karamin baki wanda ke zagaye pinky lip's , itace ta tattara dukkanin wani kyawun mahaifiyarta hjy Khadija da mahaifinta alhaji idris . me'ad takasance shiru shiru ce ,kasancewar bata fiyye son magana ba, wanda hakan yasa mutane suke mata kallon me shegen girman kan tsiya da miskila ,sai dai fa idan kashiga track dinta zata zage ta shuka maka rashin mutunci ,sam bata d'aukar wulakacin ko rainin hankali, amman idan bakashiga lamarinta ba, zakuyi shekara dubu babu daita babu ruwanta da lamarin mutu . babu cikakken d'a namji da zai kalli surar me'ad yace bai ga mace me cikar halitta ba, sai dai ya fad'i son ranshi. manage ce a M I K company's dake cikin ikoyi hotel. ahankali take jujjuya jikinta tana magana a tsanake cikin harshen tsadadden turancinta " am taking about our new product ," all of you are a ware of the reason ,why we call this crucial and important meeting ,we are here to discuss about the company's new product in this market , the importance of this meeting is the product must to do well in the market ,not just do well. " The product must be the very best in the market "ina fatan gabadayanku kun fahimci inda zancena ya dosa? suka kad'a kai ala'mun suna sauraronta sannan tacigaba da magana ahankali. " so the new toothpaste must be the very best in the market so that .... kiran wayan daya daga cikin members din dake zagaye daita ne ,ya d'auki kara sauti wanda ya karad'e ilahirin conference room din, har ya katse karshen maganar me'ad wace tayi tsaye sororo tana dubansu daya bayan daya, cike da mamaki da matsanancin 'bacin rai kafin ahankali idanunta ya tsaya cak akan wanda wayarsa ke kara ,tacigaba da kallonsa tamkar zata cinyesa tsabar bacin rai, domin abinda tafi tsana kenan arayuwarta tana magana me mahimmanci ana damunta da hayaniya mara amfani . A matukar tsorace shima ma'aruf yake dubanta kirjinsa na wani irin lugud'en baguwa da karfi, ya kai hannu ya shafa sumar Kansa sannan ya dane fargabansa yasoma kokarin d'aukar wayar ya manna a kunnensa batare da ya sake duban inda take tsaye ba yasoma magana "kana jina ina meeting karka damu kaje cikin dakin ka duba cikin wardrobe dina idan kagani ka d'auka kawai . sake ware seyx eye's dinta tayi dan tabbatarwa kanta abinda ke faruwa "mafarki ne ko gaske ?ma'aruf wayar ya d'auka alhalin tana tsaye agabansa. karewar d'aukar wayar ma ,har sautin muryarsa sun soma shiga cikin kunnuwanta suna mata kuwa , cigaba tayi da kallonsa cike da matsanancin mamaki da tashin hankali, "tabbas ma'aruf yana wasa daita tare da wasa da aikinsa , a daidai wannan lokacin, zuciyarta ce taitamata mata sake sake had'e da tsantsar tsanarsa acikin zuciyarta . "wannan bashi ne karo na farko dayake mata haka ba, a duk sanda suke taro makamancin haka, akoda yaushe shine mutun na farko dake kokarin break din rule dinta .... iya hassala tayi domin kuwa zuciyarta har tasoma tafarfasa akan sa, yayinda har lokacin ta kasa d'auke idanunta akansa ,wayarsa yake hankali kwance cike da izza da nuna ita din bakowa bace agabansa ." sai dai duk wannan abinda yake zuciyarsa cike take taf da matsanancin tsoron shugaban tasa...... mmn sudais ce 💗💗💗💗💗💗 'YAN CINKI 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 ~NA~ *AYSHA A BAGUDO* ~DEDICATED TO~ MRS ADAM ( YAR MUTAN KAGARA) page 6 to 10 ....."mr ma'aruf takira sunansa cikin zakakkiyar muryarta me dad'in sauraro da kashe jiki ,"can i please just have that phone of you's ......? cike da jin shi ma wani shegen kansa ne "yace am really sorry ma ,tare da meida wayar cikin aljihun wandonsa ya sunkuyar da kanshi kasa yana duban yatsun kafafunsa . "can you give me your phone now? ta sake yin maganar a fusace tana tsare gira. "i said am sorry ya fad'a cike da izza ,runtse idanunta tayi ahankali sautin muryarta ta fito atsawa ce "can you give me ur phone? ransa a had'e ya ciro wayar daga cikin aljihun wandonsa ya mike mata ta amsa tare da jan dogon tsaki ta d'aura wayar kan table tacigaba da maganar "now this is something I wil like to tell everybody. "if i smash the phone on the floor because of this stupidty...it's the highest level disrespect for your boss to be talking at a meeting.. "idan ma ba rashin hankali da tunani ba ," ta yaya shugabanku na tsaye tana magana me mahimmanci zaku dinga shigowa da waya, har wani jaki daga cikinku wanda yake ganin shi tsagera ne zai dinga receive Call "let me tell you all ,for the very last time. "me nace...? gabadaya suka had'a baki gurin cewa for the very last time ma, amman banda ma'aruf da zuciyarsa ta kusan bugawa tsabar takaicinta. "a tsawa tace "ina son ku sake had'a baki, ku maimaita abinda nace har kai mrs ma'aruf for the very last time ..... take suka sake maimaitawa ,tayi taku daya zuws biyu " let it be the very.. last time, that i wil cal a metting or you come to the conference room da zaku shigo da wayoyinku kai bama ring din wayoyinku ba ,hatta vibrating banaso jin , kai gbdy ma "i don't want to see your phones okay .. "yes ma. ta fuskanci ma'aruf sosai "mr ma'aruf this is ur last warning dakazo min da waya meeting ..... sannan ahankali ta fuskanci gabadayansu tace "akwai millions of people out there looking for jobs.. "basu samu ba ,masu kwalkwaluwa sannan suka san yadda zasu sarrafa tunaninsu da kwalkwaluwarsu acikin kasar nan ba irinku dakikai ba, ku kun samu amman kuke iskanci , abinda yakamata ku godewa Allah dayasa kuka kasance cikin wad'an da ke aiki acikn company nan. ahankali ta sake juyowa matukar fusace gefen da ma'aruf ke zaune sunkuye da kansa "mr ma'aruf.. ya d'ago da kyar yana amsawa da "yes ma. "ina gargadinka da wannan iskancin naka ya zama karonka na farko da karshe okay "ina nufin karonka na karshe you dare bring ur stupid phone to my meeting, " idan hkan takasance bazan koreka daga cikin meeting din ba, sai bayan nasa an tozarta min kai ,sannan nayi ratsaratsa da wannan banzar wayartaka sannan zanyi sack dinka daga aiki alright? takasara maganar a matukar hasale ."amshi banzar wayarka daga hanuna ta miko masa wayar tana me lumshe idanunta cike da 'bacin rai ,yasa hannunsa ya kar'ba wayar tare da furta "thank you ma a dakile . bata tsaya sauraresa ba tacigaba da magana cike da matsanancin bacin rai "yauwa mukoma kan abu me mahimmanci da muke duscusing before..kafin wannan stupid din ya katse mana hanzari " muna magana ne akan sabbin product dinmu na toothpaste da zasu shiga kasuwa acikin tsakankanin wannan lokacin "atakaice dai duk nasan kusan yadda muke son kasuwancinmu yakasance da yadda contains din fluoride dinmu zasu zo hannunmu ko ba haka ba? suka had'a baki gurin cewa "haka ne ma. "there is menthoi in it "we are hering very good report on that as wel dan haka kowanenku yaje yayi nazari akan tautaunawarmu domin yana da matukar mahimmanci.... can hospital kuwa, gudu gudu sauri sauri teacher chioma take a dogon korido din hospitar , kunnenta mane da waya ,cike da tashin hankali ta cire wayar a kunneta tana dubawa tagani ko kiran ya tsinke , ganin datayi har lokacin Number na tafiya yasa ta sake meida wayar kunnenta biyu biyu ta dinga taka matattakalar benen "wayyo Allah, Allah kasa ta d'auki wayar har ta karasa sauka akan step din kokarin neman layin mahaifiyar NASREEN take ... bangaren me'ad kuwa tana nan tsaye tana cigaba da dogon bayaninta akan yadda take son company's dinsu zai samu cigaba takowani bangare "dan haka we need to........ karar sautin waya ne ya sake katseta ,kame ta kyam atsaye tana me runtse idanunta a matukar fusace tace "wayar wani tacencen d'an iskan ne ki ring kuma? "waye wannan tantiri idiot din? "waye wannan dolon daya bari wayarsa tayi ringing alhalin nace ko vibrating bana bukatar ji, take gabadayansu suka shiga duduba wayoyinsu, yayinda still wayar ke sake kara . mr tahir wanda tun soma maganarta ya tsura mata idanunsa kawai yana kallon tare da cizan lip's dinsa yana ji aranshi dakace yana da iko da tuni ya tashi ya yaryarfa mata maruka tsabar haushinta dayake ji,a duniya babu macen dayake jin ya tsana kamarta .. "wani jakin mara jin magana da disobey ne yabari tsinanniyar culcuting dinsa ke damun kwalkwaluwar mutane..takarasa mgnr a fusace ? daya daga cikinsu ne yace "madam ,ai wayarki ce ke kara. gabanta yabada wani irin rassssssss tayi tsurutsuru da kyakkyawan idanunta tana kallonsu daya bayan daya ,zuciyarta na wani irin hamaukacin beting , yayinda har lokacin idanun tahir ke kanta yana kallonta yana ta'be baki ,wani irin abu taji tun daga tsakiyar kanta yana yawo daita har zuwa sansar jikinta tamkar an mata wanka da ruwan sanyi, kunya ce ko kuma nadama ce ta rufeta alokaci daya ita dai batasani ba cike da matsanancin mamaki ta tsurawa mutumin dayace wayarta ke ringa idanunta d'auke da karin bayani "yes it ur phone ma tahir ya sake maimaita mata ,ta juya bayanta ahankali inda ta'ajiye wayar tana duban screen din wayar jikinta na rawa rawa ,tabbas wayar ce ke cigaba da kara "kina iya d'auka madam watakilla kiran gaugauwa ne inji cewar mataimakinta... tsawon minti goma tana duban screen din wayar batare da tayi kokarin d'auka ba , ta juyo jikinta a sanyaye tana fuskantarsu gabanta na cigaba da bugawa, tacigaba da mgn"muna magana ne akan fluoride da mentho sai kuma abu na gaba , yadda zamu shigar dasu kasuwa da wasu bangarori acikin kasashen duniya ... takasa cigaba da mgn"am..uhm ..am da kuma wanda daman a kasuwa ta kasa karasa maganar saboda yadda jikinta da bakinta ke rawa ... yayinda teacher chioma tacigaba da kiran wayarta babu kaukautawa har takaroso harabar hospital din tashiga zariya " wayyo ni kam nashiga ukuna ta cire wayar a kunneta tana sake dealing "ina wannan matar ta ajiye wayar danaketa kira bata d'auka ba? ta sake cire wayar a kunneta tana dubawa "ki d'auki wayar nan dan Allah ,still wayar ring take amman saboda tsautsauran ra!ayi irin na me'ad taki d'aukar wayar sai ma neman izini datayi agurinsu "one minti .. ta juyo inda wayar take still dai chioma ce take kiranta acikin zuciyarta take adduar Allah yasa wannan kiran ya zama kiran lfy, dan bata ta'ba kiranta irin haka ba . tahir ne ya gyara zamansa tare shafa kasunbarsa yana kwa'be baki da fuskarsa yace "ranki ya dade ki d'auka mana killa zai zama kiran ne me mahimmanci.. tayi masa banza sai dai gabadaya ilahirin jikinta ya sake d'aukar rawa, ta d'auki wayar tana dubawa sannan ta mikawa daya daga cikinsu "can you take it to my office and just put it there for me? "idan kuma kagama karka dawo akan lokaci har mugaba gabatar da meeting kafin ka dawo, ya karbi wayar ya nufi hanyar fita ita kuma tacigaba da magana har yanzu dai muna magana ne akan flavor.. da kuma am uhmm wasu daga cikin flavor Wanda zamuyi amfani dashi acikin product .. chioma takalli gabas da yamma tana kuka tare da girgiza kai"bata d'auka ba shikenan tawa tasameni ina cikin tashin hankali ta kwasa da gudu zata sake komawa cikin reception, direban da tun fitowar yake watsa mata harara cike da da jin haushin 'bata masa lokaci datayi ya biyo bayanta da sauri yana kiranta "ke ke ina kuma zaki? " dawo nan ina kudina dakike kokarin wucewa? "ga wawa kinsamu ko, sai wani zariya kike awa jigida "kaga kayi hakuri mlm yarinyar da muka kawo har yanzu batasamu lafiya ba tukun mahaifiyarta naketa kira wayarta tayi ring ring amman bata d'auka ba dan Allah ka kwantar da hankalinka kaji zan baka kudinka. "oho sai yanxu na fuskance inda kika dosa saboda ni wawa ne , nacigaba da tsayuwa agurin nan akan matsalarki har sanda wannan yarinyar me kama da macijiya zata warke kafin na tafi gidana ko"dan Allah malama ni bani kudina na kama gabana"kasan abinda zai faru yanxu ? " dan Allah kabari naje nasamu doctor nagaya masa zai biyaka kudinka . ta juya zata wuce yasa hannuwansa duka ya janyota "na fahimta .."na fahimce maganarki amman miko wayarki nan "ka kwantar da hankalinka zan sa abiyaka kudinka. direba yace "ina wallahi bazan yarda ba ni dai miko min wayarki kawai najita a hanuna idan kin koma gurin doctor idan yabaki kudin alabashi sai ki dawo ki karbi wayarki. ya kwace wayar ya koma jikin motar ya jingina jikinsa zaman jira , ita kuma ta juya da sauri tana magana "shikenan naji ai ba laifinka bane kwata kwata baka da laifi ,laifin wancan shashar uwar tatace dataki daukar wayar .. shi kuwa direba yacigaba da tsayuwa agurin har ya daina hangota yana cike da mamaki "a'a wasu irin mugayen mutane ne wad'an nan mutane da suka haifi yarinyar kamar macijiya "ita kuma wannan stupid din tsamaninta nayita tsayuwa ne akan macijiyar nan har sai tasamu lafiya ko me ? yayiwa kansa tmbyr yana kwa'be baki. a daidai corido chioma suka had'u da doctor wanda kad'an yarage bataci karo da dashi ba tayi saurin ja da baya tana kuka tace "doctor. doctor yace "am ya'akayi ne yana duba agogon dake daure a tsintsiyar hannunsa "kinsamu mahaifiyarta a waya kuwa? "uhmmmmm ita naje kira a kasa amman wayarta tayi ring sau ba adadi bata d'auka ba . "ok dad dinta fa? inj cewar likita. "mom dinta muke da kusanci banida number dad dinta. "okay I will call thorough to her father duk abinda ake ciki i will let you know. "nagode doctor. ya wuce ita kuma takarasa zuwa d'akin da'aka kwantar da NASREEN . ******** mahaifin NASREEN zaune a makeken office din me gidansa suna tautaunawa akan lamaran daya shafi yau da kullun akan aikinsu. me gidansa sir malik yace "wad'an abubuwan suna da matukar mahimaci amman abinda nake son kamin shine ka meida hankalinka sosai akan lamarin aikinka sannan ka sake meida himma ta haka ne zaka samu cigaban dakake bukata arayuwa. "nagode sosai sir duk abinda ka fad'a na fahimata ,zanyi kamar yadda kace zan meida hankalina kuma Inshaallahu zaka sameni kamar yadda kake so ,ni dai burina ka taimakeni nasamu wannan karin girman. sir malik yace "karka damu fu'ad ,kaima ai mutum ne me kwazo sosai kuma gashi kana da matukar mutunci da girma acikin idanuna dan hk baxa kata'ba neman alfarma agurona na hanaka ba, ka kwantar da hankalinka i wil know what i am supposed to do for you. "akwai abubuwa na musamman danake son namaka bayan karin girma ni dai burina ka kwantar da hankalinka zuwa wani lokaci.. kirane yashigo wayarsa yayi sauri ciro wayarsa cikin aljihun wandonsa yana dubawa tare da cewa "excuse me sir zan daga kira. "karka damu fu'ad ka amsa wayarka kawai "hello . daga can bangaren doctor " yace hello kana yasoma yiwa fu'ad bayani abinda ke faruwa da yarinyarsa, a matukar razane fu'ad yace "what? "yarinta daga school meyasameta? yayi masa tmbyr ajere cike da matsanancin tashin hankali "kaga ganin nan zuwa yanzu ya katse kiran me gidansa dake dubansa tun fara wayarsa yace"meke faruwa fu'ad ? "kira nasamu daga hospitar wai anyi rushed din yarinyarta daga school zuwa hostopital "ok maza maza ka tashi kaje yanxu "ya mike tsaye cike da girmanawa yana me d'an rankwafawa "nagode sir. ******* bayan sun kammala da meeting ,tahir da ma'aruf har ma da matakin me'ad suna tsaye abakin get din company kowanensu fuskarsa a dagule ala'mun 'bacin rai tahir ne yasoma magana cike da matsanancin 'bacin "wai ku meyasa wani lokacin kuke behave wani iri haka ? " koda yaushe Ina kokarin nusar daku amman kamar masu kwalkwaluwar kifi bakwa fahimta, kwata kwata bakwa d'aukar shawarar da nake baku da mahimmanci akan yar rainin hankali matar nan ,abinda nake fad'a maku kenan kullun amman bakwaji muna cikin meeting wayarka tayi kara ka d'auka kayi magana kuma ,taganka lokacin daka d'auki wayar , fine tarigada takamaka red-handed sai kuma tace maka kabata wayarka kuma ka mika mata saboda kai dolo ne "common woman.. common woman for that matter dayake kaima dakikin ne kmr yadda tace shine kabata wayar bayan tagama wulakantaka sai kabata wallahi idan nine bazan bata ba komai za'ayi sai dai tayi amman wallahi kaji na rantse bazan bayar ba "abin mamaki ma sai lokacin da kake mika Mata wayar kamar wani dolo "wai so.. sorry ma..." a common woman for that matter tahir yakarasa mgnr cike da matsanancin fushi yana furzar da iska ta bakinsa .. ma'aruf yace" wani irin banzar magana kenan kake kokarin fad'a min hka ,da yake maka dadi abakinka? "misali lokacin da madam ta umarceni nabata wayar ban bata ba mekake tunanin zai faru dani? "babu wani abinda zai faru da kai malam dan nasan babu abinda zata iya yi.. "tahir babu abinda zai faru kace ? inji cewar ma'aruf. "wallahi bazata iya aikata komai ba duk cika baki ne kawai irin na mata. "really? inji cewar ma'aruf tahir yace "yes. "tahir kace babu abinda zai faru ko,? "amman bari nagaya maka wata mgn dabakasani ba,shekara da shekaru ina zaune zaman banza batare da nasamu aiki yi ba ni kadai nasan halin tashin hankali dana ciki a dalilin rashin samun aikin yi dakake kokarin ganin na aikata abinda zai sa wannan bazar matar takoreni a aiki . tahir yace " sai akayi idan takoreka ? "baka da hankali na zauna tsawon lokacin ina zaman jobless daga baya naxo nasamu aiki sai nayi focub akan aikina it's possible "nasan ka fahimci inda na dosa "yadda kake magana kamar wani d'an me arkizi alhalin ubanka ba kowa bane a kasar nan, bai ma da aikin a hanunsa ballanatana kace "a'a oo bari kayi masa magana yasamammin aikin Akarkashinsa dakake kokarin zagina , haka kawai na kwabsawa kaina a koreni abanza bazai yiwu ba wallahi gara dana bata na huta . mataimakin me'ad ne ya kwashe da wata mahaukaciyar dry har da buga kafasar daya a kasa . ma'aruf ya dube tahir yace "karamim dan iska ina fatan ka gamsu da maganata? tahir had'e rai tare da cewa " jima mana Karka nemi raina min hankali ta hanyar zagar min uba "babana yanabawa mutane maching din haya domin su dinga yi aiki suna kawo masa deliver, idan kabar aikin nan ,zan masa magana ya siya maka kaje katayin aikinka cikin kwanciyar hankali babu tsamgwama balle wulakaci...i wil ask my dad to buy you a motorcycle on an installment plan yakarasa mgnr yana hararar, ma'aruf ya had'e rai kamar zai fashe , zuciya taxo masa iya wuya mudarsir ya sake kwashewa da wata dry yana dafa kafad'ar ma'aruf "kayi hakuri ma'aruf nasan abinda tahir ya fad'a bai kai har cikin zuciyarsa ba ,kar kabari wannan maganar ta sake dagula maka lisafi ,how could his dad give you a job? "wani irin magana kake fada kenan mudansir? inji cewar tahir "wallahi ni har cikin zuciyata na fad'a masa haka, "ya daina daukar wulakacin daga wannan matar ,yasa a zuciyarsa ko babu taimakonta zai yi rayuwa . mudarsir yace "kai kai malam dakata "babanka na bada aiki me daraja meyasa kaxo kake aiki a karkashinta? "amman ku natsu kuji abinda zance muku yanzu duk wannan rawar jikin da kuke da zafin rai nifa ban d'aukar lamarin matar da girma ba ballanatana har ya tsaya min arai daga baya yaxo yana damuna "ba dai tamaka take da matsayinta ba,wanda yasa take jujjuya mu tare da gayamana duk abinda yazo bakinta ba? "kubarta tayi iskancinta son ranta tagama mu kuma sai musan ta inda zamu bullo mata "zamu 'bata mata rayuwa ta yadda zuwa gurin aikin ma zai gagareta "listen friend inji cewar tahir "me ya faru ne haka? " tun sanina da kai mudarsir banta'bajin ka fad'i maganar arziki ba ko shirya planing yadda mutun zaiyi arziki a duniya ba, sai dai yadda rayuwar mutan zai tagayyara ,yadda mutun zai daidaice da lalacewa ko raba mutun da rayuwarsa da makancinsu kawai ka iya. "yanzu dai mekake tunani zamuyi yanzu akan wannan matsalar? mudasir yace "inada master akan makarci ba "ba dai takamarta rike biro ba? nasan abinda zanyi akan wannan matsalar ta yadda aikin ma zai bar hannunta. "ma'aruf yace wannan tsarin yayi sosai gsky ni zanbaka had'in kai sosai duk abinda zakayi kayi ni zanbaka hadin kai ta 💯ta yadda zamu kai ga ci . "ku tsaya kubani minti goma ina da abinda zan fad'a "if it eventually happen ls, i might be asked replace her post saboda shine abinda nafi bukata.. kar daga baya, bayan komai ya kankama kuzo kuna min bakinckin kar abani ,ni dai idan za'a bani matsayinta nasa hannuna har ma da jikina gbdy gurin aiwatar da abinda za'a yi mata sai dai ni dai bazan biku inda za'a yi aikin ba duk abinda ake ciki kwa sanar min inji cewar tahir yana dryr mugunta, nan dai suka maganar akan mudasir da ma'aruf ne zasu je inda za'a raba me'ad da aikinta .... ******** kallo daya zakayi masa ka tabbatar da cewa ba cikin natsuwa da walwala da kwanciyar hankali yake ba, tunda ya yashigo asibitin bayan kiran daya samu na gaugauwa daga doctor. idanuwansa kawai ya tsurawa tilon diyarsa yana kallonta kirjinsa na tsananta bugawa da karfi "me ke shirin samun diyarsa dhaka ,da har ta fice cikin haiyacinta bata gane kowa? "yana son yasan kan matsalar yarinyarsa da dalilin kamuwa da wannan ciwon domin yasan ta inda zai shawo kan abun. "babban abinda ya d'aga masa hankali shine bai wuce har zuwa wannan lokacin me'ada batakaraso hospilata din ba, ya jima zaune akan dayan gadon yana fuskarta yadda diyarsa ke kwance iskar oxygen na taimakawa numfashinta, yaji an banko kofar da karfi an shigo, a sukwane ya dago tsumammun idanunsa ya watsa mata ita kuwa ko kallon inda yake zaune batayi ba, takarasa gadon da diyarta ke kwance ..... mmn sudais ce 💗💗💗💗💗💗 'YAN CINKI 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 ~NA~ *AYSHA A BAGUDO* ~DEDICATED TO~ MRS ADAM ( YAR MUTAN KAGARA) page 11 to 15 ..."wayyohlly Allah yarinyata ! wayyo tillon diyata farincikina " me yasa me ki kuma? "NASREEN dina ki bud'e idanukin ga momy'nki tazo, dan Allah karki min haka "what's it's? " please NASREEN talk to mummy . "mummy is here now, please open ur eyes and look at me .. gabadaya ta rud'e had'e da gigicewa ,cikin haka wata nurse tashigo d'akin sanye da kayan aikinsu na likitoci takaraso bakin gadon ta tsaya tana duba yanayin lafiyar yarinyar. "madam please don't disturb her she need rest . tsam me'ad ta mike tsaye ,jiki a sanyaye tana duban inda fu'ad ke zaune yana dubanta , tasoma takowa ahankali ta iso har in dayake, "honey what did doctor say? shi dai fu'ad zaune kawai yake a gurin tare da tsura mata tsumammun idanunsa yana kallonta cike da matsanancin takaicinta acikin zuciyarsa, har ta iso gareshi ta samu guri kusa dashi ta zauna tamkar kazar da kwai ya fashewa a ciki tana sake tambayarsa abinda likita yace. ya kalleta a kaskance a wulakance sannan yace "what did doctor say fa kike tambayata ? ta kad'a masa kai tana tsareshi da kyawawan idanunta batare da tace masa komai ba. a matukar harzuke yace "ke ..ina kike tun safe da'ake ta faman kiranki a waya baki d'auka ba? tayi sororo tana dubansa kirjinta na wani irin mahaukacin bugu.. "ko zaki ce ba'a kira wayarki bane da kike kallona kmr wace akayiwa karya ? "wai ke wace irin uwar banza ce ke , da bakinsa ciwon kanki dana yarinyarki ba? "nace wace irin uwar banza ce ke..? ta ware idanunta a waje saboda jin furucinsa gareta, dan bata taba jin yayi mata irin haka ba a tun iya zamasu tare . duk da furucinsa yayi mugun ta'ba zuciyarta amman haka ta danne ta rarrashi zuciyata domin batason su nuna hali agaban nurse gashi yarinyarsu na bukatar natsuwa , ahankali muryarta gurin cewa. "please honey don't say that to me ,you should know there must be a reason for me not to have picked my calls ,i was in a meeting .. "meeting .....ya fad'i hkn a fusace kana yashiga girgiza kansa cike da matsanancin takaicinta, sannan yacigaba "so the meeting was important that you couldn't see the call from ur daughter's school and call them back. "banzar kwalkwaluwarki bata gaya miki abinda ya dace kiyi ba ,bayan kin ga kira daga teacher din yarinyarki, "meyasa bakiyi tunanin ki kira wayar daga baya ba kiji meye matsalar , alhalin kinsa yarinyarmu na tare da lalura wanda at anytime za'a iya kiranmu a waya ? zaune tayi aguri daya tamkar wace aka dasa tsabar tashin hankali datake ciki. "wallahi kwata kwata me'ad baki da hankali ballantana abinda ake cewa t... a matukar tsawa ce ta daga masa hannu ta hanyar tadakar dashi "please stop stop doing that fu'ad "don't dare to do that to me "me kake nufi da nuna kanka da kakeyi kana min magana irin haka kmr kai da wata yarinyar cikinka duk ma me akayi daka d'auki zafi hk? "gaskiya bana son irin haka kad'ai na min domin yana maseefar 'bata min rai har naji brain dina ya fara craking ka daina dan bana bukata ... "even if you want to chastise me, not not in the presence of a woman .. "you are a disappointment woman to me me'ad, "wallahi nayi danasani aurenki arayuwata kwata kwata baki cancaci zama uwa arayuwarki..... rai 'bace nurse tak'ara gyarawa NASREEN kwanciya tare da lullu'be mata rabin jikinta ,sannan tasoma kokarin karasowa inda suke zaune "madam wai me ya faru haka kuke hayaniya.. ..? "ihunku na dustub din yarinyar nan ,gsky bama bukatar yadda kuke kokarin hana yarinyar samun natsuwar datake bukata,dan haka kuje doctor nasan ganinku ... me'ad ta juyo ta kalli nurse tana yatsin fuska sannan tace "kiyi hkr ba yin kaina bane tunzira zuciyata akayi. ta juyo ahankali gefen da fuad yake zaune "honey kaje doctor nasan ganinka.. bud'e bakinsa yayi cike da matsanancin mamakinta km at the same time yana dubanta.. "ya ka bud'e baki kana kallona ko bakaji abinda nurse ta fad'a mana bane cewar doctor nasan ganinka.. "what ? "idan ni naje gurin doctor ke fa ,zaman me zakiyi ? a matukar tsorace itama ta bud'e baki tana dubansa domin bata tsamacin jin haka daga garesa ba.. "i have been here since morning you go and see the doctor ... "honey what do you mean by you go.. you go ? tayi mgnr a fusace tana zabga masa uwar harara, " yanzu idan muje gurin doctor yace za'a siyawa yarinyarmu magani ni kake expecting zanje ko me ? "da kake wani cewa you go , kai zaman me zakayi idan ni naje? ",karka manta wannan bangaren hakinka ne tunda NASREEN ba shegiya bace kaine kayi silar zuwanta duniya.. "can you imagine what you are saying? "kai kai wallahi kwata kwata ba laifinki bane.. laifina ne da banzabawa yarinyata uwa ta Gari abin alfaharinah va, jifa abinda yake fitowa daga bakinki.. "ke yanzu baki ji kunyar abinda kike fad'a min ba? "dan Allah dan annabi ya issheni hk ... kacika min kunne da maganganunka marasa dadi i think bani kad'ai na haifi NASREEN ba tunda karigada karigani xuwa ,karigani kenan .. Ya tsurawa karamin bakinta idanunsa yana kallonta cike da matsanancin takaicinta Yana girgiza kai.. nurse dake tsaye tazama tamkar picture agabansu tana dubansu ta d'an waiga taga har lokacin NASREEN bacci take, ta juyo ta fuskancesu sosai kana tace "kunga ku daina jayayya akan wannan matsalar gabadayanku doctor yace yana son gani dan kuje office din doctor yana jiranku. ransu a'bace suka mike atare batare da kowanensu ya dubi d'an uwansa ba, domin kuwa cike suke da tsantsar jin haushin juna ,ita me'ad najin haushin fa'ud akan insult dinta dayayi agaban nurse ,yayinda shima zuciyarsa ke tattare da bakinciki abinda tayi masa na yana fad'a tana fad'a kuma agaban nurse, bugu da kari rasa tilon diyarsa dayaso yi adalilin sakacinta na rashin d'aukar wayarta," yanzu da wani abu yasamu yarinyar su "me zatace masa? "yasara wace irin mata yake aure data fi bawa aikinta mahimmanci akan diyar cikinta dashi karon kanshi, a tun sanda ya aureta har zuwa lokacin data haifar masa NASREEN bai da kwamciyar hankali, kasancewar aikinta data fifita akansu ,yayinda su kuma suke matukar bukace da kulawarta ,a matukar fusace ta suri hand bag dinta tayi hanyar waje tabarshi tsaye yana sake duban gadon da NASREEN dinsa ke kwance tana fidda numfashi ahankali hawaye na bin gefen idanunta, ahankali ya karasa bakin gadon yana cigaba da dubanta ya kai hannunsa ya shafa sumar kanta yana me jin wani irin ajikinsa, yana jin ina ma yana da hali,wallahi daya cire ciwon ya meida jikinsa domin shi yafi dacewa da wannan ciwon bakaramar yarinyarsa ba. " yana matukar son NASREEN arayuwarsa baya son bayason abinda zai ta'ba masa lafiyar jikinta ita kad'ai garesa.. ita kad'ai Allah yabashi a tun tsawon shekara goma dayayi aure ,kusan minti goma ya d'auka tsaye agurin yana kallonta yana Shafa sumar kanta hawaye na gangarowa ta gefen idanunsa ,ya ciro hanky cikin aljihun gaban rigarsa ya goge hawayen sannan ya gyara gashin daya zubo wanda ke kokarin rufe mata fuska sannan ya fito daga cikin d'akin. " abinda yabashi mamaki ba wuce ganin me'ad tsaye abakin kofar d'akin tana jiran fitowarsa ba, wanda shi a tsamaninsa ta dad'e da isa office din doctor, dogon tsaki yaje a fusace ya wuceta yana Allah wadai da halinta har ma da mata masu irin halinta. har suka Isa office din likita tunani yake ta yadda zaiyi da al'amarin me'ad gabadaya zuciyarsa tasoma tsirewa da halaiyenta abubuwa dayawa zuciyarsa ke raya masa akanta.... doctor najin motsin shigowarsu ya d'ago yana nuna musu gurin zama sannan ya sake meida kansa kan file din NASREEN dake gabansa, ahankali fu'ad yaja daya daga cikin kujerun dake gaban doctor ya zauna yana ware kafafunsa tare da jijiga kafarsa daya, itama dayar kujerar kusa dashi taja ta zauma tana cicci magani.. zaune suke gaban doctor suna jira daga garesa, doctor ya numfasa kana ya sake d'ago idanunsa yana dubansu daga bisani ya mikawa fu'ad hannu suka gaisa . doctor yace "ammm ..i salute ur courage for all your effort on your child, Allah yabata lfy yasa muci amfanin yaranmu gabadaya.. ahankali suka had'a baki gurin amsawa da "ameen kana suka ja bakinsu sukayi shiru suna sauraron doctor. doctor yacigaba mgn "amm thank God NASREEN has been responding better to treatment now, better than before but her condition now is some what critical than before. me'ad ta zaro idanuwanta waje tare da dafe daidai saitin zuciyarta tana duban doctor "inna lillahi wa inna ilaihi rajiun ," wannan wani irin tashin hankali hk ,ya Allah karkasa nashiga uku akan yarinyar nan .... takarasa mgnr jikinta na wani irin rawa, take kuma hawaye yasoma ciccikowa a idanunta . fu'ad batare da ya kalli inda me'ad take ba yace "doctor ban fahimci zancenka ba . doctor yace "no, just calm down okay , it's not as if her condition is that critical but you know she's a sickle cell patient ,there for, she need a lot of attention.. wanda nake tunani dole daya daga cikinku zai ajiye aikinsa at least for a mouth domin bawa NASREEN kulawar data dace . atare gabansu yaba wani irin rasssss saboda jin abinda doctor yace... "saboda zaman daya daga cikinku yana da matukar mahimmanci domin irin magungunan dazamu bata yana bukatar kaida,domin ana bukatar ta dinga shan maganin akan lokaci zuwa lokaci ,and most importantly, she need ur care, love and attention more than before... " atakaice dai yarinyarku na bukatar kulawarku da duk wani abinda iyaye yakamata suyi domin kwantarwa ya'yansu da hankali, me'ad tayi tsuru tsuru da idanu tana sauraron doctor daki daki tamkar zata shige cikin tunaninsa, yayinda fu'ad yayi shr kawai a tun sanda doctor yasoma bayani kai kawai yake girgizawa tare da had'e hannuwansa guri daya yasanya tafukan hannunwansa ya rufe fuskarsa dashi, shi kad'ai yasan irin rad'ad'in da zuciyarsa take ciki akan wannan matsalar... fu'ad ya cire hannunwasa yana duban doctor da idanunwasa da suka gama canza kala "doctor idan na fahimci zanceka sosai wani daga cikinmu zai natsar da zuciyarsa ya zauna tare daita ? doctor yace "haka nake nufi saboda kulawarku is very important agurinta. "saboda ina yawon samum masu irin lalurarta amman yadda nayi muku bayani haka nake treated a similar case dinta, before wani lokaci sai kuga yaro yasamu lafiya ,ina tunanin wannan tsarin dana kawo muku ,zai samu kar'buwa domin itama ina son tasamu irin wannan kulawar daga gareku ,ina me tabbatar muku matsawar daya daga cikinku zaiyi kokarin bata gudumuwarsa wallahi zakuyi mamakin yadda yarinyarku zata dinga samun saukin ciwon ... "dan haka atsakaninku sai ku zartar da wanda zai zauna gida tare daita, ka ko ba dan komai ba dan Allah kod'an saboda ni ku taimaki rayuwar tilon diyarku dan Allah you guy's should do this. murmushin fariciki me'ad tayi tana duban doctor "no no karka damu doctor da wannan matsalar Inshaallahu zamu san abin yi ,ai wannan bazai zama wani abun damuwa ba ,dan tabbas zamuyi yadda kace zamuyi magana da juna idan muje gida.. docto yace" thank you. shi kam fu'ad shiru yayi yashiga duniyar tunanin yadda abinda Doctor yace, gabadaya ya kasa magana saboda cajin da kwalkwaluwarsa ke yi, yana jin kmr ya zubda hawaye ne akan NASREEN yana matukar tausayawa rayuwar yarinyar ahankali ya juyo ya dubi me'ad dake zaune a gefenshi ,ganin murmushi kwance akan fuskarta, ya d'an sanyaya masa zuciya ,hannusa me'ad ta riko cikin tafin hannuta tana murzawa, da kyar yasamu ya mike tsaye suka fice daga office din likita zuwa d'akin da NASREEN take kwance , tare da sanyata gaba suna dubanta gabadaya ta sake ramewa , ji suke ina ma ciwon ya dawo kansu ta tsira da lafiyata... daren ranar sam me'ad da fu'ad basu samu damar runtsawa ba ,hatta bacci barawo wannan karon baiyi nasarar d'aukar daya daga cikin iyayen NASREEN ba, tunani kawai suke ta yadda al'amarin zai kasance, "cikinsu waye zai ajiye aikinsa domin bawa yarinyarsu faricikin da kulawar data dace ? "shi ne zai tallafi rayuwar diyarsu ya zauna agida ko me'ad da rayuwarta ce kawai ,bazata iya bawa aikinta ba, saboda mahinmmacisa gareta? fu'ad ya tambayi kansa yana satar kallon inda take . har kusan asuba fu'ad na zaune rike da hannu NASREEN ya tasata gaba yana kallonta still hannunta daya cikin nasa, yayinda me'ad ke tsaye bisa kafafunta tana kaiwa allah kukanta daman ita macece me yawon ibada, kullun daren duniya bata runtsawa batare da tayi ganawa ta musamman da ubangijnta ba, ita din mace me yawon ibada da kamewa tare da tsayuwar dare ,a duk inda ta tsinci kanta zata tabbatar da ta tsaya bisa kafafunta gurin bautawa Allah, illarta daya saurin d'aukar zafi akan abinda bai kai yakawo ba, da kuma d'aukar aikinta da mahimmanci datayi akan bawa yarinyarta kulawar data dace .. kwanansu daya aka sallamosu daga hospital suka nufo gida tare da jakar magagunguna ,yinin ranar da suka fito daga hospital me'ad na d'aki tare da NASREEN rungume ajikinta tana shafa sumar kanta tana zance zuci kasancewar week end ce ranar babu aiki "Allah sarki haka hukuncin Allah yake gashi dai daga ita har mahaifinta lafiyarsu kalau basu d'auke da wata lalura sannan su ba ss bane balle as, gabadayansu aa ne , gashi sun haifi sickle cell .. "ina matukar sonki NASREEN dina ,Allah ka raya min ita,saboda banason rasata arayuwata duk da kasancewarta sickle cell kabarni na rayu daita ,Allah karka jarabeni darashinta " hakika wannan matsalar yancine gab iyaye mata akan yaransu naganin sun kula dasu sosai fiyye da komai hawaye ne ke gangaro mata daga cikin kwarnin idanunta . ganin baccin NASREEN yayi nisa sosai yasa ahankali ta lalla'ba ta kwantar daita tare da sanya pillow tayi mata makari dashi had'e dayi yi mata kiss a goshinta sannan ahankali tashiga shafa sumar kanta tana jin wani irin tsantsar tausayin yarinyarta me gauraye da kauna mara iyaka, ta lullu'beta da blanket me taushi , sannan ahankali ta sauko daga kan gadon tasanya takalmanta ta d'auki tire dake ajiye akan bed side Wanda ke d'auke da ruwan databawa NASREEN magani ta sha, bud'e kofar d'akin tayi ta fito, kai tsaye main parlour'n din gidan ta nufa yayinda fu'ad ke zaune akan doguwar kujerar dake zagaye da parlour'n ,sanye cikin jallabiya ash colour kafarsa daya ya lankwasashi karkashin dayar kafarsa, yayinda dayar kafar ke mike system ne agabansa wanda ya d'aurashi akan cinyarsa ,yana dane dane tare da tura sakonnin , tazo ta wuce shi tashige kitchen sanye da wata yar karamar riga iya cinyarta da hula net wanda ya bayyana gashin kanta . ta ajiye tiren hannunta sannan tasoma gyaran kitchen tare da goge koina daga karshe ta isa gurun gas tana gogewa tana tunanin wanda zai ajiye aikinsa acikinsu domin bawa yarinyarsu kulawa ,aiki take sai dai zuciyarta na can ga satar kallon fu'ad dake zaune yana aikinsa, saboda farin glass dake tsakanin kitchen dinta da parlour'nta bai hanasu ganin juna ba, duk wanda ke zaune a parlour'n tabbas zai hango wanda ke cikin kitchen, haka zalika wanda ke cikin kitchen zai hangi na parlour, yayinda har wannan lokacin fu'ad na zaune wanda ya mike kafafunsa yacigaba da aikinsa hankali kwance yajiyo sautin muryarta daga cikin kitchen "honey . batare daya d'ago kansa daga abinda yake yi ba yace "yes love... "should i serve you food now? "no just give me 5 minnutes i must finish this project, it's due on Monday.... cak ta saida abinda take yi tare da shiga wani yanayi na bugawar zuciya kana a tsanake ta juyo tana fuskartashi "zakayi sumint dinsa on Monday fa kace? yace "eh zanyi sumint dinsa ranar monday saboda mahimmancisa . da auri tasoma kokarin fitowa daga cikin kitchen bakinta bud'e sannan cike da matsanancin mamaki tasoma magana jikinta har rawa yake " honey wace monday kenan kake magana akai? "Monday jibi mana ya bata amsa, batare daya d'ago ba yacigaba da danne dannesa. "ta dubesa a kaikaice tana sake mamakin jin abinda ya fad'a tayi kusa dashi sosai ta yadda kowanensu zai iya fuskantar d'an uwansa "meyasa zakace zaka gurin aiki ranar monday ? "ko ka manta abinda Doctor ya fad'a mana ne ? "me doctor yace mana ? yayi mata tambayar yana me dakatar da abinda yake sannan ya d'ago ya fuskanceta . "haba ya kake kokarin ka manta, akan NASREEN mana. "eh doctor yace dole cikin ni dake wani ya ajiye aikinsa ya zauna gida tare daita . "yauwa a she baka manta ba. fu'ad yace "so what are you talking about? me'ad ta soma fusata dan haka a zafafe tace "what do you mean by.. that, dole mutun daya zai ajiye aikinsa ya zauna tare daita agida .. "uhmm wannan kuma ai aikinki ne, ki zauna gida tare daita, ta yaya kike tunanin ni na ajiye aikina na zauna gida? "this is common sense now it's your duty a matsayinki na mace" ni me zan zauna nayi a gida? yakarasa mgnr ahankali yana kallon cikin kwayar idanunta, gefe daya kuma wani irin bugawa zuciyarsa keyi da sauri sauri . ahankali ya numfasa kana yace " kiyi tunani sosai me'ad akan wannan lamari kodayake bai zama lallai ki gane, abinda nake nufi ba tunda baki aiki da kwalkwaluwarki ya fad'i hkn yana nuna gefensa kansa.. "no no fu'ad banason irin abinda kake min "and you know I don't like all this can of thing kasan sarai banason kana min magana kana ta'ba kanka domin kokarin meidani mahaukaciya mara tunani.. ya sake kai hannusa daidai gefen kansa "wannan ai common sense ne ,kema kuma kinsa da haka ,yakamata amatsayinki na mace tunaninki yagaya miki akan kece zaki zauna agida bani ba . dakata fu'ad "automatically, its your duty to stay with her . "for what? "me kake nufin akan saboda mai? "okay tunaninki nabar aikina na zauna agida alhalin ga ki .... "me kake nufi da bazaka bar aikinka ko me ko me? "kai kanka kasan kai yafi dacewa ka zauna agida tare da yarinyarmu kasan wannan. "gsky bakida hankali da tunani wallahi ,kwata kwata tunaninki baya gaya miki gasky da har kike expecting ni yakamata na zauna gida tare da NASREEN alhalin gaki mace kina nan baki mutu ba . "nasan aikina nane, ba sai ka gaya min ba, ta hanyar meidani tamkar mahaukaciya ,"amman ni aikina yana da matukar amfani ga rayuwarmu gabadaya, dan hk ko kaki ko ka so you will be the one that wel stay at home with our daughter...... "wannan ai akinki ne me'ad meyasa kike kokarin meidashi kaina. ? "i know but my job is mo..re more important you just can't tell me to what's my du... sautin tarin NASREEN ne yakatse mata hanzari ..tarinta kawai suke jiyowa babu kaukautawa da wani irin sauri fu'ad ya zabura ya mike tsaye jikinsa na kyarma "kingani ko kinga abinda maseefarki zai haifar ko dan.. ..ai kafin yakarasa fadar abinda yake son fad'i tarin ya sake yin karfi ai da wani irin mugun sauri tayi hanyar d'akin NASREEN aguje tana ihu kiran sunanta ..... mmn sudais ce 💗💗💗💗💗💗 'YAN CINKI 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 ~NA~ *AYSHA A BAGUDO* ~DEDICATED TO~ MRS ADAM ( YAR MUTAN KAGARA) page 16 to 20 .......aguje suka karasa shiga cikin d'akin, kowannensu na rige rigen isa inda take zaune dafe da kirjinta tana cigaba da tari tamkar ranta zai bar gangar jikinta, da sauri fu'ad ya haye saman gadon ya janyota zuwa jikinsa ya rungumeta yana kiran "sorry baby!!! yayinda gabadaya ilahirin jikin me'ad ya d'auki rawa "tarasa me ma zatayi ,sai sambatu take "me kuma ya sameki baby nah ? "some one should help me plz "wa meye hk ne.. ..? zagayowa tayi dayan gefen ta haye gadon tana maimaita "me yasa meki baby nah ?"dan girman allah ki sausautawa zuciyarmu bazamu iya jure kallonki cikin wannan tashin hankali ba. "ya ubangijin ka taimakeni kabawa yarinyata lafiya tayi rayuwa kmr sauran yara. NASREEN tayi tari da karfi tare da cewa "da..dady wa...water.. a matukar firgice yace " watare me'ad give me water plz ..... me'ad wace ta sake rikicewa tace uhmmm water ? "dan Allah malam kije ki kawo min ruwa yanzu yayi maganar a fusace .. "sorry honey, ta duro daga kan gadon ta tsaya sanya takalmanta . "a fusace yace run now. " i am runing "im runing !! ta bud'e kofar da karfi ta fice batare da ta tsaya rufo kofar ba. "ahankali fu'ad yashiga jijiga NASREEN "sorry my baby ,"Inshaallahu zakiji sauki,yashiga shafa kirjinta yana dubanta. da matsiyacin gudu me'ad tashige kitchen, madadin ta bud'e fridge ta d'auko ruwa kmr yadda ta shigo da niyyar yin hk, sai kawai ta hau zariya acikin kitchen din tana zagaye kayayyakin amfani tsabar rud'ewar datayi.. da kyar Allah ya taimaka tasamu ta bud'e kitchen cabinet ta d'auki cup sannan cikin sauri ta dawo ta bud'e fridge ta d'auki robar ruwa nestly water ta fito da mugun sauri . NASREEN kuwa tarin datake sai gaba yake, gbdy ta kamkame ajikin dad dinta, tana tari babu kaukautawa abun gwanin ban tausayi, jikin fu'ad na rawa yace "kiyi sauri mana kin ... bai karasa ba, sai gata ta shigo d'akin da sauri , ta mike masa cup dake cike da ruwa, ya amsa ya kai daidai bakin NASREEN "sorry baby take some water kinji, NASREEN tasoma kur'ban ruwan ahankali ahankali. . me'ad ta zauna tare da raku'bewa agefen fu'ad tana duban yadda yarinyarta tasoma galabaita . NASREEN tasha ruwa kad'an tana sake yin tari "sorry my baby "ki d'an kara shan ruwan kiji, inji cewar fu'ad still tana makale ajikinsa . jiki a sanyaye me'ad" tace sannu baby nah Allah yabaki lfy, sai da fu'ad ya tabbatar data sha ruwan sosai sannan ya tambayata "ruwan ya isheki ? ta d'aga masa kai ala'mun eh sannan ya mikewa me'ad cup din batare daya kalli inda take ruku'be ajikinsa ba . ya rungume diyarsa tsam ajikinsa ,yana shafa mata baya yana sake yi mata sannu , itama me'ad kwantowa sosai tayi jikinsa tare da d'aura hannuta a jikin NASREEN tana mata sannu, banda sautin sannun da suke mata baka jin sautin komai a d'akin ,gabadaya hankalinsu da natsuwarsu yabar gangar jikinsu ,ya tattara ne ga tilon diysrsu ,kowanen daga cikinsu ya kasa d'aukar ciwon nata da sauki, ciwon NASREEN a zuciyarsu yake , sai dai dukkaninsu sun kasa aiwatar da abinda likita ya fad'a musu akan nuna wa yarinyar soyayya da kulawa har ma da bata natsuwar zuciya shine zai sa tasamun cikakkiyar lafiyarta . tsawon minti talatin suna tare daita , suna aikin yi mata sannu ,ahankali muryar yarinyar ta fito "mummy come and sleep here with me, takarasa mgnr tana nunawa uwar gefenta da hannunta daya. jikin me'ad na kyarma tace "you mean there ta nuna inda NASREEN ta nuna da yatsan hannuta . NASREEN tace "yes mumy , take me'ad ta yunkura tabar jikin fu'ad ta zagayo gefen inda NASREEN ta nuna mata tana furta kalmar "okay my baby. fu'ad ya kwantar da NASREEN yana shirin mikewa tsaye domin barin d'akin, yaji NASREEN ta riko tafin hannunsa cikin nata "dady sleep here too. "na kwanta anan kikace? "yes both of you are sleeping here with me . me'ad ta kwanta gefenta na dama, haka shima fu'ad ya kwanta gefenta na hagu ,suka sanyata tsakiyarsu tare da lullu'be ta da bargo ,sannan suka tsura mata idanunsu suna kallonta cike da matsanancin kauna. ahankali NASREEN ta matso jikin dad dinta ta kwanta ajikinsa tana sauke numfashi, dan kusan tafi son babanta sau dubu akan mamanta, domin dad dinta yafi bata kulawa ba tun yanzu ba ,sabanin mahaifiyarta datake nuna tafi son aikinta akanta .... shiru fa'ad yayi yayinda hannusa ke saman kafad'ar NASREEN yana shafawa ,ahankali yake tunanin abubuwan da suka faru awanin 20 da suka gabata tsakaninsa da rikitacciyar matarsa, sannan ya d'ago kansa cike da jin haushinta, suka had'a ido da me'ad, bai tsaya wata wata ba ya zabga mata harara me tattare da tsantsar danasanin aurenta dayayi arayuwarsa. itama batare da 'bata lokaci ba ta rama tana kwa'be masa baki,har NASREEN tayi bacci suna kwance agefenta suna aikawa junansu harara. daga bisa ta sauko daga kan gadon ta zagayo tana kokarin bud'e kofar d'akin, zaraf taji fu'ad ya riko laulausar tafin hannuta cikin nasa yana massaging ahankali ahankali yana cigaba da dubanta tare da jin wani sauyi ajikinsa gbdy taji jikinta yayi wani irin laushi ,amman ta dakewa zuciyarta ta sanya dayan hannuta ta zare hannunta cikin nasa, takarasa ta bud'e kofar ta fita . shima ya mikewa yayi tsam yabiyo bayanta bayan ya gyarawa NASREEN kwanciyarta tare da lullube mata rabin jikinta, atare suka shiga d'akin nata, tana karasa shiga tayi bayi ta barshi tsaye jikin kofar dakin yana aika mata da wani irin kallo dake kashe mata gabobin jiki. batayi cikakken minti biyar a bathroom ba ta fito d'aure da farin towel iya cinyarta wanda ya bayyana santala santalar cinyoyinta dake fitar da wani sheki da hasken kyau kmr wace take amfani da madara ko yougot, yayinda zuwa wannan lokacin fu'ad yayiwa kansa mazaunin a gefen gadonta tare da jingina rabin jikinsa da pillow ya mugun tsurawa kofar bayin ido. kallo daya tayi masa tasan abinda yake nufi da wannan biyota din dayayi, tasan bawai wuce jarabarsa ce taciyosa ba ,ita kuma duk abinda zaiyi sai dai amman bazata bashi had'in kai ba, ta gabansa taxo ta wuce tana goge sansar jikinta da wani karamin towel , ta isa gaban mirrow tana jujjuya jikinta da mazauninta Wanda yasa joystic din fu'ad harbawa da sauri,take ya matse joystick dinsa da kafafunsa tare da runtse idanunsa, yana jin dama bai kawo kansa ba,dan gabadaya yanayinta yagama nuna masa irin rashin mutuncin dake tattare daita. ahankali me'ad ta d'auki body lotion dinta na so white tasoma shafawa sansar jikinta . "me'ad idan kingama kizo ina bukatarki ...... , tayi masa banza tacigaba da abinda take, sai data gama murazawa jikinta , lotion sannan ta d'auki turarenta na oud moon ta feshe jikinta dashi sannan tasoma kokarin karasowa inda pray mate yake, ta daidaita tsayuwarta da niyyar zata fara sallah taji sautin muryarsa ya doki cikin dodon kunneta me'ad ! me'ad!.! ya ambaci sunanta a karo na biyu cikin d'aga murya da yanayi na fushi da kosawa... lokacin daya fahimci bata da niyyar amsawa saboda har ta tayar da sallah ya d'aga murya cikin zafin rai ya buga mata tsawa mai firgitarwa, yace "ke me'ad ba dake nake magana ba ne kika tada sallar da babu lada acikinta sai tarin zunubi ? "ina matsayin mijinki ace ina miki magana tun kafin ki tayar da sallah amman bazaki amsa min ba, kiyi sallar amman ki tabbartawa kanki baki da lada ko kwaya daya kasancewar kinsa abinda ke tafe dani gareki.. wannan karon har ta kai raka biyu na nafila har ta sallame amman ko d'aga kai me'ad batayi ba ballanatana ta amsa masa har ma yasan ko tasan da zamansa agurin , al'amarin daya sake daga masa hankali kenan da firgitarwa, domin duk lokacin da wani abu zai gindaya tsakaninsu, sai tayi yunkurin tauye masa hakinsa wanda yasara dalilin hk, wani lokacin ko zata bashi had'in kai sai yayi sha wahala da karfinsa koda kuwa hkn bazai wa zuciyarta da gangar jikinta dadi ba. zuciyarsa kamar zata fashe ganin ta sake mikewa ta tayar da wata sallar, muryarsa da jikinsa rawa suke yace "wallahi wallahi me'ad kina cikin halakakkiyar rayuwa matukar baki saurari uxirina ba, har abada bazan yafe miki hakina da kike dannewa ba . ya mike tsaye da kyar yana layi tmkr wani mashayi gbdy yanayin idanunsa sun sauya haka ma gangar jikinsa ya sauya . yasoma kokarin barin d'akin.. me'ad ta gaugauta sallamewa ta mike tsaye tasha gabansa tana dubansa a matukar firgice kirjinta na wani irin bugawa, tsoro da matsananci firgici fu'ad ke hangowa cikin idanunta, sake matsowa tayi kusa dashi sosai kmr zata shige cikin jikinsa tare da kamo hannuwansa duka cikin nata still tana kallon kwayar idanunsa ,ya kawar da fuskar gefe saboda a yadda yake jinsa zai iya marinta had'e dukan mutuwa . batare databfurta kalma daya ba, tasoma tafiya tare dashi taji bai d'aga kafafunsa ba, ta juyo ahankali tana dubansa, "muje nabaka hakinka dakake kokarin yimin Allah ya isa akai saboda baka da kunya.. a fusace ta saki hannusa tasoma ciccire kayan jikinta tana fillingin dashi sannan muryarta ta harzuke tace "fu'ad baka da kunya baka da imani,ka duba kaga halin da tilon diyarmu take ciki amman har zuciyarka ke kokarin aikata wani abu.. "kullun kake cin wannan abun kmr tuwo batare da na ta'ba yunkurin hanaka ba, yau kad'ai da nuna bana bukata ,shine har da kokarin kai karata ga mahalicina alhalin ina tsaye gabansa domin Kai kukanmu gareshi.. "kukanki dai kike kaiwa ga Allah ban dani, dan nasa ba addua kike min ba, gabadaya addu'oinki ,sun ta'alaka ne akan kanki da aikinki da kike mugun so ne "ko zaki ce karya ne? "sannan zance kullun kike bani nake ciki, da yaya kikebani hakina? "ince da karfina nake ci ba dan kina bukata ba, kullun aiki aiki dai kamar agogo... "naji duk maganganunka babu karya, but les go to the bed kayi abinda ke cin ranka, karkayi kwana watsawa jikinka ruwa.. ya fixge hannunsa da karfi cike da matsanancin 'bacin rai yana nunata ala'mun ta shiga hankalinta "kije kawai na fasa yi. "what? "abinda kunnuwanki suka jiyo miki shi nace . "baka isa ba, nace baka isa ba fu'ad sai kayi, tunda kasanyani katse abinda nakeyi akan taka bukatar . ya juya a fusace tasaya duka hannuta ta janyo shi sukayi luuuuu suka fad'a saman makeken gadonsu ,ta rukunkuneshi ajikinta ta cire rigar dake sanye a jikinsa ,tare da ware mata kafafu ta d'aura bakinta kan joystick dinsa tasoma sucking dinsa tana lumlumshe ido, tare da d'aura hannuta duka saman kirjinsa tana murza kan nipples dinsa ahankali. take wani dadi yasoma kaiwa zandariyarsa ziyara, ahankali ta yunkura tayo samansa ta had'e bakinsu guri daya, ai fu'ad najin soft lip's dinta bai tsaya tsanya ba ya cafki laulausar harshenta jikinsa har rawa yake ya dinga tsotsa ,wani irin dadi ne ya kawo musu farmaki from know where atare suka dingajin ya dawainiya da gangar jikinsu ,jiki a mace yacigaba da tsotsar lip's dinta yana lashewa ahankali ya zira harshensa cikin kunnenta yana sucking nan yaji ta fara wani irin nishi alamar ta d'auke wuta, ya kai hannuwansa duka yana murza kan jajayen nonuwanta, haba ai take zandariyarsa ta sake mikewa "uhnmmmm ya sauke naunauyen ajiyar zuciya yayinda joystick dinsa ta fara tsiyaya tana diga ,haka ya dinga shan kunneta yana murza kan nipple dinta ,joystic dinsa na tsalle ya soma zuba sambatu lokacin data d'aura bakinta kan nipples dinsa tana tsotsa tana cicciza kan, wani damka yayi mata, ta yadda bazata iya kwacewa ba , haka suka dinga murza junansu , sai data me'ad ta tabbatar dayazo hannu sannan tasoma kokarin barin jikinsa "wayyohlly allah ina kuka zaki? ta watsa masa wani irin kallo da idanunta da suka gama sauya kala "bakace bakayi ba? "ka tashi ka wuce abinka kawai "plz me'ad karki min haka wallahi a hannu nake, kalli kiga yadda na fara diga.. ta kai bakinta kan joystick din ta ciza kad'an tare tsotso ruwan dake fita daga ciki... fu'ad yayi saurin lumshe ido tareda jin wani abu tundaga tsakiyar kansa har zuwa tafukan kafafunsa yasoma jinsa agajemare yana yawo,"me'ad ya furta ahankali yana sake janyota zuwa jikinsa ya rungumeta tsam yana kissing wuyanta zuwa dukiyar fulaninta "dan Allah kibarni nayi , na yafe miki Allah ya isar dana miki ........ "nagode daka janye kalmar gareni sai dai kasani banida bukatar aiwatar da wani abu makamanci hk ahalin yanzu, "rashin lafiyar NASREEN ya tsaya min arai, solution yakamata mu nema akai.. "karki damu da wannan, tunda kece uwa ke yakamata ki zauna tare daita.... a tsawace ta mike daga jikinsa batare da ta shiryawa hkn ba ,"banason jin wannan kalmar daga bakinka fu'ad ,kasan dai sarai banason irin hk kaine zaka zauna daita bani ba. shima ya mike a matukar fusace "wai me kike nufi dani ne ? "me'ad naga ala'mun fa kinason hassala zuciyata akan matsalar nan . .."wannan kuma damuwarka ce batawa ba, "bansan nawa kake dauka salary dinki ba dazaka damu mutane akan wani banzan aikinka ba.. "okay... ya furta atakaice yana me d'aukar jallabiyarsa yasoma kokarin sanyawa yana magana " kicigaba kinji ,kicigaba da wulakantani, karki janye kudurinki ,ki tsaya ki tallafi rayuwar diyarki" kece zaki tabbata cikin bakinciki saboda ni nmj ne yakarasa mgnr yana ficewa daga d'akin.. bayan fitarsa ta zauna jagwab akan damuwar kujerar dake cikin d'akin dafe da goshinta "oh my God, wai meye hk ne? "me fu'ad yake nufi dani? "me yake nufin akan shi nmj ne? "no no no impossible nasan abinda xuciyarsa ke tunani amman Inshaallahu hkn bazai taba faruwa ba.. ta d'an jima zaune agurin tana saka da warwara har dare yayi tsakiya sannan ta mike taje tayi wanka saboda yanayinta gabadaya yagama sauyawa, ta duro alwala ta fito . daren ranar kwana tayi tana kaiwa allah kukanta da buk'atunta, wanda batasan hkn datake abu ne mara kyau ba, ta hana mijinta samun natsuwa tare daita amman ta kwana tana nafilfili alhalin tabar aikin farilla me mahimmanci akanta, wanda dayawa matan wannan zamanin suke aikata hkn arayuwarsu Allah ya kyauta .. yadda me'ad ta kwana tana raya daren hk mudarsir ya kwana gurin bokansa, da zai masa aiki akanta, ta yadda zata tagayyara tabar masa kujerarta datake takama daita . anyi komai acikin daren kmr yadda ya mudansir ya bukata, bokansa yabashi layar da zai mata amfani dashi ta hanyar sanyata cikin kujerarta a office . ******* washegarin ranar lahadi tahir da ma'aruf ne ke tafiya cikin mota ,tahir ke direving ma'aruf na zaune agefensa , sautin waka ne kawai ke tashi acikin motar tahir nabi wakar ahankali tamkar shine mawakin .. _don't worry about a thing cause every little gonna be alright singing don't worry, about a thing every little thing gonna be alright rise up this morning smile with rising sun..._ friend ! friend !! ma'aruf yakira sunan tahir har sau biyu amman sam hankalinsa bai garesa yana ga tukinsa da music din dayake saurare, har sai da ma'aruf ya sake kiransa yana ta'ba kafad'arsa "dan Allah aboki ka kashe wakar nan hk haba mutun kmr wani jujal... "wai meye ne kake damu mutane suna saka da cin duniyarsu ,ni gasky banason irin hk yacigaba da tuki yana kad'a kai . "dan Allah kayi kasa da volume din wannan wakar nan da kakeji . tahir ya rage sautin music tare da cewa "na rage me ya faru ? "there is something i want to tell you. "okay ina sauraronka ? ma'aruf ya shafa fuskarsa kana yace "ina tunanin wani abu daya , idan naje office ranar monday first person i will meet is our boss .. tahir ya d'an juyo ya kalleshi cike da mamaki sannan ya meida hankalinsa ya fuskanci tukinsa tare da furta" okay . ma'aruf yacigaba da mgn "if she wants me to remin in that company, she should inrease my salary or promote me, idan ba haka ba ina tabbatar maka zan ajiye aikin nan kawai na huta amman gaskiya bazan zauna ba ga wulakaci, gashi ba wani alabashin kirki nake samu ba,gara nakara gaba kamar yadda kagaya min shekaranjiya ,matsawar bazata min abu daya cikin biyun dana lisafa maka ba. cike da matsanancin mamaki tahir yace" what ? " zakayi resign ko me ma kace? "yes of course ma'aruf ya bashi amsa zanyi resign . " abokina zakayi resingn fa kace? me kake fad'a haka kamar wani mara tunani, kar na maka karya kaga duk decumeent din dake kan table din MD na masu neman aikiyi ne kana saurarana ko? " ba sai na tsaya gaya maka ba kai kanka kasan duk yawan takardun cv din dake kan table dinta na masu neman aiki ne, wand'a madam take neman wad'an da zata kora aiki a company, ta d'auki wasu sabbi ta maye gurbin wanda ta kora, yanxu idan kace zaka ajiye aikinka ko neman promotion letter what ever sha dakace, kasan wannan matar mara imani zatayi sack dinka ne fa, kuma wallahi kar na maka karya, idan takoreka ni banida wani abinda zan iya maka ,bawai kazo daga baya kana min knowking kullun cewar na taimaka nabaka kudin zaka ci abinci. "kaga wannan makirar matar da kake gani babu abinda zata zarta acikin wannan company yaki yiwu ba, duk abinda ta zarta yazama final.... ka fahimceni ko? "duk mutumin datace a ayi sucked dinsa, will definitely be fired... beside , you know both of you are not in gud terms kanajina ai, " so I will advise you to be calm, if you like take heed else, it's you own peril. "ni abinda zan sake ce maka kayi a hankali, sannan kabi matar nan ahankali domin tsira da aikinka," kai tsaya ma when exactly did you employed work ,that you are seeking promotion letter or whatever ? "dan haka ka natsu ka dawo cikin natsuwarka da hankalinka ,sannan ka duba lamarin tunda mudansir yasanar min da komai ,kaga idan aiki ya bar hannuta, hannumu zai dawo daga sai kayi abinda kagadama ... "amman idan kuma kasan kasamu aikin poultry ne kamar yadda obasonjo yakeyi ,daman gaku nan tsawonku daya dashi wajen gajarta , kake wani cika baki, babu damuwa ,kai zaka fara kiwon kaji fine , idan kuma kai kanka kake son zuwa neman aiki company'nsa zaka dinga aikin kwashe musu kashin kaji ,ko bawa kaji abinci, ko yawon siyar da kwai kaji company zuwa company ya rage hannuka, amman bawai bakasamu wani aikin dayafi wanda ke hannunka ba, kake bukatar ayi sackd dinka da aikin dake hannuka a halin yanzu, it will definitely be difficult... "kai kai kwata kwata ma wannan bazan tunaninka baiyi ba... ina gbdy ma baka da hankali. ma'aruf ya bud'e idanunsa dake runtse sannan yasoma mgn "ummm you know I have been planing to go on leave from next week. "eh wannan tsarin dai yayi ,amman idan Allah ya kaimu next week din nan ka amshi leave kasan dasani babu ruwana ,sannan ka sanyawa zuciyarka cewa katafi kenan bazaka sake dawowa wannan company da sunan aiki ba, bazaka sake dawowa ba, ka tafi ka tafi kenna har abadin abada ,babu wanda ya isa yasanya baki a dawo da kai matukar bamu ne agidin abun ba, "ba dai ina gaya maka gaskiya ba kanawa mutane taurin kai ba, "fine, next week you will leave ba ? "badamuwa ka tafi kawai, watakilla tafiyarka ta, zamemin alkhairi ,ni na samu double promoted, kasan kuma daman wani lokacin sai matsla ta afkawa wani aguri sannan wani yake samun cigaba arayuwarsa, ka fahimceni "may be you should quickly go for your leave i have say my own sha .... "if anything happens, don't blame me for not advising you. "saboda ku mutane bakwason gasky arayuwarku, kullun kunfi son ana yaudararku kodayake daman karya,daci ne dashi ajikin dan adam. " da yanzu yadda kayi magana nan na baka goyon baya akan abinda zuciyarka ke ingizaka nason barin aikinka ,"nace maka kayi sauri ka aikata hkn ,jeka rubuta letter barin aiki, da yanzu kana nan kana jin dadi, "domin zaka d'auka shawarar arziki naba alhalin gaba kuka zakazo kayi dani ,"dan gashi ina baka shawarar arxiki ta yadda zaka inganta rayuwarka amman sai wani cika kake kana batsewa, kana wani fad'in iska da dagawar banza, akan abinda baka dashi ,sannan babu a house dinku .. "tsaya ma na tambayeka ,yanzu idan kavar aiki nan mezakayi,? "ko zaka tare da wadancan banzayen yammatan naka guda biyu da, kafarsu bata daidaita guri daya ba , daya ta kalli badan daya ta kalli ilorin , su zakaje ka zauna tare dasu agida idan ka amshi leave ba ? "you are supposed to be thankful to have a good job that is good enough for you , you are provide your self and your parent "shine zakace zaka bar aiki, zakasan baka da wayo sai ka bar aikin nan ,dan ina tabbatar maka sai kaga kudi kace kashi ne.. "uhmmmmm ma'aruf ya sauke naunauyen ajiyar zuciya batare da ya kalli inda tahir yake ba yace "friend ,it seems you were listening to song before you can continue to play it plz,"saboda gabadaya maganganunka babu na d'auka aciki.. "ok haka ma zakace? "ma'aruf yayi masa banza tamkar bada shi yake ba. "uhm daman haka gsky take, but shekaran jiya dana dinga zigaka dadi kaji, amman dayake yau gsky na fad'a maka kaji haushina, daman gsky d'aci gareta . "na dai ji kabar ni dai haka da banzaye magangunka masu kokarin tarwatsa min zuciya inji cewar ma'aruf. "ok do whatever you like "idan kaga dama karewar leave kabar duniyar gbdy yakarasa mgnr yana kure volume din radio motar.... mmn sudais ce 💗💗💗💗💗💗 'YAN CINKI 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 ~NA~ *AYSHA A BAGUDO* ~DEDICATED TO~ MRS ADAM ( YAR MUTAN KAGARA) page 21 to 25 ........kwance yake akan makeken gadonsa kiran italy yana sharar baccinsa hankali kwance lullu'be cikin bargo me taushi da kamshi ,yaji sautin ringing din wayarsa ta karad'e ilahirin d'akin. a natse ya farka daga bacin dayake batare daya bud'e idanunsa ba, yasoma lulubar inda ya ajiye wayar ,sannan ya bud'e idanunsa da kyar, saboda baccin dake cikinsu, dan sam jiya damuwa bai barsa ya samu ishashen bacci ba sai bayan da aka idar da sallar asuba tukun yasamu bacci ya d'aukeshi . sunan wanda yaga yana yawo ajikin screen din wayar ne, yasanshi mikewa da sauri yana yaye bargon daya lullu'ba dashi kana yasoma kokarin amsa wayar cike da muryar bacci "hello sir. daga can bangaren me gidansa ne ya amsa da hello fu'ad bacci kake na tasheka . "no karka damu sir gud morning ya fad'i hkn atare yana runtse idanunsa tare shafa sumar kansa. "okay ya lafiyar jikin NASREEN hope she's getting better? "taji sauki sosai sir nagode da kulawa sir . "karkadamu ammm..., ina bukatar ganinka ogently yanzu idan baka komai. "babu abinda nakeyi sir ganin nan zuwa yanzu just give me 10 to 15 minti sir . "alright sai naganka me gidansa yakatse kiran . shi kuma ya sauko daga saman gadon yana mika had'e da yin salati sannan ya nufi bayi yayi yayi burushi tare da yin wanka shap shap ya fito daure da madaidaicin towel iya cinyarsa wani towel din na rike a hannunsa yana goge sansar jikinsa . yagama ya tsaya gaban mirrow yasoma shafawa jikinsa lotion tare da bin ilahirin jikinsa da turare me dadin kamshi ,yayi corm din sumar kanshi, ya matsa inda wardrobe dinsa yake ya fidda wasu kaya riga da wando sai farar riga me dagon hannu daga ciki ya d'aure wuyansa da jan kyalle wato tie ya karasa inda jerin takalmansa suke ya d'auki shoe baki wanda zai sanyawa kafafunsa, yakoma ya zauna bakin gadon yasaka ya Mike tsaye cikin hanzari ya d'auki karamar wayarsa ya zira cikin aljihun suit dinsa ta ciki , sai agogonsa na fata daya d'auka yana kokarin d'aurawa atsintsiyar hannunsa at the same time kuma yana ya kokarin bud'e kofar d'akinsa . cikin sauri ya fito daga d'akinsa batare da ya tsaya tunanin sanyawa cikinsa wani abu ba , daf da zai karasa bakin kofar fita daga parlour'n . me'ad dake tsaye a kitchen tana kokarin had'a musu breakfast ta kwaso a guje tana haki ta sha gabansa " kai kai ina zaka tun da sanyi safiyar nan hk? takarasa mgnr tana me daidaita tsayuwarta a bakin kofar tana jijiga ilahirin jikinta tana dubansa kasa da sama a matukar wulakacin "you can go anywhere fu'ad..we must settle this matter on ground before you go out . wata uwar hararar ya banka mata sannan yace "wata magana kenan zamuyi settle? "maganar Monday mana. "yazamuyi ranar monday waye zai zauna agida ya kula da yarinyamu ? "you know I cannot afford not to go work .. saboda rashin zuwana zai haifar da mummunar damuwa, idan baka manta ba, kasan abinda ke faruwa a campany'nmu a yanzu ,amman idan ka manta bari na tuna maka" duk kuskuren dayasa mutun yayi wasan fashin zuwa gurin aiki daidai da rana daya, baza'a kar'bi any excuse ko complaining daga garesa ba, the next thing korarsa za'a yi .... "an so what? ya furta a matukar fusace "ina ruwana da korar mutanen da'ake, wannan aikin naki fa kin gadamar yinsa ne ,if not zan iya d'aukar lalurarki batare da kinje koina ba..dan haka karkiyi tunanin ni fu'ad zan kasance daya daga cikin mazajen da suke kasancewa hajiya ba, sannan ni ba bawanki bane da zauna a gida tare da yarinya alhalin gaki a raye baki mutu ba ,dan hk in your dity life don't expecting me to be baby sitting . kina mugu mugun bani mamaki me'ad da har kike kokarin na amshi abinda yazama *'YAN CINKI* hakika kin kusan haukacewa akan wannan iskanci da kike kokarin bijirowa dashi dan har abada bazaki ta'ba samun damar meidani mijin haji. "dakata ka saurareni. fu'ad! fu'ad!! sau nawa nakiraka? "dan Allah malam kiyi mgnrki kina 'bata min lokaci . tasoma karairaya tana jujuya masa jiki sannan tace "but you have oready know your nature job ,and you know you have the chance to stay at home with our only daughter. "fu'ad ..takira sunansa cikin sanyayiyar muryarta me shiga jiki "i cannot afford it.. "i cant, i don't have the opportunity, luxury and chance that you have got with your job.. "short up there i don't have either "i need to be punctual! yayi maganar a tsawa yana mata mazurai. sororo tayi tana dubansa tare da cewa "why did you say that ? "ok kina bukatar kisan dalili ba? tace "eh. "ok yanzu lokacin da zan samu karin matsayi a office dinmu ya kusantoni ,"once I am punctual and hardwarking i will be among the people that will be promoted , kin fahimci abinda nake nufi anan ,karin albashi zan samu ata dalilin haka, dan haka bazan yarda sanadin son zuciyarki ,na zauna gida d'aukar duty'n dayazama naki ba . tunda yasoma magana ta zuba masa idanunta kawai tana kallonsa a matukar wulakance tana jin wani irin zallar 'bacin rai, na ratsata akan banzayen zantuttukansa .. . a wulakance ta gyara tsayuwarta tana kwa'be fuska sannan tace "by how much zaka samu Karin albashin da kake bud'e makoshi akansa ? "qarin dubu hamsi ne kacal akan 100k, making 150,000 a mon..... ai bai karasa maganar ba ta d'aukeshi da wani gigitaccen mari dauuuuu kake ji. "what? ya furta a matukar firgice tare da dafe kuncinsa da hannunsa daya, yana dubanta cike da matsanancin mamakinta .. "fu'ad you are most useless man in this world ... "i said you are a useless man fu'ad ,ta sake furtawa da karfi tare da tsareshi da manyan idanunta " yanzu akan wad'an kananan kud'ad'en har ka iya bud'e bakinka kake fad'ar wannan banzar maganar dadddd... 150,000 thousand .." yanzu fu'ad bakaji kunyar abinda ka fad'a ba? "i can afford to pay you that salary times three from my salary of 550,000 idan ka amince zaka zauna a gida . "you slapped me me'ad? "idan ka sake furta irin banzar maganar dakayi yanzu , i will slap you again, "zan mareka saboda bakasan darajar kanka dana iyalinka ba. "kika mareni me'ad? tare da tsura mata kyawawan idanunsa yana kallonta cike da matsanancin takaicinta da mamaki. yadda yake kallonta yasa tayi shiru ta kasa ce masa komai, sai zuciyarta dake wani irin dokawa ,gabadaya jikinta yayi mugun sanyi, ba jikinta ba hatta zuciyarta rawa take dauriya kawai take a tsayen datake a gabansa.. "kiyi magana mana me'ad kina kallona zuciyarki na nadamar abinda kika aikata min ko. "kodaye ai nasan bazaki iya magana ba a daidai wannan lokacin da zuciyarki ta kaiki karshen nadama .. gabadaya ilahirin jikinta ya sake yin sanyi, tayi saurin had'iye busashen yawun daya tsaya mata amakoshi tana zare idanu tare da tsotsa tsakiyar kanta "uhmmm ammm.. ta kasa mgn. "ai bazaki iya magana ba me'ad, be...because you know I am making sense ,you expect me to leave my job with increment of 50k na zauna gida kula da abinda yazama *'YAN CINKI* "kinga kema yanxu kin kasa furta kalmar da hankali zata iya d'auka yakarasa mgnr yana pointing daidai saitin kwalkwaluwarsa da yatsan hannusa ,abinda yasan tafi tsana arayuwarta kenan ,yacigaba da mgn. "it's just common sense me'ad akan dakikancinki ... "ahankali ta runtse idanunwata kad'an hannuta dafe da habarta sannan ta bud'e su fesss bisa fuskarsa yana kallonta kmr zai cinyeta, ahankali ta matso kusa dashi sosai ta yadda har suna iya jiyo numfashin juna, ta rike kwalar rigarsa tana sake gyara masa "I am sorry my husband , masoyina abin kaunata abin alfaharinah ,dan Allah kayi hakuri ,kayi hkr akan abinda na aikata ma a yanzu, am really sorry honey "ok yanzu kwakwalwarki ta dawo aikin dayakamata tayi a tun farko fu'ad ya fad'i hkn yana hararta .. me'ad ta sake lumshe idanunta na 2 second sannan ta bud'e ahankali "you know akwai maslaha akan dukkanin wata matsala dazata kunno kai tsakanin ma'aurata , yanzu musan wani mataki yakamata mu nemo domin magance matsalar datake kokarin kunno kai cikin rayuwarmu data tilon diyarmu da Allah ya bamu. ta sake matsoshi sosai tamkr zata shige cikin jikinsa "kana jina ko in dai akan karin albashin dazaka samu ne na 150 000 thousand naira ,Allah ya karigada ya kawo mana maslaha yanzu yanzu acikin gidan nan ,matsawar zaka fuskanceni takarasa mgnr tana murmushin jin dadi "abinda nake bukata daga gareka bai wuce ,you stay at home. ya bud'e bakinsa kenan cike da matsanancin mamakinta zai yi mgn ta dakatar dashi ta hanyar cewa "listen ! listen !!to me first don't argue with me kaji abinda zance tukun. "ka zauna a gida okay, ni kuma zan cire 150k acikin salary dina nabaka batare da 'bata lokaci ba dan kasan gurin aikinka basu biyan salary akan lokaci, kallonta yacigaba dayi cike da mamakin rashin hankali da tunani irin nata yana murmushin dayafi kuka ciwo yana girgiza kai, tsaye kawai yake agabanta amman ji yake kmr ya shake mata wuya da kofar har sai ta daina numfashi ... ta kai hannuwanta duka ta dafa kafad'arsa tana goga masa brest dinta a kirjinsa domin sake d'aukar hankalinsa wanda batasan hkn datayi kara cusa masa haushi da takaicinta tayi, domin kuwa bai ji komai ajikinsa ba illar zallar kiyayyarta data meye gurbin soyayyar dayayi mata abaya. muryarta a sanyaye tace"ka fahimceni honey zan baka kudin, sannan bazaka sanyawa motarka fuel acikin kudin ba domin zuwa gurin aiki , bazaka tashi very early to rush up to work ba, bazaka kashe kudi akan siyan kayan abinci ba, bazaka kasance daya daga cikin wad'an da trafic zai tsare a hanya ba , da daidai sauran abubuwan da suka danganci matsalolin rayu.... "you.. you must be crazy woman ya katseta a fusace yana watsa mata wani irin mugun kallon dayasa hantar cikinta kad'awa da sauri .."you are going insane ," imagine the rubbish that's comin out of your mouth.... "bule.. bule kamata yayi tun lokacin da kika fara wad'an banzayen kalaman naki nasoma d'aukeki da gigitaccen marin dazai sa ki dawo cikin natsuwarki daya gudu yabar gangar jikinki . "wallahi azim me'ad dakace ni irin namijin dake dukan mace ne, da yau na miki dukan mutuwa, dukan mutuwar bazaki iya tashi ba... you are stupid ni kike son meidawa useless husband da bai san ciwon kansa ba over my dead body ... sororo tayi tare bud'e bakinta tana dubansa a tsorace sannan tace "me kake nufi da wad'an maganganun naka? "bansani ba.. "oh my God wlh me'ad ban ta'ba tunanin haukan son aikinki ya zarta hk ba "ni kike expect na zauna gida na zama me kula da diyarmu alhalin gaki " Bari na gayamiki dolenki ki ajiye wannan banzar aikin naki ki zauna gida kibawa diyarki kulawar data dace da kanki amman bazai ta'ba yiwu ba kice ni... atsawace tace "kamin shiru ,what do you mean by it can't happen ? "dakata fu'ad bafa nason abinda kake min banson rainin irin wannan hankalin fa. "dolenki dai ki zauna gida, ko kina so ko ba kya so "you must take care of your bby by yourself not me, dakikiya kawai dabasan yancin kanta dana diyar cikinta ba.. "kai ma ai ubanta ne meyasa bazaka zauna ka ajiye aikinka kayi taking care dinta ba ? "wani excuse kake son nabayar agurin aiki da kake wannan banzar maganartaka ? "ok ni ne ma nake miki maganar banza ko?" to kisan dasanin matukar ni nake aurenki ba kece kike aurena ba dole kibar dan iskan aikin nan da kike takama da gadara dashi ,idan company ta tmbyeki dalili rashin zuwanki kece mijinki ne yace ki zauna agida ki kula da diyarki sai muji me zasu ce. cike da ihu da hargagi tace "wallahi baka isa ba, sam hkn ma ba me yiwu bane fu'ad sai dai kasan yadda za'a yi ,domin kasan taimakon da albashina yakeyi a gidan sabanin naka da bai taka kara ya karya ba . "ji stupid ..ji abinda kike fad'a ,gaya min "what does your money do in this house? a matukar tsawace ya sake furta "stupid amfanin me kudinki yake acikin gidan tare da d'auketa da wasu maruka guda biyu ajere.... taja baya da sauri dafe da kuncinta jin marin da fu'ad ya d'auketa dashi wani irin dummmmm taji yana mata kuwa acikin kunneta yayinda jiri yasoma kokarin d'aukarta ,kofar datake jingine daita ne ya taimaka ya riketa ta tsaya bisa kafafunta "shashan cin banza shasha cin wofi .. "kad'an kikagani sannan yanzu zan fito miki da nawa true colour din, zaki san baki da wayo, zan koyar dake hankalin da iyayenki suka gagara baki yakarasa mgnr tare da cewa dan Malam matsa daga hanya na wuce shasha kawai dabatasan ciwon kanta ba, kin d'auka tsoronki ake ji ne ko me ? ganin ta kyame guri daya taki bashi hanya yasa hannusa daya ya fixgota da karfi ya makata kan kujera, a guje ta mike tayo kansa gadan gadan ta shige jikinsa "ka mareni fu'ad ? "an mareki me zakiyi? " idan akwai abinda zakiyi kije kiyi, idan kuma ke kike ciyar dani daga yau ki daina stupid kawai . "ko ban ciyar dakai ba but at least kasan akwai abinda kudina yakeyi acikin gidan nan. "sannu hjy mariya.. ..dan Allah leave the road for me. ta sake motsoshi tana fuskantatshi har suna shakar numfashin junansu "bazan matsa ba ,kai yanzu har ka isa kace kudina baya amfani acikin gidan saboda kai din butulu ne, daman ku maza halinku ne butulci, ko me za'a muku arayuwa wata rana sai kunce ba'ayi muku komai ba "ki matsa na wuce ina da abin yi ,kinsa ba tun yau nake warning dinkin akan maganar abinda kudinki yake acikin gidan nan ba, amman bakijin magana ko, ni fu'ad bansaki yin abu dole acikin gidan nan ba , duk abinda nagadama na kawo kiyi hkrn amfani dashi ,idan kin siya wani abu cikin salary dinki wannan matsalarki ce dan ban saki ba . "kai kasani butulu kawai wanda bai san mutunci ba ,kuma wallahi dole ka ajiye useless work dinka, ka zauna ka kula da yari.... motsin bud'e kofar parlour'n yasa ta katse maganarta tare da juyowa ahankali .. mmn sudais ce 💗💗💗💗💗💗 'YAN CINKI 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 ~NA~ *AYSHA A BAGUDO* ~DEDICATED TO~ MRS ADAM ( YAR MUTAN KAGARA) page 31 to 35 .........diraving kawai yake cike da matsanancin tashin hankali ,yayinda gefe guda na zuciyarsa ke wani irin harbawa, saboda jin bugun zuciyarsa yake tun daga tsakiyar 'kirjinsa har ilahiri sansan jikinsa. wanda hakan ya haddasawa gefen kansa sarawa da 'karfi, gaba d'aya ji yayi jikinsa ya mutu, tu'kin ma na neman gagararsa. A hankali ya gangara gefen titi yayi parking tare da dai-daita tsayuwar motarsa ya rungume sitiyarin motar had'e da d'aura kansa bisa hannuwansa yana fitar da numfashi me tattare da hucin zafi. tun daga nesa Sajida wace daga gidan me'ad gidan misna ta wuce, ta hango motar fu'ad parke a gefen titi cike da matsanancin mamaki ta soma rage gudun motarta har sanda ta iso daf da inda motarsa take . tayi parking ta fito da hanzarinta daga cikin motarta ,hankalinta a matu'kar tashe ta doshi inda yake, tana kare fuskarta da tafin hannuta saboda hasken ranar daya dallare mata idanu , jiki a sanyaye ta 'karasa jinkin motar ta tsaya tare da kai hannuta ta k'wank'wasa glass d'in motar, wanda hakan yasa fu'ad 'ko'karin d'ago idanunsa domin ganin kowaye. A hankali ya sauke kyawawan idanunsa a kan fuskarta dake cike da mamakin ganinsa a gurin , runtse idanunsa yayi sosai yana jin wani irin d'aci a ransa mara misaltuwa .... da hannunta tayi masa alama yayi warning glass din motarsa, sai da ya furzar da iska me zafi ta bakinsa sannan yayi 'kasa da glass din, kana ya mai da kansa kan sitiyari kamar yadda yayi da farko , shi kad'ai yasan irin rad'ad'in da zuciyarsa take ciki a kan wannan matsalar dake shirin kunno kai cikin rayuwarsa da al'amuran gidansa. sautin muryarta yaji ta doki dodon kunneshi "lafiya Abban NASREEN kayi parking a gefen titi haka? "idan ma wani abu ne ke damunka, kamata yayi ka samu ka qarasa gida first, domin samun natsuwar zuciya saboda tsayuwarka a nan is very very risking.. ta 'karasa mgnr tana zagayo wa d'ayan gefen tana me k'wank'wasawa alamun ya bud'e mata . da 'kyar ya samu ya danna wani abu a cikin motar domin bata damar shigowa ba tare da yace mata komai ba saboda kansa dake cigaba da sarawa. ta bud'e murfin motar jikinta na rawa tare da janye jakar briefcase d'insa dake kujera me zaman kanta, ta zauna tana masa fari da ido muryarta a sanyaye tace " sannu Abban NASREEN na san duk damuwar nan taka ,baza ta rasa nasaba da matsalar kawata ba? ,"amman ka yiwa Allah kayi hakuri Insha Allahu komai zai zo da sau'ki, me'ad ce bata d'aukar shawara na rasa abinda ke rud'arta.... A hankali ya d'ago idanunsa tare da waigowa gefen da take zaune ,idanuwansu suka tsarke cikin juna, suna had'a ido kowanensu ya kafe d'anuwansa da kallo zuciyoyinsu na ayyana musu abubuwa da yawa . kallon cikin kwayar idanunsa ta cigaba da yi tana jin wani abu na yawo a jikinta ,had'e da hango wani irin tashin hankali kwance a cikinsu , a hankali ya soma kokarin motsa bakinsa " kika ce kin rasa abinda ke rud'ar ta ? ta d'age masa girarta d'aya tana sake masa fari da ido muryarta a sanyaye tace "eh Abban NASREEN ni dai gsky bansani ba, amman idan kasan abinda ke rud'arta ka taimaka ka gaya min ? " girgiza kansa kawai yayi ba tare da ya sake cewa daita komai ba, ita kuma ta bishi da mayataccen kallo tana yaba kyawun halittarsa, ganin yadda jikinsa yayi matukar amsar kayan dake sanye ajikinsa ya kara hura wutar soyayyarsa acikin zuciyarta ,ji take tamkar ta shige jikinsa ta rumgume shi sannan ta rarrashsshi a kan tarin damuwarsa . A hankali ta sauke nannauyen ajiyar zuciya tana furta" hamson kenan .....yau dai gani ga ka kyakkyawan mutumin da zuciyata ta dad'e da kamuwa da matsanancin sonshi, kyakkyawa son kowa 'kin wanda ya rasa ..." am very sorry da abinda kaji yana fitowa daga cikin bakina , domin na dad'e ,ba tun yau ba nake son amayar maka da abinda ke cikin zuciyata, "a gaskiya fu'ad na dad'e da afkawa cikin duniyar kaunarka ,idan ba zaka damu ba zan so ka bani damar kawo farin ciki cikin rayuwarka. " fuad ina tsanin sonka tun a ganin farkon dana maka a rayuwata, wasu dalilai ne suka hana ni fahimtar da kai tsantsar 'kaunarka gareni, amman yanzu ga dama ta samu ," ka natsu ka saurare ni ,ina son ka aure ni na maye maka gurbin da k'awata ta kasa cikewa a gidanka. bai san sanda yayi saurin dafe kanshi ba cikin matsanancin 6acin rai sakamakon jin abinda ke fitowa daga cikin bakinta, wani tsaki ya ja da 'karfi kana yace "kin zo ne ki 'kara min damuwa a kan wanda nake ciki ko me? "calm down my hamson i thoueght you feel of fended that I m disturbing you, wanda ba haka bane, ni nasan abinda nake yi, gaba d'aya nasan halin da kake ciki , nasan kana cikin damuwa fu'ad, dan haka nake neman alfarma da ka bani dama na nuna maka kalar tawa soyayyar plz.... A matu'kar firgice ya sake juyowa ya kalleta "me take nufi da shi da rayuwarsa gaba d'aya? "lallai duniya abin tsoro, haka mutane cikinta, "me yasa sam wasu matan basu da tunani da hango abinda zai je yazo? "ita din fa tamkar yan uwan junane suke da me'ad, tare ya sansu komai nasu tare tun daga kan sutura da komai, amman take furta wad'annan zantuttuka gare shi ,ba tare da wata shakka ba ko tsoro , "kai tur da mata masu irin wannan hali... kusan minti goma suna zaune haka tana gaya masa zantuttuka masu sanyi da shiga jiki ba tare da yayi yun'kurin sake cewa da ita komai ba, illa zuciyarsa dake bugawa cike da mamakinta ,duk wata kalmar soyayya da zata fito daga cikin bakinta sai tayi silar bugar masa da zuciya, har zuwa sanda zuciyarsa ta kawo masa mafitar da zata tunzura zuciyar me'ad dinsa akan wulakacinta garesa zaiyi amfani da sajida ko hakan zai kawo cigaba arayuwarsu , take ya amince da shawarar da zuciyarsa ta bashi na ya amince mata kawai ko dan koyar da ita darasin dake cikin duniya . "sajida ta kira sunansa cikin sanyayiyar muryarta me tsananin dadin sauraro "plz Abban NASREEN kace min wani abu mana, da alamun akwai abinda kake son cewa gareni .... "zaki iya maida ni gida yanzu i think bazan iya 'karasawa da kaina ba ? yayi mganar muryarsa can 'kasa, jikinta na rawa tace " me zai hana bari na kira Hakim direbana yazo ya same ni a nan, domin ya biyo ni da tawa motar . kansa kawai ya iya d'aga mata tare da juyar da kansa gefe yana kallon gefen titi , dan kwata-kwata baya son cigaba da dubanta, yana jin idan ya cigaba da kallonta komai zai iya faruwa a tsakanin su ,saboda kyawun surarta, jikinta me matu'kar kyau da hargitsa lissafi ga shi tana cikin irin shigar da yafi son mace ta kasance ciki, doguwar rigar atamfa, java gold me adon flower's ta yane kanta da 'karamin mayafi baki ,doguwa ce sosai kamar me'ad dinsa, sai dai ba fara bace sai jikinta irin karuwan jikin nan gareta kirjinta cike yake bammmm da ruwan nono , dan wani lokaci yanayin jikinta na sauyawa musamman idan tana cikin farin ciki, ba dai wani tsagwaron kyau gareta ba amman akwai kyawun halittar jiki, a kallo d'aya mutum zai iya afkawa cikin tafkin 'kaunarta, katse shirun sa tayi ta hanyar cewa kad'an yi ha'kuri yanzu zai 'karaso. kasa amsawa yayi saboda wani abu da yaji yana yawo a gaba d'aya ilahirin jikinsa me kama da shocking wanda ke haddasawa kirjinsa dokawa, cikin mintunan da basu wuce goma ba sai ga Hakim ya 'karaso a kan okada ,tana hangosa ta bud'e murfin motar ta fito a dai-dai lokacin da ya 'karaso gareta yana me rusunawa, ta mi'ka masa key'n motarta bayan tayi nesa kad'an daga jikin motar fu'ad "ka biyo mu a baya, abinda ta iya cewa kenan ta juya wanda a lokacin har fu'ad ya samu damar komawa d'ayan bangaren sannan ta shiga ta zauna mazaunin direba taja motar a guje Hakim ya biyo bayanta kamar yadda tace. fu'ad yayi shiru yana sauraron abinda take fad'a masa a kan matsanancin 'kaunar da take masa, amman ya kasa furta mata dai-dai da kalma d'aya domin maida martanin maganar data ishe shi dashi ,saboda bacin ran da yake ciki dan gaba d'aya haushi tare da mamakinta ne ya addabi zuciyarsa . A bakin get din gidan taja ta tsaya tare da yin hon,me gadin ya taso da sauri ya bud'e musu tasanya hancin motarsa ciki harabar gidan , kai tsaye inda aka tanada domin parking din motoci ta nufa tayi parking tana sake yi masa nacin ya taimaka ya amshi tayin soyayyarta ,a tare suka fito daga cikin motar sannan ta kulle ,ta tsaya a gabansa tana fuskantarsa tare da mi'ko masa key , wanda dai-dai wannan lokacin me'ad dake zaune cikin d'akin ta mi'ke tsaye da niyyar zuwa d'akin NASREEN kamar ance ta waigo zuwa harabar gidan, idanunta suka sauka, a kansu tsaye ,sai dai duhun daren da ya soma shigowa ya hanata gane kowace tsaye a gaban mijinta tana mi'ko masa hannu buga da k'ari fadadden kirjinsa ya kareta , 'kirjinta ne yayi wani irin lugud'en bugawa da 'karfi har sai da ta kai ga dafe dai-dai saitin zuciyarta da taji yana neman tarwtsewa. A hankali sajida take masa magana wacce ke sake kashe masa jiki "fu'ad ina sonka, bana tunanin zan iya sakacin da nayi a farkon haduwar mu, ka taimaka ka amincewa aurena plz..... tare da d'aura key'n motar a tafin hanunsa tana me shafar tsakiyar hannunsa wanda hakan yasa yayi saurin janye hannunsa "sajida .......fu'ad ya kira sunanta. "na'am fu'ad dina .. "zaki iya fita daga cikin gidan nan da rayuwata gbdy tun kafin zantuttukanki su soma tarwatsa min 'kwa'kwalwa? tayi shiru tare da tsura masa ido tana kallonsa , take hawaye ya soma ciccikowa a idanunta "kar ka min haka fu'ad wallahi... "dakata plz just live now ya nuna mata hanyar fita da hannunsa "bazan damu da duk abinda zaka min ba, saboda darajar son da nake maka ,ka sani duk duniya babu wacce tafi can-canta ka aura sama da ni, na ha'kura da kai ne a wancan lokacin saboda lokaci ya 'kure min ,amman yanzu ina tabbatar maka sai inda 'karfina ya 'kare akanka ..... "ni dai na gaya miki ki fita cikin rayuwata, kar ki sake kuskuren furta min kalmar so, saboda ko nakasance mahaukaci bazan ta'ba kuskuren aurenki ba, "me na tsinta a aurena da me'ad ballantana nayi tunanin auren ki? "kar kace haka plz, ka jarraba aurena fu'ad ... akwai bambamci me yawa atsakanina da me.. "shout up there yayi maganar a matu'kar harzu'ke wanda yasa me'ad 'ko'karin fitowa daga cikin part dinta "me ye bam-bamcin ki da me'ad? "yadda me'ad take haka kike ..... " kar kace haka fu'ad wallahi akwai bam-banci me tazara a tsakaninmu..tsaki ya ja a fusace ya matse key'n motarsa ya shige cikin ya barta tsaye a gurin tana kallon bayansa babu kowa a parlour'n sai 'karar TV dake manne jikin bango a parlour'n a hankali dafe da goshinsa ya nufi d'akinsa ya fad'a saman doguwar kujerar three seater guda d'aya da ke ajiye a gefe d'aya yana lumshe idanunsa . mee'ad ta shigo d'akin cikin sauri tana binsa da kallo bayan taje harabar gidan ba taga matar data kawo mijinta gida ba, muryar ta a fusace ta soma magana "wacece wannan tantiriyar da ta kawo ka gida yanzu ? "meye ala'karka da da ita da har take da 'karfin zuciyar tu'ko min miji har ma da shigo min cikin gida? shigowarta da banzaye tambayoyinta gare shi yasa shi mi'kewa tsaye ya nufin hanyar bayi "honey cant to hear what am saying? " nace wace 'yar iska ce ta kawo ka yanzu ? ta biyo bayansa tana sake tambayarsa ,yayi mata banza tamkar ba dashi take mgn ba,ya shige bayi tare da bugo 'kofar bayin da 'karfi kad'an ya rage bai bugi fuskarta ba, tayi baya da sauri tana dafe bangon d'akin gaba daya hankalinta da natsuwarta ya soma barin gangar jikinta ,idanu ta tsurawa 'kofar bayin tana mamakin abinda ya faru wanda bai ta'ba faruwa ba, a tun had'uwarsa dashi ,sam bai kasance ma nemin mata ba, ko shiga shirginsu asali ma duk macen da ya ganta bata birgesa itama sa'a taci . fu'ad na 'karasa shiga bayi ya sakarwa kansa da ya ji yana 'ko'karin rabewa gida biyu ruwa, ya kai tsawon minti talatin yana tsaye ruwa na tsiyaya a jikinsa ba tare da ya cire kayan jikinsa ba, sannan ya cire kayan jikinsa ya soma wanka a tsanake cike da 'bacin rai "me yasa na auri me'ad? ya jefawa zuciyarsa wannan. tambayar . "me yasa ban yi ha'kuri da tarin soyayyarta gare ni ba ,na tunzura zuciyata gurin aurenta ,ga shi ina cikin tsaka mai wuya da lamarinta ? "ta yaya zan auri matar da baxata iya bin umarnina ba tare da sadaukarwa gareni ...?" hakika nayi kuskure a rayuwata , tabbas nayi kuskure babba da na aureta a rayuwata ba tare da nayi tunani ba... "a zahirin gasky hakkin NASREEN sai ya kamani domin ban za6a mata uwa ta gari ba abin alfahari ba. "why why why na aureta? ya furta tare dunkule hannunsa ya naushi iska , da wannan tunanin ya 'karasa wankansa ya fito ,tana tsaye tamkar wacce aka dasa ta a gurin ,yazo ya wuceta yana goge jikinsa ya nufi wardrobe dinsa ya ciro jallabiyya black colour ya sanya, ya je ya kunna TV kana ya dawo kan kujera ya zauna ba tare da ya kalli inda take ruku6e ba, ya d'auki remote ya kunna AC . me'ad ta 'karaso in da yake ta zauna kusa da shi sosai , zuciyarta na wani irin tafarfasa ta tsura masa ido tana kallonsa , da 'kyar ta samu ta tattaro kuzarinta tare da kamo hannunsa d'aya cikinsa sannan ta soma motsa labbanta "Abban NASREEN tambayarka fa nake wacece wannan matar data kawoka plz ? " i have been talking you since, and i really has to do this before everting could have mess up wit us, kawai just tell me who is she? hankalina ya saka kwanciya saboda ban ta'ba ganinka tare da wata ba, ballanata har ku kasance acikin motarka tare.. "ka fara neman mata ne ban sani ba ko me? "plz talk to me now hankalina a matu'kar tashe yake.. fixge hannunsa da ke cikin nata yayi a matu'kar fusace sannan ya juyo a hankali yana fuskantarta sosai " me'ad !!! ya kira sunanta har sau uku da muryarsa a sanyaye sai dai da ji kasan yana cikin damuwa da tashin hankali "you really has carryover in your dity life for this idiot matter . " me'ad lokacin yana neman 'kure miki amman rashin common sense dinki ya'ki bari ki hankalta, nadamar ki ta kusa zuwa gareki ba tare da kin shiryawa hakan ba , lokacin kukan ki yayi me'ad.....sannan watan da na saninki ya kusan tsayawa matsawar baki canza wannan hali da 'kudirinki naki a kaina ba.....wallahi ina me tabbatar miki sai kin yi kuka da idanunki nan gaba saboda ami.. ... "dakata dakata malam, wani irin baki ne haka kake min ? tambayarka kawai fa nayi ba dogon sharhi na nema daga gareka ba, da kake kokarin yi min mugun alkaba'i, idan budurwa kayi ko neman mata ka fad'a ,ai sai kasanar wa mutane bawai kasoma wa mutun mugun baki ba, duk ma abinda zaka yi kaje kayi yayi wannan matsalarka ce ba tawa ba, ni dai yadda gobe zata kasance nafi bukata son sani ba wani surutunka ba. "who is going stay at home with our daughter tomorrow simple as that? "i don't know, and if you dare ask me this stupid question again i will deal with you right now, "shasha kawai kina nan kina haukan banza ana miki zagon kasa a kan wannan banza aikin naki wanda nan gaba zai jawo miki nadama mara amfani ,amman muje zuwa ya 'karasa maganr yana maida idanunsa kan tv.. zabura tayi ta mi'ke a fusace" kaine zaka yi nadama domin kuwa ga tarin nadama nan a 'kwayar idanunka ina hangowa. "nadamar aurenki ba ya juyo a matu'kar harzu'ke yana dubanta "nadamar aurenki kawai ke cikin 'kwayar idanuna da zuciyata ,wallahi mead i regret married you in my life ,a yanxu na tsani kaina da na zabe ki a matsayin abokiyar rayuwata . " na d'auka aurenki farin ciki ne gareni ashe tarin damuwa da bakin cinki ne, wallahi ban san yadda zaki kasance min kenan ba da ban amincewa aurenki ba, nayi da nasani yafi sau ba adadi a kan aurenki da nayi ya 'karasa maganar yana me jan dogon tsaki da zance zuci " ban san me ya shiga cikin tunaninna ba a kanta? ban san abinda ya kai ni amincewa zucuyarta a kanta ba? "a da can baya da mahaifinta ya'ki yarda da aurensu , ya ha'kura da ita amman daga baya ta sake dawo cikin rayuwarsa wanda silar haka komai ya faru da shi ya furzar da iska me dumi ta bakinsa . ficewa tayi daga cikin d'akin zuwa nata d'akinta, a hankali ta shiga zagaye d'akin hanunwanta sar'kafe cikin juna gaba daya ta kasa tsaye ta kasa zaune, sai zarya take tana yamutsa gashin kanta tare da ri'ke kungunta tunanin abubuwan da suka faru a baya kafin aurensu take"anya kuwa tayi masa adalci da hallaci a rayuwa.....? "kasa sukuni tayi har zuwa sanda aka kira sallahr isha'i, gabadaya abubuwa ne suka shiga dawo mata, tun daga kan haduwar da fu'ad har zuwa rayuwar aurensu da rashin lafiyar NASREEN kawowa wannan matsalar dake faruwa dasu. tana kiyo sanda fu'ad ya fita tasan masallaci yaje dan haka jikinta a mace ta fito tashiga d'akin NASREEN taba abinci da magani sannan ta dawo daita parlour'n ta kwantar daita tare da yi mata makarin da pillow ,zata juyo kenan NASREEN ta riko hannunta "momy.. "yes dear kina son wani abu ne? yarinyar ta girgiza kai tana dubanta sannan tace" momy meyasa bazaki zauna agida ki kula dani ba kmr yadda doctor yace? "nafi son ki zauna atare dani..... .. shiru tayi ta tsura mata ido kawai tana kallonta ,NASREEN ba dai fitar da zance ba, idan tayi mgn xaka d'auka shekarunta ya wuce yadda take. "karki damu baby your dady will be with you zama agida akwai matsala, kinga babu wanda zai taimaka mana, ki duba nawa nake biya school fees dinki da sauran abubuwa idan nace zan ajiye aiki komai zai iya faruwa,kiyi hakuri dad dinki zai kula dake fiye dani kinji an... k'arar bude kofar ta jiyo ne ya katseta ,dan tasan kowaye, yana gama sanyo kai taga malik abokinsa yashigo, mikewa tayi tana gaidashi cike da farincikinta ,shima ya amsa yana tambayarta me jiki "jiki da sauki gata nan sai rigima. yayi murmushi yana zama kusa da NASREEN shima fu'ad guri yasa ya zauna yana shafa kanta,ita kuma me'ad tashege kitchen cikin kankani lokaci ta shake musu Center table da abun motsa baki dan tasan sai tara yake cin abinci, sannan ta nufi d'akinta gabatar da sallah .. hira suke atsakaninsu wanda duk akan rashin lfyr NASREEN ne, sukaji sautin muryarta "dady momy said you are going to stay at home with me? ya juyo ahankali yana duban fuskar kyakkwar diyarsa batare da yace mata komai ba, gbdy yarasa me ma zai ce wa yarinyarsa ,domin yasan idan yace mata bashi zai zauna tare daita ba , zata ji babu dad'i shi kuma bayason damuwarta, dan haka ya tsinci kanshi da ce mata "yes I m going to stay with you my baby.. fara'ar dayaga ta bayyana a saman kyakyawar fusakarta yayi matukar bashi mamaki .."thank you my dad that's why i love you more.. "i love you dady..... "i love more baby ya fad'a tare da shafa kanta . malik yace " ni fa baki sona ko babanki kawai kike so? tayi murmushi wanda ke fidda kamaninta da mahaifinta sannan tace "ina sonka amman sai kabani labaru mamana da babana ....ya kwashe da dry "kaji yarinya da wayo suna zaune me'ad ta sake dawo "honey dining ya kammala "okay kawai yace mata ataikace saboda bayason jan magana " uncle malik kana nan sauraren shirme NASREEN ko? yayi murmushi "babu wani shirmen datake, hirarku muke daita, kuje kuci aninci larku biye mata dan ita taci . kukan shagwaba NASREEN ta saki "dady kana jin momy ko? "karki damu daita itace ke shirme bake ba.. me'ad ta juya ta sake komawa d'aki ,fu'ad ya mike shima "kaje kaci abinci malik. kai fa ? "bana jin yunwa koma ina banji zan iya sakawa cikin komai.."dan Allah fu'ad ka cire damuwar nan hk.. "bazan iya ba, duk randa kaga na cire damuwar nan na rabu da me'ad ne yakarasa mgnr yana barin gurin jikin malik yayi sanyi sosai kmr zai zubar da hawaye haka ma NASREEN "uncle malik meyasa dady'na zai rabu da momy? "basuna son junansu sukayi aure ba? "dan Allah uncle malik kabani labarin.. ina son jin labarin iyayena... .. runtse idanunsa yayi sosai ya kasa cewa komai kafin daga baya yasoma magana ahankali mmn sudais ce 💗💗💗💗💗💗 'YAN CINKI 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 ~NA~ *AYSHA A BAGUDO* ~DEDICATED TO~ MRS ADAM ( YAR MUTAN KAGARA) page 36 to 40 ASALIN MAHAIFINKI fu'ad Muhammed argungu d'an asalin karamar hukumar argungu ne dake jahar kebbi, cirani ne yashigo da kakaninsa garin lagos , wato malam musa da mai d'akinsa halima da yaronsu muhammed , inda sukayi masauki a unguwar g'begulori dake karamar hukumar agege, fu'ad bakabe ne daya fito daga cikin kabawan asalin jahar kebbi ,yayinda danginsa gbdy suka kasance talakawa ne tulis . tunda malam musa ya dira a garin lagos bai ta'ba zama daidai da rana daya da sunan hutu ba, kullun yana fita neman abinda zai ci da iyalisa ,ba wata sana'a malam musa yake ba illa aikin dako cikin kasuwar matuwaf zuwa ketu ,Allah yasanyawa aikin dakonsa albarka domin basu ta'ba neman abinda zasu ci sun rasa ba ,kuma tun daga kan muhammed Allah bai sake basu haihuwa ba ,dan haka suka d'auki soyayyar duniya suka d'aura akan tilon d'ansu da Allah ya basu ,duk da kasancewarsu talakawa amman hkn bai sa sunyi sakaci da tarbiyar yaronsu ba ,suna iyakacin bakin kok'arinsu akan ganin sun inganta rayuwarsu data d'ansu ,domin sunyi kok'arin sanyashi makaranta gwanati dan samun cigaban rayuwarsa . "haka rayuwarsu tacigaba cikin talauci da babu har yasamu ya kammala secondary school dinsa a ikeja high school daga nan bai cigaba da karatu ba , sai dai ya Kan fita buga bugarsa duk inda yaga aikin karfi zaiyi fassakare ne wanki da guga zaiyi . Muhammed ya taso tare da mahaifansa har zuwa girmansa , kafin Allah ya had'ashi da ramlat, wace suka kasance diyar makotasu ce ,sukayi aurensu bisa amana da soyaya. fu'ad shi kad'ai iyayensa suka samu ya tsaya a duniya ,dan haihuwarsu biyar yaran suna mutuwa akansa suka samu ya tsaya wanda sanadiyyar haihuwarsa, mahaifiyarsa ta rasu ,a cewar mutane bama tasan abinda ta haifa ba ta cika, sai rikonsa ya dawo gurin kakaninsa, lokacin daya kai shekara bakwai mahaifinsa ya rasu sakamakon ciwon hawan jinin daya kamu dashi a tun mutuwar matarsa ramlat, ba a d'auki wani lokaci me tsawo ba malam musa shima yace ga garinku. gidan ya saura daga halima sai fu'ad. fu'ad yayi karatunsa na primary har zuwa jami'a ahmadu bello, bisa tallafi na gwanati da taimakon Allah dana kakarsa inda ya karanci business administration. ,fu'ad ya sha matukar wahala gurin karatunsa saboda rayuwar babu da suke ciki ,da taimakon scholarship dana abokai da tsohuwar kakarsa halimatu yasamu ya kammala karatunsa da kyar ,bayan kamala karatunsa da bautar kasa yashiga wahalar rayuwa sakamakon rashin samun aiki , kafin had'uwar sa da mom dinki ya kwashe shekaru sama da shida yana zaman banza batare da yasamu aiki ba duk da kyawun da takardunsa sukayi. " sun had'u da me'ad ne A wata safiyar litinin . labari ya karad'e koina akan zance batakashin da'akayi a garin lagos duk gidan tv da radio daka kuna a lokacin fuskar ACP Aliyu rano ake nunawa da tawagarsa rike da bindigunsu suna harbi . ni da fu'ad ne muka shiga cikin wani d'an madaidacin shago inda muka saba yada zango ,muna shiga na ja na tsaya ina murmushin jin dadi,yayinda fu'ad dake tsaye a bayana yasa hannusa ya buge min keya "banza kawai munafukin Allah ,gulma nacinka ko? bud'ar bakina sai cewa nayi "abokaina yau fa fu'ad yayi kasuwa da ala'mun shima yau ya fad'a tarko kauna nakarasa mgnr ina kwashewa da dry har da tafa hannu. "kajika da wani zance iska inji cewar sauran abankanmu, sudais, Abdul da kabeer . kabeer yacigaba da magana idanunsa na kan kallon tv "yayi kasuwa fa kace kmr wani kayan marmari. "allah kuwa yau naga qunjinsa domin ya had'u da yarinyar da bazai iya hakura daita ba. " dan Allah malam karka damemu zauna ka kalli abinda duniya take ciki.. zaro ido nayi sa sauri lokacin da idanununa ya sauka akan TV "kai kai ai naga wannan mutumi da'ake nuno yanzu , wannan batakashin da kuke kallo agabana fa akayisa ,shi dai fu'ad bai ce komai ba yakarasa kan doguwar kujera ya zauna yana duban abinda ake nunowa a TV wanda agabansu komai ya faru. "kana nufin ka ganshi inji cewar kabeer? "Kwarai da gaske na ganshi da idanuna, "kai dai wallahi babban makaryaci ne ,yau kuma da karyar daka zo mana kenan?inji cewar abdul .. "Na girgiza kai tare da kallon fu'ad ,"fu'ad dan girman allah kayi magana zasu fi yarda da maganarka saboda muna tare da kai lokacin da abu ya faru . fu'ad na jinsa ya sake mikewa akan doguwar kujera yayi kwanciyarsa tare da lumshe idanunsa duka , ya d'aura hannunsa ya dafe goshinsa dayan hannunsa na saman ruwan cikinsa, kasancewarsa marason hayaniyya. duk surutun danakeyi banza sukayi dani suka cigaba da sauraron labarin da'ake watsowa suna kur'ba ruwan Lietop. " kunga wallahi da gaske nake kai dai fu'ad wallahi banza ne ,kana ji ana kokarin meidani makaryacin karfi dayaji amman kayi shiru. "me ka keson nace fu'ad ya fadi hkn atakaice batare daya bud'e idanunsa ba. "ka gani ba dan Allah kayiwa mutane shiru, shi kansa fu'ad din bashi da tabbas da zance dake fitowa daga cikin bakinka duba da yanayin da yayi magana to yaya kake son mu dake zaune agida mu yarda bayan karyar abincin ruhinka ne daka kashigo fa zance yarinya kake yi ,cikin minti biyu kacal kasanyo wani zance daban . "eh naji karya abincin ruhina ne, amman wallahi wannan zance ba karya bane ,koda nasaba yi muku karya ,ku matso kuji yadda abun yakasance nakarasa maganar ina me zagayo na zauna akan table ,gabayansu suka zagayeni " muna jin ka fad'i kuma wallahi kana somawa da karya zan gane ka kuma san karshen abun..inji cewar kabeer. "ina zaune wancan dan iskan yace na rakashi inji din ciro kudi ,muna isa aka fara ruwan sama tare da walkiyya.. nakarasa mgnr ina zabgawa kabeer duka ajikinsa "kai dan Allah malam da baki ake bada labari ba da hannu ba "yi hakuri abokina abinda idanuna suke hangomin ne abun birgewa ,tsawon lokaci muna tsaye har ruwan yasoma tsagaitawa mukayi tunanin mu fita saboda hango inuwar mutun tsaye"bude kofarmu ke da wuya sai naga wata kyakkwar yarinya kirar Japanese tsaye cikin doguwar rigar har kasa hannunta rike da lema ,kyakkwa ce yarinyar sosai ,ku tamabayi fu'ad dan lokacin na lura har yafini gigicewa akanta, amman sai naga ya waske ita kuma yarinyar idanunta na kansa ta tsura masa ido tana kallonsa, bud'e bakin yarinya keda wuya tace "sannu amman gsky kunjima da yawa sai wani zarar kudi kuke kmr wad'an da zaku cire kudin bank din duka. nayi saurin cewa "dan Allah kiyi hakuri ai tuni muka cira , tsayawa mukayi domin fakewa ruwa ,amman bamu aron lemarki sai mun d'an tsaya daga waje ke km sai shigo idan kin cira sai mu dawo mu tsaya ana . "a tunanina ni zatabawa lemar tunda ni nayi mata magana ta fahimta , amman sai naga ta mik'awa wancan dan isakan lema, ya nuna inda fu'ad ke kwance ,in dai takaice muku ko damuwa da kulawar data nuna masa bai yi ba ,sai ma zagayeta da yayi ya wuce yayi gaba ya tsaya tare da tura hannunwasa duka cikin aljihun wandonsa , ina lura da yadda yanayin yarinyar ya sauya, ba dan taso ba ta miko min lemar wanda kad'an yarage hannunmu bai had'e da juna ba, na matsa mata tashiga, ni kuma na fito na tsaya ina karewa halitar jikinta kallon , ina gaya muku kywaun yarinyar ya had'u sosai.cikin mintunan da basu wuce goma ba ta fito idanunta akan fu'ad ,sosai fa kura masa ido tana takowa zuwa inda yake tsaye. cikin hk ruwan saman ya tsaya cak sai kuma harbi takoina a harabar gurin, harbi fa sosai ban san yadda akayi ba sai dai ganin nayi fu'ad ya kamo hannuta sai ga yarinyar manne da kirjinsa nan take suka tsurawa junansu ido suna kallon junansu, wanin harbin yasa tayi saurin shigewa jikinsa gabadaya domin neman mafaka. cikin minti biyu kacal duk ilahirin gurin ya har gitse, jamar dake wucewa a gurin bubu wanda ya damu da halin da kowa yake ciki, kowa gudun ceton ransa kawai yake saboda gabadaya gurin ya hargitse da k'arar harbi, police na harbi ,y'anta'ada na meida musu . "ai in gaya muku na rud'e tare da gigicewa amman fu'ad da yarinyar nan ko ajikinsu kallon junansu suke karasowa garesu nayi ina girgiza fu'ad domin shi nake da yancin tabawa, nayi sa'ar ya dawo cikin haiyacinsa amman ita yarinyar ruhinta yayi nisa akansa ,girgizata fu'ad yasoma yi amman ina bata ma san yanayi ba, cikin rud'u ya rike hannunta ya kwasa aguje yasoma gudu daita, ganin harbin na sake yawa, sannan yana kiran sunana ,ni kuwa daman tuni na boye bayan inji din cire kudi ina kirma.. "kusan awa daya ana batakashin tsakanin 'yanata'ada da police har zuwa sanda acp aliyu rano yayi nasarar harbe wannan mutumin a kirji sannan komai ya lafa gurin gbdy ya turnuke da hayaki daya bayan daya mutane suka soma bayyana fuskarsu cike da matsanancin firgici daga mubuyarsu, ni kuwa sai ware ido nake naga ta inda fu'ad zasu fito, ahankali sai ga fu'ad da yarinyar nan makale da juna sun fito daga mabuyarsu aiko gama bayanarsu ke da wuya sai agaban acp wanda naji yace"a'a me'ad me km kike yi anan ? hankalinta kwance tace "uncle nazo cire kudi ne ina fatan babu abinda yasameka? ta fadi hkn ne saboda ganinsa rike da hannunsa ga jini na tsiyaya alamun an harbeshi . " ina jin dai lafiya kalau nike me'ad, waye wannan da kuke tare dashi ? da sauri ta juyo gefenta fu'ad tagani tsaye agefenta hannunwansu malake cikin juna ,jin Abind acp yace yasa fu'ad yin sauri zare hannunsa cikin nata yana shafa sumar kanshi . d'an runtse idanunta tayi kana tace "amm bansashi ba ucnle ,yanzu muka had'u dashi ta juya tana kallon fu'ad kmr zata cinyeshi muryata a sanyaye "tace sunana me'ad nagode da taimakona dakayi. "muryarsa a dake yace ni kuma fu'ad karki damu ya juya ,naga yasoma waige waige ala'mun yana nemana, ita kuma tabishi da kallo yayinda acp aliyu yakira daya daga cikin yaransa "md . "na'am yallabai . " taimaka ka'ajiye min wannan yar tawa a gida. "ok yallabai kasa daga kafafunta tayi agurin, tacigaba da kallon bayan fu'ad . ina kallonta, jiki a sanyaye tashiga bayan wata hadadiyar mota kiran toyata camry . Ina kawowa karshen labarin nace ni dai dan Allah ku gaya masa idan bai sonta ni dai ta min, ina sonta kuma aurenta zanyi, aikuwa suka ce me zasuyi ba dariya.... "kai wallahi bazan ne a gbdy labarinka fu'ad take so bakai ba ,koda yace baya sonta kana tunanin zata soka ne? take na marairaice murya da fuska "ni dai ku taimaka ku tambayar min shi idan bai sonta ya tsaya min na aureta, wallahi dagani yar babban gida ce kunga motar da za'a kaita gida dashi kuwa , kuma dagani akwai halaka me karfi atsakaninta da acp Aliyu rano.. "kai dan Allah malam rabudamu da wannan shirmen banza suka soma kokarin watsewa su barni ,nayi saurin kamo hannun sudais, kai ma tafiya zakayi kabarni? "Kai rabu dani, idan kana son yarinyar da gaske kawai ka nemi gidansu Dan gsky nasan fu'ad ba sauraranta zaiyi ba ,dan shi bashi da lokacin mace ,mata nawa suka nuna suna son shi Amman yaki? ******** bangare me'ad kuwa zuciyarta ce ke mugun buguwa a tun sanda tashiga bayan motar tare da hasko mata kyakkwar fuskarsa "tun datake bata ta'ba had'uwa da saurayin daya tsaya mata arai ba kmr shi, sai dai daganin zai yi jin kai da girman kai tattare da isa. zaune suke su uku sajida misna hailat , sun mugun tsurawa TV plazma ido dake manne da bango suna kallon batakashin da'aka tafka tsakanin 'yanta'ada da ma'aikan sack a dapemu express way dake jahar lagos "barkanmu ,a yau anyi musayar wuta tsakanin 'yansanda ,da 'yanta'ada an samu nasarar harbe wani dan ta'ada me hatsari, acp aliyu rano da jamiansa su sukayi nasarar harbe nabel wanda ya kasance babban dan ta'adar da jamian tsoro suka dade suna nemansa a fadin jahar nan. "yeeeeee babana yazamo zakaran gwaji..... sajida tasoma murna har da tsallenta "nasan kwanan nan za'ayi wa babana k'arin girma...murna take sosai tare da rungume misna dake kusa daita "gsky na taya dad dinki murna sosai inji cewar misna , hayaniya ce ta kaure atsakaninsu kowanensu na fad'ar albarkacin bakinsu. me'ad tashigo hadadden parlour'n gidan wanda ya k'awatu tamkar da tayis akayi ginin ,gashi an zagaye shi da manya furanin. hannuta rike da karamar jaka wace bata wuce a sakalata a tsintsiyar hannuta ba tana juyi sanye cikin doguwar rigar " kawayena yau na had'u da wani saurayi kuma ko wallahi kyakkyawa gaske ne kalar launi danafi so.. takaraso garesu tana murmushin jin dadi "kunji aunty dan allah da wata magana ana labari da d'umi d'uminsa ke kuma kina labarin wani saurayi , "dan Allah malama kiyiwa mutane shiru had'ad'd'e ne fa sosai, Allah ina gaya muku duk fadin garin nan babu me kyawumsa ta karasa fad'ar hk tana sake juya jikinta . "haka zakice tunda zuciyarki ta yaba dashi ba ,da baki yaba dashi ba duk kyawunsa sai kin nemo makusansa" kmr kinsani kuwa inji cewar misna . "wai ina miki wasa ne suhailat, ko dake nake maganata? ta fad'i hkn tana tsaki sannan ta fuskanci sajida da misna. "ku kuma daku fa nake mgn amman kuka min shr , ba ma zaku saurareni ba ,kuna can kallon kwazon da acp yayi "ke dai bari me'ad Allah ina cikin jin dadi yau ,ina ma mama tana raye ta dinganin irin cigaban da baba yake samu, wannan furunci da sajida tayi yasa me'ad kasa cigaba da tsayuwa a gurin ta nufi hanyar d'akinta tana magana "Allah ya jikanta sai dai ki shiyawa jinyar dad dinki bayan kingama tayasa murna k'arin girman da zai samun saboda 'yanta'ada sun harbeshi . da sauri sajida ta mike jikinta na rawa tabiyo bayanta atare suka shiga dakin "da gaske an harbi dady? "ke baki lura ba, bakiga ya dafe hannunsa na dama ba? "ina tunanin anan aka harbe....... ai sajida bata jira jin karashen zance ba, tayi waje aguje tana kiran layin dad dinta, tayi sa'a ya d'auka "hello dady.. "sajida kina lfy? " ina lafiya dady kana ina?" yanxu me'ad ke gaya min wata mgn da gaske ne 'yan ta'ada sun harbeka? "gaky ne sajida ,duk boyewar dana yi ashe ta lura, to dai ki kwantar min da hankalinki, yanzu haka an cire min harsashi , mu had'u a gida, kashe wayarta tayi tare da bud'e murfin motata tashiga ta bar gidansu mead a guje. mmn sudais ce 💗💗💗💗💗💗 'YAN CINKI 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 ~NA~ *AYSHA A BAGUDO* ~DEDICATED TO~ MRS ADAM ( YAR MUTAN KAGARA) page 42 to 44 ......Ahankali malik ya sauke kwayar idanunsa akan NASREEN dake kwance ajikinsa ,wacce bacci yasoma kok'arin d'aukarta amman son jin labarin had'uwar iyayenta ya hanata runtsawa . shiru malik yayi yana dubanta batare da yacigaba ba, ya d'auki sama da minti goma a zaune kawao yana kallon NASREEN cike da tausauawa, yarinyar tana bukatar kulawa takowani bangare, amman tarasa shirun da NASREEN taji yayi yawa ne yasa ta, bud'e idanunta dake runtse taki sunansa "Uncle malik continue now.... kacigaba ina son jin komai, domin kai kad'ai ne zaka iya 'bata lokacinka ka gaya min. "NASREEN ...ya kira sunanta a sanyaye "na'am unlce "kwalkwaluwarki bazata iya d'aukar sauran labarin ba.. "zan iya uncle am getting to 10yrs now babu abinda zaka fad'a da bazan fahimta ba.. ina jin tausayin dad dina dayawa, ina son nasani wani abu akansa takarasa maganar tana meida kanta bisa cinyarsa.. naunayen ajiyar zuciya ya sauke tare da cewa "daga bangaren fu'ad da me'ad babu wanda bansan halin dayake ciki ba, akoda yaushe muna tare da fu'ad, haka me'ad duk inda tasanya kafa ina biye daita sai dai a iya nan zan tsaya ... ya d'auke kanta akan cinyarsa ya meida kan karamin kushin din dake jingine da kujera, sannan ya mike tsaye yana duba agogon bangon parlour'n karfe tara ta wuce da wasu 'yan mintunoni, wayarsa ya ciro daga gaban aljihun gaban rigarsa yana kokarin neman layin fu'ad, sai gashi ya fito "yauwa zo kaji da wannan yar rigimar taka, ta matsa,lallai sai taji haduwarku da me'ad, ni dai nayi kok'arin sanar daita kad'an daga cikin had'uwarku sauran kuwa na barta da bagudo takarasa mata yakarasa fadar hk yana murmushi, murmushi fu'ad yayi shima sannan yakaraso inda take kwance kmr ruwa , ya komata ya zaunar daita tare da yi mata makari da pillow ta bayanta "kinji abinda uncle malik yace ? "ni ..ni naji amman babu ruwana dashi tunda yaki yacigaba dabani labarin, takarasa mgnr muryarta a shagwabe kmr zatayi kuka,kissing din goshinta yayi "don't cry my bby rabu dashi kinji bby nah ni da kaina ma sai nabaki, ai zaki fi son nawa ko? ta gyda masa kai kawai batare da tace komai ba fu'ad ya fuskanci malik "yanaga kana kok'arin tafiya batare da kaci komai ba? "kai rabani da cin abincin nan, yanzu ina ci idan naje gida sai nayi bayani daya bayan daya, an dinga yi min qausetion's kenan ,gara kawai idan na koma gidan naci gbdy, ok muje na taka maka "baby nan ina zuwa just give me w minti . har waje fu'ad ya rako malik suna sake tautaunawa akan sha'anin rayuwa, da hakuri da rayuwar ita karon kanta ... koda fu'ad ya koma parlour'n bai iske NASREEN ba ,dan hk kai tsaye ya nufi d'akinta ,inda ya isketa kwance cikin blanket dinta, ya yaye blanket din tare da d'aura hannunsa kanta "my bby kin sha maganinki? "yes dady . "ok kiyi bacci abinki Allah ya baki lfy me d'aurewa . "ameen babana, shiyasa nake sonka..... "i love you more yacigaba da zama yana dubanta tana matukar bashi tausayi yana jin kmr ya ajiye komai ya bata kulawar data dace, ita kad'ai garesa kmr yadda ya kasance, a zahirin gasky baya son yarasata duk da kasancewarta mai karancin lfy yana sonta hk... tsawon lokaci yana zaune yana tunani har sanda bacci ya d'auketa sannan ya yunkura ya tashi ya nufi d'akinsa ya kwanta lamo akan gadon yana tunani ya saka wancan ya kwance wancan, runtse idanunsa yayi sosai yana kiran sunan Allah, ahankali ya bude idanunsa wanda suka kad'a sukayi jawur saboda tuno abinda yake yi masa cikin rayuwarsa, a filli yace "nayi dana sanin aurenki me'ad dana san hk zaki zamomin arayuwata da ban yi kuskuren aureki ba...hawaye ne yaji suna sauka masa akan kuncinsa ,cikin sauri ya sharesu, lokacin ne wayarsa ta d'auki kara, ya kai hannunsa ya d'auka akan bed side ya manna a kunnesa batare daya duba ba. sautin muryarta yaji ta doki dodon kunneshi ,yayi Shiru tare da janyo pillow ya manna akirjinsa ya rungume tsam sbd d'and'anon dadin muryar "hello hello fu'ad kana jina !! ta sake maimaitawa akaro na biyu. "uhmm ya'akayi kira adaidai wannan lokacin ko kin manta ina iyali ne ? "am sorry for disturbing you , but ina son ka saurareni fu'ad kaji abinda za.... saurin katseta yayi ta hanyar cewa "sauraran me zanyi miki, karki meidani wani shasha mana ,ta yaya kike kokarin manta dangantakarki da me'ad mana ,karki manta har yanzu me'ad matsayin matata take, dan me kike kokarin sanyo damuwa acikin wace nake ciki....? " fu'ad ka saurareni mana, haba fu'ad ya dace ace nasamu kar'buwa a wajenka a daidai wannan lokacin, na d'auki sama da shekaru goma ina dakon soyayyarka batare dana fayace maka ba . " wannan damace tazo mana, kabari mu dama mana dan Allah ... karka ki amsar soyyayata saboda dan adam daraja garesa, idan ka amince zaka aureni zan ajiye komai har aikina domin na baka farinciki dakarasa. "dakata dakata malama enough is enough don't talk any rubbish.. "kinsa yadda zaki bani faricikin any not ki fahimtar da me'ad tabi abinda nake so domin a zauna lafiya? " ni dai ka ajiye mgnr wata me'ad kawai ka amince da au.. "ok baxaki iya bata wannan shawarar ba amman zaki iya shigowa gidanta amatsayin kishiyarta ko...? "ka fahimceni fu'ad ba ... "babu wata fahimtarki da zanyi idan ma aure nake da bukata ,bake zan aura ba.... bake ya dace na aura ba, ina da ido nasan inda mata suke okay, dan haka ki shafa min lfy if not zan gayawa me'ad da kaina tasan yadda zatayi dake ya katse kiran yana fitar da numfashi sama sama. "meyasa kayi haka? zuciyarsa ta kismamashi hkn, "m e yasa baka amshi tayin soyayyarta ba? take yabawa zuciyarsa amsa da, bazan k'ara wannan kuskuren ba bazan sake kuskuren auren ya'yan masu arziki ba....... a ranar fu'ad baiyi ishashen bacci ba, juyi kawai yake ga tunanin ciwon NASREEN ga kewar iyayensa dake addabarsa uwa uba matsalar me'ad da sabuwar matsalar dake shirin kunno kai, har karfe daya ta buga fu'ad bai san yadda zai yi da al'amura dake kokarin kusowa rayuwarsa ba. ahankali tunanin haduwarsa da me'ad ya dinga zuwa masa daki har zuwa lokacin da sajida ta bar gidansu me'ad agigice zuwa gidansu taga lafiyar mahaifinta . "koda sajida ta koma gida hankalinta yayi matukar tashi saboda ganin raunin harbin da d'anta'ada yayi masa, kuka take sosai tana "furta sannu dady ..shi kuma yana rarashinta da kyar dai yasamu tayi shiru. ita kuwa me'ad bayan ta tagama kimtsa kanta tattare da tunanin sabon fuskar data tsaya mata arai ta nufo hanyar parlour tana kwallawa me aikinsu kira " ummi ummi!! har takaraso parlour'n shiru babu kowa hatta misna da suhailat basu gurin, nan ranta ya soma baci tashiga kai kawo ta sake dawowa cikin parlour'n tattare da matsancin damuwa tasamu guri ta zauna tare da d'aura kafar daya kan daya tana girgizawa tare da cizon yatsanta ummi dake d'akin suhailat tana mata guga tayi saurin ajiye Iron ta fito da gudu tana haki, cikin rawar murya tace "aunty gani me'ad ta d'auke kanta cikin isa tace, "ummi ina son tambayarki... ummi ta d'aga kanta da sauri cikin tsoro jikinta yana rawa tace "kiyi duk irin tambarki da kike so. me'ad ta sake d'aure fuska kana tace "wai shin nan gidan ubanki, ko kuwa da gadonki acikin wannan gida..? da sauri ummi ta sake d'ago fuskarta ta kalli me'ad lokaci guda, kuma tayi saurin d'aukewa dan wani irin kallon da me'ad ta watso mata, sannan cikin rawar muryar tace babu ko daya sai dai kawai cin arziki danake yi acikinsa. "okay a she kinsan cin arziki kike yi amman kike neman kifi ya'yan gida sakewa, ki km fisu iko ko? ita dai ummi tayi shiru kawai tana kallon kasa dan daman hk halin me'ad din yake duk wanda yake kasanta ,sai yayi hakuri, in kuwa ba hk ba zai rasa aikinsa acikin kankanin lokaci. me'ad ta girgiza kafarta cikin isa da iko "daga yau duk sanda na sake kiranki, kikayi banza dani wallahi kinji na rantse in har baki rasa aikinki ba, zaki had'u fushina jahila kawai dabba mummuna....... mmn sudais ce 💗💗💗💗💗💗 'YAN CINKI 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 ~NA~ *AYSHA A BAGUDO* ~DEDICATED TO~ MRS ADAM ( YAR MUTAN KAGARA) page 45 to 46 ........."Wallahi Ba kiga yadda na tsanaki ba, ji nake kmr na kasheki ta had'e hannunwanta duka biyu al'amun da gaske zata iya aikatawa abinda ta furta . da sauri ummi taja baya tare da furta " Dan Allah aunty kiyi hakuri Insha'allahu bazan sake ba,zan kiyaye .... "Kar ma ki kiyayye kiga yadda zanyi dake . "Kiyi hakuri ta sake furtawa jikinta a sanyaye "Dan Allah malama banason long talk tashi ki bani guri kazama kawai. Ummi ta mike jiki a sanyaye babu laka ta fito, idan da sabo tarigada ta saba da wulakancin me'ad. Me'ad taja dagon tsaki lokaci daya taji gabanta yayi wani irin mahaukacin bugu da karfi , tayi shiru tana tunanin abinda ya sata jin hk, take fuskar fu'ad tasoma yi mata gizo acikin 'kwal'kwaluwarta ,runtse idanunta tayi kawai ta d'auki wayarta tare da mikewa tsaye ta haye sama inda mahaifiyarta take zaune da system agabanta tana tura sakonni, shigowarta d'akin yasa mom dinta d'agowa tare da cewa " yauwa gara da kika shigo, yanzu nake son aikawa akira min ke, me'ad takaraso jiki a sanyaye ta zauna kusa daita "gani sweet momy dina,ina matukar alfahari da kasancewarki mamana "uhmmmmm dan kinga abbanki baya kasar ba,? "kai momy wai meyasa kike kishi da dad ne? "nifa gbdyanku ina sonku domin banida abin so fiyye daku a duniya ku ne komai na. "kinga bason zance karya ina file din da hjy maryam tace ta tura dazu da safe? tsam tayi da ranta sannan tace" yana cikin jakata "okay je ki zo min dashi yanzu akan aikinsa nake. cikin mintina kad'an me'ad ta fito daga d'akin mom dinta , ta nufi d'akinta tasoma duba jakarta amman abun mamaki babu diary dinta ballanatana file din dake ciki, gabanta ne ya sake fad'awa , lokacin da 'kwal'kwaluwarta ta hasko mata ko dai ta yarda dashi agurin batakashin da ya rutsa daita gurin cirar kudi.. "tabbas in har bata ganshi ba definitely acan ta yar, ta furta hkn a fili tana cigaba da bincike gefe da gefen jakarta sannan cikin sauri ta fito da niyyar komawa gurin, har zata fita sai taga kmr shigarta batayi ba, basani ba, ko zata sake had'uwa da wannan kyakkyawan fu'ad , Dan haka takoma cikin d'akinta . ta fito cikin wani koren voyal dinki doguwar riga har kasa ba D'an kwali a kanta ,sai koren mayafin data yane kanta dashi, takalman kafarta suma duk kore ne, ta cigaba da tafiya cikin yanga, ta isa inda aka tanada domin ajiye motocin gidan, ta tsaya tana karewa motocin kallo ,4mart itace wace zuciyarta tabata umarnin shiga . Tun kafin ta kunna motar me gadi ya zabura ya mike tsaye, yasoma kok'arin bud'e mata get, ahankali tasanyo hancin motarta wajen gidan..a natse take tukin m . kai tsaye ta d'auki hanyar isa inda suka had'u da fuad ,cikin kankanin lokaci ta iso ,tasamu guri tayi parking din motarta ,tana bin gurin da kallo abubuwan da suka faru a d'azu da safe ne suka shiga dawo mata, tun daga kan sanda ta d'aura idanunta akansa ,har zuwa lokacin data nutse a tsakiyar faffad'an kirjinsa...fuskarsa , ajinsa, jin k'ansa da komai nashi sunyi mata ,ta dad'e bata ga halitar da kai tsaye aganin farko ya mamaye zuciyarta ba . fitowa tayi daga cikin motar ahankali tana dube dube, duk da zuciyarta na tabbatar mata bazata gansa ba adaidai wannan lokacin ,dan haka tasoma duba inda suka had'u, bata jin ATM dinta domin tasan cikin kankanin lokaci zata mallaki wani ,tafi bukatar diary din dake d'auke da manya sirrinkan rayuwarta tare da file din momy dinta, da shi kanshi fu'ad ,Saboda idanunta na matukar kwad'ayin sake ganinsa . ta kasa hakuri tsayuwa guri daya, tayi tafiya me nisa dan har ta kusan shiga alimoshi local government, amman bata ga ko mai kama da fu'ad ba da diary dinta , sannan ta dawo gida cikin wani irin 'bacin rai ,cikin sarsarrafa ta shiga parlour'n, yau kam gabadaya a sama take jin kanta, kuma duk wanda yayi kok'arin shiga track dinta zai had'u da 'bacin rainta. a daidai tsakiyar parlour'n suka ci karo da mahaifiyarta "ke kuma daga ina haka kika yi wani wujiga wujiga dake? me'ad ta dan tsosa tsakiyar kanta batare da tace komai ba, "dake fa nake magana kina jina?, kinsa banason wannan fitar ta babu gaira babu dalili ko. takarasa mgnr tana jan tsaki sannan tace "ina file din danace kin kawo min? "uhmm ammmmm daman shi naje nema ,daxu da safe ko da direbanta ya kawo na shirya zanje injin ciro kudi sai na kar'ba na saka acikin diary dina ,amman narasa komai nawa ina tunani agurin bata kashin nan ya subuce acikin jakata ,"yanzu hk gurin na koma ko zangani amman .....sai tayi shiru ta kasa k'arasa maganarta sakamakon wani irin kallo da uwar ta jiho mata .... "abinda kike kok'arin cewa baki gani ba, ko ba abinda zaki ce min kenan ba? me'ad tayi saurin d'aga kanta "kinsan ko file menene kika yarda shi? " file ne dake tattare da mahimman bayane akan kudad'en marayun ya'yanta, amman kalli yadda sakacinki yasa aka rasashi , keda zaki ajiye abu a gida amman kika fita dashi, nan fa suhailat tafiki kaifin baseera "am really sorry momy zanyi kokari na nemo.. " a ina zakigani? " zan sake komawa gurin ko Allah zai sa nagani takarasa mgnr tana narke fuska alamun shagwaba. "ke bar shi kawai zan sake tuntubarta ko tana da wani copy "thank you my mom .... hjy khadeeja ta shige d'akin mai gidan . Ranta babu dadi ta shiga d'akinta tana shiga ta fad'a saman gadonta ta kwanta flat tare da runtse idanunta ******* Misalin karfe tara na dare ranar a kwance da fu'ad yake ya ciro D'an karamin diary dinta brown me d'igon ruwan zinari, daya tsinta bayan rabuwarsu da me'ad ,yana kallonsa dagani kasan me tsada ne ,ahankali ya kai diary din daidai saitin hancinsa yana shinshina, ni'imtaccen kamshin, Dior addict daya kama jikin diary sosai ,sai kawai yasamu kanshi da lumshe idanunsa tare da bud'esu duka atare cikin wani sabon alamari da ba zai iya kwatantawa ba, a lokacin fu'ad matashi ne Dan kimanin shekaru talati cif da haihuwa ,duk inda ake neman kyau ga d'a nmj fu'ad ya mallakeshi ,fari ne tass me dagon hanci da yawon suma me kyawawan idanu farare kal kuma manya masu cike da nagarta . Cikin sand'a malik ya iso inda yake kwance ya fixge diary din yana dubawa yaga wasu mahimman file da ATM atsakiyarsa, fu'ad ya d'ago idanunsa ya kalleshi a matukar tsorace. " uhmmmmm daman nasan ka fad'a tarkon son yarinyar nan ,amman kake wani son waskewa, shiyasa fa nace idan kana sonta ni na hakura nabar maka , kaje ka nemi soyayyarta, amman ka tsaya wani jin kai ..."kana sonta ko ba hk ba abokina? "Tsaki fuad yaja a d'an hassale sannan ya juya masa baya "kai dai ayi D'an matsala wallahi, kaje man kayi introducing kanka agurinta Dan ni bata gabana ..... " shiyasa naga ka tsurawa diary dinta ido ba ,tare shakar kamshin turarenta? inji cewar malik yana me tuntsurewa da wata uwar dry. Wani tsakin fu'ad yaja "kanka ake ji, ga diary din nan a hannunka kayi duk abinda zakayi dashi ,sannan kayi kok'arin ya isa gareta a duk sanda kaje gabatar mata da kanka ,ina maka fatan alkhairi tare da samun soyayyarta ... "Dan Allah abokina, da gaske ,da gaske addu'ar samun nasara kamin? yakarasa mgnr yana me karasowa zuwa inda fu'ad ke kwance ya rike hannuwansa duka cikin nasa "na...gode abokina amman tare zamuje gidansu tunda ga addresse dinta acikin diary..? "a'a kaje kai kad'ai ,hallo dai ina maka fatan samun nasara akanta sannan ya meida idanunsa ya runtse ya cire hannunwasa cikin na malik yana dafe goshinsa da hannunsa daya. malik yayi saurin boye dryrsa sannan ya mike tamkar wanda akayiwa wanka da ruwan tsanyi ya isa makwancinsa "wannan shine karo na farko daya ganshi cikin damuwa hk, yammata dayawa suna kawo masa farmaki amman babu wace yaga tsan tsan damuwarsa akanta kmr me'ad, ayau suka soma ganinta amman da dukkanin alamu ta tafi da zuciyar abokinsa, ya kwanta yana dryr mugunta, domin a zahirin gsky shi ba son me'ad yake ba, amman ganin fu'ad yana neman waskewa akan sonta, yasa shi son shiga rayuwarsa tunda daman sukanyiwa junansu hk shi dasu kabeer , daga baya komai ya daidaita, Amman banda fu'ad da duk macen data kawo masa hari baya yarda ya amincewa soyayyarta ,acewarsa ba soyayya ce agabansa ba, yadda zai samu aikin da zai kula da kakarsa yake . "itama bangaren me'ad kasa runtsawa tayi duk ta inda ta juya fu'ad take gani acikin kwayar idanunta,wani irin canji take ji a gabadaya ilahirin jikinta, ahankali take jin feeling's na bijirowa gangar jikinta wanda wannan shine lokacin na farko dataji hk ajikinta, domin duk yadda sajida ke bata labari akan yanayi makamancin hk, bata ta'ba yarda ba, ta d'auki lamarin amatsayin shirme, ashe ba shirme bane da gaske ne?" mutun kanji wannan yanayi ajikinsa idan ya had'u da abinda yake so... kudundune jikinta guri daya tayi acikin bargonta, tana kok'arin basar da abinda take ji yana tafiya da bugun zuciyarta ,wanda a zahirin gasky mamaki faruwar hkn ya soma kamata, a kallo daya komai ba neman birkice mata....... da kyar da taimakon bacci barawo tasamu tayi bacci. Abu fa kmr wasa kullun me'ad sai fita zaga gari ko Allah zai sa ta had'u da fu'ad amman shiru ka keji ,har kusan sati daya , tana garari agari. yadda take zariyar neman fu'ad, haka malik ke zariyar nemanta domin bata diary dinta dake d'auke dakatin ATM dinta ,da kyar ya samu shigowa cikin estate dinsu ya isa bakin tafkeken get din gidansu da'aka nuna masa, yasamu daya daga cikin masu gadi gidan bayan ya gaishesa ,me gadi ya amsa yana masa wani irin kallo sannan yace" wa kake nema? "dan Allah ina neman me'ad. Me gadin yayi shiru kawai yana duban malik daga samansa har kasa, ba dan yana da wata makusa ba ajikinsa, sai na talauci da babu daya nuna ajikinsa, me gadi ya sake maimaita tmbyr da malik yayi "kace kana neman me'ad ko me? malik ya d'aga masa kai ala'mun eh. "Ita me'ad din tasan da zuwanka ? "Aa amman idan kashiga kace mata wanda suka had'u agurin injin din ci... "Dakata anan da shirmenka, sannan ka juya ka 'bace daga gurin nan , daganika irin yan yunwan nan ne, jobless marasa aikin yi," kaga yarinya yar babban gida shine ka lallabo ko? "oya maza ka 'bace tun kafin ita kanta tasan da zuwanka kasha dukan banza. Batare da mutsu ba jiki a sabule malik ya bar unguwar tamkar wanda kwai ya fashewa acikin yana mamakin girman al'amarin, sai dai kullun zai zo amman baya samun ganinta hk zai juya ya koma da diary dinta , inda fu'ad ya d'auki zafi sosai dashi "kana wahalar da kanka abanza daga karshe ka had'u da wulakaci . "ka fahimceni fu'ad Allah ba wai .."dakata malam kaje kacigaba da bibiyarta rayuwarka ce, abinda zai min ciwo bai wuce naga ko naji kace an wulak'anta ka ba, yana karasa mgnr ya fice daga d'akin yana huci. Malik ya girgiza kansa ,tabbas ya fahimci irin son da abokinsa kewa me'ad amman ya dakewa zuciyarsa, shi zai yi iya kokarinsa yaga ya had'a ruhinsu guri daya.... ******* Yau takama litinin wanda kowa yake sauri ya shirya ya samu halatar makaranta da wuri ,ko neman aiki da sauransu , ita kuwa me'ad tana gado tana juyin da tunanin fu'ad dinta ,har kafe tara sannan ta tashi tasa aka had'a mata ruwan,tayi wanka ,nan ma sai da ta'ba lokacin gurin tunaninsa ganin take kmr yana tare daita, duk inda ta juya shi take gani har mafarkinsa take, suna rayuwar aure tare. ahankali ta fito daga bathoorom gurin shiryawa ma sai data bata tsawon lokaci ta fito ta karya sannan takama hanya dan zuwa bank domin amsar sabon ATM. tun da ta cusa hancin motarta cikin harabar zenieth bank ta sauya yanayin tukinta tayi parking sai dai tajima acikin motar saboda ganin kmr mutane sun yi yawa kafin daga baya ta fito, tana taku ahankali da rangwad'a tashiga . kai tsaye gurin costume's care ta nufa , somi itace wace jinisu ya had'u daita sosai, somi na ganin me'ad ta sakar mata murmushi tare da cewa"me'ad you are welcome hade da tmbayarta abinda ke tafe daita, cikin harshen tsadadden turancinta tasoma mata bayanin abinda tazo yi, hannunta ta zura karkashin table ta zaro wani file ta mika mata tare da nuna mata wani madaidaicin office da hannunta "ki shiga can ki cike sai kawo min. "okay me'ad ta furta sannan ta amshi file din ,cikin mintuna kad'an ta cike ta fito "ta mika mata batare da 'bata lokaci ba akayi mata komai akace taje ATM ta canza pin dinta tare da mika mata envelop ,cike da rausaya ta nufi injin cire kudi bata wani canza pin dinta ba, ainhin pin dinta na da 5996 ta sake sakawa sannan ta kama gabanta wanda dayawa mutanen dake tsaye agurin hankalisu na kanta. Yau ma kmr kullun tana fita malik yazo gidan sai dai me gadin bai bi ta kansa ba ,saboda kallon wani mahaukaci dayake masa har sanda ta sanyo hancin motarta, ana kok'arin bud'e mata get shi kuma yana kok'arin isa inda motarta take, sauran security suka dakatar dashi, dan wani har ya kai masa mari ya goce da sauri. Me'ad ta bishi da wani irin kallon sani ,sannan ta kusa hancin motarta cikin gida tayi parking , ta fito tana gyara zaman glass din dake manne da idanunta ,ta kira daya daga cikin masu kula da bakin get "waye wancan mutumin da kuke dambe dashi kan sai ya iso gareni? sai da obi yayi jim.. sannan yace "wai gurinki yazo yau akalla ya kai sati kenan yana zuwa " what? ta furta arazane sannan tace. "how dare him yazo gurina akan wani dalili ? "hk dai yace ranki ya dade. "Karku sake ku bashi damar sake shigowa estate din nan ballanata har ya iso bakin get din gidan"yes ma . ta juya zuwa cikin gida tana tunanin inda tasan fuska amman sam ta kasa tunawa. obi ya juya cikin sauri ya isa ga malik yasoma tura keyarsa "dan Allah ka saura ni abunta nazo kawo mata data yar bawani abu nazo nemana gurinta ba, amman ina sam obi yaki sauraransa har sai da kai ga fitar dashi gbdy daga estate din. ******* tafe suke ita da sajida a Shopprit domin siyaya wa mahafinta dake jinyar hannunsa agida,kuma a yau din nan suke expecting dawowar abbansu me'ad daga kasar America wanda yaje cheek up , ahankali suke takawa kmr basu san taka k'asa me'ad na sake bawa sajida labarin fu'ad sannan suna daukar duk wani abun amfanin daya kai su bayan sun gama sukaje inda ake biyan kudi me'ad ta bada ATM dinta, suna daf da fitowa suka had'u da Malik cikin saurin yake binsu yana kiran sunanta" me'ad me'ad!! me'ad ta juyo tana ganinsa tayi saurin kawar da fuskarta tacigaba da tafiya "kai kawata wannan mutumin fa ke yake kira.. ki tsaya mana da ala'mun yasanki "baki da hankali aganni na tsaya da wannan ai sai mutane su raina da ajina . biyota malik yayi" dan Allah ki tsaya abunki zan baki. da sauri taja hannun sajida ,haba me'ad ki tsaya mana wulakanci bashi da amfani balle d'an adam daraja garesa "bawani abun fad'a anan kawata , wancan banza nema yake na kulashi ,ni km ina i can't suka shiga motarsu cikin sauri suka bar gurin kafin malik yakaraso. "okay mubar zancesa cigaba da gaya min labarin kyawawa nan , ko shima kmr sauran samari gari yake ? birki taja sakamakon gitawar da wani me okada yayi ta gabanta. ta Leko da kanta cikin bacin "kai ina zakaje kake sauri hk? " jiki da wata banzar mgn kisawa motarki alamar koya tuki Dan da alamun baki kware ba . " kai koya min tuki zakayi ko me ? "Kina bukatar hkn ai. "kutumar uban can... "kinga malama duk abinda za'a yi ayi ammam ban da zagin iyaye yar rainin hankali kawai, ko dan kinganki cikin wannan kememiyar motar kike tunanin zaki zageni na kyaleki? sajida ce tayi masa alamun ya wuce kawai tare da cewa "kinga manta da wannan " kibani labarin kyakyawan saurayin nan da kuka had'u last week wallahi ina jin dadin yadda kike fassalta shi, me'ad tayi shiru ta kasa cewa komai ,kafin daga baya ta furta sunansa "fu'ad kenan .... "suna me dadi tunda kike furta min sunasa naji sunan har cikin raina inji cewar sajida "Allah ko ai sai ma kinganshi kawata hadadden gaye aji farko zance fu'ad suke har suka shigo harabar gidansu sajida inda suka iske motar gidansu me'ad"kai kinga da ala'mun dady Dina ya sauka? Cikin sauri suka fito hannunwasu rike da farar laylon. Da dariya suka shigo parlour ,n inda suka iske mahaifin sajida da nata zaune suna tautaunawa akan abinda ya faru " ai ina gaya maka Aliyu tabbas zakasamu k'arin girma nan ba da jimawa ba akan wannan kokarin naka,mead takarasa kusa da mahaifinta ta rungumeshi "dady sannu da zuwa. "yauwa yar baba fatan kina lfy? "ina lfy amman ba lau ba takarasa mgnr tana nufar mahaifin sajida "gashi uncle "ka gwada wannan kaji yana da dadi sosai . " yar baba aliyu ya gaya min cewa tsalake rijiya kikeyi a wajen harbe harben da'akayi? batare data juyo ba tace "eh baba amman babu abinda yasameni ,uncle ka fa zama jarumi a gari "kalli can kagani ta nuna masa tv da yatsan hannuta, kowani gidan talbijan kai suke nunawa tun daga last Week har yau din nan sajida ta zauna kusa da mahaifinta tana gyara masa zaman bandage dake d'aure da hannunsa. Mahaifin me'ad ya gyara zamansa tare da cewa " yar baba kawo min coffee mara madara "okay dad. "uhm yar baba nima ki kawo min, me'ad ta nufi hanyar kitchen tana karasa shiga ta ja ta tsaya tana kiran "sajida ........ "na'am. "a ina kika ajiye sugar? takarasa mgnr tana kallon wasu jerin robobi dake ajiye a kitchen cabinet ,acp ya bata amsa daga zaune dayake " ai in dai wannan yar zaki tambaya ,to kuwa kin saba lamba. sajida ta kaiwa babanta naushi a dayan hannunsa mara ciwo tana dry "kai baba "kai baba ko gsky na fada? " ko sau daya bata ta'ba shiga kitchen din nan da sunan d'aura wani abu ba, bari nazo na d'auko miki yakarasa mgnr yana me mikewa tsaye "me'ad..... sajida takirata tana murmushi nima kizo min da coffee da k'arin sugar kinji kawata. " hmmm yarinyar idan zaki koyi had'a shayi Da kanki , ki tsaya ki koya ko Dan aure da zakiyi watan gobe "ni imran din ma nake tausayi inji cewar acp "in tambayeki yar baba, waye wancen yaron dana samun labarin yana xuwa gurinki kullun bayan ga maganar safwan da'aka ajiye "uhmmmm wannan Shashan , ai kwana hudu data wuce na fara ganinsa ban san inda yasan ni ba amman har sunana ya sani abun tsoro . "uhmmm? " uhmmm uncle nifa abun ya fara damuna yau ma sai da muka had'u dashi a shopping, acp ya juya zai bar kitchen din fuskarsa da ala'mun rashin yarda "uncle kar ka fahimceni ba daidai ba "ai shikenan yar baba na fahimceki .... ******** tsaye suke su duka acikin had'ad'd'en boutique dake depomu wanda yakasance mallakin mahaifin kabeer ne .wasu yammata ne su biyu suka shigo cikin harabar gurin, kowace sanye da riga iya cinyarta wanda ke nuni da yare ne, makale da yar karamar jaka suna tautaunawa, kabeer dake tsaye kusa da malik yana dan kurban fiver alive "yace kumeless tare da binsu da wani shu'umin kallo malik yayi saurin juyawa shima ya bisu da kallo ,sannan ya juyo ya kalli fu'ad yana dage masa gira kana ya sake juyowa ga kabeer "idan kabiyi wad'an yammanta kai ka zasuyi su baro ,duk bugi ne wallahi ina gaya maka. "kai dan Allah banason shirme ka juya ka kalleshi da kyau gsky sun hadu inji cewar kabeer. Malik ya sake juyowa ahankali yana kare musu kallon tsab sannan yace "uhmmmmm wad'an yammanta lagos din suna da tsabagen wayo tsiya ,su sha kwaliya su dinga maganganu irin na birgewa, amman duk fanko suke,ya dan sake kallon inda fu'ad yake sannan yacigaba "daya nagani acikinsu me nagarta da kamalar madarar kyau ...... sudais yayi saurin cewa "da gaske ? "yace uhm. "kallesu da kyau kagani duk kwaliya ce kawai "yanzu kayi kok'arin kallonsu batare da kwaliya ba kagani . "kamar yaya kenan? inji cewar kabeer . "ka aiyana da tunaninka mana .. "kai dan Allah banason shashanci da ala'mun fa kwal'kwaluwarka tasoma samun matsala inji cewer kabee . "kai ne dai mahaukaci amman ni nasan abinda nake duk da cewar akwai yammata dayawa amman me'ad dina ta zarce kowa yakarasa maganar yana ware hannunwansa duka.. "kaji mahaukaci suka kwashe da dry "matar da jiya jiyan nan tagama shuka maka rashin mutunci, wai har da wani cewa me'ad dinsa suka sake kwashe da dry suna nunashi . fu'ad dake tsaye rungume da hannuwansa duka a kirji bai kulasu ba illa fuskantar kofar shigowar dayayi tare da takaicin malik, aiko tamkar a mafarki yaga shigowarta sanyi cikin doguwar rigar abaya har kasa ta nad'e kanta da mayafin abayar hannunta rike da karamar jaka saurin runtse idanunsa yayi yana cigaba da kallonta ahankali ya mutsutsuka idanunsa" itace ko kuwa wata ce me kama daita ,tabbatar da itace yasashi saurin waskewa alokacin da suka had'a ido daita itama kallonsa ta tsaya yi cike da matsanancin mamaki ta mutsumutsuke idanunta tagani ko shaukin sonshi ne yasata ganin hk oho. muryarta a sanyaye tace "sajida ga fu'ad dina tare da nuna mashi, tsura masa ido sajida tayi, lokaci daya numfashinta ya nemi d'aukewa ganin halitar da bata ta'ba ganin irinta ba, tana ganin kyawun imran wanda zata aura amman na fu'ad ya zarta nashi,kad'an kad'an taoma jin tsigar jikinta na tashi abinda ta kasa fassalta ma'anarsa, wani irin sanyi soyayyarsa ne ya tsarga mata ya fara bin ilahirin jikinta, take ta lumshe idanunta zuciyarta na wani irin harbawa da sauri sauri, gbdy ta kasa d'auke idanunta akanshi har sanda ya juya musu baya. shi kuwa malik na ganinta yasoma murmushin tamkar wanda akayiwa bushara da gidan aljanna sannan yace "kai kabeer sudais itace fa gata can yarinyar nan wallahi itace ..me'ad najin hk tayi saurin riko hannun sajida "kinga wanda na nuna miki? "uhmm sajida ta iya cewa still idanunta na kan fu'ad "wance dake sanye da kaya shine fu'ad dina amman zo mubar nan yanzu yanzu saboda banason wancan mahaukacin ya dagula min lisafi ,sai yanzu na tina shi, ranar da muka hadu da fu'ad suna tare sai dai bansani ba taren suke ko kuwa anan suka had'u, wanda nake so daban shi kuma yana kokarin hanani rawar gaban hantsi . "haba me'ad dan Allah ki tsaya naga fu'ad din da kyau shine dai sanye da riga pinky? "eh shine amman mu wuce kawai... da sauri malik ya biyo bayansu yana kiran sunanta "me'ad...jimana me'ad!! dan Allah ki tsaya ya kwaso aguje su kabeer suka biyosa" kai majinun ina zaka bayan gasu can, cangurin fa sukayi, ba itace me kaya ruwan d'aurawa ba? "eh itace "mead dan Allah ki tsaya ita kuwa tafiya kawai take tana jan hannun sajida, "gsky fu'ad kyakkywa ne ajin farko amman me zai hana ki tsaya ki saurari wancan wata killa abokinsa ne fa. "kinga da ala'mun magana yake son yi dake. me'ad tayi mata banza sai janta take har suka shiga lift "ki daina turani mana, shi Wanda kike so ma bai san kina yi ba, ba gara ki tsayawa me binki ba, watakilla ma abokinsa ne ya taimaka ya janyo miki hankalinsa ,aguje malik ya biyosu yana ihun" jimana dan Allah ki tsaya minti daya abunki zan baki ta cikin lift sajida ta d'agowa fu'ad hannu wanda ya sake juyowa "sannu tana dariyar da za'a iya kiranta na farinciki "kibari mana sajida kina magana zai ta binki ne ya d'auka muma irinsa ne.ta fadi hkn ne a tunanita ko Malik sajida ta dagawa hannu, sajida tayi murmushi tana sake daga masa hannu. " haba sajida meye hk ne? Karki manta fa watan gobe ne za'a yi bikinki. "kinga bangane mgnrki ba nifa fu'ad nake d'agawa hannu ba wancan me bin namu ba "stop it sajida.. .." ki daina kallonsa dayawa da fa sadakin wani akanki "ki kyaleni nayita kallonsa tun yanzu kafin aurena bayan nayi auren shikenan... me'ad tayi shiru kawai takasa cewa komai har sanda lift ya tsaya suka fito da sauri me'ad janye da hannun sajida . malik kuwa sai kokarin saukowa yake daga step domin ya iske su akasa . yayinda fu'ad ke tsaye a inda suka barshe yana kallonsu batare da yayi yunkurin motsawa ba.... mmn sudais ce 💗💗💗💗💗💗 'YAN CINKI 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 ~NA~ *AYSHA A BAGUDO* ~DEDICATED TO~ MRS ADAM ( YAR MUTAN KAGARA) page 47 to 48 .....yana nan tsaye a gurin da suka barshi har sanda suka dawo suka samesa, malik ya dafa kafad'arsa yana fidda numfashi sama sama sannan yace "abokina kaga me'ad dina ko?" gsky yarinyar ta had'u iya had'uwa ,dan Allah abokin ka taimakeni ka tayani yakin shawo kanta,dan zan iya rasa raina akanta yakarasa mgnr yana kwashewa da dry.... on expecting malik yaji sautin muryarsa " Allah yasa ka mutu yanzu in har sai na tayaka yakin neman amincewarta sannan ya juya yasoma takawa ahankali ya bar malik tsaye, sake da baki yana kallon bayansa sai dai fuskarsa kunshe da dry ..kana ya juyo yana fuskartata kabeer "kungani ko zargina fa yana neman tabbata fu'ad son yarinyar nan amman miskilancinsa ya hanashi fahimta, amman ni nan zansashi ya fahimci ya fad'a tarko dan bazan bari yarinyar ta subuce masa ba.." tabbas zanceka hk yake,yana sonta, itama yarinyar da ala'mun ta kamu da matsanancin sonshi inji cewar sudais. kabeer ya numfasa kana yace "kar dai ku manta da halin fu'ad, tunda bai ce yana sonta ba ku yanzu meye naku a ciki ?balle kai malik da kabi ka hakikance akan yariyar , ka dai bi ahankali kar ka je ka jefa kan cikin wahala shi dai fu'ad bai aikeka ba har gara ma kayiwa kanka yaki neman au...shigowar wasu costumer's ne yasa kabeer katse zance yaso garesu tare da kiran daya daga cikin yan dake kula gurin.. bangarensu me'ad da sajida kuwa tunda suka shiga mota babu wanda yayi kokarin yin magana kowace da abinda zuciyarta take kismamata akan fu'ad, har suka karasa gida jiki a sanyaye suka shiga parlour'n inda suka iske hjy Khadija zaune tana kallon labarai "momy sannu da gida. "sannunku yammatana har kun dawo ? "ina siyayyar da kuka fita yi? sajida ta zauna jagwab akan kujera tana fuskantar momy "me'ad ta hana mu yi taba amsa da hkn tana runtse idanunta. "bangane hausar ta hana ba? " nan sajida ta gaya komai amman banda sunan fu'ad. momy taja numfashi da ajiyar zuciya atare sannan ta dubi inda me'ad take tsaye tana cizan lip's dinta "karki soma janyowa kanki tashin hankali kinsa dai an gama maganar aurenki da safwan jiran dawowarsa kawai ake... tun da momy tasoma mgn tayi yunkurin barin gurin dan zuciyarta baxa iya sauraran maganganunta akan safwan ba, wanda a halin datake ciki yanxu ta manta dashi balle wani magana da'aka tsayar a tsakaninsu. dare yayi sosai yanayin garin yayi sanyi baka jin sautin komai da sautin komai sai na iskar garin dake kad'awa ahankali yana bin jikin bil'adam ciki kuwa har dasu sajida da me'ad da idanunsu ke bud'e ,babu wani ala'mun bacci acikinsu juyi kawai suke akan gado suna tunani rai daya wato fu'ad, sosai sajida ke zurfafa tunaninta akansa sam bata tsamaci kyawunsa da nagartasa ta Kai yadda tagansa ba,a zahirin gasky bacin me'ad tasoma furta tana son fu'ad ba, da tsab zata rusa zance aurenta da emran ,tayi yakin neman soyayyarsa tare da aurensa, amman kashi ....me'ad tayi mata tawayar da baxata iya kai kanta garesa ba ...... sam ranar sajida bata samu runtsawa ba, har gara ma me'ad ta runtsa da taimakon mafarkinsa daya kawo mata ziyara. abu fa kmr wasa kullun mee'ad ta kwanta sai tayi mafarki fu'ad yana romacing dinta wani lokacin har saduwa daita, saboda zurfafa tunaninsa datake. parlour'n gidan momy ta fito sanye cikin doguwar rigar har k'asa da madaidaicin hijab ,tana gyara zaman takardun dake rike a hannunta tare da kiran sunanta "mead..me'ad!! ummi tayi saurin cewa "tana d'akinta bata fito ba tukun. kai tsaye hanyar d'akin momy ta nufa tana cewa karfe takwas fa har tayi me'ad amman har yanzu kina kwance, koda tashiga d'akin kwance ta isketa akan gadonta kmr yadda tazata ,ta lullu'be jikinta da blanket me taushi , momy tak'araso har inda take kwance tare da zame bargon data lullu'ba dashi "me'ad kitashi mana karfe takwas fa tayi "uhmmmm momy bacci nake ji tayi mgnr tana mika ...ki d'aure ki tashi .... tashi zaune me'ad tayi idanunta a runtse "maza tashi mana wannan fa shine karo na biyu fa dana dana shigo tashinki bazan sake dawowa ba kin san dai kina da interview yau ko? nima na shirya zuwa aiki momy ta juya abunta idan kingama ga abincinki can har ta kai bakin kofar taja ta tsaya tace "me'ad ...."na'am momy ya sunan yaron ? da sauri ta bud'e idanunta sosai sannan tace sunan wa kenan momy ? "sunan yaron dakika jarabar so har kika kwana kina marfakinsa. runtse idanunta tayi ta sauko daga kan gadon zuwa kan doguwar ta kishingid'a ,sannan tace fu....... ad "uhmmmm idan na dawo mayi magana akanshi ,sai na dawo dan gsky na kusan makara ki hanzarta tashi. goshinta ta dafe tana tunanin, "yanzu son fu'ad hk zai mata ? ta dad'e zaune kafin daga baya ta mike tashiga wanka shap shap ta fito sanye cikin riga da siket na atamfar super exclusive me zanen fuluwa ja da baki a had'e wanda ya d'an kamata ajiki kad'an, kanta babu d'an kwali kasancewar bata fiyye son d'aurawa ba sai karamin bakin mayafi data yane kanta dashi ta fita cikin takunta na yanga da nuna ita yar wani ce ta shiga motarta oil and gas dake cikin apapa. koda ta isa ta iske dubbanin mutane suna jira amman da zuwanta kiran waya kawai tayi sai gashi an bada umarnin tashigo kai tsaye batare da bata lokaci ba ta fito wanda fitowarta sai days bugar da zukatan tarin mazan dake zaune agurin ciki kuwa har da fu'ad dake tsaye rike da takardun neman aiki, zuciyarta taji tayi wani irin bugawa da karfi ahankali ta d'ago idanunta kmr ance ta waiga gefen hannunta na dama taganshi tsaye shi da wani da batasan kowaye ba, kallo daya tayi masa taji zuciyarta ta sake bugawa kmr yau ta fara ganinsa ,duk da bawai yau ta fara daura idanunta akanshi ba, sai dai kusancin na yau ya sha bambam da sauran lukuta wani irin kyakkyawan kallo take masa, yau gashi a gabanta ba daga nesa nesa ba, shima gabansa ne ya fad'i sakamakon ganinta dayayi a aininhin shigarta ta hausa fulani. ahankali take daga kafafunta har zuwa office din alhj Ibrahim wanda yake shugaba ga maikatan kuma aminin mahaifinta, bayan sun gaisa ya tambayeta lafiyar mutanen gidansu, tace "duk lfy atakaice sannan akabata aiki wanda zata dinga daukar albashi me tsoka batare da wani interview ..kusan minti biyar tana zaune alhj ibrahim ya d'ago yana dubanta sannan yace "ko akwai wani abu ne, shiru tayi na minti biyu kana tace akwai "ina sauraronki ya fad'a tare da meida idanunsa kan tarin takardu dake gabansa "akwai wani danake son ka taimakawa kabashi aiki a ma'aikatar nan. "yana ina? " shine kika tsaya jan maganar abinda zaki fad'a da confidence ai ba mutun daya ba diyata ko mutun goma kike son a d'auka za'a d'auka masengen sa ta aika yaje ya shigo da fu'ad, wanda shigowarsa yayi daidai da tashin da alhj ibrahim yayi, yakaraso shigowa sanye da suit da bakin glass frada a idanunsa take office din ya gauraya da kamshin turarensa kafafunsa rufe cikin cover shoe baki ,taja masa kujera tana nuna masa gurin zama amman yaki zama "ka zauna zaka samu aiki karkashin jagorancina matukar shi kazo neman ,idan kuma kaki zaka karad'e garin nan batare da kasamu aiki ba saboda mu 'yan alfarma gama maganarta keda wuya ya juya kawai batare yace mata ko uffan ba, ta mike da sauri tabi bayansa tana kiran sunansa "fu'ad ka tsaya zan saka abaka aiki me mahimmaci . amman ina ko juyowa baiyi ba har ya isa inda sudais ke tsaye yana jiransa ya rike hannunsa "zo mu wuce kawai ya iya furtawa "ka tsaya mana bakaji tana kiranka bane ? kana ji fa taimakonmu zatayi "banason duk wani taimako daga gareta kazo muje kawai idan km baxaka ba na wuce.... ya fixge hannunsa cikin nasa "to bazani ba shekara nawa ina neman aikin bansamu ba yau zamu samu amman kake girman kan banza ... fu'ad ba tsaya ba ballanatana ya juyo gareta yacigaba da tafiyarsa shi kuma sudais yakarasa gareta "ranki ya dad'e kiyi hakuri hk halinsa yake, shegen girman kan tsiya shi ba... "dakata karka soma furta kalmar 'batanci garesa, daya tsaya har kAi zaka iya cin albarkansa tana karasa fad'ar hk ta juya fuuuuuu zuwa inda tayi parking din motarta ta figa aguje, mutane kuwa sai zagin fu'ad suke akan wasa da damarsa da yayi. tana barin oil and gas kai coffter coffe ta zarce inda suka saba had'uwa da sajida ,dukkaninsu shiru sukayi suna kallon junansu bayan labarin da me'ad tabata akan abinda ya faru atsakaninta da fu'ad. "me zai hana ki hakura dashi, tunda yaki saurararki. "i can't sajida ina son shi bansan ina son shi ba sai yau dana yi masa kallon gani ga shi, ni dai ki tayani adduar samun shi kawai dan matsawar ban auresa ba sai dai na mutu babu aure .. "all the same inji cewar sajida "what? "no babu komai suka cigaba da zance fu'ad batare da sun kai coffen da'aka kawo musu bakinsu ba tsawon lokaci suna zantawa sannan suka mike atare daga nan gidansu sajida suka nufa ,trafic ya kamasu suka tsaya inda malik shima yana d'ayan gefen hagu bai lura dasu ba sai danja tabasu damar wucewa sannan ya gansu, nan fa yashiga binsu akan lefan dinsa . kmr ance sajida ta kalli mudubin gefenta ta hangosa yana daga musu hannu, leko da kanta tayi domim tabbatar dashi din ne "me ad duba madubin gefenki kiga wannan d'an jagaliyar fa mu yake bi inji cewar sajida "kai dan Allah tayi mgnr tana dubawa ,"tabbas mu yake bi amman nasan yadda zanyi maganinsa k'ararsa zan kai gurin uncle ya jefa min shi cikin magark'ama ayi masa dukan tsiya haba dai ke kuwa kamar shi yace kar fu'ad yasoki takarasa mgnr tana dry a daidai lokacin da suka iso kofar gidansu sajida shims yaja ya tsaya tare da parking din mashin dinsa suna fitowa daga cikin motar ya iso garesu yana cewa jimana me'ad. nasan kinsani amman kike pretending kamar bakisani ba ...dau dau ta d'auke shi da mari "how dare you calling my name? yayi saurin dafe kuncinsa yana kallonta. "me ma yasa kake bina? "kasan ko ni wacece? "dan jagaliya irinka kake bibiyata "waye ubanka a duk fad'in garin nan ? jiki a sanyaye yace" daman bawani abu bane amman idan baki tunani ba, ni ne malik wanda muka had'u agurin ciro kudi .. "and so what? "jibeka kawai wani wawa dashi ,ko iya fitar da maganar bai iya ba,da muka had'u sai akayi yaya? "daman kin yar da diary dinki ne shine fa na amsa gurin abokina fu'ad dan nasan shi ba bazai ta'ba biyoki domin yabaki ba ,shi nake ta ajiyarsa kullun ina son nabaki amman bakya saurarata.. "inna ilaihi wa inna ilaihi rajiun ta furta acikin zuciyarta ...........idanunta a kansa mmn sudais ce 💗💗💗💗💗💗 'YAN CINKI 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 ~NA~ *AYSHA A BAGUDO* ~DEDICATED TO~ MRS ADAM ( YAR MUTAN KAGARA) page 49 to 50 ....kallon kallo suka shiga yi atsakaninsu duka uku sajida me'ad malik, shiru me'ad tayi tana kallonsa batare da ta sake yunkurin cewa dashi komai ba ,sai dai gabadaya nadama tattare da kunyar abinda tayi masa a yanzu ya kamata tare da raunata wani shashi na gangar jikinta," ta wulakanta mafi kusanci ga zuciyarta bisa ga mummunar d'abi'arta...."me yasa tayi saurin marinsa? "why why why!!! me'ad? "why did you slap him..? tana nan tsaye jikinta na rawa har malik yakaraso zuwa inda take tsaye jikinta nacigaba da kyarma ya miko mata diary dinta ......nadama ce fal dankare da zuciyarta "hakika ta cuci kanta ta cuci rayuwarta ba zata ta'ba yafewa kanta abinda ta aikata masa ba matsawar yayi silar rasa fu'ad dinta....."ki amsa ko nabawa kawarki ne? jin sautin mgnrsa yasa tayi saurin dawowa cikin haiyacinta domin natsuwar tasoma barin gangar jikinta, kallo daya zaka mata kagane kalar damuwar datake ciki. sai daya sake mgn sannan jiki a sanyaye tasanya hannuta ta amshi diary dinta, shi kuma ya juya tamkar wanda kwai ya fashewa aciki yasoma tafiya , har ya kai gurin mashin dinsa yana shirin hawa yaji sautin muryarta ahankali "tsaya dan Allah sannan tasoma kok'arin takowa zuwa inda yake, jikinta a matukar sanyaye . muryarta na rawa tace "dan...dan girman Allah kayi hakuri ta furta hkn tana mai runtse idanunta kasancewar wannan shine Karo na farko data bai wa wani mutun hakuri ,bayan iyayenta da suka kawota duniya "kayi hakuri ta sake maimaita kalmar muryata a raunane tare da bud'e idanunta fess akansa tana kallon yanayinsa da gbdy ya sauya, a yanzu dayake gabanta ganin take tamkar fu'ad dinta ne tsaye a gabanta cikin matsanancin damuwa , "hakika nayi abinda bai dace ba ,da rashin kamata gareka, tun ranar farko dana soma ganinka a gidanmu nayi tunanin kmr nasan fuskarka amman alokacin na kasa tuna inda nasanka, sannan lokacin dana ganka tare da fu'ad a boutiq shima ban tantance alakarku dashi ba amman dai kayi hkr dan Allah. " babu komai ,komai ya wuce Allah ya kiyaye na gaba, hk daman rayuwar take ,da nabi shawarar fu'ad da ban jawo wa kaina wulakanci ba, domin babu abinda ya kai wulakanci kmr a tsinkaka ta hanyar mari..... ...amman babu komai "me'ad yakira sunanta ,nasan kina mutuwar son abokina fu'ad duba ga yanayin nadamarki bayan kinsa alakata dashi, amman shi mutun ne me matukar kamewa ,kai tsaye hk bazai ta'ba fuskantarki ba .... "nasani ....nasan da haka amman ko zaka iya taimaka min plz takarasa mgnr muryarta na craking ? domin zan iya yin komai akansa ,"da fari dai ka taimaka min da number wayarsa tare da sake bashi hakuri. "sajida plz ki matso kusa mana ki bashi hakuri kema bawai ki wani ja kin tsaya kina kallonmu ba. "me zance masa me'ad? "me kike son nace masa after kingama aikata son ranki ? "i think kin bashi hakurin kuma yace ya hakura. "eh amman ni dai kice masa wani abu dan Allah har yanzu akwai damuwa a tattare da shi. "dole kuwa kiga damuwa atare dashi me'ad , bashi ba koni kika karewa kallo zakiga ala'mun hk atare dani "ta yaya daga ambatar sunanki zaki maresa? " tun ranar farko daya kira sunanki na gaya miki definitely wannan mutumin yasanki wani guri amman kika nuna min sam ba hk bane yanzu wa gari ya waya? " komai sai kin saka zafin rai aciki, sosai sajida tayi mata fad'a ta inda take shiga bata nan take fita ba har sai da malik ya nuna abar zance ya isa hk "kuma har ga Allah komai ya wuce daga karshe ya karanto mata number fu'ad bayan tayi tsore, tace yabata nashi yabata sannan ya wuce . " a she dai mutumin kirki ne nake masa wani irin kallo ta furta hkn tana kallon bayansa .. ....... juyawa sukayi zuwa cikin gidan suna shiga d'akin sajida tasoma neman layinsa amman kiran duniya tayi bai d'auka ba haka takarar da wunin ranar akan kiran layinsa bai d'auka ba. shi kuwa malik a sanyaye ya karaso gida, duk da har cikin zuciyarsa yana jin abinda me'ad tayi masa ya wuce, amman gangar jikinsa takasa hakurin hk, ganin yanayinsa yasa sudais dake bawa kabeer labarin abinda ya faru a oil and gas a safiyar yau din nan ya karaso gurinsa yana tmbyrsa, shima kabeer yazo ya tsaya dayan gefensa "lafiyarka malik? " me yasameka duk ka dawo wani iri hk? yayi masa tmbyr ajere. naunayen ajiyar zuciya ya sauke tare da gaya musu abinda ya faru har zuwa Number wayar fu'ad daya bata, dan basa boyewa junansu komai, daga karshe yace "karsu sanarwa fu'ad saboda ya sha ja masa kunne da gargadin abinda zai je yazo . abinda malik bai sani ba gbdy mgnrsa acikin kunnesa yayita,wanda take ran fu'ad ya 'baci zuciyarsa tazo har wuya tana tafarfasa sai dai ya kudirici aniyar zai ganar daita kurenta ta hanyar tarkonsa data fad'a . sai gurin tara na dare me'ad ta sake gwada kiransa da dayan layinta, bugu biyu ya d'auka cikin dakakkiyar muryarsa duk da bai san ko number waye ba, "hello..... ji tayi tamkar an mata bushara da gidan aljanna ne dan dadi, lokacin dataji sautin muryarsa ta ratsa cikin dodon kunneta, tayi sallama cikin sanyayyiyar muryarta amadadin "hello din daya ce mata, ," daga can bangarensa yayi shiru kawai yana sauraran yaji ko waye duk da zuciyarsa ta soma gano masa ko wace saboda sautin muryar mace dayaji, ita km hucin Numashinsa dake fita ta cikin wayar ne yayi nasarar kashe mata ilahirin jikinta har yasa ta kasa mgn, jin shirun yayi yawa ne yasa shi cewa "waye yake kok'arin shiga cikin lokacin hutuna? murmushin fariciki tayi gefe daya kuma hawaye ya cika kwarnin idanunta sakamakon sake jin sautinsa a hassale , sai da ta sake kwantar da muryarta sosai sannan tace "me'ad ce. "wace hk? jin abinda yace ya sata mikewa zaune daga kwance datake "uhmm ammm dan Allah karka ce baka ganeni ba, gurin abokinka malik na amshi numberka ? "kit taji ya katse kiran ta sake kiransa back bai d'auka ba daga karshe taji ya kashe wayar gbdy ranar dai kwanan zaune me'ad tayi ,duk inda ta juya fuskarsa take gani da komai nashi bata ta'ba tunanin zata fad'a tarkon d'a nmj irin hk ba. washegari bata tashi da wuri ba saboda rashin baccin dabata samu yi daren jiya ba. sai gurin 12 ta tashi tashiga wanka. ta sake neman layinsa da wata number daban yana d'auka tace "barka dai me'ad ce take magana ...kit taji ya katse kiran wani irin sarere tayi agurin ahankali tayi kasa ta zauna akan gadonta sai ga hawaye yasoma ciccikowa a idanunta ta tsurawa wayar ido tana kallo gani take kmr shine acikin wayar. wani tunani tayi ,zuciyarta ke umartata data kira number malik, take batayi sanya a gwiwa ba tashiga neman layinsa, bayan ya ta sake bashi hakuri akan abinda ya faru sannan ta d'aura da damuwarta "hakuri yabata Inshaallahu zan masa mgn. "ok nagode sosai sai kaji kirana ta katse kiran shi km ya sauke idanunsa akan fu'ad dake tsaye yana shirin zuwa gurin inna kakarsa "fu'ad yakira sunansa.. ya d'ago kansa tare sauke kyawawan idanunsa akansa batare da yace komai ba "dan Allah saurari yarinyar nan ,ka duba kaga yadda ta ajiye jin kanta, gadara takama da komai nata akanka ... "an so what? "na aiketa ko nasata? "kai nifa banida lokacinta yakarasa shirinsa tare da barin d'akin ..misalin karfe 11 :00 na dare kiranta yashigo cikin wayar malik ya d'auka dan lokacin idonsa biyu yana kallon ball tare da su kabeer fu'ad ne dai ke kwance har yasoma bacci ,gaisawa sukayi sama sama "dan Allah malik ka had'ani da fu'ad "ok ya mike tsaye yayinda su kabeer suka bishi da wani irin kallo har yakarasa inda fu'ad ke kwance ya manna wayar a tsaitin kunnenshi ,sautin muryarta yasashi bude idanunsa ahankali yana duban malik dayayi saurin had'e hannuwansa guri daya yana rokonsa daya saurarera. lumshe ido kawai yayi batare da yace komai ba yaji ta sake mgn "fu'ad... dan Allah kayi hakuri da kiran danayi adaidai lokacin nan dole ce tasa hk gbdy na kasa runtsawa.. lip's dinsa ya ciza da k'arfi kmr zai huda, sannan ya kamkame jikinsa guri daya sakamakon jin muryarta, kai bazai iya cigaba da sauraronta ba, saboda zai iya shiga wani yanayi a dalilin jin muryarta da kuma ya birkita masa lisafi idanunsa ya rufe gam yana kawar da tunaninta tare da tunanin hanyar da zai bi ya musguna kmr yadda ta wulakanta malik..... "ina son mu had'u da kai gobe a coster coffee domin akwai bayanai masu matukar mahimmanci danake son mu tautauna da kai "gud dama tasamu ya furta acikin zuciyarsa, wanda a zahirance cewa yayi "okay. "nagode sai mun hadu gobe karfe biyar na yamma ya katse kiran batare daya tanka ba. bai je kmr yadda ta bukata sai dai shi yana tabbacin taje tagama tsamanin ganinsa ta wuce sai bayan kwana biyu malik ya matsa akan zance,sannan suka had'u a coster coffee dake awolowo waya gabadaya ta rame fuskarta tayi fayat kallo daya zaka mata kasan bata cikin natsuwarta da hankalinta tsawon minti talatin tana tsaye kmr ance ta juya taganshi sanye cikin riga green me adon pinky a gabanta, gashin kansa a gyare sai sheki yake" kallo kallo sukewa juna kafin daga bisani ya runtse idanunsa tare da zube hannuwansa duka cikin aljihun wandonsa muryata na rawa tace "ammmmm uhmmm sannu da zuwa gsky ka ..kayi kyau ..wannan ce maganarki mafi tsada ?ya fad'a tare da meida idanunsa ya runtse . "eh but ta mika masa karamar flower ga wannan kai na kawowa ,dan girman allah ka amsa koda kuwa bazaka amshi tayin abinda nazo maka dashi ba. a banzace ya kawar da flowers yasamu guri ya zauna yana juya mata baya zagayowa tayi ta zauna ta gabansa tana fuskantarsa "me zaka sha ice cream coffe ko shayi da madara? "da kyar ya fizgo numfashi kmr zaiyi mgn sai kuma ya fasa . Zuciyartace tayi tunanin watakilla zai bukaci coffee Dan hk take tabawa masu kula da gurin umarnin akawo masa coffee ta meida idanunta a kanshi tana satar kallonsa juyar da kanshi gefe yayi kmr baisan me takeyi ba tare da datse lip's dinsa .... Ganin ta kasa d'auke idanu akansa yasashi yi mata wani irin kallon wanda yasa kirjinta bugawa da karfi, sannan ya d'auke kansa dan shi duniya babu wanda yake jin yana matukar so kmr ita,amman ji da kanta gadara takama da kudin mahaifinta tare da wulakacin abinda tayi malik yasa yake jin kaunarta na neman riked'ewa ,a lokacin ji yake kmr ya tashi ya bar gurin sai dai kafin yayi hk sai ya wulakantata, sun jima tare da yin shiru kowanensu zuciyarsa na saka da warwara, fuad yaji shirun yayi yawa har sanda maikacin gurin ya ajiye tire me d'auke da cups guda biyu ya juya siririn tsaki yaja batare daya kalleta ba " yana da kyau kiyi abinda ya kawoki domin duk lokutana atsare suke babu wata dakika da take a wajena dazata zo face tana cikin tsari don haka kiyi gaggawa sannan ki takaita wajen maganarki dan banason mutun mai surutu ko dogon magana dan hk ina sauraranki . Me'ad tayi mugun tsaresa da idanunta tare da gyara zamanta tana saukar da numfashi" hakika so wani shu'umin abu ne wanda yake sarrafa duk wanda ya shigesa ,fu'ad da fari dai sunana me'ad kmr yadda na sanar maka a ranar farko da muka had'u muna zaune agarin nan tare da mahaifana ,ba sai na tsaya gaya maka waye mahaifina ba, kana ganinmu kasan muna da milloyoyin Kudi da bazasu lisafu ba sannan...."dakata dan Allah malama kafin ki cigaba da wad'an banzayen kalaman naki "jikeke ke wata jaruma ce ko me dakike zubo dogon bayanai hakan kmr agidan radio ? kanta ta girgiza tare da cewa "aa. "ok Kamata yayi ki yi magana me ma'ana da takaitawa kmr yadda na fad'a miki tun farko, "Ko kin d'auka da hkn da kika soma zaki birgeni ne ? "dan kin wani zo kina zancen dukiya, kin d'auka soyayya ce a ganin farko bari kiji ba wata soyayya irin haka kin siyo furi kin kawowa saurayi abu ko tsari babu sannan saurayin dasani minti kwanaki kalilan kika yi masa, ki kashe kudinki a wasu abu na kirki wata killa zaki iya samun lada.. Me'ad batayi musu ba tabishi da shu'umin kallo wanda ke bugar masa da zuciya sannan tayi wani irin murmushi duk abinda take bukatar nmj dashi, fu'ad ya tattara, aji kyau kamewa tare da sanin Ciwon kai shima ya juya ya kalleta wani irin shaukin sonta na dibarsa. " a zahirin gsky maganar dakayi tasa ilahirin jikina yayi sanyi ... " go straight to your point dan Allah malam.. tsura masa ido tayi gbdy ya d'aureta duk ta inda tayi tunaninsa ya zarta hkn cikin sanyi murya tace ".tun ranar farko dana d'aura idanuna akanka naji kamin, na dad'e ina tunani kmr bamu dace ba amman zaune da nake agabanka na tabbatar da babu nmj daya dace dani kmrka ,ka cancanta kazamo uban ya'yana shiyasa zanyi kok'arin domin naga na fayyace maka na kamo da matsanancin sonka, duk da nasan kaima hk ne dan na cika budurwar da dole nmj ya kalleni ya soni ,ba dan komai kodan kyawuna kudina da kuma tarin ilimi na, da iya kalamai duk da nasan a yanzu hk ka gama amincewa, amman zanso ka furta kanasona kmr yadda na furta maka, sannan ga sakon zuciyata danazo maka dashi takarasa mgnr cikin murya me sanyi ta mika masa wata karamar akwati , amman sam yaki amsa illa idanunsa daya tsura mata"ka amsa dan Allah ni fa sonka nake tsakani da Allah kuma a shirye nake dana aureka.. zan iya sadaukar da komai nawa akanka ciki kuwa har da rayuwata. Fu'ad yaji gbdy dry ta kufce Masa yayita dry abinda bai taba yi ba kenan dryr data bayyana hakorarnsa "ni kike so...? " yes ofcourse dole nasan zakayi mamakin kamata na furta ina sonka, amman kayi la'akari da so ba karya bane ,kuma kagaggen abu ne tunda kan Annabi adamu (a.s) kaga kuwa babu mamaki dan nace ina sonka. "Tabbas kin burgeni dan naga ala'mun kema jaruma ce da har kika iya kallon wad'an idanuwana kikace wai kina sona duk da kinsa ko acikin mafarki baxakiyi tunanin ni fu'ad zan amince da uzirinki ba, yayi shiru tare mikewa a fusace yasoma kok'arin barin gurin batare da ya amshi abinda ta miko masa ba da sauri tabiyo bayansa tana share gumin daya jikata mata fuska "ka tsaya dan Allah ko coffee din fa baka sha ba , tafiya yake tana biye dashi tare da kokarin son magana " yayi saurin daga mata hannu "karki dameni da banzayen kalamanki, I thought tun farko nace banso mgn dayawa ko? "Ummmm amman Dan girman allah ka tsaya ka saurareni bakasan yadda nake jin zuciyata . " yi min shiru tare da d'auketa da wasu maruka har guda uku ajere sannan yace "wawiya kawai kinyi zaton a banza zaki samu soyayyarta ko? Har da zuwa da shukun fure da akwatin zoben masoya, kina zaton zan amince da soyayarki ne saboda kina da kudi, iyayenki ma hk kisani wannan talakan daban yake da sauran talakoki koda nake talaka ina tabbar miki wutsiyar rakumi tayi nesa da kasa dan kije ki samu daidai dake mai kudi da duk abinda kike takama dashi . "fu'ad ka mareni a bayyanar jama'a dan nace ina sonka? "yes na mareki ko zaki rama ne? girgiza masa kai tayi kawsi ala'mun a'a, "ok na d'auka tak'amarki zai sai ki rama dakikiya kawai yana gama karasa wannan mgnr ya juya kai tsaye bakin titi yaje yana tsaida me adaidaita "kai zaka capitol road? ta biyosa da sauri "kabari na rage maka hanya nima hanyar zanbi "kai me adaidai wuce abunka tare muke dashi batare da bata lokaci ba me adaidaita ya wuce ya sake saida wani nan ma ta hana tare da fito da id card din acp aliyu ta nuna masa kana kuskuren d'aukarsa sai dai ka iske kanka amagark'ama nan take ya wuce yana cewa "kan wani dalili aiko bazam jawowa kaina ba. tafiya fu'ad yke tana binshi a baya tana rokonsa yazo ta rage masa hanya amman yaki saurarata har sukayi nisa da inda tayi parking din motarta tsaida me okada yayi kawai kafin tasoma dogon bayaninta tuni me okada ya wuce hk jiki a sanyaye ta koma tashiga motarta cikin tsananin damuwa da bakin cikin abinda fuad yayi mata ta figa motar aguje ta nufi estate dinsu kai tsaye tana wani irin mahaukacin gudu Wanda zai kayi mamaki matuka in idan akace macece take tuka wannan motar ta miliyoyin kudi ,wani irin sautin kidan soyaya ne ke tashi acikin motar tamkar zai tarwatsa motar. Yayinda samarin dake zaune a layi masu ji da kansu kuma yayan masu kudi irinta sai binta suke da wani irin kallo cikin bakinciki domin duk isarka duk iyawarka da iya wankanka baka isa tayi ma koda kallon arziki bane ballanatana kasanyawa ranka zata saurareka, hk ta ratsa har ta iso makeken gate din daya lullube ilahirin gidan hon daya ,tayi duka mutun ukun dake kula da get din suka taso suna kokarin bud'e mata get tare da jero mata sannu da zuwa amman babu wanda ya isheta kallo balle har ta amsa gabadaya idanunta a rufe suke . bayan tayi parking a inda aka tanada domin ajiye motocin ta fito jikinta a sabule still zuciyarta na mamaki tareda alajabin abinda fu'ad yayi mata wanda ko a mafarki bata taba expecting wani bil adama zaiyi mata ba da wannan tunani ta taka zuwa parlour mahaifiyarta, inda ta cusa kai tare da yin sallama aciki . Momy ta d'ago tana dubanta kallo daya tayi mata tasan tana cikin damuwa amman sai ta ajiye hkn akan aikin data fara ne, yasanya yanayinta ya sauya cikin sakin fuska momy tace " duk gajiyar hk? Naunayen ajiyar zuciya ta sauke batare datace komai ba illa kwanciya datayi akan kujera tace ".ganin nan dai momy kwata kwata bansa abinda ke damuna ba "allah ya kyauta momy tace kawai tare yin shiru kana ta sauke ajiyar zuciya momy tayi "ni kuwa me'ad ina son nayi wata tambaya . " kai momy zaki fara ko, kwana biyu kin barni nayi kiba amman yanzu zaki soma yi min zance safwan abinda kika san banason jin a halin yanzu.... Momy ta maso kusa daita tare da dafata "haba me'ad yanzu arayuwa babu wanda baya son cigaba ,idan kika aure safwan zaki samu cigaba arayuwarki da wata daraja ta Musamman.. "Kai momy meyasa zaki dinga yin irin wanna bayanan , ada kinsa duk duniya babu mutumin Dana fi muradin kasance dashi kmr sa, amman yanzu an wayi gari bana bukatar hk, momy kudi fa da kike ganinsu a yanzu nasan basa siyan kima daraja mutunci kwarjini soyayya ,dan hk momy ki daina irin wanna tunanin kiyi fatan na auri wanda zai bani farinciki ina son fuad ..... Duk da nasan takala ne tulis......kuma zan auresa duk da talau... Subuhallahi karki sake ki karasa wannan kalmar domin fiyayen halita ma yanemi tsari da ita dole ina son kiyi aure wanda duniya take damawa dashi wanda shi da mahaifinsa, suka maza masu abin hannunsu kuma bazan so ki auri Wanda bai kai ubanki kudi ba, sai wanda yafi shi dan haka a kullun adduar da nake miki kenan, ki janye batun yaron nan tun mahaifinki bai ji ba, idan dad dinki zai amince da aurenki dashi ni meye nawa aciki ?duk yadda nake son kiji dadi a gidan safwan hk zan hakura amman da zaki yarda ki amince kwarya tabi kwarya atsakaninku dana ji dadi sannan ki shiry tarban safwan yana kan hanyar dawowa . Me'ad ta ta'be baki aranta tana jin zata iya yaki da kowa akan fu'ad , ahankali ta mike ta nufi bangarenta inda ta iske ummi tana faman goge goge tayis din dake barandar . Ummi tana ganinta ta mike da sauri tana cewa "aunty sannu da zuwa, tsaki me'ad taja a maimakon ta amsa mata tayi shigewarta ummi tacigaba da abinda take yi aranta tana mamaki yanda me'ad ta d'auki duniya da zafi hk, duk da tun kafin tazo duniya anyi wad'an da suka fita wulakanta mutane amman babu wanda aka taba nunawa aka ce yayi nasara, balle itama tasanya ran wata rana zatayi nasara wannan girman kan nata ta sake ajiye numfashi tacigaba da aikinta. mmn sudais ce 💗💗💗💗💗💗 'YAN CINKI 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 ~NA~ *AYSHA A BAGUDO* ~DEDICATED TO~ MRS ADAM ( YAR MUTAN KAGARA) Page 51 to 52 .......kwance take akan makeken gadonta kiran italy tana kallon saman d'akinta ,sosai tayi zurfi cikin tunanin lamarinta da fu'ad tare da neman mafutar yadda zatayi, ahankali ta mike zaune ta koma gefen gadonta ta zauna tare da lullu'be kanta da hannuwanta duka sakamakon bugawar da zuciyarta keyi akansa ,tamabayoyi tashiga jerewa kanta d'aya byn d'aya "me yasa fu'ad yaki amincewa da tarin soyayyata garesa?"me yasa ya mareni akan nace ina sonshi? "Kodai Malik ya gaya masa abinda ya faru ne da hkn yazamo silar d'aukar fansa gareni ta hanyar disgani cikin bayanar nasi..."ga shan mari har uku ga rashin amincewa da soyayyata da bai yi ba... "yanzu ya zanyi da rayuwata ? Ta sake jehowa kanta tmby. " ina bukatar fu'ad arayuwata kuma zanyi komai akansa domin naga na mallakesa. wani abu ne data samu yazo wa zuciyata shine sake jin fu'ad datayi ajikinta yana yawo cikin jinin jikinta, tayi saurin goge hawayen da suka cicciko a kwarnin idanunta ya kawowa kuncinta ziyara, tasa hannunta ta dango d'igan hawayen tana kallo "yau itace ke kuka akan nmj?"nmj ma d'an talakawa wanda ba kowa bane...mikewa tayi ta isa gaban dress mirror dinta ta tsaya tana karewa kanta kallo daga samanta har k'asa "meye tarasa ajikinta kyau ne ko me da har fu'ad yake mata kallon ita bakowa bace? Ahankali take karewa cikar halitar da Allah yayi mata, tayi imani ko ita ta isa tasa fu'ad ya fuskanci lamarinta yasota fiyye da yadda take masa, sai alokacin ta lura da irin yadda gashin kanta data d'aure duk ya wargaje a saman kafad'unta adalilin tunaninsa ,hannuta ta kai kan wayarta tasoma neman layinsa, Amman yaki d'auka, kasa hakuri tayi tacigaba da kiransa har sai data yi masa kira yafi sau goma bai d'auka ba sannan ta nemi layin malik kira daya biyu malik ya d'auka, bayan sun gaisa tace "malik kuna tare da fu'ad ne ka had'ani dashi? " a,a ina gurin kallon ball, na dai barshi tare dasu kabeer a gida. "Okay idan bazaka damu ba zanyi maka wasu 'yan tambayoyi, amman ina bukatar jin gsky daga bakinka ."uhmmm ina sauraranki? "Ka ta'ba gayawa fu'ad abubuwa da suka dinga faruwa atsakaninmu da kai har zuwa kan marin danayi maka? sai daya ja naunayen ajiyar zuciya ya sauke da kyar sannan yace"alahakikanin gsky wasu Abubuwan yasani sai dai batu na mari bai sani ba, dan ban gaya masa ba, wani abu ne ya faru da har kikayi tmby? "Nothing ,Amman yanzu wani irin taimako zaka min malik akan abokinka?"na maseefar kwadaituwa da aurensa, ina son shi sosai kuma zan iya yin komai akansa matsawar zan sameshi, ka taimakawa rayuwata malik nasamu fu'ad, nayi maka alk'awarin zan maka komai ciki kuwa har da samammaka aiki a karkashin ikona tunda shi yaki amsa daga gareni ..? Numfashi da ajiyar zuciya ya sauke atare kana yace "zaki iya mallakar zuciyar fu'ad cikin sauki dashi kansa gbdy, bisa dalilin abu daya da sauri ta katse Shi ta hanyar cewa"meye shi malik ka fad'a meye shi zan iya yin komai akansa "meye zanyi fu'ad yasoni? "Bawani abu bane daya wuce kyautatawa, fu'ad na matukar son kyautatawa ,da km kyautatawa wanda ya cancanta most especial mara shi,ina tabbatar miki matukar kika kasance daya daga cikin masu kula da kyautatawa zaki mallaki zuciyar fu'ad cikin sauki batare wata matsala ba, ni kaina ina miki sha,awar aurensa domin idan kika sameshi amatsayin miji ina me tabbatar miki zaki yi alfahari samun miji kmrsa "shikenan malik nagode sosai da shawararka, km InshaAllahu zanyi kok'arin naga na kasance cikin masu kyatatawa mutane, gobe karka manta kasameni a oil and gas. " InshaAllahu bazan manta ba Na gode sosai Allah ya mallaka miki zuciyar fu'ad "ameen nima nagode da wannan adduar taka sai mun had'u goben ta katse kiran ta koma gadonta ta zauna inda zuciyarta take bata umarnin me zai hana ta tura masa ko da sakon text message ne tunda yaki d'aukar wayarta hannuwanta duka tasa ta rike wayar tasoma rubutu sako kmr hk. _Assalamu alaikum ina fatan kana cikin koshin lfy, daman na turo maka wannan sakon ne domin na k'ara baka hakuri bisa ga kalamaina na d'azu danayi amfani dashi ,wanda sukayi silar 'bacin ranka har ka mari kyakyawar fuskar matarka, azahirin gsky naji babu dadin abinda kayi min ,sai dai tarin soyayyar danake maka ta hana rashin jin dadin nawa tasiri ,ina sonka fu'ad har bansan yadda zan misalta maka ba, ka daure ko ba yawa nima kasoni kwatankwacin yadda nake sonka I really sorry for what I did ..sai da safe daga mai sonka Me'ad Ediris Takai_ Tana tura masa ta koma kan ganta, ta kwanta lamo tare da runtse idanunta bawai dan tana jin bacci ba, sai Dan shaukinsa dake dibarta ,gudundune jikinta tayi, lokacin da tunaninsa ya yawaita ajikinta dan har ta fara hango sunyi aure dashi da yadda yake sarrafata akan bed gurin aika mata da zafafan romancing dinsa masu birkita 'kwal'kwaluwa. A kwancen dayake a d'akinsu sanye cikin jallabiya fara sol hannunsa rike da wayarsa yana brownsin sakonta yashigo ,amman bai bi ta kai ba yacigaba da abinda yake, km ko bayan daya gama bai duba ba yayi kwanciyarsa, ranar dai me'ad bata samu ta runtsa ba duk inda ta juya fu'ad take ganin da hannunsa dake yawo a ilahirin jikinta . Washegari tun 7:00 malik ya tashi yayi shirinsa ya iso oil and gas, sai dai bai iske me'ad ba dan bata karaso ba tukun, yasamu guri ya zauna zaman jiranta, sai gurin takwas tashigo cikin hadaddiyar motarta kiran toyota Camry ta gabansa ta wuce amman bai ganta ba saboda ba'a cikin irin motocin daya saba ganinta ciki bane, bayan ta isa office dinta da kmr minti 2 tasa ayi kiransa,cikin wasu 'yan mintuna malik ya bayyana a office dinta cike da girmama ya gaisheta, ta amsa da kulawa sannan ta nuna masa gurin zama da hannunta kana ta bukaci takardunsa ,batare da 'bata lokaci ba ya mika mata, bayan ta duba ta mike tsaye "kabani minti 20 "ok badamuwa ranki ya dade. Kai tsaye office manager ta nufa domin neman alfarma. Acikin awa daya kacal malik yasamu aiki a ibadan karkashin kulawar me'ad amtsayin wanda zai dinga kula da ficen da shigen kud'ad'en kasancewar accounting ya karanta Lokacin da wannan labarin yasameshi a zaunen dayake a office dinta, yayi matukar murna da farinciki, godiya ya dinga yi mata kmr zai mata sujada, aikin daya d'auki sama da shekaru biyar yana nema sai gashi yasamu acikin awa daya nigeria kenan kayi karatun kagama sai kana da hanyar zaka samu aikiyi.. "Kabar min godiya hk nan ,ka godewa Allah daya nufeka dasamu, sai dai shawarar da zan baka ,ba wuce ka rike aikinka da mahimmanci ba ,domin mutane dayawa irinka na can suna nema kasa danaka basu samu ba , sai abu nagaba ka taimaka min nasamu fu'ad..... "Angama ranki ya dad'e InshaAllahu zanyi iyakacin kok'arina akan lamari, "ok ranar Monday zaka soma aikinka yanzu zakayi dropping account number dinka, akwai wasu kudin daza'a tura maka domin siyan sutura. "Nagode nagode!!! ranki dad'e wallahi har bansan irin godiyar da zan miki ba ,hk suka rabu malik na farinciki samun aiki ita km tana murnar zata samu fu'ad cikin sauki tasan idan yaji itace tasammansa aiki zaiyi farinciki wata killa adalilin hk burinta ya cika. Koda malik ya jewa fu'ad da labarin samun aikinsa ta hanyar me'ad, yace "tayi kokari sosai, sai dai kajira ranar zuwan wulakanci daga gareta, domin wannan aikin daka amsa daga hannunta daidai yake da ka amsarwa kanka wulakanci ne da damuwa, ni dai babu ruwa duk abinda yaje ya dawo sai dai ya kare akanka. "Wace irin magana ce hk fu'ad? " gskyar lamarin nagaya maka sai kayi taka tsantsan "Naji ni dai ka min addu'a shi nafi bukata daga gareka bawani dogon sharhi ba ,sai agame da zance me'ad , yarinyar nan ta damu da lamarinka dayawa , ka duba kagani kyau ilimi nasaba duk tana da, uwa uba gata da zuciyar taimako "ai ta taimaka maka dole ka fad'I hk mana , ni dai ina umartarka ka takaita maganarta anan dan kadameni da zance ina da abubuwan yi. Malik yayi dry sannan yace "ni da zakabi shawarata da ka amince ka aureta komai cikin sauki zaka samu aikin ma dake bulayin nema ba sai kaje ba, kana daga kwance za'a yi maka komai."to baza'a d'auki shawarar taka ba ,idan ka damu da lamarinta har hk ka aureta mana ,ai daman kana sonta. "Ina sonta bata sona kai take so, da kace ni ta nuna tana sona wallahi ina tabbatar maka babu abinda zai hanani aurenta,"yanzu ma zaka iya gwada sa'arka yana karasa fad'ar hk ya wuce ya bar malik tsaye yana kallon bayansa. ********* Duk abinda me'ad zatayi domin shawo kan fu'ad tayi, tabi abokansa da duk wani wanda tasan suna muamula, duk inda tasan zata ganshi kafafunta na gurin amman ko kallo arziki bata isheshi ba ,asalima yana ganinta zai bar gurin yakama gabansa, acikin tsakankanin wannan lokacin ne labarin rashin lfyrsa ta risketa, bata tsaya sanya a gwiwa ba ta nemi malik da yayi mata rakiya, shine yayi mata jagora har gidansu inda ta tsaya kallon ruba'b'ben gidan dake shirin zubowa "kace na ne gidansu malik? "Kwarai kuwa nan ne gidansu "kina mamaki ne? Shiru tayi batare datace masa komai ba illa tsurawa gidan idanu datayi "yanzu anan fu'ad dinta ke rayuwa tun tasowarsa? A she fili tayi zance batasani ba , "Ki daina mamaki ranki ya dad'e nan ne gidansu kuma inda yayi rayuwa acikinsa idan kin mutsu ne mushiga Kigani d'aki na d'aya na biyu nan ne d'akin kakarsa. Tana gama sauraransa ta juya ahankali Jikinta matukar a sanyaye tashiga cikin parlour gidan me cike da duhun tsiya ,hannunta rike da karamar jakarta da kyar take ganin inda take sanya kafafunta duk rana ce ba dare ba ,yayinda malik ke biye daita da manya manya fararen lododi guda biyu ,taja ta tsaya abakin kofar shi km malik yayi sallama tare da kutsa kanshi cikin d'akin sannan itama tayi sallama tashiga "a'a Malik kai ne hk da rana tsaka ?"to marhabun lale ku karaso ciki mana inna ta fad'i hk tana mai mikewa ta shimfid'awa me'ad dadduma ,Dan shi Malik tuni ya ajiye lododin hannunsa yakarasa inda fu'ad yake. Duk wanda yasan d'aki marasa shi hk d'akin yake bawani shararrun kaya ne acikinsa ba illa wani D'an madaidaicin gadon, sai kayan miyar dake ajiye gefe guda mai nuna alamun na siyarwa ne, gefe daya km wata katuwar akwati ce ajiye kallo daya tayi wa d'akin tasan d'akin marasa shi ne kmr yadda gidan yake sai da ga dukkanin Alamu yana samun kulawa ta hanyar gyara da tsaftaceceshi . cikin ladabi tamkar ba ita ba, ta durkusa har kasa kanta a sunkuye cikin sanyi murya"inna barkanmu da warhk ya gida da me jiki.. inna ta amsa cikin sakin fuska da kulawa batare datayi tunanin inda tasanta ba saboda ganinta tare da Malik . ahankali me'ad ta juya inda fu'ad ke zaune Wanda ke aikawa malik da uwar harara sanye cikin gajeren wando da T shirt fara sol gashin jikinsa kwance luf Luf tmkr na jarirai ,ta gaida uban gayyan da ko kallon inda take bai yi ba " ina yini ya jikin ? abunda me'ad ta fad'a Kenan taja bakinta tayi shiru. ya d'an d'ago kad'an yace lfy atakaice shima dan inna tayi masa ala'mun da kafarta ne ,me'ad ta sake yin wani kayataccen murmushi sannan tayi shr. Malik yayi gyaran murya sannan yace "inna ga surakarki budurwar fu'ad tazo duba lfyrsa ..inna tayi dry "kace kishiya ce shine har da bata gurin zama ,shi kuma jairin sai wani cika yake yana batsewa kmr ba yanzu nagama fama dashi gurin shan magani. Me'ad ta sunkuyar da kanta alamun kunya .malik yace " har yanzu fu'ad bai bar gudun magani? " ina fa har tsoron rashin lafiyarsa nake saboda hkn. Mead ta dago da niyyar ta saci kallonsa ,karaf suka had'a idanu atake kirjinsu ya buga, tayi saurin d'auke idanunta Dan bazata iya cigaba da kallon surar jikinsa inna na gurin, sai dai muryarta a sanyaye tace "inna me yasa aka barshi a gida ba'a kai shi hospital ? "Wannan za'a kai hospital inna ta nuna fu'ad daya yatsina fuska alamun damuwa inna tacigaba "mutumin dake gudun magani balle allura idan kika ganshi kuzarin jiki kawai garesa amman laulauyi garesa sai ki kishirya, murmushin jin dadi mead tayi ganin tasamu karbuwa agurin inna . sun jima shr sannan inna ta mike tayi waje ,shima malik yace "bari nabawa masoya guri, tsaki fu'ad yayi batare daya tanka masa ba . Yana fita fu'ad ya gyara zamansa cikin rashin jin dadi fitar da inna da Malik sukayi dan ba'a son ransa ba, dan babu yadda zaiyi ne. me'ad ta matso zuwa inda yake ta tsuguna tare da cewa "fu'ad... Sam bai kalli inda take ba hasalima cigaba da danna wayarsa dake rike a hannunsa yayi, tayi kusan minti uku sannan tayi kokari kai hannunta da zumar Kwace wayar hannunsa ya kallota a fusace tana dakatar daita da manya idanunsa domin bayason kusancinsu a yadda yake Dan shi kadai yasan abinda tafiya acikin jikinsa tsawon minti 2 yana tsare daita da manya idanunsa kafin daga baya yasoma mgn kasa kasa "karki wahalar da kanki da wata banzar kalmarki ko gaya min uzirin abinda ya kawoki,domin ina tabbatar miki sam banyi murna ganinki kusa da innata ba ,ni a bangarena bai zama lallai dole sai na soki ba ko yin wata muamula dake ba, dan haka ki daina wani rawar kafa dan sam ba birgeni zakiyi ba, dani bakowace mace ce zata iya yaudareni ba .. me'ad datayi masa kuri da idanunta tana kallonsa ta saukar da numfashi tace" na jinka fu'ad sai dai abinda nake son kasani tunda nice naganka kuma na aminta da kai, zan iya d'aukar komai tare da shanye duk wasu kalamanka gareni sannan zanyi komai dan ganin na mallakeka amatsayin uban ya'yana koda dukiyata zatakare da numfashina.. wani irin kallon banza fu'ad yayi mata irin na sama da kasan din nan sannan yace "iska na wahalar da mai kayan kara . "Ina tabbatar maka wannan iskar bazata wahalar da mai kayan kara ba ,domin zamu kasance cikin inuwa daya koma nace bargo daya . tana gama wannan mgn ta juya cikin fushi tayi ficewarta shi kuwa fuad daya bita da kallo ya saukar da numfashi cikin sanyin jiki ya mike daga inda yake zuciyarsa cike da tunaninta tabbas tana matukar burgeshi muttaka, har yana jin idan bai sameta ba komai zai iya faruwa dashi . bayan tafiyarta tashi yayi ya sake yin wanka yasanya kananan kaya marasa nauyi ya tsaya fesa turare inna tashigo hannunta rike da bakar leda mai dauke da ruwan roba da Malta Amman taga wayam babu yarinyar dazu babu alamunta cikin sauri tace " kai fu'ad ina yarinyar da malik? Kafadunsa ya daga mata alamun bai sani ba sannan yasanya kai yayi waje inda machin dinsa ke parke. tuki take cikin 'bacin rai tana ciza yatsan hannuta gbdy ta kagara taje gida domin ta samawar kanta mafuta akan lamarinta da fuad wani irin taka birki tayi dan karfi gudun kada ta buge abinda tagani a gabanta. a matukar fusace ta fito daga cikin motarta tayo waje inda tsohuwar take tattakawa ahankali saboda tsufa datayi Dan har ta d'an rankwafa "haba matar nan wannan, wani irin mugunta ce hk wato ke kin gama cin kuruciyarki A cikin tsiya shine zaki ja min masifa wato idan na bugeki kika mutu a kamani ko? to in har hk kike nufi ki sani idan na bugeki na kad'e banza dan dake da kuda daya ne agurina dan hk ki matsa kafin nabi ta kanki da mota.. tsohuwar ta d'ago da kyar ta kyalleta tace yarinya kiyi ahankali ahankali domin an yi wasu kafin ke kuma basu ta'ba cin riba ba kinga kema baxaki ciki riba. me'ad taji wani irin 'bacin rai ya turnukota sai dai lokaci daya shawarar da malik yabata ya fad'o mata "fu'ad na matukar son kyautatawa da kyautatawa marashi kenan irin wannan kyautatawa yake nufi? "bugu da kari mgnr tsohuwar ta kashe mata jiki murus,Dan HK tasoma nadamar abinda ta aikata da farko ta matso sosai kusa tsohuwar tare da rage sautin murya kasa sosai"inna dan girman Allah kiyi hkr nayi nadamar abinda na aika miki, ni kaina bansa abinda yasa wani lokacin nake reacting hk ba, amman kiyi hkr idan magana ta 'bata miki ,muje na tsalakar dake ta kai hannu zata ta'ba tsohuwar tace "dama kin bar shi yar nan zan iya tsallakawa, sai dai naji dadi da kikayi saurin gane kuskuren abinda kikayi ,ita duniyar ma guda nawa take?" ku dunga d'auka da mai kudi da talaka duk abu daya, saboda Allah da yayi mai kudi shi yayi talaka ba kuma dan baya son shi ba. "Haka ne inna na gode sosai amman kiyi hkr kibarni na taimaka miki tayi saurin komawa cikin motarta ta kirgo kudi wanda zasu kai kimanin dubu goma ta dawo inda tsohuwar take ta riko hannuta tasanya mata kudin "inna ki amshi wannan dan Allah karki aa"kai yar nan har da wata hidima to nagode kwarai da gaske Allah yayi albarka, Allah yayi miki abinda kike so Inshaallahu zaki gama da duniya lafiya. "Ameen inna na gode. fu'ad da fitowarsa kensn abun ya faru akan idanunsa duk da bai ji tautaunawarsu ba ,Amman ya ji dadin taimakon datayiwa matar har sanda ta tsallakar daita dayan bangaren tsohuwar na dariya tare da d'aga mata hannu ta koma tashiga cikin motar ta figa a guje yana kallon sannan ya taka mashin dinsa yacigaba da binta abaya batare da tasani ba ,har inda ta sake tsayawa saboda hango wata makauniya rike da yar jagoranta wace bazata wuce kamin shekara takwas ba ta mika musu sadakar dubu daya bayan ta tsaya sun tsallaka abu kmr wasa hk ta dinga taimako mutane wanda abin yacikasa da mamski "daman tana da zuciya irin hk me kyau ?"gsky idan har tana da irin wannan halin na taimakawa marasa karfi ta cancanta tazamo abokiyar rayuwarsa, adaidai jection din bankole suka rabu shi yayi titi dopemu road ita kuma kai tsaye gida ta nufa inda ta iske sunyi bakin da suka dade suna expecting zuwansa, wato safwan almustapha maitama daga kasar hollond, mahaifin safwan baban mutun ne a kashen duniya gbdy ,sannan me gidan mahaifin me'ad ne a can baya kafin yayi rites . Safwan ya dawo daga kasar Holland ne da niyyar abubuwa guda biyu, na farko cima burin auren mead daya kwalafawa ransa tun shekarun baya, sai abu na biyu cigaba aikinsa amatsayin shugaban shashi na kasuwancin Nigeria. jin ana jera mata sannu ne yasa mom dinta yin saurin fitowa dan tayiwa yar tata gargadi kada ta kawo musu wargi . me'ad ta kalli uwar cike da mamaki "ni wai momy meyasa kike min hk ne?" narigada na gaya miki na canza mind dina akansa yaje gaba ya auri matarsa ni matar fu' ... momy tayi saurin rufe mata baki "karki sake me'ad kiyi ganganci, karkiyi wasa da damarki,domin damar mutun sau daya take zuwa masa arayuwa, ina shawartaki karki bari taki ta subuce miki. me'ad tayi wani irin murmushin sannan tace, karki damu momy da subucewar wannan damar ni dai fu'ad nake so simple as that tana gama fad'ar hk tashiga cikin parlour'n mahaifinta wanda sai bakinsa masu mahimmanci yake tara acikinsa ,ta samu gefe daya ta zauna "dad sannu da zuwa ya hanya ? mahaifin safwan ya amsa da kulawa sannan ta waiga inda safwan wanda tun shigowarta idanunsa ke kanta yana kallonta saboda wani irin azababben kyau dayaga takarayi masa sai dai ta rame kad'an Wanda bai San dalilin faruwar hkn ba ,sautin muryarta ce ta dawo dashi "yaya ina yini? ya lumshe idanunsa na second biyu sannan ya bud'esu fess akanta kanwata kin yini lfy? tayi masa wani irin kallo mai bugar da zuciya sannan tace lfy atakaice. sun jima a parlour'n dad dinta ya dubeta yace ki kai yayan naki lambu ya huta mana , babu mutsu me'ad ta mike shima yabi bayanta cikin matsananci farinciki yayinda ita kuma ba'a son ranta ba Dan dai babu yadda zatayi ne. wani parlour'n ta kai shi al wanda duk gidansu babu irinsa an maserfar zuba abun duniya agurin ,an zuva komai wanda me rai yake burin mallaka. bayan ya zauna tasa aka gabatar masa da abubuwa sha kmr yadda tasaba sannan ta sake tashigowa batare da wani abu ba ta zauna shiru batace masa komai ba gbdy sai yaji baya bukatar cin komai dake gabansa illa matsowa da yaayi ya saita bakinsa daidai kunneta "ina sonki mead dayawa amman banji dadin yanayin dana ganki ba at least kinsa ina bukatar kulawa daga gareki. .tace har da gaske kana sona har yanzu ka mayar da akalar soyayyata ga wata in har kana son farincikina . A matukar firgice ya tsura mata ido yana kallonta Kafin daga baya yace "no no hkn ba zai yuwuba "saboda me ?"saboda bana sonka yanzu sannan karka kazamanto me yawan wahalar da kanka wajen sake tadda zance aurenmu domin ahalin yanzu zuciyata bata gareka , ta kamu da soyayyar waninka ,da sauri safwan ya kalleta cike da matsanancin mamaki abinda take fad'a masa yayi shiru ya kasa cewa komai illa jikinsa dake rawa.. "kaji abinda nace amman har yanzu ka kasa Cewa komai, ko magnata ta kurmanta da kai ne? . "ko daya kawai mamaki kikabani shin kin manta matsayina a gidan nan dama duniya gbdy? "sam maganganunki a yau babu girmamawa balle nuna tarbiya, "dan Allah ki gyara maganarki sam banji dadin yadda kika min ba saboda har yanzu ina sonki me'ad kuma banga abinda zai hanani aurenki ba matukar ina raye. da sauri me'ad ta kalleshi cikin mamaki tayi wata dry na rainin hnkl " amman baka kyautawa xuciyarka ba sannan bakayi tunani me kyau ba, karkayi takamar dan mahaifinka me gidan mahaifina ne bazai sa nagaya maka abinda ke cikin zuciyata ba, idan kuma kayi kuskuren aurena girmamawa zai yi wahala ka samu romon da maxa dayawa in sunyi aure suke samu ba sai nagaya maka ba dan nasan kaima agidanku akwai irina safwan kake ko wa kake ;? ina son nagaya maka wallahi ban ta'bawa yiwa kowani mahaluki karya ba ko shi waye to kaima bazan ma karya ba, safwan har ka aureni bazan maka biyyaya aure ba sannan bazakayi min kulle ba, duk abinda nake so shi zanyi agidanka,kuma ba lallai ne na dinga maka girki ba idan taka ma har Wanda nake so sai na kawoshi gidanka kuma nayi duk abinda nake so dashi ,idan har kaga zaka iya to kana iya turo a karasa mgnr aurenmu da kai ,idan km ka janye niyyar aurenka akaina sai mucigaba da muntuncinmu , tayi shiru tare da mikewa tayi hanyar kofa, har ta zira kafarta daya a kofar parlou'n sannan ta tsaya batare data jiyo ba tace zaka iya fitowa ka tafi tunda na sallameka .. tana gama fadar hk ta juya shi kum safwan da bita da kallo sannan ya saukar da numfashi ckin sanyi jiki ya tashi ya nufin parlour'n zuciyarsa cike da tunaninta tabbas yasan yana son me'ad so kuwa me tsanani har yana ji aransa matukar bai aureta ba tabbas akwai Matsala dan wannan abun datayi masa mugun burgeshi tayi shifa bai ga dalilin da zai bar wani me'ad dinsa ba alhalin yana raye bai mutu ba ,babu wannan nmj a duniya kuma kowaye sai ya nemoshi da karfinsa da dukiyarsa . ita kuwa me'ad byn tafiyarsu ta shige part dinta ta sake wanka tasanya kaya marsa nauyi sannan ta fito paloun mom dake zaune ita kadai tana kallon labarai a CNN jin takun me'ad tana saukowa daga step " momy kallon kike ke kad'ai a parlour'n ina suhailat ? momy tayi dry ai daman yanzu zan kiraki dan ina son naji yadda kuka yi da safwan. me'ad tayi saurin kallon momy tace "waye km hk an? da sauri momy tayi saurin kallo me'ad cikin mamaki da tsoro, cike da in ina momy tace " me'ad me ye nufinki? batare da ta kalli momy ba tace "nufina bawai wuce ya nemi wata ya aura ba danni har abada ta fu'.. "yi min shr me'ad kada ki meidamu kanana mutane tare da meida hannun agogo baya dan wallahi tallahi baki isa ba a wannan karon mune muka haifeki dole muyi duk yadda muke so dake wallahi baki isa kiyi mana mugunta ba dan hk ki meida hankalinki cikin jikinki tun kafin mahaifinki yaji . "momy kingama ? me'ad ta fad'a batare data kalleta ba, bata jira abinda momy zata ce tacigaba "mom ni babu ruwana da dady yasani dan nafi son hk, kowa fa takasan yake yi yanzu dan hk baxaku matsamin ba, dan kawai kun kawoni duniya, ku dai yi hkr zanyi shawara da zuciyata idan na rarrashita akan fu'ad taji zata iya rabuwa dashi fine then zan iya auren safwan ,amman idan taki hakura sai dai kuyi hakuri, duk yadda nayi da zuciyata zan gaya muku tana gama fadar hk ta mike zata fita momy itama ta mike cikin bacin rai da fushi ta riko hannunta har sai datayi kara. "momy cire min hannuna zakiyi dan kawai banason safwan ? momy dataga ala'mun fa yarinyarta tayi zurfi sai ta kwantar da murya "kiyi hkr me'ad ki zauna muyi mgn nasan zaki fahimci mamanki. me'ad ta kurawa momy ido tana saukar da numfashi momy "kema kiyi hkr ki barni da zabin raina sannan mgnr da zamuyi ,mayi idan na tashi daga bacci tana karasa fadar hk ta mke ta koma samanta momy tabita da kallo cikin takaicin domin ita kad'ai tasan bala'in daza'a yi idan mahaifinta yasan tana soyayya da talaka abunda shi ya tsana kenan had'a hanya da talaka arayuwarsa . me'ad kuwa gadonta ta haye tayi kwancinyarta tare da rufe idanunta fu'ad fess take gani acikin idanunta har ga Allah wani irin so take masa me tsuma zuciya da wuyar bari ..hk tayita tunaninsa har bacci ya dauketa bayan ta tashi momy tashigo d'akin tayita rarrashita amman furrr taki yarda da zabin iyayenta "momy tun farko banason safwan ke dady kuka matsa min ,ta yaya yanzu nasamu wanda nake ku nemi hanani aurensa. "Ba hanaki aurensa mukayi ba ki tuna alkwarin dake tsakani Dan allah yarinyata ki duba lamarin nan "momy kema uwa ce nasan kinsa abinda ake kira da soyayya tunda nasan ba hadaku akayi da dady ba, ku kuka ga junanku ,ina rokonkanki momy ku barni da fu'ad wallahi akansa zaku iya rasa takarasa mgnr tana kuka . ..tsakanin uwa da 'ya tuni itama ta sauko taji zabin diyarta yayi mata, zata bata damar ta auri zabin zuciyarta.. Ranar da kyar safwan ya runtsa kwana yayi yana zubawa cikinsa giya da tunanin abun yi, "tabbas yakamata ya d'auki mataki nemo kowaye ke kokari kawo rayuwarsa nakaso ,tun da sanyi safiyya ya baza yaransa domin bincike akan wanda mead take so . Tashin farko bincike ya zo masa akan yadda bai so ji ba ,domin duk wani abinda ya danganta da fuad da rayuwarsa sai daya zo masa daki daki ya sha mamakin" wai Dan talakawa me'ad take kokarin neman gujewa aurensa ,aransa yace" idan kinsa wata ai baki San wata ba ,nasan dai babu ta yadda za'a mahaifinki ya yarda ki aureshi, balle shi karan kanshi yaron bai sonki ,gbdy safwan yazaba yaransa a gari domin cigaba da kawo masa rahoton komai akan fu'ad. ****** ranar monday da misalin karfe 1:00 na Rana kabir yazo gidansu fu'ad domin zuwa office din Alhaji Abubakar aminin mahaifinsa Wanda zai samarwa fu'ad aikin da kaninsa ,a shiryensa yake zaune a kofar gida yana zaman jiran karasowar kabir yana hangosa yashiga cikin gidan inda yakewa inna sallama "inna mu za fita akan zance neman aikin kiyi min adduar samun nasara kansa ta dafa "InshaAllahu zaayi nasara zaka samu wannan aikin ina jin hk ajikina sai dai Wani tsananin rabo"allah yasa ni na wuce, "a dawo lfy Allah ya tsare, "ameen ya fice daga dakin . kai tsaye company da alhj Abubakar ke tafiyar da aiki suka nufa akan lefan din fu'ad suna isa suka iske jama'a wanda dayawansu neman abunyi ya kawosu, batare da bata lokaci ba suka nufi office Alhaji Abubakar inda suka iske shi yana sallah sai mataimakinsa sukagani suka gaisa ya nuna musu gurin zama "ku zauna ga guri nan ,suka zauna har zuwa sanda ya idar yakaraso garesu inda kabir yayi saurin cewa dady barka da Warhk "a'a kabir har kun iso?ya fad'i hk tare nufar hanyar office dinsa dake cikin wanda suke zaune da sauri kabir da fu'ad suka mike sukabi bayansa atare suka shiga kabir yasamu guri ya zauna akan daya daga cikin kujerun gurin tare da jawa fu'ad shima ya zauna "ai kuna da sa'a duka takardun mutun biyu din da ka kawo sun samu aiki,Amman D'an bani minti 2 ya fadi hk sakamakon wayarsa dayaji ta d'auki kara ya zagayo ya zauna mazauninsa tare da d'aukar wayar ya manna kunnesa abinda yaji ne ya kusan bugar masa da zuciya "safwan almustapha maitama ne ke mgn da kai daga nan office din jakandancin na kasuwancin Nigeria, naji ance wani mai suna fu'ad yazo neman aiki gurinka ko ba hk ba ? "Haka ne ranka ya dade. "To kasani bashi aikin da zakayi yana daidai darasa kujerarka da matsayinka gbdy. .." a,a ranka ya dade ba zayi hkn ba InshaAllahu yadda kake so hk zaa yi,"idan kabi umarnina ka tsira da aikinka kit safwan ya kashe wayar . shi kuma alhj Abubakar yashiga goge gumin dake keto masa, bayan yagama goge gumi ne ya fuskanci kabir "yauwa kabir batun aikin abokinka a gsky babu shi a halin yanzu ,Dan bazai samu aiki akarkashinmu ba sakamakon wasu dalilai da ba sai na bayyana maka su ba . "Kmr yaya dady?"da fari kace zasu samu ,yanzu km ka..fu'ad ya dafa kafad'arshi yana mai mikewa tsaye "karka damu abokina da rashin samunka aikina ka d'auka komai mukaddari ne bani da rabon samun aiki anan ne... yana karasa fad'ar hk ya juya. "Amma fu'ad...."nace karka damu kayi facing din na abdulrashid alhj Abubakar da zuciyarsa ke cike da matsanancin tausayin fu'ad yacigaba da mgn sai zance aikin kaninka shi yasamu aiki, maiduguri zashi ,zuwa wata mai zuwa ,wannan aikin mutane dayawa na nema Amman acikin sa'a yasamu kad'an jira takardar tabbatar da samun aikin domin zata iya zuwa a kowani lokacin . fu'ad yataso daga inda yake zaune yana tunanin dayasa zancen samun aikinsa ke neman shan ruwa, ya kwankwasa glass din office inda kabir ya d'ago yana dubansa cike da tausayawa, alama yayi masa da zaije kasa ya jirasa, shi ma da kai ya amsa da badamuwa . Fu'ad ya sauka kasan maikatan ya isa inda yayi parking din maching dinsa yana waige waige a gurin hannunwasa duka zube cikin aljihun wandosa ,karaf idanunsa ya sauka Akanta tana tuki cikin karewa, itama tun daga nesa ta hangosa tayi saurin ware idanunta bakinta na furta" fu'ad Dina ...... sai dai tun kafin takaraso inda yake taga ya haye maching dinsa tare kunnawa yayi gaba aiko itama tabishi abaya.......... Mmn sudais ce 💗💗💗💗💗💗 'YAN CINKI 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 ~NA~ *AYSHA A BAGUDO* ~DEDICATED TO~ MRS ADAM ( YAR MUTAN KAGARA) Page 53 to 54 .... gudu yake sosai akan titi tana binsa abaya ,yasamu ya karya wata kwana wacce zata fitar da mutun kai tsaye oshodi Express , anan machine dinsa ya tsaya cak yaki tafiya, sai ma hayakin dayasoma fita daga cikin salansar , dan hk ya sauko daga kan machine din ahankali tare da tsaida shi yana dudubawa, har sanda ta iso garesa tayi parking had'e da fitowa daga cikin motarta zuwa inda yake " abun yayi min kyau ba kad'an "gashin nan cikin minti uku kacal nazo na sameka ,"me km yasamu machine dinka ta tmbyta tana dukursowa ta karkashinsa tana kallon fuskarsa cike da matsanancin kaunarsa ,ya mike tsaye tare da rike kugunsa da hannunsa d'aya yana waige waigen ta inda zai samu makaniki kusa ganin babu alamun hk yasa da dungule hannunsa daya ya naushi iska yana furzar da huci mai zafi daga bakinsa ,ita kuma ta matso kusa dashi tana fuskantashi tace"wato fu'ad lokaci yayi da zan baka gudumuwa ,ta hanyar ajiye wannan machine din naka, mai kama Dana masu ACA'ban abbatuwa . Yana jinta sai dai yayi mata banza batare da ya ko kalli inda take ba har sanda ta maida idanunta akan machine din "uhmmmmm Allah sarki machine dinmu kenan "ko tun yaushe kake dawainiya damu? Kana Ta matso kusa dashi har suna iya shakar numfashin junansu "kana ji ko fu'ad,Kafin yanzu yaci ace ka kalli duniyar wata ,duba yanayin morar machine dinka dakayi, tazarar dake tsakanin duniya da wata Mil dubu biyu ne da talatin da biyu da d'ari takwas da sha uku ,ta sake matso shi sosai tamkr zata shige jikinsa wanda hakan yahaddasawa zuciyarsa bugawa da karfi yaja baya kad'an "meye hk kike kuqarin yi ? Sharesa tayi kmr bata manufarsa ba tace "bari na tmbyeka wani abu ra'ayinka ne hawa machin ko me ? "kinsan acikin duniyar rayuwata ba son takura balle shishigi, Dan hk ki kama gabanki kawai ya wuce yasoma tafiya dan yasan machin dinsa ya rigada ya tashi daga aiki ,da sauri ta biyo bayansa "wai abun yayi maka rashin dadi ne ko me daka wuce kabarni tsaye? Sake banza yayi daita yacigaba da d'aga kafafunsa batare daya kalli inda take ba "kana jina ko zan sai maka lafiyayyiyar mota kiran zamani saboda kafi karfin ka dinga hawar wannan kwarababben machen din , shi km wannan machine sai ka kyautar dashi amman kafin nan zan saka kanikawa suzo su d'auka domin gyara . yayi saurin juyowa yana fuskantarta har hucin numfashinsa ya bugi hancinta ,tayi saurin lumshe idanunta kirjinta na mahaukacin bugawa kusan minti biyu suna tsaye suna kallon kwayar idanun juna sannan a kasalance muryarsa ta fito "anan garin aka haifeni na tashi na girma, nasan kowani lugu da sako dake nan unguwar, akwai makanikai idan ina bukata zan nemesu da kaina, "batu na mota km kibar abunki saboda fu'ad bai bukata komai daga gareki . "no karkace hk mana bayan da dukkanin alamun rayuwarka na bukatar ha.....a matukar tsawace ya katseta ta hanyar cewa "Kimin shiru anan kafin na d'aukeki da maruka ... "Mari fa kace?"kina mamakin faruwan hknne ? Yayi mata tmbyr yana tsare gira ," Tayi saurin girgiza kanta alamun a,a "ok na d'auka kina mamaki ne kiga aiki da cikawa wawiya kawai sannan ya juya yacigaba da tafiya tayi saurin shan gabansa tana sauke naunayen ajiyar zuciya tareda rike kugunta da duka hannuwanta "ok muje na saukeka a gida tunda baka bukatar taimakona "nagode kije abunki kawai.... "Haba fu'ad me yasa kake min hk, Allah fa shi yasan abinda yake nufi daya had'amu ,kayi hakuri kabari na saukeka..a fusace yace "banaso ko dole ne? Ta. runtse idanunta ahankali tana jin d'aci da rad'ad'in ,wulakanshi gareta, kusan second biyu tana tsaye agurin tana experience din abinda rayuwa kan zowa mutun batare daya shirya ba ,ko a mafarki bata ta'ba expecting zata tsinci kanta cikin soyayya da irinsa ba ,ta d'an Jima tsaye domin ita kad'ai tasan halin tashin hankalin data tsinci kanta sannan tasoma kok'arin bud'e idanunta taga wayam babu shi babu alamunsa agurin ta kara gaba da sauri ta fito titi still bata ganshi ba ,sai ma cin karo datayi da wasu yara kusan su 6 tsaye abakin titi mutun uku makafai yayinda 3 suka kasance masu ido, da alamun titi suke son tsallakawa , tsawon minti uku tana tsaye tana dubansu yayinda mota ko d'aya batayi kok'arin tsayawa domin basu damar tsallakawa ,sbd idan ba lura kayi da kwayar idanunsu da sukayi sama ba, ba bazaka ta'ba cewa marasa idanu bane ,cike da matsanancin tashin hankali ta karasa zuwa inda suke tsaye tare da d'agawa mota ta karshe dake shirin kunno kai hannuta take motar ta tsaya cak, sannan tasoma tsallakar dasu d'aya byn d'aya, wanda hkn ya faru ne a idanun fu'ad ,ahankali shima ya fito daga inda yake zaune yana jiran ta wuce ya kama gabansa, yak'araso inda sauran yaran ke tsaye, sai waigawa tayi tagansa rungume da yaro daya, d'ayan km rike a hannunsa bayan sun gama tsallakar da yaran, tasoma kok'arin iskeshi inda yaja ya tsaya rungume da hannunwasa duka a kirji yana kallonta tmkr ranar yasoma ganinta ,tana k'arasowa ta tsura masa idanunta tana kallonsa kmr yadda yake kallonta gabadaya kowanensu zuciyarsa cike take taf da shaukin juna "me yasa kake kallona hk ? "Na canza maka ne ko kuwa har yanzu kana jin haushina aranka ?tayi masa tmbyr ajare tana sake kallon kwayar idanunsa da suka soma canza launi "a halin yanzu bana jin kiyayyarki cikin raina sakamakon kyawawan halaiyenki ki cigaba abu ne mai kyau taimako da kyatatawa kmr hk..... yana gama fadar hk ya juya zai wuce tayi saurin riko lauluasar tafin hannunsa cikin nata tana murzawa,ahankali"ina zaka fu'ad kabarni ? "Dan Allah kagaya min kana sona ko akasin hk saboda ina son na karshen komai a tsakaninmu takarasa mgnr tana cigaba da Murza laulausan tafin hannunsa ."a zahirin GSKY bazan sani ba, ko zuciyata na sonki ko akasin hk amman zaki iya tmbyr ita zuciyarta duk amsar databaki zaki iya d'aukarta amatsayin kaddararki. Ta narke masa fuska tmkr zatayi kuka alamun shagwaba "ni dai kace kana sona plx tafiya zanyi gobe zuwa Abuja takarasa fad'ar hk tana kai hannuta daidai saitin zuciyarsa dake wani irin harbawa "plz now say something to me "kace kana sona Dan Allah. "Baza'a ce ba , yasanya d'ayan hannunsa ya zare hannunsa dake rike cikin nata, yakara gaba ya barta tsaye agurin , ita km tsurawa bayansa idanunta tana kallonsa har sanda ta daina ganinsa sannan ta juya ahankali zuwa inda tayi parking din motarta. tana isa tun daga nesa ta hango safwan zaune akan motarta yana dubanta tare da yi mata kallon kasa da sama sannan yace "sweetie daga ina kike haka? Tayi masa banza ta isa jikin kofar tana kok'arin bud'ewa ya duro daga saman motar tare da riko hannunta ,a matukar fusace ta d'ago kyawawan idanunta ta. Zuba masa tana yi masa kallon kaskanci "cool down sweetie abinda nake son sanar dake akwai kuskure acikin abinda kika aikata a mintunonin da suka gabata, barin mota a irin wuraren nan Sam bai kamata akwai hatsari aciki,gashi kin bar motar dake tattare da sirrikan rayuwarki abud'e "saurin me kikeyi da har kika bar kofar motarki a bude? Tayi kokari fixge hannunta cikin nasa Amman ta kasa saboda irin rikon da yayi mata bazata iya kwatar hannunta ba ,"karki wahalar min da kanki dan bazaki iya ba ,shiga mota kawai muje gida akwai mahiman bayanan, ko nace magana ta karshe dazamuyi dake .. Qakarasa maganar yayi tare da bud'e mata kofar motar tashiga ya mayar ya rufe mata, shima ya zagaya ya shiga suka bar gurin, ascot da direbobinsa suka biyosu abaya . Kai tsaye babban parlour'n gidan suka shiga, tayi tsaye nesa kad'an dashi ta rike kugunta tana cika tana batsewa, ta matsu bai fara maganarsa domin kawowa karshen zancesu ,saboda ita Sam bazata iya aurensa ba , sannan duk duniya a halin yanzu babu wanda zai takurata akan zancen aurenta dashi "kayi sauri kayi maganar sannan idan zakayita ka takaita saboda ina da abun yi ta qarasa mgnr tana furzar da iska ta bakinta "ki duba yanayina ,da yanayin shekaruna Wanda yaci ace zuwa wannan lokacin nasamu natsuwar ajiye iyali atare dani ,mead ina sonki son mai yawa, son da bansa lokacin daya shigeni ba ,amman dai yanzu ajiye wannan a gefe, a ina maganarmu ta kwana dake? "ta kwana ne, a in da nace maka bana sonka,bazan iya aurenka ba ,ka nemi wata matar ka aura period ta fadi HK tare da runtse idanunta.. Shima runtse idanunsa yayi tare da cewa "Amman ke kad'ai ce a zuciyata ,shekara biyar kenan ina dakon sonki me'ad kuma har yau bansamu wata wacce naji ina sonta kwatankwacin naki ba, sai ke mead. duk maganar dayake mata ahankali take fita kamar yana mata rad'a ita kuwa har lokacin , kasa bud'e idanunta tayi balle ta sake furta komai ko ta kalli kwayar idanun safwan wanda ke fitar da wani irin abu acikinsa mai kama da kibiyar so ...... jin ya qara yin kusa daita tare da riko laulausar tafin hannuwanta ahankali, shi yasa tayi saurin ja da baya daga tsayen datake. "safwan idan saboda kyawuna ne I thought kaima kana da naka kyawun daidai gwargwado, sannan akwai yammata masu kyau wad'an da suka fini suke da duk abinda kake gani ajikina dakaji kake sona ka zabi daya daga cikinsu ka aura mana zakaji dadin rayuwarka dasu , zaka samu tattali fiyye da yadda kake tunanin samu a wajena, safwan ina son fu'ad fiyye da son kowa a duniya idan har ka fitar da iyayena "har ni me'ad kin fi son shi akaina yayi mgnr muryarsa na kmr zaiyi kuka? "daman kai ni ban ta'ba kawowa zuciyata kai a matsayin mi.... yayi saurin janyota jikinsa ta fad'a cikin fad'ad'd'en k'irjinsa inda bai tsaya wata wata ba ya rungume tsam sbd yarigada ya fara rud'ewa daita, "karya kike me'ad bakya son shi ni kike so, shekara biyar din da muka d'auka tare, ban ta'ba jin kin ambaci sunan wani d'a nmj ba ,asalima sunana ne acikin bakinki meyasa kike son ki gujeni yanzu alhalin ina mutuwar sonki ......... ?"ki aureni zan mallaka miki komai nawa dana mallaka ke ko rayuwata kike so zan baki amman karki barni... Tayi saurin janye jikinta tare da sake ja baya sosai tana fitar da numfashi sama sama sai alokacin ta lura babu mayafi ajikinta balle abinda takama gashinta dashi, ta bata fuska sosai tmkr zatayi kuka "me yasa ka cire min mayafi?ko kayi zaton nima kmr irin mutanenka ce ,to bari kaji na gaya maka nifa ba yar is... "Me ya kawo wannan batu mead?su waye km mutanen nawa? Yayi tsoki yana dafe gefen kansa daya ji yana sara masa kad'an kad'an sannan yace "ki samu guri ki zauna muyi mgn, naji na janye zance aurenmu hk yayi miki?"kije ki gayawa shi wanda kike son din ya turo iyayensa kawai musha biki . "da gaske!!! kake safwan ka janye batun aurena ?"sosai kuwa ai nafi bukatar farincikinki akan nawa.."sai me ?" Sai ga me'ad ta dawo kusa dashi ta zauna rike da hannuwansa "nagode nagode safwan Allah yabaka wace tafini "ai kibar wannan adduar me'ad saboda bazan ta'ba samun kmrki ba ,dubi surar jikinki fa meye baki dashi me'ad? Take ta had'e rai "Ka d'auke idanunka ajikina ,ni dai na.......gode sosai, sannnan ina neman alfarma agurinka "uhmmmmm ina jinki ki roki komai kike so? "ina son ka gayawa dady ka janye batun aurenmu sannan kayi masa zance fu'ad dan Allah idan kamin hk ka gamamin komai a duniya, kuma zan tabbatarwa kaina lallai kai mai sona ne da son farincikina. "karki damu swe ...am kanwata an gama, ba sai hira ta barke tsakaninsu ba har inda take gaya masa zatayi tafiya zuwa abuja gobe, amman kwana biyu zatayi ta dawo Dan Allah tana son kafin ta dawo yayi mata kok'ari, har kusan la'asar suna tare makale da juna kmr tun farkon shakuwarsu, kafin shakuwar ta juye zuwa soyayyar da iyayensu suka karfafata, har farfajiyar gidan ta rakashi suna cigaba da tautaunawa da kanta ta isa ta bud'e masa mota yashiga ya zauna yana d'aga mata hannu tana daga masa har motacinsa suka fita daga harabar gidan , safwan ya bar gidan zuciyarsa na wani irin tsalle da zafi tmkr ana zuba masa ruwan dalma acikinta. ********** ta bangaren sajida kuwa, tana cikin tashin hankali mara misaltuwa ,ganin yadda kullun kwanakin aurenta ke sake. matsowa ,gbdy ta rame tayi baki ta fita haiyacinta ,bata samun ishashen bacci akan mutumin da bai san da zamanta ba ,lamarin aikinta ma tattara shi ta ajiye agefe ,sai zaman d'aki da kuka, har ta kai ga kiran emran dake k'asar London yana aiki da BBC, tana kuka take gaya masa ita tafasa aurensa ba ,shima kukan ya fashe mata dashi yana tmbyrta dalili had'e da rarrashita tare da bata hakuri " idan narasaki sajida Zan iya rasa raina nima ,byn sun gama waya daita,ya kira acp yake gaya masa abinda ake ciki, acp yace" ya kwantar da hankalinsa tare da bashi tabbacin mutuwa ce kawai zata hana yiwuwar aurensu , tunda gashi ma lokaci ya kusa ,a daren acp bai runtsa ba sai daya dangana da d'akinta in da ya sketa kwance tana kuka "yayi mata kaca kaca sannan ya k'ara"matsawar kika butulcewa auren emran bani babu ke ,sai dai ki nemi wani uban Amman bani ba... wannan tashin hankali ke hanata sukuni da walwala tasha gwada kiran fu'ad, amman ko ya d'auka bata mgn ,sai dai ta saurari sautin muryarsa ta kashe, a ranta take aiyana ko ta auri emran zata kashe auren domin cikar burinta. ********** Dare yayi nisa amman fu'ad ya kasa runtsawa ,shi yasan ya dad'e da tsintar kansa cikin shaukin soyayyarta, sai dai yasan rijiya ba gurin wasan yara bane, dan haka yasoma yaki da zuciyarsa, ta hanyar yakar sabbin kibiyoyin dake hud'a kowanne sako na cikinta. Sai dai duk iya kokarinsa a wannan daren baccin dayake bukatar samu ya gaza samunsa ,surar me'ad kawai yake gani cikin kyakkwan murmushinta ,Dan hk da yayi sallar asubahi ma ya dad'e zaune yana rokon Allah saukin al'amarin amman ina mead ediress takai ta kankane koina na zuciya da kwalkwaluwarsa ta karasa gangar jikinsa bata barshi da ko saqo daya da zai sanya tunanin kansa.. ********* Kmr yadda fuad bai samu runtsawa ba hk rayuka uku nan ,basu runtsa ba mead sajida safwan, safwan na kokarin ganin ya cire me'ad da lamarinta acikin rayuwarsa, ita km sajida tashin hankalinta yadda kullun me'ad take nacin son mallakarsa wannan takaicin ke hanata runtsawa . Yayinda me'ad abubuwa guda biyu ne suka hanata runtsawa da fari farincikin janyewar safwan da kuma tunanin yadda fu'ad zai fuskanci lamarinta, wanda kusan nashi tunanin ne ya hanata runtsawa, abinda tabasayi, shi mike domin yi wato sallar dare, allah yayita da dabi'u mabanbata Amman sai ya tsaida ita,da yawon son ibada acikin zuciyarta, duk iskancinta bata bari alokacin sallah ya wuceta ,wannan kuma Allah shi ya barwa kansa sani akan manufarsa gareta , alwala tayi domin gabatar da nafilfilinta data saba, tana nan zaune har sanda aka kira sallah sannan ta tashi ta gabatar, bata yi yunkuri komawa bacci ba tasoma shirinta, Dan hk washegari byn tayi sallama da iyayenta itace mutun ta farko data yiwa inna sallama a bakin kofarta , tazo ta bud'e ita kuma ta umarci direbanta daya kwaso kayan dake bayan boot din yashigo dashi sannan tasanya kanta cikin d'akin bakinta d'auke da sallama, Zuwansa gidan inna kenan yana kalaci. Fu'ad ya d'ago kyawawan idanunsa yana kallonta kirjinsa na wani irin mahaukacin buga domin sam baiyi tunanin zai ganta adaidai wannan lokacin ba ,itama kallonsa cikin kwayar idanunsa take wad'anda atake ta gane kankancewar da sukayi gashi sunyi ja alamun rashin wadataccen bacci kmr nata, kada tayi haufi inji zuciyarta shima ya kwana cikin kwatankwacin irin situation din data kwana. Inna ta shimfid'a mata sallaya, tace "bismillah ki zauna ki kasance tare damu tasoma kok'arin zama idanunta na cikin mayatattun sexy eyes dinsa "tace anya kuwa inna ayi hk?"akan hanyar aiport nake . "Duk da hk dai yar nan wannan sammakon da kikayi bai isa ace kin sanyawa cikinki abinci ba sai dai idan kalar namu abinci ne bai miki ba... Tace"wallahi ba hk bane inna ,babu yadda mom dina batayi ba ,Dan na tsaya naci amman idan wannan jikan naki yayi min izini sai in ci ko acikin nasa ne. Fu'ad ya ajiye kofin shayinsa dayake kur'ba ahankali ahankali ,idanunsa acikin nata yace "idan ni ne sai dai ince kada Allah yasa kici, me'ad da inna suka tsurawa bakinsa ido "kina kallona inna wace bataji mgnr mahaifiyarta ba, Dan me zataji tawa? Tayi ajiyar zuciya tana mai nunasa da d'anyatsa hannunta" kai ko sannan tayi kasa da murya wanda shi kad'ai zai iya fahimtar abinda zatace "hidimomin tunaninka ne fa ya hana tsayawa na karya . ya murmusa gently abinda bata ta'ba gani ba kenan a fuskarsa, shiru tayi tacigaba da kallonsa. inna tace "manta dashi ki zauna kuci tare bari na qaro muku "a,a inna kibarshi kawai Dan banajin yunwa , ga sako can an shigo dashi karki ce bazaki amsa ba dan Allah inna ni dai fatana kin sanya min albarka "fu'ad ya runtse idanunsa Dan dadi yaji dadin abinda tayi amman bazai bari wannan kyautar shiga tsakaninsu ba ,ahankali ya bud'e idanunsa yasanya cikin kwayar idanunta sannan yakira sunanta"me'ad .. wannan shine karo na farko da hkn yafaru taji sautin sunanta abakinsa wani irin abu taji yana yawo acikin jikinta. Dama kwalkwaluwarta gbdy ta amsa da "na'am fu'ad "ki koma da abinda kikazo dashi mun gode kwarai da kulawa.... tayi kicin kicin da ranta sannan tace "ina ruwanka da abinda na kawo?"inna na kawowa ba kai ba balle kace hk ta waiga gurin inna "inna ni zanyi tafiya zuwa abuja ki min addua sannan ki sanya min albarka, kai kuma sai kaji wayata ta mike tsaye inna na kwararo mata addua sukayi sallama. Can dare har ya kwanta wayarsa ta d'auki kara yasan babu wanda zai kirashi a daidai wannan lokacin sai ita, ya mika hannu ya d'auka zuciyarsa na beating ya manna a kunnensa a kasalance yace baki kwanta ba ? Tace "na kasa bacci ne ,na sauka lfy Amman tunani na neman mayar dani mara lafiyar karfi dayaji. Ya rage muryarsa saboda kada ya tashi su kabeer yace " ke kuwa tunanin me kike hk me'ad? "Kai tsaye tace "tunaninka? Yayi ajiyar zuciya mai sanyi cikin ransa yace "nima hk tunaninki ya hanani walwala da runtsawa ,bai san cewa a fili ya fad'a ba ita kuwa kunnuwanta sun rigada sun zuko mata sautinsa, tayi murmushin jin dadi wanda ya fidda sauti, cikin ranta km godiya tayiwa Allah daya takaita mata wahala da rashin tabbas din datake hangowa alamarinsa. Daga nan sai me? Sai hira ta 'barke tsakaninsu kmr ba fu'ad ba shi kansa har mamakin kansa ya shigayi ta yadda cikin kankanin lokacin me'ad ta tankwasa zuciyarsa ta sauya mata akidar tunaninsa, na bazai saurari kowace mace ba har sai byn ya samu aiki, tare da daidaita a rayuwarsa sannan zai bud'e shafin soyayya. Amman gashi a wannan daren ya kulla soyayya mai karfi mai ban mamaki da me'ad takai wanda bai ta'ba tsintar kansa ciki ba. Tun daga ranar kullun sai sun raba dare suna wayar soyayya, har tabaro abuja, yanzu ne me'ad tasan tana cikin shaukin soyayya, ba soyayyar kuruciya ba da'ake son tursasa zuciyarta ciki . wasu emotion ke tangaliliya da rayuwarta da zuciyarta akan fu'ad dake aiki cikin zuciya da kwalkwaluwarta. bata 'bata lokaci ba gurin sanarwa da aminiyarta sajida ba ,wanda wannan sakon yayi gigita ya haukatata har yayi nasarar kwantar daita a gadon asibitin .. Mmn sudais ce 💗💗💗💗💗💗 'YAN CINKI 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 ~NA~ *AYSHA A BAGUDO* ~DEDICATED TO~ MRS ADAM ( YAR MUTAN KAGARA) Page 55 to 56 .......bata san inda hankalinta yake ba, sai farkawa tayi ta ganta a gadon asibiti ,ta fahimci hakan ne ta hanyar ganin wata nurse a tsaye akanta, dan tana bud'e ido daita tasoma cin karo tana kokarin sanya mata k'arin ruwa. tayi saurin mikewa zaune tana raba idanu tare da tuna abinda me'ad takirata a waya ta sanar mata wanda shine abinda ya haddasa mata zuwa asibiti , me'ad wace dawowarta kenan daga tafiyar datayi zaune take abayanta tana mata sannu , jikinta a matukar sanyaye, sai dai kallo daya sajida tayi mata abinda ta gaya mata ya sake dawowa cikin 'kwa'kwalwarta da gangar jikinta, idanunta gbdy sun rikid'e sun dawo kamar gauta al'amar taci kuka tagaji dan har lokacin hawaye ke bin kuncinta,tana jin tmkr ranta ake zara gbdy takaicin me'ad take ,a halin yanzu bata jin akwai halitar data tsana sama da emran daya nacewa aurenta sai km me'ad datayi wa rayuwarta karan tsaye ,tana matukar son fu'ad kmr tayi hauka aganinta ita tafi cancanta yaso ba me'ad,saboda tafi tsananin son shi da buk'atarsa . "Me yasa so yayi mata yanka kauna irin hk?"me yasa idanunta suka had'u dashi? "Ina ma batayi mata rakiya ba a wannan ranar, ranar datayi silar dagulewar duk wani lisafin rayuwarta.....takarasa zance zuci tana sake fasa wani irin gigitaccen kuka tare da fizge hannunta daga rikon da nurse tayi mata,sannan ta bar jikin me'ad ta kakkame misna tana wani irin kuka "shikenan narasa shi ko misna ? Ta furta hkn a bayyane ta sake tafiya luuuuuuu sai gashi ta kifa k'asa daga misna da me'ad har nurse din sun gigice har aka rasa wanda zai yi wani abu akai. me'ad ta durkushe bisa gwiwowinta tana jijigata cike da matsanancin tashin hankalin ,da kiran sunanta cikin k'araji, yayinda kukan datake ta rikewa tun d'azu ya kwace mata, ita kuwa nurse da gudu ta fice daga d'akin dan kiran likita atare suka dawo wannan karon har da dady da acp da hjy Khadija mahaifiyar me'ad suka biyo bayansa. likita ya d'agata da taimakon su dady suka maidata kan gadon yayyafa mata ruwa sukayi, sai kuwa ta bud'e idanunta tare da sakin wata ajiyar zuciya da karfi ,idanuta ya d'auro akan mahaifinta da iyayen me'ad "Allah sarki uwa mai dadi,ina ma tata uwar na raye da wata killa tazamo sanyi idaniyya mai share mata hawaye, acikin wannan halin datake ciki. kallon mahaifinta take tana kuka sosai a zuciyarta ta sake furta "shikenan narasa shi ko? gbdy suka k'araso gareta cikin tashin hankali saboda jin furucinta a she a filli tayi mgnr batasani ba "waye shi din wanda kika rashi? me'ad da momy suka rungumeta suna gunji kuka cikin kuka momy tace "sajida waye shi ki gaya mana ko waye shi da kike ikirarin kin rasashi, "a tunaninmu emran kike so kuma yana raye bai mutu ba, asalima yanzu muka gama waya dashi. Girgiza kai tasoma yi tana fidda numfashi sama sama "bashi ba..bashi nake nufi ba ni kad'ai nasan kowaye ,wanda nake nufi yana raye sai dai narasashi..... ".ki gaya mana kowaye shi zamu san abin yi "a'a khadeeja koma waye shi sai dai ta hakura ,sbd ni bata ta'ba sanar dani tana son wani ba byn emran,wanda itace da kanta ta kawo min amatsayin mijin aurenta, kuma zuciyata ta aminta dashi," kan wani dalili take son maidamu kananun mutane.? likita ya dafashi alamun rarrashi yana cewa "ka kwantar da hankalinka ranka ya dad'e,ka natsu ka binciketa da kyau idan har batason shi wanda ta kawo din yanxu ,sai a hakura mana , "itace dai zata hakura da koma wani d'an iska ne . "Alamarin na soyayya mafi yawa masu kwalkwaluwa irin tasu su kan d'auketa da tsananin sai daga baya komai ya daidaita, kamata yayi kasamu lokaci kayi zaman sirri daita domin sanin kowayeshi yaron, "wallahi kaji na rantse sajida bata da miji daya wuce emran koda mutuwa ce sai dai ta dauke ad'akinsa Amman... wata irin zabura tayi hjy Khadija ta rikota da sauri,wanda hkn yayi nasara katse acp ya tsura mata ido, shi kansa dady sai dayayi dayasani furuncinsa,saboda yadda yaga gbdy ta sake firgicewa, likita yayi kok'arin 'ban'bareta da kyar daga jikin momy yana fad'a tana sakin momy ta sake Sumewa alamarin daya d'aga musu hankali kenan kuka kawai suke har da acp ,momy tace wannan wani irin maseefa ne ? A zuciyarta. " Ga zance me'ad dake soyayya da d'an talaka ,wanda har yanzu mahaifinta bai sani ba ga lamarin sajida. likita yana bata taimakon gaugawa yace "ban so ka dinga fad'ar irin wand'an maganganun ba,yallabai, irin wannan lamarin rarrashi da nasiha yake bukata da kwantar da hankali yakarasa mgnr yana mata allurar bacci sannan yacigaba "koda zata farka Insha Allahu zata dawo Normal"Allah yasa suka amsa gbdy,lamarin na sake d'aure musu kai. Cikin ikon Allah kmr yadda likita ya fad'a koda ta farka tasamu natsuwar zuciya , bugun zuciyarta datake jin ya tsananta ,yayi k'asa sosai yasoma dawowa daidai, sai dai kallo daya zaka mata kasan tana cikin matsanancin damuwa. Lokacin da me'ad ta gama taimaka mata tayi wanka da sauransu ta matsa da tambaya. "waye shi wanda kikarasa sajida ,da har yayi silar kwanciyarki hospital?tayi mata shiru taki cewa komai "to mai ma zata ce mata,tace akan fu'ad tashiga wannan hali ko mai? Ai ma abun kunya ne ita da aminyarta sun kama da soyayyar mutun daya kmr wani almara. Tsawon lokaci me'ad na tare daita tare da son jin damuwarta amman sam sajida taki gaya mata komai"wato ni ban san ciwon kaina ba kenan danake gaya miki sirrukana da abinda ya shafi rayuwata ba ko ? "shikenan sai kicigaba da rike damuwarki ke kad'ai mu km zamu cigaba da tayaki da addua, Dan ni tuni zuciyata ta soma zargin kin fad'a soyayya da wani mafi kusanci damu. "ba karya kika fada...."ina ma zaki bar min shi da har karshen rayuwa bazan manta dake ba?tayi mgnr cikin ranta tana mai runtsa idanu. Kwananta biyar a hospital likita ya sallamota duba da ganin samu saukin jikinta,domin tayi kokarin tsaida zuciyarta gurin soma cire fu'ad cikin ranta, ta sake maye gurbin gurin da emran kai tsaye gidansu me'ad aka wuce daita bisa umarnin mahaifinta daya bayar. Kowa a gidan attention dinsa na kan sajida da bata duk wata kulawa tare da sanyata cikin nishadi, hkn nayi mata dadi sosai sai dai har lokacin tunaninsa yaki barinta. ******* Yau me'ad da kanta tashiga kitchen sa'baninta lokutan baya,ta had'a dinner mai rai da motsi da taimakon ummi sannan tashiga wanka har ta fito ta tsaya gaban mirrow hankalin sajida na kanta tarasa dalilin da hk kawai take jin babu aranta, a game da wanka data shiga, ahankali me'ad tayi shafinta ta shirya cikin wasu had'ad'd'iyar doguwar riga swiss less ruwan zuma tana fesa turare a kowani lugu na jikinta kararrawar shigowa gidan tayi k'ara sannan wayarta ta hau ruri tabbacin fu'ad dinta ya iso kmr yadda sukayi dashi, daman tun a safiyar yau kai tsaye takira masu gadi ta gaya musu tana da baKo su barshi yashigo, tayi taku d'aya biyu taji sautin muryar sajida cikin rauni dayasa ta tsaya batare data juyo ba "fu....fu'ad ne yazo . ?"uhmmm ta bata amsa dashi tana gyara mayafin jikinta "ok ki gaida min shi "zaiji ta sanya kai fice daga d'akin ,mead na fita ta mike tashige bayi saboda kukan daya tunkuro mata mai had'e tari ,tana shiga ta fashe da wani tsumammen kuka. Me'ad na k'arasawa farfajiyar gidan,ta d'aura kyawawan idanunta akansa sai ta nemi daburcewa , kasancewar wani azababben kyawun dataga ya kara mata, suka dubi juna da wani irin kallo mai kwantar da zuciya, kafin kowannensu ya saki murmushin mai d'auke da boyayyar ajiyar zuciya. Gaba tayi ya biyota abaya yana kallon kugunta dake juyawa ahankali wanda yasoma tayar masa da boyayyen tsumin shaawarsa da bai san yana daita ba ,da sauri ya d'auke idanunsa zuwa yanayin tsarin gidan , adaidai wani karamin parlour'n baki ta tsaya tare da kaucewa tabashi hanya yashigo parlour'n cikin kodaddiyar shadda mai hasken sararin samaniya gilashin idanunsa fari ne dan siriri, wanda ya fiddo da zahirin cikar kamalarsa na cikakken d'a nmj wanda rayuwa ke yayi ,matsalarsa dai rashin aiki da kudi, ita kanta tana da tabbacin da zai kasance mai aiki a hannunsa, matan da zasuyi rubibinsa suna dayawa da wata killa ma bata had'u dashi ba me'ad tayi nisa sosai a kallonsa, yayi murmushi yasoma busa mata iskar bakinsa a idanunta tayi firgigib ta dawo haiyacinta . "kallon ya isa hk me'ad ,sosai taji kunya abinda yace, ta wuce ciki suka zauna cikin kananan leather da suka yiwa qaramin parlour'n nasu qawanya. Tace "sannu da zuwa honey ya hanya? Yayi murmushi tare da lumshe idanunsa kmr bazai amsa ba sannan yace "lfy . tayi D'an jim tana kallonsa sannan suka gaisa gbdy suka kasa boye soyayyar dake zuciyoyinsu sun jima suna bayyanawa juna sakonni zuciyoyinsu daga karshe ta gabatar masa da abinci da abun sha amman Sam yaki ci komai "iya ganinki kad'ai me'ad ya isheni ....taji Dadin wannan furuncin nasa sosai har kasa boye farincikinta. Sajida takira mahaifinta dayazo ya d'auke da kansa, Dan bazata iya tuki ba, ta gwammaci zaman kadaitan gidansu akan tacigaba da zama tare da mead, wacce bata iya boye son fu'ad ako gaban waye,nunawa take, da yammanci ranar tana kwance tasoma jiyo jinia, ta tabbatar da mahaifinta yazo, har cikin gidan yashigo sun dade da dadyn su mead suna tautaunawa akan yadda bikinta zai kasance ,sannan daga baya yasa akayi kiranta nasiha da rarrashi sosai dady yayi, har gaban motar dazata shiga ya kai ya bude mata da kansa yana sake rarrashita ,dady na tsaye har sai daya ga wucewarsu sannan ya koma cikin gida yana girgiza kai. ******** Soyayya fa mai karfi tashiga tsakanin me'ad da fu'ad, cikin salo mai ban mamaki basu iya sati basu sanya junansu a ido ba ,kullun yana kan hanyar zuwa gidansu idan kuma bai zo ba, suna makale a waya, duk wannan wainar da'ake toyawa babu wanda ya sanarwa dady har safwan dan koda ta tmbyesa ko ya sanar masa "cewa yayi bai samu had'uwa da dady ba,gashi tafiyar gaugawa tasameshi American sai ya dawo tukun. Bata damu ba, tacigaba da bawa fu'ad kulawa, fu'ad shi din yasan me Nene so? yasan darajar abinda yake son,ya km iya tafiyar dashi ta hanyoyi daban daban, ta yadda duk wanda zata so shi,zata so shine da dukkanin zuciya, ruhi da gangar jiki koda taki Allah shi ba dan bariki bane, amman ga matar dayake so, mugun dan soyayya ne kmr ba indiye dan irin kalaman dayake furta mata azahiri da cikin waya idan ka ganshi a zahiri rantsewa zakayi kace bashi yake fad'arsu ba ,sbd tsare gida da rashin son raini ,Dan hk ne bai sha wahalar sake yiwa zuciyar me'ad kamun kazar kuku ba, bata da wani tunani sai na fu'ad ,bata da wani ra'ayi sai nashi bata da wani buri sai na mallakarsa matsayin abokin rayuwarta har karshen rayuwa. Gbdy ta mance da wani safwan dake can wata kasa tattare da dakon soyayyarta ,a wani zuwa ne da fu'ad yayi tana zaune gabansa cikin less mai taushi fari sol da zanen silver ,dinki bakaramin kama jikinta yayi Dan har saman dukiyarta yana iya hangowa, shr yayi zuwa wani lokaci sannan yakira sunanta muryarsa a kasalance "mead, na zauna nayi tunani mai yawa akan lamarinmu dake, ni talaka ne sannan d'an talakawa gaba da baya, wanda yake karkashin kulawar kakarsa ,da bata da komai ,bata aje ba sannan bata bawa kowa ajiya ba,gani zaune babu aikin yi ina sonki sai dai bansa yadda zanyi ba idan batun aurenmu ya tashi . Maganganunsa sun mata ciwo matukar da hk muryarta a d'an zafafe tace "duk nasan da hk fu'ad nace ina sonka. Ya langwabar kansa tare da tsura mata idanu kmr zai cinyeta sannan ya bude bakinsa da kyar yace "zaki iya zama dani cikin halin babu, sannan bazan iya rayuwa babu innata a kusa dani ba saboda nayi aure, Dan tayi min komai arayuwa, byn kasancewarta kaka gareni uwa ce mai tattare da matsayin uba, ta taka matsayin komai gareni zaki iya tallafawa rayuwata data innata? Ta lumshe ido cikin wata sabuwar kaunarsa dake mamayarta ta km lullu'be zuciyarta "kada ka damu baka da matsala dani fu'ad soyayyarmu had'in Allah ce ba dan wasu kyale kyalen duniya ba, kacigaba da tafiyar da rayuwarka hk ina sonka hk , ina girmamaka sbd dattakonka,ni fuad din kawai nake so bawani abu nasa ba ,ina matukar sonka ta yadda har bazan iya waiwaya ba, in hango hierarchy dinsa ,yake gani wanda shi so baya la'akari dasu.....sai byn data furta hkn kunya ta lullu'beta Dan ganin irin yadda jikinsa yajike yake tsuma km ya zubawa dan karamin bakinta idanu dake motsi yana fitar da kalamai masu sanyi garesa, tacigaba "ni dai fatana da burina ka rikeni amana ka yardani nima in yarda da kai, Allah yardadamu yabamu ikon mallakar juna idan kayi min wannan, ni km nayi maka alkwarin zama da kai muddin rai cikin kowani irin hali ,akwai ko babu dadi ko akasin sa....da sauri ya mika mata hannunsa tun kafin takarasa. "shake my hands my love..nagode da soyayyarki gareni, ina rokon Allah ya fiddani kunyar soyayyarki..yabani ikon fita hakkokinta yabani ikon sanin mahimmantata fiye da duk wani alamarin da dan adam ke burin samu suka had'e hannuwa guri daya kmr masu kulla alkwari. Ta lumshe ido jikinta na tsuma saboda had'uwar tafukan hannuwansu ,domin ji wani abu na fita daga cikinsu zuwa nata naunayen ajiyar zuciya ta sauke tana sake damke hannunsa cikin nata sannan tace "sai batu na neman aiki fu'ad kabani CV's dinka a samomaka aiki, ina bukatar ganin cikin office honey, ka yarda ka amince min.... Murmushi yayi "kibar wannan issue din, nima ina kan nema da kaina wanda ya amshi takarduna ina sa ransa samu, ki min addua yakarasa mgnr yana saka yatsun hannuta cikin bakinsa, bai tsaya bata lokaci ya fara tsotsarsu domin kwantar mata da hankali, aiko take abinda yake bukata daga gareta ya kau Dan jikinta ya d'auki kyarma dan ji tayi kmr yana zarar ranta da kyar tasamu ta kwaci hannunta fa fad'a jikinsa . ************ An yi bikin sajida na ban mamaki sannan aka kai amarya gidan mijinta dake cikin ajawo estate, 'yan kai amarya mutun Hudu basu tsaya ba ,suna kaita suka juyo bayan kowa ya fita ne ta d'auki jakarta tashige d'aki ta kulle kanta har gari ya waye sannan ta shirya ta fito ta zauna cike da jin haushi emran ita fa fu'ad take so, zuciyarta ta kasa hakura dashi gbdy ango yarasa gane kan amaryarsa, duk yadda yayi daita taki haushinsa take ji, da ganin bai iya komai ba ,komai yayi bai iya ba fu'ad ne ya iya kwata kwata baya burgeta tana zaune emran yashigo yana fara'a wai shi me amarya ya samu gefen kujerar da take zaune ya zauna tare da zura mata ido baya ko kiftawa. ita kuwa ko kallo bai isheta ba ta juya masa baya dama tagaji da kallon dayake mata kawai sai ta mike tashige dakinta . yasha mamakin abinda ya faru shi daman tun kafin bukinsu yaga ta canza tmbyr duniya yayi mata taki amsa masa . Satinta daya a gidan da yamma emran yashigo yace taxo yana son ganinta, bata kulashi ba dan bai isa ba shi km ya dawo parlour'n ya zauna yana jiranta ya jima yana zaune a parlour'n amman bata fito ba hkn yayi maseefsr 'bata masa rai ya tashi ya koma cikin d'akin yasameta a kwance a inda ya barta batare da niyyar tashi ba ,ya daka mata tsawa da cewar sajida wai me ke damunki ne da har zan dinga miki mgn kina jina byn ba dole nayi miki ba ? "wai ma me kike nufi ne tun sanda aka kawoki gidan nan kin kasa zuwa ki gaida iyayena, dan baki d'aukesu abakin komai ba, sannan ko ruwan zafi baki tab'a dafa min kin kawo min nasha ba balle kiyi min girki irin na mata da miji ki kawo naci to kisani bazsn dauka ba.. sajida dake kwance jin yayi shiru yasa ta tashi zaune tana yiwa emran wani kallon tsana tace "amman emran kabani dry dan ina jin kana da matsalar kwalkwaluwa, banda hk ka dubeni da kyau kace wai ni zan maka girki ashe zaka mutu da yunwa bakaci ba,dan ni ba yar aikinka bace kuma ba tun yau ba kasani ko ruwan zafi ban iya daurawa ba, idan kuma ka manta na tuna maka saunawa me'ad na sanar dakai sajida bata iya komai ba? Dan hk ko ruwan zafi dazaayi wanka dashi ban iya dafawa ba ,kai ko gas ban iya kunnawa ba balle km yin girki dan hk ka nemi wace zata dafa maka abinci sannan zance inje ingaida iyayenka ai basu na aura ba su dan girman kai tinda nazo gidan basu zo ganni ba balle su girmamani amatsayina na matar d'ansu, kaga nima bazanje in gaidasu ba don neman gindin zama bazanje koina ba kaji ko? idan km sai naje ne sai dai ka sakeni nakara gaba.. "au haka kikace ko? Emran ya fad'a cikin 'bacin rai "Kwarai na fad'a itama ta mayar masa tana cewa dama kasakeni naje nayi yakin neman auren fu'ad shi kawai zuciyata ke muradi ba kai ba ta fada aranta. bai kuma cewa komai ba yasanya kai ya fita yana mamakim abinda ya canza masa sajidarsa ,shi ba zance rashin girkinta ne yafi damunsa kmr yadda take nuna kiri kiri bata sonshi yanzu.. idan rashin girki ne ya Dade dasanin hkn, km har yayi tunanin nema musu me aiki amman kwata kwata yarasa meyasa ta tsiro masa da wannan halin to ko dan taga yana maseefsr sonta ne? amman yasan yadda zai yi mata momysa zai gayawa watakilla yasamu kanta . yana fita sajida taja wani dogon tsaki ta koma ta kwanta lamo tana tunanin fu'ad. Mmn sudais ce 💗💗💗💗💗💗 'YAN CINKI 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 ~NA~ *AYSHA A BAGUDO* ~DEDICATED TO~ MRS ADAM ( YAR MUTAN KAGARA) Page 57 to 58 .........Emran na fita kai tsaye bangaren ummansa ya nufa bakinciki duk ya cika masa zuciya,umma ta sarawa d'an nata lokacin daya gaya mata irin abinda sajida take masa . Umma da kanta taje bangaren sajida domin yi Mata fad'a saboda tana mutuwar sonta kmr yadda emran dinta ke sonta, Amman abinda sajida tace ya kusan sumar umma dake zaune cewa tayi " hjy ai ba nice kawai mace ba a duniya , idan yaji haushi kuma bazai iya da halina ba ya sake aure tunda yana da kudin da zai iya auren ko mata nawa ne,Dan ni ba ruwana ,abinda nake son ya gane kuma ya fahimta banzo gidansa Dan in yi masa biyayya ba,ko wani bauta, shima yasan da wannan, in karya ne ki tmbayeshi gashi nan zaune agabanki . Umma ta girgiza kai cike da bakinciki sannan tace "shikenan babu komai tunda da kanki kikace yayi miki kishiya zakuwa ayi da yardar Allah, Dan kuwa zan tabbatar da d'ana emrana ya auro santaleliyar budurwa yar gidan mutunci. "To ni hjy manene zai dameni ,byn nima har yanzu amatsayin budurwa nake babu nmj daya ta'ba takani , ni da zaki taimakamin ma da kinsa wannan d'an naki ya sallemi na huta... emran ya yunkura ya mike jikinsa na rawa zai d'auketa da wani gigitaccen mari, hjy tayi saurin taresa "kul karka soma ... akwai abinda yafi duka ko mari zafi arayuwar d'an adam, shi yafi cancanta kayi mata ba mari ba Dan ko ka mareta bazaka huce ba. Gabadaya jikinsa kyarma yake "yanzu har sunzo gurin shi sajida,?wulakantashi da iyayensa zagaye dakin yasomayi zuciyarsa na masa daci da tafarfasa, ita dai umma bata sake cewa komai ba ta tashi ta fita tana jin zafin abinda sajida tayi mata, sai dai tayi kanta alkwarin duk runtse sai ta aurawa emran mata har biyu sai dai idan shine baya so. Kwana hudu tsakani abinda daya faru da daddare suna bacci kaddara ta fad'o gidan, domin barayi ne sukayiwa gidan diran makiya, saboda jin labarin emran yashigo da wasu makudan kudi masu yawa xshiyasa sukazo dan su amshi rabonsu, gabadaya mutanen gidan suka tara a falo daya, duk sukace kowannensu ya kwanta flat a kasa ,kowa ya kwanta amman banda sajida saboda jin itace diyar acp , taki kwanciya babu yadda emran bai yi daita ba amman taki, babbansu yace" da kyau yar kanwata kinfa burgeni sosai, dan kina da zuciya mai dakiya ke matar 'barawo yakamata kizama bana na maikacin BBC ba , amman duk da hk za'a shafa miki bakin fanti da iya rayuwarki idan kika tuna zaki ji zafi, ke ba iya ke ba har ya'yanki sai bakin fenti ya shafesu, yakarasa mgnr ya kalli wani baki mummuna daga cikin yaransa yace "kai shigar min daita turakar mai gidanta, in sha jinita sannan nayi maganin abinda ke damun kwalkwaluwarta. Take yaron ya isa inda sajida take ya kama hannunta da karfi ya fixgota xuwa jikinsa, tayi waya siririyar kara tare da kiran sunan emran da mahaifinta cikin tsananin tsoro da razana. Emran yayi saurin d'agowa ya dubi ogan zuciyarsa na beating yace "Dan Allah oga kayi hakuri wallahi duk abinda kake so zan baku in dai zaku kyalemin mata amarya ce ka duba girman aure. Ogan yayi dryr mugunta yace "kada ka damu abokina zan koyar daita komai sannan zai koya mata hankali da ilimin rayuwar duniya ba cutar daita zaiyi ba, idan kuma ka sake mgn abakin ranka ya afka d'akin daaka shigar daita,shi kuwa emran bai sake cewa komai ba yana jiyo ihun sajida tana kwalla ihu da gudu ya tashi ya nufi hanyar d'akin yana kiran sunanta Amman Kan ya karasa wani ya daki kansa da tsinin bunduga anan ya zube kasa a sume bai sake jin komai ba, sai farkawa yayi ya gansa kwance a d'akin ummansa su km kannensa sun zagayeshi ya dubi umma yaga fuskarta tana cikin damuwa ya sauke ganinsa Kan wasila kanwarsa yace "wasila sun kashe min sajidata ko? Sun kashe min yar amana," amanarta mahaifinta yabani, sun kashe min ita ko? Wasila ta girgiza kai tace "kayi hkr yaya basu kashe kowa ba sai dai sunyiwa sajida fyade , wata irin zabura yayi ya mike tsaye cikin takaici, tabbas sajida ta cucesa wata daya da yin aure Amman bata ta'ba zuwa dakinsa ba kullun akwai wulakanci datake masa daban daban akan hakinsa tace"bai isa ya kusanceta, yau gashi wani katon banza wanda bashi da imani yazo har gida kuma har cikin dakin aurenta ya keta mata alfarmar aure, tabbas hakkinsane ya kamata tun baaje koina ba. Ya dawo da kallonsa wajen ummansa yace "umman yanzu tana ina? Umma ta d'auke kanta daga kallonsa tace"ina zata? "Tana dakinta mana ,wannan mugun halin nata da kunya bazai barta ta zauna cikin mutane ba . Emran bai ce komai ba ya mike cikin sanyin jiki tana can kuryar gado ta had'a kai da gwiwa tana kukan nadama da cutar kanta datayi bisa rashin kunya wanda ba halinta bane a da. Ya tsaya abakin gadon ya tura hannuwansa duka biyu cikin aljihun wandosa "ina ganin bamu ya kamata ki zauna kinawa kuka ba, kamata yayi ki bisu kiyi musu kuka ina tunani hk ne zaifi ,tunda su suka miki laifi ba mu ba, in km baxaki gane inda suke ba ya zame miki tilas kiyi hakuri Dan ba zai yiwu ki cika mana kunne ba. Sajida tayi saurin kallo emran cikin mamaki ,cikin sanyayyiyar murya daya santa dashi tun farko haduwarsu tace "amman emran ai ya kamata.. "Yi min shiru muguwa in mugunta ce ai kanki kikayiwa bamu ba, Dan hk tun kan dare yayi miki ki nemi wanda yayi miki fyade kiyi masa wannan banzar kukan naki bani ba ,yakarasa mgnr yana saukar da numfashi zai yi mgn sai km ya fasa ya juya ya fita cikin bakincikinta. Sajida ta km fashewa da wani kuka yanzu ya zatayi kenan ? Tarasa fu'ad tarasa emran tarasa budurcinta tyi biyu babu..... ********** Kwana goma kenan sajida bata saka emran acikin idanunta ba ,kai ita kan tana cikin taskon rayuwa duk batagane abinda yake nufi da hkn da yayi mata ba ,ta mike jiki a sanyaye ta nufo hanyar parlour'n inda tasame shi zaune yayi tagumi itama ta nemi kujera kusa dashi ta zauna tana kallonsa kafin daga baya tayi ajiyar zuciya da numfashi atare sannan tace" emran ina son kasakeni....gabansa yayi wani irin bugawa saboda har ga Allah yana sonta ransa a matukar bace yake daita shiyasa ya shareta, amman ji mgnr banzar datake gaya masa,wani kallon wulakanci yayi mata sannan a matukar hassale yace"ai kin san yadda ake yin sake, ki dauko takarda da biyo kiga yadda bazan sakeba, aikin banza kawai yakarasa mgnr yana furzar da iska ta bakinsa. tsam ta mike ta shiga dakinta ta fito hannunta rike da fallen takarda da biro tazo ta mika masa gashi" ka sauwake min yanzu na bar maka gidanka dan konace zan cigaba da zama da kai ba daraja zanyi ba ,batare da bata lokaci ba ya amsa yasoma rubuta mata yana cewa "idan akwai gaba da gidana kije me ya dameni.. Cikin minti biyu yace "gashi ya miko mata takardarta "na sakeke saki biyu yana gama fadar hk ya mike ya bar parlour'n yana goge zafafan hawayen da suka zowa kuncinsa ,wannan shine karo na uku daya zubar da hawaye akanta Dan tunda yake baitaba jin bacin rai kmr na yau ba yadda ta nuna kiri Kiri bata son zama dashi ,alhalin shiya kamata ya gujeta gashi har yanxu zuciyarsa na tsananin sonta yana fita harabar gidan yakira mahaifinta ya sheida masa daga ya kashe wayarsa da zumar barin kasar a gobe goben nan. "dady yasoma tsarguwa aKan rashin zuwa safwan gidansa, alhalin yana kasar , amman kiran Gaugauwan da mahaifin sajida yayi masa ya hanashi nemansa a wannan lokacin, yana fitowa mead na fitowa agigice saboda labarin mutuwar auren sajida yasameta atare sukaje, koda ya isa tarin bakinciki ya iske,domin yana xuwa acp ya mika masa farar takarda da sajida ta bashi, yana masa karin bayani "bansan abinda yarinyar take nufi dani ba? "ta kashe aurenta batare da wani mahimmin dalili ba ," yanzu emran din ya kirani yake gaya min abinda ya faru sam banga laifinsa ba sai na wannan yar iskar yarinyar, ya dubi gefen inda take rukube yace "ba dai zaman gidan kike bukata ba gaki ga gidan ina tabbatar miki har ki kare rayuwaeki bazaki taba samun miji irin emran ba, tunda dady ya rike takadar yake zabga kalmar inna lillahi wa inna ilaihi rajiun "amman sajida baki kyautawa rayuwarki ba ke yanzu a tunaninki zaki samu kmr emran? ita dai kuka kawai take har da shesheka "dady ka rokon mun babana ya yafe min dan Allah nasan fushinsa atare dani babbar matsala ce "kinsa da hk kika ki zama a gidanki byn duk abubuwan da suka faru dake ,a wannan zamani wani nmj zai iya hkn? fad'a sosai dady yayi mata sannan ya bawa acp hakuri da nasiha "akan hk Allah ya kaddaro babu yadda zasuyi sai adduar, sannan yace tazo ta roki mahaifinta yafiya. akan hanyar komawarsu gida "yar baba dady yakirata "na'am babana "kwana biyu sai nake ganin wasu canje canje agame dake sannan safwan baya zuwa gurinki ,fatan dai lfy? Dan bana son asamu matsala irin na sajida dake. tayi shiru tana souronsa batare datace komai ba har ya dasa ayar mgnrsa, a zahirin gasky taso gaya masa gdkyr lamari amman ganin zuciyarsa a hannu take akan lamarin Sajida ,tayi tunanin tabari har su isa Gida. suna isa gida direba yayi parking atare suka fito tare da dady. "barka da cikar k'arin shrkara ....me'ad ,saitin data jiyo kenan ,wanda yasa ta waigo daidai inda tafi zaton daga nan sautin ya fito safwan tagani tsaye ajikin motarsa yana mata murmushin mai cike da farincikinki ganinta, da wasu kayayyakin kyauta gareta ,har da cak ,yakarso gurinsu yana murmushi ya mika mata wannan naki mead yayi mgn yana gaisar da dady cike da girmama"aiko dai na gode sosai tare da fadada murmushin fuskarta. dady yace "dan albarka mgnrka nake acikin raina ,suka karasa cikin gidan inda sukayi masauki a babban parlour'n gidan dady ya dubeshi "ya baban naka yake yana dai lfy ko? "yana lfy ,tare da kai cup din coffe bakinsa ita km me'ad tana daga gefen hannun kujerar dady"yana Dai kula da sukari ko? "narasa dalilin dayasa ya kasa barin shan sukari gashi yana tattare da ciwo , ga itama wannan hk take kmr sha xumamu take . "kai dady yaushe kake barina nasha ,duk wasu abu da suka danganci sukari in dai ba wai baka kasar nan ba mutun yasamu yasha gidanmu ya dawo tmkr sanssani sojoji takarasa mgnr tana me mikowa safwan tiren hannunta "a'a ki ci kawai na gode yayi mgnr idanunsa na kanta "dady bari na baku guri ina zuwa ta mike tashige ciki ,inda hira ta barke atsakaninsu har inda safwan ya zayyanewa dady komai dake faruwa fada dady ya rufe shi dashi "dan me zaka min hk?" idan ka daina sonta sai akace kabata damar cigabada soyaya dan talaka dan matsiyata "dady safwan yakirasa "karka damu wallahi ina son me'ad har yanzu, na dai barta ne saboda akwai taku dana shiryawa lamarin kasan yaran yanzu sai da rarashi da dabaru ta hkn ne kadai zamu samu abinda muke so, yanxu ma hk nazo ne mu fita domin tayata murna karin shekarrata, numfasawa dady yayi duk da yaji dadin rashin janyewarsa amman hankalinsa a matukar tashe yake banda gumi babu abinda ke fitowa daga cikin jikinsa. Safwan ya mike dady sai kajini zamu fita daita yanzu, km Dan Allah karkayi mata zance "dady bai yunkurin cewa komai ba ya fice yacigaba da zaman tunani da mamakin abinda ya faru agurin ina ai baya jin zai iya hakura da wannan tashin hankali yana zaune yaji tashin motarsu sannan yasamu ya yunkura da kyar gefen kansa na wani irin sara kmr zai rabe gida Biyu.. Washegari Da misalin Karfe tara na dare ranar ta yiwa fu'ad rakiya ya tafi tana dawowa ta cimma dady, zaune a parlour'n ya zabga uban tagumi yana huci takarasa ta sauke masa tagumi tace "dady'nmu lafiya ka zuba wannan uban tagumin hk? "Har nashigo bakasan nashigo ba. Ya dubeta sosai da idanunsa da babu sauki a cikinsu yace "mead. Bata amsa ba illa zuba masa idanu datayi saboda yadda yakira sunan nata cikin kakkausar murya. "Waye wancan yaron da kika raka yanzu? Ta sauke naunayen ajiyar zuciya sannan ta sunkuyar da kanta kasa batayi mgn ba saboda batasan abinda mgnr nata zai haifar ba, har da dady ya buga mata tsawa yace "Dan ubanki ba mgn nake miki ba? cikin sarkewar murya tace "dady kayi hakuri da...daman dady ina son sanar maka ko waye shi, sunansa fu'ad kuma muna son juna dashi dan har mun yanke shawarar yin au....ji kake dau..daun..dady ya dauketa da wani gigitaccen marin har guda uku dayasa ta hantsila tayi bayan kujera tare da ganin wasu taurari sun gilma ta cikin idanunta, take ta nemi ji da ganinta tarasa, dady yana huci yacigaba "yanzu abinda zaki mana kenan? "Tozarcin dazaki mana kenan? "Karamar yarinyar dake kinsa kan mugunta, kina kokarin yiwa iyayenki bakinciki saboda yanzu kina daukar salary mai tsoka "kina nufin bazaki auri safwan ba mai kaunarki da son farincikinki "me wannan tantirin yake dashi wanda yafi safwan? "Ke yanzu ko kunya bakiji ba ki rasa Wanda zaki so sai wannan mai wuyan kmr marakin leman dan talakawa Dan matsiyata? Me yake dashi ? "Me zai baki? Bashi da abinda zai baki tunda shima bai ci ya koshi ba ,wannan rayuwar kike ganin yayi miki daidai? ga mamakin dady sai jiyo sautinta yayi" ni babu ruwana dady da wani babunsa ,matsayi ko mukami ni shi din kawai nake so, km ni bakin safwan nake ba, kawai dai bazan iya aurensa bane nabar fuad ,ni dai dady kayi hakuri ka amince na auresa shi zuciyata take so muddin ban auresa mutuwa zanyi fu'ad nake so km shine zabin zuciyata"inna lillahi wa inna ilaihi rajiun yashiga furtawa yana maimaitawa tare da maida idanunsa kan momy da hayaniyarsu tashigo daita da suhailat momy kuka ta fashe dashi ita da suhailat ganin dady na fada tana fada akan nmj da bashi da tabbas . dady yace yanzu nufinki bazaki auri safwan ba ko me ? Ni dai kuyi hakuri wallahi banason aurensa "ashe kuwa zaki mutu ashe kuwa lokacin mutuwarki tayi kusa matukar baki auri safwan ba sai dai ki canza uba " mayaudariya maci amanar kauna, kin ci amanar safwan ,yaron na yana sonki ba tun yau ba, muryarta cike da shesheka tace "nifa ban ci amanarsa ba amman idan kuna bukatar lallai sai ya auri yar gidan ga suhailat nan kubashi ya aura ,wani marin ya sake d'auketa dashi "kinfi shi ido ne bai ganta ba yace ke yake so shashar banza da wofi maza tashi kibani guri kafin na tsine miki albarka keda zabin naki ... kafin ta yunkura yayi wani kwallo daita sai ga ta zube ajikin safwan da shigowarsa gidan kenan, tsam ya rungumeta jikinsa batare daya fuskanci iyayenta ba, hankalinsa yayi kololuwar tashi ganin yadda kamaninta ya sauya hawaye ne suka zubo masa lokacin dayaga nata hawayen na tsiyaya daga cikin kumburarun idanun "haba dady zaka kasheta dan tace bata sona? "Shi fa soyayyar d nan baa ayinsa dole dan Allah dady karka sake dukanta akaina nifa tuni na hakura ya fadi hk tare da mikar da tsaye bisa kafafunta "sorry kanwata kukan ya isa hk babu me miki auren dole"Ba dai fu'ad kike so ba? Ta daga masa da kyar "to kice ya turo iyayensa "no no karka min hk safwan ba dai iyayensa ba sai dai shi kadan sa tukun , yakarasa mgnr yana juyawa tare da goge hawaye . suhailat kuka momy kuka hatta safwan kasa rike kukansa yayi ita kuwa uwar gayya ji take idan duk duniya nan zasu taru akanta bazata auri wanda zuciyarta bata so ba fu'ad take so kuma shi zata aura. ******** Bangaren sajida kuwa babu laifi, ta saki ranta kad'an banda murnar rabuwa da emran babu abinda take, sai dai idan ta tuna tarasa budurcinta ,ranta idan yayi dubu yakan baci, acp na zaune a d'akin baccinsa yana sauraron BBC sajida tashigo jikinta a matukar sanyaye tasamu waje ta zauna kusa dashi jigun ranta a dan jagule saboda ganin halin damuwar dayake ciki a dalilinta, kallo daya yayi mata ya dauke idanunsa akanta, sannan cigaban da sauraron BBC, ahankali tasoma magana cikin sanyayyiyar murya" baba kasaki ranka Dan Allah akan yarka, kasamu yakini akaina na maka alkwarin cewar bazan baka kunya baba , ina tabbatar maka babu wani haufi akaina ni kaina nasoma nadamar abunda na aikata ... "me kike bukatar daga gareni sajida? "Amatsayina na ubanki nafi kaunar ganinki karkashin inuwar aure amman kika watsa min kasa a ido "Mai kike tunani duniya zatace akaina dake karon kanki? "Ina dai rokonka baba kayi hakuri ka kasamu yakini acikin zuciyarka akaina ni bazan sake baka kunya ba....ko fushin karya ma bana iyawa dake driya tayi sosai sannan ta mike ta bar d'akin cike da matsanancin farinciki mara misaltuwa . Mmn sudais ce 💗💗💗💗💗💗 'YAN CINKI 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 ~NA~ *AYSHA A BAGUDO* ~DEDICATED TO~ MRS ADAM ( YAR MUTAN KAGARA) Page 59 to 60 Not edit ........Sajida ta nufi d'akinta ta fad'a kan gadonta cike da matsanancin farinciki ji take tmkr tasamu fu'ad tagama , tunani ne ya fad'o mata a rai ta mike zumbur tayi bathroom tayi wanka, ta canja kaya zuwa wasu hadaddun kananan kaya, riga da siket blue da dan ratsin yellow,tasanya abaya ta yafa mayafi ta fito ,she look very attractive parlour'n kasa ta sauko adaidai lokacin da motocin mahaifinta suka bar gidan,sai aunty nadiya mai aikin da'aka samo musu ce a tun sanda aurenta ya mutu a zaune ,sajida batayi mata magana ba sai ita aunty nadiyar ce tace, dining fa ya kammala . "No karki damu aunty,zan fita ne but yanzu zan dawo takarasa mgnr idanunta na ga duban agogon bango parloun dake walwalin haske kwan fitila ya sake kara haskawa, karfe 12 na safe yanzu ta wuce, aunty nadiya tace sai kin dawo. . kai tsaye motarta tashiga ta nufi gidansu misna, kmr koda yaushe momyn misna tana kitchen tana aiki domin akwaita da kaunar girki, wanda hkn ke sata tuno da amminta sam itama hk take da son girkin tsiya dan wani lokacin babanta kance "Kyan 'ya tagaji uwarta amman ke sam baki d'aukota a komai ba... Ita kuma sai tace masa" ai shi ta gado tunda ba asan nmj da shiga kitchen. ba... ta gaidasheta kana ta nufi dakin misna straight ,akwance ta tarar daita tana kallo a zeey world misna naganinta ta mike zaune da murnarta ta rungume sajida ajikinta tana jin dadin ganinta cikin koshin lfy bakamar kwanakin baya ba, itama sajida ta rungumeta tana jin dadi aranta, tana matukar jin dadin yadda misna ke nuna mata kauna sajida tace "wani guri mai mahimmanci nazo ki rakani "a tunanin misna ko gurin shakatawa zasu kasancewar tasanta da son zuwa irin wuraren. da azama misna ta diro daga kan gadonta tare da daura after dress akan riga da wando datake sanye dashi domin fitowarta wanka kenan , tare suka fito misna na rolling mayafin after dress akanta umman misna tace "sai ina adaidai wannan lokacin? Sajida tace "umma fita zamuyi amman yanzu zamu dawo, umma tace " karfe 1 ta kusa kuje kuyi sallah sai ku zo kuyi lunch sannan rana ta fara yin sanyi sai ku fita, babu musu suka bi umarninta suka koma d'akin sukayi sallah sannan suka ci abinci Wanda sama sama sajida taci dan ta matsu bata isa inda zuciyarta ke bukatar zuwa ba, sun fito suna yiwa umma sallama tace "karsu dade . tafiya suke ahankali sajida ke jan motar muryarta a raunane sajida tace "kawata baki tmbayeni inda zamu ba ? "tambayar mai zan miki byn nasan wata killa wajen shakatawa zaki. "No kin sa'ba tsaitin tunaninki ,domin kuwa ba nan zamu ba ,kina jina ko a watanin baya da suka gabata kin sha ganina cikin tashin hankali da damuwa wanda kowa ke bukatar son sanin abinda ke damuna alokacin, amman naki bada wannan kofar ,sai dai a yau zuciyata ta aminta da nasar miki da damuwata ,bisa aminta da zuciyata tayi dake, me'ad itace wacce tafi cancata tasan matsala fiyye da kowa a duniya, sai dai al'amarin damuwata ya danganceta..kina saurarata kuwa? "Ina jinki sajida sai dai maganarki tasanya kuzarin jikina yin rauni . "karki damu da furucina nasanki, nasan halinki da zurfin ciki duk wuya duk runtsi akayi sirri dake baza ta'ba jinsa akoina ba shiyasa nasanyoki cikin abinda yashafi sirrikan rayuwata. Taja numfashi ahankali ta fitar tana mai karya kwana wanda kai tsaye inda tasan fu'ad yake zama tare da abokansa ta nufa daga nesa kad'an da gurin tayi parking ta tsura masa idanunta sosai kmr zata fixgosa gareta, yana zaune tsakiyarsu kabeer suna hira wanda ba kasafai yake sanya bakinsa ciki ba. kallonsa kawai take bata ko kifta ido, ga wani irin kalar murmushi datake masa wanda ita kanta batasan tanayi ba balle wanda ake dominsa, tsawon lokaci tana zaune tana kallonsa taji an hura mata iska a idanunta, tayi firgigib ta dawo haiyacinta tana duban misna dake zaune a gefenta ," misna a yau nake son shearing wani abu daya danganci rayuwata dake "waye wancan dake zaune tsakiyar maza uku din can sanye da t shirt fari da bakin wando? tayi mata tmbyr tare da d'auke idanunta akanta ta maida kan fu'ad da bai san wainar da'ake toyawa ba . Ahankali misna tace "Idan dai har idanuna nagani kmr yadda nayi zato fu'ad din me'ad ne zaune....... "yauwa yar gari sai dai kinyi kuskuren kiransa da fu'ad din me'ad ne ,kice fu'ad din mai raboz saboda shine mutumin da zuciyata ta kamu da matsanancin kaunarsa, shine mutumin daya hanani walwala da sukuni, shi mutumin da tuaninsa ya dusashe tarin soyayyar emran acikin zuciyata ,har nake ganin duk mazan duniya mata ne shi kawai ne tsayayen nmj... "what ..kina mafarkine sajida? "Idan mafarki kike maza ki farka "karki manta halakar dake tsakanin iyayenku daku kanka, "meyasa zakiyi hk sajida? "Gsky banji dadin furuncinki ga abinda aminiyarki take so tmkr ranta ba .."nasani misna amman ya na iya da rayuwata, me'ad ce silar faruwar komai "itace ta nuna minshi daga kallo dayan dana masa narasa gane kaina,"yanzu dai ki taimakeni ta yaya kike ganin zan mallakesa shine abinda nafi bukata daga gareki? Naunayen ajiyar zuciya misna ta sauke da karfi "azahirin gsky ni banida wani taimako da zan iya miki daya wuce kiyi hkr ki hakura dashi domin shine zaman lfyarmu da kwanciyar hankalinmu kafin mead tasan da wannan zance. "haba haba sam wannan abu baiyi min dadi ba,aminan juna daku kuna son abu daya......."ki hakura dashi sajida ,a gsky banji dadin yadda kikace saboda shi kika kasa zama da emran ba domin emran masoyinki ne na hakika wanda samun irinsa ke wuya . "shawara nake bukata daga gareki bawani zance emran ba " matukar shawara kike bukata daga gareni ki cire soyayyar fuad acikin ranki ki fawwalawa Allah komai shi yasan yadda zaiyi da al'amarinsa ,babu mamaki akwai manufar da Allah yake nufi daku ,da har yasa kuka kamu da son mutun daya, mutun dayan kum wanda ya kasance bakowa ba face talaka ... Sajida ta daina sauraron misna ta meida hankalinta sosai gurin cigaba da kallonsa har sai dataji zuciyarta tasamu natsuwar datake bukata sannan taja motarta ta gabansa suka wuce amman bai san ko su waye ba kasancewar glass din motar baki ne, ta sauke misna a gidansu sannan ta koma gida cike da tunanin misna. "An kuwa zata iya rabuwa dashi? "idan ta rabu dashi tayi yaya da rayuwarta? "kenan rayuwarta zata zamo abar tausayi babu emran babu shi babu budurcinta...... ina da sake. Zuwan fu'ad biyu amman me'ad batayi kokarin sanar masa da sakon mahaifinta ba ,yanzu ma tsaye suke a harabar gidansu tayo masa rakiya motocin safwan suka sanyo kai cikin harabar gidan, tundaga nesan daya hangosu kirjinsa ke bugawa har zuwa sanda suka isa inda aka tanada domin ajiye motoci ,bayan an yi parking,ya yunkura da kyar yasamu ya fito sanye cikin riga da wando sai yar saman suit dake saman farar longselve, ya kirkiro dariyar dole yakaraso zuwa inda suke alokaci daya zuciyar fu'ad data safwan ta buga rasssssss atare batare da suncewa juna komai ba sai me'ad ce ta bud'e baki tana murmushi "fu'ad ga yayana safwan....safwan yayi saurin runtse idonsa sbd zuciyarsa dake na wani irin harbawa kmr zata fasa kirjinsa dan ji yayi kmr an diga masa ruwan dalma, sannan ta juya ta kalli safwan tace "yaya safwan ga fu'ad Dina....ahankali ya bud'e idanunsa ya daura akan fu'ad daya tsareshi danashi idon kana jiki a sanyaye suka mikawa junansu hannu domin gaisawa " mlm fu'ad ya gida da aiki? "Lfy fu'ad yace atakaice saboda ganin irin kallon kasan dayake masa mai had'e da maxurai da rainin wayo da murmushi ahad'e. Hannunsu na sarkafe cikin juna safwan yace "gsky kanwata kin iya zabe ..."allah ko yaya? "Kwarai kuwa...da gaske, kin kuwa gaya masa sakon dady ? Numfashi taja ta sauke da kyar kana tace"Abinda nake shirin yi kenan kashigo "ok kiyi kokari ki sanar masa idan da wata matsala ki hanzarta sanar min "ok yaya na gode da kulawarka . "No karki damu kanwata any for you ya juya zuciyarsa na farfasa, ya nufi cikin gidan kmr zai kifa tsabar duhun da zuciyarsa tashiga har yayi dayasanin zuwansa gidan bayansa fu'ad ya tsurawa idanu duk bai jiyo ba yana iya ganin yadda numfashinsa ke fita da karfi. byn shigarsa cikin gidan fu'ad yayi mugu mugun tsareta da ido "kikace wannan mutumin yayanki ne ? "eh tabashi amsa tana kallon cikin idanunsa. "Uwa daya uba daya? " no D'an aminin kuma mai gidan dady ne,"wani abu ne ?girgiza mata kai kawai yayi "yanzu dai kaji da kunnenka dady nason ganinka ya kenan? "Ok badamuwa zuwa yaushe yake son ganina? "anytime you are free ,"ok mubarshi nest week saboda gabadaya satinan zanyi busy kema bazaki samu damar ganina ba har sai nagama abinda nake, jin hk yasa ta narke masa fuska kmr zatayi kuka "har next week fa kace , kasan kuwa yadda nake ji idan nayi kwana daya ban sanyaka acikin idanuna ba ? "Ji nake kmr ana fixgar numfashina ni dai kasan yadda zakayi, ko kazo ko sau biyu ne naganka ,ko kuma ni na sameka inda kake. Murmushin yayi sannan yasoma rarrashinta sai daya samu ta dawo normal sannan ya wuce. Kwanakin nan gbdy acikin kunci da damuwa mead tayisa sakamakon rashin ganinsa Dan hk randa yazo da zumar ganin mahaifinta tana ganinsa bata tsaya wata wata ba ta rungume shi ajikinta tana farinciki ,saurin d'auke numfashinsa yayi saboda jin diran nonuwanta bisa kirjinsa atare sukaji tmkr Wani irin abu yana masu yawo a gabadaya ilahirin jikinsun me kama da shocking wanda take ya haddasawa nata kirjin bugawa yayinda shi km a take kwakwaluwarsa ta d'auki caji , cikin wani irin murya yace " my love you kinzo min da wani irin salo mai tsayawa a zuciya, kar da kisa nayi abun kunya a gidan siriki, a yadda yayi maganar bakaramin rud'ata yayi ba ....jin yanayinsa nason canzawa yasashi zareta ajikinsa yana fitar da wani irin numfashi da kyar da sauri ta ita kuma ta fita daga cikin parlour fuskarta cike da fara'a, itama wani irin kalar numfashi take ,a yanzu ji take ina ma amatsayin mallakinsa take. "tun bayan fitarta fu'ad yafara jin caji ajikinsa, ahankali yake jin wani feelings na bijirowa a gangar jikinsa ,lips dinsa na kasa ya ciza da matukar karfi kmr zai datse harshensa, sannan yayi saurin batsar da abinda yake jin yana masa yawo ajiki kana yacigaba da zaman jiranta. Cikin wasu yan mintunoni da basu wuce biyar ba ta sake dawowa karamin parlour'n dayake zaune zaman jiranta "taso muje zuwa ga babban parlour'n dady inda anan dady zai ganka ,bakinsa d'auke da sallama yashigo cikin hadadden parlour'n ,inda suka iske parlour'n empty babu kowa cikinsa sai k'aran tv plazma dake manne da bangon parlour'n yana aiki acikinsa hannunsa ta kamo zuwa kan kujera "ka zauna yanzu dady zai shigo, gyaran murya yayi mata batare da yace komai ba illa idanunsa dake yawo a sansar jikinta, ta juya cike da rausaya ta nufi cikin gidan tana daddana number safwan kira daya ya dauka "ya'akayi ne kanwata? "kazo yanzu ga fu'ad yazo dan Allah nafi son duk abinda za'a yi kana nan domin nasan zakayi controlling din dady . Tunda tasoma mgn numfashinsa ya nemi dauke amman yayi saurin sanyawa jikinsa jarumtar cewar"ok karki damu gani zuwa just give me some mint. byn kmr minti 30 sai ga dady yashigo parlour'n yana dingisawa fu'ad naganinsa yayi saurin mikewa tsaye cike da girmamawa yana mai gaishe dashi "uhm kawai dady ya iya cewa sannam ya zauna tare da cewa "kana iya zama. fu'ad ya Zauna zuciyarsa na d'ardar dan ganin yadda mahaifin me'ad ke kallonsa kasa da sama wanda hkn yake nuna alamun bai yaba da ganinsa ba . yayinda me'ad tasake dawowa parlour'n tare da tsayawa a bakin kofar shigowa ta tsurawa fu'ad ido dady ya yi gyaran murya kana yace "me za'a kawo maka? shayi ko lemo ko... "no no dady ba sai an kawo min komai ba ,nagode "uhmm kasha wani abu mana kai kuwa ? cike da in ina fuad yace "to ruwa ma kawai ya isa . "ruwa fa? mahaifin me'ad ya fad'a yana jinjina kai .fuad yace eh shi kawai ya isa. kai kuwa "ya zakazo gidan masu abun kace ruwa kawai zaka sha any how mead kawowa bakonki abinda ya bukata ta juya, jiki a sanyaye ta nufi kitchen dan sam bataji dadi irin tarban da dady yayi masa ba, byn fitarta dady ya fuskanci fu'ad yana tsare idanu tun kafin yasoma magana safwan yashigo cikin parlour'n cikin sallama sanye cikin kananun kaya wad'anda suka mugun amsar jikinsa sai kamshi dadden turarensa yake bazawa ya gaishe da dady sannan yakarasa ya mikawa fu'ad. Hannu"barkanmu da warhk? Shima fu'ad Hannu ya mika masa suka gaisa sannan ya samun guri ya zauna shima yana fuskantar fu'ad , yasanya hannunsa daya yayi tagumi yana cigaba da kallon fu'ad "me yafi shi har da me'ad ta zabesa ta barshi? kyau ilimi tattare makudan kudaden da shi kansa bai san adadinsu ba, duk yafi wannan dake zaune a gabanshi.. "a ina kake da zama sautin muryar dady ta karade parlour'n zuwa cikin dodon kunne fu'ad "ina zaune a gbegulori dake kan titi capito road "uhmm anan kake zaune tare da iyayenka? "eh ana nake tare da kakata dan tun daga haihuwata mahaifiyata ta rasu byn wani lokaci shima mahaifina ya rasu yanzu dai ina tare da kakata nake zaune. "ayya ina mai jajanta maka Allah ya jikansu. "Ameen na.. na gode dady. Cikin hk mead tashigo ta ajiye tire dake dauke da nauikan abinci ta juya tanayiwa safwan alamar ya taimaka komai yazo karshe sannan tabar gurin. Dady yacigaba"da dukan alamum kakarka tana riritaka dayawa ? fu'ad yayi muushin jin dadi tare da sakin jikinsa kad'an dan da adirice yake ,sannan yace azahirin gsky hk ne Sabod tana matsananci sona sosai "ya isa me kakeyi ahalin yanzu aiki ko karatu? "gsky babu abinda nake ahalin yanzu ina dai kan neman aiki a tun bayan dana gama digri Dina Amman har yanzu ban samu ba shiyasa na yanke shawarar soma sana'ar kasuwancin.. "idan na fahimci maganarka baka Da aikin yi, kai mutun ne dakayi karatu amman baka da tsayayen aikin yi, safwan kana ji fa da sanar da bai kai ga samu ba yake neman diyar babban gida ko dai baiyi karatun bane? "a'a dady digre gareni nasan zuwa yanzu nasan abinda kake son kace amman na rantse maka da Allah zan kular maka da me'ad sosai fiyye da yadda kake tsammani "uhm kace kayi karatu geo ko history ka karanta? "aa kasuwanci na karanta zaka iya kallon abun wani iri Amman muddin me'ad na tare dani kusan babu abinda bazan iya mata ba, ko maye zanyi domim na bata farinciki da..... "ya isa hk malam dady ya katseshi yana mazurai da "Karka cikani da wannan surutain banza da wofi "meye matsayinka? "kai fa ka kasance yaro ne mara zuciyar neman na kansa wanda kakarsa ke ciyar dashi tare da bashi kudin kashewa, yayi gantali yayi can yayi gantali yayi nan rayuwar kenan wadan nan takalman da kayan jikinka da machine din dakazo dashi da kudin wa kasiya? mu dubi komai a zahirance mana sannan musa gsky a hurumunta mana "ta yaya kake tunani zan dauki diyata me'ad nabawa mai matacciyar zuciya irinka? "na d'auki diyar dana fi so na aurawa ga wanda gabadaya rayuwarsa sipili ce a tunaninka hkn zai yiwu? fu'ad da kansa ke sunkuye ya dago a matukar firgice yana duban dady kamin yayi magana dady yace "ysushe kasan me'ad? "karkari tsawon wata shida. ran fu'ad ya sake kaiwa kololuwa gurin tashi ganin ga safwan zaune amman yaki takawa dady burki gashi dady bashi alamun saida zancesa hkn kuma still safwan na kallonsa A wulakance yana masa murmushin da bai san ko na mene ba, ya bude bakinsa da kyar yace "yallabai ni dai nasan idan kabani auren yarinyaka zansata farinciki "me kake bukata atare da mutun adali ince na natsuwa nagarta mai kamun kai mara shaye2, to duk ina cikin abinda na lisafa maka, ince duka matsalar akan ta rashin aikin yi ce? "ka zuba ido kagani nan gaba da kayan aiki zakaganni ,zan tabbatar maka da kai.. "meye abun tabbatarwa yaro byn gaka agabana da shirman rayuwarka zaka tabvatar min da kanka ko me? dady yakarasa mgnr yana murmushi safwan kaji fa, "wai shin wani shirin wasan kwaikwayo akeyi anan ne ko me? "wai tabbatar da kansa yake son yi wa uban me'ad yakarasa mgnr yana dry "babban magana kenan "mai yawo a gari babu aiki yake son tabbatar da kansa shi dai safwan bai ce ta tafar ba illa dryr dayake ta kunshewa saboda gabadaya maganganun dady sun matukar yi masa dadi da sanyaya ransa.. "kasani diyata me'ad nada alkwarin auren wani akanta attajiri Wanda ya fika a komai na rayuwar duniya dan hk kwarya tabi kwarya a gidan baka da matar aure period mgn ta karshe kar na sake ganin kafarka gidana.. fu'ad yasoma kokarin mike tsaye "sai anjima yallabai nagode da lokacin daka bani wani irin kallon kaskanci dady yake binsa dashi yayinda har wannan lokacin fuskar safwan kumshe take da dryr mugunta. jiki a sanyaye fu'ad yakarasa mikewa yana gyara rigarsa ta baya sannan yasoma daga kafafunsa kmr kazar da kwai ya fashewa aciki ya nufi inda yayi parking din machin din kabeer daya aro, ya hau ya zauna amman ya kasa tadashi sai dai ya kwantar da kansa kan mashin din, bai yi auni va sai jin danshi yayi akan fuskasa ya mika hannunsa ya shafo hawaye ne, shi kansa yayi makakin dalilin zubarsu akan mead ne da zai rasa ko kuma akan tozarcin daaka masa ne ? yafi minti talatin a haka kamin yasoma kokarin tayar da machine ,masu gadi suka bude masa kofar get ya fita, ya yarda bazai samu me'ad ba har abada. shi ba aure yadamu dashi ba da wuri kasancewarsa saurayi da bai taba aure ba, km ba shashanci yake ba balle ya tancance yanada bukatar mace yanzu ko aa, me'ad din kawai yake so, soyayyarta ce tasanyasa son yin aure a halin yanzu. meyasa mead tayi masa hk ?"me yasa ta boye masa akwai alkwarin auren wani akanta? tayi masa wasa da zuciya da hankali har ya iso gida bai san inda hankalinsa yake ba kuma tmbyr dayake son yayi mata kenan "hakika tayi masa wasa da zuciya, dan bazai iya cewar ta yaudaresa ba ,dan ya yarda da son datake masa na gaske ne, sannan na tsakani da Allah .. Da yammacin ranar sai ga mead tazo gidansu sakamakon abinda safwan yagaya mata daya yayi masa, da kunneta km taji lokacin da safwan kebawa dady hkr da kokarin shawo kansa daya amince da auren albashi sai su tsaya masa yasamu aiki,inda ta lsamu fuad zaune kofar gidan inna ,yana kallon sararin samaniya, da yadda hadari ya hado agarin,a zahirin gsky zaka dauka yana nazarta yanayin zuwan ruwan saman ne, amman sam abun ba hk yake ba tunanin rayuwa yake, tunani yadda rayuwa take shirin tagaliliya dashi yake, har sanda takaraso garesa bai sani ba sai jin laulausar tafin hannuta yayi saman nashi, wanda hkn yasa shi juyowa ahankali tare da sauke naunayen ajiyar zuciya ganin itace ,sai dai ganinta ya zafafa mikin dake cikin zuciyarsa, atake ransa ya sake dugunzuma, ya cire hannunsa daga nata yana mai basarwa sannan muryarsa a dakile yace"mai ya kawo gareni? "Dan Allah kibar nan tun raina bai gama dagulewa akanki , banason kusancina dake."to saboda meye fu'ad? "Saboda kin kai ni ga mahaifinki ya tsarkafeni da sarkafaffun tmbayoyinsa marasa maana da tushe , ya bata amsa a matukar fusace yana mai maida idanunsa sama jin har ansoma yayyafi. "karkayi wannan maganar fu'ad daman irin tambayar da iyaye sukayi kenan , kasa kanka amatsayin mahaifina ka duba Alamarin....dan Allah dan Annabi malam ya isa hk kawai kin gayuaceni zuwa gidanku dan aci mutuncina akaremin tanadi da tozarci ,shi kuma wannan tantirin safwan din yana zaune agurin yana min dariya "ka daina magana ta shirme mana safwan mutumin kirki ne karka tuhumaishi acikin wannan matsalar "oho ni kuma mutumin banza wanda bayada aikin yi, dan jagaliyar titi daya fada soyayya da yar babban gida, in da kace masu kudi kawai suke da alhakin da yancin fadawa soyayya ,da soyayya tayi karanci a duniya, fuad ka daina daga murya mana kana jawo hankali mutane garemu. "Gara na daga sautin muryarta ansa kece kebibiyata har kikayi silar da yau aka tozartani, banki kowa yafito yasani ba, kece kika tallata min kanki akan soyayyarki ina zaman zamana cikin rufin asirin Allah "dan Allah karkayi magana cikin fushi har da kake wani shir...datse harshenta tayi da karfi takasa karasawa. ".Kwarai kuwa dole kice hk tunda kina son kare gidanku da ahlinki, an wulakantani sam baki damu ba suna kina sona kin wani kwaso shirmen jikinki kinzo kina kara gaya min maganganu banza, sai danazo na fuskanci mahaifinki nagane irin kuskuren danayi ,ba dai aiki ba,to bazan nemanba ,km Zan aureki da rashin aikin nawa domin na tabbatarwa mahaifinki ko babu aiki zan iya kula dake yadda yakamata . wai mgnr tawa ahlin gidanku suka meida abar dry, wanda wannnan abun daaka min ina da tabbacin safwan yana da hannu aciki kuma shine ya ziga babanki akan hk. "Fu'ad ka daina magana hk mana, domin magana cikin fushi bashi da fa'ida, sannan ni ina da tabbacin babu ruwan safwan cikin wannan matsalar, "ai magana ce ta gsky idan tazo a fadeta baka da aikin yi, ko kana da? Ta jiho masa tambayar tana kallon cikin kwayar idanunsa wani irin kallo yayi mata .. "Kuji wawiya da wata wawiyar magana ya furta hkn adaidai lokacin da ruwan sama ya sauko kmr da bakin kwarya,yacigaba "ai ban tabasanin cewar ke din shasha bace sai yau, tun farko da kika nacewa sona aikinsa bana aiki ko baki sani ba ? Shima yayi mata tmbyr yana tsare gira da kamewa "oho zuwa yanzu soyayya da mutuntakan dake tsakaninki da safwan zai iya sa ki mance hk ba..? "Bari kiji nagaya miki abinda bakisani ba nasan komai tsakaninki da safwan, tundaga farko har karshe ko last week da kuka fita yawon celebrating din birthday dinki ina sane...nasan kunyi soyayya dashi ...,a yanzu kuma yaudararki yake,da furuncin ya janye batun aurenki, kina sona zaki aureni amatsayin danake. .ki tabbatar da kin rabu da safwan rabuwa ta har abada, idan ba hk ba kisawa zuciyarki fu'ad ba rabonki bane na wata ne ,yana gama fadar hk ya juya yasoma daga kafafunsa. jikinta na rawa tabiyo bayansa tana kiran sunansa fuad ka tsaya dan Allah ... Bai tsaya ba har sanda ta isa garesa ta riko hannunsa ya juyo a fusace yana dubanta "idan na tsaya na miki meye?"narigada nagama magana period sannan ki tsaya daga nan domin idan kikayi gangancin biyoni,har kikayi silar shigar innata damuwa zan miki abinda bakiyi expecting dinsa daga gareni ba. juyowar nan da zaiyi yasanya hannuwansa ya goge fuskarsa sai yaga innarsa tsaye a bakin kofa tana kallonsu ,wacce tun da zu take tsaye agurin juyawa tayi cikin gidan, nan shima yashiga ya samu guri ya zauna agefen gadonta batare daya cire kayan jikinsa ba,inna dake sharar hawaye takaraso garesa ta dafa kafadarsa ahankali sannan tasanya dayan hanunta bisa kansa, inda gbdy ta fashe da wani irin kuka mai cin rai tare da rungume kansa a kirjinta shima kukan yake son yi amman ya dake. *********** Yadda fu'ad ya kwana bai runtsa ba ,haka mead ta kwana juyi akan gadon ta,duk inda ya juya maganganun mahaifinta ke masa kuwa ya yarda ya amince ya saduda ya amince mead ta haramta garesa, soyayyarsu tazama mafarki mai dadi irin wanda dan adam kanyi, ya farka yana mai cizan yatsar kasancewarsa, tunda har mahaifinta yayi wannan hukuncin, dreams are conceived but not all dream 'a are born alive some are aborted, others are stillborn ya juya ya kalli su jabeer baccinsu kawai suke cikin sukuni alamun basa cikin matsalar rayuwa sannan basu san menen kalmar da ake cewa so ba . aganinsa babu masu saa aduniya kmr su ,tunda basu zuki gardi da dadin tattare da dacin dake cikin so baz gashi dai sun fisa rawar kai akomai amman basuyi gangancin sanya kansu cikin soyayya ba balle har tazo ta damesu tazame musu kmr cutar cancer, wanda abu ne dake yawo yayi can yayi nan tunda yana faruwa da zuciya ne kawai, amman daga baya sai ta kurda cikin kasusuwan mutun ta gyaraye koina bargo jijiya da jinin jiki har da gabadaya gangar jikin Dan Adam. wayarsa dake wuriri akarkashin pillow'NSA yasoma ruri ,tunin ya gane msi kiransa mead ce adaidai wannan lokacin yaki dauka hk tayi ta kararta tagaji "mai zata ce masa da zai fahimta? Bazai sake yarda ta luguiguita masa zuciya ba, ya yarda ya amince tunda har mahaifinta yayi furuncinsa garesa bazai bashi auren yarinyarsa ba . Ta kirasa yafi sau goma amman bai dauka, daga karshe ma yaka kashe wayar gabadaya ya kife kansa jikin pillow tare da lumshe ido cikin halin tausayin kansa, Dan ganinsa ita mead ba abar tausayi bace .... Mmn sudais ce 💗💗💗💗💗💗 'YAN CINKI 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 ~NA~ *AYSHA A BAGUDO* ~DEDICATED TO~ MRS ADAM ( YAR MUTAN KAGARA) page 63 to 64 ........Wannan ihun da karen ke yi babu kaukautawa ,yasa gabadaya jami'an tsaro dake harabar gurin, yi masa caa aka tare da saita bakin bindugunsu a daidai saitin kwalkwaluwasa suna mazurai da idanuwa tmkr zasu cinyesa . nan take tsoro da matsanancin firgici ya bayyana a Kan fuskar fu'ad, ba iya zuciyarsa kad'ai ke rawa ba hatta gangar jikinsa kyarma yake, tsabar firgici da tashin hankalin daya tsincin kansa ciki a karon farko a rayuwarsa, sai zare manya idanunsa yake yana duban tarin jami'an tsaron dake zagaye dashi yake. Kai tsaye jakar kayansa aka soma bincika , abin mamaki ana buɗewa sai ga cocaine , ba ƙaramin tashin hankali fu'ad ya sake tsintar kansa ciki ba ,zuciyarsa ta tsaya cak na wani lokaci ta daina bugawa ,kafin daga baya tasoma bugawa da karfi karfi kmr ana buga mata guduma , nan da nan aka yi arresting din shi, duk ƙoƙarin da yayi don nuna musu ba shida hannu a laifin da ake tuhumarsa dashi basu saurare shi ba, suka tasa keyarsa aka wuce da shi wajen Binciken manyan laifuka. Tsaye yake agaban shugaban jami'an tsoro na jahar gbdy, hannuwansa duka goye abayansa, yana kallon mutumin dake gabansa kmr yadda shima yake kallonsa, tsawon minti goma sannan sir kola saraki ya d'auke idanunsa akansa yace ,"fu'ad sunanka ko? Cikin sauri fu'ad yace "eh yallabai. "Ka natsu ka kwantar da hankalinka ,yanzu ka gaya mana suwaye suka sakaka wannan aiki? "ina mai tabbatar maka matsawar ka sanar mana da ko su waye suka saka ,zan sa a sakeka salin alin batare da wata damuwa ba . "Wallahi wallahi!! yallabai bansan komai ba akan abinda ake tunhumata dashi ba ,salima ban san yadda akayi wannan rud'anin ya faru ba ... "Dakata malam ,karka mana karya mana, ko bakason ka tsairatar da rayuwarka ?"yimana karya daidai yake da salwantar da rayuwarka a gidan yari. .. Cike da matsanancin tashin hankali fu'ad yace "wallahi ni dai babu wanda yasani ,sannan bansan lokacin da hodar ibils tazo cikin jakata ba,ka taimaka yallabai wallahi bansan komai ba yakarasa mgnr hawaye nabin kuncinsa...... Sir kola yayi shiru kawai yana kallonsa yana nazarinsa batare dayace masa komai ba ,tabbas alamomi sun suna kmr bashi da masaniya akan abinda ake tuhumarsa, amman kuma zai iya yiwuwa yakasance yana sane tare da sanya hannunsa ciki , Dan kusan mafi akasarin wad'an da ake kamawa da wannan laifin kowa haka yake cewa. Kai tsaye sir kola yace a fita dashi, ana fita dashi d'akin horo akayi dashi ,aka shiga dukansa domin ya fad'i gsky Yin duniya akayi dashi Amman yace shi bai san komai ba ,Dan haka akayi magark'ama dashi, ranar sam bai runtsa ba ,tunanin duniya yayi akan lamarin Amman ya rasa ta inda wannan abu ya faru dashi.. ************* Bayan watanni uku da faruwar wannan al'amari, me'ad na xaune tana kallon labarai sai kawai ji tayi an ambaci sunan fu'ad tare da cewa ana tuhumarsa da babban laifin xuwa ƙasar England da hodar iblis, ba ƙaramin tashin hankali me'ad ta shiga ba, gaba daya ji tayi hankalinta na kokarin fita daga gangar jikinta ,saboda damuwa da halin da fu'ad ke ciki, ihu mai ƙarfi ta saki ta zube kasa sumammiya, bata tashi farkawa ba sai ganinta tayi a gadon momy ,tana tambayar ta "Tunanin me kike yi haka me'ad kike so ki jefa Rayuwar ki cikin haɗari? idan wani abu kike buƙata kamata yayi ki fad'a mana amma ba ki rika ƙoƙarin hallaka kanki da damuwa ba. Cike da ƙarfin hali ta d'ago idanunta dake cike da ruwan hawaye ta kalli momy dashi sannan ta bude bakinta da kyar momy"ina cikin tashin hankali da damuwar da ku kad'ai ne xaku iya yi min maganinta, amma nasan ba lallai ne ku lura da halin da nake ciki ba" Cike da tausayawa momy ta tambaye ta "fada min ko menene Ni kuma nayi miki alƙawarin xan yi miki maganin matsalar ki matuƙar dai Abin bai fi karfina ba" Muryarta na had'ewa tace "momy fu'ad nake so shi nake son gani a tare da Ni shi kad'ai ne farin cikina idan baki nemo min shi ba hakan xai iya xama silar ajalina" A razane momy ta kalleta "Amma ba ki da hankali me'ad ban san har yanzu ke shashasha bace sai da kika yi wannan Maganar me xaki yi da fu'ad ? "yaron da aka kama shi da babban laifi irin wannan, yaron da ƙarshensa mutuwa ce makomarsa me xaki yi da gawa me'ad? A daidai wannan lokacin da suke magana dadyn me'ad ya shigo, cike da nutsuwa yake takunsa har ya karaso inda suke. "Lafiya momyn me'ad me yake faruwa?" Sauke ajiyar zuciya tayi, "wai yarinyar nan har yanzu bata hakura da yaron nan fu'ad ba, a kansa xata jefa rayuwarta cikin haɗari, anya yaron nan haka ya bar me'ad kuwa abin yayi yawa haka"? Dady na jin abinda momy ta fad'a fuskar sa gaba ɗaya ta canja babu annuri ko kad'an a tattare da shi. "Me'ad!!!" A hankali ta d'ago ta kalle shi tare da cewa "Na'am daddy" Gyara tsayuwarsa yayin "indai Ni na haife ki nayi rainonki na hidimta miki kamar yadda kowane uba yake yiwa d'ansa baki isa ki auri fuad ba ko da hakan xai yi sanadiyyar mutuwar ki, don haka ki sa a ranki babu ke babu tarayya da ɗan matsiyata mara tarbiyya,mai safarar hodar iblis. Cikin ƙarfin hali me'ad ta tashi daga kwanciyar da tayi bata san lokacin da bakinta ya buɗe ba ta fara zazzaga bayani. "Daddy baxan iya rabuwa da fu'ad ba har abada saboda ina son shi, duk wannan halin da ya shiga ku ne sanadin sanya shi a wannan hanyar saboda kun nuna bakwa son talaka kuma baxa ku bashi aurena ba, saboda ba shi da abin duniya, xan sadaukar da raina da Dukkan farin cikina wajen ganin na fitar da shi daga Wannan halin da yake ciki" Tashi tayi ta sauka daga kan gadon da kyar tasoma kokarin barin bari d'akin sai taji dukkan ciwon da ke damunta ya tafi, sai ma wani ƙarfi da taji a jikinta. Kai tsaye wajen wani abokin karatunta ta nufa ,wanda yakasance lawyer ne mai zaman kansa, tana xuwa ta labarta masa halin da fu'ad yake ciki ba ƙaramin tausaya masa yayi ba, ya kuma yi alkawarin xai bi diddigin shari'ar har a gano mai gaskiya. Ba a ɗauki lokaci mai tsawo ba lawyer ya fara aikinsa, inda aka je airport din da aka kama fu'ad aka gudanar da bincike mai tsanani, cikin ikon Allah aka gano cewa akwai hannun wasu ma'aikata a Cikin laifin waɗanda aka biya su don su kullawa fu'ad sharri. A ranar da Court xata xauna don xartar da hukunci aka shigo da wadanda ake tuhuma, ba tare da bata lokaci ba kowannen su ya amsa laifinsa kuma suka shaidawa kotu cewa Safwan ne ya basu kwangilar yin haka, a nan take kotu ta bada umarnin a tafi a taho da Safwan, Cikin kankanin lokaci aka xo da Safwan, Lokacin da aka karantar masa laifinsa bai musanta ba sai dai ya nemi kotu tayi masa sassauci. A ranar aka saki fu'ad shi kuma Safwan da tawagarsa aka tasa keyar su xuwa gidan yari. Ba karamin farin ciki me'ad tayi ba ganin yadda Allah ya fitar da masoyinta daga cikin tsaka mai wuya, godiya mai yawa fu'ad ya yiyawa me'ad a lokacin ya tabbatar da cewa me'ad son gaskiya take yi masa, har gida ta raka shi, sannan ta tafi gidan su. Bayan ya samu nutsuwa ya ƙara rubuta application na neman aiki a wani Company, cikin Sa'a Allah yasa aka ɗauke shi ana biyan shi naira dubu saba'in 70,000 kowane wata. *********** Bayan wani lokacin fuad ya sake zuwa ma ,mahaifin mead da batun aurensu, amman still mutumin yaki amincewa, ita kuwa me'ad tace duk duniya babu wanda ya isa ya hanata auren abinda zuciyarta ke so, da kyar momy tasamu ta shawo kansa inda yace bisa sharadin, zai amincewa aurensu, momy tace "wani sharadi ne dady?"ni naso ka hakura ka barsu su auri juna tunda shi wanda kake son ta aura ga yadda takasance dashi. "Babu ruwanki da yadda takasance dashi saboda nasan ba halinsa bane, yayi hkn ne bisa wasu dalilai, amman tunda kema bayan diyarki kike ba damuwa kuyi duk abinda ranku yake so ,ni dai sharadina duk runtsi duk wuya ko wata matsalar mutuwar aure kar me'ad ta sake ta dawo gidana amatsayin ni ubanta ne idan ta amince da haka fine gobe ma ya turo a daura musu aure....... Momy ta kalli mead itama momy din take kallo zuciyarta cike da matsanancin tsoron abinda dady yace Amman take wani bangaren daga zuciyarta ta shiga hasko mata babu abinda zai faru sai alkairi a tsakaninta da masoyinta fuad. Dan hk muryarta a sanyaye tace "shikenan dady Dan wannan ba zai zama da matsala ba ,na amince . "Okay kice ya turo iyayensa wani sati da sadakinsa kawai nake bukata Dan nasan bashi da abinda zai kawo, yana gama fad'ar hk ya juya ya bar parlour'n a fusace kmr zai tuntsura. Sati na cika kuwa mahaifin kabeer yazo masa amatsayin wakilinsa ,inda aka saida zance mai karfi, akan sati mai zuwa za'a aure, batare da 'bata lokaci ba satin na cika wanda yakama ranar asabar din karshen wata, aka d'aura auren me'ad ediris takai da fu'ad Muhammad argungu bisa sadaki dubu talatin. A ranar da aka d'aura auren, a ranar mahaifinta yace bazata kwanan masa a gida ba tunda an d'aura taje can takarata . Da sauri me'ad ta durkusa agabansa tana kuka tana bashi hakuri, batasan cewar tayi kuskure ba sai a lokacin datake ganin zatayi nisa dasu gashi har lokacin mahaifinta na fushi daita "dady kayiwa Allah kayi hakuri ka yafe min , Dan Allah kasanya min albarka acikin rayuwar aurena ,kamin fata alkhairi kada na tafi kana fushi dani, na tuba dady ba laifina bane so ..so...ne . Komawa yayi ya zauna a bakin gadonsa cikin daga murya yace " aure kike bukata kuma nayi miki , addua ko sanya albarkata ce dai bazan yiwa auren dana banaso ba ,kuma banga wanda ya isa yasani aikata hkn ba ki tattara kibar min gida sannan karki manta duk wuya duk dadi karki nufo gidana .... Momy ta janyota zuwa Kan kujera ta zaunar daita kusa daita tana kuka itama mead tana kuka "kukan ya isa haka me'ad ni mahaifiyarki ce ,naji na amince na yarda ina son abinda kike so ,kuma ba zan tsinewa aurenki ba ,San sanya miki albarka cikin rayuwar aurenki, shima dady nasan daga baya zai sanya miki albarka, sai dai zance da zan miki yanzu bai wuce, kinsan rayuwa aure, ba rayuwa ce irin wanda kika saba bace , akwai bambamci dayawa acikinsa, hakuri shi ke Jan ragamar rayuwar aure, dan hk ki zamo mai hakuri Allah yayi miki albarka da rayuwar aureki.... takarasa fad'ar hkn a daidai lokacin da kanwarta hjy rahmatu ta turo kofa d'akin tashigo. "Taso muje me'ad kowa yashiga mota ke kad'ai ake jira. Ta mike tsaye jikinta na rawa hjy rahmatu ta janyo hannunta ta riketa gam dan karta fadi, momy tabi bayansu tana wani irin kuka shi kuwa dady ya koma saman gadon ya kwanta lamo yana tunanin, Allah ne kadai yasan halin daya shiga a wannan lokacin, ta yaya rayuwarsa zata cigaba da gudana batare da me'ad dinsa na cikin jin dadin dayakeson ya ganta ciki ba ? ,rashin Jin dadinta a yanzu ya zame masa babban gibi ..... Kai tsaye sai gidan mijinta dake new okoba estate, wanda da tarin gudunmuwarta aciki aka kama hadadden 3 bedroom flat din aka nufa daita. Tana zaune a tsakiyar gadonta lullu'be cikin mayafi sai baza kamshi take cikin hadaddiyar gezner, yayinda su misna da wasu daga cikin kawayenta ke zaune gefenta suna hira sama sama amman ban da sajida data gocewa zuwanta, wanda ita kanta mead din take cike da mamakin rashin hallararta . ango da abokansa suka shigo d'akin cike da barkwanci bayan sun siyi bakin amarya kmr yadda yazama al'ada suka wuce gabadayansu tare da kawayen amarya ,gidan ya saura su kad'ai . Ahankali K'arasowa gareta , ya zame mayafin dake lullu'be da kanta, ya tsura mata Mayan idanunsa , itama kallonsa kawai take,bata ko kiftawa ,ga wani kalar murmushi datake sakar masa wanda ita kanta batasan tana yinsa ba,ahankali ya hura mata iskar bakinsa da sauri tayi kasa da kanta, take wani irin kunyarsa ta rufeta, gbdy jikinta ya d'auki rawa ta ja baya kad'ai ta zuro kafafunta kasa domin saukowa daga Kan gadon, cikin sa'a ya riko laulausar tafin hannunta, kasa juyowa tayi ta kalleshi, saboda wani irin kwarjini daya k'ara mata. Cikin wani salo yakira sunanta "me'ad my love my everything, yau kuma ni kike jin kunya ,sannan ina zaki tafi kibarni a daidai wannan lokacin da nake tsananin bukace dake? "Wannan ranar farinciki ce garemu gbdy , bazan ta'ba manta wannan ranar ba saboda mahimmancinta ,ina sonki.... A yadda yayi maganar da kuma yanayin sunan daya kirata dashi bakaramin rud'ar daita ya sake yi ba,cikin wani irin shauki ya janyota zuwa jikinsa rungumeta ajikinsa tsam yana shafa bayanta tare da aika mata wani salo na musamman mai tsayawa a zuciya ,wanda hakan ya saukar musu da kasalar da ba basu ta'ba jin irinta ba ajikinsu, kusan minti Goma suna rungume da juna suna aikawa junansu sakonnin soyayya sannan suka je sukayi alwala domin sake godewa Allah daya nuna musu wannan ranar, bayan sun idar fu'ad ya dade yana masu adduar zaman lafiya mai dorewa haka zalika itama tayi musu addua sosai inda yayi mata tambayoyi Akan addini ,yayi mamaki kwarai da gaske saboda tasan komai ta fanni abinda ya shafi sallah da tsarki ,ta wannan bangaren ya jinjinawa iyayenta . Da kansa yashiga gabatar mata da kayan tand'e tand'e da kuma kazar amarci kmr yadda al'ada ya tana da, sai daya tabbatar data koshi sannan ya barta . ya shiga bathroom dinta ya watsa ruwa ya fito d'aure da towel inda ya isketa inda ya barta zaune "ki shiga ki wasa ruwa ,ina zuwa, yanzu zan dawo nayi miki massaging Dan nasan a matukar gajiye kike ko? Ta kashe masa idonta daya batare da tace masa komai ba . Yana fita ta mike ta cire gabadaya kayan jikinta ta daura towel tashige bathroom bata dauki wani lokaci ba ta fito ta shirya cikin wasu hadaddun riga da bata wuce iya cibiyarta ba mai matukar shara shara ya kwanta ajikinta luf sai Dan Wandon rigar mai bud'ad'en baya wanda ya shige tsakiyar bombom dinta ,ta sake bin jikinta da bayan kunnenta da kasan noniwanta zuwa cinyoyinta da hadaddiyar humra lungu da sako ta mulke sannan ta haye gado ta kwanta zaman jiransa. Shima tsab yagama shirinsa cikin rigar bacci ya fashe ilahirin jikinsa da turaransa me tada hankali ya nufo dakin inda ya iske cikin yanayin dayafi bukata, tsayawa yayi cak yana dubanta tamkar yaga wata halita davan, lumshe idanunsa yayi, kana yayi saurin hadeye wani busashen miyo , saboda ganin halittar kirjinta a bayyane a gabansa yana hangowa muraransa abinda bai ta'ba gani ba kenan a zahirance ,take yanayin jikinsa ya sake sauyawa tsigar jikinsa suka mike ,jikinsa d'auki kyarma batare da bata lokaci ba ya isa gareta bayan ya kashe wutar d'akin ya zagayo ta bayanta ,tare da kamo laulausar tafin hannuta cikin nasa yasoma mata massaging "my love sorry kinata jirana ko? "Uhm kawai ta iya furtawa saboda hanusa dake tafiya a sansar ajikinta wanda ya saukar mata da jin wata muguwar kasala mai hade da sha'awa, haka ya dinga shafa jikinta ahankali yana hadawa da romacing dinta har ya raba da kayan jikinta, ahankali ya kwantar daita ya hadeta da kirjinsa yasoma kissing wuyanta zuwa saman nonuwanta a zafafe in a romantic waya ya dinga murza Kan brest dinta kafin daga baya ya sauke bakinsa akansu, yasoma tsantsan Kan nononta yana lumshe idanunsa tamkr yasamu loly pop ,ya dade yana tsotsar kan nononta sannan yayi kasa tare da sauke harshensa cikin kasanta yasoma sucking dinta, wani irin d'auke numfashi tayi da sauri sannan ta dawo dashi tare da ajiyar zuciya, sai da fu'ad ya rud'ata ya cukud'ata ya gama kashe mata jiki tsab Wanda ko yatsan hannunta bata iya dagawa sannan suka fad'a duniyar ma'aurata . Fu'ad bai barta ba har garin biyun dare yana juyata akan bed ,sai daya tabbatar data murzu iya murjuwa ta gamsar da kansa sannan ya barta duk wani sha'awarsa sai daya fitar daita batare da wata tausayawa sannan ya koma gefe yana fidda numfashi da ajiyar zuciya, murmushi yake ta faman yi Dan yasha zumar da bai taba shan irinsa ba . Tabbas mead ta cika macen da duk wani nmj zai so ,hamdala yakewa ubangiji daya mallaka masa zahra amatsayin matarsa Dan iya cikar mace ta cika har zarta niimarta ta dabance, babu abinda fu'ad yake sai sambatu har cikin zuciyarsa cewa yake in babu me'ad bazai iya cigaba da rayuwata ba . Ita kuwa ta galaibaita sosai hawaye ne kawai ke zuba a idanunta Dan ko iya daga hannunta batayi ,baa jin sautinta sai sheshekan kukan datake mirginowa yayi kusa daita cikin sanyayyiyar murya yace "sorry love Allah yayi miki albarka ya biyaki dukkan abinda kike nema duniya da lahira magana yake mata Amman bata San abinda yake cewa va. Gani yayi kmr bata cikin haiyacinta, ya tabata jikinta yaji zafi rau, tashi yayi ya hada ruwan zafi sosai daidai yadda bazai koneta ba ,ya dawo ya dauketa duk jikinta a sake, sata yayi cikin ruwan zafi ta fasa ihu tare da sakin marayar kuka ta kamkameshi ajikinta har da kiran sunan dady . "Ki zauna zakiji sauki, girgiza masa kai tai alamun bazata iya ba,"ya Allah ya furta cikin zuciyarsa, anya kuwa ba ciwo yaji mata ba? Cikin muryar kuka mai cike da ban tausayi tace" Dan Allah kabarni hk bazan iya ba ,zan mutu idan naciga da zama cikin ruwan nan .."ok shikenan bari na gyara miki jikinki kai kawai ta iya daga masa. Ahankali ya dinga mata wayo yana tsomata cikin ruwan zafin har ta daina jin radadin sannan ya gyarata da kyar ta iya wankan tsarki ,daukota yayi, ya cire bedsheet din daya baci yasa wani duk da ba iyawa yayi ba haka yasa ya Dan gyagyra ya kwantar daita ya mata rufa da blanket ya kwanta kusa daita yana shafa mata kanta zuwa bayanta, kuka take har lokacin Dan ji take kmr kara mata wani azabar yake da hannunsa a haka har bacci ya dauketa Wanda da gani bana jin dadi bane, shi km ya zame jikinsa yaje yayi wanka yadauro alwala ya fara nafilfili nagodewa Allah daya mallaka masa mead amatsayin matarsa ta sunna, addua yayi tayi musu da samun zaman lfy a tsakaninsu Dan farinciki dayake ciki bazai misaltu ba shirin bacci yayi ya kwanta kusa daita tare da kankameta ajikinsa kmr Wanda zaa kwacewa ta hk bacci shima ya daukeshi cike da matsanancin farinciki. A satin sam fu'ad bai bar mead ta sarara da bukatarsa ba ,gurzarta yake kmr yasamu tuwo, Allah yagani shi nmj ne da yi daya biyu baya isarshi ita kuma sam ba hk take ba, ta dai yi hakurin barinsa yaci angoncinsa a tunaninta da bai saba yi bane yasa yakeyi kmr zai cinyeta. Aurensu da wata daya fuad yace inna ta dawo gidansu tinda 3 bedroom ne amman Sam inna taki yarda tace "banda abunka fuad ina ni ina zama tare daku,?"kudai kuyi zamanku lfy Allah kade fitina kubarni nan ni dai ka dinga zuwa ina ganinka. *BAYAN SHEKARA DAYA* Me'ad ce kwance a cinyar fuad yana shafa gashin kanta, "Na tabbatar da cewa nafi kowane namiji sa'ar abokiyar xama, Yanzu nake ƙara tabbatar da cewa yar halak na aura, tunda muka yi aure babu wanda ya taba jin kanmu, muna rayuwa mai cike da farin ciki, duk yadda aka yi kokarin xuga ki a kan ki rabu da ni,amman baki yarda da hakan ba, dole na gode miki me'ad na kuma cigaba da kula da ke har karshen rayuwata. Murmushi me'ad tayi tare da shafa kwantaccen sajen da ke kewaye a fuskarsa, na gode da yadda na samu kyakkwan yabo daga wajenka fuad, insha Allah babu Wanda xai ji kanmu har abada, soyayyar su suka ci-gaba da yi mai cike da ban sha'awa ,har zuwa lokacin da suka samu haihuwar nasreen , Wanda tun daga lokacin suka Dan fara samun rashin jituwa atsakaninsu adalilin rashin kulawa da yarinyar, ganin hk yasa inna ta dawo gidansu da zama domin cigaba da kula da yarinyar, daga nan komai ya daidaita, inna ce komai na yarinyar Sam me'ad batasan meye kula daita ba, abinda ke had'ata da yarinyar shan nono shima idan tana gida ,idan zata aiki kuma, sai dai ta tsiyaya mata nono ta ajiye mata ta kama gabanta ,idan kuma tana gida system ne agabanta bata da wani lokacin kowa ,dan idan ta zauna tana daddana system sallah kadai ke tadata, sannan duk wanda ke zaune kusa daita yazama bawa koda kuwa fu'ad ,Dan ta dinga aikesa kenan ,shi kuma tsakani da Allah baya kin mata a ganinsa duk cikin soyayya ne . Zamansu da inna gwanin dadi da kulawa saboda tsananin kaunar me'ad din datake, komai mead ,aiki idan taga yayi mata yawa zagewa take ta tayata, ita kanta mead na tsananin son inna da bata kulawa Sam bata kaunar abinda zai bata mata rai ,duk abinda zai faranta mata shi take, saboda yadda take kula daita Dan wani lokacin har abincin yi musu take kafin su dawo aiki , sosai mead ke jin dadin zama tare da inna ,bata da mataslar komai ko ta fannin mijinta da kowa illa ta rashin lafiyar yarinyarta saboda tana girma ciwonta na sake bayyana ajikinta, zamansu tare da inna bai d'auki wani dogon lokaci ba, zazzabi kwana daya da yini tal yayi sanadin barinta duniya ,acikin dare inna tace ga garinku, mutuwar da ta kusan haukata fu'ad da mead, sun yi kukan da tun sanda sukazo duniya basu yi irinsa ba ,aka shirya inna zuwa gidanta na gsky. Bayan rasuwar inna mead tasha daukar masu aiki sai dai ,abun baya zuwa koina, take sallamarsu saboda bala'I datake musu duk abinda sukayi sai taci gyaransu . Har takai ga rokon ummi mai aikinsu ta gida momy tabata, itama zuwa wani lokaci tace kallon mijinta take da sauransu ta tattarata ta meidaita ,a haka da yau ta canza wannan mai aikin ta kore wancan har nasreen ta girma. Wannan shine takaitaccen had'uwar mead da fu'ad . Back to the story Mmn sudais ce 💗💗💗💗💗💗 'YAN CINKI 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 ~NA~ *AYSHA A BAGUDO* ~DEDICATED TO~ MRS ADAM ( YAR MUTAN KAGARA) Page 65 t0 66 ......nasreen kwance akan gadonta lullu'be cikin bargo mai taushi, tana sharar baccinta ,hankali kwance take fitar da numfashi yayinda me'ad ke zaune a gefenta tana gyangyadi , minti daya minti biyu zata bud'e idanunta, taga halin datake ciki, can dai taja naunayen ajiyar zuciya sannan ta bud'e idanunta gabadaya tana furzar da numfashi tana girgiza kai tare da furta "fuad kenan .... Amman babu komai , komai zai zo qarshe, ba dai gobe Monday ba?" zan sa ido inga yadda gobe zata kasance garemu " how could you ask me to stop my work? "For what.? " ai abinda ba zai ma ta'ba yiwuwa bane yake fad'a idan nabar aikin sauran abubuwan da aikin nawa yake taimakawa agidan fa ? "Shi nawa yake amsa albashinsa da har yake kokarin cewa na ajiye aiki na zauna gida, ta taja tsaki,ba laifinsa bane zan je d'akinsa yanzu nasamesa muyita tak'are . Jin motsin fitowowarsa yasa ta yunkura ta tashi had'e da kai hannunta saman sumar nasreen ta shafa ahankali sannan tak'arasa mikewa tsaye tana gyara zaman rigarta ta fito daga d'akin . lokacin da fito parlour'n da niyyar nufar d'akinsa jikinta ne yayi mugu mugun sanyi sakamakon ganinsa kwance datayi akan doguwar kujera cike da matsanancin damuwa, amman sai ta kau da abinda ta gani atattare dashi tashiga aika masa da wani irin kallo kana tasoma takowa zuwa inda yake kwance tana kiran sunansa cikin d'aga murya"abban nasreen!!! Duk kiran da take masa yana jinta sarai yayi mata banza tamkr bada shi take ba har taka'raso ta zauna kusa dashi ta shafa hannunsa zuwa wuyansa... "fuad still shiru yayi mata sai numfashinsa da yayi saurin d'aukewa dan ji kmr ta jona masa electric ne ajikinsa, ahankali ta kwanto jikinsa har nonuwanta na ta'bo fuskarsa ta saita fuskarta danashi tana shakar numfashisa domin son tabbatar Da baccin yake da gsky ko dai wani shirin ya fito mata dashi.... saurin sake d'auke numfashi yayi saboda zuciyarsa datayi saurin bugawa adalilin jin abinda yafi kauna atare daita sun kawo masa ziyara wanda take yanayinsa ya sauya,lokaci daya zuciyarsa da joystick dinsa tasoma harbawa .... Ta d'ago daga jikinsa tana yatsina fuska da tsaki "yanzu kai har kaga gurin bacci?" koda yake kana sane fa kakeyi kmr kana bacci alhalin nasan ba baccin kakeyi ba 'amman no problem I will give you as you want it...takarasa fad'ar tana mai gyara zamanta zuwa kwanciya a gefensa. "Nasan cewar kana da kafuri taurin kai, Amman idan kace kana da taurin kai nima mahaukaciya ce ,gurin taurin kai har ya zarta naka ,kaima kasan da wannan, kasan halina fa ,kasan halin wacce kake zaune daita ba sai na sake gaya maka ,nasan Kana sane kake wani baccin manufurci saboda bakason akawo karshen matsalar nan dake kasa saboda mugunta ,kasane kake yin abubuwa iri iri so that ranar monday sai gidan ya saura daga ni sai yarinyata ko Dan dai ka 'bata min rai ? " to wallahi baka isa ,Dan ba yarda zanyi ba ,shine ka wani zo ka kwanta Dan da gari ya waye ka lalla'ba ka shirya da wuri ka wuce aiki batare da nasani ba .."so that I will not have any choice than to stay at home with our child...saboda kasan zuciyata ba zata iya d'aukar barin yarinyata a gida ita kad'ai ba,that's why you are playing different prank, am really ready for you..." wallahi tallahi kaji na rantse da Allah kowa zai gaya min zance ni yakamata na zauna tare da nasreen a gida bazanji ba infact I will not listing to any body ,kai koda kuwa ubana ne zai tako kafafunsa gidan nan adaidai wannan lokacin wallahi bazan yarda ba... "kai ko inna ce zata ta fito daga cikin kabarinta tabani hakuri bazan hakura ba ,kai kuma daman kasan ina da wannan taurin kai fiyye da naka both of us must iron out the issue on ground before everything could have mess up. shine kazo kana wani baccin gulma baccin tsiya, baccin munafurci, kai yanzu bacci ne agabanka? "bansan yaushe ne kake son komai namu yazamo daban Dana sauran mutane ba ...yanzu kai abun alfaharinka ne nasreen tazo tasameka shame shame anan wai kai ubanta kana bacci alhalin ana bukatar solutions ga rayuwarta, ka bud'e idanunka kaga yadda ni bacci ya kaurace nawa idanuwa .... "But no problem na godewa Allah da yasa yarinyata ta samu bacci ,ni kuma daman ina da lokacin kowani irin wahala coz am ready for trouble tare zamu kwana anan har garin Allah ya waye, bazan baka chance din tashi da wuri ka gudu aiki ka barni da yarinya a gida ba, kana farkawa daga wannan tsinanen baccin naka da kakeyi da kwayar idanuna zaka samo cin karo dashi zaka san dani kake zance zan tabbatar maka da me'ad din dakasani tana nan bata canza ba ,in dai akan wannan matsalar ne bazaka ta'ba samun yadda kake so . "You know me and I know you uhmmmmm wallahi yau bazan runtsa ba ballanatana bacci ya d'aukeni sai mun samu maslahar wannan matsalartamu tukun . shi dai fu'ad juya mata baya yayi yacigaba da kwanciyarsa, can wuraren karfe 3 na dare ,wani naunayen bacci ya kawo mata ziyara bata San lokacin data bingire agurin tasoma sharar bacci ba ,shi kuma lokacin yasamu damar mikewa tsaye da kyar yana mika had'e da salati yana dubanta yace "wahalalliyar mata kawai, wa yagaya miki ana yiwa bacci wannan salon iskanci? "" muna nan mu zuba inda ke zamuga wanda zai ci riba, wallahi matukar nine mijinki ,kuma ni nake rike da igiyoyin aurenki sai kin zauna gida kin kula da gida da yarinyarki zance zuwa aiki nayi cancelling dinsa inga dinsa kuma banga uban da ya isa yasani janye raayina ba yakarasa fad'ar hk tare da shigewa d'akinsa. ba ita ta farka ba sai gurin asuba ta bud'e idanunta wayam taga babu fu'ad babu al'amunsa, Dan haka kai tsaye ta nufi dakinta.. Washegari bayan tayi duk wani abinda ya zama al'adarta ce sallah, wanka ,girka abinda zasu ci, ta tsaya kan wanka nasreen da shirinta ta bata abinci taci ta koshi da bata magungunanta ,sannan ta zauna ta kamo tafukan hannuta cikin nata suka zauna a gefen gado tashiga karanto mata aduoi iri iri na neman tsari da lafiyar jikinta ,ta tofa cikin ruwa ta bata tasha sannan tacigaba da yi mata addu'a yadda zan fita na barki cikin gidan nan lfy ,hk zan na dawo na sameki gidan nan lafiya lau cikin koshin lafiya da kuzari kina wasanki koina batare da wata damuwa ba albarkacin Annabi Muhammad s.a.w. "mugun ji da mugun gani Allah bazai sa naji ba ,na godewa Allah dayasa zuwa wannan lokacin kina raye sannan muna raye dake, ina sake godewa Allah , Allah yacigaba da karemin ke ya raya min ke yabaki ingantacciyar lafiya mai daurewa, duk maganar datake da adduointa a kaikaice nasreen take kallonta tana furta ameen acikin zuciyarta har sanda me'ad tagama ta sakar mata murmushin tare da kokarin mikewa tsaye nasreen tace "a'a momy ,are you going out? Tace " me zan miki idan kina bukatar wani abu just tell me? "Ni kawai banason kije koina stay with me mummy.. " what do you mean by that ? " today is Monday nasreen zan tafi aiki am going to work. " but momy.... "Uhmmmmm nasreen karki damu dad'ynki na gida and he is going to take good care of you . "Guses what? Nasreen ta narke fuska tamkar zatayi kuka Dan ita tafi son mom dinta ta zauna gida kmr yadda sauran iyayen friend's dinta keyi.. "Karki damu bby nah, zan dawo aiki yau da wuri ni dake zamuyi kallo a zeey world muna cin popcorn da chocolate tak'arasa mgnr tana dry tare da mikewa ta kamo kanta ta bata kis a goshi "be good for dady dont disturb my husband "bye bye my dear Ta rataya jakarta na dubanta kmr tasamu pictures "love you bby, say bye to mummy nasreen ta d'aga mata hannu tana mata bye bye.. "bye my love ... Mead na fita daga d'akin nasreen ta sake bata rai sosai tamkar zatayi kuka,ta rungume duka hannuwanta, a kirji ta jingina bayanta da abun gado tana turo baki gabadaya ranta in yayi dubu to abace yake , zamewa tayi ta kwanta batare datasan abinda ke mata dadi. Me'ad kuwa kai tsaye keyn motarta ta d'auka a inda ta saba ajiyewa a parlour'n, ta nufi kofar fita, ta kai hannu da zumar murd'a handle din kofar, sai me? ba sai kofa taki bud'ewa ta sake murd'awa still the same cike da matsanancin mamaki tashiga jan kofar tana kiran "a'a .... da iyakacin karfinta tana mamakin yadda hakan ya kasance,cikin hk taji sautin muryarsa daga bayanta yana cewa "kamata yayi kiyi tsale da fukafikinki ki tsallake ki bi ta cikin kofar ne ki wuce daga gidan ,ba wai ki tsaya 'batawa kanki lokacin ja ba . cak ta tsaya tare juyowa ahankali tana dubansa rike da key'n kofar a hannunsa yana takowa zuwa inda take tsaye tmkr an dasata.. " a she baki da kunya me'ad? Sannan bakisan abinda ake cewa kunya ba a al'adar hausa fulani..,"anya ma kuwa ke kina daga cikin cikakkun jinsin hausa fulani kuwa, wad'an da suka San darajar aurensu data ya'yansu? "No no bazaki kasance haka ba coz you're so shameless and now how dare you dress up and go to work? "What about your daughter whom you abandoned to? " ,I mean yarinyarki da kika Haifa acikinki wa kike tunani zai kular miki daita? "Dan Allah fu'ad ka ajiye wannan maganar agefe saboda mu rigada muyita before bai kamata kana dawo mana da hannun agogo baya ta katseshi ta hanyar fadar tana cika tana batsewa . "Oky kya fadi hk mana tunda Ke ba uwar arziki bace, Dan duk uwar arziki datasan ciwon kanta bazata fadi hk ba . "Kai ke Sam ba uwa bace wallahi, idan kuma uwace ke kina daga cikin asararrun iyaye, wallahi tallahi ita kanta nasreen datasan irinki ce uwarta daba ta roki abar kartazo duniya ... "Fu'ad.......ta kira sunansa a zafafe tana tsuma sai kuma tayi shir tare da ciza lips dinta. "Ki fad'i maganarki kai tsaye ba sai kin kira sunana ba . Sai Dataja numfashi ta sauke kana tace "Plz it's too early on a Monday morning... "Really ? Ya fada yana dage mata girarsa daya tare da rike kugunsa da hannu daya yana dubanta. "Ina rokonka da had'aka da girman Allah, just give me the key and let me be on my way to work. "Key gashi a hannuna ki amsa mana ki fita nagani ,which kind of woman are you? "What sort of mother are you? Your daughter is sick and the doctor said someone has to be with her for thirty days ...but you are expect me to stay at home with her .. " me kake magana akai fu'ad? " ko ince me kake kokarin cewa? " nice zan zauna a gida har na tsawon kwanaki 30 domin in kula da yarinyarmu ko me? "No karki zauna ki kula daita ,ki zauna gadin gidan ne ,da wata shashar tambayarki. Cike da izza da jin kai tace " I will be home stay with her not go to work ? "Exactly abinda nake bukata kenan, ki zauna gida ki kula da yarinyarki ,your common sense didn't tell you that as a woman, you need to stay at home and take good care of her. "For what reason? Ta fad'a a matukar fusace tana matsoshi kmr zata shige jikinsa.... "For what reason fa ki kake ce? "To for matsayinki na shashar mace kuma uwa, kinsa Allah wallahi ba zaki wannan tsinannen aiki ba.... shima ya fad'a a matukar fusace suna fuskarta juna kowanensu na shakar numfashin juna zuciyoyinsu na wani irin bugawa da karfi at the same time suna kallon cikin kwayar idanunsu cike da zallar 'bacin rai.... "Me kake nufi dani ne fu'ad? "Fu'ad you are the one you will stay indoor with your daughter and take care of her while I go to work and make money for us....meye salary dinka zai mana da rayuwarmu gabadaya idan na zauna gida ? "kai kasa common sense dinka kayi tunani Dan haka don't don't west my time plz.. " I don't have anything to tell you any more ,just take off your clothes and go sit there and watch over that girl shine kawai abinda bazan gaji da gaya miki ba amatsayinki na shashar uwar ...... "Ni kake cewa shashar uwa saboda ina son inganta rayuwarmu data tilon diyarmu? Kana tunani bansan ciwon kaina Dana yarinyata bane ko me you should mand your taught fu'ad ka daina gaya min duk any stupid maganar daya fito daga bakinka saboda bani kadai nake da yancin zama na kula daita ba ,kaima ubanta kana yancin zama ka kula daita.. "Short up there *YANCINKI* ne sha sha daki kula daita duk wata uwar data san yancin kanta Dana ya'yanta kije ki tambayeta zata gaya miki gskyr danake gaya miki, a yau mead kin rasa mai fuskantar ya gaya miki gsky saboda kina amsar albashi da bai taka kara ya karye ba .....Sam iliminki bai amfanar miki da komai ba ke haka naki iyayen suka miki, ? "da kace sun fifita aikinsu akan rayuwarki da yanzu bakiyi takama da wannan banzar aikin naki ba yakarasa mgnr yana busa mata numfashi wanda yasa ta lumshe kyawawan idanunta sannan ahankali ta bud'esu tare da tsura masa ido tana kallonsa...kusan minti biyu tana manne da fadadden kirjinsa zuciyarta na rawa sannan ta bude bakinta da kyar ta kira sunansa cikin sanyayyiyar murya . "Fu'ad ka rabu dani bana son wata matsala da kai ayanzu ,kaga koda na tashi a safiyar yau din nan, ban shiga lamarin kowa ba acikin gidan nan , saboda na yiwa kaina magana am telling you kuma na gayawa ubangijina ,Allah yana jin a halin yanzu haka, na bud'e bakina sannan na d'aga hannuwana duka garesa "nace Allah yadda nake son tafiya aikin nan ,bana son wahala kuma banason nayi fad'a da kowa ayau din nan in particular, "am sure my God has answered my prayers I beg you for God's sake don't let me be influenced by paternal linage custom "ina rokonka ka barni karka barin aljanun gadon gidan mahaifina su taso a yanzu su tsinkareni na shuka maka rashin mutuncin da ban ta'ba maka ba a iya tsawon rayuwarmu..... "Su taso Dan kutumar ubansu aljanun sun dade basu taso ba ,,idan aljanun gadon gidan ubanki basu taso sun tsinkareki ba ,ki bari na gidan gadon uwarki kiyi adding dinsu ajikinki sutaso, a shirye nake da duk wani iskancinki , wuce ciki ki cire wad'an yan iskan kayan da kika saka ki zauna ki kular min da yarinyata you are going nowhere....... "Me fu'ad....? "Yes of course.. "Fu'ad Dan girman Allah kabani key sannan kabarni na kama gabana bana son wata matsala da kai ... Ya furzar da iska ta bakinsa mai dumi sannan yace "It seems you are going insane common sense dinki bai gaya miki GSKy ,da abinda yakamata yakarasa mgnr yana ta'ba saitin 'kwa'kwaluwarsa ,kalli bari na tmbyeki wai na rokeki ne kafin ki aureni ko me you tell me da kika zabi galazawa rayuwata data yarinya? " baka rokeni ba amman aurenka danayi shine the most worse kuskuren danayi arayuwata, a halin yanzu na fara regreating aurenka. ... "Ni zakicewa haka?"ni zaki ce kinyi da kinsani, ni bance nayi danasani auren shashar uwa irinki ba ..." you mate are out there begging me to marry them wallahi ba irinki yakamata na aura ba mistake nayi ,kuma na godewa Allah da har yanzu lokaci bai kuremin ba ... "Wani irin girgiza tayi mai had'e da ihu ta saka ta furta "what mistake fa kace ? "Abinda kunenki yaji shi nace ba irinki yakamata na aura ba mistake me I just favoured you, idan kin mata na tuna miki .... "Ji ..kuji min mutamin nan , ni kayiwa favoured ?" Ka manta taimakawar danayi maka , na tsaya tsayin daka da rayuwata da aljihuna da komai nawa duk ka manta ba .. "koma da me zakice nima nayi miki taimako tunda na aureki ban barki kin wulakanta ba, kmr sauran kawayenki, ke yanzu kawayenki nawa ne suke zaune a gida suke neman miji irina basu samu ba ,ke Dan kin ga kina dashi a hannunki shine kike iskanci , aikin nan naki Allah yasa aljannah zaki siya dashi tunda nace bazaki ba,bazaki ba .. "Ai kuwa baka isa ba wallahi.... kai din butulo ne sannan mai manta alkairi ne, da baka manta alkairi da wad'an nan zantuttukan basu fito daga cikin bakinka, Akan taimakon junanmu da albashinka ba zai mana komai ba .. "Dan Allah malama matsa kusa dani .... "Babu inda zani come on ka bani key nakama gabana , mutumin nan ina gaya maka kabani key takarasa mgnr tana cakumarsa tare rike hannunsa da key'n yake ciki . "Ke... ke..ke !!! Meye haka kina hauka ne? " ko mai ke damun tunaninki? "Zan ji miki ciwo fa sakar min riga kinsan dai bana dukan mace ko, karki bari na fara saboda I will beat you badly "ka fara mana ina ruwana ,what I need is to give me the key nakama gabana.. "You are looking for my trouble me'ad zan miki dukan mutuwa fa ,ya daga hannunsa da niyyar kai mata gigitaccen mari ya hango fitowar nasreen daga d'akinta tana tahowa garesu da kyar take daga kafafunta rike da goshinta. Dan hk ya fasa abinda yayi niyya yasoma kok'arin banbare mead ajikinsa data cukurkudeshi Amman ina me'ad taki yarda ita lallai sai ya bata key kafin ta sakeshi . Ganin me'ad taki sakinsa sai ihu take ya bata key nasreen takira sunansu atare"mummy, dady.. kawai tayi luuuuuu ta zube kasa summammiya a take mead ta sakeshi tayo gurin nasreen tana ihun kiran sunanta "nasreen nasreen!! Dan Allah ki tashi karki wa momynki hk plz, Dan Allah ka mamin ita mukaita hospital kokarin daga yarinyar suke amman ina ko motsi batayi wani ihun ta saka,"Iam done for..... ba tak'arasa ba taga ya nufi d'akinsa daita ya kwantar daita akan gadonsa ta shigo d'akin aguje Zata isa ga nasreen ya dakatar daita "stop there I don't want see you here, ba aiki zaki ba ? " You can go for now, out of this room before I pieces you right now ya nuna mata hanyar fita da yatsan hannunsa, ganin tana tsaye kikam taki fita sai idanu data tsurawa nasreen tana kuka yakaraso gareta ya kamo hannuta yashiga janta Amman taki tafiya har sanda ta numfashin yarinyar ya dawo daidai lokacin daya turata da hannunsa duka har sai daya fitar daita waje ya bugo kofar da karfi ya dawo d'akin cikin sosai daidai wannan lokacin nasreen ta sauke naunayen ajiyar zuciya da atishawa da sauri yakaraso gareta ya rungumeta ajikinsa yana mata sannu "dady ina mumy take ta tafi aikin ko? Girgiza mata kai kawai yayi alamun aa, ta runtse idanunta hawaye nabin kuncinta "dady kace momy tazo plz ina son naganta ina sonta kusa dani .... Hawaye ne ya gangaro bisa kuncinsa "yaya mead take son yayi da rayuwarsa data yarinyarsa? Hawaye yake zubarwa sosai kmr yadda nasreen ke zubarwa kusan minti 30 tana rungume ajikinsa sannan bacci ya d'auketa ahankali ya kwantar daita , ya tashi ya fito zuwa parlour'n abinda ya bashi mamaki bai wuce rashin ganin me'ad ba ya nufi d'akinta da sauri, bata nan ya sake dawowa parlour'n yana duba key amman bai gani ba . runtse idanunsa yayi gam zuciyarsa na wani irin harbawa da sauri sauri yana jin kmr ya furta mata abinda zai natsar daita tare da gigita rayuwarta da komai nata ,amman ya kasa ya koma ya zauna Kan kujera ya rafka uban tagumi yana tunanin mataki na karshe da zai d'auka akanta karar wayarsa da'ake kira tun minti goma da wuce ya dawo dashi daga tunanin daya lula ya ciro daga aljihun gaban rigarsa yana dubawa private number ce aka kirasa dashi ,yayi shiru kmr bazai dauka ba ,sai kuma yayi tunanin d'auka muryar daya ji ne yasashi cire wayar yana sake kallon screen din wayar "sajida ya furta sannan ya mead wayar kunnenshi yayi shiru yaki cewa komai.. Bangarenta kuwa cewa tayi "my favourite ya kake da jikin bby nasreen hop she's getting better for now? "Sannan a ina makomar maganarmu ta tsaya?" plz ina son sani , fu'ad idan narasaka a wannan karon zan mutu ,wallahi mutuwa zanyi plz karkace min a'a ka taimaki rayuwata ka yantota daga shingi Dan... "Dakata malama karki cika ni da shirme din banza, wai me kika d'aukeni ne ?shasha lusari ...? "Ko ance miki nima sauna ne da bansan ciwon kaina ba ? "To bari kiji ingaya miki nayi kurakurai da dama arayuwata amman bazan ta'ba kuskuren amincewa aurenki ba sajida koda kuwa ke kad'ai zaki saura a duniya.. Muryarta na cracking tace plz fu'ad don't do this to me zuciyata na wa.. "Short up wawiya kawai ,ya katseta ta hanyar fadar hk, wai ma ance miki ina da bukatar k'ara aure ne ko me, da kike kokarin takurawa rayuwata? "Ina son matata tana sona wannan matsalar ce kawai ke damun rayuwarmu kuma ina tunanin zamu samu solutions akai, Dan haka zaki iya barin rayuwata Dan babu abinda zanyi dake idan ma aure nake da bukata nasan inda mata suke ya fad'a yana katse kiran gbdy yashiga juya kai da wayar hannunsa tare da jijiga kafarsa daya. . Bangaren me'ad kuwa Koda ta isa company dinsu duk wani ma'aikaci dake aiki acikinsa ya hallara, ita kad'aice batazo ba, Dan haka cikin sauri sauri ta daidaita tsayuwar motarta a inda aka tana domin parking ta fito mataimakinta mudansir na hangota ya k'araso da sauri ya amshi mukulin motar yana gaisheta "good morning ma. "Morning kawai tace tayi gaba abinta ,inda dubbanin ma'aikata ke gaisheta tana amsawa da kyar har tashiga makeken office dinta tare da zama akan kujerarta zamanta ke wuya, tayi wata irin zabura ta mike tsaye jikinta na rawa, take kuma zufa yasoma ketowa jikinta kmr babu iskar dake kadawa acikin office din ,cike da matsanancin mamaki ta sake zama Kan kujera da sauri ta sake mikewa saboda tiririn da kujerar keyi, Dan haka tasa hannuta taji Amman sai taji sanyi me gyaraye Dana ac na shiga tafin hannunta tayi shiru zuciyarta na wani irin dokowa. shigarta office din babu wani dadewa mudanrsi yashigo rike da jakarta da wasu file Amman yadda ya ganta tsaye sa'banin koda yaushe idan tashigo mazauni take fara nema ,ya bashi dry sosai ,sai dai yayi kokarin dakewa, abun yayi masa dadi sosai daman kuma malamin ya gaya masa zai yi mamaki , but bai zaci da wuri haka ba. Jakar ya ajiye akan table dinta da file file sannan ya nufi office dinsa yana kwashewa da wata uwar dry "shegiyar maseefaffiyar mata kawai karshenki yazo zamuga yadda zaayi zaman aiki ana takama sauran abokan aikinsa yakira suka hadu suka dinga zaginta . ********** Yau kwana biyu kenan da zuwan suhailat gidan me'ad Amman Sam hankalinta yaki kwanciya akan matsalarta, Wanda tasan a kashi dari yayarta ce mai ragamar laifi acikin dukkanin abinda ke faruwa, tayi zurfi sosai cikin tunani dan gashi har yau monday batasan yadda lamarin zai kasance ba ,sun daidaita ko kuwa har lokacin suna Kan ra'ayinsu ,tana nan zaune har sanda momy ta fito cikin shirin fita tana mata sallama , har ta kai bakin kofa ta dawo ta tsaya akanta ta kira sunanta "suhailat lafiyarki kuwa tun d'azu ina miki magana ? Firgigib suhailat ta dawo haiyacinta tana sauke naunayen ajiyar zuciya kana "tace wallahi momy ina cikin matsanancin damuwa , gsky banso gaya miki ba saboda banason ke ma damuwar tashafeki amman nayi duk wani nazarina naga ke kika fi cancantar nagayawa..jin haka yasa momy ta samu guri gefenta ta zauna "me ya faru? "Menene ki gaya min damuwarki.? *************************⬇********************** ************* Ai Hausa Novels **************** *************************⬆ ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ⬇ ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ⬆ ************************* Wani ajiyar zuciyar ta sauke sannan tace "shekaranjiya danaje gidan aunty me'ad tun daga harabar gidan na dinga jin haiyaniyarsu .Amman tunda fita zakiyi yanzu ki bari idan kin dawo zan gaya miki komai.. "Kinga gaya min yanzu, Dan gabadaya hankalina a matukar tashe yake.. "Momy ki tafi kawai idan kin dawo zan gaya miki.."ke dakata bam ma son sake jin wani exucuse saboda duk inda zani zuciyata bazata samu natsuwa ba can zuciyata zata koma ni dai gaya min koma menene... "Shikenan momy lokacin da naje gidan basu san na shigo ba ,ina daga waje na dinga jin ita da mijinta suna jayayya sosai, mutsu fa sosai ita dashi har ma sun fara yin fad'a atsakaninsu .. "Sun fara fad'a fa kikace ? "To me kuma zai hadasu fad'a su da suke zaune lfy? " ni dai lokacin Dana shiga shine aunty me'ad take koramin abubuwan dake faruwa duk dai akan matsalar rashin lfyr nasreen, ni dai na fara jin tsoro kar yadda suke sainsan nan kar yazamota daga karshe yazo ya saketa fa ... " uhm Allah ma ba zai sa ba,InshaAllahu babu abinda zai faru atsakaninsu sai alkairi ,irin wannan gidan bazai ta'ba hargitsewa ba ,balle wani abu shi saki ... "Ki daina saurin kawo zance saki cikin lamarinsu ,karki sake fad'ar hk Dan ba haka ake magana ba ,koda yaushe ki dinga yiwa yayarki fatan alkairi arayuwar aurenta.. "Yadda nake ganin kansu ahad'e kmr zasu cinye juna ina farinciki da murna Allah bazai kawo abinda zai shiga tsakaninsu ba, albarkacin annabi Muhammad s.a.w mugunji da mugun gani bazasu ganshi ba ,badamuwa dai InshaAllahu zan kirasu. "A'a momy kira fa ,ai wannan matsalar ta wuce a tsaya akira, koda ma zaki kira miijinta zaki kira kice zaki zo duba lafiyar nasreen Dan banason tasan ma nagaya miki kin dai San halinta.... "Oh ni khadeeja wannan wani irin tashin hankali ne ?"Allah ka taimakeni akan lamarin yarinyar nan, kai na ma fasa zuwa koina bari na koma ta mike ta nufi hanyar step.."ki tafi inda zaki mana koda zuwa gobe hk sai kije, irin hk fa yasa tun dana dawo naki fad'a miki.. "Ke nace ban zuwa na fasa gbdy ma na rikice narasa gane kaina gara kawai nayi zamana.. "Oky kawai suhailat ta fad'a itama tattara kayayyakinta tayi d'akinta. Wunin ranar me'ad kusan a tsaye tayisa acikin office dinta, wanda daga karshe shi kansa office din yasoma mata tirarin azabar azafi ata koina ajikinta ,idan tayi yunkurin zama saman kujerarta sai taji kmr ana tsira mata allurai ga km tiririn azaba zafi haka ta dingaye office din har ta hakura ta fito daga cikinsa. Yayinda idanun mudansir Dana abokansa ke kanta sai lekenta suke suna kwashewa da dry. . Mmn sudais ce 💗💗💗💗💗💗 'YAN CINKI 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 ~NA~ *AYSHA A BAGUDO* ~DEDICATED TO~ MRS ADAM ( YAR MUTAN KAGARA) Page 67 t0 68 ....gabadaya Kasa xaman office din tayi, ta shiga ta fita ta yi haka yafi sau ba adadi, ga tarin aiki birjik a kasa zaman jiran sanya hannunta amman kasa aiwatarwa saboda ji take kamar ana xuba mata tafasasshen ruwan xafi a jikinta, idan tayi yunkurin zama a kujerar kuma sai taji kamar ana sukarta da allura, haka ta dinga sintiri tana shiga tana fita, yayin da kuma su tahir da da ma'aruf da mudassir suke kyalkyale mata da dariyar mugunta. Mudassir ne ya dafa kafadar Tahir, "mutumina kana ganin matar nan fa gaba ɗaya ta rasa sukunin rayuwarta" A jiyar xuciya ma'aruf ya sauke tare da cewa "Kai dai bari ai yau ina ganin ikon Allah dama akwai irin wadannan Malaman a duniya, wanda suke aiki kamar yankan wuka, ai ni duk tunanina zancen da muka yi da kai wlh ya bi ruwa, baxa a taɓa samun malamin da xai iya yi mata aiki ba da jikinta zai dinga irin wannan tururin xafin gaskiya malamin nan gaske ne" "Ai kaɗan ka gani ma domin ni malamin nan ya tabbatar min da cewa Wannan aikin da take tunkaho da takama da shi har take wulakanta mutane a kansa sai ya fita a hannunta, na tsani yarinyar nan saboda irin wulakancin da take yi mana, da sannu sai aikin nan ya dawo wajen mu" Murmushi Tahir yayi tare da cewa "Fatana aikin nan yana fita a hannunta wajena xai dawo, ni ne xan dawo Manager Kuma bana so ku yi kin baƙin ciki, idan matsayinta ya dawo hannuna fa kamar komai yana wajenku ne tare xamu juya Kamfanin nan yadda ranmu yake so" Kallonta suka yi suka ƙara bushewa da dariyar mugunta, haka suka xauna suna ta tsine mata albarka a wajen nan duk juyin da tayi sai sun mata dariya, ta koma sai kace zautacciya, sai kaiwa take tana komowa duk wanda ya ganta sai yayi mamakin ganinta saboda abinda ba a taba gani bane a history din rayuwarta, saboda a kullum me'ad taxo office tana xuwa take shigewa ta xauna sai dai idan wani abu ne mai matuƙar muhimmanci yake fito da ita amma bata irin Wannan zaryar. Tana cikin wannan halin ne tayi wani tunani, da tsayuwar nan da take yi me xai hana baxa ta kira sudais ba, (sudais aminin fu'ad ne dama kuma sun yi magana da kawarta sajeeda cewa xata kira shi ta faɗa masa matsalar da take ciki a gida ko akwai abinda zai iya yi a kai) Wayarta ta dakko a gida ta shiga duba number sudais, tayi Sa'a kuwa kira ɗaya tayi masa ya ɗauka, bayan sun gaisa ne ta faɗa masa cewa tana son ganinsa yanzu a gida akwai magana mai matukar muhimmanci da take so su yi da shi. Amsa mata yayi da xai zo kamar yadda ta buƙata Suna gama wayar ta nufi bakin motarta da sauri ta shiga tayi mata key ta nufi hanyar gida, tana cikin driving taji wayarta tayi ƙara tana dubawa taga number mahaifiyarta ne, ɗauka tayi cikin ladabi ta gaisheta, tambayarta tayi jikin nasreen, amsa ta bata cewa jikin nata da sauki, magana mahaifiyarta ta cigaba da yi. Insha Allah da misalin karfe 4:00 xata xo ta sameta a gida tana so ta duba jikin nasreen. dariya tayi bayan gama sauraron bayaninta kaf "mead am so disappointed of you "Meyasa kike son maida mijinki bawa ko ince mijin hjy ni haka kikaga ina yiwa naki uban dan baki da kunya kike cewa maganar da mijiki ya fada ba maganar arxiki bce. "ence yarinya bata da lfy likita yace lallai sai daya daga cikinku ya ajiye Aikkns ya zauna tare daita domin kula da yarinyarta amman saboda maseefar son aiki kina kokarin batawa mijinki duniyarki kuma aljanarki rai . "idan baki sani ba maganar aiziki mijinki yayi miki dayace miki kece yafi dacewa daki zauna bashi ba domin baki taba ganin inda akayi haka ke ko a garin mahaukata baa taba yi ba miji ya zauna gida ya kula da lamuran gidan. "ke tsaya yanxu ko mijikin bai tsaya gaya miki abinda ya dace ba ke amatsayinki na uwa bakisan kece yafi cancata ki tsaya agida ba? indai ke uwar arziki ce indai ba akasin haka ba . "to yanzu me kike expecting mijinki ya tsaya yayiwa yarinya yar shekara goma? "beside if your husband is taking care of the Child and you go to work what do you expect people to say? "they will defiantly be misjudged, za'a ce kin maida mijink mijin tace ,mijiki ke kula da gida daga karshe zaginki duniya zatayi Kuma duk wanda yabaki wannan shawarar cutarki zai yi. "wallahi bari kiji kece kika fi dacewa ki ajiye aiki ki kula da yarinyarki, nasan abinda ke damunki fa da matsalarki, bakomsi ba saboda wadan yan kudaden da kike amsa ya fi nashi shiyasa kike behive haka... ke yanxu bakisan ceawar abarka dake cikin zaman aurenku da rashin damuwa shine komai ba? duk wani abinda ke cikin duniyar nan albarka shine kan gaba ko mutun na amsar naira daya albarka yashiga ciki wallahi zai yi abinda msi amsar one million bai yi ba. "haka ne momy inji cewar fu'ad. kinga idan kika bi umarnin mijinki kika ajiye aikin nan kika zauna a gida domin ki kula da lafiyar yarinyark zaki ga abun mamakin da zai biyo bayan biyayyar da kikayi ko bama haka ba mead wannan dutyki ne banashi bane ,abinda fa nasan bazan yarda ayiwa fsn ba bazan bari kiyi fu'ad, haka zalika idan shine yake son cutar dake sai inda karfina yakare, dan haka yazama dole ki zauna ki kula da NASREEN.... sudais ya gyara zamansa tare da cewa "momy kiyi hkr da katse miki hanzari danayi kinawa yarinyarki fad'a, "we throw the stone to the direction of the flow of the bird ..... yauwa dan albarka, Allah yayi maka albarka sosai naji dadin furucinka dan allah kasamun baki acikin zance yarinyar nan.. "no momy kar tunanin yake inda bana nan make nufi ba... ai abokina yakamata ki bari muyi masa fad'a.. muyi masa magana ta gsky akan wannan matsalar ba me'ad ba . fu'ad yayi saurin bude idanuwansa gabadaya ysna duban sudais cike da matsanancin mamakin jin furucinsa. abun mamaki shi dayake daukar dubu dari kacal yayinda matarsa ke d'aukar 55,000 par month... "kaga dan Allah malam it's going to be 15000 because 50k will soon be added, dan haka kayi saurin gyara wannan banzar maganar taka . "koda an maka karin 50k akan 100k yakai yawon nata ne? a"tamyarka nake ya Kai Nata ne kuma zata muku.. "idan kai bakaga abinda zata mana ni san abinda zatayi da wata shashar maganarka, ka gyara maganarka sannan kasan irin maganar dazaka min sudais yakarasa mgnr yana jan tsaki. "duk ma abinda zakace bazai dameni ba, gsky ce dai bakaso kuma wallahi ko zaka mutu sai na fad'a maka tunda karasa mai gaya maka, gsky fu'ad kai bulo ne basan arziki ba sannan baka iya cin arziki ba bakasan mutunci ba , yanzu wannan bawar Allah da ta dinga wahala akanka kmr zata mutu akanka rayuwarta ce kawai vata baka ba, kai yAnzu kan wannan yar karamar matsalar har sai duniya tasani abinda yakamata atsakaninku kuzuyi abunku ka yarda ka amince ka zauna agida ka kula da yarinyarku ba sai kowa yasani ba, kai yanzu idan ita ta'ajiye aikinta kai zaka iya biyan school fees din NASREEN? "ok sai yanzu na fahimci abinda kake nufi yarinka dake karatu a makarantar kudi kakeyiwa bakiciki ta bar private school zuwa public school wallahi you are not thoughtful ,in da kana da cikakken hankali irin nawa a yanzu zakayi kokarin ajiye aikinka ka zauna ka kula da yarinyarku. "In dai irin wannan hankalin naka ne wallahi tallahi gara bani dashi ka fahimceni ?" ,me ye amfanin wannan banzar tunaninka gareni ? "Meyasa Sam kai baka da tunani mai kyau acikin kwakwaluwarka? "Jifa yadda kake magana kmr wani sauna wanda bai San ciwon kansa ba ,wai bula bula kmr shasha "kodayake kai fa a gidanka mijin hjy ne kamata yayi nayi maka uzuri? " if not da kana da kwakwaluwar maza da baka fad'i abinda ka fad'a..har kake wani tsayawa yi min magana akan abinda bazai ta'ba yiwuwa ba "malam kaajiye magana ta fahimta kuma a inda ta dace ahalin yanzu promotion is going on in my office now and my salary would be increased by 50k ,that not all ,I may be assured the position of the manager ..i will be overseeing the whole company, when workers resume, yayinda idan mutane sunzo zasu dinga girmamani gud morning sir gud morning sir!! Ni zaa dinga girmamawa haka . "You are a fool fuad..... "What........? Suka hada bakinsu gabadaya har sudais gurin furta hakan tare da juyowa suka fuskanci inda take zaune rungume da hannuwanta duka akirji tana cika tana batsewa.. "Mead ni kika cewa haka ?"it seems you are mad . "You're crazy you're foll kmr yadda na fada me zakayi na fada maka me zakayi ,? "You don't have anything to do than ihun banza da wofi.. "Momy kina zaune fa kina jinta kina jin abinda take gaya min ni kike gayawa wadan nan maganganun ke har kin isa how dare you talk to me like that? "Amman zaki gane kuskurenki zan saita kwajwaluwarki ,zan koyar dake darasin dake cikin rayuwar izayar aure da bakisan dashi ba ki sawa zuciyarki iskancinki yazo kashe...."mead me nake ji yake fitowa daga cikin bakinki kina hauka ne ko kin sha wani abu be mijin naki kike gayawa haka ? "Inna lillahi wa inna ilaihi rajiun wannan wace irin masefa ce haka?"daman irin zaman da kukeyi kenan? "Dan Allah kayi hakuri fu'ad nasanka da hakura ka kara akan wanda kake da zan mata fada "momy kina bani hskuri Akan furucinsa yanzu momy wannan matar arziki ce ? Yakarasa fadar hk yana taba daidai saitin kwalkwaluwasa. "Ennnnnnn don't talk to me touching head I don't like it , Kafin ka sake harzuka kwalkwaluwata kasan na sha yi maka warning akan banso kana magana kana taba saitin kwalkwaluwarka idan kasa hannunka saitin kwalkwaluwarka yana birkita nawa brain din takarasa mgnr tare zabura ta Mike tsaye tana fuskantarshi don't ever talk to me touching head.. " wallahi da alamun ciwon hauka yasoma taba tunaninki, ke kanki kina bukatar gani doctor personally, ni kike gaya magana haka? Ni ni kirjinsa kawai yake nuna wa yana furta kalmar ni ni...shima ya mike tsaye jikinsa na rawa yasoma kokarin karasowa indatake momy tayi saurin shiga tsakaninsu tana bashi hakuri kmr zatayi masa sujada... " ooooooo ta d'aura hannuta abakinta, wallahi kaji kunya fu'ad kuma asirinka ya tono,kuma wallahi bazan daina furta maka kalma fool ba ,sannan duk inda ake neman nmj mai abun kunya idan akazo gurinka ansamu angama shameless man....oooooooo.. "Ba laifinki bane ,laifina ne wallahi, da barki danacinki ban aureki ba da yanzu ina zaune lfy danasani aurenki nayi yafi sau ba adadi.."Dan Allah malam kayi mana shiru mai abun kunya yanxu kai saboda yes sir yes sir kake son kaki zama ka kula da tilon diyarka, kasani duk duniya bakada kowa sama da nasreen uwa uba dangi duk babu sai nasreen Amman saboda karin girma da yes yes yasa ka kasa zama ka kula daita wallah shem on you kaji kunya matsayinka na uba Sam baka San yancinka ba, automatically we are not supposed to be having this argument in dai kai nmj da hankalinsa yacika ne ..idan kai cikakken nmj mai cikakken hankali da tunani ne ,nmj da yasan yadda ake amfani da kwalkwaluwa ne bai kamata mu tsaya muna jainja akan matsalar nan ba balle argument kawai kana embarrassing your self.. Momy tayi saurin fuskantar fu'ad jikinta na wani kyarma gabadaya ta kasa furta komai illa kirjinta datake shafawa alamun ya kwantar da hankalinsa yayi hakuri zatayi wani abu akan lamarin, shi kuwa wani irin tsuma yake gbdy kokarin cafkota yake but momy ta kasa ta tsare Mead ta zabga masa wata katuwar harara "ok anayi maka yes sir yes sir agurin aiki ni bana ce maka yes sir yes sir agida ? "If you call me, how do I respond to you? Bada girmamawa nake amsa maka ba ? A matukar fusace yace "kin gadama fadar haka da kinsani karkice sir , Like you have a choice ,aikin me kika amsa agurina dakikiyar banza kawai da batasan ciwon kanta ba .. " tambaya aikin Dana amsa kake, if I want to sarve ur food ,don't I always kneel down? " you should have stood and placed it on my head stupid kawai, wannan ba aikin bane ..,"ok wannan aikina ne ko ba abinda kake nufi kenan ba ..? "Naji aikina ne , idan nagama naje gurin aiki ta buga hannunta tana rike karamin Dan yatsanta "karfe nawa kake tashi ,karfe nawa nake tashi? "Did you tell me? " zuwa wannan lokacin I will wake up early, I would have gotten to work by past seven, seven din da tuni na kammala da break wanda kai sai alokacin zaka tashi kace wanka zakayi "wai bazakiyi shiru ba me'ad ina tsaye kike gaggayawa mijinki mgn son ranki Amman ina mead taki yin shiru inda take shiga bata nan take fita ba Dan haka momy ta sake juyowa ta fuskanci fu'ad kmr zatayi kuka "kayi hakuri ..."karki damu momy, tayi duk abinda tagadama ba har gorin banda dangi tayi min ba .. "An yi maka gori har da goroba ma, indai akan wannan banzar promotion din dazaka samu ne na yes sir yes sir wallahi baka ga komai acikin gidan tun duk wahalar danake akan baka gani nayi maka hidimar gidanka tsab nagama na tafi aiki nagama dukkanin wani wahala Wanda kai alokacin karfe hudu agida zata maka, you always get home by 5pm and be watching football match Chelsea man you here, ni zan dawo gida around 6 PM Wanda kafin na dawo idan nasan bamu da abubuwan amfani a gida haka zan tsaya a kasuwa na tsiya kayayyakin damuzamuyi amfani dashi da sauransu sannan na kamo hanyar gida kuma alokacin zance zan shiga kitchen kai duk kana zaune kana kallo ... " no karkije mana kiyi zamanki, ni kike expecting naje miki kasuwa na tsiyo miki abubuwan amfani? "Meye aciki idan kaje da wannan zaman kallon da kake ,ai zaka iya zuwa kai har girkin ma sai kayi meye aciki ?"ko kai sudais meye baka wa matarka idan bata nan , I think har momy kake kiranta dashi ko ba hk ba ? Sudais Yayi saurin girgiza mata kansa sannan yace "Exactly ... "Ok kana ji ai da kunnenwaka, kodayake AI abakinka na fara jin momy sudais dayake kiran matarsa dashi yayinda kai har wani zaben kalar abinci dazakaci kakeyi ni pounded yam zanci, ko kaza zanci banason kaza kalli yadda hannuna ya dawo agidanka ,ko haka ka aureni da shayayen hannu ,my arms got bigger as a result of pounded yam I pound every night.. "No karki tuka ai da kince bazakayi ba kin jira nazo nayi da kaina,shasha banzar kawai ? "Momy bai tsaya anan ba fa ..I will wash press and pack my daughter school uniform ready for school the next day ,gajiya zata kamani zanje nayi sauri nayi wanka domin na kwanta akan gado na huta nayi bacci har da min shari, lokacin ne shi kuma zai zo min da shegen jikinsa yace tashi tashi ni kiba hakina ni kuma zance ya kyaleni nagaji dayawa, Amman Sam bazai yarda zai ce shi hakinsa yake so... "Inna lillahi wa inna ilaihi rajiun fuad yasoma furtawa acikin zucciyarsa yayinda gbdy ilahirin jikinsa ya mutu murus wata irin kunya ta kamashi yaji kmr kasa ta tsage agurin yashiga, ya kula bashi kad'ai yaji kunyar maganarta ba har momy,ganin taki yin shiru tanata zubo zance, yaga kunyar mara kunya hasara ne ,yayi saurin katseta ta hanyar cewa "wannan shirmen da kike fad'a bashi bane ainihin matsalar da'ake magana akanta ,idan kuma shi zaki meida topic ,but before komai yagama tabar'barewa atsakanimu bari kiji..... "Me zanji babu?" Ai babu abinda zanji ,kai banson jin komai daga wannan bakin naka fu'ad ,kamin shiru dole na zayyane abinda ke cikina asan ba zuwa aiki kawai ne amfani ba cikin gidan ,gbdy rayuwar danayi da kai azaba kake gallaza min naje aiki na dawo nayi maka girki ,dare mahutar bawa zan huta amman kazo min da matsalarka ,bani da ikon cewa nagaji kayi fushi, idan kuma na baka had'in kai ka meida kmr bad'ad'ashiyar kaza akan bed, you just starte laying with me bama kayi cike da tausayawa ba a,a ka dinga channise dani kenan akan bed...... Wata irin razananniyar tsawa ya buga mata ba wannnan surutun naki yayi matter ba ,ki ajiye wannan maganar banzar mara ma'ana da tushe , me'ad mead !!! Wallahi kina bani tausayi saboda zaki had'u da fushina da.... " ba fushinka zan hadu dashi ba, ka kasheni idan zaka iya, karya ne bakayi duk abinda na fad'a, Baka d'aukar kafata ka jefata can dayar ma ka jefata can ka d'auki kaina ka dukar kasa, kafafuna suyi ciwo, hannuwana su rike gbdy jikina ya d'auki caji sannan washegari zan tashi zuwa aiki byn nagama girki " kai let me tell you something you are ready for it wallahi sai ka zauna acikin gidan ka kula da yarinyarmu.. "This all rubbish you are saying is nt the issue on ground shasha kawai mara hankali da tunani ai ni bansa mahaukaciya nake aure ba .. "Aaàaaaaaa ya isa ya isa but am telling sai ka zauna mutuwa ce kawai zata dakatar da haka, Amman babu D'an kutumar babakeren da zai hana hkn kasancewa kai you must stay at home, even your mother dare not.... "Ummmm my mother? Ya fad'i haka jikinsa na sake d'aukar kirma"my mother Zan sakeki fa ,wallahi me'ad zan sakeki kuma saki na har abada. "I will surprise you with divorce lest bet ki rubuta ki ajiye zan sakeki daga karshe na kara aurena za kiga ikon Allah ba dai ni kikewa wannan wulakanci Ba?" zan nuna miki ba zuciyata ce banida ba, abubuwan da suka faru abaya nake duba amman wallahi zan sa... Wata irin firgiracciyar k'ara ta saki da karfi wace tasamu nasarar karad'e ilahirin parlour'n ,take gumi yashiga keto mata ta koina a ilahirin jikinta , nan take jikinta ya d'auki rawa kar..kar.. zuciyarta ta nemi tsayawa na wucin gadi ,wani irin tsalle tayi sai gata agabansa tana huci "let giv you good news your great grandmother dare not..baka isa ba fu'ad wallahi idan ka isa ka sakeni shigiya nake you dare not ganin yadda jikinsa yake rawa yasa...... momy tayi saurin shiga tsakaninsu tare da rufe mata baki jikinta na sake d'aukar rawa, zuwa lokacin kuka momy take da idanunta "kiyi shiru me'ad kar bakinki ya jawo miki maseefa .. Wani irin gumi ne sake keto mata "momy shi bakiji abinda yace ba daga wannan yar magana sakina fa yace ,wallahi fu'ad your grandmother not dare bazan saku agareka.. "Ba uwata da kakata kika zaga ba, sai dai taki uwar, yakarasa mgnr yana d'auketa da wani gigitaccen marin dayasata durkushewa kasa da sauri dafe da kuncinta "uwarki kike zagi stupid kawai. Jikin momy na rawa tace."na nagode ko ka zageni fiyye da haka fu'ad bazai min ciwo ba ,AI kamin mutunci kuma ka mutuntani nasani. "kiyi hakuri momy ba dake nake ba Amman yau sai naci uwar uwar me'ad acikin agidan nan" ba uwata kika zaga ba har da hadawa kakata,?" wallahi sai kin gane kuranki. "ai nice uwarta kama zageni babu abinda za'a yi amman dai kayi hakuri Dan girman Allah ka duba mutuncina karka biyewa wannan yarinyar wanda zata kashe take nema. "kiyi hakuri momy "no don't worry fu'ad kana damar zagina ma,ka daina bani hkr waja min har ga Allah banji ciwo... "Hakuri me kike bashi momy byn zaginki yake, ba uwata kazaga kasan wanda kazaga ,momy ta buge mata baki kiyi min shiru yar iskar yarinya mara hali,ba dai kina biyewa yan iskar kawayenki ba ,zasu kaiki su kaiki su baro, ke gari zai waya idan kikayi kuskuren daya sakeki wallahi babu ruwana babu hannu sai dai ki karata da matsalarki, ni wannan mugun halin naki bansan inda kika samo shi ba....iya tashin hankali momy tashiga sai faman hakuri take bawa fu'ad , yayinda Sudais yayi wuki wuki da idanuwa yana zaro su waje ya had'a uwar gumi yana kadawa fu'ad kai saboda gbdyya kasa mgn yayi illa idanu dayake zarowa, shi kansa cike yake da matsanancin mamakin me'ad yana ganin rashin mutuncin matarsa a she a she akwai mamanta a rashin sense.. "Ba dai kina biyewa kawaye ba zakiga abinda zan miki wallahi sai kinyi mamakina "ni momy babu wasu kawaye dake zigani gsky na fad'a kuma daman shi baya son gsky .. " gsky gidan uwar wa kika fad'a, fuad ya furta hakan a matukar fusace yana duban sudais "kai kuma k'aramin D'an iska bawan mata ai kagama had'in husumar data kawoka ko ,sai ka kama gabanka tun ban had'uku tare ba ,"kodayake da alamun kmr kana sonta ne ko ? "bawani yana sona ,kai dai gidan ne bakason zama sai kuma ka zauna gida ko kaki kokaso you will stay at home. Cike da rawar jiki da murya sudais yace " wata irin mgn ce hk fu'ad?" wallahi ba abinda kake expecting bane karka manta da ..... Fuad Yayi saurin katseshi da cewar "no karka damu kai dai kajira na saketa sai ka aurenta.. Momy tayi saurin had'e hannuwa guri "Dan girman kabar zance sakin nan , wani irin mgn kake gayawa abokinka da babu dadin ji..? " momy bakiji duk maganganunsa ba ,saboda shi soko ne a gidansa juyasa akeyi tunda sonta yake ni kuma zan saketa so that shi sai ya aureta .. "Oooooooo let me tell you another good news fu'ad..ko ka sakeni bazan ta'ba sakuwa ba ,matsawar akan wannan matsalar wallahi bazan sakuba you are my husband for life bazan saku ba mutu kara ba.... "Ke da wa kike wannan mgnr ? "ke ai ba matar mutu karaba bace saboda ke ba matar arziki ce... "Kina ji kina gani zan sakeki kuma nayi aurena , kuma idan kin zauna kula da nasreen uwarki da ubanki zina sukayi suka haifeki, ai idan na sakeki dole kowa yakama gabansa ,ki sa ido kiyi kallo this time around I will surprise you yakarasa mgnr yana kokarin juyawa .. Mmn sudais ce 💗💗💗💗💗💗 'YAN CINKI 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 ~NA~ *AYSHA A BAGUDO* ~DEDICATED TO~ MRS ADAM ( YAR MUTAN KAGARA) page 69 to 70 ........sudais ne yayi saurin kamo hannunsa cikin kid'ima "dan girman Allah fu'ad kayi hakuri ,karka yanke hukunci cikin fushi, ba'ason mutun yayi saki alhalin yana cikin fushi, idan sakinta zakayi kabari ka natsu, hankalinka ya dawo jikinka amman ba acikin wannan halin da kake ciki ba.. ... A matukar tsawace me'ad tace "meye haka ne sudais ..? "kana hauka ne ko ka fara shaye shaye ne bansani ba,da har na d'add,akoka cikin maganata? "wani irin maganar banza ne yake fitowa daga cikin wannan banzar bakin naka irin na marasa hankali da tunani kuma 'yan shaye shaye?"saki ko me ..ko me naji kake maimaitawa ,? " wayace maka sakina fu'ad zaiyi da kake wani shirmen hauka anan .? "wai naga kmr... "short up there ......."kaga kmr me ai idan ma 'kwa'kwaluwarka na hasasho maka saki tsakanina da fu'ad maza kayi saurin cirewa domin tsakanina dashi babu wannan kalmar har abada, mutu karaba tare zamu qarasa rayuwarmu dashi har tsufa his my husband for life.... dan ko ya sakeni bazan ta'ba sakuwa ba, kuma babu inda zani, zama daram sai dai nida shi muyi zaman daduro ,amman wallahi bazan saku ba agurinsa zama daram agidansa no going anywhere.... Dan hk kazo ka wuce ka bar gidan yanzu bana bukatar sake ganin wannan fuskartaka fool kawai .... a matukar harzuke fu'ad yace "dan ubanki idan na sakeki karki tafi ,ki zauna zaki ganewa idanunki kowaye Asalin fu'ad, zan sakeki.. sai dai idan na sakeki ki fad'i ki mutu amman sai kin d'and'ani radadin da zafin saki arayuwarki ,"kuma karkiyi tunani idan na sakeki zan dawo dake wallahi wallahi me'ad matsawar na furta na sakeki ,na barki kenan har abada sai dai idan mutuwa zakiyi kiyi shashar banza shashar wofi kawai da batason ciwon kanta ba ,"nayi danasani nayi danasani aurenki arayuwata, ban san haka zaki zamemin ba, wallahil azim da ban aureki na gur'bata zur'iata ba, domin aurenki bashi da wani faida da amfani agurina facce tarin bakinciki da nadama," a gaban mahaifiyarki gaban abokina kike bayyana sirrin da Allah ya boye, tur da masu hali irin naki ...."Amman babu komai da sannu zaki gane kuranki Dan komai yazo karshe atsakaninmu... ya sake juyawa fuuuuuuuu... daidai lokacin da sudais ya isa bakin kofar barin parlour'n yana kokarin fecewa.... "fu'ad yayi taku daya biyu ya jiyo sautin muryar momy cikin kunnenshi wanda yasa take ya tsaya cak agurin , zuciyarsa na wani irin harbawa da sauri sauri, tsayuwa yacigaba dayi agurin batare daya juyo ya fuskanceta ba har sanda , momy ta sake kiransa " fu'ad ka dawo ka zauna dan girman allah ba dan ni ba ....... runtse idanunsa yayi gam saboda yadda zuciyarsa ke tafarfasa ,domin ahalin bakin cikin dayake ciki Allah Allah yake yak'arasa d'akinsa ya aiwatar da niyyarsa gareta, ko zai samawar zuciyarsa sukuni, amman yadda momy tayi masa magana bazai iya wulakantata ya wuce ba,ko babu komai tana da wata daraja da kima agurinsa, dan hk ya juyo ahankali ya zauna yana huci tmkr mayunwacin zaki. momy ta numfasa ta koma ta zauna tana fuskantarsa sosai cikin mayunwacin hali da ita kad'ai tasan halin tashin hankali datake ciki , sannan tasoma magana atsanake cikin tausasshiyar murya "kayi hakuri fu'ad, wanda aka cuta shi ake bawa hkr, kayi hkr dan girman allah ba dan na kasance suruka ko mahaifiyar matar gareka ba , dan wannan yar iskar yarinyar bata bani wannan girman da matsayin ba, kayi hkr saboda girman allah da kuma girman da Allah yabani dan nasan a haife na haifi kmr ka in dakace nayi haihuwar wuri. "bazan hanaka sakin me'ad ba har idan kaji bazaka iya cigaba da zama daita ba saboda tayi maka abinda ya cancanci saki agurinka, sannan bazan hanaka cigaba da zama daita ba saboda nasan har yanxu kuna matsananci son junanku, iya shekarun aurenku ban ta'ba jin kanku ba sai a wannan lokacin, yanxu tunda abun yazo da haka ni adawo da NASREEN gurina nacigaba da kulawa da lafiyarta tunda ni zaune nake yanzu bana aikin komai ko kuma nasa akawo muku kanwar ummi tsohuwar mai aikina tazo ta dinga kula da nasreen, yarinyar na da natsuwa da hankali sosai .... amman me kagani akan NASREEN ta dawo gidana ko kuma nasa akawo najma........ ? naunayen ajiyar zuciya ya sauke tare da numfashi da karfi, ba zai iya rabuwa da NASREEN ba ballatana har ya kaita gidan makinyinsa da bai sonsa da kaunarsa sannan bai kaunar jininsa, duk duniya agurinsa bashi da wani makiya sama da mahaifin matarsa, tun daga haihuwar NASREEN har kawowa rashin lafiyarta bai ta'ba jin surukin nasa ya bud'e bakinsa da sunan yi musu ya jikin yarinyarsu ba, idan zatayi ciwo sau dari sai dai momy ko suhailat suzo dubata amman banda shi, dan haka bai ga haukan da zai kaishi wannan kasadar ba ,wasu zafafan hawaye ne suka cicciko idanunsa "duk fa rashin gata da galihu ne yajawo masa wanan tozarcin da kaskanci "Allah sarki inna......... " ina ma tana raye dayasan abubuwa bazasu yi masa tsanani haka ba, ahankali kalamanta na karshe garesa suka dinga zuwa masa daya byn daya "fu'ad ka kasance mai tsananin hakuri arayuwarka ,da kuma rayuwa tare da me'ad ,kayi hakuri kayi hakuri daita dan Allah ta maimaita kalmar hakuri tafi sau ba'adadi ,kayi hakuri daita domin tayi maka hallaci arayuwa ,duk runtse duk wuya karka yarda ka rabu daita saboda furucin mahaifinta gareta, wannan alfarmace da zan nema agurinka ba dole zan maka ba saboda rayuwa komai Kan iya canzawa D'an adam, Amman nasan zaka min wannan alfarmar ,Allah ya albarkaci rayuwarka data zuriarka ....... saurin danne hawayen dake makale acikin kwarnin idanunsa yayi zuciyarsa na wani irin harbawa kmr zata buga ta fito daga cikin kirjinsa. "wayyo inna kmr kinsan wannan tashin hankali zai faru byn babu ke a duniya ..." "Allah nagode maka da banyi saurin zautar da hukuncina akanta ba, bugu da k'ari ma tace kona saketa bata saku ba sai dai ayi zaman daduro, shi abinda bazai so faruwarsa kenan ba "amman wallahi ko bai saketa ba sai ya d'auki 'kwa'kwaran mataki akanta ta yadda zata dawo haiyacinta. tsawon lokaci yana zaune agurinsa dafe da ha'barsa yana tunanin rayuwa gbdy ya kasa cewa komai har sanda momy ta sake kiran sunansa "fu'ad bazan maka dole ba, sai dai akwai dalilin dayasa kaji na kawo wannan shawarar bazan so ku rabu da junanku ba duk da bansani ba ko me'ad ta ta'ba gaya maka gargadin mahaifinta gareta da sharudd'ansa akan aurenku , amman zabi yarage naka ka saketa ko kuma nasa akawo muku najma... ....... "dan ko agabana ka saki wannan jairar yarinyar mai shegen taurin Kan ba zai min ciwo ba ,saboda ita ta jawa kanta, son abun duniyarta ne ke neman rufe mata ido har take kok'arin manta abinda ya faru daita abaya.. .. tunda momy tasoma magana nadama da danasani sukayi mata diran makiya wani irin mahaukacin bugu kirjinta keyi, yayinda tsoro da matsanancin fargaba suka mamaye ilahirin jikinta, hawaye ne suka shiga gangarowa daga cikin kwarnin idanunta zuwa bisa kuncinta tana gogewa wasu na sake biyo kuncinta "meyasa tayi abinda tayi a yanzu ? "meyasa idan zuciyarta ta hau sama idanunta ke rufewa ta dinga aikata ba daidai ba......? "Why why why!!! Mead why did you do this to ur husband..? "Ya Allah ka taimakeni kar ya sakeni, idan ya sakeni yaya zanyi da rayuwata ,ga kuma tarin kaunar danake masa ..? "Allah na tuba, Allah ka ceceni ka sanyaya zuciyarsa kar ya sakeni, dan ina son mijina banason abinda zai rabumu....numfashi ta sauke da karfi kana muryarta cike da kuka tace "momy ki daina cewa son abun duniya ke damuna duk wannan wahalar fa danake saboda wa nakeyinta....? " I think saboda shine da yarinyarmu nakeyi , kaso d'ari acikin albashina agidansa da yarinyarsa suke tafiya, nifa nasan abinda nakeyi momy kuma kema kinsani idan na zauna abgida rayuwa zata mana tsauri dayawa,yanxu idan wata matsalar ta taso ba fata nakeyi ba wa zai taimaka mana? "momy bamu da mataimaki fa sai Allah, kinsani nasani momy shima kansa yasan da haka , babu wanda zai taimaka mana , da d'awainiyyar rashin lfyr nasreen ma kawai akabarmu ya ishemu fama "nawa muke siyan maganinta ? "Magani daya akwai wanda muke siya more than 100k ban da sauran magunguna "yaya yake son nayi da rayuwata idan dai ba kasheni yake son yi ba? " wannan aikin nawa shine rufin asirinmu ........ tak'arasa mgnr tana zubda hawayen nadamar abinda tayi masa... Momy dake fuskantarta ta gyara zamanta kana tace "nasan da haka me'ad amman ai baki biyo ta tsarin daya dace ba sam, yanzu dai kiyi shiru muji ta bakinsa" fu'ad me kace akan shawarata? runtse idanunsa ya sakeyi zuciyarsa na wani irin mahaukacin bugu da kyar yasamu ya iya bud'e bakinsa "shikenan momy azo da mai aikin kawai dan gsky bazan iya rayuwa babu yarinyarta a kusa dani ba...... "nagode nagode !! da mutuntaka fuad Allah yayi muku albarka ,ka girmamani kuma gani kai mai Allah yasa ayi maka fiyye da yadda kamin "ameen momy. nan momy ta juya tashiga yiwa me'ad fad'a ta inda take shiga batan take fita ba, fad'a sosai tayi mata, hawaye sosai me'ad take daga karshe momy tace "kije ki durkusa gaban mijinki ki rokesa gafarar abinda kikayi masa ,idan kina bukatar rayuwarki ta daidaita, wani irin kuka mead ta fashe dashi sannan ta durkusa kasa tashiga Jan gwiwowinta domin isa garesa, yayi saurin dakatar daita da hannunsa"no momy ba sai ta bani hakuri........ "Karkace haka fu'ad ,kuskure ne tarigada tayi kayi hakuri ka yafe mata" ki karasa garesa kibashi hakuri shashar banza kawai mara mayo da tunani,da sauri ta k'arasa zata rike kafafunsa yayi saurin janyewa yana watsa mata uwar harara , tana kuka tace " kayi hkr honey na tuba bazan sake ba ....... batare dayace mata uffan ba ya mike tsam ya fice abunsa yana Jan tsaki Dan yasan da wuya ta canza halinta ..... bayan fitarsa fad'a dai momy tacigaba dayi mata, akan ta rike mijinta gam gam akwai mata akan titi suna neman irinsa basu samu ba ,sannan a wannan duniyartamu babu nmj irinsa , dan da wani nmj ne da yanzu zance ya sha bambam, "yanzu yarinyar nan da za'a kawo miki , kiyi kokari ki zauna lfy daita karki Mata mugun Dan nasan halinki,ko ki koreta idan kika koreta i don't have any option sai dai kinsa yadda zakiyi da rayuwarki dan bazan bari matsalarki ta kasheni ba... Har bakin mota me'ad ta raka momy still fad'a take mata da Jan kunne ,tana tsaye har sai data ga tashin motarta sannan ta juya zuwa cikin gida kai tsaye d'akinta tashiga tayi showel ta fito ta canza kaya zuwa riga up shoulder iya gwiwa, wacce aka tsaga gabanta har zuwa gwiwan kafarta ,ta nufi d'akin nasreen har lokacin bacci take ,dayake cikin magungunanta akwai wanda ke sata bacci sosai , kwanciyarta ta gyara mata ta sake lullu'beta tare da yi mata kiss a goshinta ta fito ta shiga kitchen domin girka musu abincin dare ,abinda tasan yafi so shi ta fara prepare din d'orawa ,wato doya Wanda zata sarrafa shi zuwa pounded yam ,da miyar egusi ,da busashen kifi da naman kaza, tana cikin aikin taji sautin k'arar wayarta dake ajiye agefe daya ta karad'e ilahirin kitchen din , ahankali ta bar abinda take tana duba screen din wayar, sunan data gani ne yasata d'aukar wayar ta manna a kunne "hello kawata ykk ,ya kwana biyu ? Bangaren sajida tace "komai lfy ya mai jiki kuma? "Da sauki kawata yau dai in gaya miki yakin karshe akayi agidan nan . "Allah kawata me ya faru kinje aiki kenan inji cewar sajida? "Me zai hana kuwa, ai zuwa aiki a yazama Dan ada, it most be dole ,naje bayan an gama bura'uba ba takarasa mgnr tana murmushin daya zame mata jiki..... Sajida ta kyalkyale da wata uwar dariya kana tace "da kyau kawa, shiyasa nake mugun sonki wallahi akwai saurin d'aukar action akan Abu ,wallahi karki sake ki yarda ,duk borouban da za'ayi kiyi Amman karki yardar masa ,ta yaya ma yake expecting ki ajiye aiki ki zauna agida, nifa kina ganina babu aikin da zan iya bari akan wani miji saboda ba duniyarsa nazo... "Haka ne wallahi kawata yanzu dai mai aiki za'a kawo mana ,nan tashiga labarta mata komai, sajida nagama jin bayaninta tace "kash ni kuwa banso kin sake d'auki yar aiki ba wallahi.."to ya zanyi sajida ni kaina banaso daukar masu aiki saboda tsaro duk I trust my husband bazai ta'ba yin abinda bai dace ba ,amman dole na d'auka ko dan momy data tashigo cikin zance ,ni kuwa sajida ina son yi miki wata magana so very important." Ina jinki kawata" "A gsky ya dace ace zuwa yanzu kinyi aure zaman ya isa hk getting to 11 yrs now kina zaune without married ga emran har yayi yara uku Amman ke kina zaune "me yasa bazaki samu wani ki aura ba tunda nasan barasa masoya kikayi ba ... "Ai mijinki ya kanainaye koina acikin zuciyata bazan iya auran wani ba ..ta fad'i hk a zuciyarta.."kina jina sajida ? Naunayen ajiyar zuciya sajida ta sauke sannan tace "ina jinki kawa mazan ne sai a slow duk Wanda yazo ba maganar aure ke kawosa ba, wani abu suke nema ni kuma bazan iya raba gindi ba ,acikin mazan duniya mutun daya nagani me nagarta, shiyasa nake addua a kullun in samu miji kmr naki..dip me'ad ta d'auke wuta tare da tsaida aikin datake tayi shiru zuciyarta na wani irin beating fastly, mgnr sajida tayi matukar bugar mata da zuciya "wai meyasa take kwad'ayin son auren miji kmr nata ? abun na maseefar taba zuciyarta da gangar jikinta. "Me ma maganarta take nufi da guda daya tagani me nagarta shiyasa take adduar samun miji kmr nata...... "hello hello.."ina jinki, sajida "wai me yasa kike kwad'ayin mijina ko kina son shi ne .....? Tayi mata tmbyr muryarta na rawa. "Uhmmmmm ammm ko daya ,ina dai son me nagartarsa ne kawai bawai ina.."dakata dakata !!sajida for the last warning banason muna magana kina nuna kwad'ayinki akan mijina, idan babu dama mu daina zancensa dake plz Dan maganganunki akwai rainin sense ciki, haba da zarar anyi mgn sai kece kina adduar samun miji kmr nawa ....idan kina sonshi ki fito ki gaya min than I will know what do .. "no no ki fahimci me'ad "babu abinda zan fahimta acikin mgnrki baya ga tsabagen rainin hankali takarasa fadar hk tana me katse kiran gbdy ta ciza lips dinta da karfi zuciyarta nacigaba da bugawa, ahankali tashiga jujjuya wayar hannunta, tunanin tashiga yi "anya kuwa babu ayar tambaya akan zantukan sajida ..? "Kai da wuya wannan abun yakasance ,Sam wannan lamari ba me yiwu bane "ta yaya sajida zata so mijinta?" kawai sha'awar me irin halinsa take bawai nufinta tasoshi ba .. da wannan tunani tacigaba da aikinta atsanake har ta gama taje tashirya dining ,ta sake fad'awa wanka wanda zuwa lokacin tuni nasreen ta tashi, bayan ta fito ta shirya cikin wasu had'add'u kanan kaya riga da siket ,sai bakin hular tauban data sanya akanta, ta nufi d'akin nasreen,inda ta isketa zaune fitowarta kenan daga bayi, tana hango momynta ta shagwa'be fuska alamun fushi , me'ad takaraso da sauri ta rungumeta ajikinta tana shafa sumar kanta "har kin tashi baby nah? " I really miss just for same hours" "Nasreen tayi mata banza Dan haushinta take ji har acikin zuciyarta saboda ta fita aiki tabarta tare da dadynta alhalin ita tafi son kasancewa tare daita , kuma tayi mata alkwarin karya,na Cewar zata dawo da wuri su kalli tv tare suna cin popcorn gashi duk babu wanda sukayi aciki. Zaunar daita tayi a gefen gadon sannan ta nufi bathroom ta dibo ruwan dumi acikin karamar roba da farin towel ta fito ,goge mata jiki tayi kasancewar wanka daya ake mata saboda yanayin jikinta ta canza mata kaya, sannan ta nufi parlour daita ta bata abinci taci ta koshi da maganinta .. tajata zuwa Kan doguwar kujera tana janta ajiki suna kallo a TV "baby feel free with momy now nasan abinda ke damunki kina tunanin ban dawo gida da wuri kmr yadda nace ba ko? "Ki tambayi dad dinki idan ya dawo 4:00 for gidan tayi min ,even grammar tazo duba jikinki kina bacci ahankali ahankali ta dinga janta da hira, tsakani uwa da d'a kafin kace me tuni nasreen tasaki jikinta har da kwanciya akan cinyar mamanta . Suna zaune har Goma ta wuce , wanda zuwa lokacin nasreen tayi bacci amman fu'ad bai dawo ba ,gbdy mead ta tashiga damuwa Dan duk runtsi tara acikin gidansa take masa tun iya tsawon aurensu bai taba wuce wannan lokacin ba sai yau. zuciyarta cike da tunani iri iri babu abinda zuciyarta bata kismamata ba ,Amman haka ta dakewa zuciyarta tare da aiyana fushi tayi me tsanani daita but zata sauko dashi, domin yau da kanta zata kai kanta garesa domin faranta ransa dan ita Kan a hannu take. ********** Misalin qarfe 12:00 daidai na dare , me'ad ta farka Dan kyar tasamu runtsawa Dan ta dade tana juyi akan makeken gadonta kafin bacci yayi gaba daita , kishin ruwan ne ya tasheta daga baccin daya d'auketa abazata bayan tagama zaman jiran dawowar fu'ad bai dawo ba , mika tayi had'e da salati ,bathroom tasoma shiga tayi fitsari tare da sake wanke bakinta ta fito,ta bud'e karamar dispersed dake gefen gadonta ta tara karamin cup tasha ruwa sannan ta sake bin ilahirin jikinta da sanyayyen turare mai dadin kamshi da fitina sannan ta nufi d'akinsa inda taci sa'ar samun kofar a bud'e . Tana shiga ta tsaya akansa tare da tsura masa idanunta tana kare masa kallo lafiyayyen nmj sak wanda samun irinsa keda matukar wuya, yana kwance yana baccinsa hankali kwance ,sanye da gajeren short niker iya cinyarsa, wani irin yanayin ta tsinci kanta ciki wanda yaushe rabon dataji hakan ajikinta, ahankali ta dinga takowa tsigar jikinta na sake mikewa tsaye ,dan har lokacin idanunta na kansa ,ta hawo saman gadon ta kwanta tare da janyosa jikinta tasoma kissing din wuyansa zuwa bayan kunnensa zuwa ripples dinsa , ahankali in a romantic way take murza Kan nipples dinsa dake zagaye da gashi ,har ta gangaro zuwa kasanshi tasanya harshenta a saman santala santalar cinyoyinsa dake sheki kwance da wadataccen gashi tasoma lasar cinyarsa ahankali ahankali yayinda hannuta ke kokarin bud'e zip din wandonsa. ta d'aura bakinta Kan joystick dinsa tasoma tsotsa ahankali da ya'yan marainansa tana tsotsa tana murza Kan nipples dinsa cikin wani irin shauki..... cikin bacci yaji kmr ana romancing dinsa tare da suckling dinsa mika yayi ahankali joystick dinsa na sake mikewa sambar kmr Kan kaciyarsa zata tsinke saboda karfin shaawa, dan har ya fara jinsa yana yawo agajimare sai dai tunaninsa yafi bashi akan mafarki yake yi ,Amman yayi kok'arin bud'e idanunsa, fessss idanunsa suka sauka akanta kyakyawar fuskarta tana tsotsar joystick dinsa while hannuwanta na Kan joystick dinsa .. Da sauri ya tureta daga jikinsa yana mai dafe Kan joystick dinsa dake zillo ... ...... Mmn sudais ce 💗💗💗💗💗💗 'YAN CINKI 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 ~NA~ *AYSHA A BAGUDO* ~DEDICATED TO~ MRS ADAM ( YAR MUTAN KAGARA) page 71 ......mamaki ne fal bayyane akan fuskar me'ad ,domin abinda yayi ya bata mamaki matuka, Amman sai tazaci ko cikin magagin bacci ne yasashi yin hk, ahankali tasoma kok'arin sake shigewa cikin jikinsa tana ta'bo sandar girma... a matukar tsawace ya dakatar daita"stop don't don't touch me, don't ever touch me in your dity life.... cak ta tsaya had'e da tsananin jin wani sabon mamakin abinda yace ,jikinta na wani irin rawa ta hau laluben wutar d'akin ta kunna sa'banin d'azu da haske bai gama haske d'akin ba. idanunta ta tsura masa tana kallonsa cike da matsanancin mamaki abinda ke faruwa ,mafarki take ko kuwa a shirin film ne wannan abu dake faruwa daita? " idan azahiri ne anya kuwa fu'ad dinta ne me tsananin son kulawa da jarabar son sex ke zaune agabanta ? shi kuwa ko ajikinsa, yake kallon cikin kwayar idanunta tare da bata tabbacin shi din ne bawani ba. muryarta a tsarke takira sunansa "abban NASREEN wai har yanzu fushin kakeyi dani alhalin nabaka hakuri? "dan Allah kayi hakuri ka yafemin na tuba bazan sake ba . "kinga dan Allah malama karki dameni bacci nakeji kibani iska plz I want to rest.... "saboda nazo d'akinka yau shine kake neman ka haukatani da wulakañcinka ko ? "Ke kika fara ni kuma InshaAllahu zan karasa miki, duk abinda kike ji ,nafiki jinsa. Tayi shiru na tsawon minti biyu tana dubansa sannan ta sake bud'e bakinta da kyar tace "to dan Allah kayi hakuri ,wallahi nayi nadamar abinda na aikata maka ta k'arasa mgnr cike da shagwa'ba had'e da kamo hannunsa ta d'aura saman kirjinta dake cike da nonuwa kmr baitace ta haifi nasreen ba ,cike da kirsa tasoma shafa hannunsa akan nononta ahankali ahankali ,ai kafin kace me tuni joystick din fu'ad ta sake mike gal tana fitar da ruwan dadi, nan da nan sabuwar sha'awarsa ta sake motsawa, joystick dinsa ta tsaya kyam kmr mashi kanta sai zuba walkiya yake..... yayinda har lokacin idanun me'ad ke kanta tana kallonta tare da sake lailaya nononta da hannunsa,wani irin shork yaji ajikinsa tamkar ajona masa electric ,da sauri ya fixge hannunsa dake Kan nononta ya mayar kan joystick dinsa tare da dafeta dan karta cigaba da mikewa banda hucin numfashi babu abinda Yake fitarwa .... murmushin gefen baki me'ad tayi saboda ganowa datayi yana cikin tsananin bukata Amman yanason tauye kansa muryarta ahankali ta fito "dan Allah Honey kayi hakuri nasan tsananin 'baci ran dana haifar maka ne yasa kake jin .....shiiiiii I don't want to here anything from you just get out ya fad'i hk yana nuna ma hanyar fita da d'an yatsanasa "ko dole ne sai nayi ...? "nace bana bukatarki ,kije ki jika kayanki kisha bana ci... "Wato ga tsohon maye kin wani kwaso jiki tsuki tsuki kin biyoni , to banayi bana bukata ,kina tunanin duk wannan salon iskancin naki zai karyar da zuciya fu'ad ne ? "you better stop this nonsense saboda bazaki samu abinda kika zo dominsa ba .."sannan karki d'auka gabadaya magannunki suna nuna min kinyi regret abubuwan da kikayi, no no i know you me'ad, i know ,you can't change ur attitude, kin sha min wulakanci saboda jikinki , yanzu i change my mind kije ki jika kayanki kisha zan kawo wacen da zata bani naci enough na koshi batare da wulakanci ba ......yakarasa fad'ar hk sannan ya koma yayi kwanciyarsa tare da juya mata baya had'e da matse kafafunsa jikinsa na tsuma "idan kingaji da zaman jiran tsammani kina iya fice min daga d'aki useles kawai . "wai meye hk ne honey? " me kake nufi dani ne da zantutukanka gareni? A matukar fusace ya zabure ya Mike zaune yana huci kmr kumurci "ubanki nake nufi dake tare da d'auketa da wani gigitaccen marin dayasa taga gilmawar taurari .. "Ka mareni fu'ad akan hakina ? "An mareki ko zaki rama ne? " idan kika sake furta uffan agurina wallahi azim sai na miki abinda baki ta'ba tsamani daga gareni ba oya out of the this room...... me'ad da tunda yasoma gaggaya mata mgn had'e da d'auketa da mari tayi sakaton tana dubansa tana tsiyayar hawaye da sauri ta yunkura ta mike jikinta na rawa tafita daga d'akin. Bangarensa huci ya hau saukewa cike da matsanancin takacin wawancinta, tayi masa kowani irin hauka da wulakanci ya d'auka ,daga wannan babin sai wannan, babu irin rashin mutuncin dabata tsiro masa dashi ba akan hakinsa Amman dayake yar rainin sense ce shine ta wani kwaso jiki ,ai ko maye ne shi wallahi ya hakura da jikinta bazai sake wata mu'amular aure daita ba,har sai ya huce wulakanta garesa, zai koya mata lesson's da wannan tunanin ya koma yayi kwanciyarsa yana sake dafe Kan kaciyarsa dake wani irin harbawa bal..bal.... tana shiga bedroom dinta ta fad'a kan gadon ta rushe da wani tsumammen kuka, nadama tayi sosai a game da abinda zuciyarta ta tunxurata ta aikata, zuciyarta tasoma hasasho mata fu'ad dinta tare da wata.... "no no it can be possible fu'ad dina nawa ne ni kad'ai danshi kad'ai aka halicceni, haka shima dan ni kawai akan haliccesa 'bacin rai ne yasashi yi min hk,Amman Nasan ba zai ta'ba iya kara aure ba alhalin gani a raye, "ya Allah ka taimakeni allah na tuba,takarasa fadar hk tana wani irin kuka "wallahi na tuba ....ganin kukan bazai fusheta ba gashi sai faman juyi take akan makeken gadonta yasa ta mike taje ta d'auro alwala tazo tashiga jera nafilfili da neman gafara agurin Allah, tana nan har akayi kiran farko . *********** washegari ta shirya tsab cikin wata hadaddeyar doguwar rigar har kasa wace tasha tsone work ,rigar tayi matukar amshi surar jikinta sai kamshi take zubawa , yayinda gbdy gidan ta turaresa da kamshi turaruka daban daban , sannan ta shirya NASREEN ta nufo parlour'n tana rausaya fuska d'auke da murmushin annuri , zaune ta iske shi yana waya, tana kallon fuskarsa taji gabanta ya daki uku uku ya bada rasssss.... take zuciyarta tasoma rawa rawa cikin fad'a fad'a yake meida martani amman ganinta yasashi canza salon maganarsa tare da rage sautin murysrsa tayi kasa sosai "uhm ammmm sorry ni kaina bansa abinda ke damun tunani ba akanki, Amman zanyi tunani akan lamarinmu saboda ina bukatar kulawarki dan.... " what? Me'ad ta furta da matsanancin karfi zuciyarta na wani irin tsalle kmr zata fasa kirjinta . " me nakeji yake fitowa daga cikin bakinka honey ? "wai me ke shirin faruwa dani ne? ya Allah ka taimakeni nan jikinta ya hau kyarma kar...kar.... tasoma kok'arin karasowa inda yake zaune yana cigaba da wayarsa hankali kwance, tana gama isa inda yake bata tsaya wata wata ba ta fixge wayar hannunsa ta maka akan tayis tana huci "da wace yar iskar tsinanneyar kake waya? " kuma Dan wulakanci acikin gidana..... "How dare you fu'ad? "Ni zaka tozarta.....ka gaya min who's she kafin a fara hadarin balai acikin gidan nan ...? ya gyara zamansa zuwa rigingine yana ta'be baki sannan yace "idan kike ji ko da nake wayar nasan bab zuciyarki zata buga kiyi mutuwar farar daya kowa ya huta da mugun halinki . "wannan fasa wayar da kikayi ko ajikina kinyi abanza saboda zan samu wata nan ba jimawa ba kuma nacigaba da abinda Raina ke.. "Short up there fu'ad,I don't like, I said banason abinda kake min fu'ad, banaso i don't like it ...how dare you talk to me like that, if I said you a fool now kaji haushina yanzu wannan wulakacin da me yayi kama? "da ubanki da uwarki sukayi kama useless kawai d'auko min wayata naga kalar hasarar da kika min zance foll kuma aikece katuwar foll dabba dakikiya kawai "common d'auko min wayata... "bazan d'auko ba kayi duk abinda zakayi ina daidai da kai ,laifi nayi maka kuma nayi realaixing mistake's Dina, na baka hakuri nabaka hakuri, raina kake son na cire na baka ko ko me? "Ni din dai zan baka hakuri ba Allah ne zai sauko daga sama ya baka hakuri ba kuma zan nemo kowace shegiya ce kuke waya daita, dan kai din nawa ne ni kad'ai bazan yi sharing dinka da ko...on-expecting taji saukar marin wanda yasata saurin yin shiru tare da d'auke wuta na wuncin gadi . "ka mareni fu'ad akan wata banza..... shiiiii "tsuguna ki d'auko min wayata kawai kona sake k'ara miki wani ....takamarki isgilanci da wulakanci wallahi nafiki kyaleki dai nakeyi Dan mu zauna lfy Amman yanzu I can't either ..bata tsaya jin me zaice ba ta juya fuuuuuu tana gunguni taji ya jawota kiiiiiiii ta juyo a matukar gigice ta fad'a cikin fad'add'en kirjinsa tare da runtse idanunta gam tsoro da matsanancin firgici ya mamaye zuciyata ,atare zuciyoyinsu tashiga bugawa cikin tsoro tace "wayyo Allah karka dakeni ..... bai ce komai ba ya kamo hannunta daya ya murd'e da karfi tsiya ta saki wata razananniyar kara ..... " Dan Dan Allah karka karya min hannu.. "Oya duka tun wuri kiyi abinda nasaki kmr yadda nace ,ta coge taki motsawa shi kuwa yashiga janta zuwa inda wayar take kife a kasa,ita kuma tana turjewa amman yaki sakinta ganin yaki sakinta sai ma sake murd'e hannunta da yayi yasa jikinta d'aukar rawa "murya ahankali tace "plz honey kayi hakuri wlh zan d'auko.. tsaki yayi had'e da durkusar daita bisa gwiwowinta d'aukar wayar tayi ta miko masa yana duban fuskar wayar ya saki hannuta tare da ingizata tayi taga taga zata fadi ta dawo ta tsaya bisa kafafunta tana kallonsa hawaye nabin kuncinta ,shi kuwa wayarsa yacigaba da kallo abinda yayi tunani shi faru wayar tayi ratsatsa ba kyan gani ahankali shima ya tsura mata idanunsa ya yana kallonta cike da zallar 'bacin rai ganin yadda yake kallonta yasa taja tsaki "akan wannan banzar wayar kake kokarin kasheni saboda bakasan ciwona ba ko? " bari kaji ingaya maka sau dari zanajika kana waya da mace , sau dari zan fasa wayar aikin banza kawai ta juya fuuuuuu tayi d'akinta ta d'auko jakarta da makulin motarta ta fito ta wuce shi zaune yana huci ko kallonsa batayi ba ta fice, sam aranar batayi niyyar zuwa aiki ba tana jiran sai momy ta kawo najma, amman ta gwamaci taje ko Dan ta ragewa zuciyarta damuwa.. sai dai tana zuwa abinda ya faru jiya ne ya sake maimaita kansa dan kusan na yau har yafi na jiya tsamari dan jikinta ne ya dinga mata kyakayi kmr tayi wanka da ruwan karara, haka ta fito aguje daga cikin office din kmr zata hantsila, sai mataimakinta tasa ta d'auko mata jakarta da takardun dazata sanyawa hannu , tashiga motarta ta zauna anan tayi aikin ranar. Kodata koma gida ta iske suhailat ta kawo najma, kallo daya tayiwa yarinyar taji Sam bata kwanta mata ba ,kuma batajin zamansu zai dore, za dai tabarta zuwa wani lokaci sannan ta sallameta ,kai tsaye d'akinta ta nufa sai datayi wanka ta sauya kaya zuwa na shan iska sannan taje taga jikin nasreen..Tare suka dawo parlour'n tana makale da yarinyarta ,tasamu guri ta zauna sai lokacin suka gaisa da suhailat inda tace "ga me aikin inji momy "naganta batare data kalli inda najma take zaune ba tace "wannan yarinyar zaki dinga kulawa daita ,magani zaki dinga bata da lokaci zuwa lokacin sannan da fatar kina matukar son yara, Dan banason yarinyata cikin damuwa....sannan kin iya girki saboda dafa mata abincin datake so idan bama nan ? Cikin sanyayyiyar muryata tace "babu laifi aunty na iya daidai gwargwado kuma InshaAllahu zan kula daita ."suhailat kaita dakin masu aiki ....suhailat ta mike najma tabita abayanta suka nufi dakin masu aiki ta nuna mata komai dazatayi amfani dashi Dan wannan karon ne na farko dazatayi aiki a irin gidajen masu kudi. yau ma kmr jiya sai gurin sha biyun dare fu'ad yashigo gidan,yana cika yana batsewa, ko kallon inda take zaune bai yi ba ya nufi hanyar d'akinsa . ta mike da sauri tabiyo bayansa tana kiransa "honey honey!!! " bai juyo ba balle ya tanka mata har yashige d'akin ,yana gama shiga yasoma sunce belt dinsa tare da balbale botiran gaban rigarsa yasoma cire kayan jikinsa "honey daga ina kake by this time mutumin nan kanason kasheni fa tun kwanakina basu cika ba ? doguwar tsuka yaja had'e da yashigewa bayi ,yayi wanka ya fito ya shirya cikin kayan bacci duk tana zaune ta rafka uban tagumi tana kallonsa, allah yasani tana matukar kaunar fu'ad so wanda bazata iya misaltashi ba, tun kafin yanxu take faman wahala da dako akan kaunarsa sai gashi adalilin aikinta zata rasa shi da kulawarsa, ita kuwa meye amfanin rayuwarta matsawar ya juya mata baya ? "to ina ma yake zuwa? " sannan gurin wa yake zuwa har ya kai dare irin hk ? tayiwa kanta tmbyr da bata da me bata amsa ,shi kuwa rai 'bace da ganinta ya kwanta abinsa tana zaune har bacci ya d'aukeshi kmr ta ta'ba shi dai ta fasa ta dade zaune tana kallonsa rungume da pillow sannan ta tashi ta koma d'akinta. ********* washegari bayan tagama shiryawa ta nufi d'akinsa ,bakinta d'auke da sallama tashiga gaban mirrow tasamesa yana fesa turarruka ajikinsa sanye cikin shirin zuwa office yayi mata maseefar kyau kmr taje tashige jikinsa babu dama , shi kuwa adakile ya amsa sallamarta saboda wani irin haushinta yake ji bilhaki, shi karan kansa bai ta'ba tunanin zai iya dakiyar da yayi ba, saboda yana maseefar sonta da muradin kasancewar tare daita dan gbdy bai san dad'in kowace irin mace ba ,sai ita dadinta yasani ,idan yana saduwa daita ji yake kmr yana yawo agajimare sbd wani irin dadi gareta Wanda bazai iya misltswa ba.... Motsawa tayi kusa dashi sosai ta yadda take iya fuskantarshi ta mirrow sai da ta hadiye wani gutun miyo sannan tace" daman nace nagaya maka an kawo mai aikin... a yatsine yace "ina ruwana daita akaina zata zauna ?" fatana ki gaya mata karta bawa yarinyata over dose, dan wallahi this time around idan kayi kuskuren dura mata magani bazan yarda ba, sai dai ku tafi tare da me aiki wannan shine kawai abinda zance. "cikin marairacewar murya kmr can baya kafin rigimar zaman gidan ta had'asu tace " plz honey kayi addua ,sannan ina bukatar komai ya wuce atsakaninmu mu dawo kmr da tunda matsalarmu tazo karshe.. "ke dawa zaku dawo kmr da? " har abada me'ad kin rasa wannan damar agurina, domin kinyi kuskuren barin damarki ta subuce miki, bazan ta'ba dawo miki kmr da ba saboda yanzu bana tataki kowa yayi rayuwarsa har sanda Allah zaiyi ikonsa .... zubewa tayi kasa bisa gwiwowinta tana zare idanu "dan girman allah karkayi min haka fu'ad, wallahi nayi danasani ka yafe min " a fusace yace "stupid bakiyi dakinsani ba tukun sai nan gaba oya get out of my room.. batace komai ba ta Mike jiki a sanyaye ta fita amman tasha alwashin zatayi hkr da duk abinda zai mata tunda ita ta fara. me'ad yau ma acikin mota tayi aikinta abinda ke sake bawa mutane mamaki kenan ,wannan sauyawar tata ta tsayawa mutane arai amman kowa yasanya mata ido saboda sanin ita din yar ra'ayi ce kuma batason shishigi, ba'asata ba'a hanata , sai gurin 5:30pm tagama komai dake gabanta ta d'auki hanyar dawowa gida tana zuwa ta fada kitchen saboda lokaci ya wuce . ********** Sauri yake ya kammala ayyukansa dake gabansa sakamakon kiran gaugauwan da me gidansa yayi masa akan yasamesa a guest house dinsa, cikin minti talatin yasamu k'arasa, ya fito cikin sauri yashiga motarsa ya fice aguje . a natse yashiga babban parlour'n hannunsa daya cikin aljihun wandosa yayinda kunnensa ke manne da waya yana karasa shiga abinda yagani ne yasashi kasa cigaba da wayarsa, tsaye yayi yana kallonta cike da matsanancin mamakin abinda ya kawota.... Mmn sudais ce 💗💗💗💗💗💗 'YAN CINKI 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 ~NA~ *AYSHA A BAGUDO* ~DEDICATED TO~ MRS ADAM ( YAR MUTAN KAGARA) Page 72 ......Ahankali me gidansa ya d'ago yana dubansa fuskarsa d'auke da murmushi, sannan yace " ya kaja ka tsaya kana mamaki,ka k'araso mana ka zauna .... jiki a sanyaye fu'ad ya k'araso yasamu guri kusa da me gidansa ya zauna har lokacin idanunsa na kanta , sannan zuciyarsa na cike da matsanancin mamakin abinda ya kawota "to me take nufi dashi...? "Ana so dole ko kuwa dazata zo gurin me gidansa? "Shifa baya son kayan nacin nan, haka mead ta dinga yi masa naci har daga karshe tasamu nasarar mallakarsa yanzu kuma ga sajida. Itama tun daya shigo parlour'n idanunta ke kansa tana kare masa kallo tsab ko kifta idanunta batayi,domin sosai kayan dake sanye jikinsa suka masa maseefar kyau ,bayan bayyanar da sumar kirjinsa da sukayi a filli saboda bai rufe maballin rigar har sama ba ,azuciyarta tace "baby kayi masefar kyau tana kada masa kwayar idanunta, wani irin sabon shaukin soyayyarsa ce ke sake taso mata tare da huda kowa wani sashi na gangar jikinta, adduarta daya Allah yasa zuwanta yayi mata amfani yazamo silar yin aurensu.. tsawon minti goma da zamansa, batare da me gidansa ya sake cewa dashi komai ba illa coffee dayaketa kur'ba kad'an kad'an yana karewa yanayinsu kallo had'e da nazarinsu ,sannan ya ajiye cup din akan D'an karamin table din dake ajiye agefensa kana ya numfasa, tare da kiran sunansa "fu'ad kasan kowacece wannan yarinyar dake zaune? Take Gaban fu'ad yabada wani irin rasssss yashiga duka uku uku sannan yace "sir na santa kawar matatace.... "Ok meye tsakaninka daita saboda tazo min da wata magana..? "Babu komai atsakanina daita face gaisuwa.. Jin haka yasa gabanta faduwa itama take kuma zuciyarta tashiga rawa "babu komai tsakanina daita face gaisuwa ta sake maimaita abinda ya fada tana kuresa da idanunta, zuciyarta na wani irin mahaukacin bugu. Naunayen ajiyar zuciya me gidansa yaja ya sauke sannan yace sajida ko ? Da sauri Ta d'aga masa kai . "Dan bamu guri ki shiga dakin can kijiramu. ta mike tsam zuciyarta na wani irin dokawa, jikinta na rawa tana jin kar ta kurma ihu ta shiga dakin daya nuna mata wanda ke facing dinta. "Fu'ad wannan yarinyar tazo min da zance tana sonka da aure, a yadda tabani labari tace sama da shekara goma ta d'auka tana dawainiya da soyayyarka tun kafin ka aure me'ad, giftawar me'ad tsakani, yasa ta dane nata soyayyar, Amman a dan tsakankanin wannan lokacin take jin bazata iya hakura dakai ba ,kodan matsalar dake faruwa agidanka ,tayi alkwarin zama da kai da amana tare da kulawa da nasreen,inda har tace zata ajiye aikinta ta zauna zaman aure da kulawar gidanka,Dan haka me zaka iya cewa yanzu akan wannan lamarin? Wani irin naunayen ajiyar zuciya da numfashi ya sauke atare, yana duban me gidansa sannan ya bud'e bakinsa da kyar tmkr me koyon mgn "sir duk naji bayaninka, sai dai Dan Allah kabata hakuri saboda banida niyyar k'ara aure ahalin yanzu, ta gidana ma ban gama daita ba balle nayi tunanin kara aure, auren ma da aminiyar matata wace Allah kad'ai ne yasan tsakaninsu ,bana jin iya aurenta ,domin kuwa aurenta shine babban abun kunyar da zan aikata arayuwa yakarasa fadar hk yana me sukuyar da kanshi kasa.... "Babu zance kunya, abinda yakamata kayi kenan... domin musguna matarka bisa ga mummunar halaiyarta, auren sajida kad'ai zai sa tashiga hankalinta ..duk wace zaka aura bazai ta'ba mata ciwo ba kmr auren sajida, bugu da kari yarinyar na sonka da alamun zata maka biyayya tunda har aikinta tace zata ajiye ta kular maka da yarinka abinda matarka ta gida ta gazayi maka kenan . "ni dai amatsayina ina baka umarnin da shawarar ka aureta kawai kasamu ingancin rayuwa nmj ne kai kana damar kara aure fiyye da daya ,karka sanyawa zuciyarka damuwa feel free kayi abinda yadace... Fu'ad ya d'ago da sauri yana dubansa gabansa nacigaba da faduwa "kayya meyasa zai yi masa haka ? "Shi fa bazai iya ba ,shi ko aure zaiyi bazai iya auren irin sajida ba ga tarin mata nan yara masu jini ajika ya tsallakesu ya auri uwar mata ina da sake bazai iya ba yayi mgnr a kasan zuciyarsa ....... "Kamin wannan alfarma nasan zaka iya min fiyye da fu'ad yarinyar tabani tausayi bugu da kari tana sonka gashi ta duba girmana tasan ahalin yanzu babu. Wanda zai iya saka ko hanaka nima din ba dole zan maka ,amman dai banason kullun ina ganinka cikin damuwa ,mata babu abinda suka tsana sama da kishiya kayi amfani da wannan damar .. Shiru fu'ad yayi yakasa magana gashi dai maganar yake son yi Amman ko bud'e bakinsa bazai iya ba ,gumi ne kawai yashiga tsatsafo masa ta koina ajikinsa "ta faru takare yanzu yaya zaiyi da rayuwarsa....? "Kace wani abu mana fu'ad kabarni ni kadai sai zuba zance nakeyi ,idan kana ganin bazaka iya min wannan alfarma ba shikenan "karka damu Allah yasa hakan .."no sir ba..babu komai zan duba lamarin ."ba wai zaka duba lamarin ba, ka fuskanci lamarinta ,sannan ku fahimci juna . "Okay sir I will know what to do .. "nagode sosai daga yanzu kaje kasoma shirinka ni kuma zan yi kokari nasamu mahaifinta da zance da zarar ya dawo kasar Dan ta sheidamin yaje dubai, "karka sanya wata damuwa aranka balle tunanin halin da matar zata shiga ai duk abinda aka mata ita jawo tunda ta kasa tsaya akan yancinta dan haka kaje waje zan turo maka ita ku fahimci juna. Jikinsa Sam babu laka ya mike tamkr wanda kwai ya fashewa acikin zuciyarsa na dokawa ya fita daga parlour'n ya bude motarsa yashiga ya zauna yana zurfafa tunaninsa "anya kuwa zai iya auren sajida? "Aminyar matarsa ce fa ,wannan lamari bazai zama da cin amana ba kuwa ? " wayyo me'ad wallahi banso kara miki kishiya ba, banso had'aki da kowa ba ,dake kad'ai na shirya rayuwata ,"me yasa kikayi abinda duniya take ganin kara aure kad'ai ne matsalahar damuwarmu..? Lokacin daya bar parlour'n me gidansa yakira sajida, ta fito da Dan saurinta ta rusuna agabansa kanta sukuye akasa tana wasa da yatsun hannunta "kije waje yana jiranki mungama magana akan komai ,kiyi kokari ki shawo hankalinsa. "Nagode sosai yallabai Allah saka da alkairi ,Allah kara girma, ya gyara naka kmr yadda ka gyara lamarina "karki damu kije kawai . Yana zaune cikin motarsa yana kallon saman motar sannan idanunsa aruntse ,yayinda hannusa ke rungume a saman fad'adden kirjinsa ta bud'e motar tashigo ta zauna, tana kallonsa kmr zata cinye shiru ne yacigaba da biyowa kafin daga bisani ta kai hannuta ta shafo gefen fuskarsa dake zagaye da gashi sai sheki suke zubawa tsabar gyaran da suke samu "abban nasreen am really sorry for disturb you na kasa jurewa ne, soyayyarka ce ke neman haukatani ,komai zanyi kaine araina, narasa sukuni ni kaina ina duba lamarin amman ba laifina bane son ne...... ya bud'e idanunsa da kyar ya watsa mata su wanda take numfashinta ya nemi d'aukewa girgiza kansa yayi kawai yana kare mata kallo "a she zaki iya son abinda mead take matsanancin so ? "A she haka amana da yarda tayi karanci da har kike kokarin aikata hk ga me'ad,? "Me mead tayi miki da kika zabi ki so abinda take ? "zanso ace wata ce ke furta min wad'an nan zantuttuka bake ba ......why why sajida wannan cin amana ne zalla? "It's not my fault nima tsintar zuciyata nayi da hakan ina sonka ba kuma zan iya ..."sajida ya katseta ta hanyar kiran sunanta ta tsareshi da idanunta tana kallonsa " zaki iya fita lamarina sajida ? "Dan Ina bukatar kibar rayuwata saboda banasonki banason wata halaka tashiga tsakaninku ya fad'a yana kafeta da manyan idanunsa wad'anda kallon cikinsu kad'ai na haddasa mata shiga wani yanayi na daban, ahankali tashiga girgiza masa kanta alamun bazata iya ba at the same time hawaye ya cicciko a idanunta "ina sonka ta yaya kake expecting zan iya rabuwa dakai? " ni dai ina son kibar rayuwa... " sajida duk abinda ke faruwa agidana Nasan kin sani ,amman duk da hk ina son matata kuma banajin zan iya mata kishiya ballanatana aurenki da zaizama auren cin amana... "Dan haka ina rokonki da ki bar rayuwata ki manta dani ,ki rarrashi zuciyarki akaina ni mijin mace daya ne .."cike da muryar kuka tace "I can't fu'ad...ta fadi hk tana fad'a jikinsa ta rungume tsam ta d'aura hannunsa daya akan bombom dinta,tana kukan kirsa, saurin d'auke numfashi yayi,zuciyarsa na wani irin harbawa, "bazan iya rabuwa dakai ba ,bazan iya fita cikin lamarinka ba ina sonka fu'ad zan sadaukar da komai nawa matsawar akanka ne, farinciki da kulawa, zan ajiye aikina zan kular maka da nasreen ,na rantse zan kyautata maka, ka amince dani ,ina sonka fiyye da yadda me'ad take sonka, soyayyarka tasa duk kallon mata nakewa mazan duniya, kai kad'ai kawai zuciyata tagani me nagarta, na yarda idan ka aure ba kasameni a yadda kake so ba ka sakeni, wallahi ina sonka duk mgnr nan datake hannunta bai tsaya guri daya ba, haka zalika bakinta na cikin kunnenshi wanda hkn yasashi suman zaune har ya kasa tsawarta mata, ita kuwa abinda take so kenan domin tasha mafarkin faruwarsa ,ahankali ta balle botiran rigarsa guda biyu ta zira hannuta ciki kirjinsa tana shafa kirjinsa dake cike da kwantacen gashi, ahankali har ta kai Kan nipples dinsa, tasan ko shi waye tasan jinsa mazan dayakasance aciki abakin matarsa, tasan kalar jarabarsa, tasan yadda take masa bazai iya jurewa ba ,ita kuwa ko kanta zata iya mallaka masa yayi duk yadda yake so daita matsawar zai aureta, da kyar yasamu yayi karfin halin zareta daga jikinsa ya ajiye mazauninta, sai dai bai iya cewa komai ba illa numfashin dayake jawowa da kyar yana fitarwa onexpecting yaji hannunta saman mararsa tana shafawa ahankali ahankali"kamin mazauni acikin zuciyarka da mararka fuad ,ka duba kagani, getting to 11 years kenan bansamu me maye min rayuwa ba duk akan kaunarka dan Allah ka duba lamarina karkace aa idan kaki amincewa komai zai iya faruwa .... Tunda suka kasance acikin motarsa ,har zuwa sanda ta kai hannunta Kan joystick dinsa, ya fara jin jikinsa ahankali gbdy yana d'aukar cajin na ban mamakin da bazai iya hakuri da jura ba ,ahankali yake jin wani irin feelings from know where yana bijirowa gangar jikinsa dama zuciyarsa ,gbdy komai ya soma tsaya masa , sannu ahankali lamarin dayake jin ajikinsa ya fara tsamari tun yana basarwa har yasoma nuna reaction dinsa ,Dan yana jin lamarin a ilahirin jikinsa , gbdy dauriyarsa ce take neman zuwa karshe sai kawai jikinsa ya fara rawa rawa ya fara tsuma kmr Wanda ya sha maganin tauri ,sake fuskantar shi tayi sosai tana kashe masa idanunta, ganowa datayi a hannun yake yasa ta dinga motsoshi still hannunta na Kan zandariyarsa tana shafawa,koda bata ganta a zahirance ba tasan sharbebiya ce da alamun zatayi dadi da gardi, Dan gashi har wandonsa yasoma jikewa, tana gama matsoshi ta sake fad'awa jikinsa bata tsaya wata wata ba ta had'e bakinsu guri daya "wayyohlly Allah kasa control fu'ad yayi bai San sanda ya cafki harshenta ba ya fara tsotsa kmr yasamu sweet, idaunsa a lumshe ya d'aura hannunsa Kan manya bombom dinta dake matse cikin siket masu shegen taushi , itama jin hannunsa Kan bombom din yasa gabadaya ta rikirkice sosai suka makale juna suna tsotsar bakin junansu still hannunsa na Kan bombom dinta yana matsawa.. banda sautin fitar numfashinsu bakajin komai acikin motar, ji take kmr ta fito masa da brest dinta ya tsotsa Dan gabadaya jikinta ya mutu murus,shi kadai take bukata, shi kansa brest dinta dake tokare da kirjinsa yafi bukata ahalin dayake ciki Amman ina bazai iya ba yana cikin mammatse bombom dinta bakinsu na hade suna tsotsar juna kmr zasu cinye junansu . zuciyarsa ta hasko masa me'ad dinsa "duk mugun halinta tana sonshi, tana damuwa da lamarinsa matsalarsu daya zuwa biyu daita rashin zama ta kula da nasreen sannan da nuna gajiyawarta a shifidarsa Wanda shi ba ruwansa da rakinta,Dan baya hanashi morar jikinta sai dai idan bai shigeta ba ,hakika wannan Abu dayake aikatawa ahalin haramun ne ya haramta tsakaninsa da sajida bugu da kari baya jin sonta....wannan tunanin yasashi dawowa cikin haiyasinsa shima fa ubane, ya zai ji idan wani yayiwa nasreen dinsa haka? "Wayyo Allah ai da sauri ya zareta ajikinsa yana mayar da numfashi ..."ki tsaya hk karki sake yunkurin kai hannunki jikina sannan kina iya fita daga cikin motata "maganar mu fa ina ta kwana? "Tana bola kije ki tsinceta out... kayan jikinta ta gyra da suka soma squeezing bataji komai aranta tasan dai idan kere na yawo zabo na yawo wata rana za....... Salin alin ta fita daga cikin motar ta nufi motarta tana meida numfashi, tana nan zaune ya fice aguje sannan tabiyo bayansa ya d'auki hanyar gida itama, da murnarta tashiga gidan ta rungume aunty nadiya data zama matar babanta a yan shekarun baya da suka wuce"aunty ina cikin farinciki burina ya kusan cika zuciyata zata kasance da abinda take muradi tsawon shekaru ,aunty kimin adduar samunsa.."Allah ya tabbatar idan alkhairi ne agareki da rayuwarki "ameen aunty nagode ta nufi d'akinta ta fad'a saman gadonta tana juyi wayyohlly Allah fu'ad ina sonka dayawa dan Allah kasoni koda rabin wanda nake makane ta mike tsaye tana duba agogo lokaci ya wuce sosai kai tsaye bayi tashiga ... Shi kuwa fu'ad Yana shiga gidan kai tsaye inda aka tanada domin ajiye motocin gidan ya nufa yayi parking sannan ya fito yayiwa motarsa key ,ya nufi cikin gidan a parlour'n ya isketa tsaye tana tsintiri cikin had'addiyar doguwar riga har kasa wace akayi dinki palazo, tayi masefar kyau , idanunsa na sauka akanta yaji kirjinsa ya buga da matsanancin karfi. itama idanunta na sauka akansa, Tsuru tayi masa da ido tana kallonsa sannan ta meida idanunta kan agogon bango dake manne a parlour'n karfe goma har ta wuce ta da wasu mintuna runtse idanunta tayi tana tsuke karamin bakinta, sannan ahankali tasoma takowa zuwa inda yake tsaye yana dubanta, kokarin saita numfashinsa da natsuwarsa yayi tun kafin takaraso inda yake tana gama karasowa garesa ta kai hannunta daidai saitin zuciyarsa datake hango yadda take bugawa tare da kai hancinta daidai kirjinsa daya manta bai meida botiran da sajida ta bud'e masa ba. kamshin wani azababben turare taji ya doki hancinta , take zuciyarta tashiga sanar mata wace ke amfanin da irin turaren , sai dai tasan ba nata bane sai dai na wata ne daban .. Idanunta ta tsura masa sosai kirjinta na mahaukacin bugu sannan tace "ka fara neman auren ne ko neman mata ka fara ....? "Duk abinda zuciyarki ta gaya miki ya bata amsa atakaice yana bi ta gefenta ya wuce ya nufi hanyar d'akinsa zuciyarsa na wani harbawa da sauri sauri itama tabiyo bayansa da sauri " honey don't try to do that to me ..after all we have settled the issue on ground let's continue our life,yayi mata banza ya kusa kansa cikin d'akin yana shiga d'akin ya bugo kofar garan kad'an yarage bai buge mata fuska ba. ta tsaya shiru tana duban kofar sannan ta tura tashiga ciki ta iske shi gaban mirrow yana balbale sauran botiran gaban rigarsa"fuad takira sunansa "karkamin haka wallahi na tuba karka kara aure me kake son nayi maka ka gaya min am ready for it, zanyi amman karka min kishiya ,banason kishiya,saboda na tsani sharing din duk wani abinda nake so . yayi mata banza yacigaba da abinda yake zai shige bathroom tayi saurin riko hannunsa cikin nata hawaye kwance acikin kwayar idanunta " fu'ad Dina da inna karka min haka Dan Allah bazan iya ba I can't take it ...... "Kayiwa darajar Allah da inna ka yafemin abinda nayi maka, sharrin sheid'an ne dana zuciyata.. Ya fixge hannunsa a fusace " innar da kika meida kmr tissue, kullun kika tashi iskancinki akanta kike karewa...bama wannan ba karki damu rayuwata plz.. "ai kin daina sona shiyasa kike wulakantani ,to kibari masu sona su shigo suyi min abinda nake bukata . durkushewa tayi agabansa tana kuka "waye yace maka na daina sonka ..? "wallahi ina sonka kai kanka kasan wannan ranar bazata zo ba ,bana ma faran ranar da zan daina sonka, kai ne dai ka daina sona tunda gashi kana kokarin kasheni tun kwanakina basu cika ba "ka gaya me kake son nayi maka ? "Zan canza wallahi zan dinga baka had'in kai a shimfid'arka sai yadda kayi dani ,komai kake so zanyi maka wallahi bazan sake sa'bawa umarninka ba .... Kuka take sosai tana rokonsa . Jin kukan na ta'ba masa zuciya yasashi runtse idanunsa tare da cewa "naji kin fad'i komai baki fad'i batun ajiye aiki ba, ok shi fa tare aka halicceki dashi ko bazaki iya ajiyewa ba? "No karkace hk honey wannan aikin nawa shine rufin asirimu ni da kai da tilon diyarmu kamin uzuri, "ni dai kayi hakuri dan Allah am really sorry for what I did... Bai ce mata komai ba yashige bayi ya barta durkushe yana shiga ya sakarwa kansa ruwa, kafin ya fito ta kwashe kayan daya cire ta nufi washing room dashi sannan ta sake dawowa d'akin inda ta iske ya fito sanye da jallabiya "muje kaci abinci "a koshe nake.... "honey...... yaushe rabon kaci abincina ? "Ka daina cin abincina ka daina mua'mula ta aure dani gbdy kokarin cireni kakeyi azuciyarka ,ka taimaka fu'ad nasan nayi ...plz ki takaita mgnrki hk ina bukatar hutu kina iya fita plz...... tsimi tsimi kmr baita ba ta fito daga d'akin ta nufi nata d'aki tana rike da kugunta tashiga zagaye d'akin"komai fa yana neman tsaya min ni me'ad," yanzu me yakamata nayi na dawo da mijina hannuna? Ina bukatar shi banason rasashi ,ya Allah ka taimakeni karkasa fuad ya juya min baya.. " ko sajida zan kira ta bani shawara akan wannan sabon lamarin dake shirin kuno kai cikin gidana "no no bana tunani zata iya min magani wannan matsalar . "Ke kanki ki zauna kiyi tunanin zaki iya shawo Kan matsalarki inji cewar zuciyarta gbdy ta kasa zama hawaye take sosai damuwa tayi mata yawa ga matsalar gurin aikinta data rasa dalilin dayasa idan tashiga office dinta take jin zafi ajikinta ga matsalar rashin lfyr nasreen yanzu kuma ga abinda fu'ad yake son Bullo mata dashi.."ya rabbi ka taimakeni ... *********** Shiru yana zaune a inda tabarshi yana tunanin abubuwan sa suka faru tsakaninsa da sajida, sosai lamarin ke bashi mamaki da daure masa kai "wai yau shine ya sha bakin wata mace ,macen ma aminyar matarsa , ya Jima zaune abun na ta'ba zuciyarsa, lamarin ya maseefar tsaya masa arai, ahankali ya Mike ya fito daga d'akinsa yana cigaba da tunani zai aureta ne kmr yadda me gidansa ke bukata ko kuwa zai dojewa aurenta ne ? Yana fitowa ya ga wulgawar najma ta nufi d'akin nasreen bai ga fuskar yarinyar ba ,sai bayanta ya hanga doguwa ce Amman ba can ba ,kad'a kansa yayi sannan yashige kitchen coffee ya had'awa kansa ya fito rike da cup din yana kur'ba har yak'araso parlour'n ya zauna tare da d'aukar remut ya kunna tv ya canza channel zuwa CNN yana zaune har 12:00 dot kuma har lokacin zuciyarsa ta kasa samun natsuwa, ya sake mikewa yashiga d'akinsa yana shiga ya iske wayarsa na kara yakarasa cike da sanyi jiki ya d'auka yana duba screen din wayar wata number yagani wace bai Santa ba da kmr bazai d'auka ba saboda bai cika d'aukar wayar da baisani ba Amman dai zuciyarsa ta umarceshi daya d'auka Mmn sudais ce 💗💗💗💗💗💗 'YAN CINKI 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 ~NA~ *AYSHA A BAGUDO* ~DEDICATED TO~ MRS ADAM ( YAR MUTAN KAGARA) Page 73 .......Sautin muryar sajida yaji ta doki cikin dodon kunnenshi, Wanda hakan ya saukar masa da jin wani yanayi na daban sakamakon tuno moment dinsu na dazu, goshinsa ya Dafe yana me Jan dogon tsaki tare da furta "matsala........ Bangarenta itama naunayen ajiyar zuciya ta sauke lokacin dataji sautin muryarsa sai dai taji haushi abinda ya fad'a ,Amman sai kawar da hakan ta kwantar da muryarta sosai tace "na ta kuraka ko ? "Am really sorry nima banso hakan ta kasance ba ,na kasa bacci ne sakamakon tunaninka daya addabi ruhina, shiyasa kaga kirana a daidai wannan lokacin,but kai me kakeyi da bakayi bacci ba har yanzu...? Tayi masa tambayar tana sake kamkame wayar a kunenta tana jin is like suna makale da junansu .. Fu'ad lumshe idanunsa yayi yana jin wani sabon yanayi a game daita wanda bai San ko na mene ba ,yana bin ilahirin jikinsa tare da kaiwa kowani shashi na gangar jikinsa ziyara , yayinda duk wata kafar gashi dake kwance ajikinsa suka soma mikewa,ahankali har suka mike duka , ya furzar da iska me dumi ta bakinsa "wai meke damuna ne ? Ya tmbyi zuciyarsa yana shafa sumar kansa sannan yasamu guri ya zauna daga gefen gadon yana bud'e idanunsa , cikin murya me cike da kasala yasoma kira sunanta "sajida .....meye matsalarki dani dakike kok'arin shiga rayuwa? "I think na gaya miki ki fita harkata ina son matata and bazan iya kara wani aure a halin yanzu ba ,kuma ko auren zanyi not you sajida saboda gbdy bakya daga cikin tsarin matar danake so ....dan hk tun wuri ina umartarki da ki bar rayuwata plz tun tunanina bai soma canzawa akanki ba. Pillow ta janyo ta manne akirjinta ,tana yadda zuciyarta ke wani irin beting fastly "me yasa kake nacin na bar rayuwarka fu'ad a halin ina sonka fiyye da komai a duniya ? " me yasa baka sona fu'ad? "Na mallaki duk wani abinda cikakken nmj yake bukata daga kyakkywar mace ,why why da bazaka soni ba fu'ad..? "tabe baki fu'ad yayi kmr yana gabanta sannan yace "ina ruwana da wani kyawunki ,wallahi idan za'a jeramin dubunku ba abinda zanyi daku saboda matata fiki komai danake bukata, sannan ba kyau akeyiwa ba ,hali akewa, wallahi in dai nace miki kin tsarinki yayi min zan aureki nayi miki karya sajida , kawai saboda babu kyau wulakanci ne yasa kikaga nake raga miki, domin duk wanda yace yana sonka yagama maka komai arayuwa, to be your last warning sajida da zaki kirani arayuwarki saboda banason hkn sannan bana bukatar mu'amula dake..... "Haba fu'ad me yasa kake min haka ko dan nace ina sonka....? "Exactly...abinda kika fad'a haka ne ,saboda kince kina sona yayinda ni kuma bana bukatar hakan ,zanso ki fahimta hakan azahirance , saboda idan kika lura ni dake bamu dace ba duba ga yadda kuke da matata,sannan Baki min ba Dan hk ki barni na karashe sauran rayuwata da matata bana bukatar wata sabuwar matsala ayanxu so Dan Allah kiyi hakuri ki janye kudirinki akaina ni yanzu ba soyayya bace a gabana .. cikin fushi da bacin rai daba San lokacin daya dira acikin ranta ba tace "haba fu'ad Dan nace ina sonka, ta yaya arziki na binka kake gudu? "KaSanin bazan ta'ba neman Abu ban samu ba balle abinda zuciyata ta kwallafa rai akai na Jima ina dawainiyya da dakon soyayyarka ,ina sonka kuma sai kazama nawa saboda. Babu ruwana da wata matarka ko dangantar dake tsakaninmu ,bugu da kari dan dady na yana min abinda nake so ,ahalin yanzu babu abinda yafi bukata kmr yaga nayi aure tunda nayi bika ta lallami kaki to zakaga abinda zan biyo baya sbd dole kazama mallakina.... Shima a matukar fusace yace "kin dad'e bakiyi fushi ba ,kuma wannan abinda kikayi yanzu yana cikin abinda yasa bazan so ki ba, idan kina takama da kudi ko wani abu ,to ni banida komai , ke dadynki ne gatanki ni kuma Allah ne gatana shi zai tsaya min a dukkan lamurana, sannan shine bai doramin sonki ba da ina sonki sajida zan iya aurenki to banasonki ....dan hk karki sake kirana akan wannan banzar issue din ya k'arasa fad'ar hk yana katse kiran ya cillata saman gado ya juya ya kwanta flat tare da dafe goshinsa. Tsaki taja "har ni zance ina sonshi yaki amincewa, duk da kyau'n da Allah yayi min ga tarin kudi? "Me matarsa tafini dashi dayake wulakantani akanta ? "Ai kuwa duk abinda zai faru sai dai ya faru Amman sai na aureka fu'ad koda kuwa zaka mutu byn na aureka...... ********* Daren ranar tarihi ne ya sake maimaita kansa Domin daga me'ad sajida fu'ad duk babu wanda ya runtsa acikinsu kowa da tunani dayake har garin Allah ya waye Dan har gara ma ta kwana yin nafilfili ne ..... ******* Tunda najma tazo gidan take yin abinda ya kawota, tare da kaffa kaffa da kanta ,Dan tasha jin labarin me'ad agurin yayarta ummi, Sam bata da mutucin ga masu aikinta duk kankatar laifi zata iya tozarta mutun akansa, gashi batasan darajar mutane ba acewarta ,shiyasa abinda aka kawota dominsa shi takeyi ,sosai take bawa nasreen kulawa tare da janta ajiki dan har yarinyar ta fara sabawa daita, yau takama ranar asabar , ta tashi da wuri domin killace gidan duk da baya daga cikin abinda ya kawota gidan, sai data share koina ta gyara tazo inda me'ad ke zaune tana tura sakonni a system dinta, sanye cikin wata hadaddiyar Riga da wandon jeans , tayi maseefar kyau cikin kayan sai kamshi ne ke fita ajikinta sam bazaka ta'ba cewar itace ta kawo nasreen duniya ba ,yayinda nasreen ke gefenta zaune tana zuba mata shagwaba iri iri . Takaraso nesa kadan dasu tare da gaisheta cike da ladabi ,bata ko kalli inda take tsugune ba balle ta amsa mata tacigaba da aikin gabanta. Najma cikin bakinciki da takacin wanda bata da ikon magana tunda Allah yayi abincinta a wajenta yake dole ta sawa zuciyarta hakuri har ranar da Allah zai yaye mata ahankali tace " nasreen tashi muje ki sha magani .."kawo mata nan me'ad tayi mgnr atakaice batare data dago ba. Nasreen kuwa d'aura kanta tayi a saman cinyar mamanta tana zuba shagwaba "momy..... "Yes baby what did you want? "zanci indomi wit egg.. "Sai ki tashi kije ki soma dafa mata abinda ta bukata ko, ta kuma jifanta da wannan maganar atsawace cikin isa da nuna ita din wata ce me iko Akanta.... Najma ta mike ta tashi duk jikinta yana rawa tayi wajen aiwatar da ,abinda uwar d'akinta ta sata ta fito barandar gidan anan taci karo da wani kyakyawan mutun matashi wanda ba sai an gaya mata ba ,tasan mijin aunty ne Dan haka gwiwa biyu ta durkusa har kasa tace "ina kwana... Fu'ad yayi kuri da ido yana kallonta cikin tsananin mamakin ganin wannan kyakkywar yarinyar wace shekarunta bazasu wuce shabakwai ba amatsayin me aiki ,sosai ya tsura mata idanunsa cike da tausayawa yasan babu da rashi irin na talauci ne ya haifar da hakan gareta, "Allah sarki rayuwa azahirin gsky talauci bai yi ba ,bai sani ba kodan ya fito daga tsantso talakawa ne yasa yake mugu mugun tausayawa talaka .... Ita kam kallon da yake mata ne yasa jikinta d'aukar rawa ta mike da sauri ta bar gurin ta nufi d'akin da me'ad ta nuna mata tun farkon zuwanta gidan ,cikin sauri tashiga store ta d'auki indomin data kaita ta sake dawo cikin rawar jiki da sarsarfa a hanyar suka kuma cin karo da fu'ad wanda ke tsaye a wajen data barshi. Shi kuwa bayanta yabi da kallo yana ta kallonta duk tausayinta ya cika masa zuciya, Da irin rayuwar data samu kanta ta babu, wanda har yasa take aikatau agidan mutane Dan su samu rufin asiri .. Tana tsaye acikin kitchen din tana dafa indomin zuciyarta harbawa tare da hasko fuskar mijin uwar d'akinta ,tunda take bata taba ganin halittar data d'auki hankalinta alokaci daya ba kmr shi ,ya had'u sosai babu karya ,duk macen data ganshi taga cikakken njm, ahankali damuwarta ke juyewa zuwa farincikin dabasan dalilin faruwar hkn ba . Bayan najma tagama dafawa nasreen indomi ta kawo mata har inda suke zaune da me'ad ,ta janyo center table ta d'aura mata sannan ta nufi d'akinta cikin sauri ta kwaso magungunanta ta dawo ta raku'be agefe tana jiran tagama tabata magani , tana nan har tsawon minti talatin tsayuwar jiranta, saboda itama nasreen kmr yanayin uwarta gareta gurin cin abinci ,ana ci kmr ba'a son ci,tana kallonta ta ture plate din gefe alamun takoshi sannan cikin rawar jiki ta nufi dispenser ta tara cup ta tsiyayi ruwa ta dawo tasoma balbale magani ta miko mata cikin rawar jiki Dan batason tayi kuskure agaban uwar d'akinta. nasreen ta 'bata rai sosai tana turo bakinta Dan tasoma gajiya da shan magani saboda makoshinta na mata zafi a duk lokacin da zata sha ," najma bazan shan maganin nan yanzu ba ki bari zuwa anjima am so tired with it.. da sauri najma ta sake matsota "ki d'aure kinji nasreen an san shan magani da wahala amman d'aurewa ake kinji nasreen din ummanta.... me'ad tayi jimmmm Tare da barin abinda take ta D'an juyo ta saci kallonta sannan ta d'auke kanta duk da batason yarinyar sai dai taji dadi sosai da kulawarta ga tilon diyarta. "amshi ki sha kinji nasreen din ummanta ..... Ta sake girgiza mata kai da kyar dai da rarrashi da komai ta samu ta lallabata sha sannan ita kuma ta tattara magungunanta tayi d'aki dasu. ta dawo ta d'auke plet Wanda zuwa lokacin me'ad ta bar parlour'n zuwa d'akinta da waya manne a kunneta . Har zata koma ta zauna kusa da nasreen sai Ta samu kanta da son sake ganin fuskar kyakyawan mijin aunty... Ahankali ta isa bakin barandar tana lekensa tana waigen bayanta gudun kar me'ad takamata tana kallon mijinta , tana tsaye tana sake tsintar kanta cikin matsanancin farinciki mara misaltuwa, "kai mutumin nan ya had'u fa kmr wani balarabe , anya ma bai had'a jinsi da rabawan asali ba kuwa ? Tayiwa zuciyarta wannan tambayar tana murmushin jin dadi "kai wasu dai sun marewa rayuwar duniya "shi da matarsa da yarsu masu shegen kyau duk da yadda mutane suke zuzuta nata kyau,ganinsu family din gidan yasa ta raina nata, Dan ko kama kafar nasu kyawun batayi ba ,"ina ma za a had'a? haka tayita zance zuci tana murmushi kmr wace akayiwa albishiri da samun gidan aljannah. cikin haka me'ad ta dawo parlour'n ,inda idanunta ya sauka akan najma tana kalle mata fuskar miji batare daya sanin tana tsaye ba.. Gabanta ne yayi wani irin bugawa yashiga dukan uku uku me zata gani yau kuma ? "Ba dai mijinta take satar kallo ba? " inna lillahi wa inna ilaihi rajiun tashiga furtawa acikin zuciyarta gabanta na sake dokawa, yayinda ahankali tashiga d'aga kafafunta zuwa inda najma ke tsaye tana cigaba da kallonsa ,me'ad nagama karasowa bata tsaya wata wata ba ta damki bayan wuyanta batare da tace mata uffan ba ta nufin hanyar karamin parlour daita, sannan ta sakar mata wuya tare da ingizata tana aika mata da wani irin mugun kallo a kaskance, wanda take hanjin colin najma tasoma cakudewa ta hau mazurai jikinta na rawa ,take tayi saurin durkushewa kasa ta dukar da kanta kasa tana wasa da yatsun hannuwanta tana jiran jin abinda zai fito daga bakin uwar d'akinta . adduar take aranta Allah yasa bata kamata tana kallon mijinta ba, kafin kace tuni gumi yashiga tsatsafo mata zuciyarta na bugawa kmr yadda na me'ad ke harbawa ,tsawon minti goma najma na durkushe Amman Dan tsabar wulakanci me'ad bata ce mata komai ba ,baya ga idanun data tsareta dashi Wanda ita najma take jin kmr ta tashi ta zura aguje tabar gidan. sai data gama kallonta a wulakance sannan ta yatsina fuska tace " ke Dan ubanki me yasa kike kallon mijina? "na kawoki gidana Dan ki dinga kallon mijina ne? "Ko daman abinda ya kawoki kenan ki dinga satar kallon mazajen mutane yasa kike yawon aikatau agidajen mutane? Tayi mata tmbyr tana zabga mata uwar harara. Najma tayi saurin d'ago kanta tana girgiza mata kai .. "Aiki na kawoki kiyi min ba kallon mijina ba ... ? "Lalura ce yasa nace akawoki min ke Dan ubanki domin ki dinga kula min da yarinyata, Ba wai kishiga hurumin gidana ba Dan I can't take this nonsense, shara wanke wanke da sauran ayyukan gidan bance kimin ba, kinsa kanki ne non of my business Dan bakurtuwa bace ni zan iya abina , ni dai magani kawai nace kibawa yarinyata akan kaida tare da bata kulawar datace while kudin aikinki kuma momy ce zata dinga bawa iyayenki Dan haka banga dalilin da zai saka ki dinga labe kina kallon min miji ba ko kina son shi ne? Da sauri Najma ta d'ago ta kalli me'ad cikin mamaki jin furucinta ,"yanzu ita tunaninta kenan ita har ga Allah bawai sonshi take ba ya dai mata kyau ne kawai yasa ta kalleshi . A matukar tsawace me'ad tace "me nene kikayi saurin kallona, ko karya nake miki ba kallon mijina na kamaki kinayi ba ? Najma ta sunkuyar da kanta cikin fargaba "wayyohlly Allah ka ceceni meye kaini kallonsa gashi najawo kaina tozarci..? "Dan ubanki daga yau na sake ganin kin la'be kina kallon min miji sai na miki dukan mutuwa sannan na tattaraki na aikawa iyayenki da ragowar gangar jikinki stupid kawai yara kanana daku sai jarabar iskanci tsiya ,yanzu ma kisawa ranki ba kisamu gidan zama ba ,at anytime zan iya gargad'anki kibar min gida wawiya shasha kawai maza ki tashi ki koma dakinki banason ganin wannan shegiyar fuskar taki.. najma ta tashi duk jikinta yana rawa "kiyi hakuri Dan Allah.. Wunin rana cikin damuwa me'ad ta wuni tana tunanin, ita ba abun ta kori yarinyar ba ace bata da hakuri tacika maseefa,if not da wallahi bazata sake kwana mata agida ba, rarrashin zuciyarta tayi sosai sannan ta dan dawo daidai ....yayinda najma bata sake gangancin kallon fu'ad ba hatta hotonsa dake manne da parlour'n gidan bata kuskuren kallo, da zarar taga shigowarsa take barin gurin, gbdy a matukar tsorace take da matar gidan. ******** Shi kuwa fu'ad tunda yasanya najma a kwayar idanunsa yarasa meke damunsa ,shi dai haka kawai take bashi tausayi yana zaune yana tunanin rayuwa da yadda sajida take fautarsa babu dare babu rana duk inda yayi tana biye dashi wata rana har gidan take biyosa tayita satar kallonsa da zarar idanun me'ad zai kai gareta sai tayi saurin d'auke idanunta . yana cikin wannan tunanin ne yaji sautin muryarta "ina yini abban nasreen tayi mgnr tamkar yadda me'ad Kan kirasa wani lokacin, Yayi Firgigib alokacin da har taje bakin kofar shiga kitchen. "Zo nan fu'ad ya fadi hakan cikin sanyayyiyar muryarsa me matukar dadi da kashe jkin wanda ya saurara, sannan yacigaba zo nan ki zauna ... Najma tayi saurin juyowa ta kalleshi cike da matsanancin mamakin tana nuna kanta gabanta na wani irin faduwa ,ya d'aga mata gira tare da cewa "kizo nan dake nake karki damu kanwata tamabaya nake son miki in dai bazaki damu ba Mmn sudais ce 💗💗💗💗💗💗 'YAN CINKI 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 ~NA~ *AYSHA A BAGUDO* ~DEDICATED TO~ MRS ADAM ( YAR MUTAN KAGARA) page 74 .....sunkuyar da kanta tayi kasa sosai ,sannan ahankali tasoma takowa zuwa inda yake zaune xuciyarta na wani irin luguden bugu da karfi sakamakon idanunsa dataji suna yawo a gbdy sansar jikinta. har tak'araso kanta na sunkuye akasa batayi kok'arin d'agowa balle ta samu damar kallon idanunsa dake tsare daita,cike da matsanancin sanyi jiki ta samu guri ta zauna a gefensa a takure tana fargaba kada uwar d'akinta tasameta zaune kusa da rabin ranta tashiga uku . Tsawon minti biyar bai ce daita komai ba illa idanunsa datake ajikinta, jin shirun yayi yawa ne yasa najma tace "zan iya tafiya saboda tsoro nake ji wallahi..... wannan furucin nata yasa fu'ad yin firgigib dan ya tafi duniyar tunanin ya saukar da numfashi da kyar yana lasar lips dinsa na kasa sannan yace "uhm dama so nake in miki wata tmby, da fatan zan samu gamshiyar amsa? Muryarta na cracking tace "kar..karka damu kayi duk wata tambayarka sai dai wallahi a matukar tsorace nake takarasa mgnr kmr zatayi kuka ...... "Ki saki jikinki babu abinda zai faru, kafin nace komai yaya sunanki? "sunana najma ta fad'i hkn tana sake dukar da kanta kasa sosai dan gabadaya wani irin yanayi ta tsinci kanta ciki da bata ta'ba jin irinsa ba. "najma ya sake maimaita sunan acikin zuciyarsa ,saboda dad'insa da yaji , muryarsa a tausashe yace "amman ba real name dinki bane ko......? "uhmmmm hauwa shine asalin sunana"ok hauwa nayi matukar mamakin dana ganki a cikin irin wannan yanayin wanda sam bai dace da yarinyar k'arama kamarki ba, Amman sai gashi na tsinceki acikinsa. "karka damu da yanayin daka ganni ciki domin duk rayuwar 'yan gidanmu a haka ta faro, kuma babu mamakin a haka zamu k'are muna aikin bauta Dan tallafawa rayuwarmu, najma ta fad'i hk cikin murya mai rawa ala'mun tana son yin kuka. fu'ad yaji ya sake narkewa akan kogin tausayinta, dan kamarta kamata yayi ace tana tare da iyayenta ko tana makaranta gurin d'aukar darasi, ko kuma tana d'akin aure amman yanzu gata a wulakance tana aikin bauta a inda bai zama dole asan yancinta ba . Hakika talakawa na matukar shan wahalar rayuwa, idan ma sun dogara da karatu, sai suyi karatun su gama aiki ya zamemusu wata jarabawa ta musamman me tsananin wuya.... Najma ta matsu ya sallameta kafin me'ad tasanyo kai ta iskesu tare Amman yaki bata dama sai ma idanunsa da tsura mata yana kallonta.. sautin muryar me'ad taji ta kwalla mata Kira dan haka a matukar zabure ta mike tsaye ta fita aguje ta nufi inda take ,dan wani irin maseefaffen tsoron me'ad din takeyi kmr rai da ajali, fu'ad yabi bayanta da kallo cikin tausayawa har ga Allah yake jin tausayinta wanda kusan da wannan zuciyar ya taso na tausayawa talaka 'yanuwansa ,Sam arayuwarsa bai ta'ba zai aure diyar me kudi ba sai ta Allah takasance dashi ya rikitacciyar matarsa. Tana isa gurin me'ad wata uwar harara ta banka mata "dan ubanki me nasaki kiyi da kika je kika zauna ko kin tsaya kalle min miji ne yau ma? da sauri najma tace "wallahi aunty ban kalleshi ba shi... "yi min shiru zaman uwar me kika tsaya yi kmr keda gidan ubanki wannan talaka......... "talaka ai mutun ne mai godiya ga duk yanayin daya tsinci kansa dan yafi mai yin zamba cikin aminci sau d'ari, kuma yadda gidan nan bana ubanta bane kema haka zalika bana naki uban bane, dan haka babu wani me tutiya dashi balle har wani ya gorantawa wani.... tare suka juyo me'ad da najma duk da me'ad tasan mai yin wannan maganar amman ta kasa hakuri gara dai ta juyo ta sake tabbatarwa zuciyarta. fu'ad ne tsaye kafin daga baya yakaraso zuwa inda suke fuskarsa a d'aure ..ya Matso gareta kmr zai shige cikin jikinta ya kai bakinsa cikin kunnenta. "Yarinya zaki gane kuskurenki da kuskuren abinda kika shukawa idan lokacin hkn ya kusa yayi mgnr kasa sosai ta yadda yasan ita kad'ai ce zataji abinda yace . me'ad tayi shiru tana kallon fu'ad abinda bai ta'ba mata ba kenan yi mata fad'a gaban kowa balle gaban me aikinta ,dan haka cikin 'bacin rai da daga murya tace "ke jeki kiyi abinda ya kawoki gidan nan da kika yi wani tsaye akanmu kina kallonmu kmr wata tsohuwar mayya...... najma da daman abinda take jira kenan ta bar gurin jikinta na rawa..... me'ad ta dawo gefen fu'ad ta tsaya batare data kalleshi ba "fu'ad ina son nagaya maka koda goma ta lalace kasan tafi karfin biyar fu'ad , duk nasan dalilin dayasa kake min irin haka da min kallon gani gani , bakomai bane facce kawai da naki ajiye wannan aikin ne . "Kasani har kullun bazan gaji gurin gaya maka tasiri da mahimmancin shi wannan aikin da taimakonsa ga rayuwarmu ba. duk yadda nake son ka fahimta nassn ka fahimta hkn fiyye da tunanina, kawai so kake ka nuna min qunjinka akaina amatsayinka na d'a nmj me ragamar komai . "Let me tell you something dakace kaine kake d'aukar salary dina bazan ta kura kaina ba saboda nima Hutu ne gareni na zauna agida naci na sha na kwanta na huta kmr sauran mata masu 'yanci da gata ..., "Amman tunda baka d'aukar sama da abinda nake d'aukar ko daidai da salary dina kasawa ranka zuwa aiki dole kuma yanzu na fara zuwa dan idan na zauna bansan me naka salary zai tsinanna mana ba.." and to be your last warning da zaka min fad'a gaban wannan yar iskar yarinyar ,duk abinda zakayi let it be beween me and you , abinda dai kake so ne bazai ta'ba yiwuwa ba na ajiye aikina na zauna agida jiran tsamani daga karshe na dawo bara agurinka kana min wulakanci it can be possible.. .. "shikenan tunda haka kika za'bawar kanki zakiga ikon Allah zakiga abinda zai faru acikin gidan ,zaki sha mamakina wallahi duk wani takama da gata da jin kai da kikeji ni fu'ad nayi miki alkwarin sai na sauke miki shi ,sai kinyi kuka idanunki akan..... "babu wani abinda zai faru sai ikon Allah ta katse shi hankalinta a matukar tashe tana haki ," banida kowa sai Allah kuma kullun inagaya masa duk wani sharrin dakake nufina dashi allah ya meida shi kanka, alkhari dake tattare dakai kuma Allah ya kusantoni dashi.." haba ta yaya ga gsky kiri kiri bazaka yi aiki daita ba kana neman take abinda kasan barinsa a zahirance bazai ta'ba yuwa ba ,kuskure nayi ,na d'aukarwa zuciyata nayi maka laifi ,ajiye duk wani abinda nake ji akaina na baka hakuri me kuma kake so daga gareni ? "idan kuma ba raina kake farauta bismilla gani agabanka ka kasheni ka huta daganina a doron duniya is better ka'ajiye komai mu rungume juna da tilon diyarmu da allah yabamu arayuwa abinda ya faru atsakaninmu yana faruwa har ma fiyye damu har bisa ga yanxu banyi girman ba ina sake baka hakuri ka yafe min , fu'ad har yanzu sonka na nan acikin zuciyata bai sauya ba kuma zan rayu da kai koda kuwa baka sisi basoda ba Dan wani abu naka sonka ba ......... tana gama fad'ar hk ta juya cikin matsanancin 'bacin inda ta iske najam tana ta aikin sharar dabatasata ba, bata kalli inda take ba tashige ta nufi shashinta .. washegari sajida da me'ad suna zaune Wanda shigowarsu kenan ,najma tashigo inda suke Sajid naganinta ta mike tsaye tana kallonta wani iri "ke lafiya daga ina haka? najma tayi saurin zubewa kasa ta sunkuyar da kanta bata sake yunkurin kallonta sajida ba, sai ma fuskantar me'ad da tayi tace "aunty sannu da dawowa sannan ta gaida sajida, sajida batare da ta amsa ba tayi saurin kallon me'ad muryarta na rawa " ,me'ad ta ina kika samo wannan mahaukaciyar? ta fad'a cikin daga murya ...uhm me'ad ta sauke naunauyen ajiyar zuciya kema fa kya fad'a wai nan me kula da NASREEN ce abun kazanta ko? najma ta mike zata bar gurin me'ad ta tsayar daita da cewa "ke daga yau karki sake zuwa idan kinga ina da baki kinj ko? najma ta kad'a Kai alamar to sannan ta tashi cikin sanyi jiki ta fita .. sajida ta saukar da numfashi tarasa dalilin data tana ganin yarinyar lokaci daya ta tsaneta ,ta juyo ta fuakanci me'ad "wai ni me'ad menene yake son faruwa agidanki anya babu wani kulli agame da yarinyar nan? "me'ad ta ta'be baki "me yasa kikace hk? "saboda ina jin tsoron kada abban NASREEN ya ....sai tayi shiru ta kasa karasa abinda take son fad'a. sajida nasan abunda bakinki yake son fad'a amman ina son kisani har abada fu'ad nawane ni kad'ai ne kuma mijina ne har tsufa ,masu ajin ma bai sauraresu ba balle wannan abar ,karma ki sake furta wannan kalmar ko hasasho yuwar hkn mijina mijin mace daya ne .. ************ Duk yadda fu'ad yake tunanin yana tausayin najma abun ya zarta hkn ,shi dai akaron kansa yarasa dalilin da tsagwaron tausayin yarinyar ya tsaya masa azuciya ,"tabbas Yasan bai Son yarinyar a Amman yana bukatar ya yantota daga bakar rayuwar datake ciki "amman ta yaya zai soma taimakon nata batare dayasamu wata matsala ba ? Yayiwa kansa tmbyr da bashi da amsarta kuma bashi da me bashi amsarta . Yana cikin wannan tunanin yaji ana knocking kofar office, kai tsaye yaba da umarnin shigowa yana me dukar da kansa domin cigaba da aikinsa da tunani najma ya dakatar dashi . Tashigo office din cike da doki son d'aura kwayar idanunta akansa ahankali ta meida kofar ta rufe har da sanya mata key ,sannan tayi tsaye a guri daya, tana kallonsa tmkr an dasata tsabar farinciki ganinsa datayi ,"yaushe rabon datasanya shi idanunta? " gbdy ya kulle duk wata hanyar da zata sadasu da juna, shiyasa yau tayi kundin balar biyosa ofishinsa domin tsaida mgn daya me yiwuwa ayita ta k'are . Jin shiru shiru wanda yashigo bai yi mgn ba yasashi d'ago kyawawan idanunsa masu matukar kyau da tsoratarwa ya saukesu akanta tsaye sanyi cikin after dress baka har kasa ta yane kanta da bakin mayafinta sai wani shaning take ,sai dai daga saman after dress din abud'e yake wanda duk me fuskantarta zai iya hango cikar halittar kirjinta , haka tashigo dashi abude ko kuwa sai da tashigo ta bud'e shi ,shi dai bai sani ba kallo daya yayi mata ya dauke kansa daga kallonta yana mamakin kasada irin nata...fuskarta kunshe da dry tasoma karasowa zuwa inda yake tana girgiza masa jiki da nonuwanta tana gama Karasowa garesa ta koma laulausar tafin hannunsa cikin nata lummmmmm ta lumshe idanunta tana jin sanyi sonshi na ratsata ta koina ajikinta... A matukar fusace ya zabura ya mike da niyyar d'auketa da wani gigitaccen Mari kawai sai ganita yayi ajikinsa ta rungumeshi tare da had'e bakinsu guri daya tana kallon cikin kwayar idanunsa tare da shafa masa nonuwanta tana kashe masa ido...wani irin uhmmmmm yasoma ji ajikinsa nan da nan joystick dinsa ta mike gal kmr zata fasa masa wandosa ta fito, gbdy tasoma rikita masa tunaninsa har yake jin acikin wannan halin zai iya cinta kai tsaye...saboda yadda take masa bakinsa ta saki byn tagama tsotsa kmr zata cinye "fu'ad takira sunansa me yasa bakasona..? "Me kakeso nayi maka ka aureni?"ina sonka zan iya maka komai...plz ka aureni takarasa mgnr tana kamo hannunsa ta d'aura saman tudun nonuwanta "wayyohlly yana jin hanunsa Kan nonuwanta ta sake susucewa joystick dinsa na sake mikewa har tana iya jiyo har bawanta, yayinda shi kuma yake jin kmr yace tayi masa goho yacita ya huta ba dai ya aureta ba ..dan a yanzu ya fahimci sajida ba sonshi take ba shaawarsa take..ahankali ya lura da yadda take kallon joystick dinsa dataki kwanciya duk yadda yaso yayi control din kasan, ai bata tsaya wata wata ba ta kai hannunta samanta tasoma shafawa, yayi saurin d'auke numfashi yana runtse idanunsa gam tare da cizan lips dinsa da iyakacin karfinta, yayinda joystick dinsa ke sake mikewa tana fallasa asirin kanta ita kuwa sai aikin shafawa take tana kallonsa kafin ahankali ta sakar masa wanda sai daya sauke naunayen ajiyar zuciya ta rungume sa tsam ajikinta, tayi lamo akirjinsa , zubar hawayenta kawai yake taji ajikinsa yadda har ta fara jiqa gaban "ka yarda ina sonka duk wannan abinda nake yi duk cikin sone, duk tsawon shekarun danayi zaune, na zaman jiranka ne ,idan kaki aurena ya kake son nayi da rayuwata? Duk maganganunta ji kawai yake ba Dan suna shigarsa ba ,saboda shi idan duk duniya gatanta ne shi fa bai jin zai iya aurenta, kokarin dagota yake daga jikinsa Amman sam taki yarda sai sake manne masa datayi tare da wayon nunkusar da abu mafi tasirin ajikinsa "ita kanta tasan a wannan lokacin karya ne idan ta mallaka masa jikinta yaki, cikin wayo da dabara ta sake hade bakinsu guri daya tasoma kissing dinsa tun daga wuyansa har zuwa kirjinsa datasamu nasarar balle botira, shima bai San sanda ya kai hannunsa Kan nonuwanta ba ta cirosu yasoma murza kansu yana matsesu, kafin daga baya yasoma ya zare bakinsa ya kai kan nonuwanta, yana tsotsar kan gbdy sajida tagama jikewa kmr yadda shima ya jiki tasoma tafiya dashi suka baro mazauninsa zuwa doguwar kujera ta kwanta ta janyosa jikinta yacigaba da tsotsar nonuwanta tana bankaro masa kirji... Mmn sudais ce 💗💗💗💗💗💗 'YAN CINKI 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 ~NA~ *AYSHA A BAGUDO* ~DEDICATED TO~ FAIZA HAMMADU BARAU (YAR NUMAN) Page 75 ...cikin wani irin yanayi me wuyar misaltuwa Sajida ta zare kan brest d'inta d'aya dake cikin bakinsa dayake faman aikin tsotsa tamakar yasamu sweet, tasanya duka hannuwanta ta Janyoshi zuwa jikinta sosai ta yadda gashin fuskarsa ke gugan brest dinta, wanda hakan ya sake haddasa mata jin wani irin dad'i na sake shiga kwakwalwarta da sansar jikinta. yayinda ahankali k'amshin turarensa ke kaiwa hancinta ziyarar dake sake hura wutar soyayyarsa ,take jikinta ya hau kyaqayi dan abinda bata jinsa ajikina ba kenan wannan shine karonta na biyu dataji wannan sanyayyiyar dad'in daga garesa ji take tmkr ana zarar ranta hannunta tashiga kai kawo dashi ajikinsa tana lasar cikin kunnenshi . Ahankali ta sake tsunduma shi cikin tafki sha'awa wacce ke da wuyar bari, ta hanyar sake kai brest dinta daidai bakinsa. shi kuma kamar wani mayunwacin zaki jikinsa na kyarma ya sake d'aura harshensa akansu yana tsotsa while dayan hannunsa na aikin murza kan d'aya, wata irin mika tayi tare da shigewa cikin jikinsa tana fitar da wani numfashi hade da kai hannuta ta kamo joystick dinsa tana lailaya Kan, wani irin d'aukewar numfashi Fu'ad yayi joystick dinsa tashiga haniniya tana ambaliyar ruwan dadi gaba d'aya ji yayi duk wata jijiya dake aiki a jikinsa ta amsa tana bukatar mahad'in rayuwarta sosai ta dinga lailaya Kan kaciyarsa dake k'ara girma tana kunburowa da tsiyaya ,ina zai barta da wallahi tsaf zata zuke ruwan dake fita daga cikinsu, bata jin akwai abinda zatayi kyakyami daga garesa koina kamshi yake fitar a sansar jikinsa duk inda kai hancinta kamshi take ji ..ahankali tasoma k'ok'arin rabasa da kayan jikinsa ta hanyar balbale ma'balin rigarsa inda take gbdy halitar kirjinsa ta bayyana gashi ne kwance tundaga saman kirjinsa har marasa suna zuba sheki , itama a wannan yanayi wani abu take ji yana yawo ajikinta tun daga tsitsiyar kafafunta har tsakiyar kanta uwa uba kasanta daya jike ,tayi mugu mugun tafita haiyacinta babu abinda take so da buk'ata ,kamar tajishi cikin jikinta yana sarrafa ta, dan tunaninta da hakan kawai zata iya mallakarsa cikin sauki Dan tasan da zarar ya d'and'ana zumarta shikenan zai manta kowa da komai ya rungume ragamar rayuwarta .bank'aro masa kirjinta tayi shi kuma yacigaba da laulayasu yana murza Kan nipples dinta, magana take son yi masa Amman tasan ko ta bude bakinta da zumar ce masa wani abu mgnr bazata fito ba saboda shaukin dake dawaiyya daita "Ta k'arasa zare masa rigarsa ta ajiye wanda zuwa lokacin tuni tayi wurgi da after dress dinta tana aika masa da zafafan romancing masu rikitawa, kwakwaluwar Fu'ad ta kuma d'aukar ,duk wannan abinda take masa basabon abu bane saboda yana samunsa agurin matarsa kusan fiyye da hakan Amman bai San me yasa ya biye mata tare da k'ok'ari kusanta kansa da haram ba . Sunyi nisa sosai cikin duniyar romancing din juna tana lailaya joystick dinsa shi kuma yana aikin tsotsa nipples dinta inda sajida tasoma k'ok'arin fito da joystick dinsa domin saita cikin kasanta byn tayi gefe da pent dinta gefe shima gbdy tsuma jikinsa yake, babu abinda yake bukata kmr ya jishi cikin jikinta yana k'ok'arin shigarta yayi saurin dawowa cikin haiyacinsa jikinsa na wani irin rawa sakamakon bugun k'ofar da ake tayi da k'arfi tare da sautin muryar wasiu abokin aikinsa dayaji har cikin kwakwaluwarsa. a matukar zabure ya mik'e daga jikinta zai tashi tayi saurin rike shi cikin wani irin shauki tanason meidashi jikinta"pls Fu'ad karka barni zero zan shiga cikin wani hali ka taimaka to, ko iya romancing ne ..... Ya fixge jikinsa "tashi ki bar min office dina yayi mgnr muryarsa can kasa kmr wani mashayi ..."ta yaya kake expecting na tashi na wuce fu'ad batare da nasan matsayina ba? "Kalli ka duba halin danake ciki 10 yrs now ina faman jiranka, kai fa kana da mata ni kuma fa ta sake fixgoshi sai saman kirjinta "Dan girman Allah fu'ad ni bance dole kayi wani abu dani ba asalima zance aurenmu ne yakawoni, Dan Allah ka taimakeni ka taimaki rayuwata ka aureni......ai bata gama rufe bakinta ba ya d'auketa da wani gigitaccen marin dayasa taga wulgawar wasu taurari sannan yak'arasa mikewa yana huci yana meida rigarsa da mabali cikin wani irin fushi yace " maza tashi ki bar min office banza shedaniya, wadda tafi said'an dafi jarababba kawai maci amanar ruhi, ke dai kin lafta babban asara a rayuwar ki, mace kamar jaka babu kamun kai kina yawon bina, ke dai anyi asarar haihuwa keda tunkiya meye marabar ku? bak'ar jaka me son jefa bawa a halaka tir da halin dabbanci irin naki wawiya ki tashi ki fita kibar min office tun ban kassaraki ba wallahi..... sbd banason cigaba da kallon wannan banzar fuskan taki sannan kisawa ranki kmr me'ad taji wannan lamarin ba dai kinji kuma kin gani ba ...... Tashi tayi tana meida nonuwanta ma'ajiyarsu sannan ta zira after dress dinta tana gyara zaman rigarta ta tsura masa idanunta tana murmushin takacin zagin dayayi maya sam baza kace ita akama wannan zazzafan mari ba,ahankali ta tako har zuwa inda yake tsaye dafe da goshinsa yana cika yana batsewa takira sunansa cikin wata irin murya"Fu'ad duk abinda zaka yiwa Sajida, bazata tab'a jin haushinka ba, ko jin bakin ciki ba face sake kanainaye zuciyarta da mallaketa dazakayi, abinda bazan gaji da furta maka ba shine ina sonka kuma agaban ko waye zan furta hkn koda kuwa gaban aminiyata ce .... dan hk sai anjima ta sanya kai ta isa jikin k'ofar ta bud'e har zata murd'a handle sai kuma ta juyo fuskarta d'auke da murmushi tace "kasan yadda zakayi dani fu'ad, ko ka aureni ko kuma mu dinga zuba love akoina muka had'u....... Ta sake juyawa ta bud'e kofar,amadadin taga mutumin daya kwafsa musu gurin cima Burinsu sai gama wayam babu kowa da alamun wanda yayi knocking din ya gaji da tsayuwa ya kama gabansa.. Tana fita yashiga zagaye office din rike da kugunsa yana shafa sumar kansa kirjinsa na wani irin bugawa "wani jaraba da maseefa ne ke shirin kusanto rayuwarsa? "Kasan yadda zakayi dani ko ka aureni ko kuma mu dinga zuba love a duk inda muka had'u..ya sake furta furucinta na karshe yana cizan lips dinsa, take yashiga tunani mafuta yadda zaiyi da yadda zata barshi ta bar rayuwarsa. "anya kuwa bazai hakura ya auri Sajida ba? dan wannan salon iskancin nata garesa yayi tsamari, karfa wata rana ayi me gaba d'aya abinda bazai so faruwarsa ba kenan ,zuciyarsa ce take tunzirasa Akan ya hakura ya aureta yayinda wani bangaren na zuciyarsa ke hanasa, sai dai yafi d'aukar shawarar zuciyar data aminta ya auri sajida , "to kuma yayi yaya da taimakon da zuciyarsa ke son yiwa najma abar tausayi ? ya Jima tsaye yana shawagin tunani batare dayasan abinda yakamata yayi ba . Ganin tunanin bazai bar kanshi ba yasashi kiran me gidansa kira daya biyu ya d'auka tare da ambatar sunan "Fuad ya'akayi da lamarin aikinka komai dai yana tafiya daidai? "nasan kaji dad'in wannan cigaban daka samu yanzu ? "haka ne Sir nagode sosai da kulawarka gareni Allah yabar girma. "Ameen" "Daman nakira ne saboda ina son ganinka akwai magana me mahimmanci danake son mu tautauna dakai, "ok ina jiranka" "wani lokaci ke nan zanzo ? "Karka damu a duk lokacin dakake son ganina zaka ganni kai din ba kamar kowa bane ... "nagode sir idan natashi aiki zan biyo a ina zan sameka? "Kasameni a guess house d'ina "alright Sir yakatse kiran yana sake yi masa godiya bisa karamcinsa garesa. Koda ya tashi daga aiki kai tsaye gurin me gidan nasa ya nufa yasamu guri agefensa ya zauna tare da risinawa "barkanmu da war haka Sir" "ya kake Fuad fatan ka wuni lafiya ? "Eh Lafiya lau Sir" "Yauwa ina sauraran ka meke tafe da kai d'ana dan duk naganka wani iri kamar kana tattare da damuwa? Fu'ad yaja numfashi da kyar ya sauke kana yace " gaskiya da matsala me gida , matsalar kuma duk akan Sajida ne yalla'bai wallahi banida niyyar auren Sajida bisa wasu dalilai nawa sai dai adaidai wannan lokacin bani da zabin daya wuce na auren ta.. "Na yarda na amince zan aureta amman gaskiya ba'ason raina ba, sai abu nagaba akwai wata yarinyar agidana dake taima kawa matata gurin kula da Nasreen azahirin gsky yarinya tana matukar bani tausayi shine naga babu hanyar da zanbi gurin taimakawa rayuwarta kamar na aurenta, zan had'asu duka na aura dan haka kana iya samun mahaifin sajida da zance . tunda yasoma magana me gidansa yake binsa da kallo har sanda ya dasa aya sannan yace "wannan ba matsala bane matsawar zaka iya sponsoring dinsu 'in sha Allahu ni kuma zan nemi mahaifinta Allah yayiwa rayuwarka Albarka ,Allah yabaka ikon kula da lamarinsu . "Ameen" ya amsa mishi tare da mai sallama ya fita, yana fita yashiga motarsa zuciyarsa fal da tunani anya kuwa baiyi rashin hankali ba,na zartar da hukuncin auren Sajida ba? Da wannan fargaban ya isa gida . Bayan tafiyarsa me gidansa ya kira Sajida ya sanar mata abinda Fu'ad yazo masa dashi, yace ta gayawa mahaifinta zaizo cikin satin su gana sai dai bai gaya mata su biyu Fu'ad din zai aura ba, sosai Sajida taji dadi wannan kiran har ta dinga gani , abubuwan da suka faru tsakaninsu ne yasa hakan ta faru cikin sauri. Daren ranar fu'ad ya kasa runtsawa uwa uba ya gaza rike kansa ,duk inda ya juya zuciyarsa sai ta motsa cike da bukatuwa , wata irin kafurar shaawa ce take bijiro masa tare da addabi ruhinsa da gangar jikinsa,yayinda joystick dinsa ta mike kyamm tace dole sai taci abincinta, ahankali yasanya hannunsa ya janyo agogonsa dake ajiye saman mirrow ya duba lokaci karfe 1:00 ta wuce da wasu mintina ya waiga gefensa inda take kwance yasan zuwa lokacin ta dade dayin bacci ,ba yanzu tashigo dakin ba akalla tasamu awa biyar da kwanciya . Hannuwansa yasanya ya dafe joystick dinsa yana runtse idanunsa saboda yadda yake jin jikinsa bazai iya hakuri ba ,iya hakurinsa ya k'are ,kar yaje ya jefa kansa halaka alhalin ga matarsa, ya Mike ya sauko daga saman gadon yashiga toilet saboda yana bukatar rage mararsa ya sake wanke bakinsa ya fito yana shafa sumar kansa idanunsa ya tsurawa lafiyayyiyar matarsa me shegen kyau kmr ita ta halici kanta, sam shi dai bai ga makusa ajikinta ba sai dai ta fannin taurin kai da maseefar son aikin tsiya ,kwance take tana baccin hankali kwance kmr yar tsana duk da yaki bata had'in kullun tana makale ad'akinsa ,gadon ya hau tare da janyota jikinsa yasoma kissing jikinta wuyanta zuwa saman nonuwanta, a zafafe cikin bacci yaji ana romancing dinta Wanda ba sabon abu bane agareta dan yasaba to mata haka koda kuwa sunyi saduwar aure a farkon dare bazai hana cikin dare taji yana lalubarta domin sakeyi, Amman yaushe rabon hkn ta kasance atsakaninsu ? "Yanzu batayi mamaki Dan tasan wallahi fuad bazai taba iya daukar dogon lokaci ba matukar ba neman mata ta fara ba ,daman kuma akwai lokacin data tanada domin fito masa a mutun dinta sak da sauri tasanya idanunta cikin nasa da suka gama rikidewa zuwa green,hade rai yayi sosai Dan bayason takawo masa raini Dan bai shirya shiryawa daita ba .. jikinta a matukar sanyaye tashige cikin jikinsa ta kanainayesa tasoma aika masa Danata salon tare da had'e bakinsu guri daya tasamu nasarar cafko laulausar harshensa. kwakumeta yayi tsam ajikinsa yana lasar wuyanta zuwa cikin kunnenta tare zame yar rigar baccin datake sanye da jikinta, itama ahankali ta tashiga zame short niker dake jikinsa suka saura babu kaya ,gbdy sun fita haiyacinsu hankali kwance fu'ad ke saffara matarsa batare da wani fargaba ko jin tsoro ba, jikinta na kirma tayo kasa kad'an ta d'aura bakinta tana tsotsar joystick dinsa, sosai take sucking dinsa tare da lashe kanta "assssss ...uhmmm abinda fu'ad kawai yake iya fada yana fitar da numfashi da kyar.sai data rudashi sosai tayi sama zuwa chest dinsa tana murza nipples dinsa while bakinta na faman aikin sucking dinsa, wani irin numfashi fu'ad yake fitarwa idanunsa gbdy sun rufe sun birkice babu abinda yake muradi kmr yajishi cikin jikinta cak ya dauke ya daura saman cikinsa ya dannan Joystick dinsa cikin kasanta yana kissing brest dinta har yagama shigewa wani irin zazzafan numfashi taja yasoma zira mata sandar girma ahankali ya meidaita zaune shima ya zauna kafafunta lankwashe cikin nasa still joystick dinsa na cikin jikinta, kusan fu'ad bai barta ba sai daya tabbatar daya gamsu iya gamsu itama kuma babu laifi tayi kokari duk bata wuce round Amman tabiye masa suka raya daren ... Washegari da wuri ta tashi tashiga kitchen domin sake wanke masa zuciya, ahi kuwa duk yadda yaso ya d'aure mata hkn yaki yiwu Dan haka dole ya D'an saki ransa har yayi breakfast yaso kwarai yaga ko gilmawar najma ne saboda kusaan kwanaki goma kenan bai sanyata a idanunsa ba ,Amman duk iya zaman da yayi bai ga alamunta ba ,gashi lokaci na tafiya hk ya tashi ya wuce . *********** Me gidan fu'ad yasamu mahaifin Sajida da zancen inda sam dattijon yaki amincewa da maganar dayazo daita "wannan ai shirmen banza ne ,kuma shine babban abun kunyar da zata aikata arayuwarta ,"Sajida ta auri mijin Me'ad sam ni dai babu hannuna cikin wannan lamarin, "sannan ina rokonka dan girman Allah kar ka sake zuwa min da makamanciyar wannan zance Dan ina ganin girmaka, babu yadda me gidan Fu'ad baiyi da mahaifin Sajida ba,Amman yace sam ba dai da yawunsa ba haka jiki a sanyaye ya tafi.. Ai ko yana tafiya ya rufe Sajida da bala'i ta inda yake shiga bata nan yake fita ba"daman kinsa abin kunya da zaki aikata kenan shiyasa, ki kaki yarda ki sanar da kowaye zaizo neman aurenki, to wannan abun kunyar ba dani ba wallahi, barikiji ingaya miki Me'ad tamkar 'yar uwa take gareki .. "daddy ka saurari uzirina ........."babu abinda zan saurara matsawar akan wannan abun kunyar ne kuma bana bukatar a sake tada zance nan ya wuce fuuuuuuu ya nufi d'akinsa kamar zai kifa . kuka ta rushe dashi tare da d'aura kanta saman cinyar Aunty Nadiya "ki taimakeni aunty wallahi da kyar nasamo kansa ya amince zai aureni gashi dady na neman hanawa . Aunty nadiya ta d'aura hannunta saman kanta cike da matsanancin soyayya "ki daina kuka Sajida mahaifinki yafiki gaskiya wannan babban abun kunya kike shirin aikatawa arayuwarki. " ki zauna ki nazarci halakarku da Me'ad zumunci ne me k'arfi tun daga Kan iyayenku har zuwa kanku bai kamata hakan ta faru ba, duniya zata zageki "wallahi Aunty akan auren nan banki duniya ta tatsine min ba, matukar zan rayu da Fu'ad shekara goma ina zaman jiran wannan ranar amman dady nason rusa min farin cikina ta zabura ta mike tsaye cikin matsanancin tashin hankali "da kaina zan sanawar Me'ad d'in. "ko shikenan ba ....zan gaya mata yadda nake son mijinta Dan bazan iya rayuwa babu shi ...tana gama fad'ar haka ta nufi d'akinta tana wani irin kuka . ********* Najma tsaye tana faman had'awa NASREEN abinda zataci kafin ta dawo daga school sanye cikin kod'ad'un kaya tun wanda tazo dashi bata sauya ba, sun yage guri ya kai uku gashi babu yadda za'a yi ta d'inke duk inda ya yage ta had'a da d'an uwansa ta kulle hakan yasa, zanin kayan ya dangale mata sosai daman kala biyu tazo dasu daga wannan na jikinta sai wani shima ya tsufa sosai, yayinda Fu'ad da shigowar sa kenan zai shige d'akinsa yayi mata kuri da kyawawan idanunsa cike da tausayawa "wai kamar batare take da masu kudi ba an kasa taimaka mata da wasu kayan.. kmr ance Najma ta juyo taga yayi mata kuri yana kallonta take gabanta yayi wani irin fad'uwa ta matsa daga can cikin kitchen din domin boye kanta yayinda har lokacin gabanta bai daina fad'uwa ba. Fu'ad ya taka har zuwa bakin kitchen din ya tsaya batare daya shiga ba "Najma tsorona kikeji ko kunyata ? Yayi mata tambyr yana saita kwayar idanunsa akanta. Najma tayi saurin girgiza kai "dan Allah kayi hakuri ka daina min magan Aunty batason hakan tace idan na sake yi maka magana sai ta yanka ni gunduwa gunduwa. Fu'ad yayi murmushin "Me'ad kenan me rikicin ganga sannan yace "karki damu barazana take miki babu yankaki daza tayi.. Najma tayi saurin kallosa "wallahi zata iya kaga kuma in ta yankani ta yanka banza, kuma na yarda da hakan dan a shekarun baya ta ta'ba watsawa Aunty Ummi yayata ruwan zafi har ta kone a fuska, Fu'ad yaji tausayinsu sosai ,aransa yake sake jin kwad'ayin taimaka mata koda kuwa zai rasa ransa ne ya saukar da naunauyen ajiyar zuciya sannan yashigo cikin kitchen din sosai still idanunsa na kanta "Najma ina son ki taimaki kanki ta hanyar amincewa da aurena domin ina bukatar naganki kina rayuwar 'yanci... Najma tayi saurin kallonsa hantar cikinta na wani irin kad'awa gbdy ta kasa gane manufar maganar sa da inda ta dosa, ya jinjina mata kansa "zaki aureni ...? " ina son taimaka miki Amman gbdy atunani banga irin taimakon daya dace Dana miki ba kamar na aureki . da sauri Najma ta mike daga tsugunne datayi tana girgiza kai jikinta na wani irin rawa cikin wani irin tsananin tsoro da razana ,yayinda wani irin, azzafan gumi yashiga tsatsafo mata a fuska duk kuwa da AC dake aiki a kitchen d'in... " Fu'ad ka haukace .... tunda kake furta irin wad'an mugayen kalaman irin na mutumin daya haukace.. basai ya juya ba yasan mai yin wannan maganar Me'ad dinsa ce to yaushe ta dawo gidan ? Yayiwa kansa tmbyr kirjinsa na mahaukacin bugu.. ita kuwa Najma tuni ta kame dan azabar tsoro da fargaba Me'ad takaraso gaban Fu'ad ta tsaya idanunta cike da ruwan hawayen bakin ciki ta kalli cikin kwayar idanunsa ,ido cikin ido "fu'ad kabani mamaki kuma bani kunya tunda duk matan duniya babu wacce kagani kake son had'ani daita amatsayin kishiya sai wannan abar wace iyayenta suka dogara daita Amman wallahi baka isa ba dan banga abinda wannan abar tafini ba, banda lalata gidanka dazakayi.... Fu'ad ya matso sosai har suna iya jiyo hucin numfashin junansu yana kallon cikin idanunta "hakika me'ad kinyi babban kuskuren sai dai kisani ni fu'ad a yanxu yarinyar karama kmr Najma nake son aure yarinyar karama wace zata min ladabi da biyayyar danake bukata bazata min iko da takama da wani aikinta ba ko nuna min ubanta wani kosa ne a Nigeria , dan nayi alkwarin zan sake auren amman yar mara shi wato yar talaka irina da kuke rainawa saboda ganin kaskancinsu acikinku.. "anya fuad dinta bai haukace ba kuwa da har yake furta mata wadan nan kalaman masu yanayi dana mahaukata ? gbdy me'ad tarasa abinda zatayiwa Najma dan ta huce, dan duk duniya a yanzu babu wanda ta tsana take jin zata iya mata komai kmrta wadda take ganin wani namiji mai hankali komai lalacewarsa bazai iya cewar yana sonta ba, duk kuwa da irin kyawun halittarta, amman sai gashi mijinta wanda duk duniya bata had'ashi da komai ta fifitashi akan komai na rayuwarta iyayenta da komai nata wai shine yake bukatar mallakarta amatsayin mata ta fad'i kalmar a fili.. "take Najma ta d'aura hannunwanta duka bisa kanta "wayyohlly Allah nashiga ukuna daman nagaya maka Aunty kasheni zatayi tunda banida gata.. Me'ad tayi kukan kura ta janyo tunkuyar da ruwan zafi yake ciki yana tafasa tayi kan Najma dashi Najma ta kidemi tayi bayan Fu'ad batasan lokacin data kankameshi ba, tana kururuwa da ihun neman dauki. Fu'ad yayi saurin rike mata hannu dan yasan halinta zata aika balle yanzu da bata cikin haiyacinta "meye hk Me'ad kike k'ok'arin kashe yar mutane ? "kina hauka ne ko kin sha wani abu ne ni da kike son yin kisan kai bayan kinsan idan kin kasheta kema kasheki za'ayi, ni Yakamata ki illata ba ita ba saboda ni nace zan aureta . Me'ad bata sauraresa ba kaitsaye tayi kan Najma dake tsaye tana kuka jikinta na rawa fu'ad yayi saurin riketa ya rankwafar da tunkunyar ruwan zafin ya kelaya a kasa, amman Me'ad bata hakura ba tayo cikin kitchen d'in da gudu ta wawuri doguwar wuka ta biyo Najma .... Najma tayo hanyar waje tana ihu inda shima Fu'ad ya biyota ya riketa gam sai ga Sajida tashigo gidan a matukar firgice takaraso Me'ad ta tsaya tana haki wallahi sai na kasheki ..... cikin kidema Sajida ta sake motsosu zuciyarta na wani irin mahaukacin bugu take tambayar Me'ad abinda ke faruwa "sajida nashiga uku wai agabana Fu'ad yake rokon wannan yarinyar da ta taimaka ta aureshi. "ke Me'ad Sajid ta furta da k'arfi jikinta na wani irin rawa zamuyi mummunar sa'bawa dake, ta yaya zaki dubi wannan abar kice Fu'ad d'ina danake burin mallaka matsayin miji zaice yana sonta wannan maganar ma ai karyace wallahi bazata'ba zama gaskiya ba, takarasa mgnr cikin daga murya ..... tunda Sajida tasoma mgn zuciyar Me'ad ta tsaya cak ta daina aiki na wunci gadi sakamakon sakon da kunnuwana suka jiyo mata daga cikin bakin Sajid, idan dai kunneta ba karya ya jiyo mata ba fu'ad dinta taji ta furta cikin yanayin na tashin hankali "to me hkn yake nufi itama sonshi take ko shine yake sonta kmr yadda yake son auren najma? kusan minti goma tana tsaye jikinta na kyarma har lokacin tsaye kawai take bisa kafafunta babu wani wadatacen numfashi dake kai kawo ajikinta har sanda taji sautin muryarsa cikin kunnuwanta suna mata kuwa "kina mamaki jin abinda tace ko? "kina mamakin jin furucinta ko akaina ? "tabbas nasan zakiyi mamaki jin hk , har zuciyarki tayi kokari tsayawa ta daina aiki.. "kwanakin baya na tab'a gaya miki wata mgn alokacin da kika fasa wayata nace "idan kikaji wace nake waya daita zuciyarki zata buga sabida tashin hankali abun..to bakowa bace wace muke waya daita adaidai wannan lokacin face aminiyarki Sajida dake tsaye agabanki ayanxu , babu daren da zai zo Sajida bata kirani ba sannan babu garin da zai waye Sajida bata kirani ba sakoninta kuwa basu kirguwa acikin wayata domin son mallakar abinda yake mallakinki wanda ke , kike k'ok'arin bazantarwa bisa wani bazan dalili naki , gata nan ki tambayeta batace tana sonta ba , zata ajiye aikin da ke kika gagara ajiyewa dan dai kawai ta aureni gata nan .. "Kin raina albashina Amman ni ban rainasa ba har ina yunkurin kara aure har biyu dashi.. Me'ad ta juyo zuciyarta kmr zata tarwatse ta fito daga cikin kirjinta, jikinta ne dauki rawa kar kar idanunta Kan kallon Sajid. Sajida ta kalleta ido cikin ido tace "tabbas gsky fu'ad ya fad'a miki tunda muka had'u dashi a wancen lokacin naji ina mutuwar sonshi wanda Allah ne ya jarabeni da sonshi ada na boye amman a yanzu bazan iya boyewa kowa irin son da nake masa ba. cikin rawar murya Me'ad tace "so fa kikace Sajida me yasa zaki min haka? "Ki rasa Wanda zaki so sai mijina? "na aminta dake kece mafi kusancin abunda na yarda daita a duniya na kuma aminta daita "why why why sajida zaki min hk "so fa kikace kikayiwa fu'ad anya kuwa kina cikin haiyacinki? "anya cutar hauka da mantau bata kama kwawaluwarki ba da zakice kina son mijina fu'ad? "Cikin kuka ta matso kusa daita tare da kamo hannuta"kice karya ne sajida bakya son mijina.. "Ta yaya zance banason shi aminyata? "Alhalin ina son mijinki fu'ad so kuwa me tsansni son da ni kaina bazan ce ga daga inda ya fara ba balle insan inda zai tsaya, ina sonshi bazan ji shaka ko shayin furta shi akoina ba ko gaba kowaye saboda so ba karya bane, kuma bazan miki karya ba wallahi ina son fu'ad mijinki so na hakika wanda nake fatan zai kai mu gayin aure.. "sajida me'ad ta furt da karfi tana dafe kirjinta tare da furta kalmar inna lillahi wa inna ilaihi rajiun cikin matsancin damuwa sannan ta juyo tana fuskatsrsa idanunta cike da ruwan hawaye tace "da gaske ne abinda kunnuwana suke ji ayanzu "dan Allah fu'ad kace karya ne bakason yarinyar nan da tun sanda na fara sanyata cikin idanuna naji na tsaneta fiyye da komai sannan ka karyata min kallamar wannan maciya amanar abota .... "uhm duk ina sonsu kuma aurensu zanyi kmr yadda na aureki ,aduk abinda ya faru kece silar faruwarsa"wallahi fu'ad bazaka ta'ba auren wannan yariyar ba haka zalika bazaka auri wannsn maci amanar ba takarasa mgnr tana juyowa tare da damk'ar wuyan sajida "mijina sajida mijina kike so? " daman abinda ke ranki kenan shiyasa kullun kike hanyar zuwa gidana da sonji halin dayake ciki .......? "shiyasa kullum kike adduar samun miji irinsa ta a she sonshi kikeyi ta d'auketa da wani gigitaccen mari wanda yasa taga gilmawar wasu taurari ko numfashi sajida ta gagara yi yau zan kasheki so that nima na hakura da duniyar gabadaya. a gigice fu'ad yayi kanta yana kiran sunanta "wai kin haukace ne ko me da zaki dinga neman kasheta "eh na haukace maciya amana kawai sai Allah ya saka min na barku da fitowar Rana da faruwarsa .. .. ta sake dauke sajida da wani Marin gabadaya tagama birkicewa kallo daya zaka mata ka tabbatar da cewar bata cikin hankalinta ta wujijiga sajida da karfi wacce gabadaya numfashinta yagama tsayawa ,tsaye kawai take bisa kafafunta ,sannan tayi wani irin jifa daita , sajida tayi luuuuuuu zata fad'i kan dutse cikin zafin nama fu'ad ya banbare najma dake makale ajikinsa ya kai hannunsa zai tarota ,a matukar tsawace tace "kar .......kar ta 'bata fu'ad Wallahi idan ka sanya hannunka ajikinta zan aikata abinda sai kashiga uku .... cak ya tsaya jikinsa na rawa. Yana kallo Kan sajida ya bugi da dutse kara daya tayi bata sake motsawa ba . Ta wawuri wukarta da subuce ta rike gam kana tace "ke kuma karamar yar iska tayi mgnr da iyakacin karfinta har sai da najma ta zabura ta zura aguje tsabar tashin hankali data riski kanta ciki ."tsaya Dan ubanki tambayarki zanyi kafin na yankaki da hanuna, kuma kinsa idan na yankaki na yanka banza saboda babu abinda za'a yi kasancewarki mara galihu, ina son ki gaya min yaya kike jin mijina aranki kema kina son shi ne kmr yadda wannan sumammiyar ta fad'a....? Najma tayi saurin girgiza kai idanunta cike da ruwan hawaye "ki bud'e baki stupid ki gaya min kina son mijina zaki aureshi kamar yadda yace "wallahi tallahi aunty banason shi ko kad'an Dan bamu dace da juna ba Ni iyayena talakawa ne Dan haka zan auri irina bazan ta'ba auren mijinki ba duk runtsi .. "yi min shiru Dan ubanki munafukar Allah kasheki zanyi in kuma kikaga ban kasheki ba to kwanakin ne bai cika ba tana gama maganar ta zabura ta sake yin Kan najma rike da wukar tayi mata yanka yafi biyar a hannunta Amman Dan azabar naci take rike daita sai alokacin fu'ad yayi karfin halin daka mata tsawa da cewar "kawo wukar nan tunda naga abun naki ya zama iskanci ga wata kin sumar kina kokarin kashe wannan ,yana mgnr yana takowa zuwa inda take tare da kokari son kwace wukar hannunta "fuad kada kazo wajena Dan kai nayi nufi ba wannan munafukar ba zan kashe kowa a huta Dan bansa amfanin badi babu rai ba bata sauraresa ba ta sake nufar najma cikin zafin rai ta sameta a gefen kafad'a ai kuwa nan da nan jini yasoma zuba. fu'ad yayi saurin dosar wajenta bai tsaya wata wata ba ya fixge wukar yayi jifa daita saman zink sannan ya wanketa da wani mari ta fashe da kuka tare da durkushewa kasa bisa gwiwowinta " Dan abinda ya faru daita ko acikin mafarki bata ta'ba zaton zai faru ba fu'ad yayi mata wannan cin fuskar akan wasu banzaye ahankali cike da matsanancin sanyi jiki yakarasa gareta inda take durkushe tana kuka yasanya hannuwansa duka ya d'agota yana share mata hawaye, rungumeta yayi ajikinsa tsam yana Dan dukan bayanta Amman ina kuka take sosai , yayinda har lokacin sajida ke kwance sume akasa babu alamun numfashi atare daita ,cike da bakinciki mara misaltuwa tasoma kokarin barin jiknsa "fuad ka cuceni ka cuci rayuwata , "me na maka dana cancanci wannan wulakanci da tozarcin ?"yar aikina da aminyata kake yunkurin aure alokaci daya.."duk Akan aikina wanda shine rufin asirinmu ..."am really sorry love I didn't mean to hurt you Amman..... "Banason jin komai daga bakinka daman ka gaji dani har kana wulakantani tare da yunkurin sakina, am ready for it now "ka sakeni domin zanfi bukatar saki akan na zauna ka auri wannan abar da tare da wannan maci amanar "bazan iya sakinki ba me'ad da zan sakeki da tuni a wuce gurin ni dai plz ki natsu ki dawo haiyacinki koda ban auri sajida ba kibarni na auri najma bawai ina son yarinyar bane hk kawai take bani tausayi.. suman tsaye tayi agurin jikinta na sake d'aukar rawa kmr wace aka jona mata wutar lantarki idanunta sukayi wani irin canzawa "dont don't repeat it coz it's not possible, how can this possibly ka auri wannan to ka kaita ina bakagani fu'ad juya ka kalleta up and down she's not your type Amman tunda zuciyarka ta aminta bari na aunata barzahu takaraso inda najma ke tsaye tana kirma tana gama karasowa ji kake tasssss tassss saukar mari dama da hagu tasoma neman abinda zata buga mata. idanunta ne ya sauka akan wani karfi wanda duka daya idan tayiwa najma dashi tabbas zata tashi aiki . gadan gadan tayi gurin karfin ta d'auka fu'ad yayo kanta "plz me'ad karki buga mata..... gocewa tayi bata bari ya kai hannunsa jikinta ba , da sauri ta nufi Kan najma daidai lokacin da direban nasreen yasanyo hancin motarsa cikin gidan idanunta ya sauka akan abinda momy'ta ke shirin yi da sauri tun direban bai gama daidaita motar ba ta sanyo kafafunta waje ta kwaso aguje tana "furta momy karki buga mata plz ai bata gama rufe bakinta ba me'ad ta daga karfen sosai da iyakacin karfinta zata bugawa najma.. nasreen ta tsaya cak tare da rufe idanunta saboda tsoro ta saki wata razananniyar kara sai gata tana kokarin yin kasa da sauri me'ad ta saki karfen hannunta wanda a sauka akan kafar najma itama ta saki kara har da fitsari. aguje me'ad da fu'ad sukayo Kan nasreen fu'ad ne yayi nasarar isa gareta ya tallafota zuwa jikinsa ya rungumeta yana kiran sunanta, itama me'ad jikinta na rawa take kok'arin amsarta daga hannunsa "barmin yarinyarta karki k'arasa kashe min ita ........ Mmn sudais ce 💗💗💗💗💗💗 'YAN CINKI 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 ~NA~ *AYSHA A BAGUDO* ~DEDICATED TO~ FAIZA HAMMADU BARAU (YAR NUMAN) Page 76 ........ wani irin k'ara ta saka tare da d'aura hannuwanta duka saman kanta "shikenan tawa tasameni nasreen Dina zata mutu tabarni ...."wayyohlly nasreen ki taimaki mamanki ki tashi karki ki mutu kubarni cikin wannan halin damuwar danake ciki ,idan kika mutu wazan kama naji dadi? "wayyohlly Allah,"nashiga uku nah ... "help me to carry her to hospital this man, ka tashi ka wani zauna kana kallonta saboda kasan idan ta mutu baka da hasara zaka kuma samun madadinta ni kuwa fa wazan kama...? a rud'e fu'ad ya d'auki nasreen da bata numfashi ya sa'bata akafad'arsa yasoma tafiya daita cikin sauri sauri, me'ad ma ta mike azumbur ta biyosa abaya rike da gefen rigarta tana wani irin kuka me ta'ba zuciya. A haukace ya isa inda motarsa take parke ya bud'e gidan baya ya kwantar daita, me'ad tayi saurin shiga ta d'aga kanta ta zauna ta meida kanta saman cinyarta tana wani irin kuka jikinta banda kirma babu abinda yake ,shi kuma ya zagaya cikin sauri yashiga gaban motar ya zauna ya kunna motar yana mai danna hon da karfi ........ me gadin gidan da tun sanda rikicin yasoma faruwa akan idanunsa yashige d'akinsa ya boye ya leko ta window, ganin motar fu'ad ne yayi saurin fitowa ya bud'e masa get sannan fu'ad ya figi motar aguje ya bar gidan . wani irin gudu yake shararawa akan titi wanda yaja hankalin mutane dayawa kansa ,domin duk wanda yaga irin gudun dayake sai ya tsaya yabi bayan motar da kallo, cikin lokaci kankani ya isa asibiti tun bai gama daidaita tsayuwar motar ba me'ad ta fito jikinta na rawa tana ihun kiran nurse....nurse!! shima ya fito a kid'ime batare daya tsaya rufe motar ba, ya sake d'aukar nasreen dake kwance babu alamun numfashi atare daita. sautin muryar me'ad yasa wasu daga cikin likitoci fitowa da hanzari suna tura gadon marasa lfy domin sunsa duk me irin ihun nan hk a matukar bukace yake da taimako,batare da 'bata lokaci ba aka kwantar da nasreen. kai tsaye d'akin likita aka nufa daita aka akwantar daita akan gado sannan aka soma bata taimakon gaugawa ,likitoci kusan guda biyar ne suka rufa akanta domin k'ok'arin dawo da numfashinta ,wanda da kyar aka samu numfashinta ya dawo daidai sai dai bata farka ba. Yayinda fu'ad da me'ad gabadayansu sun fita haiyacinsu ,sai zariya suke suna kai kawo a reception, most especial me'ad da hawaye yaki tsayuwa acikin kwarnin idanunta, kuka take sosai kmr wace akace mata tarasa nasreen din, ahankali fu'ad ya waigowa gefen datake zariya tana kuka ya tsura mata ido yana duban yadda gbdy ta gama birkicewa ta hargitse ta dawo abar tausayi ,matsalarta kenan a duk sanda nasreen ke cikin wani hali gbdy zata rasa sukuni da kwanciyar hankali Amman ta zauna domin kula daita da lfyr ce bazata iya ba ... ahankali ya d'auke idanunsa akanta had'e da Jan tsaki... shi kansa cike yake da matsanancin fargabar abinda likita zai fito ya sanar musu,cikin hk suka hango fitowa wata nurse daga d'akin da'aka kwntar da nasreen ,gbdy sukayo kanta "how is she? suka furta atare cike da matsanancin tashin hankali? "she's feeling better now ta basu amsa atakaice cike da tausaya musu sannan tacigaba da mgn "doctor is already attending to her, Dan haka kusamu natsuwa ku kwantar da hankalinku InshaAllahu babu abinda zai faru da yarinyar ku....."you said doctor is with her inji cewar fu'ad?"haka ne likita nabata kulawa just keep praying for her, everything will be fine okay. sannan ta barsu tashiga wani d'akin opposite dinsu. suna nan tsaye ta sake dawo ta wucesu cikin sauri tashige d'akin . me'ad ta k'arasa jikin bango ta d'aura kanta tana wani irin kuka ..., sai alokacin abubuwa suke dawo mata daki daki , "sajida aminiyarta, aminiyar datafi yarda daita a duk cikin aminanta, wai itace yau aka wayi gari take son mijinta har take burin mallakar aurensa, wannan wace irin cin amana ce ...? "Sajida kin cuceni kin ci amanar yarda da amince dana miki ,kin cuceni kin yaudareni, kin ha'inceni.. Amman nasan Allah bazai barki haka ba ,da yarda Allah sai allah ya nuna miki illar cin amanar wanda ya aminta da dake , matukar yarda da na miki ta tsakani da Allah ce sai Allah ya nuna miki atafin hanuna, saboda daidai da rana daya ban ta'ba tunanin zaki yi min hk ba ,na yarda dake kin cutarda dani ...na aminta dake kin ha'inceni "me na miki kika za'bi ki min haka? "Duk duniya ki rasa wanda zaki so sai mijina..kuka take sosai tana maganar ashe har maganar ta fito fili batasani ba . Tausayinta ne yashiga ratsashi ,da bin lungu da sako na sansar jikinsa , jiki a sanyaye yak'araso zuwa inda take ya kai hannunsa ya dafa kafad'arta, da sauri tayi wata irin juyowa tana kallonsa cike da zallar tsana da 'bacin rai sannan ta cire hannunsa tayi jifa dashi "karka sake kai hannunka jikina mayaudari maci amanar kauna.......abinda ta iya fad'a kenan ta bar gurin zuwa harabar asibiti tana kuka kmr wata zautaciya..." yau tazo mata da abubuwa daban daban wanda kowane daga cikinsu akwai d'aci da muni gareta, mijinta ke son me aikinta da aminiyarta.... alhalin tana raye bata mutu ba wannan abu da matukar ciwo .."why fu'ad ?"ban cancanci hk daga gareka ba ,bansa zaka min haka ba ,Amman tunda wannan shine besty solution dakake ganin zaka d'auka akaina I will live you for them wallahi na hakura da kai nabar musu kai ta karasa mgnr tana kuka ahankali ta durkushe kasa tare da d'aura kanta saman gwiwowinta tacigaba da kuka ..... Can gidan kuwa najma taci kukanta kmr ranta zai fita da kyar tasamu ta yunkura ta mike tsaye tana d'ingisa kafarta da k'arfe ya saukar mata kai, tasoma tafiya jikinta na karkarwa ,kai tsaye hanyar cikin gidan ta nufa inda tashiga ta d'auki kayanta kwaya daya dake cikin bakar leda ajiye, har lokacin hawaye take sharewa ita bakincikinta bai wuce yadda zatayi da rayuwata ba ,domin a matukar tsorace take da halin data ga me'ad din take ciki , gara ta gudu tun bata dawo gidan ta kasheta ba , kmr yadda tayi niyya ba. ahankali ta fito harabar gidan inda idanunta ya sauka akan sajida dake kwance kmr gawa, nan da nan hankalinta ya sake tashi sai lokacin ta tuna yadda akayi take kwance cikin wannan halin, girgiza kanta tayi tana takaicin hali irin nata nacin amanar aminiyarta datayi, ta isa inda me gadi yake tsaye tare da direban nasreen yana labarta masa abinda ya faru akan idanunsa, ta nuna musu inda sajida ke kwance"ku taimaka mata Dan Allah karta mutu mushiga uku ,duk da ni dai tafiya zanyi yanzu . sai lokacin hankalinsu ya kai gareta ai kuwa da sauri me gadi yaje dibo ruwa shi kuma direba ya isa gareta yana dubanta atsoroce, daidai lokacin da me gadi ya kawo ruwa tuni najma ta fice daga gidan . Ruwa suka zuba mata sosai sannan ta sauke ajiyar zuciya da karfi dishi dishi take kallonsu kanta na jujjuyawa had'e da sarawa kusan minti goma da kwara mata ruwa ta dawo haiyacinta sosai tana sake dubansu dafe da gefen kanta "ranki ya dad'e wai me ya had'aki da hjy ne har hkn ta faru atsakaninku?"gsky zan so ki tashi ki fice daga gidan nan tun kafin ta dawo ta sameki tak'arasaki. maganganunsa tsab suke shiga cikin kunnenta , ahankali tasoma mikewa har ta mike tana bin bango tare da cewa direba "ahuwa taimaka ka kaini gida dan Allah, bazan iya tuki ba ... da sauri ya zaro duka idanunwansa waje "wa ni zan kaiki gida ranki ya dad'e? Ta d'aga masa batare datace masa komai ba "a'a wallahi bazan iya ba ,,Dan idan hjy ta dawo tasamu labarin ni na kaiki gida kashina ya bushe ,ki dai lalla'ba kija kanki shi zai fi miki alkairi . Sororo tayi agurin tana kallonsa da mamaki , me'ad kenan jarabar duniya kowa tsoronta yake ji tayi maganar acikin zuciyarta "ita me'ad tayi yunkurin kashewa Akan d'a nmj, nmj da zai iya rayuwa babu ita aduniya. Nmj da tabbas garesa balle alkwari yanzu inda takasheni fa me take tunani zai faru?"ita ba matsiyaciyar me aikinta bace daba gata da galihu bace balle tayi tunanin idan ta kasheta ta kashe banza. Tafiya take ahankali tana zance zuci har ta iso inda motarta take tashiga ta zauna tana jin yadda gefen kanta ke cigaba da sarawa, wayarta ta d'auka takira direban gidansu ,cikin minti goma sai gashi ya iso yana rusuna mata cike da girmamawa tace "ya kai ta asibintin da take zuwa ... ********** Sai gurin takwas din dare nasreen ta bud'e idanunta tana wani irin kukan bakinciki, nurse ta shigo d'akin cikin sauri ta ajiye karamin tiren hannunta wanda ke d'auke da kayan aiki akan table tare da janyo wani flat table gaban gadon nasreen wace tana ganin shigowar nurse ta d'auke kanta ta meida gefe tana cigaba da kukanta . nurse ta meida tiren kan flat table had'e da sanya safar hannu nasreen ta juyo gefenta hawaye na bin kuncinta "nurse ta kirata muryarta na rawa "I don't want to see you don't come near me plz ,I don't want to see .... nurse ta bud'e baki da hanci tana dubanta kafin daga bisani tace "ki bari nayi treatment dinki mana ,amatukar tsawace nasreen ta mike zaune "go I don't want to see you, sannan ta koma ta kwanta tana Janyo numfashi da kyar. "What's wrong with you nasreen? " bakiga halin da kike ciki ba, kina bukatar kulawarmu, Kibari na dubaki mana .... "please, go! Ihu kawai take tana furta go "I don't want to see likita ne ya fad'o cikin d'akin da sauri yana tambayr abinda ke faruwwa "doctor I wanted to treat her,but she asked me not to touch her, nor come close to her . doctor yayi shiru yana duban nurse din sannan ya meida idanunsa Kan nasreen dake kwance tana kuka har da shesheka ,"ammm ya fad'i hk tare da k'arasawa gadon da nasreen take ya tsura mata ido kawai yana kallonta gbdy ya kasa cewa komai. yarinyar na mugu mugun bashi tausayi lamarinta na ta'ba zuciyarsa ,waigowa yayi tare da cewa nurse "you can go. "Ok sir ta fad'a tana cire safar hannuta kana ta bar d'akin . Doctor ya matso tare da tura table din dake d'auke da magani gefe sannan yasamu guri ya zauna daga gefen kafafunta yana kare mata kallo ahankali ya kira sunanta "nasreen, you will be fine, okay? "Ammm permit me to take of yourself I will treat you by my self and you will be fine is that clear? Ahankali ta waigo hawaye nabin kuncinta tace " doctor all i want from you is to kill me ,"give me poison ,i just want to die ,I ,i heter my self banason cigaba da wannan rayuwa ,ina bukatar barin duniyar nan ....sororo doctor yayi tare da bud'e idanunsa yana cigaba da kallonta kirjinsa na wani irin bugawa saboda jin lafazinta "abun mamaki yarinya karamar irinta ke furta wannan kalmar .. tana son tasha poison ta mutu to akan me kenan ? "Ina son na mutu doctor bana bukatar cigaba da rayuwa a duniyar nan ta sake maimaitawa tana kuka.... Cike da matsanancin tashin hankali ya furta kalmar "death.? "Yes doctor I want to die....ta juyar da kanta... "What ? Ya sake furtawa yana dubanta a matukar tsorace , kasa tashi doctor yayi daga cikin inda yake zaune illa dubanta da yaciga da yi tare da rafka tagumi . Shiru shiru me'ad na jiran ganin fitowar likita Amman shiru hkn yasa ta nufi d'akin din da gudu tana kuka shima fu'ad cikin sauri yabiyo bayanta, gbdy kallo daya zaka mata kasan bata cikin natsuwarta, tunda suka zo asibitin batayi yunkurin komawa gidan ba , "to idan ma ta koma tayi me ? " ne zata koma tayi a wannan gidan ? Haka tayita zariya acikin asibitin har zuwa wannan lokacin, sannan bata kira kowa daga bangarenta ba ,Dan har gara fu'ad ta lura da yaje gidan ya dawo, Amman ita zuwansa ba damuwarta bace, damuwarta ahalin yanzu bata wuce ta lafiyar tilon diyarta ba . Zaune suka iske doctor ya tasa nasreen gaba yana dubanta, da sauri tayo gurin nasreen tana kiran sunan "doc...... AI kuwa nasreen ta zabura ta mike zaune tare da dakatar da uwar ta hanyar cewa "go back mummy I don't want to see you, plz go !!!! Shi kansa doctor sai dayayi shock a zaune agurin,wannan abinda me faruwa gaske ne ko mafarki ne ? A matukar firgice me'ad da fu'ad suka shiga kallon kallo atsakaninsu suna zare ido. da kyar fu'ad yayi karfin halin cewa "did you hear her? Yana kallon kwayar idanun me'ad. "Did you hear what she said? Runtse idanunta tayi hawayen bakinciki biyu biyu na gangaro mata, magana take son yi Amman ko tace zatayi maganar bazata fito ba saboda cikin halin tashin hankali datake ciki ,Dan haka ta bud'e idanunta dake cike da ruwan hawaye ta d'aurasu Akan yarinyarta tana mata kallon karta mata ..... Hawaye sha'be sha'be a kwance a kuncinta nasreen ta sake cewa "I don't want to see any of you here, Plz just go... doctor ya d'ago ya dubesu yana girgiza kai sannan yace "fatan kunji abinda yarinyarku tace ? "Yanxu dai kuje daga waje tukun am coming to see you guy's. "Doctor including me ..? Fu'ad ya fad'a cike da tsantsar mamaki da tashin hankali, yana duban nasreen dinsa. a matukar fusace doctor yace "you guy's leave plz.."both of you should leave! Me'ad ta nuna kofar fita idanunta na kan nasreen dake kuka ,da hannun doctor ya nuna musu hanya alamun hk yake nufi . jiki a sanyaye me'ad tasoma d'aga kafafunta still idanunta na Kan diyarta wanda zuwa lokacin tuni fu'ad ya bar d'akin dafe da goshinsa . bayan fitarsu doctor ya sauke naunayen ajiyar zuciya yana me d'aura hannunsa akan bakinsa "ammmmm nasreen ya furta ahankali,"just calm down okay. "I understand you Amman meyasa kikayiwa iyayenki hk alhalin suna matsanancin kaunar suga kin rayu? "No doctor don't say that basa sona wallahi ,sun fi son na mutuwa ......... "Kullun cikin fad'a suke a tun sanda kace cikinsu daya zai ajiye aikinsa ,nan tashiga koro masa komai tun daga farko har zuwa abinda idanunta ya gane mata momy'nta na yunkurin aikatawa "shiyasa ni dai ka taimakeni kabani poison na sha na mutu ....... "doctor ya girgiza kansa kawai sannan yace "ki daina furta wannan kalmar bata da kyau ga duk wani cikakken Muslim ,"ko bakinsa duk Wanda yayi yunkurin kashe kansa da kansa amatsayin kafuri zai tashi agurin Allah ba ? "Dan haka karki sake furta wannan kalmar bata da kyau okay,? Ta matso wasu hawayen batare da tace komai ba," ya Mike ya bar d'akin zuwa office dinsa, inda yasa ayi masa kiransu ,da gudu me'ad tashigo office din tana goge hawayen idanunta. Zaune suke agaban doctor gabadayansu a firgici suke, kowanensu da abinda zuciyarsa ke kismawa Akan wannan kiran da likita yayi musu, doctor ya zuba uban tagumin yana sake tunanin zantuttukan nasreen kalma daya ce tafi kowace kalma muni da daci garesa kmr "doctor give me poison I want to die ...... "Wannan Kalmar tayi matukar gigitashi da tsaya masa arai, tsawon minti goma suna zaune still doctor yaki ce musu k'ala Me'ad ta matsu ta matsu bataji abinda doctor yakirasu dominsa ba ,yayinda zuciyarta ta dinga tsinkewa da rawa rawa ,banda zare idanuwa babu abinda take ,ganin shirun yayi yawa yasa me'ad kasa hakuri tace "doctor, what's exactly happened to my child? "Ina jin tsoro doctor kar wani abu ya sameta ,I think ba ciwonta bane ..? Doctor yayi shr yacigaba da jimami yana ta'be baki . "doctor wai meke faruwa ne kabarmu zaune cikin tashin hankali Dan Allah ka sanar mana da abinda ke faruwa da yarinyarmu ? Inji cewar fu'ad. Ahankali doctor ya kallesu kana ya dukar kansa na minti biyu sannan ya sake d'agowa yace "do you guy's want to know what is going on? Da sauri suka had'a baki gurin cewa "yes muna bukatar sani . "Both of you are not good parent to child ." what ? me'ad ta furta tare da barin bakinta a bud'e . Fu'ad yace "har dani kake nufi ko da wannan datake zaune kake mgn ? Doctor yace "dukanku nake mgn , sannan duk inda aka kira iyayen arziki masu son yaransu da son farincikinsu ,idan irinku suka fito wallahi kamata yayi aka maku ayi muku dukan mutuwa ,ko kuma ad'aureku ajikin kujera har ku mutu .... "what suka furta atare? " yes I mean it inji cewar doctor yana masu kallon banza "saboda gabadayanku mugaye ne sannan baku da halin kirki you are not a good parent at all...for ten years old girl to be considering death as an option.. "what doctor ? Inji cewar me'ad gabanta na wani irin mahaukacin bugu "yes she ask me to give her poison because her parents do not like her yet you call yourself parents. "kai kai doctor it can be possible ya dafe goshinsa yana girgiza kai..numfashi me'ad tasoma ja kmr me cutar asm "um umm uhmm sai kuma kuka ya kwace mata, take kuma jikinta ya sake d'aukar rawa ta juya ahankali tana zabgawa fu'ad harara had'e da kallon banza . bai kulata ba illa muryarsa cike da in ina yace "doctor can I go see her and talk to her? "You can't see her right now.. "ah! Suka furta atare suna duban doctor. Doctor yace "am telling you you guy's can't see her. Me'ad ta watsawa fu'ad wata katuwar harara kmr idanunta zasuyo waje "ai kaga abinda kayi ko ,kaga abinda sanadin matsalarka zata haifar ko ? "Bari kaji in gaya maka wani sabon labari ,wallahi wallahi idan wani abu yasamu yarinyarta bazan yarda ba ,Idan kuma ta mutu heeeeeeeee....."kai dai kayi adduar kar wani abu yasamu yarinyarta kawai ,Dan idan wani abu ya ta'ba lfyrta sakamakon abinda ya faru kasawa ranka kaima mutuwa zakayi......dan wallahi tallahi kotu ce zata rabu da kai ,takarasa mgnr tana kuka "ni nasan wahalar Dana sha akanta tun daga d'aukar cikinta har zuwa yau din nan .."haihuwarta kawai kikayi Amman na fiki son nasreen da bukatar lta araye "uhmmmmm uhmmmmm!!! Tashiga sauke ajiyar zuciya tana kuka tana jijiga kafarta. "plz can I go and see her plz? "I need to talk to my daughter inji cewar fu'ad da gbdy ya susuce kuka kawai yake son yi ko shima zai ji sanyi aransa, "nasreen dinsa ke adduar mutuwa, tana bukatar mutuwa saboda matsalar shi da mahaifiyarta..wannan wace irin rayuwa ce? ,"ya Allah karka kashe min ita, ina sonta , ya dafe kanshi tare da dukar da kasa gbdy yasoma jin duniyar tana jujjuyawa dashi "wani irin zunubi ya aikatawa ubangijinsa haka,da abubuwa suke faruwa dashi hk? Zuciyarsa ce tayi saurin kwa'bersa" karkayi sabo fu'ad kai muslimi da kasan da kaddara me kyau ko akasin hk, ka d'auka duk abinda ke faruwa dakai kaddaraka ce tazo da hkn wanda bazaka ta'ba gogewa ba ,a sukwane ya d'ago idanunsa da suka yi jawur tmkr garwashin wuta yana duban me'ad .. "Ba yanzu bane lokacin kukanka fu'ad, kajira lokacin da yarinyata zata mutu, ranar zaka sha kallon abinda zai faru atsakaninmu," doctor idan duk damuwar nasreen ni ake cewa naji na yarda na Amince, but na yau babu hannu ciki shine musababbin faruwar komai, Amman wallahi nasreen Dina ta mutu sai duniya tasan damu, Dan ina tabbatar maka gidan tv daban daban za'a dinga watso labaranmu. "just imagine doctor ya fad'a yana mata kallon banza "that was exactly what I was still talking about, "is this the way you supposed to be doing now? Tayi saurin girgiza masa kai tana zaro idanuwa "see .. both of you can't see her " ah fu'ad ya furta yana me bud'e baki "yes wallahi bazan bari ku ganta ba ,hk kawai kuje da maseefarku ku k'arasa yarinya mara lfy ......"Dan girman Allah doctor kabarni ni kad'ai naje naganta nasan zata saurareni, after all ina bukatar ganin yanayin jikinta,ina bukatar jin dumin jikin yarinta.."duka acikin babu wanda zakayi ,ku tashi ku tafi plz ina da abubuwan yi ... Tsam me'ad ta tashi tasoma d'aga kafafunta tmkr wace bata da laka ajikinta,while hawaye na tsiyaya a saman kuncinta har ta iso harabar asibitin, daya wadatu da hasken wutar lantarki tasamu guri daga gefe ta zauna a kasa still tana cigaba da zubar da hawaye , ahankali ta sanya hannuwanta duka ta rungume jikinta tare d'aga idanunta sama tana kallon sararin samaniya, tana tunanin rayuwa kuka take sosai kmr ranta zai fita ,"wayyohlly Allah nah... ..ina zan saka raina naji dadi? "Ya Allah ka d'auki rayuwata na huta da ganin tarin bakinciki dake kokarin kusanto rayuwata, "Allah na rokeka ka kasheni kafin naga abinda fu'ad yake shirin aikata min .... tana cikin wannan halin fu'ad ya fito yana dube duben nemanta can ya hangota zaune takure da jikinta tana kuka . ya runtse idanunsa sannan ya k'araso inda take ya tsaya akanta "mead ya kira sunanta da sanyayyiyar murya "me yasa kika barni kika dawo nan kina kuka? Wannan karon Yayi mgnr muryarsa cike da tausayawa sannan ahankali. Ya matso sosai kusa daita tare da durkusawa agabanta "why did you left me there and weeping outside ? Bata kula shi ba tacigaba da kukanta tana goge hawaye, wasu na sake gangarowa ya sake matsota sosai kmr zai shige jikinta, "don't do this to me plz ,the doctor has promised us that she will be fine let's keep praying for her, after all ,we are not god dole mujira hukuncin Allah garemu ... ya kamo laulausar tafin hannuta cikin nasa "dan Allah ki natsu ki kwantar da hankalinki babu abinda zai sameta "am..am scared I don't want lose her takarasa mgnr tana mai sakin wani irin kuka .. ta kwanto jikinsa tana kuka yanyota yayi jikinsa ya rungumeta tsam ya manna fuskarta daidai saitin zuciyarsa dake bugawa, yasoma rarrashinta "you are not going to lose her ,okay? " InshaAllahu zamu rayu tare da diyarmu, ki daina kawo mata mutuwa, Dan zamu iya mutuwa mu barta babu ruwan Allah. Cikin halin datake ciki , ta tuno da abinda yake son shuka mata, ai batare da 'bata lokaci ba ta fixge jikinta daga nashi ta Mike tsaye tana kallonsa kafin daga bisani tasoma tafiya cikin sauri tana kuka ,shima ya biyo bayanta yana kiran sunanta "mead ina zaki, ki dawo idan gida zaki na kaiki. tayi masa banza tacigaba da tafiyarta har takarasa bakin titi tana kokarin tsaida abun hawa "karki soma me'ad..karki soma shiga kowace mota. "Zan shiga so that idan na shiga ka sakeni ,wanda daman abinda nafi bukata kenan daga gareka tana fad'ar hk ta juya a fusace daidai lokacin da wani me adaidaita ya tsaya agabanta yana tmbyr inda zata. Tun kafin ta bud'e bakinta fu'ad yayi saurin cewa "ka wuce kawai tare muke daita, idan km kayi k'ok'arin d'aukarta sai dai wani ba kai ba ,yakarasa mgnr ya kamo hannuta da niyyar komawa cikin hospital, tasoma turturjewa" kabarni fu'ad banason abinda kake min, "me yasa kake son kasheni tun kwanakina basu cika ba ..? "Kece kike son kashe kanki da kanki ,amman karki damu bazaki mutu yanzu ba ,har sai kinga aurena da matana guda biyu. "Ina ai bazan so ki mutu tun yanzu ba matata, kece fa kikace am your husband for life, har tsufa muna tare ko kin manta da kin furta hkn ? "Ki tuna idan kuma kin manta gashin na tuna miki,aurena da 'yammatana babu fashi ,zance saki sakanina dake babu shi ,Dan HK muje kisamu natsuwar zuciya. Ta tattara iya karfinta ta fixge daga rikon da yayi mata ta juya cikin sauri tayi tafiyarta ,sai dai taku daya zuwa biyu yayi ya damketa tare da yin sama daita jama'a kan titi da idanunsu ke kansu suka bisu da kallo, har sanda ya sanyata cikin mota shima yashiga ya kule yana me fuskantarta.muryarsa a matukar sanyaye yace "Keleni me'ad, sannan ki natsu kibani aron hankalinki muyi mgn ta fahimta ."matukar Akan zance aurenka ne bazan ta'ba fahimtarka ba ,ince ba'ayin aure dole?"Dan Allah dan Annabi ka rabu dani da nace ina sonka zan rayu da kai yanzu kuma banayi kaje byn sajida da najma ka k'ara wasu ,ni dai me'ad ban sake komawa aurnka Allah ya had'a kowa da rabon...bata k'arasa ba taji ya buge mata baki "idan kika sake furta wannan kalmar zan zaki had'u da fushina da baki ta'ba ganin ba ,yanzu dai mu ajiye komai har sanda nasreen zata samu lfy aure kuma babu fashi zanyi ,let me tell you good news, ki godewa Allah watakila najma kawai zan aura saboda mahaifin sajida yaki amincewa da batun auren ..tunda yasoma mgnr take kuka har yayi shiru,tana zaune ta dawo tmkr mutun mutumi ,jinta na neman d'aukewa ,Allah sarki a she hk rayuwa zata zo mata? Ganin hankalinta na neman gushewa yasa ya matsota ya kamo hannuwanta duka cikin nasa yasoma massaging dinsu yana kallon cikin kwayar idanunta dake tsiyayar hawaye, Yasan tana mugu mugun son shi ,sannan yana da tabbacin duk duniya babu macen dazata so shi fiyye daita ..ahankali ya janyota jikinsa yana k'ok'arin rungumeta ,ta kasa saida shi saboda zuwa lokacin gbdy jikinta bai da laka kallonsa kawai kmr wata ta'ba'bbiya ,tsawon lokaci suna manne da juna batare da suncewa juna k'ala ba ,kusan a mota suka kwana makale da juna, sai dai mead bata runtsa ba kwance kawai take ajikinsa numfashi kawai take iya fitarwa shima Dan tasan dole ya fito tunda akwai rai ajikinta. ****** Washegari babu laifi nasreen tasamu natsuwar zuciya, daman firgici da tsoro ne ya haifar mata da suman datayi , sai dai fad'uwar datayi kasa yasa hannunta na hagu ya D'an bugu, har gurin ya kunbura abinka da sickle cell k'ashinsu bashi da kwari, koman yaya suka ji ciwo yanzu gurin zai kunbura. suna zaune tare daita kowanensu na rike da hannunta daya ,suna k'ok'arin bata kulawa doctor yashigo dubata yanayin jikinta, sosai ya ji dadin yadda ya isketa atsakiyarsu me'ad na bata apple abaki sannan tayi mata hira, irin sanya farinciki. Tashi sukayi atare suka tsaya ajikin bango, batare da sun kalli junansu ba,doctor yashiga aikin duba jikin nasreen yana mata wasa. Kwana nasreen biyu a hospital doctor yabasu sallama, lokacin fu'ad bai nan yana can tare da me gidansa, kai tsaye me'ad hanyar gidansu ta dauka da nasreen, Dan bata jin zata koma gidansu da sunan cigaba da rayuwa fu'ad, zuciyarta cike da bakinciki, wai shin me zatawa sajida da najma arayuwa ta huce? Kodayake bata jin najma, tafi jin sajida Dan a yanzu ta sauya shawarar akanta ,Dan har in takashe sajida, bata more rayuwa ba ,tunda bata zauna a duniyar ba balle taga bakinciki, yanzu tafi yarda da shawarar zuciyarta wanda babu tantama abinda zata mata har ta mutu sajida bazata ta'ba mantawa daita ba,gaba idan ance ta kalli mijin wata tace tana so ,ko taci amanar wanda ya Aminta daita bazatayi ba ,murmushin mugunta tayi adaidai lokacin da ta iso bakin get din gidansu inda tashiga matsa hon, madu gadi na ganin motarta ce suka hau k'ok'arin bud'ewa cikin rawar jiki, tasanya hancin motarta tana hura hanci, tayi parking a inda aka tanada domin ajiye motoci sannan ta fito har lokacin fuskarta a murtuke take, ta dubi nasreen dake zaune tana kallonta, dan ita a tunanita gidansu suka nufa sai kuma taga momy'nta tayo gidan kakaninta dasu, me'ad ta Dan saki fuskarta kana tace "bby fito muje ... *"Uhmmm to ga dai me'ad an kwaso jiki an dawo gida uba...ko yaya zatak'aya da mahaifinta ?" ko kuwa ta manta furucinsa akanta ne?* Mmn sudais ce 💗💗💗💗💗💗 'YAN CINKI 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 ~NA~ *AYSHA A BAGUDO* ~DEDICATED TO~ FAIZA HAMMADU BARAU (YAR NUMAN) Page 77 ......nasreen taji abinda momy'ta ta fad'a sarai amman taki motsawa daga inda take zaune, illa idanun data tsurawa momy'nta tana kallonta cike da tambayoyi. ahankali Me'ad ta zagayo inda take zaune tana kallonta "bby let's go now tana me kamo tafin hannunta ta fito daita daga cikin motar, sa'an nan ta meida murfin motar ta rufe, tasoma tafiya rike da hannun ta. yayinda ma'aikatan gidan suka shiga gaisheta cike da girmamawa, hannunta kawai ta iya d'aga musu tacigaba da tafiyarta batare da juyowa ba, Momy tana zaune a parlour'n tana waya Me'ad tasanyo kai cikin parlour'n a matukar birkice bakinta d'auke da sallama, momy na ganinta tayi saurin katse kiran saboda yanayin data ganta ,wujiga wujiga tamkar wace tayi shekara tana jinya. "me'ad lafiya kuwa naganki haka kmr wacce ta tashi a jinya? "ko kuma kunyi Abind kuka saba ne da mijinki kika kwaso jiki zuwa gida? momy tajirowa me'ad wannan tambyar Tana dubanta a matukar tsorace me'ad tasamu guri ta zauna a gefen kujerar da momy ke zaune batare da tace mata komai ba, illa wani tashin hankali data tsinci kanta ciki. NASREEN ta isa gurin momy tashige jikinta tana gaisheta ,momy ta rungumeta ajikinta tsam kana tace "ykk nasreen? "yana ji jikin naki da zafi ko bakida lfy ne? Naunayen ajiyar zuciya me'ad ta sauke kana tace "fitowarmu kenan daga hospital yau kwananmu uku NASREEN babu lafiya Tak'arasa mgnr muryarta na rawa kmr zatayi kuka. momy tayi Shiru tana kare mata kallo had'e da nazarin yarinyarta, a kallon da take mata ta fuskaci tana cikin matsananci damuwa da tashin hankali, yayinda ita kuma me'ad din tashiga share hawaye wasu na gangaro mata... "To meye kuma abun kuka ? " ko ciwon ne yayi tsanani? Me'ad ta girgiza mata kanta wasu sabbin hawaye na sake gangarowa bisa kuncinta. " meke damunki me'ad dan banji dadin ganin yanayinki ba ? " sannan meye damuwarki ahalin yanzu da kike zubda hawaye ko duk akan matsalar ciwon NASREEN ne? ta sake girgiza kai kawai tana share hawaye, momy ta fuskanceta sosai hankalinta a matukar tashe "ke me'ad ki bud'e idanunki ,ki saka cikin nawa ni mahaifiyarki ce da duk duniya baki da kmr ni kuma nice nazama dole nasan damuwarki da abinda ya kawoki gida adaidai wannan lokacin daya kamata ace kina gurin aiki ne ko gidan aurenki "ki sanar dani damuwarki da abinda ke damunki domin Nasan mataki d'auka.. me'ad ta kalli momy fuskarta cike da tsantsar damuwa da tashin hankali still hawaye na tsiyaya daga cikin idanunta tace "momy ina cikin babbar matsala ,ina cikin damuwa da tashin hankali, momy na cuci kaina da kaina na yaudari kaina,na zalinci kaina, na jawo kaina maseefar datafi karfina.... Momy nayi aure batare da farincikinku ba ,most especial dady, banyi muku biyayya akan aurena da fu'ad ba , gashi ayau an wayo gari komai na neman ta'bar'bare min, narasa gane komai nawa ,rayuwa na neman juya min baya , "ahalin yanzu na dawo gida ne saboda bana jin zan iya cigaba da rayuwar aure da fu'ad ....... jin wannan maganar yasa jikin momy yayi sanyi ta gyara zamanta tana duban me'ad cike da matsanancin tashin hankali, sannan tace "amman meye dalilinki na fad'ar duk wad'an nan maganganun hk ? "abinda akayi shi tsawon shekarun goma sha meye na dawo shi ahalin yanzu? "sannan meye dalilinki na cewar bazaki sake rayuwar aure da fu'ad ba wani mummunar abun yayi miki ? Momy ta tambayeta jikinta na wani irin rawa haka zalika gabanta na fad'uwa .. me'ad ta kalli momy ganin damuwa kwance akan fuskarta ,yasa wani irin tausayin mahaifiyarta ya saukar mata, ta sauke naunauyen ajiyar zuciya sannan ta kwashe duk abinda ya faru ta gayawa momy. momy tayi wata irin zabura daga zaunen datake rungume da nasreen ta mike tsaye kana ta zaunar da nasreen jikinta na d'aukar kyarma , dan maganar ta bugi zuciyarta matukar , ahankali tasoma kai kawo acikin parlour'n, lokaci guda kuma ta koma ta zauna ta kalli me'ad tace" yanzu ina najma take sannan a wani hali Sajid take ciki? "momy nagaya miki na barsu agidan ,dan tunda abun nan ya faru ban sake taka kafata cikin gidan ba ,kinga sai suji dadin yin aurensu da tushe . "shikena me'ad to yanzu meye abun yi? me'ad tayi murmushi me tattare da takaici abinda sajida tayi mata ,sannan tace "momy kada ki damu ni nasan yadda zanyi da Sajida ,wallahi Momy sai tayi datasani tunanin auren fu'ad arayu.... "datasani uwar me zatayi tunda ke bakiyi dakinsani ba a aurensa da kikayi ? Wannan Sautin muryar ta katse mata hanzari ,ko ba'a gaya mata ba tasan sautin muryar mahaifinta ne yashigo parlour'n ,atare suka jiyo daga ita har momy suna mamaki jin Furucinsa. Ahankali ya tako har zuwa inda suke yana tafi da hannunwansa Duka cike da tsansar jin dadin ganinta cikin damuwa da tashin hankali"ku daina mamakin jin abinda na fad'a "arayuwa kowa abinda yake so yake da burin mallaka, "kmr yadda kikayi tsayin daka kikace duk duniya babu wanda yayi miki sai d'an talaka dagin matsiyata, itama hkn ce zata kasance daita Dan hk banga abun tada jijiyoyin wuya ba ..... "Me'ad.... !!! dady Ya kira sunanta har sau uku in a serious thought wanda yasa kirjinta bugawa da sauri batare da tasan da hakan ba, "na'am dady ta amsa masa wasu hawayen na ciccikowa a idanunta sannan tasanya kwayar idanunta cikin nasa zuciyarta na sake lugud'en bugu da karfi saboda fargaban jin abinda zai sake fad'a. " yanzu dai me kika zo yi gidana ? "hope ba kashe aurenki kikayi ba akan mijinki zai aure aminyarki da yar aikinki? "idan kashe aurenki kikayi ko yaji maza maza ki tashi ki bar min gidana, dan babu masaukinki acikinsa. " idan kina tunanin zaki kashe aurenki ne ki dawo gidana ki zauna kiyi saurin canza tunani ,dan idan kin kashe aurenki har abada bazaki zauna tare dani ba. "idan kin manta sharrud'ana akanki bari in tuna miki . " yaji ,mutuwar aure alkahari kowani iri ne damuwar rayuwa ,yasameki bazaki tunkaro hanyar gidana ba," kikace kinji kin gani kin yarda kin amince , kika zabi auren d'an matsayata akan mu iyayenki da mukayi silar zuwanki duniya. "daman kuma wannan ranar nake zaman jira zuwanta wanda nasan komai daren dadewa zata zo gashi tazo kuma na godewa Allah datazo ina raye cikin koshin .. " dan haka tun wuri ina shawartarki ki tashi ki koma gidanki, idan ba sakinki yayi ba, idan kuma ya sakeki ne sai kin nemi gurin zama amman ba'a gidana ba. "haba dady wace irin mgn ce haka ? "da me kake son taji? "Ina ruwana da abinda zataji, nace ina ruwana lokacin danake rokonta ta auri safwan me tayi min?"in ce komai ya faru ne akan idanunki ? "kamata yayi ka duba lamarin da rabon dake tsakaninsu , idan basu auri junansu ba ,ta yaya kake tunanin za'a samun rabon NASREEN ? "NASREEN din banza ina ruwana da wata nasreen? "kuma wallahi bari kiji ingaya miki ni nan me d'aurawa mijinki aure ne da sajida matsawa tana son shi da gaske shima kuma yana sonta , ke koni sajida tace tana so zan aurenta balle wani mijinki din banza da wofi ,oya zo ki bar min gidana kije ki rungumi matsalarki ,ki bar rayuwarmu, dan tuni na manta da na haifeki arayuwata ,a halin yanzu diya daya gareni itace suhailat yar albarka yarinyar kirki kuma InshaAllahu zatayi albarka saboda tana min abinda nake ..... cikin kidima da tashin hankali me'ad ta durkushewa agaban mahaifinta tana wani irin kuka "dan girman allah dady kayi hakuri ka yafemin , na yarda nayi kuskure arayuwata,Amman na tuba dady karka min haka ,karka juya min baya, banida wad'anda suka fiku ,ka yafemin nasan hakinka ne ke bibiyata ya fixge karfarsa daga rikon datayi masa. "baki ga komai ba tukun me'ad sai ranar da kikaji na d'aura auren sajida da mijinki ,kijira abinda zai biyo baya sai fu'ad ya zame miki annoba arayuwarki sai ya tarwatsa rayuwarki da farincikinki ,ke hatta wannan aikin da ni nasan wahalar dana sha kafin ki sameshi da har kike tinkaho da dashi, wallahil azim matsawr ina da haki akanki shima sai yabar hannunki kmr yadda Fu'ad ke shirin barin hannunki ...... "ki tashi ki bar min gidana ya k'arasa mgnr cike da hargagin 'bacin rai ... Kuka me'ad take sosai tana Jan gwiwowinta tana bashi hakuri ,momy ma ta durkusa agabansa tashiga bashi hkr. "kayi hakuri Dan girman Allah kabarta ta zauna tare damu ,yanzu ina kake tunani zata ga yarinyar mara lfy atare daita ? "khadaji ....dady yakira sunanta a zafafe "na'am dady. Ta amsa masa jikinta na rawa. "a iya tsawon arayuwamu, mun ta'ba samun wata matsala dake ? momy tayi saurin girgiza kanta tana jujuya hannuwanta alamun dai yayi hakuri . "to karki bari musamu matsala akan wannan yar isakar yarinyar mara jin magana . "gidan nan ma tukun naki ne ko nawa ? Momy tayi saurin girgiza masa kai tare da cewar "naka ne. "to nagodewa Allah daya kasance nawa ne ba naki ba, kuma lokacin dana tashi gidansa baki sanya sisin kwabonki ciki ba ,Dan haka bana bukatar ganin me'ad cikinsa taje can gurin wad'anda take tunani sun fini daraja agurinta, sannan ya fuskanci me'ad sosai yana huci "minti biyu kacal nabaki ,ki d'auki yarinyarki kibar min gidana bana bukatarku cikinsa, hakuri tashiga bashi amman sam yace bai san da zance wani hakuri ba sai ta bar masa gidansa . Ta mike ta tashi tsaye jikinta na rawa ta janyo hannun NASREEN ta rike cikin nata gam kmr wace za'a kwacewa ita, tasoma tafiya tana kuka ,momy na kuka , hatta NASREEN kuka take sosai tana tausayawa momy'nta "yanzu saboda ta auri dady'nta yasa babanta yayi mata wannan wulakanci, daman grandpa dinta bayason auren iyayenta ? Hakuri take son bashi Amman tashin hankali datake hangowa tattare da momy'nta da ita kanta yasanya ta kasa magana sai kukan datake har da shesheka. Jikin momy na 'bari tabiyo bayan me'ad tana kuka tana kiran sunanta....shi kuwa dady ko ajikinsa, Sam bai ji wani abuba dangane da halin da ta tsinci kanta ba. me'ad ta tsaya tare da cewa " momy ki daina kuka ki koma kawai duk abinda ya faru dani ,ni na jawowa kaina na zabi d'a namiji akan mahaifina ,na fifita soyayyar fu'ad akan ta mahaifina, yau wa gari ya waya? ""yanzu ina zaki? "duk inda Allah yayi momy zan tafi na bar rayuwar kowa, zanje nayi sabuwar rayuwa tare da diyata, zan rungumi kaddarata.... "amman ki rokon min dady yayi hakuri ya yafe min abinda nayi masa wallahi nayi danasani arayuwata, ki min addua momy ko zan daina jin rad'ad'in da zuciyata ke min ... ta juya tacigaba da tafiya har ta isa jikin motarta tashiga ta tayar , ta fito daga cikin gidansu tana wani irin kuka. Gudu kawai take shararawa akan titi, duk hanyar data gani ,bi take saboda bata San inda zata ba ,banda bugawa bubu abinda zuciyarta keyi, kuka take sosai tana dukan sitiyari motar "me yasa nayiwa mahaifina abinda nayi masa akan soyayyar fu'ad ta furta a fili? " me yasa ban bi zabinsa ba nace lallai sai fu'ad zan aura gashi komai na neman birkice min ? Ta sake fashewa da wani sabon kukan ,hakika na cuci kaina, iyaye duk lallacewarsu sun wuce wulakanci ,ballanatana irin nawa iyayen da samun irinsu ke da wuya, dady uba ne har da rabi ,wanda ke maye gurbin uwa idan tana raye ko amace . "sun haifi ne sun min gata ,mahaifina ya inganta rayuwata sosai yabani abinda duk wani d'an Adam zaiyi tinkaho dashi arayuwar duniya ,bai rageni da komai ba a tun tasowata ,komai nace shi za'ayi . ",me yasa nayi masa abinda nayi masa? " me yasa banyi masa biyayya ba alokacin dayace na auri safwan? " why why why !!! Me'ad meyasa nayi abinda nayi ? "Wayyohlly Allah na cutar da kaina, Kuka take sosai Sam ta manta da nasreen dake zaune agefenta sai da taji yarinyar ta riko hannunta a matukar afirgice tare da sakin razananniyar k'ara sannan taja birki da karfi ta tsaya cak tana Jan ajiye zuciya, hawaye sha'be sha'be kwance Akan fuskarta, itama nasreen din kukan take sosai har lokacin da shesheka ,tana jin tausayin dady'ntan sosai fiyye da mahaifiyarta , Amman ayau tausayin momy'nta ne ya rinjayi nashi har batasan a mizanin dazata ajiye hkn ba, rungumeta me'ad tayi ajikinta tana kuka "am sorry bby gudun danake ya tsorotaki ko.. ? Nasreen ta d'aga mata kanta al'amun Eh tana kuka. "am sorry na daina bazan sake ba kinji bbynah, ta d'aura idanunta akan agogon fatan dake d'aure da tsinyayar hannunta , lokacin shan maganin nasreen din yayi ,Dan HK ta kai hannuta sit din baya ta d'auko ledar maganinta da ruwa ta balla ta bata ta sha sannan ta mai daita ta kwanta akan kujera, itama ta meida bayanta akan kujerar datake zaune akai, byn tayi baya kad'an daita, ta runtse idanunta still hawayen idanunta suki tsayuwa har lokacin nadama ce fal cike da zuciyarta. Kusan minti talatin tana gurin tana zance zuci wayarta ta d'auki k'ara sauti me dadi da ta'ba zuciyar Wanda ya saurara,ko bata duba wayar ba, tasan ko waye me kiranta, sakamakon sautin dataji "fu'ad dinta ne ,dan shi kad'ai tasanya wannan sautin saboda matsayinsa gareta ," mutumin data sadaukar da rayuwarta da komai nata akansa, mutumin da shine silar 'batawarta da mahaifinta,a yau tayi datasanin a had'uwarta dashi a wancen lokacin" duk duniya tasani kowa yasani babu halittar da mahaifinta ke so sama daita Amman an wayi gari sanadin had'uwarta da fu'ad komai ya canza, soyayyarta ta juye zuwa kiyayyar da batasan ranar gushewarta ba.. Wani kukan ne ya kufce mata tasanya duk hannuwanta ta toshe bakinta ,"tarasa fu'ad rashi na har abada, sannan tarasa soyayyar mahaifinta, ga aikinta datake ganin shine gatanta da rufin asirinta shima tana nema rasashi adalilin takasa samun natsuwar zuciyar gabatarwa. akalla bazata tuna karshen shigarta office dinta da sunan yin aiki ba, gashi tun rashin lfyr nasreen bata taka kafafunta zuwa cikin ma'aikatar ba, ko kiran chairman bata samu damar yi ba ,batasan me zai biyo bayan faruwar hkn ba ,tun yanzu tacire rai da tsammanin da aikinta bisa kaidodinsu ,na ko fashin rana daya mutun yayi zai fuskanci babbar matsala da chairman. "zuwa yanzu tasan komai ya rigada ya tsaya mata ,shikenan rayuwarta zata zamo abar tausayi mara amfanin .. Fu'ad yakira wayarta sau babu adadi ,Amman batayi yunkurin d'auka ba sai hawayen datake zubarwa . jiki a sanyaye nasreen takamo hannunta"momy !!! dady na kira ,should I pick the call? "No......tace mata atakaice tana me runtse idanunta"why momy ki d'auka mana.......," koni na d'auka plz...? "Pick....ta fad'a saboda batason k'arin damuwa akan wacce take ciki . Nasreen ta d'auki wayar tare da cewa "hello dady nah. " hello my bby How are u doing ? "Am fine dady . "Ina momy'nki take ? "gata a kusa dani tana kuka,Jimmmmm yayi da ransa sannan yace "okay bata wayar..... nasreen ta miko mata wayar "momy dady yace nabaki.. Me'ad taki kallon inda take ballanatana ta amsa wayar hannunta ,"momy plz now ki amsa wayar dady'na. Sam me'ad taki, " ta amsa tace masa me byn cutar da yayi mata ? "Me zatacewa mayaudarin irinsa? "Mayaudari maci amanar kauna ......"Har abada wata kalma bazata sake shiga tsananinsu ba, kowa yaje yayi rayuwarsa .... yana jin yadda nasreen ke mata nacin ta amsa wayar Amman taki , tswon minti biyar wayar na tafiya sannan nasreen ta meida wayar zuwa kunnenta tana sauke numfashi "dady........ "taki amsa ko ya fad'i hkn Dan yasan abinda zata ce masa kenan ? "Don't worry bby, yanzu kuna ina, na dawo hospital doctor yace yayi discharging naki ,na dawo gida bangan bbynah ba,gashi nayi missing dinki ,I want to see ur beautiful face, tayi murmushin jin dadi sannan tace "ai daga hospital gidan grandpa muka wuce nan tashiga koro masa duk abinda ya faru akan idanunta ,fu'ad ya samu guri ya zauna yana mai runtse idanunsa yana jin wani irin zallar 'bacin rai da tunda yazo duniya bai ta'ba jin irinsa ba, wani irin tafarfasa zuciyarsa ke masa "why me'ad ? Ya furta a raunane. "Me yasa zata masa hk.? Ahankali ya hau sauke numfashi cike da takaicin dabbancin abinda me'ad tayi masa, ya d'auka iya shekarun da sukayi tare shi daita sun zama abu daya, sannan sun wuce wannan nevel din ,tazama shi shima yazama ita, sun chakud'e guri daya ta yadda duk runtsi duk wuya babu wanda zai ji kansu balle mahaifinta, daya fito ya nunawa duniya bayason zamansu tare, Sautin muryar nasreen dayaji cikin dodon kunnenshi ne yasa yayi saurin bud'e idanunsa "dady da gaske ne zaka auri aunty sajida da najma me aiki Dan kayiwa momy'na kishiya dasu? Yayi shiru kawai ya kasa bata amsar tambayarta, sai ma d'aura hannunsa da yayi ya dafe goshinsa dashi yana shashshafawa ahankali ahankali ,while kirjinsa na bugawa da sauri sauri. "daddy matukar da gaske zaka auresu ne ,plz change your mind, dan banason kayiwa mamana kishiya saboda banaso ganita cikin damuwa, saboda nima zan shiga cikin damuwa yanzu haka kirjina ciwo yake min dady tak'arasa mgnr kmr zatayi masa kuka ..... Muryarsa a matukar kasalance yace "bby kina bukatar kulawa wanda momynki ta kasa tsayawa ta baki, ni kuma amatsayin na mahaifi ba hurimina bane ,wannan hanyar kad'ai ce zatayi min maganin matsalata saboda nasan idan na auresu zasu kula dake shine dalilin.... " Amman ki za'bawa dady'ki mutun daya acikin auntynki sajida ko najma wanda kike son na aura ta zauna tare dake amatsayin second momy dinki, wace zata cigaba da kulawa dake da dady'nki.. "ni banason dukkansu ,ni banason kowa ni nafi son mummy'na kawai .......... ya sake runtse idanunsa gam" yanzu kuna ina? " zanzo na sameku na dawo daku gida, ta d'aga kanta tana duban yanayin gurin ta cikin mota, idanunta ya sauka akan wani green sambod da aka rubuta *main land bridge* Dan hk ta sanar masa a matukar firgice ya bud'e idanunsa ,gabadaya ya gigice ya kid'eme muryarsa na rawa yace "main land bridge? "Yes dady shine abinda nagani ,yace "ki sa wayar a handafree. Aiko take nasreen tayi abinda dadynta ya umarceta cikin d'aga murya yace"me'ad kina hauka ne, dazaki kai min yarinya har main land bridge? "Wai meyasa kike son meida kanki wawiya ne akan yar kankanuwar matsala? Tayi masa banza taki cewa dashi komai ,shi km ya dinga zuba mata bakaken maganganun ta inda yake fita bata nan yake fita ba still tana jinsa taki cewa komai, Dan idan tace zatayi mgn zagi ne zai fito daga cikin bakinta da hk tacigaba da sauraransa kawai take tana jin zallar 'bacin rai na ratsata, hawaye na bin kuncinta ji take a duniya yagama tozartata, ya gama wulakanta da abinda yake son mata,ganin taki kulasa yasa ya sausauta muryarsa, "Kiyi kokarin dawo min da yarinyata so that ke ki cigaba da zama agurin tunda abinda kika za'barwa kanki kenan . yana gama fad'ar hk ya katse kiran,Wanda alokacin ita kuma tayiwa motarta key dan tasan Sarai zai iya zuwa ya samesu agurin tunda yaji inda suke. me gadin gidansu takira taji ko fu'ad din na gida , ya tabbatar mata da yanzu ya fita, hasashenta ya tabbata kenan, zuwa zai yi ya amshi nasreen din ya barta da tarin bakinciki da damuwa, kai tsaye gidansu ta nufa, bata tsaya bata lokaci ba tashiga ta dibi abubuwanta datasan masu amfani ne gareta, dana yarinyarta ta kulle kofarta ta fito tashiga mota tabar gidan. Yayinda fu'ad Yayi maya tafi sau hud'u akan main land bridge, ya hau ya sauko Amman bai ga alamun tsayuwar motarta ba ko alamun wata motar daban ba ,gashi yana kiran wayarta taki d'auka haka ya hakura ya koma gida yana jin zallar bacin rai yana shiga gidan jikinsa yabashi tazo gidan . Da sauri ya fito ya isa gurin me gadi yana kwalla masa kira ,me gadi ya k'araso ya tsaya agabansa "maman nasreen tazo ne byn fitata? "Eh yalla'bai tazo bata ma dade sa fita ba wani irin takaici yaji kmr ya d'aukeshi da mari, a fusace ya juya ya komai cikin gida yana huci gabadaya ya rasa meke masa dadi ,hankalinsa ya sake tashi so yake yasoma neman inda najma take Amman bashi da natsuwar zuciya a kalla ya kusan minti goma tsaye yana tunanin mafuta ya duba agogo karfe karfe biyar ta kusan ciki" ina bai ga ta zama dole duk yadda zaayi sai yaga me'ad da nasreen tare da dawo dasu gida sake bazama yayi ya fito harbar gidan kallo daya zaka masa kasan baya cikin natsuwarsa yashiga motarsa aguje ya bar gidan. ********* A bangaren mahaifiyar me'ad kuwa kuka take a tun fitar me'ad gidan ,taso kiran fu'ad Amman ta kasa saboda a yadda zuciyarta ke cike da 'bacin rai zata iya gaggaya masa komai yazo bakinta ,abinda bazata so faruwarsa ba kenan atsakaninta da surinkinta ,me mutuntata da ganin kimarta, ita batace kar ya kare aure ba ,"amman meyasa sai sajida da najma? Tasan zai auresu ne Dan kawai ya kuntatawa zuciyar mead dinta... gidan yayi shiru kmr anyi mutuwa Dan koda suhailat ta dawo daga makaranta taji labarin abinda ya faru mutuwar tsaye tayi agurin, itama hankalinta yayi mugu mugun tashi.. ta dinga mamakin cin amana irin na sajida a ganinta har gara auren najma akanta..... Bangaren me'ad kuwa yawo ta dingayi acikin gari, daga wannan titi zuwa wancan titi,tarasa inda zata taji sanyi aranta ,tayi tunanin zuwa dangin momy'nta Amman sai taga kmr zata tonawa kanta asiri ne, a yanzu ta d'auki darasi me girma a zamanta da sajida, bazata sake yarda da kowa ba arayuwarta ,zata koyi rike sirrikanta ,zata bawar cikinta damuwarta bazata sake sharing secret dinta da kowa ba bayan mahaifiyarta, itama Dan tasan bazata gayawa duniya bane ko ha'intarta sai dai ta d'aurata bisa turba .daga karshe zuciyarta ta bata shawarar takama hotel kawai ta cigaba da rayuwarta har zuwa sanda mahaifinta zai sauko ya amsheta ,bazatayi fushi dashi ba ,haka zalika bazata gaji da rokonsa ya yafe mata ba, har sanda zai furta ya yafe mata. Dan hk Kai tsaye wani had'ad'en hotel ta nufa me suna city hotel, cikin Dan kankanin lokaci ta isa kawataccen hotel din Wanda hotel ne ,na isasu ta d'aki ,daya daga cikin mai'aikatan hotel din yayi gaba rike da key'n d'akin ita kuma tabiyosa abayan rike da hannun nasreen ,byn ya bud'e mata d'akin ta mika masa key'n motarta domin shigo mata da kayanta, ya amsa juya cikin sauri, suka shiga ta meida murfin kofar ta rufe . Komai na agyare neat a acikin Had'add'en d'aki . Ko cikakken minti biyar baayi ba maaikacin yashigo da akwati kayansu ya ajiye ya sake fita, ita kuma takarasa tayiwa kofar key tare da barin makuli ajikin kofar ta dawo ta tsaya atsakitar d'akin tana k'arewa falle d'akin daya kallo wanda ya k'awatu sosai , doguwar kujera kwaya daya ajiye , da TV bango sai air condition ,babban wardrobe na zuba kayan sawa daga gefe, mirrow da bedside, daga can bangaren toilet ne me murfin glass . d'aki ne mai matukar kyau da fad'i ,ta d'auki lokaci tsaye tana k'arewa d'akin kallo sannan ta K'arasa ta kunna ac tare da rage karfinsa saboda nasreen , Jikinta a matukar sanyaye ta janyo hannun nasreen jikinta ta rungume yarinyar naji dumin jikinta muryarta a sanyaye tace "muje bbynah kiyi wanka nasan kin gaji dayawa ko? Murmushi nasreen ta sakar mata sannan ta sake shigewa jikinta, "momy meyasa kika kawomu nan ? "Mu koma gida nasan dady zai shiga damuwar rashinmu, plz momy mu koma ... "Shiiiiiii kiyi shiru da zance komawar nan har abada nasreen bazan komawa mahaifinki ba ,idan kuma kinfi sonshi da son zama tare dashi akaina fine I can take you to him right now. "Ki kwantar hankalinki zamuyi rayuwa kmr muna gida kinji bby, zan siya miki duk abinda kike ,zamu dinga kallon TV tare muna enjoy ki manta da wani dady okay"taja hannunta suka shiga bayin tayi mata wanka da ruwan zafi ,tana tsaye akanta tayi alwala suka sake fitowa tare daita daure da towel. tsab mead ta gyarata ta sauya mata wasu kayan masu kauri, ta Mike mata hijabi, "kiyi sallah kafin na fito, sannan ta juya ta sake komawa cikin bayi. Mmn sudais ce 💗💗💗💗💗💗 'YAN CINKI 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 ~NA~ *AYSHA A BAGUDO* ~DEDICATED TO~ FAIZA HAMMADU BARAU (YAR NUMAN) Page 78 ........tsaye tayi acikin bathtub din ,ruwa na tsiyaya akanta zuwa sansar jikinta,Wanda ke saukar mata da natsuwa kad'an saboda har wannan lokacin bakinciki abinda sajida da fu'ad ke shirin yi mata, yaki barin zuciyarta da gangar jikinta, "ta yaya zata iya sharing din fu'ad dinta da wata macen ,macen ma aminiyarta da suka taso tare... ? "Suke yin komai nasu tare sannan babu abinda bata sani ba na sirrukan rayuwarta.... "A gurinta Fu'ad ba kmr sauran maza bane ,daban yake acikin mazan datake kallo , sannan natsatse ne kamili Wanda yasan ciwon kansa ,tana son shi fiyye da rayuwarta sai dai bata jin zata iya ganinsa yana rayuwa tare da wasu matan byn ita,tafin son duk runtsi duk wuya su kasance tare suka k'arasa rayuwarsu . Ahankali take tuna moment dinsu dashi ,duk da ba wani bashi had'in kai takeyi ba ,amman hkn baya hanata jin dadin abinda yake mata. "Anya kuwa zata iya rabuwa dashi kmr yadda ta fad'a tayi rayuwarta ita kad'ai sai yarinyarta? "Anya kuwa ba wata cutar Kan zata sake yiwa rayuwarta ba ? Tayiwa kanta tambayar tana jin jikinta yana sauyawa, ahankali take jin feelings dinsa na bijiro mata duk da bata tsamaci zata ji hkn ba akansa, a wannan tsayuwar datake komai na rayuwarsu ke dawo mata daki daki cikin kwakwaluwarta ,yanzu ace agida ne kuma suna zaune lafiya dashi zai shigo bayin ,ya tsura mata kyawawan idanunsa masu maseefar burgeta da tsaya mata arai ,yana kare mata kallo ko kifta idanunsa baya son yi daga karshe kuma ya k'araso gareta ya riko kugunta yana me had'eta da jikinsa tare da shafa kirjinta yana goga mata gashin dake zagaye da fuskarsa zata lafe akirjinsa , koda kuwa bai yi niyyar yin wanka ba ko kwanciyar aure daita ba ,ganinta tsaye babu kaya zai janyoshi yayi koda kuwa acikin bayi ne yayinda ita kuma zata shiga tutturesa tana kukan shagwaba ita tagaji bazata iya da jarabarsa Amman ba zai ta'ba kyaleta ba har sai yacima burinsa akanta duk yadda tayi ta yakice tunaninsa abun yaci tura haka tayi ta tunaninsa .. ganin tunaninsa daya d'arsu a zuciyarta yaki barin tayi abinda yashigo daita ,yasa ta sauke naunayen ajiye zuciya sannan tasoma sa'bawa jikinta sabulu ,sai dai duk inda ta gogo sabulu ajikinta sai taji kmr tafin hannunsa ne ke yawo ajikinta Dan haka tayi Shap shap tayi wanka ta d'auro alwala ta fito ,koina a d'akin ya kama kamshi room freshener da'akayi amfani dashi . jakar kayanta ta bud'e ta ciro doguwar riga ta sanyawa jikinta ta k'arasa inda pray mate yake ta tada sallah byn ta idar da sallah s ta janyo akwatin kayansu ta fiddosu daya bayan daya tasoma jerawa cikin wardrobe nasreen na tayata miko mata, wasu suna hirarsu cikin farinciki duk da ita ba wai nufinta tayi hkn ba ,Amman ya zame mata dole ko dan kwanciyar hankalin diyarta da lafiyarta ,batayi sha'awar kunna makeken TV dake makale da bangon d'akin ba ,Amman saboda ta d'bewa nasreen kewa yasa ta tashi taje ta kuna ta dawo tacigaba da aikin jera kayan. byn tagama jira kayansu ta tmbyi nasreen ko zata ci abinci Dan ita bata jin cin komai ,yarinyar tace " ba yanzu ba sai zuwa anjima momy , Dan kafin me'ad ta yanke shawarar zuwansu hotel ta sai mata snacks taci a mota . Kwanciya tayi akan gadon tabar nasreen na kallo ,ahankali ta runtse idanunta domin ta samu hutu da natsuwar zuciya, Kafin lokacin sallar magri tayi ,tunanin mijinta ne ya sake sanyo kai cikin zuciyarta dama gangar jikinta, wani irin sabon yanayi ta tsinci gangar jikinta ciki yayinda wani feelings dinsa yashiga bijiro mata idanunta har sun sauya, da kyar tasamu ta yakice shi ta Mike ta janyo system dinta data jona a caji ta kunna tasoma dudduba sakonin da aka turo mata ,cikin haka kiran chairman din company din datake aiki yashigo wayarta, take gabanta yashiga dukan uku uku ,da kmr karta d'auka Dan bata son K'arin tashin hankali akan Wanda take ciki ,ammam ta sanshi tasan halinsa shima ba kwanwar lasa bane ,Akan company dinsa babu abinda bazai iya yi ba ,Dan HK tayi saurin sanyawa jikinta kuzari ta d'auka ta manna wayar a kunnaneta tana gaisheshi a natse ya amsa tare da cewa "muna bukatar ganinki gobe by 10 :am atakaice tare da katse kiran ,jikinta yayi sanyi kmr wace akayiwa wanka da ruwan sanyi ,gbdy takasa cigaba da operating system din dake gabanta, ta ture system din gefe ta janyo nasreen ta rungume ajikinta hawaye na gangarowa daga cikin kwarnin idanunta ,"jikinta na bata aikinta ya kusan zuwa karshe.....har aka kira sallah magariba tana makale da nasreen tana jin karfin gwiwa a duk sanda ta rungumeta yayinda take cikin damuwa,ahankali ta zameta daga jikinta ta kwantar a saman cinyarta ta tsura mata ido kawai tana kallonta wani irin kaunar yarinyar nabin jikinta bacci take har lokacin tana sauke numfashi ahankali, ta Mike ta tashi taje tayi alwala bayan ta idar da sallah bata tashi ba tacigaba da zama tana lazami tarenda kaiwa Allah kukanta. ********* Misalin karfe tara na dare mumy ta samu dady ad'akinsa cikin yanayi na rarrashi take ce masa "dady sam abinda kayi bai kamata ba ,yakamata kabi komai ahankali hannunka baya ru'bewa kace zaka yanke ka yar duk abinda me'ad tayi maka duk lalacewarta bazaka ta'ba canzata amatsayin diyarka ba ,kalaman daka furta mata a yau din nan yayi muni dayawa..... dady yasoma magana cikin 'bacin rai "ina amfaninta arayuwata? "Meye amfanin D'an da bai jin maganar iyayensa da yi musu biyayya? "Ni tsine mata ma naso yi tabi uwa duniya kowa ya huta ,dady yana fad'ar hk numfashinsa ya fara sama sama sai faman haki yake ,mummy tana ganin hk ta fara salati game da waige waigen Kafin kace me tuni dady ya fara fita haiyacinsa ,mummy tayi matukar rud'ewa sakamakon numfashinsa daya tsaya a matukar gigice ta kwallawa suhailat kira itama tashigo d'akin a rud'e tayo gurin momy dake jijigasa , tare da taimakon sulahait suka dawo da dady parlour'n, ruwa sanyi mummy ta dinga shafa masa sannan ya dawo haiyacinsa ya jike sharkaf da ruwa kwance ya ganshi ajikin momy wacce idanuwanta tuni sun dade da yin luhu luhu saboda kuka, dady ya d'ago idanunsa ya kalli momy da take faman tofa masa adduoi, da kyar dady ya iya bud'e bakinsa "wai ,abinda nake tunanin ne ya faru..? Mummy tace " a'a babu abinda ya faru ina dai tunanin BP dinka ne ya tashi bara nai ma doctor waya yazo ya duba ka. Jikin momy na rawa ta tashi daga gun datake zaune tana rungume da dady tmkr wani karamin yaro ,bedroom dinta ta nufa ta d'auko wayarta dake ajiye akan gado ta fara lalubo lambar cikin kankanin lokacin takira doctor ya d'auka ,ta fad'a masa duk halin da'ake cikin doctor yace "gashin nan zuwa . Doctor Peter ya faka motarsa ya fito da sauri ya nufi hanyar da zata sadashi da parlour'n dady ,Amman a wannan lokacin momy tai masa jagora zuwa bedroom din ,doctor ya fito da kayan aiki yasoma dubashi ,byn ya gama ya kalli mummy yace " "madam ya'akayi hkn ta faru jininsa ya hau dayawa sosai ? "yakamata ku kiyayye 'bacin ransa domin ya samu cikakkiyar lafiya mai dorewa mumy tace "doctor yanayin rayuwa ne kawai Amman za a kiyaye InshaAllahu. Doctor Ya bar magunguna da dady zai yi amfani dasu ,allurar bacci akayi masa domin ya samu ishashen bacci sannan yakama gabansa . Ta bangaren fu'ad shima yana cikin tashin hankali mara misaltuwa, duk inda yasan zai ganta yaje har dama inda bayi tunani ba, hankalinsa yayi maseefar tashi yarasa inda zai sa ransa yaji dadi shi kam a yadda yake ji acikin ransa bazai iya hakura da neman me'ad ba ,kodan tilon diyarsa mara lafiya har hawaye ya zubar aranar ya samu guri gefen titi yayi parking din motarsa ya d'aura kansa a saman sitiyari yana kukan tausayin halin da nasreen dinsa Zata shiga a sanadin wannan tashin hankali, yasan me'ad bawani kulawa zata bata yana jin tsoron ya rasata, ya dade agurin sannan ya tada motarsa yayi hanyar gida ,koda isa gidan kasa zama yayi sai faman zariya yake acikin parlour'n sakamakon sautin bugun zuciyarsa daya addabi kunnensa "wayyohlly Allah nah ya furta yana me rike kugunsa da hannu daya ..... Daren ranar kuwa kwana me'ad tayi nafila Sam takasa runtsawa , saboda tashin hankali datake ciki yafi karfin tunaninta , tunanin mahaifinta yafi komai addabar zuciyarta, tayi shiru agurin tana lazimi tana jin kmr takirasa ta sake bashi hakuri ,daga inda take zaune ta mika hannunta ta d'auki wayarta tasoma neman layinsa ,takira wayarsa yafi sau biyar ba'a d'auka ba kawai ta rushe da kuka tana cigaba da addu'a, sai kusan ukun dare bacci 'barowa yayi awon gaba daita. Washegari da wuri ta tashi ta shirya nasreen cikin uniform din school itama ta shirya kanta ,ta tasota gaba, tana gaba tana binta abaya har reception,ta bada makulin d'akin domin killaceshi sannan suka fice . kai tsaye wani had'ad'en restaurant suka nufa tayi musu order abinci, ta turawa nasreen abinci agabanta tare da yin tagumi ta tsura mata ido "ki ci abinci ..... "Momy ke meyasa bazaki ci ba ?Tayi mgnr muryarta na rawa kmr zatayi kuka "kici kawai nasreen bazan iya ci ba ....... take idanun nasreen ya cicciko da kwalla "why momy.....ta fad'a hawaye na gangaro mata"tun jiya banga abinda kikaci ba ,idan bazaki ci ba nima bazanci ba takarasa mgnr hawaye na biyo kuncinta sharrrrrr .. me'ad tayi saurin kai hannuta saman fuskar nasreen tana goge mata hawaye ", no my bby dont cry I will eat tasoma k'ok'arin dibar abinci ta kai bakinta "gashi ina ci kema ki ci kinji bbynah banason damuwarki ina matukar sonki duk da dadynki nagani kmr banasonki ,adalilin ban ajiye aikina ba Wanda hkn bashi zai nuna bana sonki ba ,nice nayi silar zuwanki duniya idan wuya ake ci naci idan dadi ne naci" ta yaya mutun zai d'auki ciki har na tsawon wata tara yayi na kuda ya haifi d'ansa ace masa bai sonshi ..... "ki daina d'aukar maganganun mahaifinki, abaya nasan nayi sakaci , rashin kulawa dake Wanda bashi yake nufin bana sonki ba ....ina sonki nasreen fiyye da kaina sannan a shirye nake Dana sadaukar da rayuwata akanki, akan mahaifinki nayi komai har sanda na mallakeshi matsayin miji gareni ,ina kuma ga ke dani kad'ai nasan azaba da wuyar Dana sha tun daga haihuwarki har zuwa yanzu. Ta k'arasa mgnr tana bata abinci abaki suna ci tana kwantar mata da hankali har suka gama tayi dropping dinta a school takama hanyar zuwa office,Akan hanyarta ta zuwa aiki duk inda taga Almajiri sai ta tsaya tabashi sadaka maganin maseefa .. Ahankali ta Sanyo hancin motarta cikin ma'aikanta tsirarrun mutanen da suka yi sammakon zuwa suka bita da kallo , inda take jikinta ya bata akwai abu dake tafiya a kasa, wata irin damuwa me tattare da tashin hankali ne sukayi mata diran makiya ,amman hk bai hanata sanyawa zuciyar Kwarin gwiwar ba ,ta nufi gurin data saba ajiye motarta tayi parking tana fargaban fitowa ,kusan minti talatin tana zaune works nata faman shigowa ciki har dasu mudansir da ma'aruf suka fito atare suna kyalkyake dry da alamun suna cikin nishadi suka shiga cikin ma'aikatan batare da sun lura daita ba. tana zaune tahir shima yashigo ya wuceta. ahankali ta fito da system dinta tasoma operating domin k'arasa tura sakonin da'akayita turo mata daga daren jiya zuwa safiyar yau din nan ,bata fito ba har sai da taga shigowar chairman sannan ta fito adaidai karshen dogon korido ta had'u da mudansir yayi saurin k'arasowa inda take ya amshi jakar hannunta da system, ita kuma tacigaba da tafiya ta nufi hanyar office dinta da niyyar shiga ta gani ko zata daina jin zafin dayake mata. Mudansir yabiyo bayanta da Dan hanzarinsa "madam yau fa akwai meeting da chairman "nasani ta bashi amsa atakaice tana kusa kanta cikin office dayake tun shigowar mudansir ya bud'e, wanda ya zamemasa kaida . ai da wani irin sauri me'ad ta fito daga cikin office dinta kmr zata hantsila tana furta kalmar "inna lillahi wa inna ilaihi rajiun lahaula wala kuwata illa billa.... Shi kuwa mudansir kad'an yarage bai kyalkyale mata da dryr mugunta ba saboda yadda yaga tafito aguje kmr mota .... numfashi take fitarwa ahankali tana jin zafi ajikinta, tayi saurin barin jikin kofar Dan tiririn dake ta'ba fatar jikinta, ta nufi conference room, koda ta isa ta iske chairman zaune tare da mataimakinsa Wanda yakasance ba indiye ne ,shine na biyu a company sai ita, duk sauran wad'an da ke zaune agurin akarkashin ikonta suke, ahankali ta samu guri ta zauna a natse zuciyarta na bugawa ,wannan shine karo na farko da za'a yi taro ta tsinci kanta cikin matsanancin fad'uwar gaba ,duk taron da za'a yi cike take da natsuwar zuciya da kwarin gwiwar tare da isa da mallaka da nuna ita din wata ce acikin ma'aikatar ,sai gashi yau babu wannan zarra da isa da mallaka sai tsagwaron tsoro dankare da zuciyarta. Shiru ne yabiyo bayan zamanta , kafin daga bisani chairman yayi gyaran murya yasoma magana cikin kwararren turancinsa wanda bazaka ta'ba cewar ya had'a jinsi da hausa fulani ba"acikin yan kwanakin nan abubuwa dayawa sun faru Wanda yasa dole mu tautauna akai, Abu na farko da campay tasoma fuskanta shine karancin income din da company bai samu ,ta hanyar sakacin manager. Me'ad ta d'ago idanunta da sauri ta d'aura akansa tana kallonsa , chairman ya fuskanceta da kyau kana yacigaba da mgn "sakacin rashin tsayuwarki akan aikinki da rashin bawa aikin mahimmanci yana kokarin janyo mana babbar hasara, a halin yanzu dakatarwa ce tafi dacewa dake ,Amman saboda wannan shine karo na farko da muka ta'ba samunki da wasa da aiki, yasa zamu yi sausaci akai ,Dan hk daga wannan lokacin bama bukatar sakaci ko rashin bawa aikinki mahimmanci, Dan idan muka sake samun rashin ingancin tsayuwarki aiki zamu sallameki...... tunda chairman ya fara magana ta nemi miyo ko daya tarasa abakinta, zuciyarta ke wani irin bugawa da sauri sauri ,duk karfin ac dake aiki acikin conference room din ,hkn bai hana gumi tsatsafo Mata ba.. take furucin mahaifinta yashiga dawowa mata "aikin da kike takama dashi Wanda ni kad'ai nasan irin wahalar Dana sha akansa kafin ki sameshi shima zai bar hannunki ...... "inna lillahi wa inna ilaihi rajiun kawai take furtawa a zaunen dake agurin gumi na sake tsatsafo mata , iya abinda ta iya fahimta kenan daga bakin chairman duk sauran maganganun da yacigaba dayi babu abinda ta fahimta hatta Wanda sauran ma'aikatan suka taunana bata fahimci komai ba ,sakamakon zuciyarta data tsaya ta daina aiki na wani lokaci ... Lokacin da zuciyarta tacigaba da aiki ta dawo cikin hanlinta ta nemi kowa tarasa acikin conference room din sai ita kad'ai zaune ,ashe tuni taron ya watse . runtse idanunta tayi sosai, wasu zafafan hawaye suka shiga kokuwar zubo mata "me ke shirin faruwa da rayuwata ? "gidana babu dadi ,bani da jituwa da mahaifina , aikina na neman subuci min ,tabbas wata maseefa na kusanto rayuwata "ya Allah ka kawo min sauki cikin lamarina ,ya Allah karka barni haka, na tuba Allah kasanyaya zuciyar mahaifina akaina ya yafe min abinda nayi masa ,domin nasan bakinsa ne ke bibiyar rayuwata, ta Dade zaune agurin tana kuka ,ganin kuka da tunani bazai bar kanta ba yasa da kyar tasamu ta mike tsaye tare da gyara zaman mayafinta zuciyarta bata shawarar ta nemi mutane suje su bawa mahaifinta hakuri ya yafe mata, mahaifin sajida shine mutun na farko da zuciyarta ta hasasho mata Amman ina bazata taka kafafunta zuwa gidansa ba, 'yarsa tayi mata katangar karfe Dan wannan gidan har abada bazata sake sanya kafafunta cikinsa ba ,ta kofar baya ta biyo Dan batason jama'a su ganta ,Dan zasu fahimci halin da take ciki .. kmr jira ake duk inda ka yi acikin ma'aikatar maganar me'ad ake da irin matakin da chairman yace zai d'auka akanta, su mudansir kuwa ansamu abinda ake so ,sai murna suke har da rawa kmr wad'anda akayiwa albishiri da gidan aljannah " kai mutumina wallahi ina cikin farinciki mara misaltuwa ka koma gurin malamin nan naka ya sake k'ara wutar aiki, ayi ayi akoreta wallahi ban so uzirin da chairman yayi mata ba ,naso yayi mata me gabadaya ne injin cewar ma'aruf.. wata uwar dariya mudansir ya kwashe dashi "sha kuruminka abokina komai daki daki yafi ka zuba ido kasha kallo muna nan za'a yi mata me gabadaya.. Tahir ya saukar da ajiyar zuciya daman kuma tun da suka soma mgn bai tsoma bakinsa ba sai yanzu yace "gsky na fara jin tausayinta me zai hana abarta hk idan ka lura tayi sanyi ba kmr lukutan baya ba . "Kunji shirme banza ,kai ta tafi can kabawa mutane guri ,da alamun ka soma sauya ra'ayinka na bukatar matsayinta daka furta tun farko? "Ko ban sauya ra'ayina ba nima da wasa na fad'a mgnr , ina ni ina matsayinta, ku kanku kunsa wasa nake yi bazan ta'ba samun matsayinta ba sai wani ikon Allah. Maaruf yace "mudansir rabu da da wannan shirmammen banza da alamun cutar hauka tasoma kama..... ai bai kai ga karasa mgnr ba tahir ya cakumi wuyan rigarsa da iyakacin karfinsa "ni ne cutar hauka ta kama,? "ni zaka cewa hk saboda kai Mara imani ne da tausayi " ina zamu da hakinta ? "Meye ribarmu idan munyi sanadin rabata da aikinta da har zaka dangantani da kalmar hauka? Mudansir yayi saurin shiga tsakaninsu "haba tahir meye hk ne ? wasa yake maka fa bai kamata ka d'auki zafi ba ma'aruf ya fizgo mgn da kyar yace "rabu dashi ance masa me cutar hauka yayi duk uwar da zai yi ,mahaukaci dolo sauna dakiki..tahir ya kai masa mari sai ga jini ya balle abakinsa abu kmr wasa suka dinga zagin kansu da son yin dambe, da kyar mudansir yasamu ya rabusu tahir yana huci yace "ni... ni ...na cire hanuna acikin shirinku daman kuma ba dani akaje gidan malam ba ,daga yau babu hannuna cikin shirinku duk abinda zaije yazo karku sani ciki azzalume Kawai ya fita yana banko musu kofar da karfi . suka tsaya sororo suka bi kofar da kallo kirjinsu na mahaukacin bugu"kaji abinda wannan D'an iskan ya fad'a ko ? Ma'aruf ya fad'a yana naushin iska "rabu dashi shima zan gama dashi wata killa kafin ita tabar aikin shi zai rigata barin aikin. Kai tsaye tahir harabar ma'aikanta ya nufa inda ya iske me'ad tsayen tana zariya abar tausayi, kunnenta manne da waya "wallahi ta bani tausayi ya fad'a acikin zuciyarsa yana jin kmr yaje ya sameta ya sanar daita abinda aka yi mata,Amman yana jin tsoro saboda yasan halinta, yasan yadda take da saurin d'aukar zafi, karshen abun ya juye ya dawo kanshi ,shi kad'ai . kad'a kansa yayi kawai ya kama gabansa ya koma bakin aikinsa . ************ Zaune Alhaji ediris takai yake agaban amininsa kuma abokin shawararsa mahaifin sajida suna fuskantar juna kafin daga baya yasoma mgn a natse cikin sanyayyiyar murya "me yasa zaka hanata auren abinda take so, ? "A ganina daga me'ad har sajida abu daya ne agurimu ta wani fannin ma har gara sajida tunda duk rashin son da batawa emran ta hakura ta auresa daga baya Allah ya kawo rabuwa atsakaninsu, Dan haka banga dalilinka na hana auren fu...ya datse harshensa yakasa karasawa saboda baya tunanin zai iya karasa sunan wannnan D'an matsiyatan, shi kansa bazai so sajida ta auresa ba saboda irin tsanar da yayi masa Amman domin kuntatawa me'ad zaiyi tsayin daka ruwa da tsaki akan yaga yaron ya aureta shi da yasan inda zai ga najma har ita sai yabata makudan kudi ta auresa , kawai dan yaga me'ad cikin bakiciki kmr yadda tayi silar jefa safwan da shi kansa da har yanzu wannan bakinciki yaki barinsa. "abinda bazai ta'ba yiwuwa bane wannan AI cin amanar kauna da yarda ne Sam sajida baza ta'ba auran mijin me'ad ba har abada ...iniji Cewar mahaifin sajida . Dady yace "ta ina aurensu yazama cin amana ? "Gsky ni banga wani cin amana ba acikinsa ba. Mahaifin sajida yace "Ko babu cin amana ai ana barin halak Dan kunya, "banda wannan halak din mahaifin me'ad ya fad'a yana furzar da iska . muhawura ce tashiga tsakaninsu kowa na kawo hujjarsa Akan auren daga karshe dcp aliyu ya Mike ransa a matukar 'bace ya bar parlour'n saboda idan yacigaba da zama agurin zasu raba gari ,da shi da amininsa da Allah kad'ai yasan tsakaninsu . Mahaifin me'ad bai bar gidan ba har sai daya gana da sajida inda yake ce mata "ta gayawa wakilan fu'ad su zo su sameshi idan sun tashi ,ita kanta sai alokacin tasan tayi kuskuren son mijin aminiyarta , Amman yazatayi da tata zuciyar datayi kudin balan kamuwa da matsanancin soyayyarsa? Bayan kwana biyu sajida tasamu me gidan fu'ad da maganar zance aurenta da fu'ad, Amman ta boye masa gurin Wanda zashi neman aurenta,"yace karta damu InshaAllahu zaije ....fu'ad Wanda ya kasa samun natsuwar zuciya gabadaya ya tattara zance wani auren najma da sajida dayake son yi gefe saboda bulayin neman me'ad da sanyin idaniyansa ya taho guest house din me gidansa inda yafi tunanin zai samesa ya nemi izinin agurin aikinsa domin samun gano inda iyalinsa Suke,yashigo cikin parlour'n dayake zaune yasamu guri ya zauna yana sauke naunayen ajiyar zuciya tare da dafe goshinsa sannan ya gaishe dashi . Ya amsa yana ajiye magazine din dake rike a hannunsa,yana dubansa "yanzu nake shirin nemanka nan ya karo masa abinda sajida ta bugo ta gaya masa. wata mummunar tashin hankali ya tsinci kansa ciki take gefen kansa ya Sara ya d'ago agigice yana dubansa batare dayace masa komai ba me gidansa yacigaba da mgn yanzu sai ka sanar min da inda gidansu ita dayar yarinyar take sai ayi abun gabadaya a huta ,sosai fu'ad ke kallonsa da idanunsa da suka gama canza kalla har lokacin sunan mutumin dayaji yafito daga cikin bakinsa yake masa yawo acikin kwakwaluwarsa "to me hakan yake nufi da mahaifin me'ad yabada goyon bayan wannan aure? Zuciyarsa tabashi amsa da ya yana nufin abubuwa dayawa . a matukar zuciye ya runtse idanunsa yana tsuma bai tsaya gayawa me gidansa matsayin mutumin dazaije gurinsa neman aure ba .... Mmn sudais ce 💗💗💗💗💗💗 'YAN CINKI 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 ~NA~ *AYSHA A BAGUDO* ~DEDICATED TO~ JIDDATULKHAIRI MARUBUCIYAR MATAR DATTIJO Page 79 ......Jikinsa ne yacigaba tsuma , kansa gaba ɗaya ya kulle, yayi mamakin jin abinda mai gidansa ya fad'a mishi, hankakinsa gaba daya yagama tashi ,xuciyar sa ta shiga rud'ani, "wai me surukin nashi yake nufi da shi, ? "wane irin zato surukin nasa yake masa, ? "me yasa ya gwammace kar'bar auren sajeeda alhalin lokacin da zai aure me'ad kin amincewa yayi ? Tambayoyin da ya rika yiwa xuciyarsa kenan . "Yasan zai yi hkn ne Dan kawai ya bak'antawa me'ad rai .. .. A fusace ya mike zai bar parlour'n, cikin natsuwa mai gidansa ya kira shi "fu'ad ina zaka je haka,? Tsayawa yayi yana haki batare dayace masa komai ba . " me yasa naga yanayinka gaba daya ya canja? Dawo ka zauna" A hankali cikin nutsuwa fu'ad ya dawo ya zauna yana fuskantar mai gidansa. "Gaya min menene damuwar ka fu'ad, naga daga yin wannan Maganar gaba daya ka canja daga farin ciki zuwa akasinsa, hankalinka ya tashi damuwa ta bayyana a idanunka, fad'a min idan akwai wata matsala ne musan yadda zamu shawo kanta " Sunkuyar da kai fu'ad yayi sannan ya fara yin magana cike da ladabi da girmama ga mai gidan sa "Yalla'bai shi fa wannan mutumin da zai kar'bi auren sajeeda ba kowa bane face mahaifin me'ad" Wani irin shock mai gidan nasa yayi lokacin da yaji wannan maganar, "mahaifin me'ad fa ?" Ya maimaita yana kallon fu'ad cike da neman K'arin bayani "Kwarai kuwa yalla'bai mahaifin me'ad ne ,"Abinda yake ƙara d'aure min kai shi ne ta yadda zai yi ya amshi auren sajeeda alhalin a da can baya lokacin da xan auri me'ad 'ke'kashe ƙasa yayi yace baxan aureta ba, to yanzu kuma wane dalili ne zai sa ya amince na auri sajeeda tabbas nasan akwai wata manufa a cikin zuciyar shi". Shiru mai gidansa yayi yana nazarin Wad'annan maganganun da fu'ad ya fad'a masa, bayan sun kammala maganar da zasu yi ne suka yi sallama fu'ad ya tashi ya bar me gidansa zaune yana mamakin abinda ke shirin faruwa. Yana fitowa harabar gidan Motar shi ya bud'e ya shiga sai yaji kamar baxai iya yin driving din ba saboda wannan Maganar da aka yi masa ,tambayar kansa ya shiga yi me Mahaifin me'ad yake nufi da wannan batun da da'akazo masa da shi da rana tsaka, ? tunani ya rika yi gami da nazari, ba ƙaramin caji ƙwaƙwalwarsa ta rika yi ba a haka har ya isa gida wanka yayi ya sake fita neman me'ad sai bai samu ganinta bai yi tunanin zuwa gurin aikinta ba ,saboda yasan halinta ,kad'an daga cikin halinta su siyar da hali agurin shi kuma abinda bazai so faruwarsa kenan ba . A ɓangaren me'ad kuma, har yanzu tana fama da matsalar da ita kanta bata san asalinta ba, ba kuma ta san dalilin da yasa ta tsinci kanta a wannan halin ba,sannan har wannan lokacin bata daina tunanin hakunci da chairman din office din su ya fara tunanin yanke mata ba ,ta hanyar dakatar da ita amma sbd kwarewar ta ga iya aikin da jajircewa wajen tsayawa tayi aikin yadda ya kamata yasa ya d'aga mata kafa gabadaya ta fige ta rame tafita haiyacinta ban da kuka babu abinda take .. Hankalinta kullun sake tashi yake ganin yadda kullum matsalarta gaba take yi bata baya ,hkn yasa ta sake dagewa da addu'a da sadaka da kiyamullaili a kan Allah ya kawo mata karshen wannan matsalar da take ciki, duk da wannan jajircewar da take wajen addu'a da sadaka still dai har yanzu bata iya xama a office dinta domin gudanar da aikinta kamar yadda yakamata ,yayinda tsakanin su mudansir da tahir amintarsu ta dawo sama sama ko nace ta kusan Yankewa, saboda kusan kowa yanzu harkar gabansa yake sai dai a kasan zuciyar mudansir yana jin cewar bazai iya barin tahir hk ba sai ya bisa da bita da kulle. sajida zaune a d'akinta tana tunanin yadda aurensu zai kasance da fu'ad , ita tana jin idan duk duniya zasu had'u akanta matsawar fu'ad ya amince da aureta zata aureshi ko da kuwa mutuwa me'ad zatayi ,ita Sam bataji kunyar ko tsoro acikin dady'n me'ad zai kar'bi aurenta ,a ganinta ma meye aciki Dan ta auri fu'ad? "Tana son shi bugu da kari kuma ita me'ad tayi wasa da damarta ta hanyar rashin kulawa da gidanta, yanxu hk tana da labarin duk abinda ya faru daga korar da mahaifinta yayi mata har zuwa neman da fu'ad ya haukace agari yana yi akanta, gashi ita tasan hotel din da me'ad take gaya masa ne kawai ba zatayi ba ,tana nan tana jiran yagaji da nemanta ya hakura ya dawo haiyacinsa suyi aurensu a wuce gurin Dan ta najma me sauki ne ita me tasan yadda zatayi daita a karshe matukar ya aureta bazai ta'ba tunanin wani aurenta ba hatta me'ad din karon kanta zatasa ya manta daita arayuwarsa ,tana cikin wannan tunanin kiran khalid yashigo wayarta,taja dogon tsaki tare da furta another problem sannan ta d'auki wayar "meye ne zaka dameni bafa nason takura "Ki fito ina jiranki a harabar gidanku ya fad'a atakaice tare da katse kiran . khalid matashin saurayi ne D'an kimanin shekaru a shirin da shida zuwa da bakwai ,abokin aikinta ne dake bibiyarta da sunan friendship har ta kai daya fito fili ya bayyana mata sirrin dake ransa , Amman fur taki amince masa asalima sai yanke halaka tayi dashi saboda bataga wani abin so ajikinsa ba ,kuma tun daga ranar bata sake barin sun had'u da junansu ba balle ya karanto shirme ,shi kuma babu abinda yake kwadayi da son gani kmrta .duk da bata sanar masa ba yasan komai akan yadda take mugu mugun son fu'ad . Ta fito sanye cikin wando da rigar body hook Wanda ya matse jikinta sosai ,A tsaye ta sameshi jikin motarsa dake kusa da nata motar ,ya hard'e hannuwansa duka akirji, tun sanda ta fito ya tsurawa surar jikinta idanunsa,yana kallonta daga sama har kasa yake kare mata kallo tsab irin macen da yake burin so da mallaka kenan arayuwarsa ,ji yake duk duniya babu mace me kyawunta sannan yana ji tmkr ya isa gareta ya rungumeta akirjinsa , yanayin yadda yake kallonta kwata kwata baiyi mata ba ,Dan har ya sata jin wani iri ajikinta saboda gabadaya ya tsurawa nonuwanta idanunta kmr zai cinyesu , kallo daya tayi masa ta d'auke idanunta akansa ta haye saman motarta ta zauna tana kallon wayar hannuta batare da tace masa komai ba Khalid kyakkyawa ne shima sai dai bai kai fu'ad a komai ba , gyara tsayuwarsa yayi tare da matsowa gabanta still rungume yake hannunwansa a kirjinsa ahankali yasoma mgn cikin sanyayyiyar muryarsa "plz sajida kinsa na dad'e ina binki ta hanyoyi daban daban , ina sonki kuma tsakanina da Allah ,ki manta kowa ki bani damar na shigo cikin rayuwarki dan Allah.... Ta busar da iskar bakinta idanunta har lokacin yana kan wayarta, kanta tashiga girgizawa sannan d'ago ahankali tana dubansa a yatsine kana tace " Khalid Kake ko wa ? "Wai me kake tunani Akaina ne? "meyasa ba zaka fahimceni ba sannan ka fahimci ina na dosa ,?" Try to understand me Khalid ....."bana son ka bana kaunar wata halaka da kai kuma halakar da mukayi abaya ta mutunci Allah yasanya mata albarka Amman dan Allah ka fita cikin rayuwata , saboda kai ba irin namijin danake so bane ,you not can of man I like" " am not can of man ?ya tambayeta yana tsareta da manya idanunsa "yes of course ta bashi amsa tare da shayi ko wata fargaba ba sannan ta maida idanunta kan wayarta tacigaba da abinda take. muryarsa cike da rauni da in ina yace "meye bambamci tsakanina da kalar namijin da kike so? "khalid.....bana tunanin yau ne zan fara gaya maka wannan mgnr ,I have my type, ina da type din namijin da nake so , wanda zuciyata take so da muradi ba kai ba ,kuma zan tabbatar da na bawa xuciyata abinda take so tak'arasa mgnr tana hura masa iskar bakinta me zafi sannan ta tsaresa da idanunta "just forget about any love you have for me coz I can't love you kaje gaba da rayuwarka watakila zakayi cath up wata tasoka but not me .... "but ai ni ke zuciyata ta za'ba kuma take muradin rayuwa daita ina sonki saji...."enough khalid don't ever say that rubbish again..bazan ta'ba sonka ba koda kuwa zaka mutu ka dawo sajida nada ra'ayin mijin datake so okay ,"ina son namiji kamili natsatse wanda yasan darajar da ciwon kansa, dogo baki me faffad'an kirji me sex eyes me haiba da Kammala, ma'aboci kyau wanda a duk sanda na kallesa zanji Feelings dinsa na ratsani ... " idan na kallesa zan ji dadi acikin zuciyata sannan zai sani na jini a new level ba kai ba me zaka min ? "me zanji a tattare da..... ...? "common short up there my friend karki tozartani akan wannan sifoffin da kika lisafa ... ni meye na rasa ajikina ? " meye banda shi acikin abubuwan da kika lisafa? ta kai hannunta ta gyara gashin kanta daya zubo gefen fuskarta sannan tace "karka fad'i abinda kasan ba haka bane, da kace duk abubuwan dana lisafa kana dashi khalid ta ina ? "Ina suke ? "ina abinda na lisafa? "Sam ni banga komai ba danake so na namiji ajikinka , da kana da abinda na lisafa da yanzu mun wuce gurin ,abu na karshe da zan gaya Maka ka bar rayuwata .. Muryasa a matukar sanyaye yace plz sajida wallahi ina .." "Ka daina ronkona plz Dan ba zaka ta'ba samun abinda kake so ba kalleka fa D'an Allah wani gaja gaja da kai . kai yanzu bakiji kunyar cewa Kana sona ba a girme na girmeka nesa ba kusa ba Khalid me zan ji aurenka ...? zai yi mgn ta katseshi ta hanyar cewa "stop beging me khalid kaje kaso wata plz.. ya sauke naunauyen ajiyar zuciya tare da zura hannunwansa duka cikin aljihun wandonsa yana fitar da wani hucin Numfashi me gyaraye da tsagwaron 'bacin rai"ammm.. amm naji baki sona sai mijin aminiyarki kike so, saboda shi ne wanda ke da dukkanin tsifofin da kika lisafa ,tell me i want know? Ta d'ago fuskarta a d'aure tana dubansa shima kallon cikin idanunta yake cike da isgilanci rainasa din datayi "khalid am not long interested on you just live my life plz ... ya juyar da fuskarsa kad'an yayinda dryrta ta subuce masa yayi murmushin mugunta sannan ya juyo ya fuskanceta "dole ki waskewa mgnta saboda kinsa nasan komai , auren cin amana kike kokarin yi amman bari nagaya miki wani good news, ki hakura ki aureni saboda nasan duk abinda kike bukata daga cikakken nmj wallahi zan miki ,Zan iya cika wannan bombom din naki tsab da zan mararki Dan hk ki daina rainani yaro ne ni a zahirance Amman baki San badini na ba ..kuma ki rubuta ki ajiye a inda bazai goge ba ni ne zan aureki as ending ....... A matukar tsawace tace "plz just go tana nurfafashi tmkr me cutar asma " i don't want see you near me ta fad'i hk cikin murya mai rawa ala'mun tana son yi masa rashin mutunci " "sajida ...yakira sunanta muryarsa a kasalance "khalid can you live plz ? "dole ne nace bana yi bana sonka bana kaunarka bazan iya soyayya da kai ba ka bar rayuwata mana "naji amman yakamata ki duba girman son danake miki ki bari muyi ...."no no we are not talk to anything just go ...get out ..live ..bye... ta fad'a a matukar harzuke tana me dafe gefen kanta data ji yasoma Sara mata "plz i beg you sajida tayi saurin d'aga masa hannu out bey tana nuna masa kofar get da hannunta. jimmmmmm yayi yana kallonta sannan ya meida hannuwansa duka cikin aljihun wandonsa yasoma d'aga kafafunsa kmr kazar da kwai ya fashewa aciki tsaki taja ta gyara zamanta tayi consentret akan wayarta datake aikin turawa fu'ad text message tana jin lokacin da me gadi ya bud'e masa get ta juya a matukar fusace "you stupid man if you ever open get to that stupid boy you wil see what wil happen to you," a'a kunji min jaraba da maseefa irinta primature... karami yaro dashi sai jarabar naci ko ya zaiyi dani oho? "nace banayi banayi !! ana so do.... shiru tayi ta kasa karasa mgnrta taja tsaki kawai .... cikin sauri fu'ad ya fito daga cikin d'akinsa yana waya sanye da farar singlet da wando sai dai ya d'aura rigar t shirt a saman singlet din bai sanya botira ba "okay ina jinka tana wajen har yanzu ? Can bangaren kabeer yace "tana wajen Amman kayi sauri da alamun ta kusan gama abinda tazo yi .."dan Allah ka tsayar min daita . Kabir yace "kaima kasan halin wannan rikitacciyar matar taka ba tsayawa zatayi ba ,yanzu ma data ganin bazata tsaya ba .", okay ganin nan zuwa suna tare da nasreen ne ? "A'a injin cewar kabir cikin sauri fu'ad ya isa ya bud'e motarsa yashiga ya kunna tare da danna hon.....da karfi me gadi ya bud'e masa ya fita aguje. sai dai yana zuwa yashiga bud'e idanun yaga ta inda zai ganta ,kai tsaye inda kabir ya gaya masa ya nufa da sauri Amman bai ganta ba Dan hk yak'araso gurin kabeer yana riko hannunsa "ina take kabeer ...? Cire hannunsa kabir yayi cikin nasa yace "wallahil yanzu nan ta wuce naso na bita sai dai banzo da mota ba ,goshinsa ya dafe yashiga zagaye gurin tare da ya furta Allah yana me runtse idanunsa "why me'ad me yasa kike son ruguza mana rayuwarmu alhalin kinsa muna bukatar juna ..? Da sauri ya sake dawowa inda kabir yake tsaye yana dubansa cike da matsanancin tausayawa "wani hanya tabi kabir ...? Kabir ya nuna masa hanyar da tabi ..yabi hanyar da kallo yana tunanin yabita ne ko ya fita harkarta ya hutawa rayuwarsa, shi daman ba saboda ita bane yake wannan wahalar... Jiki a sanyaye ya k'arasa jikin motarsa yana kokarin bud'ewa kiran sajida yashigo wayarsa ya ciro wayar daga aljihun gaban rigarsa yana duba screen din wayar,number da ya gani ne yasashi Jan tsaki , kmr bazai d'auka ba sai kuma ya d'auka "uhmmm meye kuma? "I lost a lot of things arayuwata amman banaso kaima na rasaka fu'ad hope sir malik ya isa maka da sakona? "Wani banzar sako kenan "sajeeda ya kirata ransa a matukar 'bace"karki k'ara min matsala da damuwa akan wanda nake ciki ,wai ma Sajid me kike nufi dani ne ? "Babu komai sai alkairi kuma InshaAllahu zai tabbata ,tun da har ka furta tare da amincewa aurena wannan kawai ya isheni nacigaba da rayuwa har zuwa sanda zamu mallaki juna sannan kuma karshen matsalata tazo ,ka daina zurfafa tunaninka ,ka daina damuwa I promise zan baka dukkanin kulawar dakake bukata ,zan baka kulawar daka rasa saboda irin son Da nake ma ... "common that was not on fear, sajida bakya sona ki duba kiga yadda nake cikin tashin hankali akan matsalar gidana nasan kinsa komai amman ke k'ok'ari kike kawai a d'aura mana aure. "Tabbas aurenmu shine agabana kuma shine abinda nake buri a halin yanzu sannan zanyi Iya kokarina naga na mallakeka , yanzu dai kana ina ,Dan ina son mu had'u da kai akwai maganar da zamuyi very important" "bani da lokacinki a halin yanzu neman inda matata da yarinyata nake "ta kwashe da wata uwar dry sannan tace "ka sani ko nasan inda matarka take da yarinyarka just try and come...jikinsa yayi sanyi yasoma ya rage murya "Dan Allah ko kinsa inda take ne ki gaya min ...? "Uhmm a'a ban sani ba ,Amman ka dai kazo akwai Wanda yasani "rubbish ya furta a harzuke ganin raina masa wayo take son yi akwai siyar data sake shirya masa ,shi kuma ya ranse ba zai sake barin su had' u ba either ko tazama matarsa ko km sun rabu ..."ba zaka zo ba kenan ?"yes of course banzo wawiya kawai maciya amana ke auren ma na fasa inga uban da zai sani aurenki ...ta saki wata razannaniyar k' ara tare da durowa daga saman gadonta tana furta "what? "Abinda kunnenki yaji shi na fad'a na fasa aurenki kibar rayuwata simple as that " Muryarta na rawa tace" Dan girman Allah Allah fu'ad kar ka fasa au..sai kuma kiyi ya katse kiransa tare da shigewa motarsa ya bar gurin aguje.. ********** Yau takama Monday Wanda ko bature na tsoron ranar da girmamata rana ce da duk wani ma'aikaci ke jin tsorota da taka tsantsar daita ,me'ad tana zaune acikin motarta kmr koda yaushe tana tunanin yadda xata bullowa wannan matsalar da ta addabe ta , taji an kwankwasa glas din motarta da sauri ta d'ago kanta, tare da bud'e murfin mota ,daya daga cikin staff din company ne ya bayyana agabanta bayan sun gaisa yake fad'a mata cewa chairman yana son ganinta a office din sa. A sanyaye ta fito daga cikin motar tare yiwa motar key , da sallama ta shiga office din tare da neman kujerar da ke ajiye a gefe ta xauna gabanta na wani irin fad'uwa , bayan sun kammala gaisawa da chairman ya shiga jefa mata wasu tambayoyi. "Har yanzu na kasa ganin wani canji daga gare ki me'ad ,dan Allah ki fad'a min abinda yake damunki bana so ki boye min komai, Ni dai nasan da ba haka kike ba sam ban sanki da sakaci ko wasa da aiki ba, me yasa Yanzu abubuwa suke neman tabar'barewa Company? Ina jiran amsa daga gare ki kuma bana so ki boye min gaskiyar abinda ke faruwa da ke. Kuka mai tsanani me'ad ta shiga yi, sai da tayi kukan da ya ishe ta sannan ta zayyana mishi dukkan halin da take ciki. Ya tausaya mata sosai kuma yayi alƙawarin insha Allah matsalar da take ciki da mahaifinta yazo ƙarshe godiya tayi masa, yacigaba da mgn yana duba file din su ma'aruf "kinsa cewa wannan rashin zamamki cikin office dinki , sammu akayi miki ? mead ta d'ago kanta a matukar firgice tana dubansa cike da mamaki da matsanancin tsoro, "kina mamaki ko ,?tayi saurin d'aga masa kai alamun Eh "karkiyi mamaki mead akan samu irin haka . bakinta na rawa tace " ni kuwa wa nayi laifi da har zai min samu akan aikina ? Chairman yace "kina son sani ko su waye ? Jikinta na rawa tashiga girgiza masa alamun eh" "okay ina zuwa "ya d'auki wayarsa ya kira messenger cikin minti biyu yashigo jeka ka cewa acp ya shigo min da yaran nan kafi ya wuce dasu "okay sir ya fita da sauri .. Ahankali taji an bud'e kofar gabadaya ta kasa juya saboda jikinta daya d'auki rawa har sai da charman yace "ki juya mana kiga yan iskan da suka miki aika aika da kokarin rabaki da hanyar abincinki " jikinta na cigaba da kyarma ta soma juyawa ahankali har ta juyo gbdy idanunta ya sauka akan tahir da mudansir da ma'aruf dukanindu hannunwansu da handcuff, take gabanta yayi wani irin dukan uku uku yashiga fad'uwa tashiga nunasu da hannunta bakinta na rawa "ku..ku ne kuka min sai kuma ta rushe da kuka "laifin me na muku da kuka shirya min wannan munakisar? "A halin yanzu ba sai kayiwa mutun komai ba zai nufeka da sharri inji cewar chairman "wasu mutane suna nan su kawai basa son ganin cigabanka ,sun fi so kullun suganka kana bara akan titi 'acp a wuce dasu sannan ayi musu azaba me rad'ad'i har sai sun gaya muku malamin dayayi musu wannan aiki, if possible ma a asakasu a under ground har sai sun fad'a Dan babu yadda banyi dasu ba, alokacin Dana kamasu suna tad'in Dana takurasu ne ma sukace tare da tahir akayi komai " Acp yace"Karka damu kana zaune zamu zo maka da good news. "Okay nagode sosai tare da mikawa acp hannu sannan suka juya suka bar office din . Wani irin kuka me'ad take kmr ranta zai fita chairman nacigaba da bata hakuri"ba kuka yakamata kiyi ba illa ki godewa Allah da asiri ya tono if not ,hk kina ji kina gani aikinki zai bar hannunki "nagode nagode har bansa kalar godiyar da zan maka ba ,a yau na k'ara sani duniya ba'akin komai take ba, nasan watakilla sunyi min hk ne saboda yadda nake takura musu akan aikinsu ,kuma fa ni ina yi musu hkn bada wata manufa ba sai Dan su tsaya akan aikinsu kar ya subuce musu Amman babu komai nagodewa Allah daya nuna min su a tafin hannuna ...... Tun daga wannan lokaci chairman ya nemi manyan mutane wad'an da yasan suna muamula da mahaifin me'ad Sannan ya nemi mahaifin sajeeda domin shine kan gaba a komai agurin mahaifinta,domin a zauna da shi a bashi hakuri a roke shi gafara a kan laifin da me'ad tayi masa. sunje kmr yadda Chairman ya bukata sai dai da kyar alhj ediris ya yarda me'ad tashigo masa gida . Bayan sun gama gaisawa suka soma magana akan abinda ya kawosu"alhaji jabir yace "alhj ediris abinda ya kawo mu akan batun yarinyarka me'ad ne.. Dady yayi sauron katse masa maganar ta hanyar cewa "ni bani da wata yarinya me'ad arayuwata ,yarinya daya gareni kuma sunan suhailat Dan hk kayi wata mgnr ban da wannan" da sauri me'ad tashiga Jan gwiwowinta tana kuka "Dan girman Allah dady kayi hakuri ka yafe min ,kayi hakuri wallahi nayi nadama ka daina cireni acikin ya'yanka ...kuka take sosai tana bashi hakuri "Dan Allah ku bashi hakuri ya yafe min wallahi na tuba bazan sake ba, ku gaya masa duk abinda yake so zanyi masa bazan sake ketare zancesa ba, na tuba dady nabi Allah da manzonsa nabinka ka taimakeni ka taimaki rayuwata banida kamarka ,kaine ubana, bani da wani uban dayafika kamin komai arayuwa ka inganta rayuwata ka gatantani kayi min komai ,kayi hakuri nasan ban kyauta maka ba ..... "Banice yakamata nayi maka abinda nayi ba .....,Amman banida yadda zanyi ,bani da yadda zanyi da kaddara data gitta akaina, kayiwa darajar Allah kace ka yafe min ko al'amurana zasu daidaita jikin jama'ar dake gurin yayi sanyi hk ma dady karan kanshi . Sai dai yayi shiru yana aikin jijiga kafarsa, nan kowa yashiga topa albarkacin bakinsa, wannan yayi nasiha yayi shiru ,wani ma yakama da kyar dai akasamu jikinsa yayi sanyi gbdy , ya sauke naunayen ajiyar zuciya Wanda ke nuna ya sauko. mahaifin sajida yace "me'ad matsa kusa da mahaifinki sosai ki sake rokosa gafara kinji " cikin rawar jiki ta sake tsugunna har ƙasa ta roke shi gafara, bai yi gardama ba yace zai yafe mata amma tare da sharad'in kowa yayi tsuru tsuru agurin suna kallonsa tare da mamakinsa " Mahaifin sajida ne yayi karfin halin cewa "wani sharadi ne wannan ? "Sharadina shine zan raba aurenta da fu'ad saboda ni fu'ad din ne gaba daya bana sonta dashi ......."na tsine shi na tsani naga suna tarayya da 'yata , indai har tana buƙatar yafiyata to tabbas sai ta rabu da fu'ad.. kuma rabuwa ta har abada idan har ta amince da haka zan yafe mata kuma za ta zauna a gidana ta ci-gaba da rayuwa tare dani kmr can baya amma fa batare da auren fu'ad ba.. Mmn sudais ce 💗💗💗💗💗💗 'YAN CINKI 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 ~NA~ *AYSHA A BAGUDO* ~DEDICATED TO~ JIDDATULKHAIRI MARUBUCIYAR MATAR DATTIJO Page 80 ......'kwa'kwaluwarta ce ta tsaya ta daina processing na wani lokaci kafin daga baya ta cigaba da bugawa, ji take mgnrsa ba iya cikin kunnuwanta kad'ai suka tsaya ba har cikin zuciyarta take jin komai ,ta sake matsowa sosai kusa da mahaifinta wasu zafafan hawaye suka shiga gangarowa akan kuncinta. Tafukan hannuwanta ta d'aura a saman kafafuwansa dady Cikin mataanancin kuka, gabadayan idanunta dake zubar da ruwan hawaye ta tsurawa mahaifinta tana kallonsa tana son ya karyata mata abinda taji ya fito daga cikin bakinsa, yace "mata wasa yake mata ba gaske bane ,saboda d'acin kalmar tafi kowace kalma muni da zafi me ta'bo zuciya da wuyar mantawa , Amman sake maimaita kalmar da dady yayi ya tabbatar mata da iyakacin gaskiyarsa yake nufin raba aurenta da fu'ad a. take ta dinga furta kalmar "inna lillahi wa inna ilaihi rajiun "shikenan ta faru dani takare ta fad'i hk acikin ranta cikin matsanancin tashin hankali" yaushe ne zan sake samu 'yancin da rayuwa mai dadi kmr rayuwarta ta baya ? ,tun kafin jamar gurin suyi yunkurin mgn tashiga fad'i" shikenan shikenan !!! dady naji na amince na yarda da wannan sharad'in naka matukar zaka ya femin , domin ni yanzu nafi son farin cikinka a kan farin cikin kowa, duk abinda kake so shi zanyi ,bani da za'bin daya wuce naka .. Tana mgn tana kuka zuciyarta na rawa da gargadinta a kan abinda take shirin aikatawa rayuwata .. "tana son fu'ad tamkar ranta, kuma bata jin cewa xata iya ci-gaba da rayuwa ba tare dashi ba,Amman a halin yanzu ta za'bi farincikin mahaifinta akan ta cigaba da zama dashi ,zata cigaba rayuwarta babu shi acikin duniyarta , ta gwamaci ta yiwa mahaifinta biyayya a karo na farko ko rayuwarta zata daidaita ,koda kuwa rabuwa da fu'ad din zai zama silar barinta duniya..... a yanzu ta yarda ta fad'a kowane irin yanayi ne matuƙar dai mahaifinta zai yi farin ciki ya amshita amatsayin diyarsa sa'banin shekarun baya ,da ya fita lamarinta ...... "xata yi k'ok'arin k'arasa fitar da ragowar soyayyar fu'ad daga cikin xuciyar tayi rayuwarta da iyayenta da tilon diyarta. Kanta a sunkuye ta cigaba maimata mgn "Daddy na yarda ..,dady na amince duk Abinda kake so a halin yanzu zan yi, ba ni da wani buri a rayuwata sama da na faranta maka, sama da na kyautata maka nayi maka biyayya a kan duk abinda kake bukata daga gare ni, duk abinda kake so xan yi maka shi Daddy.... Takarasa mgnr tana wani irin kuka me ta'ba zuciya kuka take sosai tmkr ranta zai fita gabadaya duniya ta cukud'e mata waje daya bata ta'ba hk tashin hankali irin wannan da take ciki yake da muni da ciwo ba ,ta d'auka rashin son da dady yakewa fu'ad zai tsaya a iya hk ne ,ta d'auka rad'ad'in tuni ta tsaya a wancan lokacin ,ta d'auka ko darajar samun nasreen atsananinsu zai sauk'ak'awa zuciyarsa kiyayyar fu'ad ..... Amman da kalamansa na yanzu ta fahimci komai ya sauya agareta ,ta gane ita din ba kowa bace, tasoma fahimtar talaka marashi da galihu ya fita kwanciyar hankali sau dubu. yanzu wakilla najma datake kallo mafi kaskancin gani akanta tafita kwanciyar hankali da walwala . "yau din tazo mata da tashin hankali da rud'anin rayuwa maramisaltu "ya zatayi da kaddarar data gifta mata da rayuwarta gabadaya? Parlour'n ya d'auki shiru ,gabadaya jama'ar dake zaune acikinsa sun rafka uban tagumi, ban da sautin kukan me'ad bakajin sautin komai acikin parlour'n ..... Yayinda Mahaifinta yaji dadin jin kalaman daya fito daga bakin 'yar tasa, a nan take ya fahimci me'ad dinsa ta sauya ,ta samu natsuwa, ta k'ara hankali fiyye da lokutan baya, sannan da gaske take nufin nadamar abinda tayi masa a baya ,sannan a halin yanzu yasan ko zuwa gaba yace mata "ga abinda yake son tayi masa tayi batare da sa'bawa umarninsa ba. cike da matsanancin farinciki da jin dadi yace "me'ad na yafe miki duniya da lahira Allah kuma yayi miki albarka, Sannan amatsayina, na mahaifi gareki ina umartarki daki baro hotel din da kika kama ki dawo gidan ubanki da zama . Alhaji gali yayi saurin sauke hannunsa dayayi tagumi dashi tare da numfasawa yace " yanzu alhj ediris wannan d'ayen hukuncin daka yanke kana ganin abune me bulewa, raba ma'aurata da rana tsaka alhalin suna son junansu..? "Ni aganina hkn bai kamata ba ,idan shi yaron laifi yayi maka kamatayi a nemeshi ya baka hakuri ba rabashi da matarsa ba alhalin tana son shi ... Da sauri me'ad ta d'ago idanunta da har wannan lokacin basu daina tsiyayar ruwan hawaye ba tace "No.....dady kubar hukuncin da mahaifina ya yanke akaina kawai kada ku tursashi ,ni koda ina son fu'ad zan iya rabuwa dashi, ballanatana ahalin yanzu babu d'igonsa sonsa ko daya araina ni dai ku taya sake bawa mahaifina hakuri, nagode nagode da kulawarku gareni ,yadda kuka tsaya kuka gyara tsakanina da mahaifina, ina muku adduar allah ya biya muku bukatunku na alkairi, nagode nagode har bansan irin godiyar da zan muku ba .. jikinsu yayi mugun mugun sanyi babu wanda ya sake yunkurin cewa komai bisa lafazin bakin me'ad ,hk kowanensu ya tashi jiki a sanyaye suka soma mikawa juna hannu suna sallama da juna tare da k'ok'arin barin parlour'n,a tare suka fita har me'ad kowane yashiga motarsa itama tashiga nata motarta da niyyar d'auko nasreen daga school sannan . kasa tukin tayi ta gangarawa gefen titi tayi parking tare da d'aura kanta saman sitiyari ta fashe da wani irin gigitaccen kuka, gbdy tasoma datasanin barin gidan mijinta datayi ...kuka take sosai yayinda zuciyarta ke sake bud'ewa a wajajen ,da duk ciwoka suka samu muhalli, jikinta yayi mata sanyi,zuciyarta ta dinga tsinkewa har take jin tmkr batayiwa kanta adalcin rabuwa dashi ba,"ina Zata sake samun madadinsa? "Ina Zata samu jarumi jajjirtaccen miji irinsa ? bata San lokacin data d'auka tsaye agurin ba zuciyarta ke mata zafi had'e da tsinkewa ahankali take sake jin ciwon abinda fu'ad din yayi mata , sai da taci kukanta ta koshi sannan ta tada motar tabar gurin . a kan hanyarta ta dawo gida bayan ta d'auko nasreen, yarinyar take tambayarta abinda ke damunta "momy me ke damunki da alamun kina cikin damuwa koma nace kmr kinyi kuka ko..? "Bby banyi kuka ba idona ke min ciwo ,hk gefen kaina kmr zai fita kimin addua kinji bby .... ta k'arasa mgnr tana meida hawayen da yayi k'ok'arin zubowa . nasreen ta d'aura hannunta akan na momy'nta dake Kan giyar mota sannan muryarta a raunane tace " momy allah ya baki lfy ,but ki daina damuwa,Dan Nasan damuwa ne akan auren dady ko? " but momy ina tabbatar miki dady ba zai auri daya daga cikinsu ba ,saboda dady najin mgnta ba zai yi abinda banaso ba ,nagaya masa banason yayi miki kishiya da aunty sajida da najma. .. girgiza kanta kawai me'ad tayi "yaro duk inda yake yaro ne ... hanyar da nasreen taga me'ad ta d'auka ne sa'banin masaukinsu yasa ta sake fuskantarta sosai "momy ina kuma zaki kaimu ba hotel zamu ba ,? Tayi uwar tmby jikinta na rawa rawa "Dan Allah karki kaimu gidan grandpa yacika fad'a dayawa sannan kuma bayason dady'na nima...."short up there my friend I don't want here any from you just keep your mouth short ...tacigaba da tukinta batare da ta sake kallon inda take ba . yayinda nasreen ta sakar mata kukan ita baza taje gidan grandpa ba, gara ta kai ta gurin dadynta..... kukan datake yana ta'ba zuciyarta kuma batason kukanta saboda ,da zaran jikinta ya d'auki zafi shikenan .. ciwonta zai tashi Amman babu yadda ta iya da rayuwata ,hkn datayi shine kwanciyar hankalinta da samun natsuwarta ,duk ita tajawo komai daya faru dasu sai dai bata bakinciki da hukuncin da mahaifina ya zarta akanta ... har suka shigo harabar gidan kuka nasreen take, taki fitowa daga cikin motar sai da me'ad ta zagaya ta fito daita tashiga turturjewa ita sam bazata shiga cikin gidan ba "Dan Allah momy karki shiga dani banason gidan ....plz momy . alhj ediris dake saman barandarsa tsaye idanunsa ya sauka akansu sai yau yagama k'arewa yanayin yarinyar kallo , kyakkywace kmr me'ad dinsa ,sai dai kusan yanayinta na ubanta ne ,abubuwa kad'an ta d'auko na uwarta .... Haushi ne yakamashi ganin yadda ake dambe daita akan bazata shiga gidansa ba, to me hkn yake nufi kenan...? Ransa a matukar 'bace ya saki wata razananniyar tsawa tare da cewa "ki barta anan kishigo abinki idan bazata shigo ba ,wata irin gigicewa nasreen tayi tare da kwakume me'ad ajikinta "Wayyohlly Allah momy tsoro nakeji .....momy momy tsoro nake ji ki fita dani daga gidan nan tsoro nake ji ..... ahankalin me'ad yayi mugu mugun tashi take hawaye ya balle mata yashiga gudana a saman kuncinta, ahankali ta rungumeta ajikinta tashiga shafa mata kanta zuwa bayan ",cool down my baby nothing wel happen to you, just trust your mom....ki saki jikinki babu abinda grandpa zai yi miki he really loves you rarrashinta ta dinga yi yayinda har lokacin idanun dady ke kansu, ya kasa d'auke idanunsa akansu jiki a sanyaye me'ad ta yunkura tare da d'aukarta ta rungume kasancewar nasreen din bata da wani girma gashi babu kiba sai zallar farin fata da tsagwaron kyawun data d'auko daga iyayenta. ..... suna shiga cikin gidan me'ad ta kwantar da nasreen akan doguwar kujera 3 siter tana shafa kwanta yarinyar ta runtse idanunta gam batason ganin kowa har lokacin bata daina furta "tsoro take ji ba a fitar daita daga gidan . Me'ad tasamu guri ta zauna a gefen kujerar da momy ke zaune ta zuba uwar tagumi tana zubarwa da hawaye saboda duk abinda ya faru acikin kunnenta akayisa "Sam bataji dadin furucin dady ba ,Amman tasan tana yin wata mgn nata ne zaiyi zafi . me'ad ta kai hannunta zata cire tagumin datayi kenan suhailat tasanyo kai cikin parlour'n dawowarta kenan daga exam dinta karshe daga shi za'a turasu bautar k'asa. da sauri ta k'araso ta rungume me'ad tana murnar ganin sai dai ganin yanayinsu ya sanyayar mata da gwiwa tayi tsuru tsuru tana kallonnsu zuciyarta na wani irin bugawa "aunty me'ad momy lfy na ganku wani iri ko wani abu ne ya faru da dady byn fitata? Kuka momy ta fashe dashi sannan tashiga koro mata duk abinda ya faru . wata irin zabura suhailat tayi tana furta kalmar inna lillahi wa inna ilaihi rajiun sai maimata kalmar take hankalinta a matukar tashe cikin tsananin rud'u ,tana duban me'ad da wata irin gigitaccen duba muryarta a sarke tace " me ya zanyo kikayi mummunar wannan tunanin anti? Me'ad ta cije le'benta alamun damuwarta ta kai makura "ai kinga irinta ko anti?" kinga irin taurin kan naki ba ? "gashi zaki yi sanadiyar kashe auren dake kad'ai kika San irin wahalar da kika sha akansa . "watakilla da kinyi hakuri kin zauna ad'akin mijinki da yanzu duk hkn bata faru ba, Dan nasan ko bade dady zai yafe miki wallahi tallahi matsawar aurenki ya mutu ki sani kin yanki tikitin zawarci na shekara Goma sha.... ko fiyye da hakan ga dai karamin misali nan akan aunty sajida banda sauran mata da basamu sani ba ,me'ad tayi saurin runtse idanunta saboda sunan sajida da suhailat ta ambata. Suhailat tacigaba da mgn " kin guji mijinki Dan zai k'ara aure ke yanzu a tunaninki idan aurenki ya mutu mara mata ne zai zo yace yana sonki zai aureki? Sam ki canza tunani ki koma kibawa dady hakuri ya janye wannan furucin NASA ...suhailat takarasa maganar da sheshekar kuka Wanda ya k'ara dama lisafin me'ad har ta kasa kuka illa girgiza kai kawai datake kmr wata kadangaruwa.."take ciwon so yashiga dawainiyya daita a zaune datake ahankali ta sake runtse idanunta gam fu'ad zuciyarta tasoma hasko mata ," ta yaya zata iya rabuwa dashi ? Anya kuwa bata yaudari kanta ba ? Ta bude idanunta tare da zubawa suhailat ido gbdy ta kasa mgn suhailat ta sauke wata ajiyar zuciya mai bayyanan ne ciwo akirji "bari naje nasamu dady Dan Allah ya sausauta rayuwarma guda na wace ,idan da sauran zama tsakaninku sai rabo yazo ya kasheshi azo ana kuka..... ganin ta yunkura ta Mike me'ad tayi saurin meidata mazauninta "kiyi hakuri suhailat karkije ni kad'ai nasan kunci Dana shiga a sanadiyar fushinsa gareni, yau nasamu da kyar ya sauko har ya sake amincewa dani amatsayin diyarsa, Dan Allah karkiyi abinda zai sa a sake maimata tarihi fu'ad dai ni na kawoshi nace ina sonshi a yau kuma nace banasonshi ..... dan kowa ya d'auka wata halaka ko dangantaka bata ta'ba shiga tsakaninmu ba .. tana gama fad'ar hk ta mike hawaye nabin kuncinta tashige d'akin momy ta fad'a kan gado, ta kwanta ruf da ciki ta fashe da wani irin gigitaccen kuka "na barka bari na har abada kai din ma baka cancanci na sake butulcewa mahaifina akanka ba ,kai din maci amanar kauna ne gareni Allah yasa rabuwarmu tazama alkairi a rayuwata Allah ya had'a kowa da rabonsa na alkairi..... ********** Bangaren mahaifin sajida kuwa daga gidansu me'ad kai tsaye gidansa ya nufa ana k'ok'arin bud'e masa get idanunsa ya sauka akan Khalid da wasu daga cikin security's din bakin get ke dambe dashi na lallai sai an barshi yashiga gidan ,ai kuwa ana k'arasa bud'e masa ,atare suka shiga gidan .bayan direbansa yayi parking a inda aka tanada domin ajiye motoci da sauri ya fito batare daya rufe murfin motar ba ya k'araso bakin kofar da mahaifin sajida yake ,ya bud'e masa kafafunsa yasoma sanyowa waje sannan gangar jikinsa ta bayyana inda gbdy security's suka caaaa akansa kowanensu na rusunawa cike da girmamawa shima Khalid yakaraso yayi kmr yadda sukayi mahaifin sajida yabishi da kallo yana tunanin inda yasansa Amman duk tunaninsa yayi bai gano inda yasan yaron ba ,juyowa yayi ga security ganin K'arin bayani yake nema daga garesu yasa suka shiga rige Rigen gaya masa abinda ke tafe da Khalid ya jinjina kai yana sake karewa yaron kallon tsab yaro ne karami sosai Dan nesa ba kusa ba yasan sajida ta girme masa zatayi kani kusan na uku dashi hannun mahaifin sajida ya d'aga musu alamun suka gamansu sannan yace wa Khalid "biyo yaro ,yana gaba khalid na biye dashi abaya har cikin wani rantsentsan parlour'n dayaji kayan more rayuwar duniya yace ya zauna yana zuwa ,shi kuma yak'arasa ciki ,Khalid ya zauna tare da yin balance yana murza tafukan hannuwansa tsanyi ac Dana murna na ratsashi tmkr Wanda akayiwa albishiri da an bashi auren sajida. Mahaifin sajida nashigowa parlour'n sautin muryarta yasoma jiyowa cikin fad'a "Dan iskan yaro kawai ko me zanyi da kai ? "me zan ci da kai yaro karami da kai sai tsaurin ido ,okay Dan kaga ranar farko kayi nasarar shigowa, shine yau ma ka kwaso jiki kazo Allah yasa suyi maka dukan mutuwa su karairaka useless kawai, tana ganin mahaifinta tayi saurin waske tana susa tsakiyar gashin kanta sannan tayi masa sannu da zuwa ,ya amsa ransa a sake sannan yashiga d'akinsa bayansa tabi da kallo tana adduar Allah yasa bai ga Khalid ba . shigarsa d'akin bai fi minti goma ba ya sake fitowa ya nufi inda Khalid yake bayan ya bada umarnin akawo masa abun motsa baki . Yashigo bakinsa d'auke da sallama, Khalid na ganinsa ya sake rusunawa had'e da amsa sallama ,mahafin sajida yasamu guri opposite din Khalid ya zauna yana fuskantarshi, tsawon minti goma yana zaune yana kallon Khalid tare da nazarinsa ,me aiki tashigo rike da tire ta janyo karamin stood ta ajiye tiren akai ta juya . "meye ne sunanka mahaifin sajida ya fad'a yana gyara zamansa? Cikin rawa murya yace "Kha..Khalid ismail money mis road ne sir.." dady ya maimaita sunan saboda yasan Ismail mony mis road, ya jinjina kai kana yace "malam Khalid ga abun motsa bakin nan kasoma dashi tukun muyi mgn " "a koshe nake dady "kai kuwa kasha ko kad'an ne "ok na gode sosai ,yasa hannu ya tsiyaye tattaciyar ruwan inibi acikin cup ya cur'ba kad'an ya ajiye cup, yana sake gyara zamansa shima ya fuskance mahaifin sajida kmr yadda yayi masa kuri da ido . "Kace Khalid Ismail mony mis road kai din D'an cikinsa ne ? "Eh ....."ikon Allah" " me ke tsakaninka da sajida diyata? Batare da 'bata lokaci ba Khalid ya zayyane masa komai ."ka tabbatar kana sonta ? Khalid yace "sosai ma dady sai dai ita din ce kmr take raina ni a cewarta na...."ka manta da duk wani raini kai dai ba dai kana sonta ba kuma kana da inda zaka ajiyeta ba ? Khalid ya girgiza kansa alamun Eh " to ka turo min mahaifinka muyi magana ta kunne da kunne dashi yana gama fad'ar ya Mike "kayi k'ok'arin ka ci duk abinda aka kawo maka sannan ya juya ya fita daga parlour'n, ai ko babu kunya khalid ya zauna ya take cikinsa ,Dan yana son cin irin abubuwan Amman mugun son kudinsa daya gada Gurin mahaifinsa baya bari fitowa yayi yana d'ad'd'agawa security's kafad'u ,a zuwan shima yanzu wani ne acikin gidan. ************* Sajida fu'ad zaune agaban me gidansa, yayinda fu'ad sai faman cika yake yana batsewa tare da zabga mata harara ,saboda ya tsani yadda take zuwa kawo complain dinsa ga uban gidansa, daya zame masa tmkr uba garesa. Cikin murya kuka tasoma mgn "sir Malik ka taimakeni kar zance aurenmu ya rushe gbdy narasa gane Kan fu'ad aka. " dakata dakata !! Munafuka ta yaya zaki gane kaina, muguwa azaluma maci amanar kauna? sir kana kallon yarinyar nan katuwar muguwar makira ce ta bugawa ajarida, kwata kwata batasona da matata, sannan son datake ikirari tana min karya ne....... "Saboda zaka fadi hk ? Inji cewar sir Malik "na karyata hkn ne saboda ina dalilina ,Dan da ace son gsky sajida take min da ta tausayawa rayuwata ta gaya min inda matata da 'yata suke.... Kallonta sir malik yayi "ke kinsa inda matarsa take ne ? Tayi saurin girgiza masa kai alamun eh " "Kaji ko Amman tana kallona agari ina yawo bulayin nemanta ta kasa gaya min to ni kuwa me zanyi dake sajida? "Bari nagaya miki wallahi wallahi bana sonki kuma ban taba jin digon sonki a zuciyata ba ,na dai amincewa aurenki ne saboda yanayin da kike k'ok'arin ganin kin sanyani ciki alhalin ni ba ma'abocin hkn bane . Sannan baki son matata sajida.."karka ce wallahi ina .."short ya buga Mata tsawa "ta ina kike sonta? " tambayarki ki gaya min baya ga zuga min ita da kike okay kin d'auka ban sani ba ? "Kisani bazan ta'ba aurenki ba ,ke ko mutuwa me'ad tayi bazan aureki ba ..."karka fad'i sir malik yayi saurin katse shi " wallahi wallahi aaaaaaaa karka rantse "wallahi bazan aureta ba wannan shine maganata takarshe daita yana gama fadar hk ya Mike ya bar parlour'n, durkushewa tayi agurin tana kuka "Dan Allah kataimakeni kace masa ya dawo duk abinda yake tunani ba hk bane ,wayyohlly Allah kuka take kmr wata karamar yarinyar "ki kwantar da hankalinki zan rarrasheshi zan sa yayi kaffaran rantsuwar da yayi InshaAllahu ke dai ki cigaba da addu'a idan da rabo sai ayi da wannan maganar ya kwantar mata da hankali ta wuce. ******** Bayan mead ta dawo gida da sati daya , fu'ad yasamu labari tana gidansu ,Dan haka yayiwa gidan diran makiya , inda ya iske dady a parlour'n farko na gidan ya hakince acikin kujera , yashigo bakinsa d'auke da sallama , zuciyarsa babu wani fargaba ko tsoro ya gaishe da dady cike da girmamawa ,Wanda iya sallamar kawai dady ya amsa shima aciki , ya samu guri ya zauna batare da anyi masa izini ba . parlour'n ya d'auki shiru kusan minti talatin dady bai tambayi abinda ya kawosa ba, hk zalika shima fuad bai yi mgn ba har sanda nasreen wacce tagaji da jiran , tasanyo kai cikin parlour'n Dan shigowar mahaifinta ya faru ne akan idanunta da gudu tashige jikinsa tana murnar ganinsa "I miss you my special dady.....shima rungumeta yayi tsam ajikinsa yana sauke naunayen ajiyar zuciya kana yace "I really miss you too my special bby how are you doing ? "Am fine dady wani irin sanyin dadi ne yake jin yana ratsashi , yayinda zuciyar dady kad'an yarage batayi bundiga ba ,tsabar takaici da taanarsa ga fu'ad.. ahankali sautin muryar nasreen ta fito "dady kazo tafiya damu ne ? "Yes my bby jeki momynki ta fito mu wuce gida "gidan ubanwa kenan zata da kake mgn a gadarance? "a'a fu'ad ya fad'a cike da matsanancin mamakin dady sannan yacigaba da mgn "wace irin mgn ce hk dady kake fad'a ? "gidan mijinta mana zata" " 'Yarka me'ad ..? "uhmmmmm 'yarka ce sai dai ni kuma *matata ce ta sunnah* da duk ragamar rayuwarta ke tafin hannuna... " yi min shiru , kasani me'ad 'yata ce kuma ta dawo gidan ubanta bazata sake komawa gidanka tayi rayuwar kunci ba da babu ba ,Dan hk minti biyu kacal na baka ka bar min gida. "No no dady kar muyi hk da kai ,banason wata mgn ta sainsa tashiga tsakaninmu da kai saboda har yanzu kana nan matsayinka na uba gare...."dakata malam banason zance banza ni ba ubanka bane kasan ubanka, nima nasan iyakacin ya'yan Dana Haifa " "Okay tunda haka kace ina buƙatar *matata* abani *matata* na wuce daita muje tacigaba da rayuwar kuncin da babun da kace. Nan fa mahaifin me'ad ya fusata " baka isa ba ,wannan zance banza ne ka fad'a, ayau kuma ayanzu zaka sauwakewa 'yata igiyoyin aurenka dake kanta tayi rayuwar 'yanci " ", a matukar fusace fu'ad ya mike tsaye jikinsa na wani irin rawa yana yiwa mahaifin me'ad din wani irin kallon me cike da tsantsar tsama .sannan muryarsa a kausashe yace . "Wai daddy me kake nufi dani ne,? " me nayi maka ne daddy me na tare maka arayuwa, kake min irin wannan kiyayyar.? " shin a rayuwa ba a aure ne ko ba a soyayya ne na taimaka na auri 'yarka domin mu rufawa juna asiri, after ina sonta, kuma ita ma kasan tana sona, ka bani *matata* kawai mu koma gida mu je mu ci-gaba da rayuwar aure da ita" dady yace" baxan ta'ba barin ka tafi da 'yata koina ba, sannan ina da dalilai da yasa bana sonka , kuma har abada bazan ta'ba kaunar ka ba, saboda ni Safwan nake son tayi rayuwa dashi ba kai ba me digirin zero ....... Ka saketa tun wuri tun bamu had'u a kotu ba taje ta auri Safwan shi ne abinda nake buƙata kuma wannan ne cikar burinna a rayuwa me'ad ta auri safwan..... Furzar da wani numfashi mai zafi fu'ad yayi sannan lokaci daya ya kwashewa da uwar dry yana furta "Good naji duk abinda ka fad'a amma Ni ina son *matata* kuma baxan ta'ba sakinta ba, kuma ko kotun duniya zaka kai ni ,ka kai ni a shiryena Nike Amman bazan saketa ba , duk runtsi duk wuya duk talaucina muna tare , "dady idan duk duniyar zasu taru akanmu bayan kotun dakace , idan sama da kasa zasu had'u, idan za'a dinga hadari malaiku daga sama bazan saki *matata* me'ad ba, kuma idan har sai na saki me'ad sannan Safwan xai yi Aure,wallahi wallahi wallahi!!! sai dai Safwan ya koma ga Allah bayi aure ba, ko kuma ku yi aure a kan aure" yana gama fadar haka ya juya afusace tare da nasreen ya bar parlour'n, zuwa harabar gidan ,me'ad wace tun shigowarsa gidan ta kasa samun natsuwar zuciya sakamakon nasreen tagaya mata zuwansa " ta fito aguje tana haki ta rike hannun nasreen dake kuka saboda tashin hankalin daya faru akan idanun "sakar min hannun yarinya .......... ya tsaya tare da juyo idanunsu ya tsarke cikin juna, atare zuciyoyinsu suka buga, ido cikin ido suke kallon juna me'ad ce tayi saurin d'auke idanunta acikin NASA "uhmmm repeat what you just said now? "Yarki ko 'yata ?ya furta muryasa a kasalance tare da tsareta da kyawawan idanunsa. "Tambayarki nake kinyi shiru ,okay kema kin San gaskiya ko wannan property din belongs to me, kmr yadda mahaifinki ke kokari motsa kunjinsa akanki Dan hk sakar min hannun yarinyar..durkushewa tayi agabansa ta fashe masa da kuka "kabar min yarinyata ,idan ka rabani da ita mutuwa zanyi ,Dan Allah kabar min ita ..ahankali ya saki hannun nasreen sakamakon wani tunani dayayi ,barin nasreen zai iya taimaka masa takowani fanni, wallahi this time around zai bawa mahaifinta mamaki zai zame masa kadan garen bakin tula....rungume nasreen tayi ajikinta tana kuka shi kuma ya juya ya isa yashiga motarsa ya bar gidan .. Bangaren dady kuwa sai zariya yake a parlour'n, ya kai gauro ya kai mari "aikin banza akin wofi kawai wannan yanzu har surukin arxiki ne? " ina fad'a yana fad'a, koda yake tsiya da talauci babu abinda basa saka mutun yayi ,sai dai ka rubuta ka'ajiye sai na raba wannan auren koda kuwa da karfin ikona ne ..... Mmn sudais ce 💗💗💗💗💗💗 'YAN CINKI 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 ~NA~ *AYSHA A BAGUDO* ~DEDICATED TO~ *AUNTY BASEERA WANNAN PAJIN NAKI , INA MATUKAR GODIYA BISA GA SOYAYYARKI , ALKHAIRINKI,KULAWARKI GARENI ALLAH YA BARMU TARE*🤝🏻🤝🏻🤝🏻 Page 81 .....kai tsaye fu'ad gida ya nufa zuciyarsa na wani irin tafarfasa,yana shiga parlour'n ya fad'a Kan doguwar kujera 3 siter yana fitar da numfashi me gauraye da zafin ciwon abinda surukinsa yayi masa ,ahankali tunaninsa ya cigaba da gudana lokacin daya sautin kukan matarsa yashiga dawo masa tana bashi hakuri"kabar min yarinyata, idan ka rabani daita mutuwa zanyi ..."Dan Allah kabar min ita .... runtse idanunsa yayi sosai tare da mikewa zaune da kyar, gabadaya ilahirin jikinsa yayi mugu mugun sanyi, ga wani irin matsifaffen ciwon da kansa keyi akan furucin mahaifinta ga tashin hankali daya barota ciki , da kyar ya iya bud'e idanunsa ya Mike tsaye yashiga zariya acikin parlour'n dafe da goshinsa , yana tunanin mafuta " ya Allah ka kawo min hanya me sauki da komai zai daidata gareni ,Allah kar kasa wannan bawa naka yayi nasara akaina ......."ya dade yana zurfafa tunaninsa ,bai San lokacin daya d'auka tsaye agurin ba, kafin daga bisani, ahankali ya d'aga kyawawan idanunsa ya saukesu akan wrist watch din dake d'aure da tsintsiyar hannunsa, karfe shadaya ta wuce da wasu 'yan mintuna, tsaki yaja "hk kawai wannan tsohon na neman hadasa masa ciwon kai na babu gaira babu dalili ,a sukune yasoma tafiya zuwa d'akinsa yana 'bal'bale botiran gaban rigarsa yana shiga bathroom ya k'asara cire kayansa gbdy ya watsa Kan kujera . Bathtub yashiga ya tsakarwa kansa ruwa, take yaji wata natsuwa ta musamman ta saukar masa tare da bin ilahirin sansar jikinsa ,ahankali kuma yake jin hankalinsa na kara kwanciya ko babu komai yasan halin da matarsa da 'yarsa suke ,bugu da k'ari yasan inda suke Wanda a duk lokacin dayake da bukatar ganinsu zai gansu, wanka yayi shap shap ya fito kugunsa daure da towel fari ,while dayan hannunsa na rike da wani karamin towel yana goge sansar jikinsa dashi ,byn yagama goge jikinsa white boxer and white singlet ya saka yabi ilahirin jikinsa da turaren daya zame masa jiki ,sannan ya fad'a gadonsa zuciyarsa na matukar bugawa da karfin gaske. "Dole duk runtse muna tare dake me'ad ,ko baki min halicci komai ba arayuwata bazan iya sakinki ba ,da zan sakeki da tuni bamu kawo wannan lokacin ba ,"ka saketa ko mu had'u a kotu maganar dayake tayiwa fu'ad yawo kenan acikin kwalkwaluwa ..dogon tsaki yayi inda zuciyarsa tashiga hasko masa kamannin safwa yayi saurin runtse idanunsa ya d'aura hannunsa akansa tmkr me shirin yi kuka yace" i a m mad iam stupid matukar nayi kuskuren sakin me'ad wa wani katon banza da wofi ..ina sonki matata duk kece silar fad'awarmu cikin damuwa ga wani tashin hankali na shirin afka mana. wayarsa ya janyo ya fara dialling number me'ad domin yaji muryarsa sannan ya kwantar mata da hankali Amman har 5 missed calls bata d'aga ba, tsaki yaja yayi jifa da wayar akan gadon "matsalar kenan taurin kai . rungume hannunwansa yayi a saman kirjinsa yana kallon saman d'akin ,yayinda zuciyarsa ke hasko masa ita ji yayi hannunwansa daya rungume akirjinsa bazasu wadatar dashi ba ,yasa ya janyo pillow ya matse akirjinsa yana jin tmkr itace rungume ajikinsa, ahankali yana tunaninta ke fixgarsa ya kai hannunsa ya janyo bargo ya lullu'be jikinsa wani irin tsuma jikinsa ke yi tmkr zaki ga joystick dinsa sai mikewa take alamun tana bukatar abincinta wani tsakin yaja mtsssss hade da sanya hannuwansa duka ya dafe saman joystick da kyar yasamu bacci 'barawo yayi awon gaba dashi cike da matsanancin kaunar matarsa ...... Washegari ya tashi tattare da kuzari da farincikinki yashiga bathroom yayi wanka ya fito ya shirya zuwa office ,gabadaya ya nemi tarin damuwarsa ya rasa sai zallar farinciki dake dawainiyya dashi ,haka ma a office aikinsa yake gudanarwa cike da kwanciyar hankali ,a cewarsa matsalarsa ta kau damuwarsa tak'are tunda yasan inda iyalinsa suke Dan shi Sam bai d'auki mgnr dady da wani mahimmanci ba ...... ******** Alhj Ismail money mis road ya samu zuwa gurin mahaifin sajida bisa nemawa D'ansa auren diyarsa , inda har an tsaida magana me karfi atsakanin ,sannan an saka ranar aure nan da wata daya kacal me zuwa, mahaifin sajida ya hana Khalid sanar mata ko kusanta inda take har sai an kawo masa ita amatsayin matarsa ,haka zalika ya hana aunty nadiya ta fad'a mata ko yin wani abinda zai sa tagane . Anata shirye shiryen aurenta batare da saninta ba ,itama bata lura da yadda aunty nadiya ke zariya zuwa kasuwa ba ,lamuran gabanta kawai tasa agaba, na yadda zata mallaki fu'ad yazamo abokin rayuwarta, Dan har wata abokiyar aikinta datasan da mgnrta da fu'ad din ,tayi mata alkawarin Zata kaita gurin wani hatsabibin malaminta yayi mata aiki akansa, ta yadda da kansa zai kawo kansa gareta farinciki sajida tayi sosai sannan tace" banason na mallakesa ta wannan hanyar kafila ......"ai kuwa yadda yake da taurin kan nan da nuna isa ,bazaki ta'ba mallakarsa ba sai kin sa an rankwafar miki dashi tukun kisamu kansa "shikenan kafila zan bi shawarki but ki bari na sake tuntu'barsa zuwa nan da two weeks kafin muje nan suka bar mgnr zuwa sanda sajida ta fad'a... ********** Me'ad tacigaba da zuwa gurin aikinta, sai dai har yanzu wannan lokacin bata iya shiga office dinta, dama cikin ma'aikanta gabadaya Dan chairman ya canza mata wani office kafin sanda za'a gama binciken su mudansir, Amman har lokacin jikinta bai daina mata tirin zafi ba Dan haka ta dawo zaman mota. Bangaren su mudansir kuwa, idan ka gansu ba zaka ta'ba ganesu ba ,adalilin dukan mutuwar da policewa suka yi musu, iya azaba an azabtar dasu saboda rashin fad'ar gsky da sukayi, kowane daga cikinsu kanshi yayi wani irin kunburi saboda azabar duka ,bama zaka iya tantance waye mudansir tahir ma'aruf ba acikinsu ,sai da mudansir yaga suna daf da mutuwa sannan yayi bayanin inda malamin dayayi masa aikin yake,kai tsaye gidan bokan da akewa lakani da malami wanda ko kusa bai dace da amsa wannan sunan ba ,saboda mugun aikinsa da kuma irin ta'asar dayake aikatawa, rashin imani had'e da rashin tausayi sune abubuwan da suka baibaye zuciyarsa , bashi da maraba da irin bokayen nan na kan tsaunaka ,domin kuwa kallo daya zaka yi masa ka tabbatar da rikakken matsafi ne ,koda suka isa sun iske dubbanin jama'a tundaga kofar gidan har cikin gidan masu neman biyan bukata ,mutane na ganin rundunar polisawa na k'ok'arin shigowa kowa yashiga hankalinsa wasu ma tuni suka arci na kare kar a had'a dasu . batare da bata lokaci ba suka samu nasarar shiga inda boka yake ta,asa da wata mata kafin yi mata aiki a matukar firgice ya tashi daga jikinta yana kwaso kayanta Dana shi ya rufe jikinsa dashi ,ita kuma ta kudindine jikinta tana kirma, basu tsaya wata wata ba suka damko wuyansa sukayi hanyar waje dashi tsirara haihuwar uwarsa, ya turje yaki tafiya ,yana neman ba'asin dalilin dayasa zasu shigo har cikin gidansa suka mashi ,wannan mutsu da gardamar da yayi musu yasa suka rufeshi da dukan mutuwa tunin ya bada had'in kai . Aka fito dashi nan mutane suka ihu, masu guduwa nayi masu runtse idanunsu nayi ,daya daga cikin police yashig Janshi a kasa ,kai tsaye office dinsu suka nufa dashi , lokacin da'aka tambayesa game da aikin da yayiwa su mudansir bayi musu ba Amman lokacin da'aka nuna masa mudansir muryarsa kawai ya iya ganewa da abubuwan da suka faru atsakaninsu Wanda mudansir din ke kara yin bayani akansu ,hkn ya k'ara tabbatar masa dashi din ne mutumin dayayiwa aikin asiri da allurai ga shugaban aikinsa. Cikin tashin hankali jami'an tsaro suka shiga yi masa tambayoyi daki daki shi kuma yana basu amsa, inda yace asirin zai karye Amman sai sunje ma'aikanta da office dinta saboda abubuwan da'akayi amfani dasu suna dayawa .kuka tahir yakeyi sosai tmkr ransa zai fita ya durkusa kasa gaban boka yana kuka yana rokon boka daya fad'i gsky mutun nawa ne suka zo yin asiri gurinsa duk rashin eimanin boka sai da tausayinsa yakamasa,yayi kmr ya fadi gsky sai kuma ya fasa yaki cewa komai dan a wannan stage din kowa ta kansa yake babu wani zance taimako . Gabadayansu aka tasa keyarsu zuwa company, suna isa aka tsaidasu agaban tafkeken get din ma'aikanta mutane nata wucewa suna kallonsu ,yayinda tsirarun jama'ar company da suka San abinda suka aikata sukayi caaa suna kallonsu tare da Allah wadai dasu ,Allah sarki tahir yayi kukan dayasani har hawaye suka daina fitowa daga cikin idanunsa , bayan an gama kare musu kallo sannan aka shiga dasu cikin company kai tsaye office din me'ad akayi dasu ,boka yayi shiru yana kallon office din hankalinsa a matukar tashe gbdy yama rasa ta ina zai fara. A zafafe daya daga cikin polisawan yayi magana cikin zafin rai da d'aga murya "what are waiting for? ganin bokan na nuku nuku tare da zare idanuwa"kayi abinda yakawo mu mana cikin rawar murya yace "yalla'bai kujerar datake zama za'a nuna min batare da 'bata lokaci ba aka nuna masa ya isa yashiga sarakulensa ,sai ga allurai su bayyana Wanda bazasu lisafu ba ,ba chairman da me'ad ba, hatta polisawa sun razana da ganin wannan tashin hankali ,boka ya cire gbdy allurai sannan ya dinga bin koina acikin office din yana ciro layu Wanda bil adama bai isa yaganewa isanunsa ba, sai dai a irin wannan lokacin. duk wani abinda akasawa me'ad a office dinta da cikin ma'aikatar sai da aka ciresa sannan aka tasa keyarsu zuwa caji office inda daga nan za'a gurfa nan dasu agaban kotu .... Tun daga wannan lokacin komai ya daidaita ga me'ad tasamu natsuwar zuciyar cigaba da yin aikinta yadda yakamata, sai dai duk abinda za'a yi ta daina tsoma bakinta aduk abinda bai shafeta ba, alamuran aikinta kawai tasanya agaba , matsalarta daya ahalin yanzu fu'ad ne...... tayi iya yinta ta ciresa aranta Amman abun yaci tura, kullun soyayyarsa k'ara wanzuwa take acikin zuciyarta, shiru tayi tare da yin tagumi da hannunwata duka ,tana tunaninsa cikin hk akayi knocking din kofar office dinta, naunayen ajiyar zuciya ta sauke tare da cewa"come in cikin murya tkmr mara kuzari ,sannan ta dukar da kanta domin cigaba da ayukan dake gabanta. "Turo kofar yayi ahankali ya shigo fuskarsa a daure babu alamun murmushi ko kad'an sannan ya meida kofar yayi key ,sanye yake cikin wani had'ad'en suit Wando da Riga black sai long selve pinky daga cikin rigar hannunsa daure da agogon fata baki ,yayinda gashin kanshi ke kwance luf luf tmkr ta jinjuri.. Kamshin turarensa daya kai wa hancinta ziyara yasa tayi saurin d'agowa a matukar firgice idanunta ya sauka akansa take gabanta yayi wani irin fad'uwa t "fu'ad ta furta jikinta a matukar sanyaye while zuciyarta na wani irin harbawa da sauri sauri ta tsura masa idanunta yayi bala'in canza mata . ahankali ya fara taku zuwa inda take , tare da tsura mata kyawawan idanunsa masu shegen kyau da rikitarwa, tana can kallonsa ya kamo fuskatarta da hannunwasa duka cikin sarkewar murya yace "oh my goodness god I really missed you so much love sannan ya mikar daita tsaye ya kamo hannuta ya zagayo daita zuwa Kan doguwar kujera me zaman mutun uku ya zauna had'e da zaunar daita akan cinyarsa, yasanya hannunsa daya ya d'ago ha'barta ya Sanya kwayar idanunsa cikin kwayar idanunta ,wani abu taga ya fito daga cikin idanunsa yashiga nata me kama da kibiyar so ..tayi saurin lumshe idanunta batare datace masa komai ba.. sai lokacin murmushi ya bayyana akan fuskasa "am here for you love na baro duk wasu mahiman aikina saboda nazo gareki domin muyi sharing farincikin abinda yasameni ayau, kasancewar nasan duk duniya you are the first person dazatayi murna wannan abinda daya sameni yakarasa mgnr yana kissing din lips dinta ,sannan ya ciro wata farar envelop acikin aljihun wandosa ya mika mata "amsa ki bud'e ki gani an yi min double promotion a wajen aiki tare da transfer zuwa cross river..... Da kyar ta tattaro natsuwa tasanyawa jikinta tace "Allah yasanya alkairi Amman karka kara tako kafafunka zuwa inda na......."shiiiiiiiiii ya fad'a yana zare karamin hijabin datake sanye dashi, cikin sauri ta turesa yayi baya kad'an zata mike ya fixgota ta fad'o saman fad'ad'den kirjinsa ,ya rungumeta tsam had'e da matseta ajikinsa yana kissing wuyanta ,tasoma mutsu mutsun turesa Amman yaki sakinta sai ma kissinh dinta hungrily daya cigaba da yayi,Tare da k'ok'arin had'e bakinsu guri daya , yayi yayi ta bud'e bakinta taki da kyar yasamu nasarar bud'e bakin tare cafko laulausar harshenta yasoma tsotsa yana rike da fuskarta da hannu biyu ,wani irin kissing dinta yakeyi tun tana iya jurewa har itama tasoma meida masa martini, suka shiga romancing din junansu cikin wani irin shauki ,fu'ad bai barta ba har sai dayasamu natsuwar dayake bukata daga gareta . Adaidai wannan lokacin kira yashigo wayarta. "Ture fu'ad din tayi kad'an ,ta janye jikinta tana sauke numfashi da ajiyar zuciya atare ,sannan tasoma k'ok'arin d'aukar wayar ..cak taji ya kamo tsintsiyar hannuta ya amshi wayar ya ajiye a gefensa yana kallonta yana busa mata iskar bakinsa Wanda ke sake dilmiyar daita tafkin kaunarsa. a natse ya kai yatsan hannunsa kan lips dinta yana wayo da yatsansa har zuwa saman kirjinta yana mgn "ki bud'e envelop din nan ki duba matsayin da mijinki ya taka acikin D'an kankanin lokaci, abinda mahaifinki yake da burin gani kenan, ya ganki cikin farinciki Wanda nasan wannan arziki bashi kike bukata ba sannan duk duniya babu wanda zai iya baki wannan farinciki byn Allah daya haliceki sai ni.." "me'ad yakira sunanta a raunane while bakinsa na daidai wuyanta yana aikin busa mata Iskar bakinsa Wanda ke kashe mata sansar jiki ,ahankali jikinta ya dinga sakewa yana narkewa tsigar jikinta suka mike tsaye yrrrrrr , zuciyarta ta ding beating da tarin kaunarsa "ban manta halaccinki gareni ba ,sannan ban kasance me manta alkairi ba ballanatana na manta naki, da kikayi min Wanda sadaukarwa ne gareni , Nasani kin yi hidima dani da rayuwata gabadaya ,kuma nagode da hkkn ya k'arasa mgnr yana mai mikewa tsaye tare daita ya manneta ajikinsa suna fuskatar juna ,wani irin d'auke numfashi yayi da sauri saboda kirjinta daya tokare nashi kirjin, ahankali numfashinsu ke tsarkewa da juna yana juyewa zuwa wani shauki na daban me zafafa damkon kauna da karfafafa soyayya. "me'ad ki kular min da kanki duk da kince kin daina sona Wanda ni nasan karya ne hkn bazai ta'ba kasancewa ba muddin ina raye ...... "Idan kuma hasashena bai zamanto gaske ba ,kiyi k'ok'arin ki dawo da soyayyata sabuwa fill acikin zuciyarki saboda babu kalmar rabuwa acikin tsarinmu kmr yadda kika sha Fada min abaya, Dan ko kin barni ni bazan barki ba sai dai mubi juna ...... yana gama fad'ar hk ya kamo fuskarta yayiwa lips dinta light kiss "bye take good care of yourself for me before na dawo a fafata ya juya yasoma tafiya yana taku kmr bai son taka kasa , tabi bayansa da wani irin kallo kirjinta na dukan uku uku har ya bar office din idanunta na Kan kofar ta kasa d'auke idanunta akan kofar daya fita. ahankali cike da matsanancin sanyi jiki ta k'arasa tayiwa kofar key ta dawo ta d'auki hijabinta ta saka sannan ta d'auki farar envelop din daya bar mata ta koma mazauninta ta zauna tana sauke ajiyar zuciya sannan ta bud'e envelop din inda ta ci karo da wata farar takadar tasoma dubawa a natse . gyara zamanta tayi sosai saboda abinda idanunta yagani fu'ad ne ya kusan taka matsayin MD na companies din dayake aiki tare da Karin albashi na dubu dari duhu da hamsi Akan 150k dayake amsa a watanin baya da suka gabata,sababbin motaci guda biyu da gida....runtse idanunta tayi hawaye suka gangaro bisa kuncinta ahankali ta furta "Allah kenan babu yadda bai iya da lamarinsa ba ,abinda suka dade suna jiran zuwansa, azahirin gsky tayi matukar farinciki ,duk da batare zasu ci wannan samuwar datazo masa ba wunin ranar kusan cikin farinciki da annashuwa tayisa ........ ************** Asabar din karshen wata march ,kofar gidan tshohun commissioned of police na Nigeria makil yake taf da dubban jama'a dake cikin garin lagos da wajenta , suka sheida d'aurin aurin khalid Ismail money mis road da sajida Aliyu a lagos state central mosque a kan Sadaki mafi kankanta..... Mmn sudais ce 💗💗💗💗💗💗 'YAN CINKI 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 ~NA~ *AYSHA A BAGUDO* ~DEDICATED TO~ *AUNTY BASEERA WANNAN PAJIN NAKI NE , INA MATUKAR GODIYA BISA GA SOYAYYARKI , ALKHAIRINKI,KULAWARKI GARENI ALLAH YA BARMU TARE*🤝🏻🤝🏻🤝🏻 Page 82 ........tana tsaka da bacci ,tayi wata irin zabura ta mike zaune akan gadonta tana zare idanuwa ,gumi na karyo mata ta koina a sansar jikinta tmkr ac dake cikin d'akin ya daina aiki . kirjinta ne yashiga mahaukacin bugu da karfin gaske, yayinda kunnuwanta ke sake jiyo mata abinda ya farkar daita daga baccinta,sautin muryar maroka tacigaba da jiyowa suna tashi ta koina ,a kofar gidansu maroka ke yin kirarin Amman ji take timkr acikin d'akinta sukeyi ,tayi wata irin zabura ta mike tare da hantsilowa daga saman gadon jikinta na wani irin kyarma...... ta fito daga ita sai rigar bacci iya cinyarta . tana k'arasowa parlour'n nan tashin hankalinta ya karu sakamakon fuskokin mutanen daban daban tagani makil acikin parlour'n suna cike da matsanancin farinciki, wanda hkn yasa tayi tsaye turus tana binsu da wani irin kallon mamaki yayinda hankalinta ke k'ara tashi ,sakamakon yadda marokan ke maimata kirari Tare da ambato sunansa Dana mahaifinsa da kakanninsa "yeeeeee kuwa jama'a ku sheida an d'aura auren sajida Aliyu da khalid money mis road jikan sani gilo... Allah ya sanyawa aurensu albarka ,"hakika khalid kashigo gidan girma tare da sa'ar mallakar 'yar gata shalele agurin mahaifinta , hjy sajida ikon Allah yarinya irin arziki wacce ta taso cikin arziki ,hjy sajida kiyi min arziki ki sha min arziki ,arziki nke so daga gareki ,ina son kujera hajjin bana da sabuwar mota yar yayi , take dady yace an bashi ,"khalid kaima irin arziki ne wanda ya gada tun daga kan ka kannin kakaninsa, ka nuna halin girma khalid banda makodo domin gadon gidanku ......ai kuwa aka kashe dariya. "shin gaskiya ne abinda kunnuwanta suke jiyo mata daga bakin maroka nan ko kuwa har lokacin mafarki take yi? Tayiwa kanta tambayar tana mai kai hannunta ta muntsini gefen kuncinta taji ko mafarki take ko kuwa a zahiri ne abinda ke faruwa an d'aura aurenta da Khalid .. ..... jin zafin da taji ne yasa ta fahimci a zahirance ne ba mafarki ba ,take jikinta ya d'auki kar karwa ....... wata daga cikin makociyar ce tayi bud'a " eyyyyyirrrrrr "ga amarya nan ta fito ,nan hankalin mutane gabadaya sukayo kanta kowa ka kalli fuskarsa agurin cike take da tsantsar farinciki da annashuwa. cikin haka sai ga aunty nadiya ta fito daga cikin d'akinta rike da Wasu kaya zumar zuwa ta tasheta a bacci tasanyata tayi wanka tasa batare dasanin komai ba . da sauri sajida tak'aro gareta "aunty yaushe duka wannan abun ya faru batare da sanina ba... ? "Wai ma auren wa aka d'aura yanzu ? aunty nadiya takamo hannunta cikin nata tace "ki natsu sajida ki dawo cikin natsuwarki mu ... .. Tayi saurin katse aunty nadiya ta hanyar cewa "bazan ta'ba dawowa cikin natsuwata ba har sai naji zahirin gsky abinda ya faru plz auntu ki gaya min auren wa aka d'aura ? "saboda 'kwa'kwaluwata tashiga rudu da gigita akan abinda kunnuwana suke jiyo min daga waje . Aunty nadiya ta kamo hannuta cikin nata "muje d'akinki muyi magana . fixge hannunta tayi da karfi daga cikin na aunty nadiya jikinta na rawa, hawaye na bin kuncinta "duk abinda zaki gaya min ki gaya min shi anan ,anan nake son jin komai tak'arasa mgnr tana durkushewa kasa bisa gwiwowinta ,itama aunty nadiya kasa tayi kmr yadda sajida tayi had'e da raunata muryarta Dan kar mutane su fahimci yadda auren yakasance "kukan ya isa hk sajida ,aurenki da Khalid aka d'aura yanzu.. wata irin gigita tayi daga tsugunnen datake tare da d'aura duka hannuwanta bisa kanta" shikenan abinda take tantama gaske ne ya ta faru takare ... take jinta da ganinta ya d'auke na wuncin gadi tashiga kallon jama'ar dake tsaye akanta suna mamakin abinda ke faruwa... cikin HK tawagar angwane suka sanyo kai cikin gidan bisa al'adar jahar Lagos ,byn d'aurin aure ,ango zashigo tare da abokansa domin gaida dagin amaryasa, sannan suyi hoto da amarya,suna shigowa parlour'n idanunsa ya sauka akan durkushe tana kuka, Sam khalida bai yi tsamanin ganinta hk ba, saboda a tunaninsa ya d'auka zata hauka yi fiyye da hkn. aunty nadiya najin shigowarsu ta mike tsaye ta koma gefe guda cike da jimami, shi kuwa khalid da sauri ya k'arasa inda take zaune tana zare idanuwa ya tsuguna agabanta tare da baza babbar rigasa ya rufeta dashi dan kar abokansa su karewa yanayinta kallo, yanayin da shi kad'ai ya cancaci ganinsa.. idanunsa ya tsura mata yana kallon yadda hawaye ke bin kuncinta gabadaya ta gigice ta fita haiyacinta, kallo dayan dayayi mata ya gane kalar tashin hankali datake ciki, matsota yayi sosai kmr zai shige cikin jikinta muryarsa a kasalance yakira sunanta"sajida tashi ki koma d'aki, ki suturta min jikinki ,ki daina mamaki da hukunci Allah, kinga yadda alamarin ubangiji yake ko? nayi magana da harshen malaiku Allah ya amsa .... tayi masa shiru kasancewa bata cikin hankalinta ,Dan kwata kwata bata San abinda yake fad'a ba ,maganar duniya yayi mata Amman ko gezo batayi ba agurin, ta dawo tamkar mutun mutumi yayinda abokansa suka shiga tsokanarsa ... bai juyo ya sauraresu ba yacigaba dayi mata mgn ,kusan minti goma ya lura da tasoma dawowa cikin haiyacinta, Dan haka yasanya duka karfinsa ya cici'beta ya rungumeta bisa kafad'arsa Wanda take parlour'n ya haigitse da ihun jama'a..aunty nadiya kanta sai dataji kunya ta kamata "aunty nadiya ina ne d'akinta ? Inji cewar Khalid Da sauri tayi gaba shi kuma ya biyota abaya hannuwansa duka rungume daita .. bud'e yaga d'akin da aunty nadiya ta nuna masa sannan ta juya byn ta mika masa ledar hannunta Wanda kayan sajida ne aciki ,agefen gadonta ya ajiyeta yaje ya kulle kofar ya dawo ya tsaya a tsakiyar d'akin yana karewa d'akin kallo . d'akin neat ,koina kamshin turarenta yake fitarwa ,ya Jima tsaye yana kallon d'akin da take rayuwa aciki Wanda ya nika NASA sau dubu ........ ahankali yasoma taku zuwa inda take zaune tana tsiyayar hawaye gabadaya tashin hankali datake ciki bai barta ta iya furta daidai da kalma daya ba ,kuka take sosai tmkr karamar yarinya, ta kasa goge hawayenta, gabadaya komai ya cakud'emata daga wannan sai wannan ajiye zuciya ta sauke bata jin jure wannan auren shima, domin wannan auren daidai yake da nisantata da fu'ad dinta "why why why !!! Dady why did you do this to me gabadaya duniya tasoma mata dumi ,jikinta yayi mugun sanyi ga matso idanunta hawaye masu zafi suka sulalo bisa kuncinta. hannunsa ya kai ya janyo karama kujerar stood gabanta ya zauna yana fuskantarta hk gwiwowinsu manne da juna, had'e da lalubo tafukan hannuwanta ya rike gam cikin nasa yana murzawa ahankali,abinda yasa kenan tayi saurin d'ago idanunta tana kallonsa, ganin tana kallonsa wani iri yasa ya marairaice murya had'e da karyar da kai ya koma abun tausayi agabanta sannan yace "haba sajida... wani irin damuwa kike son haifawa kanki hk ? "Kalli yadda zuciyarki take bugawa da mugun karfi akan aurenki da Khalid......." Dan girman Allah ki natsu ni kaina bayina bane, haka zalika ba shirina bane ,komai ya faru ne da izinin Allah, Dan hk ki daina damuwa ,kinsa tun ba yau ba banason ganinki cikin damuwa ,sannan duk duniya babu abinda na tsana irin damuwarki ,banason kina yawon damuwa most especial akaina ,"yanzu fad'a min meye matsalarki ? D'auke kanta tayi tare da yatsina fuska Wanda HKN ya rigada ya zame mata jiki Dan koda yaushe ba'a rabata da yatsina fuska idan dai tana kallon mutun to hk zata dinga yatsina kmr tana kallon kashi ,ballanatana wannan yatsinawar ta dabance me d'auke da tarin ma'anoni dayawa ce. dayan hannunsa yasanya ya juyo da fuskarta , inda yashiga nacin tayi masa mgn ko hankalinsa zai kwanta Amman taki sai hawaye kawai take zubarwa tana ihun ya cuceta tare da tsine masa acikin zuciyarta . "Tashi muje kiyi wanka yasoma k'ok'arin rabata da kayan jikinta Wanda hkn yayi nasarar ta'bo nonuwanta, nan fa ta fixge jikinta tare da mikewa tsaye tana haki tana auna masa wani irin wulakantaccen kallo . A matukar zafafe tace "out of this room kafin zuciyata tagama dugunzuma akanka .... "Aikin banza ,karamin yaro da kai ,sai shegen iyayin tsiya da naci" nace bana sonka banasonka dole ne wallahi sai kay dakasani aurna arayuwarka ta k'arasa mgnr tana juya masa baya inda hakan yabashi damar karewa yan madaidaitan bombom dinta kallo sannan ya kwashe da wata uwar dariya "danasani danasani !! ko me naji kince? "Uhmmmmm abinda baki sani ba , kece zakiyi da kinsani ba Khalid daya rufa miki asiri ba ,Amman har abada Khalid bazai yi dayasani ba ,saboda sunanh ya habbaka ba zina ba .. "Na d'auka abun naki zai zo da sauki shiyasa kikaga inata lalla'baki Amman tunda wulakanci ne abun muzuba, " nima nan da kika gani tatacce ne wanda zai iya yin fiyye da abinda zaki yi ,sannan ita zuciyarta taki k'arewar dugunzuma tayi bindiga ta fashe Bob....... sannan wannan yaron da kike rainawa zai shayar dake mamaki ,zakiyi nadamar had'uwarki dashi arayuwarki, sai kin zubda hawayenki Akan wannan yaron ya nuna kirjinsa dayatsansa ,abu na karshe da zan gaya miki shine ki shirya anjima akwai zuwa dinner.. "da wa zaka wani banzan dinner ni ko wa ? " are you sick or what? "dake zamu je dinne , kuma ki tabbatar da kin shirya kafin lokacin, idan ba haka ba kiga aikin yarinta "to sannu ubna aliyu .. kuma wallahi bazan aje Koin ba, kai kayi kad'an din da zanjewa dinne aikin banza kawai . Ji kake tassssssss ya dauketa da wani gigitaccen Marin dayasa ta d'auke wuta tana zaro idanunta dake cike da ruwan hawaye .. "dan girma Allah karki shirya har sanda zanzo sannan ya juya ya bar d'akin cike da matsanancin takaicinta . cike da tashin hankali ta fad'a Kan gadonta tana wani irin kuka "mari ...marina fa wannan D'an iskan yaron yayi batare da na iya daukar wani mataki akai ba ? "Wayyohlly Allah meke shirin faruwa dani ne ,na baro gidan emran da zummar cika burina Akan fu'ad, gashi ban samesa ba na bige da auren yaro ..... bayan d'aurin auri ango ya zarce da walima a gidan saukar bakin mahaifinsa dake ebutte meta road. aunty nadiya nata fama da jama'a, kawayenta yan'uwan ta, Dana 'yancin arxiki, mak'ota da abokan arxiki dan ko ta ina acikin gidan jama'a ne makil gbdy hidima ta sha kanta, gidan cike yake taf Ba masaka tsinke musamman lokacin da dangin mahaifiyar sajida suka zo daga Minna Cikinsu akwai ya'yan wan mahaifiyarta da suke uwa daya uba daya , Aysha da jidda wanda suka kasance sa'anni Sajid ne, sannan akwai wasu daga cikin kawayenta misnah mincy hajaracy wanda labarin auren yasame bagatatan duk sunzo duk da ba sajida ce tagayacesu Ba .. kanwar mahaifinta ce tashigo d'akin ta isketa kwance tana kuka ,tashiga ta kurata Akan lallai sai ta tashi tayi wanka amman juyin duniya Sajida tace bazatayi wani wanka ba ,balle wata kwaliyar banza akan auren yaro karami sa'an Dan cikinta har dare tana kwance taki motsawa duk wanda yayi mata mgn bata sauraransa , Kuka kawai take , sallah ce kawai ke tada ita . karfe takwas daidai motocin dibar jama'a domin zuwa wajen dinne ta iso , nan ma bakaramin tashin hankali akayi Ba domin tace babu inda zata, Yayinda Khalid yana waje tare da abokansa , Aysha ta fito ta sheida khalid cewar sunyi iya yinsu amman amarya tace bazataje koina ba . Ango khalid dake zaune cikin motar sanye cikin wani lallausar yadi mai sharara fari sol har kana iya hango farar singlet dinsa da manyan damtsensa masu nuna alamun karfi da cikakkiyar lafiya da mazantakansa na matashin saurayi me jini ajika. kallon yadi kadai ya isa ya shedawa mutun ki manta tsadarsa, ahankali ya d'ago tsumammun idanunsa byn yagama suraron bayanin aysha yace "yanzu tana ina ? tace "tana d'akinta yace "aunty nadiya fa? "tana cikin mutane hidima tayi mata yawa ahankali ,"dady na ciki ne ? "Yana Amman yana shashinsa gama jin hk keda wuya ya yunkura ya fito daga cikin motar adaidai lokacin da kiran kanwarsa khadija yashigo wayarsa ya ciro wayar daga aljihun gaban rigarsa ya manna a kunne "ya akayi khadija ? "yaya ku kad'ai fa ake jira jama'a sun cika kowa ya kosa " "kuyi hkr gamu nan zuwa , da sarsarfa ya taka matattakalar binen da zai kai mutun d'akinta kai tsaye. tana zaune abakin gado sai faman cika take tana batsewa tkmr wata macijjya Sabod rigimar da'ake ta faman tafkawa daita akan lallai sai ta tashi ta shirya Khalid yasanyo Kai yashigo cikin d'akin ko sallama babu ba ita ba hatta jamar dake fama daita sun yi matukar razana da ganin wannan zakin mazan ma'aboci Haiba da kamala sai dai kallo daya zaka masa ka tabbatar da kuruciyarsa a fili wato bazai wuce 26 yrs da haihuwa ba, Suna ganinsa Suka soma k'ok'arin barin d'akin ... d'akin ya saura daga ita sai shi bai yi mgn ba illa Idanuwansa daya tsura mata yana kare mata kallo tun kayan daya barta dasu ne ajikinta, yayinda ita ko kallon inda yake tsaye bata ba illa jijiga kafarta daya da take ta faman aikin yi . ahankali murysrsa ta fito "malama ki tashi kije kiyi wanka " A matukar fusace ta d'ago had'e da cewa "idan ba'ayi ba.. ? "nace bazani ba ko dole ne? "duk wani abu agurunki zai iya zama ba dole ba ,amman zuwanki wannan dinne din yana da matukar mahimmanci arayuwata, saboda wannan shine al'amari na farinciki gareni , ya kai hannunsa ya shafi gefen fuakarsa "wai meyasa ma zan damu kaina akan dole sai naje dinne da shohuwa iriki ? ya tmby kansa yana tsareta da idanunsa tare da takowa zuwa inda take . sauri zaro idanunta waje tare da dafe daidai saitin zuciyarta datake jin yana daf da tsayawa ,while idanunta na kan dubansa a matukar firgice. "nice tsohuwar ta fad'i hk cikin murya mai rawa ala'mun tana son yi masa rashin mutunci? "uhmmmmm da ke mecece ba tsohuwa ba ? "Dan Allah malama ki tashi kije kiyi wanka ki shirya minti goma kacal na baki idan kuma kikayi kuskuren k'ara ko second biyu ne akai , wallahi wallahi sai dai ki iske kanki abayi ina miki wanka da kaina "what ? ta furta tana yatsina fuska had'e da masa kallon ta'b'ba'be mara hankali. Yayi mugun tsareta da idanunsa "ko kina da ja ne acikin abinda nace ? hk kawai ta tsinci zuciyarta kasa amsa masa sannan wani bala'in shakar maganarsa tashigeta ,dan a yadda take ganin takusan zai iya yin fiyye da abinda yace zai yi barin ma lokacin data Tina marin safe ai batasan lokacin da tashi tsam tashiga bayin ta barshi zaune zaman jira fitowarsa . Dialling number aysha daya kar'ba yayi ,kira daya biyu ta d'auka yace "ta turo masa me make up sannsn ya katse kiran ya nufi barandar d'akinta "Yasan ko ita wacece , amman bai San me yasa yaji sonta acikin zuciyarsa ba.. sai dai zai yi kokari dankwafar da shi wannan son dayake mata domin yasamu damar ajiyeta a mazaunin dayafi bukatar takasance . Bata wani lokaci ba ta fito inda ta iske mai make up zaune zaman jiranta dogon tsaki taja tare da kokarin sanya kaya ,sannan ta zauna duk ranta a dagule ,an tsara mata make up na garari wanda ya canzata zuwa matashiyar yarinya, tayi wani irin masefaffen kyau, sai kamshi jikinta ke fitarwa har aka gama tana zaune batare da tayi yunkurin mikewa domin halarta zuwa gurin dinne ba ,yatsina fuska tayi had'e da cewa mai make up "Kinga dan Allah kina tafiyarki zan kule d'akina dan babu dan iskan dinne da zanje..... yarinyar tace to tasoma hanzarta tattara kayayyakinta tasanya ka ta fice... ta mike kenan da niyyar kulle dakin batasan yana tsaye a barandar d'akin Yana fuskartata ba . bai tsaya wata ba yasoma takowa inda take ya cire links din hannunsa Ya nad'e hannun rigarsa ya sunkuya ya sunkuceta yayi sama daita wanda hkn yayi sanadiyar da d'ankwalinta ya cire ya fad'i ya nufo hanyar parlour'n kasa daita a parlour'n kasa ya iske yan'uwanta da kawayenta suna zaman jira , aiko suna ganinsu sukace me zasuyi ba dariya Ba ,take kowace daga cikinsu ta ciro wayarta tana d'aukarsu hoto tare da mamakin wai wannan wani irin ango ne mara kunya ? aysha tace "ba takalmi da dan kwali akanta zbatare da tsayawa 'bata lokaci ba yace " kibiyota dashi ai khalid bai direta sajida akoina Ba sai cikin mota abokan ango in banda dry babu abinda suke suna jinjinawa kunjinsa, aysha da me make up suka karaso gurin atare tasanya mata takalmanta akafafunta sannan aka sake d'aura mata d'an kwali , ana tada motar ta fashe da wani irin kuka "yanzu banda lalacewa a kalleta ace wanna abun ne mijinta wallahi har gara emran da auren Khalid arayurwa wallahi ba karamin abun kunya dady yaja mata ba . Kuka take sosai shi kuwa ko ajikinsa ,guri daya hankalinsa yayi mugu mugun tashi yadda ta dinga Surfa masa zagi iri iri ,bai tan kata ba illa daidaita hannunsa da yayi ya bata gwab abakinta, ai da sauri tayi shiru "wallahi kisa sake wata mgn anan zakiga aiki da cikawa Dan HK kinsa irin mgnr da zaki dinga gaya min, ni ba sakarai bane shasha lusari irin wancan,Shanshan tsohon mijin naki yana gama fad'ar hk yayi shru yana jiran ta sake cewa wani abu har suka isa 3 star dake ikeja Awolowo way bata sake cewa kala ba sai kuka take .. daidai inda zasu zauna direban yayi parking abokai da yanuwa suka nu fosu domin tararsu ,khalid ya sai walkiya suke acikin hasken fitilu daya haskaka gurin ya fito ya zagayo daidai inda take tare da rusunawa kmr zai shige jikinta "to yaya akayi tsohuwar amaryar khalid zaki fito ne ko na sake nad'e hanun rigata? ai ba shiri ta fito zuciyarta na wani dukan uku uku gabadaya Tasom tsorata da yanayinsa sai nuna mata tashen balagar tsuntsaye yake ..... dariya sosai tabashi ganin yadda hanzarta fitowa ya kamo hannuta cikin NASA ita kuwa ji tayi kmr ta d'aura hannuwanta duka bisa kanta ta rutsa kuka dan bakinciki, shi kuwa sai murmushi yaje ya matso kusa daita sosai "kina ji ko tsohuwar amarya ki saki jikinki da ranki if possible ma kiyi murmushi kmr yadda nima nake yi ko kuma yanzu nayi miki abinda, zai tabbatar miki da kuruciyata a fili. wayyohhly Allah ta furta tare da kirkiro murmushin dole wanda yaja hankalin masu d'aukar hoto da video kansu ya kai hannunsa yana gyara mata zaman sarkar wuyanta da Goggoronta ,aiko take tashiga zabga masa wata katuwar harara ,batasan sanda bakinta ya subuce ba tace aikin banza kawai duk abinda mutun zaiyi dai ba zai taba burgeni ba, tunda bashi zuciyata take so ba, wata irin damka yayi tsintsiyar hannunta taji tmkr jijiyo hannunta zasu tsinke Dan azaba , yayinda har lokacin masu d'aukar video da masu d'aukar hoto nayi aikinsu , hka zalika jamar dake gurun nayi Da wayoyinsu har sai da suka isa mazauninsu sannan ya saki hannuta, tayi saurin sauke naunauyen ajiyar zuciya tana shafa tsintsiyar hannunta tare da tsine masa.. aranta take mamakin karfinsa.. bayan sun zauna aka soma bud'e taro da addua sannan aka shiga program ... Mmn sudais ce 💗💗💗💗💗💗 'YAN CINKI 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 ~NA~ *AYSHA A BAGUDO* ~DEDICATED TO~ *AUNTY BASEERA WANNAN PAJIN NAKI NE , INA MATUKAR GODIYA BISA GA SOYAYYARKI , ALKHAIRINKI,KULAWARKI GARENI ALLAH YA BARMU TARE*🤝🏻🤝🏻🤝🏻 Page 83 ........d'aya daga cikin abokan ango ne ke tsaye bisa kafafunsa rike da abun magana ,yasoma karanto tahirin khalid da makarantar da yayi ,har zuwa kan matakin da yake yanzu, inda yake bayyana kwalayensa da matsayin na mataimakin sajida . yace "khalid uwar d'akinsa ya aura saboda kankaba da tsaurin ido irin nasa gashin nan sai yanga da yauki ake masa ....... dariya gabadaya hall din ya d'auka tare tafa masa hannu hamza yacigaba da magana kmr hk "sai dai mu agurinmu musan mace bata fi karfin namiji ba, matukar namijin ya amsa sunansa nmj,da kuma yadda namijin yasan kansa dan haka ta wannan fannin zan iya cewa abokina bayi tsaurin ido had'e da kankaba ba ...... aka sake kwashewa dariya "Allah yasanyawa rayuwar aurensu albarka yadda muka taru anan Allah ya hadamu mun zo suna haka . mc ya amshi abun magana yana dry " ameen sai dai kuma gasky wannan abokin naka baiyi kankaba saboda kowa da irin ra'ayinsa .. Ita kuwa sajida tun da ta zauna Kan kujerar da ta ke mallakinta amatsayinta na amarya, hankalinta yasoma barin gangar jikinta, gabadaya tunaninta ya azzara ne akan burin zuciyarta," wannan karon ma irin zaman rayuwar datayi da emran zatayi da khalid kenan, tayiwa kanta mgnr zuciyarta na kokawa .... Dan a yanzu har tasoma hasasho yanayin zaman nasu , Dan sam bata ji zuciyarta zata amince ta hakura ta amsa rayuwa dashi amatsayin miji gareta . a halin yanzu hankalinta a matukar tashe yake tana sake mamakin yadda khalid ya makalewa aurenta dole, yayinda ga en mata nan birjik a gari da suka fita komai ,"ayanzu datasani take da bata zauna ta hakura da auren emran ba, ga kuma abinda karshenta ya dawo ta bige da auren jinjiri "wace irin rayuwa ce hk ? "wace irin kaddarar ce haka ta giftawa rayuwarta? gabadaya komai ya rigada ya cakud'ewa mata tarasa nemowa kanta mafuta "yanzu ya zatayi da rayuwarta? sosai tayi zurfi cikin tunani Dan kwata kwata ita zantuttukan hamza abokinsa baa shi ga kunnunwata ,hankalinta da tunaninta suna can ga fu'ad dinta ,tana jin ina ma wannan ranar ta kasance ranar aurensu ce da fu'ad dinta sanyin idanunta, hasken zuciyarta, lizamin rayuwarta ,bugun zuciyarta... "ina ma mafarki take, ba'a gaske bane duk abinda ke faruwa daita? har sanda khalid ya lalu'bo tafin hannuta cikin nasa fuskarsa cike da matsanancin farinciki batasani ba ,Yayinda ta koina acikin hall din murya mc ne ya karad'e gurin ,inda yace "ana son ganin ango da amarya a flow, waigowa Khalid yayi ahankali yana dubanta fuskarsa na sake fad'ad'a farincikinsa. Amman ganin yanayinta al'amun tashiga duniyar tunanin yasa take murmushin dake fuskarsa d'aukewa cak zuwa wani malolon bakinciki da tarin damuwa, ransa yasoma 'baci zuciyarsa tashiga rawa rawa Dan ko ba'a gaya masa ba yasan wani tunani take yi daban wanda ba nashi bane . "shi kuma wulakancin da bazai ta'ba lamunta dashi ba kenan yana zaune ana tunanin waninsa ,ransa a matukar 'bace ya kai bakinsa daidai saitin kunneta had'e da tausasa muryarsa tmkr bai so yin mgnr yace "ke tsohuwar kawai kiyi maza ki dawo cikin haiyacinki da natsuwarki ana bukatar ganinmu yanxu Dan kin wani shantake atunanin iska .... tunanin abinda bazai ta'ba fissheki ba ..... yana gama fad'ar hk ya mike tsaye tare daita yana kirkiro fara'r dole zuciyarsa a dagule, alokacin shi kad'ai yasan tashin hankali da zuciyarsa take ciki .. Ahankali yake rike da hannunta yana tafiya ,ita kuma tana biye dashi abaya masu d'aukar hoto da masu d'aukar video suka matso kusa dasu sosai suka shiga aikinsu ,na d'aukarsu har sanda suka sauko daga mazauninsu zuwa tsakiyar hall ,inda mutane suka sake rud'ewa gurin d'aukarsu hoto, sauti na musamman aka sakar musu Amman sajida tayi tsaye ta kasa motsa koda D'an yatsanta ne ,ganinta sam bata ga wani abun rawa ba...... Idan ma rawa zatayi ta rasa Wanda zata tsaya yi rawa dashi sai Khalid ..? "Ina wannan abun kunyar ba da ita za'a yi ba ,ganinsa take agabanta tmkr mazuru ne agaban zaki .... Duk da ransa a matukar 'bace yake ,Amman ya d'aure yayi k'ok'arin sanyawa zuciyarsa da gangar jikinsa jarumta ya kai hannusa daya ya kamo hannunta, while dayan hannunsa na kan west dinta ya matsota ya manneta ajikinsa yana jujjuyawa daita ahankali ahankali . ai take hall din ya d'auki ihu mutane suka dinga fitowa daya bayan daya, Suna lika musu kudi , tsawon minti 30 sukayi a flow suna rawa ko nace Khalid yake rawa sannan suka koma mazauninsu still hannunsu na sarkefe da juna .... Bayan sun zauna aka soma ciye ciye da shaye shaye, yan'uwansa suka dinga shiga rawa suna cashewa son ransu, can mc ya sake neman amarya da ango inda yake cewa "uwar ango da kanta zata nuna bajintarta ..haka ba Dan ran sajida yaso ba suka sake fitowa, sai dai abinda ya d'aga mata hankali da bata mamaki bai wuce yadda taga mahaifiyar khalid din taki kallon inda take amatsayinta na matar d'anta ,d'anta kawai ta fuskanta tana zuba masa ruwan kudi shima yaciro rafar yan dari biyar biyar yashiga lika mata , suka ware amarya gefe tmkr basu san Allah yayi halittata agurin ba. nan fa yan'uwa da abokin arziki suka fito suka dinga yi musu liki wasu daga cikinsu ,su likawa sajida wasu kuwa kiri kiri suka ki, sai mahaifiyarsa hjy zainab da Khalid kawai suke ta fama yiwa liki . anci an sha an gwangwaje, yayinda ango ya dinga hawa da sauka da amaryarsa, iya hakurin sajida ya k'are inda tace "wallahi ba zata sake tashi fita koina ba , daginsa nayi mata kallon wulakanci da gani gani, daman kasan abinda ka shiryawa zuwa na kenan Dan a wulakantani yasa ka matsa sai nazo? yadda sukewa auren namu rashin dacewarsa haka zalika abun yake agurina ,wallahi wallahi tunda ka zabi zama dani ka tsiyowa kanka wulakanci da bakinciki tattare da babban tashin hankali har sai ranar daka sakeni dan bazan ta'ba iya zama da kai amatsayin miji ba ..... jin bai ce mata komai ba ya sake bata damar cigaba da maganarta "dan Allah ka kalleni ka kalli kanka nayi maka kama da kalar matar aurenka ban da tsaurin ido irin haka? "me zanji a aurenka? "me zaka iya min? "aikin banza kawai daza'a kawo mutun tsakiyar dangi ana masa kallon tozarci ,da wulakanci bama za bar mutun da abinda yake ji ba da tarin gajiya, dan girman Allah mutun ya sake kankabar riko hannuna da zumar tashi zuwa wani guri ta k'arasa mgnr tana juyar da kanta gefe had'e da jan tsaki.. . yayi tmkr bai jita ba, yana sake kirkiro murmushin karfin hali duk da azahiri gaskiya maganganunta suna shiga cikin kunnuwansa had'e da kai wa kwalkwaluwarsa farmaki daki daki yake nazarin magnganunta ,ganin sai faman mita ta keyi tana maimata kalmar bazata sake tashi ba, yasa shi cewa "duk ki gama rantse rantseki na banza sai dai banso hkn ya faru ba, Amman sai kin tashi, matsawar aka kiranmu. " zance gajiya kuma kirki damu kina da d'an shila a hannunki wanda zai iya d'auke miki duk tarin gajiyarki. taja gutun tsaki aciki ranta taki cewa komai ,Dan kar ya nemi rainata cikin bayyanar nasi . sai faman cika take tana batsewa azahirin gsky rashin kallon arzikin da mahaifiyarsa da wasu daga cikin daginsa da suka yi ta mata ,ya dameta matukar sannan yayi mugun tsaya mata arai .. Hall ya hargitse da hayaniyar jama'a inda ta nemi ango tarasa yashige cikin jamarsa .. gashi duk rabin mutane sun fara wuce wa, ai ko ranta ya sake dagulewa da kyar take janyo numfashi tana fitarwa tsabar bakinciki batayi auni ba sai gani tayi hall din yana neman watsewa sai ita kad'ai zaune akan kujerar tsiya da zuciyarta tayiwa suna da hkn ,da wasu tsirarun mutane , tun ranta na 'baci yazo ya daina, sai dai hankalinta a matukar tashe yake cike da matsanancin tsoro da faduwar gaba . tayi tsuru zaune tana mamakin ikon Allah tattare da zallar wulakancinsa gareta ..can sai gashi cikin sauri ya dawo yana cewa "tsohuwar amaryata tashi muje, ko yanzu ma kina son na d'aukeki ne? Tsam ta mike tsaye tayi gaba tare da yin kasa can da muryarta tace "uwarka ce karewa tsohuwa dan rainin sense kawai . Da wani irin kallo yabi bayanta dashi mai tattare da ma'anoni dayawa wanda yasa Jikin sajida a sanyaye tashiga motar zuciyarta na wani irin bugawa da karfin gaske, tafiya kadan yayi yasamu guri gefen titi yayi parking ya kashe motar hannunsa ya kai ya kara volume din music yacigaba da bin wakar ,duk iskancita ya shiryawa hakan, kuma zai yi maganinta da izinin Allah tsawon minti goma suna tsaye haka , gashi dare na sake karatowa yasa tace "kai malam tsayuwar me mukeyi anan ? "kai ...ka mai dani gida dan ban saba tsayuwa a irin wuraren nan ba,dan nasan tsabar tsagwaron wulakanta bawa ne da rashin sanin ciwon na gaba da kai yasa ka wani zo ka shanya mutane anan tayi mgnr tare da manta waye khalid din da kuma abinda mgnr tata zai iya haifarwa ,ai kuwa ko rufe bakinta bata gama yi ba taji saukar mari biyu hagu da dama . A firgice ta zaro idanunta waje tayi tare da saurin dafe kuncinta tana fuskantarsa a matukar firgice, wannan shine karonsa na farko da hannunsa ya sauka akan kuncinta "ka mareni? shima yayi mugun kafeta da manya idanunsa yace "ko zaki rama ne tare da janyota zuwa jikinsa ya rungumeta tsam ,yasoma shashfa sansar jikinta dake kyarma ,so yake gaya mata tayi hakuri saboda shi kansa ba'a son ransa ya aikata hkn ba, amman ya kasa furta komai dan bazai iya bata hakurin ba ta sake rainashi. "kina jina ko ina bukatar ki tattara gbdy hankalinki da natsuwarki gareni ,bazan tillastaki ba haka zalika banza takuraki ba gurin kwatar da hanlinki gareni,tabbas ni yaro ne sai dai ba irin wanda kike tunani ba, muryarta cike da sheshekar kuka zata bud'e bakinta kenan yayi saurin d'aura bakinsa kan nata "shiiiiiiiiii banason jin komai daga bakinki ya zarce da lasar lips dinta tayi k'ok'arin kawar da fuskarta ,Amman yaki yarda yayi nasar caf laulausar harshenta jikinsa har rawa yake ya manneta gam ajikinsa ,yana wa bakinta wani irin tsotsa na fitar hankali akan titi ,sai daya sha bakinta son ransa sannan ya sakar mata bakin yana fidda numfashi sama sama ta tattaro miyon bakinta zata tofa masa a fuska ,ko me ta tuno ta fasa ta guntse miyon . Murmushin takaici yayi sannan yace "yakamata zuwa yanzu ki bambance matsayin da kika bani sannan ki san irin mijin da kika aura yana gama fad'ar hk yace "ki hadeye miyon nan kafin na miki mai gabadaya kana ya tada motar aguje ya bar gurin, ita kuwa bakinciki abinda yayi mata bai sa tayi mgn, sannan bata jin duk abinda zai yi mata ,ba zai ta'ba kaiwa fu'ad ba, kallon fu'ad kawai idan tayi yanayinta na sauyawa. idan kuma jikinsu ya had'u guri daya ,zallar shaukinsa kawai ke gamsar daita ba irin wannan salon da d'an iskan yaron nan me tashen balagar tsuntsaye yake mata ba ta kasa had'e yawun ta dukar da kanta bisa cinyoyinta hawaye na gangaro mata . sun hau titi sosai khalid yace "better dan yin shirun zai fiyyewa mutun amfani amman idan ba tsoro ba tsohuwa ta sake bud'ewa mutane baki ta yi wata mgn anan ko ta maimata abinda tace, bata kula shi ba dan ta lura so yake yaga yayi silar rabata da rayuwarta batare da burinta ya cika ba. adaidai lokacin daya kusan bakin get din gidansu ya d'an waigo ya kalleta sannan yace "ko na d'an tsaya daga nan ne in dan rage miki zafi naga sai gumi kike fitarwa? batace masa komai ba taji yayi hon. masu gadi suka bud'e masa tangameman get din gidan ya shigo harabar gidan tun bai gama daidai tsayuwar motarsa ba ta fito ta nufi cikin gidan tana tsine masa. murnushi kawai yayi ya bar gidan yana kisma irin azabar da gallaza Mata idan tazo hannunsa . ************ Kwance fu'ad yake akan makeken gadonsa a cikin hotel din da company dinsu ta d'auki nauyi ,idanunsa a runtse,ba bacci yake ba , duk wani tunaninsa sun tattara sun koma ga matarsa ne da tilon diyarsa, sai bawar Allah najma da yake jin zuciyarsa ta kasa hakura akanta ,zuciyarsa da ruhinsa suna matukar bashi karfin gwiwar gurin taimaka mata ,ba Dan yana sonta ba sai Dan inganta rayuwata. tunanin duniya yayi akan lamarin taimakon rayuwarta ,Amman ya rasa takamaimai hanya daya da zai tsayar domin agazawa gareta baya ga aureta .... shiru yayi tare da lalu'bo bargo ya lullu'be jikinsa yana jin wani sauyi na daban ajikinsa agame da matarsa gabadaya bacci ma ya kasa ziyartarsa balle yayi nasarar d'aukarsa ahalin yanzu matarsa kawai yake bukata a kusa dashi yana jin tmkr yaje ya taho daita batare dasanin kowa ba ,yayinda wani bangaren na zuciyarsa ke k'ok'arin hanashi na aikata hkn ,jayayya da mahaifinta ba shine faida garesa ba illa hakuri, hakuri yakamata yabawa zuciyarsa akan surukin nasa ko babu komai akwai darajar me'ad da nasreen tsakani , lisafin kwanakin komawarsa gida yake gashi ayyuka gabadaya sunsashi gaba, Wanda duk silar tsanin arziki ne garesa Allah sarki innata ya furta yana kamkame jikinsa "ina ma kina raye inna kiga yadda rayuwar fu'ad dinki ta sauya? ya bud'e idanunsa yayi ahankali hawaye na zubo masa "kin sha wahalar rayuwa dani kin inganta rayuwata Amman gashi komai yana faruwa dani byn babu ke , na yarda da hukuncin ubangiji Allah ya jikanki yayi miki rahma yasa alhanna ce makomarki ya meida idanunsa ya runtse duk yadda yaso bacci ya d'aukesa abun ya tura joystick dinsa banda harba babu abinda take ,ahankali ya kai hannuwansa duka bisa joystick dinsa yana shafawa ahankali ahankali jikinsa na tsuma ya d'auki lokaci kafin bacci yayi nasarar d'aukarsa. Duk acikin kwanakin zuciyarsa makaleta take da son d'aura idanunsa akan me'ad, Tare da son jin muryarta Dan ko ya kira bata d'aukar wayarsa sai dai tabawa nasreen su sha hirarsu yayinda shi kuma yafi bukatar yaji sautin zazzakar muryarta cikin kunnuwansa suna masa kuwa...Allah Allah ya dingayi watanin biyu din daya dibawa kansa na komawa gida su cika ya tattara yaje ga matarsa, matar rufin asirinsa. ******** Friday karshen sati Wanda mafi asakarin ma'aikatan dake aiki a garuruwa daban daban suke k'ok'arin zuwa gida week end , suke saukowa daga matattakalar jirgi ,ciki har da fu'ad Wanda ke sanyi cikin laulausar farin yadi fari sol mai sharara Wanda hatta farin singlet dinsa ana hangowa ,farar fatar jikinsa sai sheki take zubawa agogon diamond ne d'aure da tsintsiyar hannunsa, sai kamshi turaren dio yake fita daga jikinsa, gashin kansa kwance luf sai zuba sheki yake kallo daya zaka masa kaji yashiga zuciyarka tare da Burgeka ,ahankali yake takowa har ya k'araso inda had'ad'd'iyar motarsa kirar toyata Camry ,ke tsaye zaman jiransa . kabir aminsa ne yazo d'aukarsa ,ya bud'e murfin motar yashiga ya zauna fuskarsa d'auke da wadataccen murmushi yana shiga motar gabadaya gamshin turarensa ya gauraye motar ya mikawa kabir hannu suka gaisa sannan kabir ya tada motar suna tafe suna hira cike da tsantsar farinciki "abokina kafa samu lafiya komai ya kasance mana yadda muke so. "kai dai bari kabir al'amarin ubangiji kenan ,a kullun ina sake godewa Allah bisa ni'imar da yayi min da kuma mai gidana sir Malik yayi min komai arayuwa shine tsanin komai na rayuwata ,"haka ne inji cewar kabeer "yanzu ina muka nufa sabon gidanka ko tsohon ? Murmushi fuad yayi sannan yace" ka kaini gidan rikitaccen surukina ina bukatar sanya mata acikin idanuna...... kabir yace "kai dai kace zakaje rage mara kawai Dan yanayi kad'ai ya isa ya tabbatar da hkn ya k'arasa mgnr yana dry tare da dukan sitiyarin mota . fu'ad yayi saurin had'e rai " banson wulakanci da rainin wayo fa ,to meye ruwanka idan ma rage marar zan je yi ? Wata dryr kabir ya sake kwashewa daita "ni da nasan hali ..kar dai ayi abun kunya gidan suruki ... "ai kuwa k'arewar abun kunya har lalata sai nayi wallahi.. hira suka cigaba dayi acikin hirar kabir ke bashi labarin yadda auren sajida ya kasance... Tsaki fu'ad yaja sannan yace "maganinta kenan ,abinda ya cancacin mai hali irin nata kenan har suka iso kofar gidan alhj ediris fu'ad yace "kabir yi Parking gaba kad'an da gidan sai nashiga da kafafuna, zarcewa kabir yayi gaban gidan tare da tsaida motar yayi parking fu'ad ya fito rike da da karamar akwati yana gyara zaman rigarsa da tsayuwarsa sannan ya juya har yasoma tafiya kabir yayi masa hon ya dawo ta gefensa ya tsaya "na wuce ne ko yaya Dan naga sai wani rawar jiki da kafafu kake yi ? ,"rawar duniya nakeyi ..zaka iya wucewa idan nagama zan kiraka yana gama fad'ar hk ya juya . Shigowarta gidan kenan ta shiga bayi domin yin wanka ko cikakken minti Goma batayi ba fu'ad yasanyo kai cikin harabar gidan ,kai tsaye number me'ad ya kira aka ci sa'ar tana hannun nasreen da sauri yarinyar ta d'auka tana murna "hello dady nah ... bangaren fu'ad shima yace "hello my bby nah ,ki fito yanzu ur dady is outside aguje ta kwasa tana tsalle batare data tsaya sauraran abinda zaice ba, tayi harabar gidan dashi idanunta suka fara cin karo da gudu takarasa tashige jikinsa ta rungume shi "dady I really miss you "I miss you too my bby ya fad'a tare da rungumeta tsam ajikinsa yana sauke naunayen ajiyar zuciya when last daya sanyata acikin idanunsa. Hannunsa rike da hannunta suka shiga cikin gidan kai tsaye parlour'n mumy ta nufa dashi yasamu guri ya zauna ya ajiye akwatin tsabarta ita da momy'nta itama tasamu guri ta zauna kusa dashi tana zuba masa surutu . haiyaniyarsu ce ta fito da mumy tana ganinsa ta saki fuskarta sosai Sam bata nuna masa wata damuwa ba , ya D'an zamo daga kan kujerar dayake zaune ya rankwafa ya gaisheta cike da girmamawa"mumuy mun yini lafiya ya gidan ? ta amsa tana tambayarsa yanayin aikinsa had'e da , tayasa murna K'arin girman dayasamu ya ji dadi kwarai da abinda tayi masa ,ta juya ahankali ta shiga kitchen ta d'auko wata special foodflaks dake d'auke da abinci ta d'aura atire da ruwan roba na nestly water Dan daman basa rasa abincin agidan ta kira nasreen yarinyar tashigo had'ad'en kitchen din tana murmushin farinciki ganin dadynta. Mumy tace "yau kuma babu dama anga dady ko ? Nasreen ta girgiza mata kai tana rungumeta "oya d'auki tiren nan ahankali ke kai parlour, nasreen ta d'auka ta fito ta kawo gabansa ta ajiye momy ta fito daga kitchen din ta tsaya agabansu "Kaci abinci idan kuma akwai abinda kake bukata kayi magana a d'aura maka yanzu "babu komai momy, na gode sosai da kulawa wannan ma ya isa tayi murmushi irin nasu na manya sannan tashige d'akinta.. Sam shi ba wai abinci ne agabansa ba zuciyarsa me'ad kawai take son gani da kwadayin son kasancewa tare daita , Dan hk ahankali ya kamo hannun nasreen cikin NASA yace "bby where's ur momy ? Ya tambayi nasreen. Nasreen tace "tana d'akinta yanzu ta dawo daga aiki tayi maganar can kasa had'e da nuna masa hanyar d'akin "ok ya saki hannunta ya Mike tare da cewa "ki duba abubuwan Dana zo miki dashi duk abinda bai miki ba idan nafito ki gaya min ,sannan ya nufar hanyar d'akin data nuna masa ya kai hannunsa zai yi knocking sai kuma ya fasa ya murd'a handle din ahankali yaci sa'ar kofar a bud'e take ya tura kad'an ya sanya kai yashigo cikin d'akin tare maida kofar ya rufe ,ya jingina bayansa da jikin kofar ya murd'a key ya tsurawa bayanta ido . zaune ya ganta akan pray mata tana lazimin Wanda tun aurensu bai ta'ba ganin wannan lokacin ya wuceta ba ta aranar juma'a .. .. ya sake gyara tsayuwarsa ya jingina da kofar sosai yana jin tana sake shiga ransa gani yayi gabadaya yanayinta ya sake sauya masa ta canja ,Dan ta rame sosai . Yana nan tsaye har ta idar ta yunkura ta Mike tsaye ta d'auki daddumar sallarta da niyyar niketa kmr ance ta juyo bayanta , idanunta ya sauka akanshi , cikin fararen kaya ,saurin murza idanunta tayi da hannunta daya ,mafarki take ko kuwa dai gizon dayasaba yi mata ne ? Take gabanta yayi wani mugun fad'uwa,shi kuwa ya bala'in tsura mata kyawawan idanunsa yana kallonta sannan da sanyi jiki yake k'arasowa zuwa inda take ,ahanali ahankali har ya ida Isowa, ya kai hannunsa duka biyu ya kamo fuskarta dake cike da tsantsar mamakin ganinsa cikin d'akin yana shafawa ahankali tayi saurin runtse idanunta "sauraniyyar masu kyau ya furta me'ad ta bud'e idanunta tasanya cikin kwayar idanunsa ranta na mata sanyi, bugu da kari taji matukar farinciki sunan daya fad'a mata ,matsota yayi sosai ya rungumeta tsam ajikinsa yana shafa bayanta "I really miss you my love ,tasoma kokarin kwacewa Amman yaki sakinta sai ma Wani irin kissing dinta da yake,na fitar hankali ,tun tana kaucewa tare dakiyar zuciya har ta kasa jura hkn ,Dan daman itama gabadaya a wannan lokacin a matukar bukace take dashi ,kwanakin datayi batare yin wani abu ba ko jin dumin jikinsa ita kad'ai tasan halin datake ciki. ahankali tasoma maida masa martani ganin tsayuwa bazata kai su ba yajata zuwa Kan gado ,Dan alokacin babu abinda jikinta zai iya tabukawa domin hanashi ta'ba jikinta ba saboda mutuwar da yayi ,kwantar daita agadon yayi ya haye samanta yacigaba da sarrafata hijab din jikinta ya zame ,ai bai gama shiga tashin hankali ba sai da kwayar idanunsa ya sauka a sansar jikinta wannan rigar dake jikinta da shi da babu duk daya ne tun daga wuyanta ya fara kising dinta har zuwa kirjinta lokaci daya me'ad ta manta zancen mahaifinta akanta tare da sharad'a d'insa na yunkurin raba aurensu tsabar tsuman da jikin yake ,sosai ya kamkameta ajikinsa yana aika mata da zafafan wasanni ahankali yake shafa nonuwanta taji wani irin dadi yana shiga cikin kwalkwaluwarta Dan haka ta turo masa manya manya nonuwanta masu cike da ruwa yana shafawa yana tsotsan nipples ,sha'awarta ta sake ta'azzara Kan nonuwanta suka Mike kmr yadda joystick dinsa take a mike, da hannuwansa biyu ya kamo nonuwanta yana tsotsa yana murza mata dayan nipple dinta ,nan fa wani sanyi dadi ya rufeta kasanta ya fara fitar da ruwan ni'ima ,gabadaya ta rude ta rudar dashi tasoma yunkurin rabashi da kayan jikinsa ,shima yana tayata har suka cire rigarsa ,yacigaba da shafa kirjinta zuwa kasanta ahankali ya zira fingers dinsa cikin jikinta yana fingers dinta wani irin d'auke numfashi tayi jikinta na kyarma wani irin yarrrrrrr take ji ajikinta, batasan lokacin data ta Mike zaune shi kuma ya rigin gina da abun gado ,ta kwance zariyar wandonsa ta kamo joystick dinsa tana murzawa ahankali ahankali sannan ta saka cikin bakinta ta fara tsotsa ,wani gurnanin dadi yake fitarwa yana shafa sumar kanta dake kwance a saman bayanta yana furta "uhmmmmm assssssss tmkr me cin yaji ,hannunwansa duka yasa ya kamota ya d'aura saman cinyarsa ya saitai joystick dinsa cikin ajikinta tare da rike kugunta ita kuma duka hannuwanta na makale da wuyansa yasoma having sex daita, banda dadi babu abinda suke ji suna fitar da mishi very slowly "wshhhhh uhmmmmm ahankali fu'ad ya dinga binta yana danna mata joystick sako sako ,Wanda ya sake narka da zuciyarta garesa ta dinga jin tana yawo agamare ..nonuwanta ta dinga goga masa a fuska yayinda joystick dinsa still ke cikin jikinta yana aikin tsoka mata ,ganin tana bukatar yasha nonuwanta a wannan lokacin yasa kamosu yana murzawa tare da d'aura bakinsa ya tsotsa ita kuma jikinta sai rawa yake tana lumshe ido kusan minti 20 suna cin juna ganin tana daf da kawowa gashi shi baiyi komai ba ,kuma yasan halinta da zarar ta kawo sai dai ya d'auki na Manzon Allah s.a.w dan cewa zatayi tagaji, yasa yayi saurin zare joystick dinsa.wata irin numfashi ta sauke da ajiyar zuciya atare idanunta gabadaya sun canza launi sun dawo kalar madara, yace ta juya masa baya ,tasan abunda yake nufi, dan haka tayi masa goho , ta lafe sosai akan gado tare rarumo pillow ta rungume akirjinta, tayi sama da bombom dinta kugunta yashige tsakiya ,kafafunta a had'e shi kuma yana daga bayanta ya zame wandonsa, sai daya kai bakinsa ya lashi gidan dadinta sannan yashigeta yana fitar da wani numfashi "uhmmmmmm ya dinga zira mata ahankali ahankali..shiiiiiiii shiiiiiiiii kawai kake jin fu'ad yake fitarwa,ita kuwa sai ihun dadi take fitarwa da Dan karfi "uhmmmmm uhmmmmm uhmmmmm wayyohlly.....yayi saurin kai hannunsa ya rufe mata baki ,jikinsa na kyarma ya dinga shigarta da karfi karfi ta yadda zataji dadi sosai , ita kuma ta dinga jin dadinta batare da kawo ba tana sake bankaro masa bombom dinta . yana da kyau idan uwargida tasan tana da saurin kawowa da wuri akan mijinta, to yakamata tasan yanayin da mijinta yake jima'i daita ,mai yi sau uku ne alokaci daya ko akasin hk . Idan mai yi sau uku ne alokaci daya , yayinda ita bata wuce sau daya , to ga dama tasamu ,uwargida ta kasance mai yiwa mai gida goho yaci ya koshi har sai yayi realizing sau daya sai su canza style, koda batayi realizing ba zata ji dadin ajikinta sosai , idan kuma shima mai saurin kawowa ne, to yayi sucking dinta sosai ya shata ya tsotseta tassss ,ya dinga zira harshensa cikin hujin kasanta , ko tsotsar Kan Belin ta ,matukar mai gida ya tsotse kasanta yaddda yakamata ya tsotsi Kan belinta yadda akeyi ahankali, tabbas zataji dadi har ma tayi realizing ruwan sikwati Wanda mafi yawa daga cikin mata suke ganin kmr fitsari mace takeyi a wannan lokacin alhalin ba fitsari bane ruwan dadi ake masa ,shi kuma alokacin sai ya shigeta koda ruwan na fitowa. 🤭🤭🤭lol. Mmn sudais ce 💗💗💗💗💗💗 'YAN CINKI 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 ~NA~ *AYSHA A BAGUDO* ~DEDICATED TO~ *My besty friend forever and ever murjanatu mrs faal* Page 84 ........wani irin sex yake daita cike da matsanancin shaukinta ,idanunwansa gbdy sun gama rufewa bubu abinda yake muradi kmr yacigaba da kwasar ni'imarta ,kusan tsawon minti shabiyar yana caccakarta sannan ahankali cikin tsuma ya zare joystick dinsa very slowly acikin jikinta yana mai jin wani irin sabon dadi dake tabbatar da k'arin sha'awarta, gashi har wannan lokacin bai ga al'amun tayi realizing ba . janyota yayi zuwa jikinsa ya manna bayanta da fad'ad'd'en kirjinsa ya rungumota tsam yana fitar da hucin Numashi, hannunwansa duka bisa kirjinta yana murza nipples dinta cike da wani irin salo ,ita kuwa babu abinda take sai numfashi take fitawar ahankali, tana lumshe ido tare da matse yatsun hannunta da take jin tmkr ana sa allura ana caccakarta dashi ,ya rungumeta sosai ajikinsa yasoma kissing dinta a wuya zuwa cikin kunnenta,wani irin tsuma jikinta yake ,take tsigar jikinta suka sake mikewa ........ fu'ad yasan ta kan mace, yasan yadda ake sarrafa d'iya mace da lamarinta, wanda samun irinsu a wannan lokacin yake da matukar wahala,zuwa yanzu tasan bazata iya rabuwa dashi ba, bazata iya yakice tarin soyayyarsa dake dankare da zuciyarta ba, barinsa ahalin yanzu tamkar cutar kai ne gareta,tasan muddin tayi sakacin rabuwa dashi tabbas ta cuci kanta da rayuwarta gabadaya wanda ba zata ta'ba yafewa kanta ba. shigewa tayi jikinsa ta lafe tana kissing din gashin dake kwance a kirjinsa batare da tasan ta aikata dan gabadaya ta mance duk abinda ya faru atsakaninsu ...... Jikinsa na kyarma ya Kai bakinsa cikin kunneta ya zira harshensa cikin yana tsotsa while hannunsa daya na kan brest dinta yana aikin murzawa sannan ahankali muryarsa ta fito " my love kin gaji ko ..? ta d'aga masa kanta ala'mun eh " Shiru yayi na wasu 'yan dakiku yana sake aika mata da wasu salonsa dake birkita mata lisafi, "shi kasan yasan tayi k'ok'ari sosai fiyye da sauran lokutan baya datake nuna gajiyawarta garesa "kin gaji? ya sake maimaita fad'ar hk yana shafa sansar jikinta . da kyar muryarta ta fito very slowly "nagaji over ka barni haka plz...." " kinyi realizing ne? "ta girgiza masa kai kawai tana sake shigewa jikinsa " Ya runtse idanunsa sosai dan yadda take masa yana kara birkita masa lisafi ," kina ganin zan iya barinki haka batare da kinyi ba? batayi mgn ba Illa naunuyen ajiyar zuciya data sauke da kyar , Muryarta na rawa tace ni.. ni.. Na gaji ne kawai ka barni hk " "no bazan iya barinki haka ba, har sai kinyi, ta'ba nan kiji ,ya kamo hannunta ya kai kan joystick dinsa da duk wannan kusantar da yayi mata joystick dinsa taki kwanciya tana tsaye kyam ,"kinji yadda take har yanzu still ina tattare da bukatar k'ari, ya k'arasa mgnr yana lumshe kyawawan idanunsa akanta sannan ya kwantar daita had'e da zamota kad'an da gefen gadon ya sake shigarta ahankali bayan ya d'age kafafunta sama had'e da tokare hannuwansa da katifar ya cigaba da aikin cakarta ahankali ahankali, tana lumshe ido tana d'ago masa kasanta .. A zahirin gsky daman shi baya son yadda take saurin yin realizing da sauri ,domin yafi morar jikinta yadda yake so muddin bata kawo ba . wani irin dadi taje ji tun daga tsakiyar kanta har zuwa sansar jikinta , ahankali wasu wurare ajikinta suke sake amsar salonsa da sakoninsa, "uhmmmm hhhhhhhh sune kawai saitin dake fitowa daga bakinta, baka jin komai acikin d'akin sai fitar sautin numfashinsu. hannuwansa duka yasa ya talla'bo bombom dinta sama sosai ya dinga shigarta da sauri da sauri saboda ya fuskance tana daf da yin realizing, sakamakon kamkame shi ajikinta datayi tana wani irin mika , sabon dadi ne kawai ke shiga cikin kwalkwaluwarta da gangar jikinta, shima ya kamkameta tsam tsam, jikinsa na kirrma atare sukayi realizing wannan karon, wani irin zazzafan numfashi suka sauke suna rungume da juna gabadaya jikinta yayi week ya sake sosai Gabobin jikinta sun bud'e had'e da amsawa , komawa yayi Kan gadon ya jingina bayansa da abun gadon ya janyota jikinsa yana shafa mata gashin kanta zuwa bayanta, numfashi ta cigaba da fitarwa ahankali tana lumshe idanunta, ta kasa tashi tashiga bayi saboda yadda take jin ga'bo'binta . da kanshi ya kaita bathroom sukayi wanka ta kasa sakin jikinta dashi ,sai lokacin ta dinga jin kunyarsa da kunyar abubuwan datayi masa na sakar masa jikinta datayi alhalin tasan halin da'ake ciki. , Gabadaya taki yarda ta had'a ido dashi ya lura da hkn sarai Amman ya basar daita, ya riko hannunta suka fito daga bathroom sannan ya kai hannunsa jikin kofar bayin ya d'auki towel dinta yasoma goge jikinsa, itama ta d'auki karamin towel tana goge jikinta tana tsine ksi. "gaban mirrow dinta yaje ya tsaya yana karewa halitar jikinsa kallo batan ya gama goge jikinsa ya d'auki kwalbar Turarent ya feshe ilahirin jikinsa dashi ya sanya kaya , ta cikin mirrow yake kare mata kallo murmushi yayi saboda yadda yaga sai wani yatsina fuska da tsine kai take ala'mun gajiya da kunya. "kin gaji ne nazo nayi miki tausa Kafin na wuce? Ta kasa d'ago kanta illa yatsun hannunta data kamo tana murzawa ahankali ahankali , yayi shiru yana meida link's dinsa "yaushe zaki dawo d'akinki ? yayi mata tambayar da tasa zuciyarta dukan tara tara ko dai batayi tunanin zai yi zancen komawar a halin taahin hankalin da'ake ciki. "You have to talk to your dady me'ad ya barmu muyi rayuwar auremu ,saboda muna tsananin son junanmu ,ko yayi kokarin rabamu bazamu iya rabuwa ba, dan ni bazan iya wata rayuwa batare da junan ba .... ya k'arasa mgnr yana takowa zuwa inda take zaune ya zauna ya janyo wayarsa ya kira kabir sukayi maganar second biyu ,sannan ya kamo tafin hannuta daya cikin nasa ,dayan hannun kuma ya d'ago fuskarta dashi yana kayataccen murmushinsa mai tsada da bugar da zuciya, tayi saurin runtse idanunta "wai meye hk ne love? "Ba dai kunyata kike ji ba.. ..? Tayi shiru taki bude idanunta zuciyarta na wani irin rawa "any how sha koma menene ni dai ya'azamuyi ki dawo gareni ? taja numfashi da kyar ta fitar kana tace "Kawai mu hakura da juna Dan bazan iya fuskantar mahaifina da wani zance makamancin wannan ba, Domin da amincewata ya aiwatar da komai. "uhmmmmm ai kuwa zaki had'u da 'bacin rai mai tsanani Dan bazan juri zuwa gidan nan ba, sannan zan k'ara aure tun da had'in bakinki ake neman ganin bayana. .... gabanta ya buga da sauri ta bude idanunta fess kan fuskarsa tana kallonsa kmr zatayi kuka. "ya naga kinyi da fuskarki wani iri,ala'mun ba kya son na kara aure? " ke bazaki kasance tare dani ba sannan ba kya son wata ta kasance dani ,alhalin kinsa bazan iya d'aukar dogon lokaci batare da mace ba, duk iya tsawon watanin Dana yi batare da mace ba dauriya kawai nake yi ... ya matsota sosai tmkr zai shige jikinta "Dan Allah love kisan abun yi atsakaninmu ,ko ki dawo gareni ko kuma ki taimaka ki sanar dani yadda zan nemi ganawa da iyayen najma na aureta, yayi mgnr yana kunshe dariyar da ke neman subuce masa saboda yadda fuskarta gabadaya ta sauya . tun da ya sako zance najma, numfashinta ya tsaya , bakincikin maganarsa ta caki kahon zuciyarta, "kenan har yanzu zuciyarsa na Kan yarinyar nan bazai fasa aurenta ba? Ta jefawa kanta wannan tmbyr tana ambatar sunan Allah tare da zare hannunta cikin nasa ta dafe goshinta dashi tana takaicin yadda ta sakar masa jikinta yanzu ya mora son ransa . "da tasan zuciyarsa na kan yarinyar har lokacin, ba zatayi sakacin sakar masa jikinta ba, ta dade zaune kafin tasamu tayi control din kanta ,tabbas sai tasa natsuwa in dai tana son komai ya daidaita atsakaninmu da rayuwarsu tana sonshi matuka amman akansa wannan karon bazata butulcewa mahaifinta ba . ahankali ta yunkura kmr wace akayiwa dukan mutuwa tasoma k'ok'arin mikewa tsaye zata rabe gefensa ta wuce ranta a hade, yayi saurin riko tafin hannunta Wanda yasata tilas tsayawa ta juyo a fusace tana kallonsa, shima ya tsura mata kyawawan idanunsa tsawon minti biyu yana kallonta sannan yace "Nasan bakiji dadin kalmata ta karshe ba, Amman kiyi hakuri babu dadin da kikaji, Akan babu dadin da kika min kuma na yafe miki ,yacigaba da kallonta da kyawawan idanunsa ,ya matso jikinta sosai yana yawo da hannunsa jikinta "a zahiran gsky me'ad bazan iya zama haka babu mace kusa dani, lokaci yayi da zamu sanya karfi da karfi mu magance matsalarmu tare, ni na rasa dalilin dady na son rabumu , Amman gabadaya na lura acikin lamarin kin fi kowa laifi ,domin kece tsanin komai " "nasan da haka sai dai kaima kasani kai ne dalilin zuwana gida wanda silar hk ya zame min alkhairi tunda gashi mahaifina ya yafe min 'bacin ran danayi silar jefashi a dalilin aurenka, ni dai a halin yanzu bansa yadda zanyi ba ,kawai ka sauke min kmr yadda dady ya bukata kaje ka auri ita wacen yarinyar da kake naci ,daman ni tuni nasoma hakura da kai takarasa mgnr hawaye na gangaro mata. "shhiiiii ba kuka nace ki min ba mafuta zamu nema Dan wallahi bazan iya sakinki ba zance auren najma kuma ni ne nasa kaina, kuma zan aureta bisa taimakonta, sai dai idan Allah bai kaddaro hkn atsakaninmu ba. Amman kiyi hakuri ki Nemo mana mafuta "ta fixge hannunta cike da matsanancin 'bacin rai ta yo baya kad'an ta fuskance shi "hakuri fa kake bani ? "Hakuri na koma gidan na sake bijirewa umarnin mahaifina kake nufi ? "ko kuma hakuri da zance k'ara aurenka dakake sake tabbatar min ? Ya d'anyi gyaran murya sannan yace "ina baki hakuri ne Dan inganta rayuwarmu, ki saurareni ina bukatar muyi magana takarshe dake ,babu musu tasamu guri ta zauna tana haki shima ya k'araso ya tsugunna agabanta hannunsa dafe da gwiwowinta " ki godewa Allah daya takaita aurena da sajida, Dan na samu labarin aurenta, nabsani auren sajida zai fi miki ciwo da tsayawa arai akan najma,dan haka ki yarda ki amince min da auri najma ko babu komai ina bukatar taimakawa rayuwata.. "da siffan aurenta ne kawai zaka iya taimakawa rayuwata? Fu'ad na sanka over 10 year's, nasan abinda zakayi da abinda zuciyarta keda tabbaci akai ,ka fito fili kace min kawai kana son wannan yarinyar Amman ba wai taimakonta ba , kana dai cewa taimakonta zakayi is better fu'ad kace min mead son yarinyar najeyi zan aureta, zanfi yarda akan taimako, dan idan taimako ne, akwai hanyoyi daban daban da zaka iya taimakonta dashi, ba lallai sai ta hanyar aurenta ba, well duk abinda kayi babudamuwa, dan for me right now bani da wata matsala daita da kai karon kanka, ruwanka ne ka aureta ko ka fasa aurenta " what I need from you shind ka sauke min aurenka nasamu free arayuwata dan.... " "dakata plz ya mike tsaye daga durkuson dayayi agabanta cikin fushi yasoma mgn ahankali "na fuskanceki me'ad da fuskantar inda kika dosa akaina ,kina son na sakeki kisamu free ki auri safwan ko ba haka ba ..? "Kina son ki barni ki aure wancan tantirin dan iskan daya kasa d'auke zuciyarsa akanki ? Ya fad'i hk yana fuzar da iska mai zafi . "ki fito ki fad'a min kina son safwan kawai ,ba wai umarnin mahaifinki ba " "no abban nasreen ka fuskanceni ,banason safwan tun farko, karka manta nice da kaina na gujeshi da aurensa gabadaya, tayi mgnr a matukar gigice tana k'ok'arin kamo hannunsa cikin nata "ba nufina ka sakeni Dan na auri safwan ba,ina son mu rabu ne dan samun natsuwar mahaifina.. ya fixge hannunsa a matukar fusace "wata biyu kacal na baki ki tattara ki dawo gareni idan ba haka ba wallahi zanyi k'arar mahaifinki kotu tun shi bai rigani ba . ya juya yasoma taku dan barin d'akin . yana fita ta rushe da wani irin kuka jikinta na rawa ,ta isa jikin window d'akinta ta tsaya hawaye na gangaro mata. Shi kuwa lokacin daya fito parlour'n ya iske mumy tana faman zariya hannuwanta duka goye a bayanta gashi ta had'a uwar gumi ,tana ganinsa ta saki naunayen ajiye zuciya muryarta cike da in ..ina tace "ha..har ka fito ? "Na fito momy akwai damuwa ne ? Yayi maganar yana shafa sumar kansa. "No babu komai ta fad'i hkn tana Allah Allah ya bar gidan. "ya isa gurin nasreen dake kwance Kan doguwar kujerar daya barta bacci yayi awon gaba daita ya shafa suman kanta yayi kishing dinta a goshi sannan yayi mumy sallama ya fice daga parlour'n, tsab ya gama karantar yanayin mumy da abinda take nufi dashi Amman shi bashi da cause da kowa ,kuma duk lokacin da yayi masa dadi zai zo gurin iyalinsa. Adaidai habar gidan ya tsaya ya fito mai gadin gidan da hannunsa sannan ya koma jikin motar me'ad ya jingina jikinsa tare da rungume duka hannunwasa a faffad'an kirjinsa, mai gadi ya k'araso inda yake da sauri ya rusuna cike da girmamawa ya gaisheshi ,fu'ad ya amsa "ammm malam sule wata yar tambaya nake son maka idan bazaka damu ba " Sule mai gadi ya gyara tsayuwarsa sannan ya tattaro duka natsuwarsa ga fu'ad yace "yalla'bai Allah yasa nasani "kasani ma akan tsohuwar mai aikin gidan nan ummi nake son yi maka tambayar "ina ne unguwarsu ? Sule mai gadi yayi shiru yana sauraronsa har sai daya ji ya takaita zancesa sannan yace " apapa suke zaune wuraren bandir, ana gidansu yake nan dai sule ya bashi full addres din da zai samu najma sannan ya fita ta karamin get yana masa godiya ,duk wannan tautaunawa da sukayi akan idanun me'ad sukayi shi ,hankalinta yayi mugu mugun tashi duk da batasan maganar da sukayi ba Amman jikinta ya bata address din najma ya tambaya ta fashe da wani sabon kuka "wayyohlly Allah ina son mijina ,ina son kasance tare dashi muddin rai banason rabuwa dashi Amman bazan iya jurar yin abu biyu akansa ba ,sa'bawa mahaifina da kallonsa tare da wata suna rayuwa irin wace muke yi dashi ba ,ya Allah ka saisauta min ,ka kawo min karshen wannan damuwar da nake ciki ,ka cire zuciyar mijina akan wannan yarinyar ,Allah ka canza zuciyar mahaifina ,ka saukar masa da natsuwa ,kasanya masa hakuri akan lamarina da mijina haka tayita kuka tana addua .. Fu'ad na isa inda yace kabir ya jirashi ya bud'e murfin motar yashiga ya zauna yana fitar da numfashi sama sama , batare da yace komai ba ,shima kabir bai yi yunkurin cewa dashi komai ba yaja motar akan layinsu suka hango ta howar motar dady wanda ke zaune abayan Mota ana tukashi ,"kabir tsaya mu gaisa da dady "inji cewar fu'ad. Slow down din motar kabir yayi tare da yin hon , shi kuma direban dady ya ja tsaya ya tsaya saboda gane ko su waye . Ahankali dady ya d'ago idanunsa domin ganin dalilin tsayuwarsu, gama d'agowarsa ke da wuya idanunsa ya sauka akan fu'ad dake k'ok'arin fitowar daga cikin motar . take ransa yayi mugun 'baci yaja dogon tsaki yana bawa direban umarnin barin gurin ta hanyar buga masa tsawar da tasa ya rikice," kada ka sake min wannan aikin banza , daga ganin motar wasu matsiyata kaja burki ka tsaya saboda rashin sanin aikinka, ka sani ko baraye ne ma ,Wanda irin haka na faruwa sosai a duniyar nan tamu ,ta inda yake shiga bata nan yake fita ba yana ta faman fad'a. Direba ya sake rikicewa da mazurai yana duban fu'ad ,shi dai asaninsa surukinsa ne dake aure d'iyar cikinsa," to me yasa zai masa wannan wulakanci? Jikinsa na rawa da bakinsa ya murza sitiyari Dan bai kashe motar ba "kayi hakuri mai gida ba'a za sake ba . Dady bai kula sa ba ya maida idanunsa kan jaridar dake ajiye a gefensa. Fu'ad ya dade tsaye agurin yana tunanin da mamakin abinda yayi wa dady arayuwasa da yasa baya son shi ,da kaunar ganinsa arayuwarsa, kusan minti goma sannan kabir yace ka shigo mu wuce "ya zakayi haka Allah yake lamarinsa,mahaifin me'ad baya sonka ne bilhakki da diyarsa ,ba wai dan rashin airzikinka ba ,Amman ya za'a yi Allah ya rigada ya had'a ,kuma shi kad'ai ya isa ya rabaku da me'ad, "karkayi fushi dashi , kai dai duk runtsi duk wuya karka saki matarka ko dan mahaifinta, matukar kayi kuskuren sakinta to kuwa yayi galaba akanka abinda bazanso kasancewarsa ba kenan . jiki a sanyaye fuad ya dafe goshinsa abubuwa sun taru sunyi masa yawa . kabir yacigaba da magana yana tuki "sai abu naga akan auren wancan yarinyar mai aikinka ,ni bazan hanaka aurenta ba ,Amman fa kasani auren yarinyar bashi ne mafuta ba ,sai ma K'arin damuwa, tunda kana son matarka kuma kai ma kasan tana sonka har yanzu "to meyasa zaka damu kanka akan lallai sai ka k'ara aure alhalin ta gidan ma baka gama daita ba ? "bazaka gane munufar abinda ke cikin raina ba kabir ni nasan dalilin dayasa kaji nace maka zan auri yarinyar " "zan gane idan kagaya min manufar taka ni dai ba wai ina side din me'ad bane kawai ni banason ka k'ara aure ne tention yazo yayi maka yawa duk da yanxu ka taka wani matsayi ,"yanzu dai kagaya min manufarka ta son auren yarinyar? Batare da 'bata lokaci ba fu'ad ya zayyane masa komai ,dogon tsaki kabir yaja yana dukan sitiyari motar " aikin banza kai yanzu karasa taimakon da zaka mata sai na aurenta alhalin zuciyarka bata sonta Anya kuwa wannan maganar taka akwai zahirin gaskiya acikinta? "Zahirin gaskiyar kenan na gaya maka kabir bana sonta taimakawa rayuwata kawai zanyi " "Karya ne fu'ad kana sonta..fuad ya juyo da sauri ya kalli kabir batare da yace masa komai ba "yes kana sonta mana mamakin kake yi alhalin kasan gaskiya na fad'a maka . "na rantse maka da girman Allah kabir bana son yarinyar nan taimaka rayuwarta kawai nake son yi tana matukar bani tausayi Amman zance so me'ad kawai nakewa shi, saboda itace macen data had'a duk wani abinda nake bukata, ka yarda dani zan aureta ne Dan taimako " "Ok tunda baka sonta taimako ne me zai hana kasamu wani natsatse ka tsaya masa ya aureta ,ba lallai sai kai ba .... fuad yayi mugun tsareshi da kyawawan idanunsa yana kallonsa kirjinsa na wani irin mahaukacin bugu, zuciyarsa na rawa Wanda bai San dalilin jin haka ba. "idan kuma baka yarda ka aura mata wani daban ba saboda wasu dalilai ,to ka aura min ita ,kasan halina kasan komai nawa kasan bazan cutar daita ba ,duk abinda kake so zan mata, ni burina kawai ba wuce kabar me'ad tasamu kwanciyar hankali ba ,idan ka k'ara aure hakan zai sa mahaifinta ya tabbatar mata da rashin damuwar da bakayi daita ba ,haka zalika itama zataji babu dadi aranta ,"kai ko auren ma zakayi kabari komai ya daidaita atsakaninku ,kasanya manya cikin maganar a kawar da matsalarka da mahaifinta, shine kawai abinda zan baka shawara akai bawai kaje ka k'ara aure ba .. Fuad yayi shiru yana sauraran zantuttukansa ,da wannan tautaunawar suka bar unguwarsu me'ad . Shi kuwa dady ransa a matukar dagule ya isa gidan, direba nagama parking ya fito fuuuuuuuu yashiga cikin gidan yana huci tamkar mayunwacin zaki a parlour'n ya iske mumy tana k'ok'arin maida tiren abincin da fu'ad bai ci ba, tana ganinsa tayi saurin shigewa kitchen ,ta ajiye tiren ta fito tana yi masa sannu da dawowa a madadin ya amsa mata sai ya jiho mata tambayar data k'ara rikitar daita " wannan matsiyacin yaron yazo gidan nan ne? Mumy takama mazurai tana kallon kowace kusurwa dake cikin parlour'n kafin ya dora da fadin "na rantse da girman Allah zan 'bata wa kowa rai acikin gidan nan , matukar za'a dinga barin wannan yaron yana zuwa gi .. "Ban fahimceka ba dady akan me kake magana akai ? Mumy ta katse masa hanzari. a fusace dady yace " ai kinsa ko akan wa nake maganata kar ya sake zuwa min gidana bana bukatar ganinsa cikin gidan idan ba haka zan tashi hankali kowa 'ya dai tawace bata uban kowa ba . "haba haba dady wai me yasa kake yin irin haka ne? "Edi......mumy takura sunansa Wanda yaushe rabon da takirasa da sunan " Banason abinda kakeyi min a enough is enough ,"ta yaya zaka yi k'ok'arin hanashi zuwa gidan nan alhalin matarsa da 'yarsa na cikin gidanka ? "Akan wani dalili ? "idan bakason yazo maka gidanka ka bashi matarsa mana ,nifa bazan yarda ka kashe wa yarinyata aureta ba ,alhalin ba samun miji irin mijinta zatayi ba ,shi wanda kake son ta aura me yafi fu'ad din dashi? " I think kudi ne ko ba haka ? "Kai yanzu kasan me gobe zata haifar ? "shima yanzu yasoma taka wani matsayi wanda bakasani ba ko nan gaba zai zatar na safwan . "Ada naso auren me'ad da safwan Amman ayanzu wallahi tallahi banason shi da me'ad, Dan ko ta aureshi ba zata samu kwanciyar hankali ba ,duk uba na gari bazai so 'yar cikinsa ta rabu da fu'ad akan safwan ba, babu abinda safwan baya sha ,giya taba kokin da sauransu ,shine kake k'ok'arin kashe mata aure akan shi wallahi bazai yiwu ba takarasa mgnr tana daga hannunwanta sama.... "a she kuwa tabbas zaki had'u da mugun 'bacin raina , zaki tattara ki bar min gidana matukar akan wannan D'an iskan yaron ne . Dan ni komai safwan zai yi arayuwa ni shi nake son me'ad ta rayu dashi ,Dan har yanzu yana sonta fiyye da wancan gaular yaron ,Dan haka tilas na d'auki mataki, Dan me'ad bazata sake cigaba da rayuwa dan wannan matsiyacin ba "waye matsiya? Mumy ta jiho masa tambaya ranta na mata suya .... "Kinsa ko wa nake nufi . "me yake dashi ? "Me ya mallaka? " company's dinsa nawa ? "Waye ubansa a duk fanin Nigeria kinga kuwa dole ni agurina ya tabbata matsiyaci Dan duk arziki da zai yi bazai ta'ba kankare wannan sunan agurina ba ... Yana gama fad'ar haka ya wuce fuuuuuu ya nufi hanyar dakinsa. "Kai kake ganinsa amatsayin matsiyaci Amman ni agurina yafi dangote komai ,tunda bai bar diyata cikin gararin rayuwa ba , kuma babu Wanda yasan matsiyaci sai Allah, haka kawai zaka tsani d'an mutane babu wani dalili ,wallahi duk runtsi bazan yarda ka kashe mata aure ba ,mutun sai kace jahili... ******* Mahaifin sajida ya nemi Khalid ta waya inda ya ce "masa ya zo ya d'auki matarsa ,ganin tsawon kwanaki uku kenan da d'auri auri ,bai zo ba sannan wani daga cikin daginsa bai tako ba gashin duk abinda yakamata ayi ma amarya a gidanta ya kammala ,hatta gara sai da dady yasa aka cika mata d'aki dashi . khalida bai yi sanya a gwiwa ba ya shirya cikin had'ad'en kananan kaya wando baki da riga long selve green mai ratsin Baki baki ajiki ,ya gyara kwantacen gashin kansa da yayi askin afro, Dan shi ko irin askin da ango kan yi bai yi ba ,illa bayan keyarsa daya bari aka gyara masa ,yayi wanka turare ta koina ajikinsa kamshi ke tashi na fitina yayinda hannunsa na dama ke daure da agogon fata kafafunsa sanye cikin wasu takalmin Gucci baki ,yayi kyau sosai, kuruciyarsa ta fito Dan kana ganinsa kaga sabon matashi mai jini ajika . Karfe tara daidai agidan surukinsa tayi masa,kai tsaye ya shigo gidan bai tadda kowa a parlour'n ba ,Dan haka d'akinta ya nufa batare da ya yi knocking kofar ba yasanya kai cikin d'akin. Zaune ya isketa a gefen gadonta Sanye cikin Riga da siket na atamfar julius Holland ,d'inki yayi mugun amsar jikinta ,domin ya fitar da shape din jikinta sosai ta yadda duk wasu kyawawan halittar na jikinta suka bayyana, sai kamshi dad'd'an turare ne ke fita a sansar jikinta ,sosai tayi zurfi cikin tunanin, tunda aka d'aura aurenta taje diner ta dawo bata sake sanya kafafunta waje ba, haka zalika ko parlour'n kasa bata sake sauka ba ,mahaifin dai yasameta a d'akinta yayi mata nasiha sosai a game da aurenta da Khalid, amma ita Sam bataji zata iya hakurin zama dashi ba, ita ko bazata auri fu'ad ba gara ta zauna babu aure . yanzu haka tunanin yadda zata soma warware matsalolin dake shirin kunno kai cikin rayuwarta take ,ita ba mahaifiya ba ,gashi bata da yaya ko kanne dukkan wani girma ya tattara ne akanta , bata da mai bata shawara, babban abinda yafi damunta shine yadda zata raba kanta da auren wannan premature din ... wani sauke ajiyar numfashi tayi ta gyara zamanta cikin yanayi na zurfin tunani ,ahankali ta d'ago idanunta sakamakon jin yanayin kamshi d'akin ya sauya ,aiko idanunta ya sauka akanshi tsaye jingine da jikin k'ofar d'akin ya rungume hannunwasa duka a kirji ,yayi mugun tsareta da idanunsa yana kallonta , kallo daya tayi masa ,ta d'auke idanunta akansa Dan Sam batason ganinsa acikin kwayar idanunta, tana jin da Zata iya, da ta tashi ta makure masa wuya ta kashi shege kowa ya huta .. Ahankali yasoma takowa zuwa inda take zaune ya zauna cinyoyinsu na gugan juna ,tsaki taja had'e da saurin mikewa ta nufi hanyar fita daga cikin d'akin Khalid yayi saurin tare gabanta bai bari ta fita ba ,fuskarsa Sam babu walwala kamar yadda nata mata babu .. "Malam premature ka matsamin na fita nace bana sonka ko ana dole ne ? Tsananin mamakinta kawai khalid keyi , shi yanzu meye laifinsa dan ya aureta? "Tayi play dinsa like a fool sai kuma gashi daga karshe yayi winning dinta. .. "duk yadda zaki kai da guduna kaddara ta rigada ta had'amu guri daya ,you are mine sajida, ke din tawace,ina kuma tabbatar miki sai Allah ya taimaka min gurin gefa soyayyata cikin zuciyarki ,so ki daina wahalar min da kanki ,ko kina sona ba kya sona zaki rayu da Khalid har abada Dan bari na gaya miki new gud news har ciki haihuwa Khalid zai miki .... yadda yayi maganar cike da karfin hali ya bata mamaki sosai sannan ta kasa d'auke idanunta akansa ,Khalid daban yake acikin premature din da take matasa irinsa ,yadda yake gudanar da alamuransa cike da isa da gadara sosai yake bata mamaki .. wani irin kuka ne kufce mata ,muryarta cike da matsanancin kuka tace "Allah kiyaye min yin ciki da kai ,sannan har abada ni sajida bazan ta'ba sonka ba, I hate you in my life bazan taba sonka ba ...shr yayi tare da tsura mata idanunsa yana kallon yadda take kuka muryarsa can kasan makoshi yace "bakya so na ? Tayi saurin girgiza masa kai ,"but ai ni ina sonki sannan zan 'bata tsawon rayuwata tare dake ,zan canzaki na canza gurbatacciyar zuciyarki da batasan zahirin abinda ake kira so ba ,Zan tabbatar miki da abaya can ba soyayya kikayi ba shawace take dawainiyya dake ,I love you sajida and I want spend the rest of my life with you I want you to become mrs khalid..dubansa take sosai cike da matsanancin bakinciki kalamansa masu maka da zantukan kuruciyar yara ,bata an kara ba taji ya janyota jikinsa ya rungumeta tsam ajikinsa "ki daina furta ba kya son mijinki Dan baki San abinda gobe zata haifar ba ,ta bud'e bakinta zatayi magana kenan ,ya had'e bakinsu guri daya yashiga tsotsar bakinta da iyakacin karfinsa ,tayi kokarin kwatar bakinta Amman yaki barinta shan bakinta yake kmr zai cire mata baki gashi ya toshe mata hanci dole tasa ta dinga bashi hadin kai ,shi kuma yasamu damar tsiyaya mata miyon bakinsa tana hadiyewa.tsawon minti goma yana rungume daita yana tsotsar bakinta duk da yadda taso kwace jikinta Amman yaki sai daya so Dan kansa sannan ya saketa ya rike hannunta ita kuwa sai numfarfashi take fitarwa na wuya , tana kallonsa ya ciro wayarsa daga cikin aljihun rigarsa yasoma dialling number dady tare da sanyawa a hands free .kira daya biyu dady Ya d'auka. Khalid ya gaisheshe tare da gaya masa yazo d'aukar sajida ne ,dady yace" to ..madalla kashigo daga ciki mana ya zaka tsaya daga waje ? Muryarsa cike da in..ina ..yace ammm ai yanxu haka ina d'akin sajida ,koda nashigo banga kowa ba ,"ok to babu komai Allah yayi maku albarka ya yabaku zaman lafiya ,idan ka tashi ka wuce da matarka kawai ayita hakuri sukayi sallama ,ahankali ya saki tsintsiyar hannunta "ina mayafinki ? Tayi masa banza ta shiga goge hawayen bakinciki bai tsaya 'bata lokaci ba ya d'auki hijabin sallarta yasanya mata sannan ya d'auki karamar akwatin kayanta dayayi saura Dan komai akai gidanta, "ki biyoni kawai idan kikayi kuskuren canza min tunanina a yau jikinki ne zai gaya miki , yayi gaba abinsa ai da sauri ta gyara zaman hijabinta tabi bayansa zuwa harabar gidan Wanda har ya saka akwatin a bayan mota . Da kansa ya bud'e mata gaban mota ta shiga su duka babu walwala a saman fuskokinsu sannan ya zagaya mazaunin direba ya bude yashiga yashiga yasanya seat belt sannan yayi motar key suka bar gidan . Karfe Goma cif agidansu dake Williams estate yayi musu Dan madaidaicin gida ne ,me shegen kyau ya fito ya bud'e get din gidan sannan ya dawo yashiga motarsa ,yashiga cikin gidan ,yayi parking ya sake fitowa ya bud'e mata kofa "oya madam Dina a office ,tsohuwar matata agidana barkanki da zuwa gidan pre me ma kikace... ?"I want here it again ... tayi masa banza ta fito tana duban yanayin tsarin gidan " shafa goshinsa yayi sannan yace "ai nasan zuwa yanzu bazaki iya cewa komai ba ,muje daga cikin tukun ya maida murfin motar ya rufe ya matso kusa daita ya riko hannunta suka nufi cikin gidan mai d'auke da dakuna guda uku kacal zagaye da parlour'n babu TV bango, balle kujera a parlour'n da babu ac ,babu komai a parlour'n ta fad'a aranta, ya karaso gareta ya rungumota ta bayanta hannuwansa duka zagaye da cikinta .. Mmn sudais ce *************************⬇********************** ************* Ai Hausa Novels **************** *************************⬆ ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ⬇ ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ⬆ *************************