: *GABA* *GADI* *Littafi* *na* *daya* *Labari* *Da* *rubutawa* *Jamila* *umar* *tanko* ( *JUT* ) *Wanan* *littafin* *na* *kudi* *ne* *mai* *bukatar* *karanta* *tawa* *zai* *Biya* *500* 0023843938 *unity* *bank* *jamila* *umar* *tanko* *An* *fara* *rubutawa* a *ranar* *lahadi* *19th* 9 *2021* *da* *misalin* *karfe* 6:30 *am* . ********************** ? ************************** ********** Ai Hausa Novels **************** *************************? ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ? ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ? ************************** Sadaukarwa : Ga kanwata Marigayiya 'Zubaida Umar Tanko' wacce Allah Ya yiwa rasuwa shekara 2 kenan 28th 9 2021 . Allah Ya jikanta, Ya raya yaran data bari akan sunna.Amin. *Bissmillahir* *rahamanurahim* 馃啌 1锔忊儯 GABA GADI Babi na daya : Sun tafi da murna sun dawo da gagarumin bacin rai, bacin ran da ba zai musaltu ba .Tun daga Airport na Malam Aminu Kano da ke birnin kano direban da ya je daukarsu ya fahimci hakan. Babu walwala, babu Annuri a fuskokinsu. Ko gaisuwarsa ma basu amsa ba. Haka suka bude bayan mota suka zauna. Hakan ne ya tabbatar masa cewar Mummy da Daddy babu lafiya abinda bai taba gani ba tunda ya fara yi musu aiki. "Wai shin meya bata musu rai haka ? Ko sakon rasuwa aka aika musu, don sun dawo da wuri ba kamar yadda suka saba dadewa idan suka je London ba ? Ko fada suka yi a junansu? " Habibu direba yake tambaya a zuciyarsa. Har suka isa gida ko tari babu wanda yayi a cikinsu. Wannan bacin ran nasu shi ya hana su cin abinci balle hira, ko kallon talabijin. Babu wanda yake ganin gilmawarsu tunda kowannensu ya Shiga dakinsa ya datse. Kwanaki uku kenan da dawowarsu 'yan sannu da zuwa sun zo ba adadi sai dai 'yan hidimar gidan su ce su na daki su na baccin gajiya, dan haka baa samun damar ganinsu. Masu aiki koda yaushe su na jere abinci akan tebur haka suke zuwa su tarar da shi baa ci ba su kwashe, su jera sabo shima kuma a haka zasu zo su tarar baa ci ba . Tabbas jikinsu ya fada musu gidan nan babu lafiya. Domin basu taba ganin irin haka ta faru a rayuwarsu ta gidan nan ba. Kullum da safe yaransa sai sun shigo don su gaishe su amma sai masu aiki su ce su na daki su na bacci. Wannan ma sabon al'amari ne wanda basu saba gani ba. Kwanaki uku kenan dan haka sun tabbatar ba lafiya ba gashi wayoyinsu dukka a kashe. In ma a kunne ko an kira baa dauka. Yaransu su bakwai yau sun hallara a cikin babban falon gidan da zunmar yau sai sun ga mahaifansu ko da kuwa dakin Zaa balla . Bugun kofar da suke yi ya karfafa in dai mutum ba bacci mutuwa yake yi ba dole ya farka . General Nafi'u ne ya bayyana a bakin kofar dakin fuskarsa murtik babu walwala, babu annuri, idanuwansa sun kada sun yi jajawur, ya wurgawa kowannensu harara yana yi musu duba irin na rashin fahimta. Su dukka suka duka suka gaishe shi, bai amsa ba ya kawar da kai gefe ya fada cikin fushi " lafiya ku ke buga min kofa? Ko na ci bashin wani ne ban biya ba ?" Daga Jin wannan amsar sun san tabbas General ya kai kololuwar fushi . Sai suka hau kallon-kallo a junansu aka rasa wanda zai bashi amsa. Sai Sosa keya da gashi suke yi . General ya sake daga murya cikin tsawa " shin wa ya baku izinin ku wuce falo har guda uku, ku zo kofar dakina ku buga min kofa ? Muhammad ya yi karfin hali ya ce " Oga, kwana biyu ba mu ganku ba daga kai har Mummy tunda ku ka dawo daga tafiya. " Abubakar ya ce " kwana uku ma kenan idan za mu tafi wajen aiki kullum da safe mu na shigowa don mu gaishe ka sai mu iske baka falo masu aiki sai su ce kana bacci ." General ya ce " me ya shafe ku da baccinmu? " Umar ya Sosa keya ya ce "ranka ya dade baccin ne yayi yawa kamar ba lafiya ba hankalinmu ya tashi ." Aliyu ya ce " gaisuwa ce baba ." General ya ce " ku rike gaisuwarku ." Ya na fada ya buga kofa ya rufe dakinsa. Ya barsu anan a tsaye aka hau kallon-kallo. Usman ya kwashe da dariya "yau Boss fa ba kanta. Me aka yi masa haka ne ? " Muhammad ya harari Usman ya ce " kada ka sake yi mana dariya ba abin dariya ba ne . This matter is serious. " Mu'awiyya ya ce " normal ne kawai , ku zo mu kauce kawai sai ya yi normal ma dawo ." Hamza ne bai ce komai ba ya yi shiru kawai yana tunani ya juya ya nufi kicin ya sami masu aiki yana jero musu tambayoyi game da matsalar da take afkuwa a cikin gidan nan. Rabecca ta zaiyana masa duk abinda suka lura da su tun bayan dawowarsu daga tafiya . Hamza ya fito a Sanyaye, a falon farko ya sami 'yan uwansa a zazzaune su na tattaunawa. Abubakar ya zabura ya kalli Hamza ya ce "ka tambayi masu aikin abinda yake faruwa ? " Hamza ya gyada kai ya ce " sun shaida min tun ranar da suka dawo daga tafiya basu kara cin abinci ba kuma basu sake jin motsin su ba . Kowanne yana dakinsa ya kulle. " Suka zauna har tsawon awa guda su na tattaunawa akan yadda Zaa shawo kan wannan matsalar don a samo mafita . Hakan ya cinma ruwa . Gashi gaba daya wajen aiki zasu tafi kasancewar yau litinin har wasunsu ma sun makara . A dole suka tashi suka watse an tsaya akan a hadu da daddare a cikin gidan . Amma su dukka sun yi amanna Na'ila ce kadai take da amsar wadannan jerin tambayoyin. Motocinsu tsala-tsala a jejjere guda bakwai haka kowa ya Shiga tasa ya kama hanyar ofishinsa. Birnin London Na'ila na zaune a takure a bisa gadonta a dakinta. Wayar da ke gabanta ta fara ruri, ta zabura ya Duba sunan lot.col Muhammad ne wato babban yayansu. Ta safe kirji yayin da ta ja da baya daga kusa da wayar kai kace hannu zai zuro daga cikin wayar ya kama ta. Har wayar ta katse bata amsa ba , sabon kora ne daga Con.Muhammad . Daga nan ta tabbatar wani babban al'amari zai fada mata amma tsoro ya hana fa dauka . Yana gama kira sai ga kiran Hamza shima take dauka . Abu kamar wasa kiran major Abubakar ne babban yaya na biyu . Rigiji gafji sai ta daka tsalle ta bar kan gadon ta bar wayar akan gado tana ta ruri. Ta dafe baki dan idan bata rufe ba zata iya sakin sakin ihu. Kiransa na katsewa babu jimawa kiran Asp Aliyu ne ta fallo da gudu ta leka wayar sai ta daka tsalle gefe tabbas babban mugun da ya fi kowa fushi ne ke kira. Ta fada a bayyane ina zan sa raina? Yaya zan yi ? " Kira biyu Asp Aliyu ya yi mata sannan abin mamaki sai ta sake jin wani kiran ya shigo wannan Karon Bar. Usman ne, ah ai shikenan ta tabbata sun ji komai kuma da alama su na tare . A guje ta shige bandaki ta datse ji take kamar zasu fito daga wayar su damko ta. Ta godewa Allah da ba a kasar take ba da bata san yadda Zaa yayyaga ta ba . Karar wayar ce dai ta ci gaba da tashi babu Tantama wannan Karon tasan yaya Mu'awuya be cikakken dan jarida kuma ta san ba zai Duba ta a matsayin kanwarsa buga labarin nan zai yi . "Na Shiga uku" ta fada yayin da ta sulale ta zauna a gefen bahon wanka. Hawaye zafafa ke kwaranya. Babu abinda kwakwalwarta bata fada mata ba shin ta kashe kanta ne a zo a tsinci gawarta kowa ma ya huta ko kuwa ta Shiga duniya a rasa ta ne har abada ? "Kada ki fara tunanin kashe kanki, kin san hukuncin mutumin da ya kashe kansa a wajen Allah a addini ya mutu kafiri. Azabar Allah kuwa tafi ta Sojoji da 'yan sanda da yan jaridar da kime gudu a duniya ." In ji zuciyar Na'ila. Ta fada a bayyane " tabbas gara in sha azaba a duniya da in je in hadu da ubangijina ina kafura. Wa'iyyazu billahi ." Ta yi zunbur ta Mike ta bude kofar bandaki ta fito tana tafe tana sanda. Tana dosar wajen wayarta haske ne ke ta kai kawo da alama sakonni ne suke ta shigowa. Nan ma ta hadu da gagarumin tashin hankali. Ta zauna a hankali ta jawo wayar ta bude sakonnin. Duk wanda ya kira ta ya turo sako wasu da Hausa wasu da turanci su na bata umarni idan taga missed calls dinsu su ta kira su ana nemanta da gaggawa, kiran tana da amfani matuka. Haka tana Shiga watsapp ta sami sakonnin wasu daga cikinsu akan ta kira su da gaggawa. Hannunta na rawa ta ya goge WhatsApp dinta gaba daya ma .sannan ta koma Facebook shima ta goge shi yadda ba zaa sake samunta ba . Ta Shiga U-tube da Instagram a inda take da fellowers sama da milliyan 1 ta goge su gaba daya. Ta rusa kuka kamar ranta zai fito ta fada akan gado wannan Karon babbar aminiyarta ce Siyama ta ke kiranta ta yi kamar zata amsa sai ta fasa ta na tunanin tana tare da Major Abubakar dan shi zata aura . Siyama ta ci gaba da kira ba kakkautawa amma Na'ila ta ki amsawa. Sakon Siyama ne ya shigo tana mai fada mata ta masa waya su yi magana ta gaggawa. Ta dafe kirji ta ce " innalilahi wa inna ilaihi rajuun. Shikenan ai abinda nake gudu ya afku ." Kiran Siyama ne ya dawo da tunaninta kan wayar ta yi sauri ta masa ba tare da ta yi magana ba . Siyama ce ke magana cikin rada " Na'ila kina ji na ? Bandaki na shigo ina yi miki waya , ha Major Abubakar nan a falo yanzu ya shigo da sassafe kamar yana cikin damuwa . Ya na ya yi min tambayoyi akanki da abinda ya faru a London sun ga Daddy da Mummy a cikin damuwa . Na'ila yaya zan yi ? Me zan ce masa ? Ki amsa wayarsa ki fada musu gaskiya kawai . Yau na Shiga uku yaya zan yi ? Kin san hukuncin da Abubakar zai iya sauka akai na idan na yi masa karya . Ki fitar da ni Na'ila zai iya fasa aurena ma . " Siya ma ta fashe da kuka. Na'ila ma kukan take ta ce Siyama ba zan iya fada musu ba na yanke shawara daga nan ma gaba zan kara ba zan iya dawowa Nigeria ba . Kuma kada ki sake ki fada musu ke ce sirrina kuma na baki amana ." Siyama zata yi magana kenan Na'ila ta katse wayar ta ma kashe gaba daya . Tashin hankali ya tabbata a zuciyar Siyama a lokacin da ta kara kira ta ji wayar a rufe. Ta bi ta WhatsApp zata yi mata magana ta ga wayam ta bita Instagram da Facebook babu ma acct din . Ta wanke fuskarta a Sanyaye ta fito tana tafiya dakyar . Ta isa falo ta iske abin kaunarta saurayin da ta fara so wanda take tsakiyar so masu burin yin aure nan da wata 3 wato Major Abubakar Genaral Hassan . Yana tsaye a tsakiyar katafaren falon gidan yana ta kai kawo daga wannan bango zuwa wannan da alama wani abu yana nukurkusarsa. Yanayin da ya ganta bai saba ganinta ba dan haka wani katon zargi ya sake zargo ta. Data ga alamar haka sai ta yi karfin hali ya kirkiri wani basasshen murmushi dakyar. Ta gaishe shi cike da ladabi ya amsa . Ya fada a shelake " bacci kike ne na tashe ki . Amma tunda a Duba muke waya muna chats na ji ki garau daga cewa gani a kofar gidanku na ji kina in'ina. Gashi kin dade baki fito ba na kira wayarki na ji number busy . Da wa kike waya bayan kin san na iso ina cikin falonku? " Daga na ta bude baki ta kasa Mayar da labbanta su rufe, kalma daya ta kasa furta da amsa masa wadannan jerin tambayoyin. "Hmmmm, Hmmm. Kawai take fadi . Ka zauna mana." ta fada jikanta na rawa . Ya Girgiza kai ya ce " sauri make zan wuce Kaduna NDA na makara ma . Na zo in ji amsa kawai . Me ya ke faru ne a wajen Graduation dinku a London? " Bai rufe bakinsa ba ta zabura ya ce " Komai wallahi ." Ya kura mata ido sai ya ga ta kasa ido da shi jikanta yana karkarwa. Can ya gyada kai ya ce " ba komai ko ? Kuma kin tabbata kin fasa min gaskiya ? " Ta dago da Sauri ta dube shi cikin rawar murya ta " eh haka ne ." Ya gyada kai ya ce " ok . Tunda kin tabbatar ba ki Boye min komai ba . Kin yi waya da Na'ila da safen nan kuwa ? " Ta sake zabura har da dafe kirji sai ta tunawa kanta cewa zai gane fa . Sai ta daure ta yi murmushi ta ce " A a ba mu yi ba . " Ya tambaya a shelake " kin tabbata ? " Ta gyada kai kafin ta ce wani abu a bakin kofa ta tsince shi har ya isa can yana tafiya . Ta bi bayansa da gudu ta ce " tafiya babu sallama ? Ka tsaya ka sha tea ." Harara ya wurgo mata mai firgitarwa har suka isa jikin motarsa babu wanda ya kara magana a cikinsu . Da alama ransa ya sake baci . Kalmar da ya fada mata kafin ya rufe kofar motar ita ce " kinsa hukuncin da zan iya dauka akan mutumin da ya yayi min karya ko ?" Kafin ta ce wani abu ya rufe motar ya ja dogon ribas. Masu gadi suka danno a guje suka bude masa get . Ya fice da gudu. Siyama dakyar ta kai kan baranda ta sulale ta zauna . Ta Dora hannu akai ka fashe da kuka zafafan hawaye masu kama da hawayen tiyagas ne suke ta rugugin fitowa daga idanuwanta layi layi. Ta yi sauri ta sauke hannu daga kanta a lokacin da ta yi ido hudu da yayanta Engr. Muqaddas . Ta yi saurin warwarewa ta tsatsafo da murmushi amma hakan bai hana shi ganewa da halinda take ciki ba. Ta gaishe shi ya amsa a ciki-ciki gami da galla mata harara ya wuce abinsa. Sanye yake da bakar suit kafadarsa a rataye da jakar laptop dinsa a kafada. Ya bude motarsa kenan zai Shiga sai ya ji magana daga bayansa. Bai firgita ba ya ji muryar Siyama ce . " Yaya ! Na'ila kuwa ta masa kiran wayar da ka yi mata ? "Ya ji haushin tambayar nan matuqa. Ko amsa bai bata ba . Ya ajiye jakar laptop dinsa a kujerar gefensa ya Shiga mota ya zauna ya kunna. Ta yi sauri ta riqe kofar motar ta rike Zata sake tambayarsa wani abu . Tsawa yayi mata kada ki karaso nan, matsa min da gani. Shi munafunci dodo ne ya kan ci mai shi . Kuka kuwa yanzu ku ka fara da ke da ita dayar munafukar Na'ila . Kada ki sake tara ta da maganar da ta shafe ta in ba haka ba zan fasa miki baki . Na ga fitar Major a fusace shima karyar kika yi masa ? Kin san halinsa ai. Ku ci gaba . " Ya ja motarsa da gudu ya fice, ya bar ta anan a tsaye tana makerketa. Masu gadi kawai take kallo ta ji su na bata shaawa ina ma ta zama su don rayuwarsu ta fi ta ta kwanciyar hankali da walwala. Tabbas bala'in da ya tunkaro su ba a san iyakarsa ba . Ubangijin da Zai kare ta Shi ya umarce my da mu fadi gaskiya duk runtsi dan haka Shima sun yi masa laifi. London " Mummy! Mummy !! ki amsa min waya dan Allah ke kadai kika rage min a duniya " Na'ila take fada cikin kuka da hawaye faca-faca, a lokacin da take kira tana sake kiran mahaifiyarta fiye da sau ashirin amma ta qi ta amsa. Karshe ma ji ta yi an katse wayar, da ta kara kira ta ji an kashe wayar gaba daya . Ta dora hannu aka ta fasa kuka mai tsanani , wayarta ce ta fara ruri ta suro da sauri a tunaninta zata ga sunan Mummy sai ta ga sunan Siyama. Ta yi kamar ba zata amsa ba sai ta zabura ya dauka . "Siyama na kashe kaina da kaina . Mummy ma bata amsa min waya ba tun ranar da suka tafi ." Na'ila ta fada cikin rugugin kuka. Siyama ta face majina da hankici ta " Na'ila na mutu kin kashe ni nima . Yau na rasa Major Abubakar na yi masa qarya. Ke kuma kin rasa Engr. Muqaddas kin yi masa qarya. Mun rasa mazan aure. Kada ki tafi ko bar ni gani nan zuwa London din mu Shiga duniyar tare babu yadda Zaa in iya rayuwa a cikin mutanen nan kashe ni zasu yi. " Siyama na gama fada ta kashe wayar, ba tare da ta jira masa daga Na'ila ba , don ta gama yanke hukunci bata neman wata shawara kuma . Babu sauran kuzari a jikin Na'ila tana kwance akan kafet din gaban gadonta ne a lokacin da take rubuta wani sako mai firgitarwa ta wayar hannunta. Dakyar take ganin kalaman da take jerawa. Ta na rubutawa mahaifiyarta da mahaifinta sako ne, sakon dai iri daya ne . Da farko ta nemi gafara a wajen Mahaliccinta Allah , ta Allah gafara a wajensu iyayenta, Sannan ta ce su nemar mata gafara a wajen Yayyanta guda bakwai , neman gafara a wajen masoyinta mijin da zata aura Engr . Muqaddas. Daga yau sun rasa ta . A cikin daya Zaa yi biyu: ko ta bar duniya ko ta Shiga cikin duniya . Ta na me basu hakuri da shawara akan kada su tarki nemanta a waya ko a London. Don ba zasu same ta ba . Bissalam . Tana turawa ta cire layin wayar ta kakkarya, waya me matukar tsada a take ta kwarankwatsata a kasa tayi filla-filla. Qararrawar kofar falonta ce ta hau qugi babu qaqqautawa. Ta yi kamar ba zata bude ba ta ga basu da shirin bari. Ta taso a Sanyaye ta je ta leqa ta huda. Tabbas ha wanda zata huce haushinta a kansa ya iso . Dan haka a fusace ta bude qofar. Sitibin ne fuskarsa cike da faraa ya Miqa mata wata magzine gami da ce mata Congratulations Na'ila Good job . " Bata amsa masa ta juya gefensa ya Ganshi tare da wani bature . Ya Miqa mata hannu da Zimmer su gaisa sai ta kawar da kai gefe ya qi Mike masa hannu . Yayi murmushi shima kalmar Congratulations ya furta mata . Ta cika da mamaki. Ta Duba bangon mujallar wani katon hotonta ne ya cika bangon. Sai ta zabura ya Dafe kirji ta fada a bayyane " innalilahi me yake shirin qara faruwa da ni kuma ? " Sutivin ya fada " my Shiga daga ciki na zo miki da babban bako John. Baki gane shi ba ne ? John kuwa popular ne kowa ya san shi a kasar nan dole ma zaki san shi ." Ta kalle su biyun a shelaqe " idan na gane shi me Zaa iyu ? " Sityvin yana kokarin tura kai zuwa cikin falo Na'ila ta sa hannu ta kare bata yarda ya Shiga ba . Ya yi murmushi ya ce " sorry ko kina da bako ne ya sa ba kya so mu shigo ? A gaggauce mu ma sauri muke yi . Na zo miki da Albishir cewa John zai yi aiki da ke za ki samu kudin da kowa a danginki sai ya yi sallama da talauci ....." Bai rufe bakinsa ba ta " bana so . Bana buqata. " Ta sa hannu zata rufe kofa sitivin ya jawo ta wannan Karon mari ta sakar masa gami da yi musu tsawa mai firgitarwa . Leave me alone I don't want see u in my house again. Stevin ya yi sauri ya kama Kunci baki a bude dan mamaki, yayin da John ya ja da baya a tsorace yana tambaya . Lafiya ? Me yake faruwa kuma ? Bata amsa musu ba ta Shiga ta datse gidanta. Kallo dayabra sake yiwa mujallar sai ta runtse ido ta wurgar a kasa ta fada kan kujera ta bude sabon shafin runtuma kuka mai tafe da kunar zuci . Domin karanta sabon littafina GABA GADI a biya # 500 ta cikin wannan acct din . Zaa a yi adding din wadanda su ka biya a sabon grp . Unity Bank Jamila umar tanko 0023843938 Evidence of payment ta wanan number 08037196708 11/14/21, 7:18 AM - MY MTN 2: GABA GADI EP 2 Ta yi kuka har qarfinta ya qare, a kwance take kan kujera ta yi lamo babu kuzari a sanadiyyar rashin abinci da ruwa a jikinta . Ga qunar zuci da tafasar kwakwalwa. Ta yi juyi sai gata ta runtoma kasa dabas ta fado. Tana ta burgima akan kafet din da yake shinfide a tsakanin kujeru. Ta fada a bayyane " ina ma qasa ta bude in fada ciki . Dama ace kwanciyar nan da na yi in tsinci kaina a lahira . Bana son in ci gaba da rayuwa a cikin duniyar nan da nake ciki . Allah Ka yafe min, rayuwata ta salwanta. " Hannunta ta ji ya taba wani abu, sai ta hau lalube ta jawo abinda take tabawa. Mujallar dazu ce dan haka sai ta daure ta yaga ledar da aka manne. Ta zaro mujalla ta qurawa hoton bangon ido , tabbas ko sau daya ka taba ganinta a duniya daga ka kalli hoton nan za ka gane ta. Sunanta baro-baro a kasan hoton, Nihal Nuren Mubin sai aka fadi karin maganar mai kama da habaici wanda yayi daidai da abinda ta aika . Zaune ta tashi da sauri hannuna na rawa ta nemo fejin da labarin yake . Albishir ake yi wa masu bibiyar abin cewa bayan hotunan da aka saki zaa saki bidiyon a ranar asabar me zuwa, a manya-manyan sinimomin da ke ciki da Kewayen qasar, YouTube, Facebook, Instagram har da ma sauran ababen kallo na social media. Ta zabura tana laluben wayarta dan ta dakatar da mahunta sakin bidiyon nan , sai ta tuna da cewa ai wayarta ta dade a lahira ba zata taba dawowa ba . Ta yi magana cikin rawar murya " saboda kudi ne yasa suka yi min haka ko ? To zan biya ko nawa ne." Wayar da take kan tebur wato 'land line' ta jawo ta danna lambobinsu ta ci saa an amsa. Da ta fadi sunanta su ka ji muryar sai suka shaida ta. Ta fara magana cikin fushi da daga murya " ku fadi ko nawa ne zan biya ku kada ku tona min asiri . " Dariya ta ji an barke ana ta yi ana qyaqyatawa har da buga qafa. Biliyoyin euro din da aka zaiyano mata zaa iya siyan rabin kasarta Nigeria da shi. Duk tulin dukiyar da take tutiya zuri'arta su na da ita ba zata fanshe ta ba . Ta fada cikin tsawa " kotu zata raba ni da ku muddin ku ka nuna bidiyon nan ." " shin Nihal kin manta kin saka hannu ? Ai da amincewarki aka yi ." Steven ne ya tuna mata . Kafin ta yi magana sun katse wayar. Da ta sake kiran wayar ba su amsa ba . Ta sulale ta kwanta yayin da ta fara tunanin qasashen da baa cika zuwa ba, wadanda ba sa cikin lissafin duniya . Wadanda basu taba ganin baqar fata ba ma . Wadanda aka ce su na cin mutane . Tabbas idan ta kutsa cikin qasar har ta mutu babu wanda zai yi tunanin nemanta a can. Idan kuma an ci saa sun cinye ta shikenan ma an huta . Qasashen masu qananan ido cikin kauyukansu da basu da hanyar mota sai gada da kwale-kwale, idan aka ci saa ma Kada ce a cikin ruwa take zama ajalinsu. Ta fada a bayyane " Allah Ya sa idan na je tsallake Ruwan kada ta cinye ni ." A guje ta tashi ta shiga cikin daki, riga t- short da Wando Jeans ta saka ta dauki jakarta karama wato puse, abinda ta tabbatar ta saka a ciki shine ATM card dinta da kuma passport dinta. Kanta babu dankwali balle mayafi. Ta saka takalmin shiga bandaki wato silifas. Ta fito da gudu daga cikin gidan bata damu da rufe kofofin gidan ba . Burinta kawai ta matsa daga inda aka taba saninta. Kano Nigeria... Dare yayi misalin karfe takwas, Yayyan Nihal sun hallara a babban falon gidan , fuskokinsu gaba daya a cikin damuwa dan ada su na zaton abin nan wasa ne, yanzu sun tabbatar babbar matsala ce. Sun rasa Nihal a waya da duk wata kafa ta social media . Sun tuntubi duk wanda su ka san zasu sami labarinta a acan, sun duba ta baa same ta ba . General Nuren suka hango ya fito daga cikin dakinsa a sukwane. Ya na tafe da sauri har yana tuntube ya kusa faruwa. A waya yake magana a cikin fushi da daga murya . " Ambasador! Ka tura yaranka kowacce kusurwa, boda da filayen jiragen sama da na qasa da suke fadin garin. A hana ta fita daga qasar, Nihal nake so in gani a kasata, a damka min ita a hannuna ko a raye ko a mace . Na sake fada na maimaita a shiga ko ina a fadin cikin kasar a nemo min ita ." Ya harare su ya wuce su ya fita da sauri , dukkansu su ka bude baki su na kallon-kallo . Zabura su ka yi da gudu su ka bi bayansa amma tuni ya shige mota ya fita da gudu, wannan karon ma da kansa yake tukawa baya bukatar direba. Ko ina Zai tafi oho. Major Abubakar ya daki bango ya fada cikin fushi " me yake faruwa ne ? Mu na da haqqin mu sani mu ma fa, amma ake Boye mana kamar wadansu bare .Me ya sami Nihal ?" Wayarsa ya zaro da sauri ya kira Siyama, bata amsa ba sai ya kira yayanta Muqaddas. Muqaddas ya amsa da sauri Abubakar ya ce " Ina Siyama? Ta qi amsa wayata . Ka fada mata duk abinda ya cutar da qanwata kwaya daya tal a duniya, ba zan yafe mata ba . Sai na tabbatar na yi mata hukunci daidai da abinda ya sami Nihal." "Malam ka rabu da ni. Ka san halinda muke ciki ne ? Yanzu haka za ka ji alamar ina ta nishi, gudu nake da qafata a cikin filin jirgin kano . Ina neman Siyama ance jirginsu ya tashi zuwa Abuja . Ta bar wasika cewa ta tafi London su hadu da Nihal zasu Shiga duniya ba zaa sake ganinsu ba har abada." Muqaddas yana gama fada ya kashe wayar ba tare da ya jira amsa ba . Tashin hankali da karar da Abubakar ya yi shi ya jawo hankalin sauran a guje su na tambayarsa. Ya dago da jajayen idanuwansa ya dube su ya ce komai ya gama dagulewa Siyama ma ta gudu zasu hadu da Nihal su shiga duniya . A Tare suka fada "mu je wajen Mummy ko kofar mu balla mu duba mu gani ko tana raye ma, idan tana raye kuwa yau sai an fada mana mugun abinda yake faruwa amma ake boye mana ." Da sauri suka isa bakin qofar dakin mahaifiyarsu Aliyu da Umar sun tukirkire sun yi baya zasu tako da gudu su saka qafa su balla kofar sai Muhammad ya hana su . " ku dakata Ciwon Mummy baya son bayani da tashin hankali . Mace ce mai saukin kai idan mun lallabata Zara fada mana komai ." Su duka suka ja da baya suka bashi waje. Ya karasa jikin qofar ya kwankwasa sau daya sau biyu sai ya saka kunne a jikin kofar domin ya jiyo motsin bude kofar bandakinta, yana magana cikin sanyin murya da kallashi. " Mummy 'yayanki ne gamu nan gaba daya mu 7 muna cikin tashin hankali. Ki bude mana qofa mu shigo dan mu duba lafiyarki. Mummy ke kadai muke gani mu ji dadi a ranmu, idan damuwa ta taba lafiyarki ko kika rasa ranki na tabbatar mun yi sallama da farin ciki mu ma. Mummy ki yafe mana ki tausaya mana muna sonki " Gaba daya suka hada baki " Mummy muna son ki ki bude kofa ." Baa dauki lokaci mai tsayi ba su ka ji an bude kofa . Professor Shatu ce ta bayyana a bakin kofar idanuwanta sun yi luhu luhu abinka da farar fata. Ta rame ta kuje. Su dukka suka durkusa sua gaishe ta . Ta amsa amma dakyar take magana daga gani bayan bacin rai akwai karancin rashin abinci a jikinta. " Mummy ki fada mana dan Allah me yake faruwa da Nihal? " Usman be ya tambaya cike da damuwa. Zasu yi mata magiya ta daga hannu ta tsayar da su sannan ta daddana wayarta ta Miqa musu Muhamma be ya karba ya fara karanta sakon a bayyane . Sakon Nihal ne da ta turo mata wanda take neman gafara daga wajen Allah da iyayenta da Yayyanta da Saurayin da zata aura. Sakon karshen ne ya gigita su da ta ce a daya Zaa yi biyu ko ta bar duniya ko ta shiga duniya . Kada ma su yi wahalar nemanta a London don ta kara gaba . Da gaske babu wanda bai gigice ba su ka fara jejjero mata tambayoyin da ba ta san amsoshinsu ba . "Mummy me aka yi mata ? Me ya faru da ita ? Da ta turo miki sakon ke me kika ce mata ? Ba ki tsayar da ita ba ? " Amsa daya zuwa biyu ta basu ta ja kofarta ta rufe " Ban san abinda ta aika ta ba gaskiya, mahaifinku bai fada min ba ya ce idan na amsa wayarta bai yafe min ba . Abinda nake so da ku shine ku gaggauta barin bakin kofar dakina kafin ya zo ya tarar da ku yayi zaton wani abu muke kunsawa. Nihal kuma ina yi mata addua Allah Ya jikanta ku yi mata hukunci daidai da laifin ." Bayan nan sai ta shige ta kulle dakin da mukulli. Hamza zai sake bugawa Muhammad ya rike shi ya ce " kada ka buga mata kofa . Ku zo mu fita kawai ," Ya wuce gaba su na biye da shi a fusace kowannensu yake . 11/14/21, 7:18 AM - MY MTN 2: GABA GADI EP 3 A farfajiyar get suka tsaya kowannensu gwani ne wajen zafin zuciya , babban abinda ya fi damunsu shine rashin sanin takamaiman abinda yake faruwa . Tun kafin ma su ji abinda ta aikata, sun qudiri niyyar sai sun casa Nihal, sai ta gwammace bata fito a tsatsansu ba . Abubakar ya juya ya dube su ya ce " me ku ke tunani ta aikata haka da har ya tunzura Daddy , ya firgita Siyama ta kasa fada? Ku duba ku ka biyayyar da Siyama ta ke yi min, ta san bana son karya da boye- boye amma ta kasa fada min har ta gwammace in rabu da ita in fasa auren , har ta gwammace ta gudu ta bar iyayenta akan ta fadi abinda yake faruwa . Ba kwa ganin abin nan ba karami ba ne ? " Usman ya ce " na kasa tunano me Nihal zata aika da har ya rikita su haka . Kalli yadda Daddy yake magana a waya har yana tuntube saura kadan ya kifa. " Mu'awiya ya ce " kalmar a kawo masa Nihal a raye ko mace ta gigita ni ." Muhammad ya dago da jajayen idanuwansa ya dube su ya ce " kowa ya fada min me yake tunanin Nihal zata aikata da zai jawo London da Kano gaba daya ta hargitsa haka ? " Aliyu ya ce " ko kirista ta zama zata auri kirista. In ba haka ba me zai sa Daddy da Mummy su shiga irin wannan damuwa haka ? " Gaba daya suka hada baki "wa'iyyazu billah. Allah Ya kiyaye ." Hamza ya ce " ko wani ta kashe acan ? " Suka hada baki " A'uzubillahi Allah ma ya kiyaye." Umar ya ce " Allah Ya sa ba cikin shege ta kunso ba . Kun san fa karatun mace a turai babu muharrami. " Muhammad ya cije baki ya daki kansa ya ce " kai haba . Muna raye kanwarmu ta aikata daya daga cikin wadannan abubuwa wallahi wallahi da kuwa da hannuna zan kashe ta kuma na kashe banza ." Abubakar ya ce " abin dai da baa so a fada ne amma na san an yi daya daga cikin abubuwan nan da muka yi harsashe. In ba haka ba me zai tayar da hankalin Daddy da Mummy haka ?" "Mummy fa ta san komai boye mana take yi kawai don girman laifin ba zai fadu ba ." Hamza ya fada yayin da kwalla ta cika masa ido . Muhammad ya buga qafa ya ce " daya daga cikinku ya shirya, London din zamu je mu taho da ita . Kamar yadda Daddy ya fada ko a mace ko a raye . Daga ita har kawarta Siyama zasu gwammace dama ba su taba sanin ire-irenmu ba . " Gaba daya suka hada baki "da ni Zaa je, da ni Zaa je." Shigowar Motar mahaifinsu suka Hango, yana tsayawa ya fito sai ya gansu sun zagaye shi . "Sannu da dawowa Dad. " Suka hada baki a lokaci guda. Bai amsa musu ba sai ma harara da suka samu . Kokari yake ya keta ta tsakiyarsu ya wuce. Muhammad ya ce " Daddy muna cikin damuwa , muna so mu ji abinda yake faruwa." Daddy ya ce " idan ta yi tsami za ku ji ." Ya wuce abinsa. Abubakar ya zabura ya ce " Daddy mu na da hakkin mu sani don 'yar uwarmu ce ." Daddy ya fada cikin fushi a lokacin da ya bude qofar falo tana qoqarin shiga ya ce "babu ruwana da dangantakarku da ita ." ya barsu a tsaye. Umar ya fusata ya ce " wannan tsohon fa ya manta da cewa yanzu mun girma ne ? Mun zama magidanta, mun wuce yara. Yadda yake mana hukunci da horo irin na da kamar a bariki, iron sojoji sun kama masu laifi yanzun ma haka yake so ya ci gaba da yi mana." Muhammad a fusace ya ce " ku jira anan bari in je wajensa. " ya wuce ya tafi . Babu jimawa sai gashi ya fito a guje, suka tare shi cikin dimuwa suka tambaya ko lafiya ? Ya na sheshsheqa ya ce " could u imagine da bindiga ya biyo ni." Aliyu ya kwashe da dariya, gaba dayansu suka yi kansa da tsawa " meye abin dariyar?" Ya ce " hukuncin Daddy ne ma ya fara bani dariya ma." Wannan karon Abubakar ne ya juya da sauri ya shiga cikin motarsa ya fice , Muhammad ya dubi sauran ya ce "kowa ya tafi, mu hadu gobe da sassafe a babban falo." Ya na gama magana ya Shiga motarsa ya fice . Mu'awiya ya bi bayansa shima a cikin motarsa. Yayin da sauran suka nufi bangarensu domin kowannesu ya na da ginin gida a cikin gidan . Toh fa! Kwamacala kenan . Tabbas Nihal ta yi gaskiya da ta ce gara ta shiga kasashen masu kananan idanuwa ta bace, gara kada ta cinye ta akan ta tunkari hukuncin da wadannan zasu yi mata. Major Abubakar ya kira Engr Muqaddas a waya, Muqaddas ya shaida masa su na filin jirgi har yanzu su na jiran isowar Siyama. Domin sun saka wasu ma'aikatan immigration na Airport din Abuja su hana ta shigewa. Har ma an yankar mata tikitin juyowa kano. Abubakar ya shaida musu gashi nan zuwa Airport din shima zai jira isowarta. Asuba ta gari Siyama Abba Muse !!! Sun hallara da sassafe kamar yadda yaya Babba ya umarce su . Kafin su fara magana Fitowar mahaifisu janye da akwatin kayansa ne ya katse musu hatsari. Kowa ya bude baki yana mamaki. " Daddy ina kwana." su dukka suka hada baki . Gami da tasowa da sauri kowa yana so ya karbi akwatin da yake ja. " ku matsa ku bar min akwatina." Ya fada yayin da yake qoqarin ficewa daga falon . A baya suka bashi ba tare da kowa ya iya kara yin wata magana ba . Habibu direba ne ya iso da sauri ya karbi akwatin ya saka a but gami da bude masa bayan mota ya Shiga ya zauna . Muhammad ya karaso da sauri ya rike kofar motar ya dukar da kai ya ce Daddy mun yanke shawara mutane biyu daga cikinmu zamu je London mu dubo Halinda Nihal ke ciki . " " Kada a kuskura a ayi wannan tafiyar ban saka ku ba . " Daddy yanzu ina za ka je ? Ko London din da za bi ta ? " Hamza ya tambaya Harara ya wurga musu ya ja murfin motar ya rufe ya ce da Habibi " Ja motar mu tafi pls , suna bata min lokaci ." Kowa ya sankare a tsaye ya bi bayan motar da kallo . Ransu ya sake baci tabbas . A zuciye Conel Muhammad ya juya ya nufi cikin gida sai su ma suka bi bayansa kai kace kaza ce da 'yayanta. Bai tsaya a kunna ba sai a bakin qofar dakin Mummy . Ya fara bugawa har wasu daga cikinsu suka taya shi bugun amma bata bude ba. " Mummy kina da labarin Daddy ya yi tafiya yanzu ? Ya fada miki kuwa ? " Abubakar ya tambaya Sun cika da mamaki da su ka ji ta basu amsa. " Eh na sani ." Suka hada ido cike da mamaki . "Ina ya ce miki zai je?" Umar ya tambaya Mummy ta ce " ban sani ba ." Muhammad ya cije baki ya sunkuyar da kai kasa kama mai tunani . Sannan ya dago da jajayen idanuwansa ya dube su. Ya ce " ku bar ta kawai . Da alama fushi su ke yi da junansu ." Mu'awiya ya ce " kin ci abinci kuwa ? Ko In kawo miki tea?" Wannan karon bata amsa ba, kuma bata sake amsa musu ba ma, har suka gaji su ka tafi . "Me na ke gani ? Me yake shirin faruwa da rayuwar Nihal 'yar auta 'yata guda daya da na fi kauna daga cikin 'yayana?" Zuciyar Mummy da Daddy ce ta fada a lokacin da kowannensu ya shiga tunani. BAYAN KWANAKI BIYU Da misalin qarfe hudu na yamma. Motar General Nuren Mubin ce ta kutso cikin farfajiyar gidan. Bar Usman da Dr.Hamza ne kowannensu ya daga labulen wundo yana leqe daga bangarensa. Bayan General ya fito, sun cika da matukar mamaki a lokacin da suka hangi Nihal Nuren na biye da shi a baya, cikin matsanancin firgici tana tafe tana sanda. Suka yi wuf da sauri suka fito. "Daddy sannu da dawowa." Su ka fada a tare. Ya waiwayo da sauri ya ce " yauwa Hamza ku ce da 'yan uwanku ina neman kowa da kowa gobe da safe a falona. Wadanda basa gari ayi musu waya su dawo . A cewa Muqaddas ya kawo Siyama zuwansu yana da matukar amfani. " Cikin damuwa su ka amsa masa, yayin da harararsu ta dira akan Nihal sai ta zabura ta kara sauri a tafiyar da take. Kallo daya zaka yi mata ka san a firgice take kuma a wahale . Baka iya hangi kwayar idanuwanta saboda kuburin fuska. Habibu direba ne ya zo giftawa yana janye da manyan akwatunan Nihal har guda uku. Daga nan suka tabbatar ta kauro gaba daya . Usman ya tambayi Habibu daga "London ku ke?" Habibu ya ce " A' a a Abuja muka jira isowar Nihal ." Usman ya kalli Hamza, Hamza ma ya dube shi su na cikin damuwa . Usman ya ce " ban ga alamar ciki a jikinta ba ." Hamza ya ce "daman waye ya ce lallai-lallai ciki ta yi ? mu jira goben mu gani. Zo mu je mu kikkira su, Conel yana Lagos, Major yana Kaduna , Asp Aliyu ya tafi Abuja, Kenan ace duk su juyo. " 11/14/21, 7:19 AM - MY MTN 2: GABA GADI NA JAMILA UMAR TANKO EP 4 Baa samu hallara taron ba sai bayan sati guda hakan ya faru ne daga General Nuren shine ya daga, domin yana so sai ya gama bincike akan gejin laifuffukan da ta aikata da kuma tunanin hukuncin da ya kamata a yanke mata. Da misalin qarfe goma sha biyu na ranar asabar. General Nuren na zaune a bisa babbar kujerar falon, matarsa Professor Shatu a kusa da shi. Daya kujerar kuma Ambassador Abba Muse ne da matar Justis Hassana Abba Muse, wato iyayen Siyama. Sauran kujerun zuwa kujerun dining table Yayyan Nihal ne su bakwai da yayan Siyama Engr Muqaddas daman su biyu aka haifa a gidansu. Siyama da Nihal suna tsugunne a tsakiyarsu an yi musu da'ira, tun ma baa saka su ba, da kansa suka yi kneel down suka daga hannu sama su na makerketa. Kwakwalwarsu tuni ta hango musu gadon asibitin da zaa kaisu nan da 'yan mintuna talatin. Wani lokacin kuwa cikin kabari kawai suke hangowa domin da alama zasu yi kwanan farko a labari yau. Gafara kawai zuciyoyinsu suke nema a wajen Ubangijinsu. Musamman idan sun kalli gaftara gaftara takalman da su ke kafar sojojin nan da 'yan sanda . Mu'awiyya dan jarida har ya fara daukarsu a hotuna yana jotting din muhimman bayanai . Wani sharbeben belt suka hango a hannun Conel Muhammad . " Daman mutum yana sanin ranar mutuwarsa?" Siyama ta radawa Nihal . Nihal ta gyada kai ta ce " gashi kuwa mu mun Sani. " Zafafan hawaye ya fara kwaranya daga idanuwansu. Kowa na zaune an yi carko-carko, shin da addua zaa bude taron nan ko da ashar? Oho. General yayi gyaran murya sai Nijal da Siyama suka dauki kuka suka rungume juna. Major Abubakar ya daka musu tsawa ya ce "ku saki juna ku wawware, ku matsa." Jikinsu na kakkarwa, su ka marmatsa. Geberal ya kira sunan Siyama cikin tsawa da furgici "Siyama Abba! Tashi tsaye ki bamu labarin abinda ya faru bayan mun kaiku London karatu mun juyo da ni da iyayenki? Siyama ta miqe tsaye jikinta na rawa ta fara magana cikin karkarwar murya ba tare da an gane yaren Hausa ko na turanci take yi ba ." Asp Aliyu ne ya taso a fusace " Ya fisgo ta ya dire ta a tsakiya gami da yi mata tsawa " yar rainin hankali kin fi kowa Zakin murya idan kika sami gulma. Za ki yi yaren da zamu gane ko sai na harbe ko?" Ta dora hannu aka ta kwalla ihu da kuka, kira take "Wayyo Ummata ki taimake ni ." Zafafan hawaye ne ya fita daga idanuwan mahaifiyarta don tausayin 'yarta mace kwaya daya tal kuma 'yar auta, amma a yau ba zata iya taimakonta da komai ba sai addua . Siyama ta ce " Na cewa Nihal kada ta yi amma ta yi, kuma zan fada ta bani amana ta ce kada in fada." Su Muhammad su dukka su ka hada baki " me Nihal din ta yi ?" Muryarta na rawa ta ce " a tambayi Nihal sai da na hana ta wallahi ." Major Muhammad Ya zabura ya taho da sauri da belt a hannunsa zai taya ta amsa tambayar da ta kasa bayarwa, kai tsaye Siyama da Nihal suka makale juna su na ihu. " Professor Shatu ta fusata " ta dakatar da Major ta ce " kada ka taba su, ku na tsorata su, ku bari su amsa tambayar da ake yi musu mana kafin ku hukunta su ." General ya ce Siyama ta zauna Nihal ta tashi . Nihal ta hau makerketa ta miqe tsaye. General ya harare ta ya ce "fadi da bakinki abinda kika aikata a London. Ina so duk jumla daya ki saka kalmar GABA GADI a ciki ." Sai aka hau kallon-kallo a junansu. Saboda rashin fahimta kalmar. General ya gyara zama ya ce "Nihal Nuren wanne course Daddy da Mummy su ka ce ki je London ki karanta.?" Cikin rawar murya ta ce " GABA GADI Medicine suka ce in karanta. " General ya gyada kai ya ce "sai aka yi yaya? Ki bamu labari ." Nihal ta kalli fuskokinsu har tsuma suke kowannensu yana so ya ji karshen labari. Nihal ta sunkuyar da kai ta ce " GABA GADI sai na canja course. " Wasu mugayen tambayoyi ta ji su na jeho mata "Ke! Har kin isa ma ki yi abu GABA GADI ? Da izinin wa ? Wanne course kika koma ?" Nihal ta ce " GABA GADI na koma karatun Fim. " Hohoho sai suka ji kamar zaki mai tsananin jin yunwa ya hango nama. Ji Duke kamar su jawo ta su yi ta duka. Kan ka ce kwabo falon ya hargitse da hayaniya.General ya ce su bari ta kai qarshen labarin. Nihal ta matse hawaye cikin firgici ta ci gaba da cewa "na gama digiri GABA GADI na wuce masters." Ta yi shiru General ya harare ta sai ta ci gaba da cewa "GABA GADI har na fara acting din Fim, na fito a finafinai guda biyu a can." Gaba daya aka dauki salati dukka falon domin bayan ita da Daddy sai Siyama babu wanda ya san abinda ta aikata sai yanzu kowa ya ji. Da gaske Mummy ma bata sani ba ." Nihal ta zame ta zauna ta rusa kuka " ku hukunta ni daidai da laifina ko ku kashe ni ." Siyama ta rusa kuka " wallahi sai da na hana ta, ban taba raka ta wajen daukar fim (location) ba . Daddy ba ruwana wallahi ." Muqaddas ya zabura ya ce da Siyama " rufe mana baki munafuka .Tun farko da zata canja course kiyi waya ki fada mana . Ke ba kin zama pharmacist ba." Kowannensu saga cikinsu jikinsu tsima yake, jira suke a ce kule, su ce cas su kadddamar mata . General ya bada umarni a yi shiru sannan ya umarci Nihal ta sake tashi tsaye ta ci gaba da amsa tambayoyi. Nihal ta miqe ta ci gaba da karkarwa . Za ta iya hango hawayen da yake rugugin kwaranya daga idanuwan mahaifiyarta . Tabbas wannan shi ya fi tayar mata da hankali. Ta yi nadama da da-na-sani dama bata yi ba. General ne ya katse tunanin da take yi, ya ce " wanne hukunci ya dace da ke? Kin qi jin maganar iyayenki? Kin qi jin maganar 'yan uwanki. Kin qi jin maganar kasarki . Nihal ta fada cikin sanyin murya " a yi min hukuncin da ya dace na yi laifi ." " Ni kike so in hukunta ki ko yayyanki?." Ta ji gabanta ya fadi ta yi sauri ta daga ido ta dube su , kowa ya dunkule hannu umarni yake jira kawai . Ta ce " na fi son su hukunta ni , bana son hukuncinka Daddy ." Sai mamaki ya kama gaba daya bil adaman da suke cikin falon . " Shin me Nihal take nufi da ta ce gara kartai su dake ta, su daure ta, tsallen kwado, aikin gida, tsangwama. Kenan gara duk wadannan azabar akan hukuncin mahaifinta shi da babu duka babu zagi. General ya maimaita " gara hukuncinsu akan nawa hukuncin kenan ? Ta gyada kai ta share hawaye ta ce " dukana zasu yi watakila su karya ni a kai ni asibiti amma hukuncinka"....sai ta rushe da kuka . General ya fada a shelake " kuma hukuncina ne ya fi dacewa da ke har kuma na shirya miki komai . Babu duka, babu zagi. Yayyanki ba zasu hukunta ki ba ni ne da hannuna zan hukunta ki. " Mamaki ya cikawa kowa ciki, su ka gyara zama, ana kallonta. General ya ce a kira masa kaka talatu, tsohuwa mai aikin wanke-wanke a gidan tun suna yara . Ta zo ta durkusa tana karkarwa . General ya ce da ita " Hajiya Talatu ina so ki kawo min kayan sakawarki riga da zani kala biyar ki hado har da na jikinki wannan da General daura, daman hakan na fi so ba sai an wanke ba . " Ta fahimta amma ta kasa gane abin da yin hakan yake nufi .Haka ma 'yan wajen . Ba dadewa sai ga Talatu dauke da tsummakarai ko linki babu . Tana karkarwa ta zo ta zuba a gaban General. Ta ce " a yafe ni dukka kayan sun yi dauda ban wanke ba " General ya ce " na ji dadin hakan Talatu a je a samo min buhu na shikafar da ta kare." Ya juya ya kalli Nihal ya ce ta je daki cikin kayanta sababbi leshina da shaddoji da atamfofi ta dauko kala biyar amma ya zama dogayen riguna ko riga da zani . Ta zabura ta tafi daki da sauri jikinta na rawa . Ba jimawa Nihal da talatu suka bayyana . General ya ce Nijal ta bawa Talatu kayan nan kamar yadda ta bata nata an yi musanya kenan ." Nihal tana rawar jiki ta miqawa talatu. Talatu zata yi magana General ya yi tsawa ya ce ta karba kawai na ta ne ta bar cikin falon. Sai ta hau godiya ta tafi da murna . Leshina ne babu na kasa da dubo dari da hamsin sai atamfofi super Holland da shadda gezna. Lallai wannan shine gaba ta kai ni gobarar titi a Jos. Kowa dai kansa ya daure General ya kalli Nihal ya ce "ga sabbabin kayan da zaki dinga sakawa, ki dauki sauri daya ki ajiye a gefe, sauran ki zuba a buhu. Ki Shiga daki ki cire kayan jikinki ki saka ki fito. " Nihal ta bude baki don mamaki da tashin hankali tana tafe tana sanda. Kalmar nnalilahi wa inna ilaihi rajuun ta ke ambato. Ta kwasa ta hada da buhu ta Shiga daki . Babban tashin hankalin da ya same ta ma shine yadda zata saka kayan da suke wari, sun kode hamata a yage. Duk da girman jikinsu daya da Kaka Talatu ina zata kai katuwar riga mai katan wuya? Ta ina zata iya daura zani ita da bata saba dinki mai zani ba? "Me yake shirin faruwa ne General?" mahaifin Siyama ne ya tambaya a gigice. Hannu General ya daga masa alamar ya dakata. Yayin da kwakwalwar mahaifiyar Nihal ta tabbatar mata da muguntar tasa ce ta tashi . Da wani hukuncin da zai yi maka ka gwammace gara a yi ta dukan mutum har ya mutu. Abubakar ya ce " Daddy ka bari mu casa maka ita mu daure ta kamar shekara guda ko in kaita bariki sojoji ta yi ta tsallen kwado tana noma ." General ya Girgiza kai ya ce " ai qasusuwan Nihal ba zai dauki wahala da yawa ba ai zai gutsire. Ku zuba ido kawai ." Nihal ce ta fito sanye da qatuwar riga da zani ga dankwali da mayafi duk da atamfa daya aka dinka. Bata iya daura zanin ba balle daura dankwali, ga buhu a hamata. General ya ce ta je bandaki ta dauko silifas kada ta saka takalmi mai tsada . Hankalin kowa ya tashi daga ta gifta sai warin dusa da hayaki. Ta zo ta tsaya yayin da Aliyu ya kwashe da dariya, Abubakar ya dungure masa kai ya harare shi. Hamza ma dariya ce ta kusa subuce masa shima ya toshe baki. General ya dubi kowannesu ya ce " na kai Nihal karatu don ta zama cikakkiyar gynaecologists ta karanci bangaren mata. Mata masu mutuwa wajen haihuwa kamar yadda gyatumata ta rasu a wajen haihuwar kanwata Baraatu. Abin nan a raina na ce duk sanda Allah Ya bani 'ya mace sai ta zama likitar mata ta zo ta taimaki 'yan uwanta mata musamman ma masu ciki da masu nakuda. Na sha zaman jira sai daga karshe Allah Ya bani mace murna biyu nake yi na sami mace wacce zan saka mata sunan Mahaifiyarta zulaihat sannan zata karanci likita ta taimakawa mata musamman na karkara masu ciki. Domin a rashin kulawar likita yayi sanadin mahaifiyarta ta rasu. Nihal ta tafi da zummar cika min burina sai kawai GABA GADI ta canja course. Dan haka nima GABA GADI zan hukunta ki." General ya yi shiru kamar mai tunani ya ce " kin karanci fim don haka babu a inda ya dace ki yi aiki sai a acting industry. Ba kiyi laifi ba da kika fara Fim a turai domin abinda kika karanta kenan . Anan ma muna matukar bukatar irinki a industry , dan haka ki zo mu je kiyi Fim din hausa don ki taimaki al'ummar kasarki da yarenki da al'adarki. " Gaba daya kowa ya zabura yana magana yayin da Mummy ta dafe kirji ta zazzare ido. kowa ya maimaita "Hausa Fim???" General ya gyada kai ya ce " tabbas wasan kwaikwayo na Hausa.Dalili kuwa mu Hausa ne . Babu wani karatu da bashi da amfani kuma ya kamata ta amfani al'umma abinda ta karanta." Ambassador Abba ya yi magana cikin daga murya da gigita " General ! Ka kuwa san abinda kake cewa ? Ka yarda ka tura zuriaarka zuwa wajen watsewa? 'Yan Hausa fim me suke koyarwa banda raye-raye da lalata dabi'un yara ." General ya Girgiza kai ya ce " daidai kenan ita da ta yi digiri ta yi masters akan abin zata kawo musu gyara mai yawa su na bukatarta sosai." Ambassador ya zabura ya miqe tsaye a fusace ya ce " ka manta an saka ranar aurenta da Muqaddas? Ta yaya zan bari d'ana ya auri 'yar Hausa fim ?" General ya ce " ai daman bai kamata ta auri bare ba, sai ta auri dan uwanta dan Hausa fim." Nihal ta kwala ihu ta durkusa a gaban mahaifinta ta na neman gafara akan ya bar ta kada ya kai ta Hausa fim bata so. Muqaddas ma a gigice ya zo ya durkusa har da Siyama su na rokonsa. Justic. Hassana sai yanzu ta yi magana ta kalli Mahaifiyar Nihal ta ce " Professor kina ganin wannan danyen aikin Zaa aikatawa yarki kin yi shiru." Professor ta matse hawaye ta ce "da ma ku daina bata bakinku ku na rokarsa don kamar zuga shi ku ke yi. Na yi imanin duk duniya babu wanda ya isa ya hana shi aikata wannan danyen aiki . Ku yiwa Nihal addua kamar yadda nake yi mata Allah Ya sa hakan ne ya fi alkhairi a rayuwarta. " Nihal ta zo ta kankame mahaifiyarta ta na kuka " Mummy yanzu sai ki bari a kai ni in yi Hauaa fim. Shikenan rayuwata ta salwanta." Mummy ta turo ta itama hawaye take yi " ta ce lokacin da zaki canja course ba ki nnemi shawarata ba ai ." Abubakar ya fada " me nake gani ne kamar almara ? Daddy zaka rugaza martabar ka da ta iyalinka gaba daya." Hamza ya ce " daddy yin haka kuskure ne ka dai kara yin tunani ." Muhammad ya ce " Daddy pls ka yi hakuri ka rufa mana asiri . In har dole ne sai ta yi fim ka Mayar da ita can London ta yi anan ne zasu iya biyanta kudi mai yawa kuma duniya ta kalle ta . Amma me zata samu a Hausa fim. Iyakacinta a santa a kasar Hausa kawai." Hamza ya ce " idan ma Hausa fim kake so ta yi ka bata kudi me yawa ta shigo da kyamarori masu kyau ta zama excecutive producer kuma director ba wai ka kaskantar da ita haka ba. Me zata samu ? " Umar zai yi magana " tsawa General ya sakar musu ya zabura ya miqe tsaye a fusace " zan fasawa duk wanda ya kara yi min magana baki . Na gama magana yau Nihal ba zata kwana a gidana ba . A industry zata kwana . "Ambassador ya tashi a fusace ya ja hannun 'yarsa Siyama ya ja hannun Muqaddas ya juya ya dubi General ya ce " 'D'ana ba zai auri 'yar Hausa fim ba haka 'yata ba zata auri yayan 'yar Hausa fim ba ." Ya fice yayin da Justis. Hassana ta bi bayansa a fusace itama . Ko kallonsu bai yi ba haka bai damu ba dan an fasa auren 'yayansa, shi dai fatansa ya cika burin da ya kudina. Abubakar ya dafe kai ya ce " shikenan ai an raba ni da Siyama . Daddy ka gani ko ? An dinga yi mana gori kenan." General ya miqe tsaye ya damko hannun Nihal ya fice . "Daddy Daddy ka yi hakuri dan Allah." Haka suka Dunguma suka bi su a baya. Nihal na rusa kuka sai da ta bawa kowa tausayi had da masu zubar da hawaye a cikinsu. Ko kallonsu bai yi ba . Ashe duk wannan abinda ake yi me adaidaita sahu ya sa aka nemo masa, yana wajen get yana jiransu, ya tura ta ciki shima ya Shiga suka tafi. Haka suka bi adaidaita sahu da kallo ba tare da sun san yadda zasu hana shi ba . Mu'awiyya ya ce "ai shikenan mun zama dangin 'yan Hausa fim, duk wata fosta idan aka Kafe ta irin fuskarmu Zaa gani dan mu dukka kanwarmu daya. " " kai ba zai yiwu ba wallahi." Muhammad ya fada yayin da ya juya cikin gida da sauri . Abubakar ya ce "kawai gara mutum ya koma kudu da zama wallahi Zaa dade baa ganni ba ." Dr Hamza ya ce "Daman zan tafi karatun Phd dina Daddy ya hana ni tafiya wai sai na koyarwa jamia an amfana da ni gaskiya gara in tafi . " Kowa ya koma cikin gida yana tunanin yadda zai bar kasar Hausa, gara su bar garin da a aikata wannan danyen aikin abin kunya ne a wajensu . Mummy bata falo har ta koma cikin daki ta kulle tana kuka . Yau ne ranar data sake yin nadamar auren Nuren, har an daura mata aure da dan uwanta ta ki yarda sai da aka warware. 11/14/21, 7:19 AM - MY MTN 2: GABA GADI Ep 5 General da Nihal su na tafe a adaidaita sahu yayin da kowannesu yana tunanin abinda ya ishe shi . Ya juya ya kalle ta itama ta kalle shi cike da damuwa . Ya ce " kar ki zaci zan kai ki wani katafaren kamfani ne don ki je ki fara yin Fim , A a ina so ki faro daga farko kwarewarki ta sa ki sami Karin girma ki shigo birni. Shine abinda ake nufi da 'kan ta waye' , dan haka kiyi biyayya kada ki sake ki nuna musu kin fi su iyawa ko ma kin san wani abu da ya shafi fim idan kina so ki yi nasara." Ta gyada kai yayin da zuviyarta ta harba don fargaba . General ya nemi da dan adaidaita sahu ya kai shi shagon nan da zasu karbi sako .A bakin wani shago suka tsaya shi kadai ya Shiga ba jimawa ya fito a lokacin da Nihal ta runtse ido ta yi kuka harte ishe ta . Sai bayan sa ta ji ya zauna a kusa da ita ne ta yi sauri ta bude fuskarta. Kanta a sunkuye bata so ya ga jajayen idanuwanta. A cikin tashar Kano line suka sauka yayin da General ya biya mai adaidaita sahu kudi na ban mamaki. Yayi ta godiya ya tafi su kuma suka tunkari wajen motoci masu yin lodi. Sai suka tambayi motar Wudil aka ce masa ko ya hau me zuwa Dutse ko ya hau me zuwa Wudil kai tsaye amma tana da tsaye-tsaye akan hanya . Ya yanke shawara gara su hau marar tsayawa a hanya har Wudil. Aka nuna musu motar Dutse wata sharon. Ya zauna a kujerun tsakiya, Nihal da bugun kayanta a hamata ta zauna a kusa da shi . " Alhajji sai kun harhada jikinku mutane hudu zaa saka anan fa." In ji kwandasta. Ta zaci zai saye kujerun dukka don su baje sosai sai ta ga ya matsa jikin wundo, wata mata ce me goyo ta shigo daga ita har jaririn karni da zarni suke yi. Nihal ta dube shi sai ya dauke kai yana kallon taga, warin kayan jikinta ma kawai ya isheta balle an kara mata da wadansu kala-kala . Yunkurin amai ne ya yunkuro mata General ya dube ta ya ce "ki bude buhun kayan kiyi a ciki daman kayan masu datti ne sai ku je rafi ki wanke a kauye." Ta ji kanta yana juyawa kamar ba a duniya take ba kuma kamar ba da Mahaifinta take tare ba . Ko dai ta yi gamo ne, aljanu ne suka sace ta suka yi shigar mahaifinta suka kawo ta duniyarsu? Domin ko a mafarki bata taba zaton zata hadu da rana irin wannan ba . " Ni ce kuwa ? Wannan Daddy na ne kuwa ? A ina muke ? Ina zamu je? Wudil dai na san hanyar garinsu ne Gaya. Can zai Mayar da ni da zama ?" Kwandasta ne ya katse tunanin da ta tsunduma tana yi ya ce " ke 'yar Baba matsa sosai, ga mutum daya fa zai shigo. " Nihal ta cika da mamakin yadda zaa yi wannan zaman mutane 4 manya a kujerun nan . Wani mahauci ne me tsire har da qaton daronsa a kan cinyarsa. Su ka matsu, suka takure kamar kayan cikinta zai zubo. Ta fashe da kuka ta ce "Daddy ka biya kudin seat din dukka, bana numfashi ." Ya harareta ya ce " ina na ga kudin biyan naira dari 700 har sau 4? " Matar da take kusa da Nihal ce ta kyalkyale da dariya ta ce " yaro man kaza, ta zaci sassako kudin kake yi Alhaji. Bata san yadda ake wahala ba ne a qasar nan. Su na kwance ake nemo musu komai, amma mu sai mun yi surfa sannan muke samu mu ci ." General ya ce " fada mata dai Hajiya gara ta san rayuwa , don bata san halin da talaka ya ke ciki ba ne." Bai rufe bakinsa ba jaririn ya daddage ya kutso koren kashi, ashe ko dan diras bata saka masa ba, sai ga kashi har kumfa yake bayan mugun kara kai kace babur ake tashi. Ba Nihal ba har General ya kusa ambulo amai. Matar nan kuwa ko a jikinta sai ta dauki murna da hamdala. "Alhamdulillah ya samu yin kashi ai maganin shawara da sabara na bashi ita take damunsa. " Ta daga shi sama sai ga kashi mai yauqi yana disa, ta saka zanin ta share masa sannan ta miqawa Nihal. Ta ce " baiwar Allah riqe min shi in kalmasa inda babu kashin in kwantar dashi ." Nihal ta zabura ta ce " bana iya daukar jariri ai." General ya harare ta ya ce "karbar mata shi ki rungume. Da kin zama likitar haka zaki cewa patients dinki?" Nihal ta fada a zuciyarta " na Shiga uku yau .Allah Ka yafe min, na san laifin da na yi ne yake bibiyata. " Nihal ta yi sauri ta karba sai ya kwaro mata tunbudi har kirjinta. Matar nan ta sake yin hamdala gami da cewa " cikinsa ya saki kenan tunda har yayi tunbudi, ai in fada miki kwana uku babu kashi aka kwatanta min wajen masu maganin gargajiya kin ga ikon Allah ko gida bamu je ba ya warware." General ya tura kansa ta windo yana shaqar iska domin hancinsa ya gauraye da karni kamar zai yi amai daurewa kawai yake yi. Matar nan zabura zata saka zanin nan mai kashi ta goge jikin Nihal. Nihal ta zabura ta ce " ki bar shi zan goge da kaina. Karbi baby ki ." General ya juyo ya dubi Nihal ya ce " karbi jaririn za ki ce.Ina ta san kalmar wani Baby ? Ke malama dole ne fa ki koyi yaransu, kada ki je kina yi musu ingausa Hausa da Turanci. " Ta sirnano da hawayen takaici ta bude buhun kayanta ta zaro wani zani, ta goge tunbudin sai wari biyu ya hadu. Yawu ya cika bakinta ta bude zanin ta zuba ta sake kunshewa ta mayar cikin buhu. General ya gyada kai ya ce " yauwa haka ake yi, kinga ko baki wanke ba in kika shanya sai ki saka kayanki ba wani abu ba ne. Baki ga matar nan yadda ta yi ba , da ta lunkube kashin sai kawai ta dora yaron a kai." Tun daga nan Nihal ta tabbatar zata shiga aljanna saboda azabar da ta tunkaro ta babu tantama kankarar zunubi ne. Ta tunano rayuwarta ta dazu da safe ma a cikin dakinta a kan gadonta ko ina kamshi, baa ma kai da nisa ba maana bata ma hango rayuwarta a London ba a wuraren shakatawa masu daraja ba . "Astagfirullahi waatubu ilaihi". take fada tana nanatawa. Mota ta cika tab da bil adama da kaya kamar zata fashe . Sai dai kash! babu batir me kyau dan haka sai da qartai su ka daddage su ka tura su . Bayan batir ma motar tana bukatar abubuwa da yawa dan wani kara take da hayaqi, sai daga baya Nihal ta gane cewa motar ma ba da mukulli ake kunna ta ba waya da waya ake hadawa sannan ta tashi . Bata taba sanin ana yin haka ba sai yau . Innalilahi wa inna ilaihi rajuun kawai take kira a zuci domin tunda aka haifeta bata taba hawa motar haya ba sai yau , motar ma ta hanyar qauye. General ma addua kawai yake yi ba zai nuna ba ne amma fa hankalinsa ya tashi yadda ya ga over load da aka yiwa motar ga rashin lafiyar inji da tayoyi. Suka yi addua aka shafa aka kama hanyar Wudil. General ne ya dauko wata kwarababbiyar waya wacce ko masu gadi da masu wanke-wanken gidan bata taba ganin mai irinta ba . Ya kira wata lamba. " salamu alaikum Malam Tukur! Malam Nuren ne da Habu ya hada mu, wanda ya ce maka zan kawo yarinya. Yauwa ka shaida ni ko to ga mu nan mun taso daga kano . A Wudil a ina zamu sauka ? Toh daga mun tsallako gada wajen ruwan nan ko ? Alhamdulullah ashe ma yanzu ku na cikin aiki kenan, haka ake so. Sai mun zo ." Nihal ta zazzare ido tana kallonsa tana kuma kallon wayar. Ya harare ta ya mayar da wayarsa aljihu. Mamaki bayyananne zaka gani a fuskarta. Tafiya yankin azaba kowa a matse ga wannan me goyo da jaririnta sun hana Nihal sukuni sai mutsu-mutsu suke suna buge ta, ga kayan kazanta kala-kala su na fitarwa bayan kashin yaron matar ma tari da kaki take tana tofowa duk akan wannan zanin, ta ci goro kakin jajawur. Allah ne kadai ya san me take ji yau a cikin zuciyarta domin abin baya fasaltuwa. Daf da garin Wudil Mota ta fara gardama a dole direba ya gangara gefe ya tsaya aka ce kowa ya fito sai an daga inji an gani . Suka firfito gaba dayansu sai yanzu Nihal ta lura kayan da yake jikin mahaifinta ba na sa ba ne , kodaddu ne har hamata ta yage. Da yake yana da tsawo da kiba sun yi masa kadan har ma sun dage masa. Takalmin qafarsa ya sude har ya huje, wata tsohuwar hula ya ciro daga aljihunsa ya saka a kansa . Ashe shagon da suka tsaya dazu kayan ya Shiga ya canja. Da General ya ga kallon da take yi yayi yawa sai ya ce " meye kike kallona ne ? Talaka ai shi yake haifar talaka ko ? Ta ina Zaa ga Babanki fes ke kuma da tsumma? Ba zamu iya jira har sai sun gama gyaran nan ba zo mu hau babur ya karasa da mu kada su tashi ." " Babur ? Nihal ta maimaita. Bai tsaya bata amsa ba ya kara gaba. Bata ankara ba ta ganshi ya haye bayan wani babur, ya nuna mata na kusa da shi ya ce ta hau . Dakyar da sudin Goshi ta hau, ya umarce ta da ta rike sosai dan a babban titi suke . " kwandasta da direba fadi suka "Alhaji yaya zaku tafi? Yanzu fa zaa gyara ." Ko kallo basu ishe shi ba suka kara gaba . Ana tafe tana salati har suka isa inda aka ce su je. Ba tare da ya yi tambaya ba ya hango dandazon mutane masu shirin Fim da 'yan kallo ana ta daukar shiri. Tana sauka daga kan babur sai ta koma gefe ta tsugunna ta kwaro amai, sai da ta amayar da duk abinda ta ci. Nihal ta cika da mamaki da taga yarda mahaifinta yake acting irin na 'yan kauyen da basu taba zuwa makaranta ba . Shi da masu babur ma sun dade ana magiya akan su yi masa ragi tamanin tamanin zai biya, su kuma sun ce sai naira dari, karshe dai director Tukur ne ya zo ya cika hamsin din . General ya dage shi a dole kudin hannunasa kenan. Wannan al'amari ya fi karfin kuka dan haka Nihal kallo kawai take yi tana jinjina iko da irada na Ubangiji mai jujjuya lamuranSa a duk lokacin da Ya so . Suka qarasa wajen da ake daukar shirin a baki ruwa . Dandazo almajirai ne da 'yan gari yara da manya kowa da kalar warin jikinsa. Ta kalli masu hada shirin da masu acting din sai ta tabbatar ta shigo wata duniyar da ta daban ba duniyar da ta saba gani ba . Ta tuno yadda ake daukar shiri a qasar England ta jera ta dora akan sikeli ta tabbas bai kamata a kira su da suna daya ba . Babu ma hadi bata san ma sunan da zata kira wannan abin ba dan bai yi mata kama da Fim ba . Mahaifinta ne ya katse tunaninta a lokacin da ta juyo yana zubar mata da daraja a gaban mutane . Ya ce " wannan diyata ce mace guda daya tal da nake da ita. Daga kauyen Dan ciyau muke can kusa da Bosuwa ta karamar hukumar Gumel." Tukur ya gyada kai ya ce " na san Gumel amma Baba kun yi zagaye, dama baku biyo ta kano ba, da ta Gujungu ku ka biyo ta Gagarawa. " General ya ce " ai babu kudin motar ne sai da zo kano dan uwana ya ranta min ." Tukur ya yi dariya ya ce " Allah sarki ai haka rayuwar take, daga ta karbu a wajen masu kallo watarana Mota zata siya maka Baba." General ya face majina ya saka gefen hannunsa ya goge sannan ya goge a jikin rigarsa, babu mahalukin da zai gan shi ya ce ya taba shiga aji, ko yana da naira dubu daya tasa ta kansa ba . Nihal tana kallonsu ta kasa kwatanta tashin hankalin da take ciki ba , kunya ta kama ta ji take dama kasa ta bude ta afka. Sai gani-gani super star suke yi mata, matansu da mazansu. Su na yi su na toshe baki su na dariya su na nuna ta. Dariyar da suke yi kuwa ita ce yadda wannan burtuntunar Zata zo ta ce zata shiga Fim. General ya dage wai ya fi so a saka ta a fim ta fara a gabansa. Su ka taru su na yi masa bayani ai baa shirya yi da ita ba kowa sai an bashi script ya karanta kafin a zo nan . Abin mamaki sai Nihal ta ga ya kece da kukan karya wai a dole sai an saka 'yarsa a fim . General ya ci gaba da cewa "tun tana karama take son ta Shiga fim , shine na ce sai na cika mata burinta kuwa. A taimake ni yaro, in wani abu ake biya a ranta min zan je in nemo bashi in biya." " Ah babu wani kudi idan ta iya acting zaa ci gaba da daukarta. Kallonta suke yi sama da kasa kayan jikinta ma kadai ya isa abin tsantsani. Ta ina zasu saka ta a cikin wannan fim din ma banda abin tsoho . " Cabdijam! Mutumin kauye ma sai dai a bar shi , kawai ka nuna masa zaka saka ta don ya tafi ya bar mu mu yi aikinmu." Haruna camara man ne ya radawa director Tukur. " Shikenan Baba za mu duba mu gani . Amma kai da kuke nesa a ina zata zauna ? " Tukur ne yake magana . General ya ce "akwai gidan kanwata amma a Gaya ne, idan akwai in da kuke sauke baki ku ajiye ta . Gata nan amana na dakata a hannun Allah a hannunka." Nihal ta tsugunna da buhunta a hamata domin jiri take ji bayan tashin zuciyar warin kayan jikinta ya ishe ta . General ya yi sallama da su Tukur akan ya bar ta anan zaa samo mata masauki, amma ya tabbatar masa zata jima bata sami shiga ba kasanceaar bata da wayewa kuma bata shafa mai ta yi fari ba irin na bleaching an fi daukar farare. General ya kira Nihal gefe kamar su na ban kwana. Ya ce mata " wannan shine ake kira da kan ta waye. Ki na yi a hankali daga kauye har Allah Ya sa ki shiga birni. Kada ki nuna kin taba sanin wani abu wai shi wayewa ko arziki .ki yi biyayya Allah Ya bada saa .kina da kudi a jikinki kuwa ? " Ta Girgiza kai ta ce " bani da Naira sai dallar kuma ka ce kada in dauko komai nawa. " Ya ce " gaskiya ne , ga dubu biyar ki dinga dan cin abincin da kika ga ana ci amma dai ki boye dan na nuna musu bamu da ko sisi. Kin tuna Lokacin da na kai ki karatu London sai da na kai ki wajen gyenea doctor ta auna ki aka tabbatar ke cikakkiyar budurwa ce ko ? Haka bayan kin dawo daga karatu shekaranjiya na kaiki asibiti an duba ki ko an ce babu matsala ko ? Alhamdulullah ba ki watsa rayuwarka ba haka yanzu duk ranar da kika cika aikinki na fim zan ce ki dawo gida, sai na kara kaiki asibiti an auna ki . Ki kiyaye kada ki watsa rayuwarki anan . In kika yi haka kin san abinda zan iya yi da wanda ba zan iya yi ba . Amma fa na yarda da tarbiyyar da na baki, ina so ki ci gaba da neman tsari daga sharrin shaidan da mutane, mu ma muna yi miki addua Allah Ya tsare ki Ya sa ki fara a saa ki fama a saa." Ta amsa da " Amin na gode ." Sai ta zubo da hawaye zazzafa . Ya ji kamar shima ya fashe da kuka sai ya daure. Ya kara yiwa 'yan waje sallama ya juya ya tafi . Tausayi ya hana shi ya waiwayo ya sake kallonta. Tana kallonsa ya haye acaba ya kara gaba . Sai ta sulale ta zauna tana kuka kamar ranta zai fita . Shewa ta ji 'yan matan nan sun yi gami da tafa hannu . Su ka kalle ta suka tabe baki suka ce " su fim manya , ko wanne tsami ma sai ya zo ya ce wai fim ya zo zai shiga. Ahayye yirit." Director Tukur ya daka musu tsawa " ke Amina kwalisa! bana son haka fa, wannanai cin fuska ne . Yaya kuke yi mata dariya ne." Amma fa shi ma dariyar yake yi yana zumde baya so dai Nihal ta gane . 11/14/21, 7:19 AM - MY MTN 2: GABA GADI Ep 6 General Nuren bai iso gida ba sai da misalin karfe tara da rabi na dare. Masu gadi basu shaida shi ba da farko sai da yayi magana suka shaida muryar. Mamaki ya kama su da suka ga ya shigo da kafa da kodaddun kaya yana tafe yana dingishi kamar wani masaki. Bai amsa gaisuwarsu ba ya wuce cikin gida . Ya ci saa ya sami jerin abinci a kan teburin binci (dining table) . Idanuwansa sun rufe bai hango matarsa a zaune a daya falon ba, har sai bayan da ya cika cikinsa. Ya zo ya wuce ta babu wanda ya yiwa wani magana a cikinsu dan kowa haushin kowa yake ji. Ta bi yagulallun kayan da yake jikinsa da dingishin da yake yi da kallo cike da takaici tabbas kallo daya zaka yi masa ka tabbatar ya sha wuya . "Daman ai haka rayuwa take in ka ce sai wani ya sha wahala hakika kanka zai dawo, abinda ka shuka shi za ka girba." Shatu ta fada a zuciyarta. Ta na da magana da shi ne shiyasa ma ta zauna zaman jiransa, maganar tana da amfani kuma a daren nan take so ta yi dan ba zata iya kwana da ita ba . Ya na bude dakinsa ya shiga kafin ya rufe ya ga tayi zuruf ta fada. Ya kalle ta cike da mamaki, ko bata fada masa ba ya san ta tara shi ta zo don ta fesar. Ya tura kofa ya rufe ba tare da ya kalle ta ba . Bandaki ya wuce kai tsaye yayi wanka, ya dauro alwalla ya fito daure da tawul. Wani qaton ciwo ta hango a qafarsa har an daure da bandeji, gaban ya fadi hankalinta ya tashi amma bata nuna ba ta yi kamar bata gani ba. Jallabiyya ya saka sannan ya dinga jero sallolin da ya rasa. Ya dade yana adduabayan idar da sallah amma rabin addu'ar Nihal yake yiwa domin ya tabbatar ya yanke hukunci ne me cike da garaje. "Shin a matsayinta na mace wacce ta saba da jin dadi da kashe dallar da euro in bata da kudi wacce irin rayuwa zata fada ? A matsayinta na wacce bata saba da aikin wahala ba wanne ciwo ne zai same ta idan ta yi aikin wahala ? A matsayinta na wacce bata saba kwanciyar tabarma da cizon sauro ba wacce irin cutar rashin bacci da malaria ce zata same ta? Allah na baka amanar Nihal Ka kare ta ka bata juriya Ka bata mafita ." Sannan ya shafa. Ya juya ya dubi matarsa wacce ke zaune har yanzu akan kujera, ta dora qafa daya akan daya tana girgiza kamar 'yar tauri, babu annuri a fuskarta har ma bata son kallon fuskarsa. Ya yi gyaran murya ya ce "ina sauraronki. " Ta fada cikin gadara gaba gadi ta ce " ina so ka sake ni." Gabansa ya yanke ya fadi domin bai taba jin irin wannan kalmar ta fito daga bakinta ba, a tsawon shekaru arabian din da su ka yi tare. Sai ya daure kamar bai damu ba ya fada a shelake " daman na daure ki ne ? " Daman ta san zaa rina wai an zaci zanin mahaukaciya, tabbas yau zata hadu da bakaken maganganun da ya saba mayar da martani da su. Ta ce " auren ne na daina domin na gaji da zama da mutumin da baya jin bari kuma kowa bashi da 'yanci, sai abinda ya ga dama yake yi kuma dole kowa ya bi." Ya mike tsaye ya nade abin sallarsa ya ajiye a gefe, ya tafi jikin kofa ya sake murda mukulli ya tabbatar kofar ta kullu sai ya zare mukullin, ya kashe fitila ya hau gado ya kwanta. Ta fusata ta kunna fitila ta ce " magana nake fa ka kwanta ka rabu da ni , na ga ka kulle daki ka dauke mukulli. Me hakan yake nufi ? " Ya yi murmushin bada haushi ya ce " hakan yana nufin na kulle zuciyata babu wata sai ke haka ke ma kin kulle zuciyarki babu wani sai ni. Bari ma in fada miki kalmar da za ki fi ganewa babu yaji, babu saki a cikin auren soja haka muna anan a tare har mutuwa. Albishirinki! ko kin mutu ba za ki bar cikin gidan nan ba haka ko na mutu ba zan bar gidan nan ba . Haka a kiyama daman tare zaa hadamu domin baki taba sanin wani d'a namiji ba sai ni haka nima ke kadai na sani. Ke ce uwar gidana sai kishiyoyinki guda dubu saba'in. " Ya ja mayafi ya rufe fuskarsa. Bakinta a bude ta kasa furta kalma daya dan takaici. Ta fara tunanin ko da zautacce take magana . Yaya zaa yi ya ce ko sun mutu ba zasu bar gidan nan ba? Gawar zaa ajiye ta dinga wari, ba zaa a binne ba?" Ya tabbatar ta shiga rudani don haka sai ya taimaka mata, ya ye mayafin ya dube ta ya ce " na bar wasiyya idan na mutu a binne ni a cikin gidan nan haka ke ma zaa binne ki a kusa da ni .kin ga muna cikin gidan nan dai. Ki kashe min fitila ki zo bayana ki kwanta na gama wannan maganar ba na so a sake tayar da ita kuma ." " Hmmm! Lallai ! A shekaruna da ilimina sai an zabar min abinda da zan yi kenan." Bai amsa mata ba takaici ya sa ta kwana akan doguwar kujera, sai da asuba suka farka . Ya boye mukullin nufinsa shi da ita yau babu shiga babu fita sai dai su mutu tare a daki. Nihal Nuren Mubin Ta yi mawuyacin bacci marar dadi wanda bata taba yin irinsa ba tunda Allah ya halicce ta. A falon darakta Tukur aka kai ta, kan wata kwarababbiyar kujera marar tsoka sai qashin katako. Hakarkarinta ne ya sankare don haka sai ta sauka qasa kan ledar da babu shara ta kwanta, ta yi fulo da buhunta. Sauro da zafi suka addabe ta a sanadiyar rashin wuta, babu fanka balle Ac ga duhu. Ta tashi zaune cikin dare tana ta susa tana rusa kuka. Kukan da bata yi dazu ba sai yanzu ta yi shi. Ta fara kokonton anya iyayenta su ne iyayenta na gaske kuwa? Dan idan su suka haife ta ba zasu bari ta zo nan ta zauna ba. Laifin da ta aikata a ganinta bai yi girman da mahaifinta zai yanke mata wannan hukuncin ba.Ta na tunanin yadda rayuwarta zata kasance tare da 'yan matan fim din nan wadanda suka raina ta su na yi mata dariya da shewa su na tafawa, zumde da yafice baa tsaya anan kadai ba Amina 'yar kwalisa ma cewa ta yi ta dauko mata jakarta ta biyo ta a baya. Kenan 'yar aike za ta zama, sai ta yi bauta kafin a saka ta a fim? Amma da ta tuna disgi da qasqancin da mahaifinta ya jawo mata a bainal nasi bai kamata ta ga laifinsu don sun wulakanta ta ba . Bayan duk wannan bala'i warin jikinta da tsantsanin makwancin, qishirwa da yunwa ne suka addabe ta . Kaikayin jikinta ya qara faskari , ashe borin jini ne ya hadu da raunin cizon sauro jikinta yayi burdun-burdun da ta tashi da safe ta gani. Fuska ta kumbura ido yayi luhu- luhu. Muryar darakta Tukur ta jiyo a tsakar gida shi da matarsa mai suna Sadiya su na rigima, da ta kasa kunne tana saurare sai ta fahimci a kanta su ke yin fadan sai ta ji hankalinta yayi mummunan tashi. Kwana dayan da ya kawo ta tayi ne Sadiya bata amince ba, ta yi rantsuwa baquwar nan ba zata sake kwana a gidanta ba kuma daga kanta ba zata sake yarda ya kara kawo mata wata 'yar iska gida ba. Shi kuma yana ta bayani yana bata labarin yadda mahaifin Nihal ya takura shi ya biyo ta wajen amininsa ya roke shi aka kawo ta ba tare da ya san yadda zai yi da ita ba.Ya tabbatar mata yau zata bar gidan zai kaita gidan haya dakin da su Usaina Danga da Mami Harka su ke, ta zauna tare da su. Nihal ta yi wuf! ta fito sai ta durqusa har qasa ta gaishe su. Tukur ya amsa, amma matarsa bata amsa mata ba , ta dauke kai sai harara sama da kasa take yiwa mata. Tukur yayi gyaran murya ya ce " yaya ma kika ce sunanki?" Ta amsa cikin ladabi "Nihal Nuren Mubin. " Sadiya ta tabe baki ta ce " lallai su Nihal manya. Daman dan zaa shiga fim har sai an sato sunan 'yan gayu an maqala?" Tukur ya ci gaba da cewa " anjima zan aiko yaro ya zo ya raka ki gidan da muke sauke baqi mata 'yan Fim, a can za ki ci gaba da zama har mu ga yadda zai yi ." Nihal ta gyada kai ta yi godiya. Ya juya ya kalli dansa Isa ya ce ya dauki kofi ya je wajen me kosai ya siyowa bakuwa kosan naira dari, kokon ashirin a saka sukari na naira biyar. Nihal ta kalli yawun baccin da yayi qawanya a kumatun isa, dattin jikinsa da Ruwan tsohuwar butar da aka dauraye kofin, sai ta zabura ta dakatar da su ta ce ba zata sha ba ta qoshi. Tukur yayi shiru kamar mai tunani, domin ya ga tuwo da miyar kuka na dare da aka bata ma bata ci ba. Wannan dai ba zaa ce bata saba cin irin wannan abinci ba saboda qauyen da ta fito ma ya fi nan ragargajewa. Shin bata cin abinci ne kamar wata waliyyiya? Sadiya ce ta katse tunanin da ya tsunduma yana yi. Tsintsiya ta dauko ta wurgawa Nihal. Ta ce "a share falon da aka kwanta ki hada da tsakar gida. Ga wanke-wanke can ki yi min kafin a tafi in da aka ce zaa tafi. Yawon ta zubar, yawan rawa a titi aka fito. " Tukur ya dakawa Sadiya tsawa " ke ! Mahaukaciya wacce bata san darajar dan adam ba . Da kudin fim din dai aka auro ki da shi kike ci kike sha." Ya juya a fusace ya fice, yayin da Sadiya take tsalle tana direwa tana zazzaga masifa ta bi bayansa har zaure. Zafafan hawaye ne ya sirnano daga idanuwan Nihal.Ba aikin da aka saka ta ne ya bata mata rai ba, baqaqen maganganun da wannan kucakar take fada mata ne. Dukka masu aikinta kakaf sun fi wannan wayewa da arziki. Sai ta tuna wanda ya jawo mata wannan qasqascin, shine Mahaifinta, dan haka bai kamata ta ga laifin kowa ba . Cikin sanyin jiki Nihal ta dauki tsintsiya ta shiga falo ta fara shara, gashi bata saba ba a haka dai tana haki ta share ko ina. A bakin bandaki ake tsugunnawa a yi wanke-wanke, warin bandaki ne kawai yake busowa yana dukan hancinta. A guje ta fita qofar gida ta kwararo amai. Ta goge bakinta ta dawo ta ci gaba, ba tare da ta bari kowa ya gane ba. Ta na gamawa ta ji sallama a qofar gida ana cewa "wai Nohel ta zo a kai ta gidan da zata zauna in ji darakta Tukur." Muryar wani saurayi ce . Da farko bata gane da ita ake ba yadda yake kiran sunan kamar zai ce Hell fire . Sannan ya sake maimaitawa "baquwar nan da ta kwana a nan an ce ta taho da kayanta a kaita inda zata zauna. " Ta fada cikin sanyin murya "ganin nan zuwa." Ta shiga falo ta dauko buhun kayanta, kafin ta fito Sadiya ce a tsaye a bakin kofa tana kallonta a yamutse . Sadiya ta tabe baki ta ce " dauki buhun kayanki ki fito, kada a sibare min wani abu a jefa a buhu ." Wannan karon wani murmushi na tsananin takaici ne ya bayyana a fuskar Nihal, saboda maganar ta yi mata zafi sosai a zuci. Ta ce " Hajiya Sadiya ba kowanne talaka ne marar tsoron Allah ba, haka ba kowanne baqauye ba ne yake daukar wulakanci. Ki mutunta dan adam domin Ubangijin da ya halicce shi ma Ya daraja shi . Musamman mace 'yar uwarki da take neman yadda zata yi a rayuwa ya kamata ki tallafa mata, idan tana aikata wani hali marar kyau ki yi mata nasiha ta daina. Idan tana neman taimako ki bata daidai qarfinki, koda kuwa barin dabino ne. Allah Yana tare da masu taimako ." Sadiya ta tabe baki ta ce " a qara gaba malama, a tafi gidan hadaka gidan camama. An sami falo da luntsumemiyar kujera an baje an dauka anan zaa zauna shine dai haushinki. " Nihal ta yi murmushi ta gyada kai ta fice zuciyar cike da dariya yadda ta kira kujerar nan da sunan luntsumemiya. Tabbas Nihal ta tabbatar sai yanzu ta shiga makaranta don ada ba karatu ta yi ba .Yanzu ta shiga aji daya na furamare a karatun sanin rayuwa. Sai ta tsinci kanta tana farin ciki gami da murmushi. Murmushin ya kasa barin farfajiyar kumatunta, a sanadiyyar jin dadi don ta fara kwasar ilimi. "Ashe talaka ya fi kowa qyamar talaka dan uwansa? Domin mu masu kudi a kullum ana yi mana wa'azi akan kada mu wulaqanta talaka, mu taimaka musu da dukiyarmu. " Ta tambayi zuciyarta. Ta fita qofar gida tana wuwwurga ido tana neman mai yin sallama da ita . Hashim ta hango tabbas ta gane fuskarsa don ta ganshi jiya a cikin 'yan rawa a wajen daukar fim. Murmushin da ya ga tayi sai ya saka shi murmushi, suka gaisa sannan ya sake yi mata bayani . "Babu damuwa, mu tafi." Nihal ta fada . Tafiya suke yi Hashim yana bata labarin irin shaharar da yayi da yawan finafinan da ya firfito. Tambayar ta yake ko ta taba ganin Fim mai suna kaza? To ai shine abokin actor. Ba ta isa ta ce masa bata taba kallon Fim din Hausa ba. Dole ta amsa masa da "eh na gani ai na shaida ka, ka iya acting gaskiya ka burge kowa." Sai ya ji kansa ya fashe tabbas ya shahara, ya ci gaba da bata dubarun yadda zata bi ta karbu a masana'antar Finafinai . Wadannan hanyoyi kuwa su ne: ta yiwa manyan stars biyayya kuma dole ta dinga yawan shishshigewa daraktoci da furodusoshi. Ta yi masa alkawari zata yi hakan sannan ta yi masa godiya sosai. Tafiyar babu nisa sosai, suka isa wani gida na suminti ne mai dauke da dakuna tara . Tabbas gidan haya ne kowanne daki mata ne daga adadin biyar zuwa shaida . Amma wasu dakunan na matan aure ne . Abin mamaki kai tsaye ta ga Hashim ya fada cikin gidan, su ka isa bakin qofar wani daki, ya kwalla kiran sunan Mami Harka. Mami Harka ce ta bayyana a bakin qofa, fuskar nan ta dafe ta yi jajawur saboda bilicin, an sha jan janbaki da hoda ga shudin eye shadow kai kace da tabarya ta yi kwalliyar, ga hudar hanci an makala katuwar barima ana taunar cingum kamar wata saniya, duk a cikin shikashikan wayewa ne. Dariya ce ta kusa subucewa Nihal sai ta daure. " Irin wannan kira haka kamar na kashe 'yar sarki .Hashim meye ? " Mami Harka ta fada cikin yamutsa. Hashim yayi dariya ya ce " ranki ya dade super star ayi min afuwa. Ga baquwar da darakta ya ce a kawo, za ku zauna tare. " Ta harari Nihal sama da kasa ta yamutse fuska. Nihal ta zabura ta duka ta gaishe ta. Sai Mami ta ji kanta ya fashe, haka sai ta sauke haushin ta da ta fara ji . Ta ce " shige ciki za ki ga tabarma baqa nan ne kwanarki. " Hashim ya ce " ba zaa bata aron 'yar katifa ba ma sai tabarma?" Ta harare shi ta ce " ka ji dan rainin hankali. Waye ya bamu tabarmar ma a lokacin da mu ka zo? Idan ta yi fim sai ta tara kudin katifarta kowa da kudinsa ya siya ." Nihal ta shiga dakin ta iske dakin tas-tas a share kuma qato ne sosai, katifu guda hudu ne a jejjere, kusa da kowacce katifa akwatuna ne masu taya. An malala sabuwar leda ga sabbabin bokitai da butoci sai qamshin turaren wuta ne yake ta tashi. Sai Nihal ta ji dan sanyi a ranta. Ta ajiye kayanta a gefe amma bata zauna ba ta sake fitowa ta same su a bakin qofa a tsaye har yanzu su na magana . Nihal ta dubi Mami cikin ladabi ta ce " Mami harka dan Allah ina son ki bani aron bokiti zan yi wanki ." Mami ta harare ta, ta ce " ai baki kira ni da kalar sunan da zan iya ara miki bokiti ba ." Hashim ya ce "Aunty Mami zaki ce , tuba take ranki ya dade." Nihal ta dukar da kai ta ce "Anty Mami ayi hakuri." Mami ta baje katuwar murya mai kama da muryar maza ta ce " ban ma fada miki dokokin zaman dakin nan ba. Ba na son kazanta dan na ga alamar ki tsabtar ki ragaggiya ce, kalli kayan jikinki duk dauda.Ki na mace wai kuma da sunan kin zo ki shiga harkar fadakarwa, ai a jikinki ya kamata a fara ganin misali. Ba na son raini, babu aron kaya ki nemi komai naki, banda kawo mana gayyar qawaye cikin daki. Banda shaye-shaye da kawo samarin banza cikin daki. Banda sibarannabaiye. " Da alama Nihal bata San wannan kalmar da ta fada ta karshe ba. Dan haka sai ta nanata ta "Sibaren- na -bayye." Hashim fahimci bata gane ba don haka sai ya fassara mata hausar. Ua ce " bi ma'ana bata son sata." Sai Nihal ta sunkuyar da kai qasa hawaye ya cika mata ido, tana jin zafin wannan kalma ta sata da ake danganta ta da ita. " Shiga ki dauko baqin bokintin, in an gama a wanke a dawo min da shi." Mami ce ta fadawa Nihal . Nihal ta yi godiya ta dauko buhun kayanta da bokiti ta fito. Mami ta na yamutsa kamar ta ga kashi ta nuna mata bakin famfo da igiyar shanya . Hashim ya lura Nihal bata da omo ko sabulu kuma sai ya tuna cewa har sai da darakta ya cikawa Babanta kudin acaba dan haka bata da komai. Da sauri ya fita waje babu jimawa sai gashi ya shigo dauke da sabulu kato, da omo da sabulun wanka gift ya miqa mata. Ta jika kayan a bokiti kafin ma a cuda ruwan yayi bakikirin kamar ruwan kwata. Ta ji dadi sosai da kyautar da ya yi mata . Mami Harka ce ta fito rataye da gyale da jaka, ga wani takalmi mai tsini tana tafe tana yanga ana dage hannu. "Zan fita, ke baquwa ga dakina nan a hannunki kada in rasa komai nawa. Idan za ki fita ga kwado nan akan windo ki datse min. " Mami ce take bada umarni. Nihal ta amsa cikin ladabi . Hashim ya ce " za a fara daukar shiri Fim din Tataburza ko? Nima ina cikin Fim din, Darakta ne ya aike ni Kano amma yanzu zan dawo in Allah Ya yarda, zan same ku acan. An ce a hanyar Gaya zaa yi shooting din ko ? " Mami ta ce " sai ka zo." Ta fice tana karairaya. Ya fuskanci Nihal ta rasa yadda zata cuda kayan, sai cakudawa take kamar ta sami kwado yauwa ko na zogale. Hashim ya cika da mamaki . Ya yi dariya ya ce " ke yanzu kina nufin a haka kayan nan masu uban datti zasu fita . Ah shiyasa mana kayan suka yi datti da yawa, ashe jika-jika kike yi. Kawo ki gani ." Ya karba ya dinga sabawa da qarfi sai baqar kumfa ce take kwaranya. Ya daga ido da sauri ya kalle ta sannan ya sake kallon kumfar. Ko bai yi magana ba Nihal ta san abinda yake nufi, kunya ta rufe ta, hawayen takaici ya cika mata ido . Sallama su ka jiyo a zaure, muryar wani mutum ne ya ke magana ya ce " ana neman baquwa me suna Nihal Nuren Mubin." Sai ta ji gabanta ya fadi ta leqa da sauri ta kalli mutumin, bata taba ganisa ba tunda take a duniya. Ya tambaya ko ita ce Nihal? Ta masa da eh ita ce . Sai ya fara yi mata bayani, nan da nan ta gano bakin zaren. Dan haka sai ta nemi da su fita qofar gida su qarasa maganar a can, don bata son Hashim ya jiyo abinda suke fada. Mutumin tsaf da shi a waye yake yana ta qamshin turare, ya gabatar mata da kansa, ya ce sunansa Shazali shi dan asalin nan garin ne amma ya fi zama a Kano . Babanta Alhaji Nuren ne bar kudi ya ce a dinga siyo mata abinci safe da rana da dare daga Kano. Abinci masu kyau da lemo da ruwan roba ana kawo mata. Sannan kuma ya ce duk wani abu da take so akwai qaton shagon da zata dinga zuwa tana karba. Sai ya hau yi mata kwatancen shagon don ya zaci 'yar gari ce. Sai ta yi murmushin takaici duk da ta ji dadi sosai a ranta. Ta yi imanin duk in da mahaifinta ya ke yanzu ya fi ta shiga damuwa da tunanin halinda take ciki. Ta san ba zai bari Mummy da sauran yayyanta su san in da ya kawo ta ba . Zasu zaci wani katafaren gida da kudi zai bata wanda zata fara shirya fim dinta. Ya miqa mata wasu manyan ledoji guda biyu, daya tana dauke da robobin take away guda uku manya . Sannan ya miqa mata wata katuwar leda mai dauke da flask din ruwan zafi da kayan shayi. Ta gyada kai ta yi godiya . Sai ya nemi data bashi lambar wayarta in zai aiko da sako ya sanar mata ko in ta na bukatar wani abu ta kira shi. Ta ce bata da waya, dan haka sai ya rubuta lambar wayarsa ya bata. Ta karba kamar ranta ba ya so . Shazali dai ya tafi zuciyarsa cike da mamaki ya kasa gane abinda ya ke faruwa anan. Shi dai ya san an bashi kwangila ta maqudan kudi kuma zai cika aikinsa. Ta shiga cikin gida amma sai ta boye kayan a cikin mayafinta . Hashim ya kalleta ya ce " ashe kin san mutane a garin nan?" Sai ta zabura ya girgiza kai ta ce " a a ban san kowa ba, abinci ne aka kawo min 'yan uwanmu ne zasu je Gaya sai suka tsaya suka bani. " Ya ce " Allah sarki! shiga daki ki ci, zan karasa miki wankin in shanya ." Ta yi ta godiya har ta shige daki tana gode masa gami da addu'oi na albarka . Ta ji dadin hakan sabo da masifar yaunwa take ji . Ta na shiga ta haye kan tabarmarta ta bude kayan nan, sai ta ji kamar sakon daga aljanna aka kawo mata don farin ciki. Kaza ce guda a gashe ta sha kayan hadi, daya robar dankalin turawa da soyayyan kwai , daya robar kuwa fried rice ce da nama, ga lemo kala-kala da ruwa masu sanyi . Ta gyara zama ta dira a kan kazar nan, tana hadawa da dankali da wainar kwai tana cikawa gami da korawa da lemo. Tabbas ta na jin baqar yunwar kwana da kwanaki babu abinci, rabon ta da cin abincin kirki ta manta daga biskit sai dan lemo, ta dade bata iya ci tun a London. Saboda fargaba da furgici da tunanin hukuncin da zaa yanke mata, amma yanzu ta san makomarta an yanke mata hukuncin hankali ya kwanta . 11/14/21, 7:19 AM - MY MTN 2: GABA GADI EP 7 Ta ci rabin kaza da dankali da kwai gaba daya ta ji ta koshi har kamar ma koshin zai zame mata illa. Ta na zaune tana tunanin yadda za ta yi domin tana so ta taimaki Hashim ta bashi sauran ya ci , amma bata so ya gane tana da wani abu ta fi so su dauke ta yadda su ke daukar ta din . Ga shi har omo da sabulu ya siyo mata don ya na zaton ba ta da ko kwabo. Idan ya ga kaji da kwai ai zai yi tunanin tana da wani abu ashe. Amma yadda ya taimaka mata ta so ta taimake shi don ta tabbatar ya dade bai ci kaza da lafiyayyen abinci irin wannan ba. Hashim ne ya katse mata tunanin da ta tsinduma a ciki . Ya ce " Nohel na shanya miki, zan tafi ." Ta yi dibi-dibi ta zaro dubu daya daga cikin dubu biyar din da mahaifinta ya bata zata bashi sai ta tuna da cewa ita fa talaka ce liqis, ina ita ina kyautar dubu daya . Dan haka sai ta mayar ta miqe da sauri ta fito tsakar gida . Ta yi dariya ta ce " har yanzu baka iya kiran sunana ba ? Nihal ne ba Nohel ba ." Ya kwashe da dariya ya ce " sunan ne kamar sunan Yamalawa wato larabawan Yemen, gashi ke kuma ba daga Malam madori kike ba balle in ce larabawa ne . Amma dai kin yi kama da baqaqen buzaye. " Ta girgiza kai ta ce " ko daya, ni bahaushiya ce ." Ta yi masa godiya sosai ta raka shi har zaure . Har ta juya zata tafi sai ya zabura ya tsayar da ita. Ya ce " kin ga da kin shirya da na biya miki kudin mota mun tafi Kano, daman wajen wani babban darakta aka aike ni, da sai in gabatar da ke in an sami Fim a saka ki ." Nihal ta ce " nan gaba sai in bika . Yanzu dai idan ka dawo ka zo ka raka ni wajen tela ta dinke min kayan da su ka yage kuma a rage min girman wuyan, wasu zannuwan kuma a mayar da su siket. " Ya kalle ta cike da tausayi sannan ya ce " na ga kayan ma duk sun tsufa kamata yayi a sami wasu atamfofi ko biyu ne a dinka kawai, kada a bata lokaci akan kayan da suka tsufa . Amma bari a biya ni kudin aikin fim dina ko atamfa leda - leda 'yar dubu bibbiyu sai in siya miki, na yi miki wannan alkawarin ." Hawaye ne ya cika mata ido sai ya lura da hakan don haka sai ya gaggauta barin wajen dan kada ta sa shi kuka shima . Ta sulale ta zauna a kan dakilin qofar gida tana ta rusa kuka . Ashe haka rayuwar talaka take kasancewa abin tausayi? Wani ya tausaya masa wani ya wulakanta shi . Allah sarki Hashim kai ne mutum na farko da ka damu da ni ka taimake ni a yadda nake talaka . Almajirai take kallo kaya a yayyage suna ta neman yadda zasu yi su rayu. Ta tashi da sauri ta shiga gida ta raba shinkafar nan gida biyu ta kazar ta zo ta basu . Zo ka ga wawaso da danbe. Suka dinga jero mata mata addu'oi. Tabbas ta ji dadin wannan addua "Hajiya Allah Ya karba. Allah Ya sa ki ga annabi. Allah Ya biya miki bukatunki na alkhairi. " Sai sake zabura ta zaro naira dubu daya ta basu ta ce su je su ci wani abinci . Sai addua ta lunku akan ta da . Kunci da zafin zuci da su ke ta addabarta sun gushe . Tabbas sadaka maganin masifa ce, ta kudiri aniyyar kullum zata dinga yin sadaka tunda ga almajirai nan sun wadata a ko ina. Lallai ya kamata ka kasance mai yawan sadaka a rayuwa idan kana da shi . A London ko a unguwanninsu na masu kudi ga abin da zaka bayar sadakar amma babu mabuqatan. Ta jima a zaune ta na kallon masu wucewa da yake gidan yana daf da babban titi. Sai ta ga kamar kowa a gigice yake, wasu suna tafiya su na surutai wasu kuwa tuntube suke a sanadiyyar rashin nutsuwa. Da yawa shigarsu ta tsumma ce 'yarkace- yarkace da su. Kujajjun takalma ne sanye a qafafuwansu, kaushi da faso kuwa sun wadata ba za ka taba cewa qafar bil'adama ce ba, babu mata babu maza , babu babba babu yaro . " Allah sarki 'yan qasata, qabilata, In har za ku kalli Finafinaina da nake niyyar yi nan gaba tabbas zan kawo muku gyara da mafita a rayuwa. Allah Ya taimake ni Ya cika min burina. Amin ." Nihal ta fada yayin da ta tashi ta shiga gida. A daki ta zauna ta na jiran kayan su bushe sannan tayi wanka ta canja. Sai ta ji zaman kadaicin ya ishe ta akwai wahala babu wuta balle ta ji fanka, babu talabijin, babu waya da zata yi chatting tayi browsing. Ta shiga wanka ta dade tana dirzar jikinta saboda da dattin da tayi da yawa.Ta saka wankakkiyar atamfa sai ta ji wasai babu wari sai dai qamshin omo. Da yamma Hashim ya dawo daga kano ya kawo mata tsarabar biredi, dariya ce ta subuce mata ya zaci murna ce nan kuwa mamaki ta yi yadda ake tsaraba da biredi . Ya takura mata akan zaman daki ba zai yiwu ba ta zo su je wajen daukar shirin da ake yi, idan su na ganinta a wajen shine zasu tausaya mata su saka ta a cikin shirin, kuma shine abinda ya kawo ta garin kenan . Su ka isa wajen da ake daukar shirin ta na gaishe su bata ishe su kallo ba ma, haka ta lura Darakta Tukur bai sakar mata fuska ba . Ta na gefe tana kallokawai. Da magruba ta kawo kai sai aka tashi kowa ya watse. Mami Harka ce ta kalle ta a shelaqe ta ce ta dauko mata jakar kayanta ta biyo ta da ita zuwa gida . Haka ta dauka ta na biye da ita har suvka iso gida . Sai suka iske 'yan dakin sun daddawo, Asabe da Iyantu. Bayan Nihal ta gaishe su sai Mami ta gabatar da ita . Suvka kwashe da dariya suka tafa . " Au ita ma Fim din ta zo shiga?" A hakan ? Iyantu ta fada cikin gatsali. "Kuma an saka ta ?" Asaba ce ta tambaya. Mami ta ce " ina fa ? Ai za ta dade ta na jira . Shiga Fim wasa ne? Ki taho yarkace- yarkace da tsumma ki ce kin zo shiga Fim. Babu wayewa, babu kayan gayu. Babu 'yar farar farar nan ta bilicin, lallai za ki dade." Asabe ta ce " amma yarinyar tana da fata mai kyan gaske mai sheqin duhun haske ." Ta zo ta shafa kumatun Nihal . Nihal ta qufula, hakuri kawai take bawa zuciyarta . Ba ta iya jure wulaqanci. Kallonta suke yi sama da qasa kallo na qasqanci . Iyantu ta cewa Mami "kin fada mata dokar zaman dakin nan kuwa?" "Na karanto mata komai da komai, amma na ga alama ta na da saurin daukar karatu, dan na ga ko ina tsaf-tsaf ta sake saharewa. Na mata fadan sata in ma tana yi ka da ta taba na mu ." In ji Mami. "Ta gwada tabawa ma ta ga yadda ake fasa bakin yarinya ." Asabe ta fada yayin da ta ke shirin shiga wanka . Ko tari Nihal bata yi ba balle ta basu amsa, ta tashi ta fita ta yi alwalla ta zo tayi sallar magrib.Ta jira lokacin sallar isha'i ta tashi ta yi.Ta dade ta na addua ta na neman kariya da juriya da haske akan abinda ta tunkara. Wasa-wasa Nihal ta yi sati uku ta na wuni a wajen daukar shirin fim, har wasu kauyukan kurkusa take raka su amma baa taba saka ta ba, sai kyara da aike kawai take sha. Abinci kuwa wani lokaci idan Mami ta ci tana rage mata, ruwan pure water ma sai wanda ya tausaya mata yake siya mata. Amma basu Kula da cewar idan ta karba ma bata sha kuma bata ci sai dai ta faki ido ta fita waje, ta bawa almajirai. Abincinta a boye take zuwa ta karbo a wajen Shazali ya nuna mata shagonsa haka ruwan roba take sha don tsoron shan pure water take gani take zata kamu da cuta. Idan zaa kai dare bata taba shan komai ba har sai ta dawo . Ta na ta karantar yadda ake daukar Fim da yadda 'yan Fim suke acting. Tabbas akwai kurakurai masu dinbin yawa, za ta iya cewa ta basu maki 2%, kenan wannan ba Fim sunansa ba idan ta hada da yadda qa'idar fim take . Darakta Tukur ne ya tausaya mata ya dube ta ya ce " ke yarinya zo karanta wannan script din kawai ki yi mana wannan sin din saboda Maimuna bata nan mun gaji da jira ." Nihal ta cika da murna ta miqa hannu za ta karba sai. Amina 'yar kwalisa ta zabura ta ce " waye zai karanta script? Wannan kucakar? Kai ma darakta da gangan ne ka so ka bata lokacinka. A ina ta taba zuwa makaranta balle ta iya karatu? Ai kawai ka fada mata da baki in kwakwalwar zata iya riqewa." Maimakon darakta ya tsawatar sai ya yi dariya ya ce " Amina baki da dama .To shikenan bari in fada mata ." Ya juya ya kalli Nihal ya ce " kada ki tsorata kada muryarki ta yi karkarwa in kin ga an dora kyamara a kanki. Abinda ake so ki yi shine ki zo da gudu ki ce kanwata ce ba lafiya ka taimaka a kaita asibiti . Sai ki durqusa kina roqar mai babur din. Za mu saka miki ruwa a ido yayi kamar hawaye." "Yauwa ga Maimauna ma ta zo gara ta karbi sin din ta, wannan bata mana Fim zata yi . " Amina 'yar kwalisa ce ta fada cike da murna . Dirakta ya juya da sauri ya kalli Maimuna wacce ta sauka daga kan babur. Ya yi dariya ya ce " Shikenan ke baquwa koma ki zauna anjima zaa yi rawa zan saka ki a cikin 'yan rawa ." Mami ta zabura ta ce " rawa kuma, wannan fa kamar ba zata iya komai ba . Kada a zo ana bata mana lokaci ka san mutumin da bai taba yin fim ba, fama ake yi da shi ." Nihal bata yi magana ba sai ma tausayi da suke bata, ta koma ta zauna, zuciayarta tana tafasa kamar zata qone. " wannan yarinyar tausayi take bani wallahi baa taba saka ta a Fim ba sai dai ta yi ta wahala abin tausayi. Gashi zaa saka ta aka yi mata bukulu. " Najaatu ce ta fadawa Mami. Hawaye ya kwaranyo daga idanuwan Nihal dan ta fara jin tausayin kanta da kanta. Najaatu ce ta tsaya a kanta ta ce " daina kuka qawata zaa saka ki, haka mu ma muka yi mun sha irin wannan wahalar kafin a saka mu. " Hashim ne ya qaraso inda suke shima an gama yin na sa sina-sinan. Ya ce " au Nihal kuka kike ? Meye abin kuka ? Darakta ya ce zaa saka ki a cikin 'yan rawa. " Nihal ta goge hawaye ta kirkiri murmushi ta ce " ba kuka nake yi ba fa . Ya wuce ai. " Da la'asar sakaliya bayan ta idar da sallar la'asar Hashim ya taho da sauri ya ce " Nihal ki zo in ji darakta da sauri . Ta tashi da sauri ta isa wajen da dandazon mutane suke . " yauwa ku bata anko daya ta saka zata shiga cikin 'yan rawa. Doguwar rigar atamfa leda-leda ce aka dinkawa 'yan amshin rawa da waqa. Isma'il ne a bangaren Kula da sutura dan haka da ya dubi yanayi da tsayin jikinta sai ya zabo mata riga daya ya miqa mata daidai da jikinta . Abin mamaki sai Nihal ta girgiza kai ta ce " ba zan yi rawa a Fim ba ." Isma'ila ya maimaita cikin daga murya cike da mamaki " ba zaki yi rawa a Fim ba ? Kamar yaya ? " Nihal ta maimaita cike da gadara " ba zan yi rawa da waqa a fim ba saboda ba ya cikin al'adarmu. " Hankalin kowa ya juyo kanta mamaki marar musaltuwa ne ya bayyana a kan fuskokinsu. Aka zagaye Nihal ana yi mata tambayoyi na isgilanci da raini. Amsa daya take bayarwa ita fa ba zata yi rawa a fim ba, acting ko wanne iri ne a bata zata amma banda rawa. Amina da Mami suka yi shewa suka tafa suka ce " lallai yarinyar nan 'yar yi ce . Idan ta zama super star wacce gadara za ta yi ? A haka ma a cikin tsumma tana girman kai ." Ran darakta Tukur yayi mummunan baci . Ya harare ta ya ce "sai kiyi ta zama a haka, kuma idan kika cika wata daya a dakin da kike zaune ki nemo kudi ki biya haya, yanzu ma roqarsu na yi na ce wata daya zasu baki kyauta. Ko ki hada kayanki ki tafi garinku, zan kira ma mahaifinki ya zo ya dauke ki dan baki da wani amfani ." Ta fusata ta fice daga wajen, Hashim ya bi bayanta da sauri yana kwalla mata kira ta haye acaba ta tafi gida. Maganar ake ta yi kowa yana tofa albarkacin bakinsa. Sun fi zaton saboda baa saka ta a sin din Maimauna ba ne ta ji haushi . " Amina ta ce "tunda na ga yarinyar nan na ji jinina da na ta bai hadu ba na tsane ta ashe bakin hali gara ta . In har ina garin nan ba zata taba zama jaruma ba kuwa wallahi. " Da daddare Hashim ya zo qofar gidan su Nihal yana ta yiwa mata Nasiha akan ta zo su je su bawa darakta hakuri akan abinda ta aikata. Da farko ta qi yarda, sai da ya dage sannan ta bishi. Gidansa suka nufa aka yi musu sallama da shi, ya fito qofar gida. Da ya ga Hashim tare da Nihal ne sai ya juya a fusace zai koma cikin gida . Da sauri Hashim ya kama hannunasa ya riqe ya durkusa har qasa yana bada hakuri. Nihal ma ta zo ta durqursa ta na bashi hakuri. Darakta Tukur ya more albarkacin bakinsa, ya fadi duk wata baqar magana da ya tanadar mata sannan ya ji sanyi a ransa. Daga baya ya hakura . Bayan an yi haka da kwana biyu ne Darakta Tukur ya kira ta, ya ce ta shiga wani Fim mai suna ' A TARE- ATARE. Narka-narkan shirme ne cikin shirin babu ma'ana ko daya. A ka bata matsayin budurwa da take taimakawa boka da dakan magani. Kowa ya tsaya cak ya na so ya ga karkarwar da Nihal zata yi idan aka dora mata kyamara kamar yadda sababbin shiga suke yi a ranar farko . An cika da mamaki da suka ga ta dake kuma babu alamar tsoro ko jin kunya a tare da ita . Duk abinda aka fada mata ba shi ta fada ba amma da aka lura sosai sai aka ga maganarta ta fi yin ma'ana kuma ta fi isar da saqon da ake buqata. Har da su Amina sun fara yi mata cari akan ta fadi abinda baa ce ta fada ba sai Darakta da masu daukar hoto su ka jinjina mata har suna tafa mata. Ran su Amina ya baci hankalinsu ya tashi da suka ga ana ta qarawa Nihal yawan sina-sinai. Gashi Amina ta yi rantsuwa in har tana raye ba zata taba bari Nihal ta zama Jaruma ba . An gama daukar shiri kowa yana kokarin hada kayansa, Nihal da Hashim sai dadi suke ji su na tafe su na labari. Sun zo wucewa Amina na zaune sai kawai ta sakawa Nihal qafa ta yi tuntube saura kadan Nihal ta kifa Hashim ya tare ta . Amina na tashi tsaye sai ta kifawa Nihal mari, ba wacce aka yiwa marin ba ma wadanda ke kusa sai da suka firgita. Nihal ta kama kunci ta durqusa domin ta fita daga cikin hayyacinta har ta rasa duniyar da take ciki . " yauwa qarawa shegiya. " Iyantu ta fada a lokacin da take sheqa dariya. Amina 'yar kwalisa tana tsaye a kan Nihal tana gunzuma mata zagi wai taka ta ta yi . Anan ne Darakta Tukur ya fusata ya nuna bacin ransa sosai har ya bawa Amina gargadi na qarshe in har ta qara zagi balle marin wata zai cire ta daga Fim kuma ba zai sake saka ta a wani Fim ba nan gaba. Mazan wajen da ma wasu daga cikin matan sun bawa Amina rashin gaskiya kuma kowa ya ga abinda ya faru, Amina ce ta saka mata qafa da gangan. Har yanzu Nihal na tsugunne ta na so zugin ya ragu ta dawo wannan duniyar da muke ciki kafin ta yi tunanin matakin da zata dauka . Domin ta tabbatar ba zata taba bari a mare ta a banza ba , ta san darajar kanta ta san hakkin kanta . Hashim ne ya tari fadan yana zagin Amina tana zaginsa. Ba su ankara ba Amina su ka hango an cillo ta can gefe, kafin ta yunkura ta miqe an bi ta da mari kwarara guda uku . Baa bar ta haka ba da qafa aka dinga ball da ita . Nihal Nuren Mubin ce ta nuna mata ita sojoji ne suka bata horo tun tana goye a baya . Qashinta yayi kwari sosai ya na lankwasuwa ko ta ina, ta yi tsallen kwado kala kala, ta yi fareti, an daga kafafuwanta sama kanta a qasa. Duk yayyata ne suke gana mata wannan azaba tun tana qarama. Dambe kuwa ita da Hamza da Mu' awiyya babu wanda baa yi ba, su ne saqonta. Allah ne ya raya ta kuma mahaifiyarta tana tsaye a kanta ba dan haka ba da mazan nan sun karairaya . Nihal bata fada amma idan ta fara fada ba irin fadan mata take yi ba, na maza ne mazan ma sojoji. Hohoho masu kawo gagaji wajen ceton Amina ma sun sami nasu elbow din, fadan chinees kawai take da qafa take harbi. " ku taimake ni ku janye ta zata kashe ni ." Amina take fada cikin wahalalliyar murya . Dakyar maza suka raba fadan nan . Nihal ta juyo da jajayen idanuwanta ta harari sauran matan su Mami kenan ta ce " saura ku ku yi hankali da ni ." Dankwalinta da takalmanta ma'ana kuzajjen silifas dinta Hashim ya daukowa Nihal ya bata ta saka. Darakta Tukur cewa yake " ta yi min daidai, domin kun takura mata kun kai ta qarshe ne ." Aka tafi da Nihal gida dakyar ta yarda ta tafi . Daga wajen shooting gidan me gyaran targade aka wuce da Amina 'yar kwalisa. Targade hudu ne wurare mabanbanta. Dadi ya kama Hashim tabbas Nihal ta yi masa daidai domin baya son sokoncin nan da take yi duk su na ta aikenta da kyara. Mami ta shigo daki a fusace ta ce iske Nihal ta harare ta ya ce "tattara kayanki ki bar dakin nan, daga yau zuwa gobe zama mu dake ya qare." Ta razana da ta ji amsar da Nihal ta bayar " babu in da zan je ." Nihal ta ja fulo ta kwanta . Sai aka hau kallon-kallo Mami da sauran 'yan dakin .Ba tare da kowa ya qara magana ba . Asuba ta gari Nihal Nuren. Bayan sati guda ne Hashim ya zo ya ce Nihal ta taho ga babban darakta daga kano ya zo zasu dauki wani shiri, tana so ta roqe shi ko zai saka ta a wasu Fina-finan na sa. Ta tashi da sauri ta biyo shi su ka isa wani gida da suka ara zasu fara wani shiri . Nihal da Hashim suka Shiga falon kai tsaye, wajen darakta Idris suka nufa suka durqusa suka gaishe shi yayin da Hashim ya nuna Nihal ya ce ita ce yarinyar da ya taba bashi labari sabuwar zuwa da ya taimaka ya saka ta a Fim . Kallon Nihal yayi ya yamutse fuska ya tambaya cikin isgili " wa zan saka a Fim,wannan yarinyar ?" Jikin Hashim yayi sanyi suka koma gefe suka rabe yayin da darakta ya ci gaba da harkokinsa. Nihal ta ga mata wayayyu da mazan ma, ba kamar na kauye ba tabbas wadannan 'yan Fim din birni ne . Su na ta kallonta dai tana kallonsu. Anan suka wuni babu Wanda yake kallonsu. Abinda ya bawa kowa mamaki shi ne yadda ta ke nunawa mai kyamara yadda zai saita kyamar da kuma yadda mai riqe fitila zai dinga riqewa. Sai gashi ana tambayar ta wasu abubuwan idan sauti ya qi fita ko murya tayi karkarwa. Actor mai tashe Bashir Auta sai yanzu ya karaso a cikin luntsumemiyar motarsa fara mai baqin gilasai Gaisuwa da shishigi qananan suke yi masa , Hashim ya zabura ya ce da Nihal " kin ga Bash Auta ." Ta tambaya " waye shi?" Mamaki ya kama Hashim sai ta tuna ta yi sauri ta ce " Au bash Auta ne na gane shi ." Yana tafe yana qobarewa yana taqama. Aka fara daukar shiri, shine zai yi tsalle daga kan bishiya ya diro qasa. Su ka dinga shirme sai da Nihal ta tabbatar babu abinda suka sani sai ta yi carab ta basu shawara akan a daura masa igiya ya diro amma a zahiri ana riqe da shi . Ta nuna musu dubarun yadda zasu yi abubuwa da yawa.Daga nan sai aka bata wani sin daya aka ce ta shiga. Hohoho! Nihal bata gama da arnan gabar qauye ba ta zo ta qara tsokano 'yan birni. Rayukan jarumai mata 'yan birni ya baci. 11/14/21, 7:19 AM - MY MTN 2: GABA GADI EP 8 Su ka hau yi mata gani-gani da harara da yamutsar fuska kamar sun ga kashi. Ita da Hashim suka cika da murna saboda ya tabbatar mata wannan babban fim ne kuma babban kamfani gashi ta fito a ciki . Da yamma sai aka kawo motoci aka ce su shiga zaa tafi garin dutse wajen duwatsu anan ne zaa ci gaba da shooting . Nihal da Hashim ba su saka ran bin su ba suka koma gefe suka tsaya su na kallo. Darakta Idris ne ya hango su tsaye ya qaraso in da suke da sauri ya ce su shiga cikin babbar mota su ma a tafi da su . Su na shiga suka zauna sai suka yi kicibus da manyan hararar Jarumai har da alakoron tsaki. Nihal ta sunkuyar da kai qasa ta ce a ranta " wannan tsanar ta menene ? A baya a rayuwata kowa sona yake ban taba ganin wanda ya tsane ni ba sai a garin nan ." Su ka isa garin Dutse lafiya amma ba cikin gari ba ne wajen gari. Aisa wacce aka yi mata laqabi da Aisa buzuwa Ita ce Jarumar fim din, akwai sin din da za ta yi gudu sannan ta yi tsalle ta dane wani tsauni. Abin haushi ta kasa yin katabus. Nihal ta fada a ranta "wannan wasan yara suke yi ko Fim? Abinda ake so a dinga yinsa kamar da gaske kashi 80% da jikinka ake so ka yi kyamara ce zata qarawa sauran 20% din ." Nihal ta ga abin nan ba zai taba tafiya daidai ba sai ta je ta fara nunawa Jaruma Aisa yadda za ta yi, da abu ya fassaka daraktan birni Idris Hayat ya ce Nihal ta saka kayan Aisa ta shiga ta yi wajen da duk zaa yi tsallen in ya so sai a dora fuskar Aisa. Haka kuwa aka yi sun ga abin mamaki tashi sama kawai take yi ta na dira. Basu taba yin Fim da aka taba yin wannan bajintar ba. An sha tafi da ihu da jinjina domin ta burge su matuqa. Aka gama wannan aka zo wajen fada, maza ne 'yan daba su ke rigima a tsakanin wannan kungiya da waccan kungiyar. Nan ma Nihal ta ga shirmen yayi yawa kaiwa dukan daban faduwar daban. Haka idan aka kai sara kwata kwata babu alamar an kusa taba wanda zaa sara sai ka ga mai saran yayi can wanda aka sara ya yi wani wajen. Dole rayukan masu kallo ya baci zasu ce an raina musu hankali. Abin mamaki sai ga Nihal tana koya musu fadan canis. Juyi take tana tashi sama tana harbin iska. Tabbas wannan daga gani ta je makarantar koyon kareti ba a gari kawai ta koya ba. Ah sai mamaki ya sake mamaye zuqatan daraktoci da furodusoshi har da jarumai mata da maza .'Yan kallo kuwa baa magana ihu ake ana tafi. Sunanta carab a bakin kowa fadi suke "sai Nihal Nuren an gaishe ki." "Wannan yarinyar kuwa a qauyen nan ta ke?" Darakta Idris ne tambaya . Darakta Tukur ya ji kansa ya fashe " eh a hannuna mahaifinta ya damqa min ita, ai training dina ce." Darakta Idris dai ya kalle shi bai sake magana ba . A ransa ya ce " training dinka a ina? Finafinan naka ba mu na gani ba.Yaushe aka taba yin irin wannan bajintar?" Darakta Idris ya rufe jarumai mata da fada yana fadin "kun ga yadda yarinya take acting da zuciya daya kamar da gaske, nan da nan ake kammala sin amma ku ayi ta fama . Lambar wayarta Darakta Idris ya tambaya ta ce bata da waya. Tukur yayi sauri ya bashi ta sa ya ce shi zaa tuntuba idan ana nemanta. Nihal da Hashim sun fito bakin titi su na neman mota zuwa wudil ko acaba da zai kai su tasha su hau motar Wudil sai gobe kuma in Allah Ya kai mu. Jaruma Aisa da Hasiya Carkwai ne suka biyo su a baya . Basu ankara ba suka ji an dira a gabansu, fuskokinsu a turbune babu annuri. Aisa ta kama qugu tana girgiza ta ce " ke baqauyiya 'yar iskar qauye! kada ki sake ki shiga gonata yau dai kin yi nasara. Gobe zaa dawo location kada ki kuskure in ga qafarki anan idan kuwa kin qi tabbas duk abinda ya biyo baya ke ki ka sani." Hasiya carkwai ta ce " ki fada mata kawai hukuncin da zamu dauka , 'yan daba zamu sa su kakkarya miki qafa na ga yadda za ki koyawa mutane fadan canis din ." Hashim ya fara basu baki gami da lallashi yana fayyace musu Nihal ba da niyyar ta kwance musu waje ta zo ba alkhairi ne ya kawo ta . Nihal bata ce komai ba ta tsayar da mai acaba za ta je ta hau. Hasiya carkwai ce ta figo ta sai ga hannun atamfar jikin Nihal ta yage tun daga sama Nihal qasan yana reto. Aisa ta ce " banza qazama kalli tsummar atamfar da take sakawa wai a haka zata ce zata shiga huruminmu. Ke da kika samu ma har kika tsaya a kusa da mu muna magana, ba na'ima ba ne. Kin isa ki ganmu ma in a kano ne. " Dan acaba ne ya shiga fadan ransa ya baci ya ce " Haba bayin Allah Yaya zaku dinga zaginta kuna wulaqanta dan kunga bata magana. Ni ma fa dan iskan gari ne kada ku zaci dan kuna yin fim kun fi kowa?" Nihal ta haye babur ta ce su tafi . Hashim ya biyo su da gudu ya na tsayar da su. Nihal ta ce kada su tsaya su tafi kawai. A hanya kuka mai tsanani ya rikito mata ta yi ta kuka, dan acaba yana bata baki. Ta ce tasha zai kaita zata tafi Wudil ne , nan da nan ya ce shima can ya nufa dan haka su tafi kawai . Kura da iska duk sun cika mata ido haka ta daure tunda motocinta masu Ac sun yi mata nisa. Ta nuna masa inda zai kai ta, ba gidansu ba ne shagon Shazali ne in da take zuwa ta karbi abinci. Nihal ta tambaye shi kudinsa sai ya ce ta bar shi saboda ya tausaya mata . Ta dauko naira dubu daya ta bashi da yaqi kaba sai ta tura masa a aljihu. Ya cika da mamaki a lokacin da ya zaro ya ga naira na dukan naira har dubu ce. Ya kwalla mata kira ya ce " 'yan mata kin san kuwa nawa kika bani ?" Ta juyo ta yi murmushi ta ce " na sani, na ka ne dukka ." Yayi dariya ya yi mata addua " Allah Ya sa ki zama super star ki fi su Aisa shahara. " Ta ji dadin adduar nan sai ta amsa da amin ." Hashim ne ya taho a sukwane ya sauka daga kan babur a qofar gidan Nihal , saurin da yake yi ma shine dan ya zo ya biya mata kudin babur ya san bata da ko sisi. Ya shiga ciki da sauri qofar dakin ma a rufe babu kowa sai ya cika da mamaki da fargaba a inda ta maqale. Gashi bata san gari ba ko dai sun bata ne ? Daga baya ya fi zaton ko fushi tayi akan wulaqancin da su Aisa suka yi mata ta tafi wani waje ta zauna tana kuka ne . Ya dade a zaune a qofar gidan yana jira bata zo ba . Ya dauko kwarababbiyar wayarsa ya kira Tukur Darakta ya ce " oga wata matsala ce ta taso min ta kudi, zan kai tsohuwa asibiti dan Allah Ka bani naira dubu biyar a cikin kudin aikina. " Sai da Tukur ya gama cashe masa da fada da gori sannan ya ce ya zo gida ya same shi . Hashim ya tafi da sauri gidan Tukur ya karbi kudin . Bai tsaya a ko ina ba sai a shagon Tanimu mai shagon atamfofi da leshina da mayafai. Atamfofi biyu ya siya masu arha naira dubu bibbiyu da dari bibbiyu sannan ya sayi mayafi naira dari takwas kalar da zata shiga da kowacce atamfa. Gidan Marka mai dinki ya wuce daman ta san Nihal tunda sun taba zuwa tare a lokacin da ta kawo yagaggun kayanta ta dinke mata. Sai ya biya ta dubu daya ya ce ta dinka masa zuwa gobe da safe . Ta Amince zata yi hakan tunda ya biya kudi da yawa . Kofar gidan su Nihal ya dawo ya ci gaba da jira, bai jima ba sai ga ta, ta sauka daga kan acaba . Ta tsorata da ta ga mutum a tsaye a bayanta . Ya yi dariya ya ce" ke matsoraciya ni ne fa. A ina kika shiga ne ? Na zaci ai bata ki ka yi ko me babur ya sace ki ." Ta yi murmushin karfin hali ta ce " haba dai na san gari ai ." Shi ya biya mata kudin acaba naira hamsin sannan suka qara kan dakalin qofar gida, Nihal tana ta boye yagaggen hannun rigarta da mayafi ta kasa sakewa. Hashim ya kula da haka sai ta qara bashi tausayi . Ba zai fada mata ya kai mata dinki ba, so yake ya bata mamaki gobe da safe . Hashim ya ce " Nihal sai kin yi hakuri musamman da Allah Ya baki wata boyayyiyar baiwa, wacce za ta kai ki ga shahara duniya gaba daya zata sanki nan gaba . A tarihin Fim industry gaskiya baa taba samun macen da ta iya tsalle da fadan canis irinki ba daga bakin daraktoci nan na ji su na fada. Dole ki sami maqiya mahassada. Kin san wani abu ne dole fa mu dage da addua don baa shiga harkar Fim GABA GADI a shahara kuma a wanye lafiya kalau ba. Sai mun je wajen malamai sun yi mana addua an baki layu da guru kin daura saboda maqiya . Zan raka ki wajen malamina a wani qauye nan kusa . Me yasa kika ga kowacce rawa sai an saka ni ? Ai na tsare jikina na sha rubutun farin jini ne." Dariya ta kama Nihal ta rufe baki dan kada ya gane ta ce " Allah ko ? To shikenan ." Su ka yi sallama akan sai da safe zai zo da wuri su koma wajen shooting . Nihal ta shiga daki ta iske su dukka suna nan. Babu wacce ta amsa sallamarta sai Najaatun Gujungu. Aka hau yasar mata da habaici. Mami ta ce "Wallahi idan mutum ya na shishshigi a kauye ya kwana lafiya ya kiyayi shishshigewa 'yan birni . Daga ji sun zo aka yi carab aka tafi neman wajen zama . " Ba ta kula su ba tana ajiye mahaifinta sai suka ga hannu a yage. Su ka kwashe da dariya suka tafa. Iyantu ce ta ce " dan tsumman da ake ji dashi na fita unguwa shine ya yage? Allah sarki su super star manya. " Naja'atu ce take ta qifta musu ido akan su daina amma suka qi. Najaatu ta ce " Nihal gobe kiyi min magana idan zaki fita akwai wata atamfata da nake so in bayar, zan baki . " Nihal ta kalle cike da farin ciki ta ce " na gode Allah ya kai mu." Ta tafi ta yi wanka ta dawo daki, su ka cika da mamaki da suka ga ya farko sabuwar rigar bacci fil daga leda ta saka. Sai aka hau kallon-kallo a junansu. Mami Harka ta ce "na fada mu ku yarinyar nan wai ita a dole 'yar gayu ce wato mu take kwaikwaya har rigar bacci aka siyo an daina kwanciya da tsumma. " Iyantu ta ce " ba kya ganin wai ita a dole sai ta yi turanci rannan fa ce min ta yi please akwai micro wave a room din nan kuwa? Da na sake tambayar ta sai ta qi maimaitawa ta ce babu komai ." Asabe ta ce " tana son yin turanci gashi kuma baa iya ba. Ni ma rannan wai tawul zata ce sai da tayi wata malkwada wai ita baturiya wai towel. " Su ka kwashe da dariya suka tafa . Najaatu ta ce "gaskiya bana jin dadin abinda ku ke ya bakuwar nan shiyasa ma ban cika kwana a dakin nan ba. Ita bata shiga harker kowa kun saka mata ido ." Nihal ta ja fulo ta kwanta a kan tabarmarta ta juya musu baya , haka suka hana ta bacci su na ta shewa har sai da kanta ya fara ciwo. Asuba ta gari Nihal Nuren Mubin!!! Da safe misalin qarfe tara Hashim dauke da ledar kayan dinki ya iso gidan su Nihal, daman ta hana shi shigowa cikin gidan kai tsaye, a zaure ya tsaya ya baza murya ya kwala sallama. Ta gane muryarsa sai ta fito da sauri. A kofar gida suka tsaya, bayan sun gaisa sai ya miqa mata leda me dauke da sosai mai zafi sannan ya miqa mata babbar leda mai dauke da atamfofi da mayafi . Ta karba cike da mamaki ta tambaya " mene wannan ? Na waye ?" Yayi dariya ya ce " naki ne ki shiga ciki ki bude ki gani . Na baki awa guda ki shirya ki zo mu tafi yau a kusa da kano zaa yi a wani gari da ake kira Cinkilawa a qaramar hukumar Warawa yake. Zaa kawo motoci sai mu shiga mu tafi . Ta shiga daki ta warware kaya, sai ta cika da mamaki da ta ga dinkakkun atamfofi guda biyu har da gyale. Ta ji dadin da bata taba ji ba sai ta sake cure Hashim tabbas mai kaunarta ne. Ta yi mamakin yadda aka yi ya san kalolin da ta fi so, katari kawai aka yi . Ta wutsiyar ido ta hango su Mami suna kallonta ashe baccin qarya suke yi. Ta ci kosai guda biyu ta ji zai tayar mata da zuciya kasancewar da man kwanti aka soya. Sai ta ajiye a gefe ya shiga wanka. Iyantu ce ta tashi da sauri ta hau daddaga kayan, su na kallo, sun yi niyyar su saka reza su tsatstsaga sai Najaatu ta kwashe ta hana su. Da Nihal ta shigo dakin ta kula kamar akwai wani abu da ya faru domin taga an baza mata kayan kuma sun yi carko-carko su na kallonta kamar basu da gaskiya. Ta saka kayanta ta shirya tsaf da sauri, ta yafa gelenta wanda yayi marching da kayan. Bata kula su ba sai ta yiwa Najaatu sallama ta fice. Mami ta ce " idan ba mu yi hankali ba da zarar kudi sun fara shigowa yarinyar nan zata waye ta yi can sama ta fi mu . "Kun ga yadda ta yi bala'in kyau da ta saka sabuwar a atamfar nan, dan ma leda-leda ce. Toh ina ga idan ta fara saka super holland? Sai mun yi da gaske wallahi. Yaushe ta zo garin ne?" Iyantu ce ta fada . Najaatu ta ce " ashe kina da aiki kuwa , yarinyar da ta dogara da Allah Shi kadai ba Zai taba bari wata hallitta ta cutar da ita ba wallahi. Duk in da qarfe ukun dare ta yi ta gama bacci . A tsaye take tana sallah har asuba sannan ku ce zaku iya hana ta daukaka, " Nan dai Iyantu ta yi kan Najaatu su ka hau fada da zage-zage, wai don me zata fadi haka? Da Nihal ta fito sai Hashim ya gagara gane ta sai da ta yi masa magana . Ya dinga mamakin yadda ta canja ta yi kyau ashe tsumma ne ya ke zamar da ita kamar wata 'yar talla. Su ka yi ta dariya Hashim yana yi mata tsiya. Ta masa godiya sosai bisa dawainiya da kulawar da yake yi mata. Ta yi masa addua Allah Ya sa ya zama babba Jarumi ya Bash Auta gwanin na sa. Ya cika da mamaki da ya ji Nihal ta ce ba zata je wajen daukar shirin "yan birni ba . Ta ci gaba da yi masa bayani ta ce Akwai wani darakta Aliyu wanda Tukur ne ya hada su ya ce zata zo yau ta yi masa aiki. A cikin garin Wudil zaa yi can zata je . Hankalin Hashim ya tashi yayi ta magiya ta qi yarda. Wayar Hashim ce ta fara qara Darakta Idris ne yake kira , daga Hashim din har Nihal ne suka zabura . Darakta yana magana cikin rikicewa. "Ku na ina ne ? Ga motoci an kawo zaa tafi location ban ganku ba . Ina Nihal ?" Hashim ya miqa mata waya da sauri, ta karba suka gaisa ya ce "ku taho da gaggawa zaa wuce." Ya kashe waya ba tare da ya jira amsarta ba. Hashim ya yi tsalle yana murna ya ce "kin gani ko daman sai da na fada miki . Kin haye kawai tunda Darakta Idris ya san da zaman ki ." Mami ce da Iyantu suka fito tsegumi suna so su ga in da Nihal za ta nufa, sun yi fakare sun tsaya sun gama sauraren abinda ake fada a waya . Nihal ta zo ta zauna akan dakali ta ce " na fada maka ba na son in sake zuwa wajen daukar shirin Fim din 'yan birnin nan bana son rigima . Na ce maka ba zan je ba ." Mami ta zabura ta ce " kai Hashim wai wanne irin shishshigi ne wannan? sai Cusa ta kake tana gwale ka, ka rabu da ita mana tunda bata san alkhairi ba . Hashim ya tsaya yana ta yi musu bayanin irin muhimmancin Nihal a Fim din birni. Ba tare da ya san kamar wuta yake hura musu a qagon zuci ba . Darakta ya sake kiran Hashim ya ce " ku na ina yanzu ? Ga mu nan zuwa kawai mu dauke ku akwai waje a motar ta mu duk an yi gaba." Hashim ya kwatanta masa, babu jimawa sai ga wata dankarareriya Mota qirar jeep baqa, mai baqin gilashi ta tsaya a in da suke . Aka zuge gilashin windon gaba Jarumi Bash Auta ne ya bayyana. Sai a yau su Mami suka taba ganinsa ido da ido. Da aka zuge gilashin baya Darakta-daraktoci ne Idris ganinsa sai an cike form shine ya bayyana. Sai ga su Mami su na durquso su na kwasar gaisuwa suna gabatar da kansa a matsayin suma jarumai ne a wannan masana'anta. Asabe da Najaatu ne suka fallo da gudu suka fito gaba daya su ka yanyame jikin motar su na ta soki burutsu a dole a fim suke so saka su. "Ke Nihal ta so mu wuce mana, kina zaune kina mallon mutane. " Darakta ya fada a lokacin da suka hada ido da Nihal tana zaune akan dakali. Bash Auta ya ce " ah daman ita ce waccan ? Kai! yaya naga ta canja ba kamar jiya ba ...." Bai gama fada ba Darakta ya ce " ka yi shiru Malam kada ka tunzura dan na ga kamar bata son zuwa. In babu ita kuwa yau akwai matsala. " Nihal ce ta qaraso in da suke ta gaishe su cikin ladabi sai. Aka ce ita da Hashim su ghiga baya su zauna tare da Darakta . Nihal ta ce" mazan ne ya kamata su hadu a baya ni a bani gaba ." Haushi da mamaki ya kama Bash Auta tayaya zaa ce wannan kucakar da ya kamata ta yi biyayya dan a saka ta a fim amma ita take bada direction. Ransa bai so ba Darakta Idris ya roke shi ya dawo baya, bayan ya tabbatar masa da cewa yarinyar ta fi su gaskiya bai dace ta gwamutsa da maza ba. Nihal Nuren ce ta haye gaban mota yayin da mazan suka shiga baya. Zo ka ga bude baki dan mamaki da hassana kiri-kiri sun bayyana akan fuskokin su Mami. Nihal ta kalle su ta yi murmushi ta ce " sai anjimanku." Ta ja galas sama ta rufe aka ja mota aka tafi . Asharai kala-kala suka dinga saki. Mami ta ce " shikenan muna zaune ta zo ta fi mu. Ai Hashim da Tukur ne munafukai su suka kaita suka hada ta da manyan daraktoci." " Wallahi ba zai yiwu ba ko da asiri yarinyar nan sai ta koma garinsu ." Asabe ta fada. Iyantu ta ce " daga gani da asiri ta shigo in ba haka ba yaushe ta zo? Watanta guda kenan da zuwa fa ." Mami ta ce "mu je mu yi mata wurgi da kayanta a tsakar gida daman ai wata ya qare bata biya ba kudin haya ba." Asabe ta ce "mu je mu yi mata Watsin da kaya ta dawo ta tsinci kayanta a tsakar gida ." Najaatu ta ce " kada ku yi haka, ku bari ta dawo ta kwashi kayanta da hannunta ta tafi ." Ba su saurare ta ba cikin gida suka shiga da sauri suka fara yi mata watsi da buhun kayanta da filo a tsakar gida daman tabarmar ba ta ta ba ce . Kudinta naira dubu takwas ne ya fado daga cikin buhun suka kwashe suka ce a kudin hayar dakinsu zaman da ta yi. Burushinta na baki da sabulu da soson wankanta duk a zube a tsakar gida. Najaatu ce take bi tana kwashewa tana zubawa a buhu. Itama sabon suna suka rada mata su na kiranta da Munafuka annamimiya. Ta na ta amsa musu da " na gode , ba zan yi zalumci ba haka hassana ce ke damunku kuma insha Allah Nihal sai ta shahara." Darakta Aliyu ne ya aiko yaro ya ce ya yi masa sallama da Nihal. Yaro ya rada sallama ya ce " wai Nihal ta zo in ji darakta Aliyu yana kofar gida." Mami da Iyantu ne su ka fice da sauri suka iske Darakta. Ya sanar musu Nihal yake nema zaa tafi wajen daukar fim . Sai gabansu ya fadi aka hau kallon-kallo a junansu. Mami ta ce " yanzu Aliyu mu na garin nan ka tsallake mu ka nemo wannan wawuyar qazama a cikin tsumma." Ya ce " zamu yi maganar nan gaba ina take yanzu sauri muke ." Iyantu ta ce " waya ya ga son maso wani ai kai kake ta tata ita kuwa ta sami wadanda suka fi ka maiqo da kayan aiki da kudi ." Kansa ya daure ya kasa fahimta sai da suka tambayi sunayi, su ka shaida masa da luntsumemiyar mota aka zo aka dauke ta ita da dan korarta Hashim zuwa daukar shiri tare da Darakta birni Idris Hayat. Sai gaban darakta Aliyu ya fadi hankalinsa ya tashi banda Nihal babu wacce zata yi masa yadda yake so . Sun zaci zai zabi daya ta meye gurbinta sai ya hau babur dinsa ya tafi jikinsa a sanyaye. "Nan gaba fa ban san iya shahara da yarinyar nan zata yi ba, kalli ku ga har an fara yi mata layi tana har sai ta zaba ." In ji Asabe Mami ta ce " ya kamata mu hadu da su Amina 'yar kwalisa mu yi meeting mu nemo mafita domin idan muka zaune a garin kallon ruwa kwado zai yi mana qafa." Nihal Nuren Mubin ce da su Aisa ake kallon-kallo a lokacin da motarsu Darakta ta tsaya a gaban su. Nihal ta fito daga gidan gaba, ga ta ga babban darakta ga Bash Auta Jarumi mai tashe mai kudi ga Jan aji. Nihal ta fara tafiya tana sanda, Hashim ya rada mata ya ce " ki cire tsoro zasu raina ki fa , duk wacce ta taba ki ki yi mata irin yadda kika yiwa Amina ." Nihal ta ji wani karfin zuciya ya tunkaro ta sai ta saki jiki . Bata kallon idanuwansa ma balle ta san su na harararta . Aiki yayi aiki Nihal ce ke sukuwa akan doki Kamar ba mace ba. Amma yadda tsarin yake a matsayin Amina ce. Idan aka dauki bayanta sai a dauki fuskar Amina. Domin Amina ba zata taba yin kwatankwacin abinda Nihal ke yi ba . Haka kowa ya fuskanci Amina tana jin haushin Nihal musamman da Amina ta yi wani furuci a gaban kowa ta ce "ada da Nihal din bata nan ba hakuri kuke yi da yadda muke yin acting din ba, sai yanzu dan ta yi mu ku rufa ido zaa dinga tafa mata ana ihu." Da aka zo rawa da waqa darakta ya ci gaba da tambayar Nihal ko tsarin yayi ? Ya nemi da ta shiga cikin 'yan rawa ta nuna musu domin sun tabbatar zasu sake samun wata sabuwar idea. Sai Nihal ta ce bata taba yin rawa ba, ba zata iya ba. Sun dai ji ta ne kawai amma basu yarda baa yadda suka ga alamar ta zata iya yin rawa sosai, yadda jikinta yake malkwadawa duk yadda take so . Aka wuni a wajen kuma a ranar aka qarqare shirin . Darakta Tukur yana wajen duk abinda ya shafi Nihal shine wakilinta. Haka maganar kudi, da shi aka yi tsada , amma darakta idris ya fi son ya damqawa Nihal kudin aikinta a hannunta don kada Tukur ya cinye mata nan gaba ta qi zuwa . Abin mamaki yana miqa mata naira dubu ashirin sai ta miqawa darakta Tukur. Wannan abu ya ba su mamaki kuma ya burge su sun tabbatar Tukur ne wakilinta yanzu . " shikenan Tukur za mu dinga tabo ka ta waya idan ana buqatar Nihal a Fim." In ji Idris. " ke 'yar kauye ki sayi waya mana ance ki bada lambar waya kin ce baki da waya ko kunya bakya ji. Ashe ma ba ki hadu ba." Bash Auta ne yake yiwa Nihal wasa a gaban kowa. Mutum mai Jan aji da ji da kai yau gashi yana shishshigewa yar qauye. Sai su Aisa suka tabbatar yarinyar nan fa zata zame musu barazana nan gaba . Hashim ya zabura Hashim cewa Bash " ga wayar da muke sharing ni da ita kullum mu na tare dan korarta ni . Ba mu lambar taka. " " Ah ai shikenan tunda ta ce bata da waya kuma bata damu ko a takarda ta rubuta lambata ba." Hankalin Hashim ya tashi ga samu ga rashi sai qifqiftawa Nihal ido yake akan ta zo ta karbi lambar waya . Ta kada kai ta yi gaba abinta ko kallonsa bata sake yi ba yayin da mamaki ya kama kowa . Darakta Tukur ya miqawa Hashim naira dubu daya ya ce su yi kudin mota shi da babur ya zo, su hadu a gidansa da dadare. 'Yan kano suka shiga motocinsu suka zo suka wuce Nihal da Hashim a bakin titi su na jiran mota mai zuwa Wudil. Su ka Kula Hashim ne ke daga musu hannu Nihal ko kallonsu ba ta yi ba . A hanya ne suka yi ta hirarta Bash Auta ya ce " Darakta tabbas idan yarinyar can ta zana super star yaya zata dinga kallon mutane ne ? Ka ga wani jan aji da take yi tana yanga. " Darakta ya yi dariya ya ce "tana cikin tsumma ga talauci wanne jan aji kuma? Yadda na fahimta halittar ta ce yanga, wallahi akwai wadanda Allah Ya ke halittarsu a haka kuma ka gansu a kauye amma yanayinsu da dabi'unsu na 'yan birni. Babban furodusa Umar ya ce "sunanta ne ma yake bani mamaki. Na qanqararrun yan gayu.Tsakani da Allah ina 'yan kauye suka san wannan suna Nihal ?" Suka kwashe da dariya Bash ya ce " maganar gaskiya fa idan ma ita an shigo birni an aro Nihal din Babanta fa Nuren Mubin ta ina bakauye zai yi wannan qaqalen? Darakata dariya kawai yake yi ya ce " haka kawai take burge ni ." Aisa ta tabe baki ta ce " gara da ku ka gane da kanku Cesar yarinyar nan mayaudariya ce, a sunanta ma sai da ta yi rinto. " Bash ya ce "koma dai menene ta taimaka ki, yanzu za ki burge kowa a fim din nan, sai a zaci ke kika acting din nan . Duk abinda ta yi fa a matsayin kece kika yi. Z aki kara yin suna da daukaka akan abinda ta yi ." Hasiya ta ce " maganar gaskiya gara bakauyiyar nan ta daina burge ku, rufa ido ne duk wannan tashi saman da take yi. Haba dan Allah kamar ba mace ba ta dinga wani dogon tsallen da maza ma sun kasa yi ." Su Bash dariya kawai suke sheqawa da suka ji wannan kalmar ta rufa ido . Sun san ta tsorata mata, hassana ce kawai . Nihal da Hashim sun isa gida da magruba suka iske wannan wulaqancin, kayanta ne a zube a waje ashe bayan Najaatu ta harhada kayan a buhu da ta fita sake zazzagewa suka yi a qasa suka barbaza. Kafin ta yi magana Mami ta fito ta bata amsa " a qara gaba tunda nan ba gidan tsoho ba ne, mai face majina ya goge a riga ." Nihal ta ji ba zata iya daure jin kalaman tozarcin da ake yiwa mahaifinta ba wanda ya yi mata komai a rayuwa. Ta cije baki ta kalli Mami gami da nuna mata hannu ta ce " na yarda ki yi min dukka wulaqanci amma kada ki kuskure ki sake zagin Mahaifina, iyayena su ne gaba da komai bayan Allah da Manzonsa. " Mami ta tuna casuwar da Amina ta sha har yanzu tana can ta na jinyar targade din haka sai ta yi shiru . Hashim ya fusata ya ce "nawa ne kudin hayar na wata in biya ku daga nan zuwa anjima? Amma ku bar ta ta shiga ko salla bata yi ba ." " Naira dubu Goma ne kash. In ka isa ka biya yanzu ba sai anjima ba ." Asabe ta fada Nihal ta daga hannu ta dakatar da shi ta ce " kada ka roqe su, ba zan sake zama da su ba. Sai gashi kun yi min sata alhali ku ne masu gargadina akan kada in yi muku sata, tunda make ban taba sace kudin kowa ba ku dauki komai ma bana so ta juya ta fice a fusace . Hashim ya yi dibi-dibi yana neman daya sabuwar atamfar da ya siyo mata itama bata ciki sun dauke sai tsummakarai su ka bari. Hashim ya tsaya ya zage su tas ya na kiransu da barayi sai Allah Ya saka mata . Ya ji zafin kudinsa da ya tatike ya mata dinki suka sace dan ma ta saka guda daya da sauki . Bayan sun fito kofar gida ne Hashim ya ce " yanzu yaya zaa yi kenan? A ina zaki kwana? Ko gidan Tukur zamu je ki kwana daya a gidansa ki fada masa yadda aka yi ya biya miki haya da kudinki na wajensa. Ke ma kiyi kuskure da kika dauki kudinki dukka kika bashi mayen kudi ne fa. " Nihal ta girgiza kai ta ce " ba zan sake kwana a gidansa ba matarsa ta yi min wulakanci. Haka kada ka sake ka tambaye shi kudin nan in zai riqe ma dukka na yafe masa. Ka tafi kawai zan san yadda zan yi. " " A a ba zan bar ki a titi ba mu je gidan Marka mai dinki ki kwana ita ta sanki kuma ita kadai ce a gidan daga ita sai yaranta mijinta ba mazauni ba ne ." Nihal ta qi sai da ta ga naci da magiyar Hashim ta ishe ta sannan ta yarda suka tafi . Marka ta sakar musu fuska ta yi Amanna Nihal ta kwana daya a gidan. Tun a gabansa aka kawo mata tuwon dawa miyar kuka baqiqirin sai warin daddawa take yi da ruwa a kwanan sha. Sai da ya tabbatar ta sami masauki sannan ya tafi. Yana fita Nihal ta miqe ta ce zata je ta dawo a kwashe abincin ta koshi. Wajen shazali ta nufa ta karbi abinci da ruwa ta zauna ta ci a cikin office dinsa, sannan ta shaida masa tana son ya fita gobe ya samo mata karamin gida na haya sabo fil take so na sumunti mai dauke dakuna uku ko dakuna biyu . Sannan kowanne daki a sayi katifa babba a saka da labule da zannuwan gado, tana son bokitai da manyan robobin tara ruwa . Ya tabbatar mata ta bashi daga yau zuwa gobe da yamma . Ta sake karbar naira dubu goma a wajensa ta tashi ta tafi. Ta isa shagon Musa in da take karbar duk abinda take so, rigar bacci sabulu, omo soson wanka ta karba . Ta kwashi alewa da biskit mai yawa ta kai wa yaran Marka . Suna ta murna kuwa dan haka Marka ta sake sakar mata fuska, suka yi ta hira har sai da suka raba dare. Asuba ta gari Nihal Nuren . 11/14/21, 7:19 AM - MY MTN 2: GABA GADI EP 9 General Nuren Mubin yana zaune a babban falonsa yana kallon labaran tara . Gefensa kuwa uwar gidansa ce Prof. Shatu, bata sakar masa fuska har yanzu shishshige mata yake ta yi duk in da zai je sai ya takura mata ya ce sai ta raka shi . Kallon ma dole yayi mata ta zauna, kallo take ba dan tana fahimtar abinda ake cewa ba. Shi kadai yake kidansa yayi rawarsa, ya yi kallonsa yayi sharhinsa da eh kawai take binsa. Tabbas ya san bai kyauta ba amma kuma taurin rai da taurin kai da jajircewarsa ta sa ba zai janye ba har sai Nihal ta cika wa'adin da ya kudira a ransa. Shi a cikin lamuransa baya yafiya, ka na b'ata masa rai toh sai ya linka maka linkinsa . Sallama suka ji suka hada ido suka kalli masu shigowa garadan maza a layi su na ta shigowa da yake kowannensu dogo ne masha Allah. 'Ya'yansu ne tun daga kan Muhammad babban har zuwa Mu'awiyya dan autan maza bayan sun shishshigo sai suka durqusa suka gaishe da mahaifansu, sun amsa musu cikin sakin fuska sai kowa ya sami kujera ya zauna aka rasa wanda zai fara magana a cikinsu. Saboda daman haka ne sai sun shirya magana a waje daga sun zo gabansa sai yayi musu kwarjini su kasa magana . Aka fara qifce-qifcen ido wannan na cewa wannan ya fara wancan na zungurar wancan . Prof.Shatu ta fahimci hakan dan haka ta zubawa sarautar Allah ido ta tabbatar wannan al'amarin babba ne. Ta ce a ranta "in ma da niyyar ku yi masa nasiha ku ka zo akan Nihal ina mai baku shawara da kun fasa ba zai taba sauraronku ba." Asp.Aliyu ya fi su taurin zuciya tun su na yara shine yake iya tunkarar General da magana duk da yana iya haduwa da mari ko harbi da qafa amma baya dainawa. Aliyu ya ce" Daddy wajenka muka zo. Daman tun bayan tafiyar Nihal fiye da wata daya kenan, ba ma cin abincin gidan nan, ba ma sakin fuska, bama zaman falo saboda muna fushi da hukuncin da ka yanke akan qanwarmu. " General ya dago da sauri ya dube shi ya fada a shelaqe " da wa kuke fushin. Ai ban ma san ku na yi ba. Oh daman fushi ku ke yi ai bana kallon fuskarku balle in san ku na yi .Yaya aka yi yanzu, kun huce ne ? Ko yunwa ce ta koro ku, ku na so ku ci abincin ne ?" Aliyu ya juya ya kalli 'yan uwansa saboda wani ya kawo masa agaji ya karbe shi, domin kalamansa sun qare. Muhammad ya gyara zama ya ce Daddy " na tsayar da shawarar kawai zan koma Enugu da zama ba zan iya zama a arewa ba, zuciyata ba zata iya daurewa ina ganin kanwata a fim tana tiqar rawa ba ." General tabe ya ce " ina baka shawara dama Afghanistan ka kaura can ne ake yaqi ka je ka kwantar da tarzoma. Ka ga acan babu yadda zaa yi Fim din Hausa ya qarasa musu can ." Muhammad ya bude baki yana mamaki da wannan baqar amsa. Major Abubakar ya murtuke fuska ya ce " gaba daya ma a kaina abin ya qare na rasa abokina Maqaddas, na rasa matar da zan aura Siyama gaskiya nima dai gara in tafi Malaysia karatu daman an tura ni ban tafi ba tun last year yanzu gara in tafi ." General ya qirqiro wani murmushi mai kama da kuka ya ce " dama qasar koria ka kaura anan ake hada bom da Mizanai. Dr Hamza ya ce " daman ina so in je in yi PHD jamia ta bani damar tafi London zan tafi yanzu. General ya ce " ka yi kokari Idan ka gama doctoring degree din Department din su Nihal su dauke ka lecturing, kada ka dawo qasar nan ma." Mu'awiyya ya ce " ga shi sunana ya bazu a harkar aikin jarida sunan nan ba boyayye ba ne daga Fim dinta ya fito zaa gane kanwata ce daman mun fi yin kama da ita . Gaskiya ban san yadda zan yi da zaman garin nan ba ." General ya ce " ka koma birnin sin China ." Umar ya ce " gaskiya gara in shiga duniya ." General ya ce " duniya tana da fadin gaske na yafe maka ka shige ta, kada ka dawo daga can ka wuce qiyama. " Bar.Usman ya ce " ni dai zan iya maka duk Daraktan da ya saka ta a fim saboda wannan laifi ne. General ya ce " wanda ya kai ta fim zaka maka a kotu ba furodusa ko Darakta ba . Ina ga mun yi sallama ko ? Kowa ya tashi ya fara hada kayansa gobe da safe ina so in ga gidana wayam daga ni sai mata." Su ka juya su ka kalli mahaifiyarsu suka hada baki " Mummy kina ji ko ? " Ta gyada kai ya ce " ina jin ku. Ku daina damun kanku na fada muku addua kawai za ku yi mata Allah Ya tsare ta a duk in da ta ke ." General ya yi tsawa ya ce " dalla a tashi a tafi ina kallon labarai ku na damuna." Su ka tashi su na tafe su na layi saboda takaici. A farfajiyar tsakar gidan su ka tsaya su na shaqar iska dan ta rage musu takaici. Dariya Aliyu da Hamza suka yi ta yi, yayin da hawaye ya dinga kwaranya a idanuwan Muhammad da Abubakar saboda baqin ciki ya ishe su. Mu'awiyya ya ce " Allah zan Daddy buga Daddy a jarida kowa ya san halin da yake jefa mu. Haba dan Allah kamar wasu bayi ." Muhammad ya harare shi ya ce " baka da hankali ka buga shi a jarida ka tonawa kanka asiri. Ai mutane ma zasu yi shaida cewar uban nan na mu yayi mana komai rayuwa kai zasu zaga ." Qarshe dai sauran suka huce akan masu dariya Aliyu da Hamza da gudu su ka bi su da dukka . Al'amarin Nihal kuwa daga gidan Marka wajen daukar Fim din Darakta Aliyu ta wuce acan suka wuni, wannan ne karo na farko da ta fara jan ragamar fim a matsayin cikakkiyar Jarumar fim din . Ta wargaza gaba daya labarin ta sauya shi amma a cikin siyasa, Aliyu ya fahimta sosai tsarinta ya fi nasa yin maana. Ya ji dadin hakan kuma nan da nan aka yi sinasinai masu yawa a ka gama. Hashim ya samu shiga amma a matsayinta babban abokin actor. Tunda labari ya canja daga salon soyayyar da aka gina shi ya koma kan zamantakewa dan haka babu ma muhallin yin rawa da waqa. Duk da haka Aliyu ya dage sai an yi rawa da waqar amma akan qawar jaruma waqar ta sauya aka mayar da ita tunani qawar Nihal take yi a zuci dan tana son saurayin qawarta. "A je a haka tunda baragadar dai sai sun yi amma ba da ni ba." Nihal ta fada a ranta a lokacin da take zaune akan kujera tana kallonsu su na ta tiqar rawa . Hashim kawai take kallo da wani qaton baqin takalmi kambas da yellow Jeans da ya siyo a gwanjo wai shi a dole sai ya zama super star. Takaici ya ishe ta dan ba yadda za ta yi ta hana su ne. Sai daf da magriba aka tashi da zummar gobe zaa karkare. Naira dubu biyu Aliyu ya miqawa Nihal gami da bata haquri gobe zai qara mata dan wani abu. Ashe gara ita naira dubu guda aka bawa Hashim kuma murna yake. Dariya ce ta subuce mata ba tare da ta shirya ba, ta yi godiya suka fito hanya. A tunaninsu dariyar murna ce nan kuwa yawan kudin ne ya bata dariya ta tuna yawan maqudan kudin da ake biyanta a turai a wuni daya kacal. Hashim yana ta yi mata kasafi yadda zasu samo daki me arha ta zauna ga dubu biyunta ga dubu dayarsa daman yana da wata dubu biyu a boye, ya zama dubu biyar kenan. Nihal ta miqar da dubu biyun nan tana tisa su tabbas guda biyu ne kudin aikinta na farko da aka fara biyanta a hannunta. Ta fada a bayyane "Allah na tuba Ka yafe min." Dan ta tuna sanda ake yi mata kyauta miliyan daya ta raina. Tabbas wannan wani darasi ne da aka aiko ta ta koya a rayuwa. Yau gashi sai da ta wuni tana aiki ga yunwa da qishirwa duk akan naira dubu biyu . Ta miqawa Hashim kudin ta ce " ungo hada dukka na baka." Ya cika da mamaki ya ce " a hada da na wajena a kama dakin? Kina da naira dubu ashirin a hannun Tukur fa ." Ta ce " kada ka damu ." Yayi mata duba na rashin fahimta su ka ci gaba da tafiya . Hashim ya ce " me zaki ci yanzu? A ina zaki kwana? Dole yau ma sai dai ki kwana a gidan Marka me dinki, zan sake roqarta." Ta girgiza kai ta ce " A'a ba zan kwana a can ba na gano gidan wasu 'yan uwanmu can zan dinga kwana. Ka da ka damu can zan je. Zan hau acaba in tafi gobe mu hadu a location kawai ." Kafin ya ce wani abu ta hau babur ya wuce. Ofishin Shazali ta nufa kamar tare suka iso ko fitowa daga mota bai yi ba ya dawo daga kano . Bayan sun gaisa sai ya miqa mata leda mai dauke da abinci mai zafi, daya ledar kuwa ruwa da lemo ne da ice cream masu sanyi . Ta ji dadin hakan saboda tsananin jin yunwar da take addabarta amma jikinta yayi sanyi da ta tuno irin baqar yunwa da Hashim yake ji amma bata san yadda zata dinga bashi ba. Ko me zai samu ya ci yanzu? Ba zai wuce tuwon baqar dawa miyar kuka ba . Kullum maganarsa kakarsa ta surfa dawa ya kai niqa. "Allah sarki Hashim babu yadda zan yi ne domin bana so ka gane ko ni wacece. " A cikin ofishin Shazali ta baje akan tabarma ta ci ta qoshi amma duk cinta bai wuce ta ci rabi ba, rabin anan take barinsa ko ta yi yunkurin zata fita da shi ta bawa almajirai sai Shazali ya ce ta bari yana da almajiri. Bata sani ba ko 'yayan hajinsa ne almajiran. Da ya ga ta nutsu ta dawo hayyacinta sai ya yi mata albishir da cewa tun da yamma komai na sabon gidanta ya kammala. Sai ta ji dadi a ranta dan haka motarsa ta shiga ya kaita. Ba haka ta zata ba domin gidan yayi kyau har da get karami. Sannan daga ciki flat ne me falo da dakuna 3. Lallai Shazali yana da test ya san abinda ya dace da ita . Ya zuba kujeru a falon guda biyu, sai cikin dakuna kowanne da katifu manya da filo. Ga karamin jannareto sabo, ga bokitai a bandakuna sababbi. Sabon gida ne, ya tabbatar mata ya biya kudin shekara guda amma da ya fadi kudin hayar gidan sai ta ji arhar ta baci . "Daman gida a kauye baya tsada? Kenan in siyan gidan ma zaa yi ba zai yi tsada ba ." Nihal ta tambaya . Shazali ya ce " ai kuwa siyarwar su ka fi so ma dan dai ya dade a haka ne baa siya ba suka bayar haya. Ana so a siya ne ?" Ta girgiza kai ta ce " ba yanzu ba a bari ayi shekarar a gani. " Ta sake zayyano masa abubuwan da take buqata gobe ya siyo mata. Ta bashi umarni ya dinga aiko mata da abincinta gida tunda yanzu ita kadai ce a gidan ba sai ta dinga zuwa ofishinsa ba. Ta yi bacci mai dadi yau wanda bata taba yin irinsa ba tunda ta bayyana a garin nan, babu sauro babu zafi babu taurin tabarma. Ta sha wanka a shaya kasancewar akwai ruwan famfo a gidan . Talabijin ce ta rage mata kawai. " Allah abin godiya .Nihal ta fada a lokacin da ta tashi yin sallar tsakar dare a cikin sujjada. Asuba ta gari Nihal Nuren Mubin. Da misalin karfe 10:45am Nihal ta fito daga gate din gidanta ta datse sannan ta tari acaba ta hau, bata tsaya a ko ina ba sai a wajen daukar shirin. Ta iske su Hashim an dade da hallara. An sha aiki tun qarfi amma a yau aka qarqare kafin magaruba. Naira dubu uku Darakta Aliyu ya qara mata , Hashim kuwa dubu daya da dari biyar ya samu ko dubu biyun bai kai ba. Su na fitowa kan hanya sai ya ga Nihal ta miqawa wani makaho naira dubu daya, za ta kara masa wata dubun sai Hashim ya zabura ya fisge kudin. Ya ce " kina da hankali kuwa? Rabarwa zaki yi alhali ko dakin zama baki da shi." Ta yi murmushi ta ce " ya kamata in sadakar da kudin aikina na farko dan neman albarka. " Ya kasa bata amsa dan ya rasa ma a yadda zai fassara wannan al'amari. Shin tabin hankali zai kira ta da shi ko rashin tunani? Nihal ta rasa da yaren da zata yi masa bayani ya fahimta don ya tafi gida ya daina bin ta. Ya dage sai ya raka ta ya ga gidan yan uwanta. Su ka hau acaba suka isa qofar gidan a wajen gari gidan yake amma tabbas gidan 'yan gayu ne dan ya qeru. Akan dakalin qofar gidan su ka zauna yayin da Hashim ya lura an datse gidan da qaton kwado. Ya zabura ya ce " ai gidan a rufe yake. Basa nan ne ? Yaya za ki yi toh? " Ta yi dariya ta ce " sun fada min za su je Kano biki amma komin dare za su dawo. Zan jira su babu damuwa, ka tafi gida kawai sai gobe amma gobe bani da aiki ba zan fito da wuri ba sai da yamma zan zo in same ka, mu hadu a daidai gidan Marka ." Ya amsa da " Ba damuwa amma yanzu me za ki ci? Wuni guda baki ci komai ba, ko gurasar da Darakta ya siyo baki ci ba. Ko in karbo miki biredi da tsire?" Ta girgiza kai ta ce " ka tafi kawai kada ka damu ." Ya tashi ya tafi da alama ba zai hau acaba ba dan kada ya taba kudin hanyar dakin da zai kama mata, cancana kudin nan yake. Ta ji tausayinsa ya kamata ta fada a bayyane " dama zan iya taimakonka a yanzu, ka rabu da talauci kamar yadda kake daman tashi-fadi har sai ka inganta rayuwa." Sai ta fashe da kuka sannan ta tashi ta dauko mukulli ta bude qofar get din ta shiga ta datse. Addua kawai take ta tottofawa a kowacce kusurwa ta gidan domin gidan yana bata tsoro zama ita kadai. A bakin kofar falo ta iske ledojin abinci Shazali ya kawo mata domin yana da mukullin get guda daya . Ta bude qofa ta shiga da ledojinta. Abinci ta fara ci sannan ta yi sallah ta yi wanka ta kwanta . ** ** ** Ita da ta cewa Hashim su hadu da yamma sai gashi a bakin get din gidan da misalin qarfe tara na safe . Idonta biyu wannan karon rubutu take tana zayyano abubuwan da ShaAli zai siyo mata, ta gaji da daura zani dogayen rigima abaya take so guda uku da takalma. Ta ji ana buga get bata yi mamaki ba ta dauka Shazali ne, ta na fita sai ta ga Hashim cike da murnarsa. Ko gaisawa basu yi ba ya ce " ki zo da sauri. ta samu fa. An zo nemanki, akwai aiki har guda biyu daya na Tukur daya na abokin Aliyu ne, wato Darakta Musa. Domin Aliyu ya bashi labari kin iya acting. Zo mu tafi da sauri ana can location ana jira ance in kira ki ne." Ta ji kamar ta kwala ihu domin ta gaji. Sai ta tuna abinda ya kawo ta kenan kuma dole ta yi. Awa daya ya yi yana jiranta ta shiga ciki ta shirya sannan ta fito, ta datse get suka tafi . Ya tambaye ta cike da mamaki "ba kowa a gidan ne na ga kin datse ta baya ." Sai da ta yi inda-inda sannan ta hado kan amsar " eh basu kwana a gida ba ashe sun bar min mukulli a maqwabta sai da suka leqo suka ganni ina jira sannan suka kawo min, amma yau zasu dawo ." Lallai kin caba kin huta da wulaqancin su Mami Allah Ya musanya miki da mafi alkhairi. Au na manta ban fada miki ba a fim din nan dukka biyu akwai Amina 'yarkwalisa, akwai Mami da Asabe dan Allah kada ki kula su ku yi fada, kuma kada ki ce ba zaki yi ba saboda su sai su ji dadi su zata tsoronsu kike ji." Ta ji dadi a ranta da aka ce har da su, ai kuwa saboda su din ne ma za ta yi Fim din zasu gane akwai banbanci tsakaninsu da ita mai tsumma. Ofishin Darakta Tukur suka fara zuwa, yayi murna da ganinta sai ya kwatanta musu wajen daukar shirin ya ce su hau acaba zai same su acan. Sun isa wajen sun iske kowa ya hallara nan fa ransu Mami ya baci da suka ga har da Nihal. Ta yi sallama basu amsa ba sai harara da murguda baki suke yi mata . Sun zaci za ta hau rabe-rabe saboda tsoronsu amma sai suka ga GABA GADI ta kutsa tsakiyarsu ta zauna fuskarta cike da fara'a. Nihal ta dubi Hashim wanda ya sankare a tsaye yana fargaba ta ce " Hashim ka tafi wajen maza ka zauna zan zauna tare da 'yan uwana mata abokan sana'ata. " Hashim yana tafe yana waiwaye sai bai ji wata ta sake yin magana ba dai. Addua Ya ke Allah Ya kiyaye tsautsayi da asarar qashi da tsoka, yana gudun kada a casu ka fasa baki ayi karaya . " Amina 'yar kwalisa yaya jikinki?" Nihal ce ta tambaya gami da dafa kafadar Amina . Hohoho zo ka ga takaici da baqin cikin da ya dirsu a zuqatansu. Naja'atu ta yi dariya ta ce " Nihal baki da dama ashe, daman kina magana haka?" Tsaki Mami harka ta ja ta ce da su " dalla ku taso mu bar wajen nan ." Ta na tafe a gaba su na biye da ita kamar wata kaza da 'yayanta amma banda Najaatu bata bi su ba ita ta zauna tare da Nihal. Hira suke ta yi Najaatu tana ta son dukan cikin Nihal ta ji tarihinta. Ita wacece? Me ya sa ta zo ta shiga Fim? Amsa guda bata samu ba sai ma dai ita ce ta ke ta bawa Nihal tarihin rayuwarta. Najaatu ta ce ita 'yar garin Bauchi ce ta gudo ne a sanadiyyar zaa yi mata auren dole, har yau iyayenta ma basu san in da take ba . "Subhanalllahi me yasa kika yi haka? Kuma ana saka ki a fim din? Finafinai nawa ki ka yi kawo yanzu ?" Najaatu ta tabe baki ta ce " ina fa, kullum sai dai in yi musu rakiya, dakyar ma ake saka ni a cikin 'yan rawa ko 'yar aike." " Ai ba zaki taba ganin daidai ba saboda babu albarkar iyaye." Nihal ta fada GABA GADI babu kokonto. Naja'atu ta yi shiru can ta ce "ke ai babanki ne ya kawo ki da izininsa kika shigo shiyasa ki ka fara ganin hasken abin." Nihal ta yi murmushi ta ce " haka ne ." Tukur ne ya qaraso da sauri sai kowa ya taso ya zo wajensa ya tsaya cike da ladabi, ya fara rarraba aiki sai ga Nihal da Amina 'yar kwalisa an hada su a matsayin kawaye a cikin Fim din. Nihal ta dage ita bata iya karatun script ba sai dai a fada mata da baki. A yi ta fada mata ana maimaitawa daga qarshe ma Hashim aka saka ya zauna da ita ya dinga karanta mata kafin a zo kanta . Nihal ce ta dafa kafadar Amina 'yar kwalisa a yayin da ake daukar shirin ta yi murmushi ta ce " qawata ki na da ji da kai amma ki sani ki daina wulaqanta mutane don baki san daraja da martabar da Allah Ya yiwa wanda kike wulakantawa ba. Zai yiwu ya fi ki asali , arziki , ilimi , Lima da martaba." Wannan ba ya cikin script amma yayi daidai da sakon da ake so a isar a cikin fim din. Amina ta zabura ta hada da ashar ta ce " gaskiya darakta ka raba ni da wannan yarinyar. Yaushe aka rubuta haka a script din in ba so take ta fada min magana ba?" Tukur ya ce " banda abinki Nihal fa bata iya karatu ba dole ki yi mata uzuri. Abinda ta ga ya dace take fada idan ta fada kuma sai ya fi hawa." Haka dai aka gama daukar Fim din nan kamar zaa yi fada amma Nihal bata kula su ba . Tukur yayi qirmisisi bai bawa Nihal ko sisi ba haka bai yi mata zancen kudinta na wajensa ba ita kuma bata tambaya ba. A cikin satin nan gaba daya Nihal bata zauna ta huta ba, aiki take ta yi daga safe har dare amma kudin data samu bai kai naira dubu goma ba. Ta raba gida biyu ta bawa Naja'atu rabi Hashim rabi ba tare da dayansu ya san an bawa dayan ba . Shi dai Hashim tara mata kudinta yake yana jira su cika a kama hanmyar daki . Nihal ta takura sai Hashim ya kaita gidansu ta ga iyayensa tana ta yi mata hanya-hanya yana gudun kada ta je ta ga tsantsar talaucin da suke ciki. Yau da safe ta ce qafarsa-qafarta sannan ya amince suka tafi yana fargaba kada ta raina shi ta daina kula shi. Hashim ya yarda ya kai ta gidansu, ya kasancewar maraya a hannun Kakansa da kakarsa ya girma. Tsohon ya dade a zaune komai sai an yi masa a sanadiyyar ya sami shanyewar barin jiki. Tsohuwar ce me kwari sai ta yi surfe an biya ta su ke cin abinci, sannan tana saqar tabarmar kaba. Nihal na shiga gidan sai ta ji hawaye ya cika mata ido don tausayi, gidan kasa ne duk yawancin dakunan sun rushe an saka zana an zagaye. Hashim yayi dibi-dibi ya rasa kujera me kyau da zata zauna akai, da kyar aka samu wani buhu aka shinfida mata a inuwa a tsakar gida. Ko ina shanyar dusa ce da qanzo. Bayan sun gaisa da tsofaffi sai Inna ta ce mata tana da labarinta a wajen Hashim. Kan ka ce kwabo hira ta barke a tsakanin Inna da Nihal kamar sun saba . Hashim yana ta tsoron kada Inna ta baro masa, dan ya ga ta shiga bata wani dogon tarihin da baa tambaye ta ba. Hashim yayi-yayi Nihal ta taso su tafi ta qi tafiya ta ce ya tafi ya barta. Bai san Ilimi ta ke kwasa ba, tarihin da-da-da ta ji wanda bata taba ji daga bakin iyayenta ba. Ta na ta nade sunayen abubuwa da yadda asalin aladar Hausa da masarautarsu take. " Hashim ina wannan kudin yake?" Nihal ta tambaya Yayi sororo yana kallonta ya na ta qifta mata ido akan tayi shiru kada ta yi maganar kudi a gaban tsofaffi . Ta kawar da kai gefe kamar bata gane abinda yake nufi ba ta ce " kawo dukka." Ya miqa mata nasa da nata ya kai dubu goma sha hudu bai ankara ba sai ya ga ta damqawa Inna gaba daya. Ta ce " Inna na ki ne dukka ku ci abinci ." Inna ta fashe da kukan dadi ta shige daki tana rusa kuka ta bayan da ta damqe maqudan kudinta a hannunta. Ta na dadewa bata ga dubu daya ba ma balle dubu na dukan dubu har guda goma sha hudu . Nihal ta fice daga gidan ba tare da ta yi masa wani bayani ba. Hashim ya zabura ya biyo ta a baya ya na tambayarta menene dalilinta na yin haka? Kudinsu kenan fa kakaf ta dauka ta yi kyauta da su . Ta tambaye shi "da na yi kyautar da kudin wa na bawa? Hashim kana da imani kuwa? Inna ta ban tarihi mahaifinka ya rasu tun kana ciki baa haife ba, mahaifiyarka ta rasu a ranar da ta haife ka ko ganinka bata yi ba. Kakanninka ne su ka dauke ka a cikin tsumma. Inna ta shayar da kai Nononta har kabilata kwari sannan sai sun yi noma sun yi surfe su ke samu su ciyar da kai. Amma yau ka zama mutum naira dari ta gagare su alhali kana da dubu goma sha hudu a aljihu. Ka bani mamaki ban ji dadi ba . Dan me kake tausaya min amma baka jin tausayin tsofafin da qarfinsu ya kare akanka? A yanzu ne suke tsananin bukatarka. Inna ba zata sake yin surfe ba kai ne kake da hakkin ka ciyar da su." Ya ji kunya da nauyi ya kama shi ya tabbatar bai kyauta ba. Amma kuma hukuncin da Nihal ta dauka akansa yayi tsauri, ai da sai ta raba kudin gida biyu ta bar masa rabi. Nihal ce ta katse masa tunanin da ya tsunduma ya na yi ta ce " a satin nan zan biya ka kudinka dubu goma sha hudu. Kada ka damu na san kana da bukata kai ma." Ta juya ta tafi a fusace ta hau babur ta bar shi a tsaye ya na nadama. Idan Nihal bata da aikin Fim to tana tare da Kakar Hashim tana daukar ilimi, shaquwar da suka yi ta kai har basa jin dadi idan basu ga juna ba. Nihal tana da takarda da biro tana rubutawa. Abu kamar wasa har unguwa suke tafiya tare ko su yi bulaguro zuwa kauye su wuni cur acan biki ko suna a kauyakun da ke kusa da Wudil. Ta na sake samun ilimin zamantakewa da al'adun Hausa domin har yanzu a qauyukan basu zubar da al'adunsu na gado ba na ainahin Hausa Fulani. Qanin Inna bafaje ne ya yiwa sarkin kano hidima kafin tsufa da ciwo ya kama shi ya dawo gida. Ta sami tarihin sarautar qasar Hausa sosai a wajensa. Ya na jin dadin yin hira da Nihal domin ta na da saurin gane abubuwa, babban dadin da ya fi ki shine yawan kyautar kudi da ta ke bashi na ban mamaki. Idan su ka kai yamma har dandali take zuwa tana zama tare da 'yan Mayan kauyen tana nade waqoqinsu irin na al'adarsu. Muryoyinsu gwanin dadi, zaqaqan baituka masu dauke da hikima, sakonni masu muhimmanci suke isarwa, babu kida sai tafi babu rawa babu girgiza babu shigar da zata fitar da tsaraici. Babban abin sha'awar babu cudanya da mata da maza, mata su na yin nasu maza ma haka . Ta ga yadda budurwa ke haduwa da saurayi a yi soyayya har ta kai ga yin aure wanda yayi daidai da al'ada da addini cikin jin kunya da mutanta juna. Ta halacci bikunkunan qauye da yawa ta nadi abubuwa da yawa wadanda bata taba sanin su na faruwa ba . Laptop ta ce Shazali ya siyo mata, baa dauki lokaci mai tsayi ba sai ya kawo mata sabuwa fil a kwalinta . Ta na ajiye a gefen katifarta kullum da daddare in ta zo kwanciya sai ta yi rubutun fim . A haka ta rubuta fina-finai masu yawan gaske kuma masu ma'ana. 11/14/21, 7:19 AM - MY MTN 2: GABA GADI EP 10 Watannin Nihal uku cur a garin Wudil da kewaye, ta fito a cikin fina-finai goma sha uku, ban da wadanda ta dan firfito a na birni da kuma wadanda aka yi amfani da jikinta a ka dora fuskokin wasu. Sai a yanzu ne aka fara sakin finafinan da Nihal ta firfito tabbas an fara hasko ta, mutane su na shaida fuskar yayin da sunanta ya fara reto a qwaqwalen masu kallo. Aisa buzuwa ta samu daukakar da bata taba samu ba a lokacin da aka saki wannan fim din da ake tunanin ita ce ta yi bajintar nan. Ko ina yabonta ake ana sake jinjina abinda ta yi. Kafin ka ce kwabo ta sami goron gayyata daga manyan firodusoshi akan ta zo ta shiga manyan finafinan da za su yi. Sai dadi take ji tana taqama tana daga kai har zabe take yi. Yayin da aka dinga yi mata tayi da kudade masu yawa, tun daga nan ta ji a jikinta kakarta ta yanke saqa wannan shekarar ta ta ce. Darakta Idris bai isa ya tona wannan asiri ba saboda daukakar Aisa akan fim din shima daukakarsa ce har ma ya fita morewa saboda yana kwasar romon riba a kasuwa. An siyar da fim din sosai, an haska shi a manyan sinimomin dake cikin biranen qasar nan. Idanuwan Muqaddas kem akan finafinan Hausa ya na so ya ga abar qaunarsa, sai a yanzu ya ci karo da Fim din da ta fito guda daya. Ya sha takaicin ganin Nihal a cikin tsumma ta na gwagwarmaya da qauyawa. Sunanta ne ma da ya gani ya sake gasgatawa ita ce amma ba kowa ne zai gane ta ba, in har ka san ta ada da. Ya ja bakinsa yayi shiru bai nunawa kowa ba gudun kada rai ya baci, dan shi har yanzu ita ce zabinsa duk da mahaifansa sun ce sun gama magana ba zai aure ta ba. Kasuwar Aisa tana ta ci amma in da gizon ke saqar shine da aka bata fili ta maimaita kwatankwacin abinda ta aikata a wancan Fim din sai abu ya gagara. Kan kowa ya daure aka kasa ganewa, aka yi-aka yi ta kwatanta ma ko bai kai yadda ta yi a wancan karon ba amma ta gagara aka yi. Daga nan sai kokoto ya shiga zuqatan mutane aka kasa gano bakin zaren. Darakta Abbas.H.Abbas ne ya zare farin gilashin da yake fuskarsa ya ajiye akan tebur ya kalli Darakta Idris Hayat ya ja doguwar ajiyar zuciya ya ce " na yi mamaki na yi takaici matuqa akan abinda Aisa Buzuwa ta yi mana jiya." Darakta idris ya dauke kansa daga kan karatun script ya dubi Darakta Abbas ya tambaya cike da zumudi me "Aisa ta yi muku ?" Abbas ya yi tsaki ya girgiza kai ya ce " ganin yadda ta yi bajinta a wannan sabon fim din da ka fitar kwanan nan mai suna SIRDi. Sai na gayyace ta akan ta zo ta yi min wannan babban fim din nawa, ta dinga yanga tana ja min rai sai da na lunkuba mata kudi sau uku akan kudin da nake biyan sauran jarumai. Could you believe an tafi location daga nan har Jos amma Aisa ta kasa katabus ko hawa qaramar bishiyo ta kasa. Na yi mata magana ta yi fushi kamar zata yi min rashin kunya. Bash Auta yana cikin fim din ya ce min in zo in same ka za ka fada min gaskiyar al'amari. Idris ka ajiye maganar adawa saboda kowa yana son na sa ya fi na kowa kyau. Kai abokina ne tun muna yara ba za ka so in yi asarar miliyoyin kudina ba. Ka fada min gaskiya wanne siddabaru ku ka yi ? " Su ka kwashe da dariya su ka tafa hannu. Idris ya bude kwanfiyutarsa ya dubo fim din sai ya juyo masa da fuskar kwanfiyotar gabansa daidai fuskar Nihal ya ce "dubi yarinyar nan sosai ." Abbas ya danna puse ya kalle ta ya sake kallonta ya ce " kai ban santa ba, ban ma taba kallon fim dinta ba ." Idris ya gyada kai ya ce " ba za ka santa ba daman dan ba fitacciya ba ce, a qauye take hidimarta tana can cikin 'yan camama." Abbas ya gyara zama ya ce "ban fahimce ka ba fa. Me kake so ka ce min ne ?" Idris ya yi shiru na 'yan lokuta ya ce " maganar gaskiya baqauyiyar nan Allah Ya yi mata baiwa wajen iya tsalle da fadan canis. Kai in fada maka har yadda ake riqe fitala da saita kyamara ta iya. Amma za ka sha mamaki idan na fada maka cewar ko script bata iya karantawa ba, dan bata je makarbata ba." Mamaki marar musaltuwa za ka iya gani a kan fuskar Abbas. Ya tambaya " meye alaqar tattaunawar da muke yi da wannan baqauyiyar?" Idris ya ce " na bar maganar nan a matsayin sirri kai ne kadai zan fadawa gaskiya saboda kai abokina ne kuma tabbas ka kashe kudi masu yawan gaske bana so ka yi asara. Duk acting din nan da ka gani Aisa ta yi a fim dina wanda ya burge ka ya ja hankalinka ka neme ta, to ba ita ce ta yi ba wannan baqauyiyar ce ta yi. Haka hoto da ka gani ya fito fes da taimakonta wajen saita kyamara. " Gumi ne ya ke ta ketowa Abbas duk da A.c da ke busowa a cikin ofishin, kansa ne ya daure. Bash Auta ne yayi sallama ya shigo bayan ya miqa musu hannu sun gaisa sai ya sami kujera ya zauna. Da alama shima ya zo wajen Idris ne ya na da magana da shi. Abbas ya ce da Idris "zo mu fita waje mu qarasa maganar. " Idris ya ce " ah! ba damuwa Bash ya san komai a gabansa aka yi komai shiyasa ma ya ce ka zo ka same ni zan fada maka komai." Bash ya ce " oh maganar 'yar qauyen nan me hikima?Ai yarinyar nan garari ce gaskiya da ta yi boko kuma da 'yar birni ce zaa yi kata'i. Wato ita daban ce, ba normal mutane ba ce. Ba zaa taba samun kamar ta ba gaskiya abinda ta aikata babu mai iya yinsa. " Abbas ya yi ajiyar zuciya ya ce " yanzu meye abin yi?" Idris ya yi dariya ya ce "yadda mu ka yi haka kai ma za ka yi, kawai a dauko bayanta sai a dora fuskar Aisa. A tafi a haka domin fa 'yan kallo su na son buzuwar nan Aisa, farar fatarta da gashin nan har baya yana tafiya da imanin su ." Bash da Idris suka kwashe da dariya suka tafa. Abbas ya tashi ya saka farin gilashinsa a fuska yana ta kai kawo a cikin ofishin yana tunani, tabbas ya shiga damuwa sai su ka rasa meye dalilinsa na shiga damuwa haka. Ya juyo ya dubi Idris ya ce "sake bude min hoton yarinyar nan in gani." Idris ya zabura ya jawo laptop dinsa ya ce " Ah akwai sinasinan da ta dan firfito ma amma a 'yar aike ne dayan kuma a matsayin 'yar wanke-wanke amma duk da haka ta burge wasu da yawa akan kalaman da ta yi amfani da su wajen isar da saqon. Ka san na fada maka bata yi karatu ba ko script bata iya karantawa ba abinda ake karanta nata daban abinda take fada daban sai kuma ka ga abinda ta fada ya fi yin ma'ana." Abbas ya dawo ya zauna su ka hada kai su 3 suna kallon sinasinan da Nihal ta firfito. Tabbas ta iya magana kuma a nutse, ga ta da zazzaqar muryarta, maganganunta akwai hikima. Abbas ya tsayar da fim din ya daga ido ya kalli Darakta Idris ya ce "ka na ganin an yiwa yarinyar adalci kuwa? A dinga daukar acting dinta ana hadawa da fuskokin wasu? Wannan kamar an dakushe ta ne, ba za ta taba zama jaruma ba kenan fa, kuma ana ci da guminta." Idris ya dafa kafadarsa ya ce "abinda za ka lura shine ita fa wannan baqauyiyar ba ta da tsada, ko dubu goma ka bata ko ashirin murna take, daga ita har uban gidan na ta Tukur Wudil, Daraktan fim din shirmen nan na qauye. Su kuma Jaruman birni an san fukokinsu saboda fuskokin ake siya ana kallon fim. Idan ka dauko fuskar 'yar qauye ka saka komai acting din da ta yi babu mai kallon fim dinka, asara kawai zaka yi saboda baa santa ba." Bash ya ce " wannan gaskiya ne gara dai a dinga daukar bayanta ana dora fuskokin manyan, tana dan firfitowa a wasu sinasinan a hankali idan ta yi suna sai a dinga nuna ta gaba daya din. Amma kasada ne ka saka miliyoyin kudinka, sannan ka saka 'yar qauye babu tantama sunan fim dinka asara." Idris da Bash su ka kwashe da dariya. Abbas dai baya dariya sai wani tunani ne me rikitarwa ya dinga addabar kwakwalwarsa. Can ya dago ya dubi Idris da Bash ya ce " ni kuwa zuciyata ta na tunzura ni in tunkari wannan al'amari ko da kuwa zai zame min asarar, zan dauki qaddarar." Cikin rashin fahimta su ka dube shi suka tambaya "wanne al'amari kenan ?" Abbas ya fada cikin muryar sadaukarwa ya ce " zan yi jihadi saboda Allah zan saka yarinyar nan a matsayin Jarumar fim dina gaba daya a saka acting dinta a dora fuskarta ko da kuwa fim din ba zai karbu ba. Dalilinna na yin haka shine sai na ga kamar ana daqushe ta, an qi nunawa duniya baiwar da Allah Ya bata saboda wasu dalilai na daban. Ko dan saboda bata da gata ko dan bata da hanya bata san kowa ba a industry ba. Hakan kuma da muke yi shine yake kawo koma baya a cikin sana'armu. Son kai yayi yawa kawai wa ka sani wa ya sanka ake yi." " A'a abokina kada ka fara yin wannan kasadar an fada maka yarinyar nan fa ba fara ba ce, ga rashin wayewa ko boko bata yi ba. Ta yaya zata iya karanta script? Zama zaka yi ka yi ta fada mata daya bayan daya? " Bash ya ce " amma yarinyar kalar fatarta mai kyau ce ko bata yi bleaching ba har ta fi wasu masu bleaching kyan fata. Ina ganin fa tana da kyau kawai rashin samun sutura me kyau ne da kuma rashin wayewa. Nima na fara ganin maganar Abbas ta na kan hanya in har an taimaka mata ta fito ta waye zata bada a abinda ake so. Ai yarinyar tana da saurin gane abu daga an fada mata take riqewa." Idris yayi shiru kamar mai tunani can ya dago da kai ya dubi Abbas ya ce " ka je dai ka yi tunani sosai kafin ka yanke hukunci, gobe ka dawo min da abinda ka yanke kada ka yi saurin zartar da hukunci ka dawo kana da-na-sani." Abbas ya gyada kai ya ce "haka ne, ka bani lokaci zan je in yi tunani ka tura min fim din a cikin hard drive dina zan je in kalla a nutse inga acting din yarinyar. Yaya ma ka ce sunanta?" Bash ya yi carab ya ce "Nihal Nuren Mubin." Abbas ya maimaita ya sake maimaitawa ya tambaya cike da mamaki ya ce " haka sunanta na gaskiya yake? Kuma ku ka ce 'yar qauyen qayayau ce ko makaranta bata taba zuwa ba? Anya sunanta na gaskiya kenan?" Su ka kwashe da dariya su dukka ukun. Bash ya ce " mu ma abinda ya dinga bamu mamaki kenan, har muka iso kano sunan nan muke ta nanatawa." Idris ya tura masa Fim din a cikin hard drive ya miqa masa, Abbas ya karba ya yi masa godiya gami da yi musu sallama ya fice, ya bar su su na ci gaba da hirar Nihal da irin bajintar da ta yi a fim dinsa, da yadda mutane suka shiga mamaki. Da yadda sunan Aisa ya daukaka a duniyar yan kallo. Ba Aisa kadai ba har Bash ma an jinjina masa yadda yake fada da hawa da sauka akan bishiya, duk kuwa a cikin irin aikin Nihal ne. 11/14/21, 7:19 AM - MY MTN 2: Jamila Umar Tanko (JUT) GABA GADI Ta yi kuka har qarfinta ya qare, a kwance take kan kujera ta yi lamo babu kuzari a sanadiyyar rashin abinci da ruwa a jikinta. Ga qunar zuci da tafasar kwakwalwa. Ta yi juyi sai gata ta runtoma qasa dabas ta fado. Ta na ta birgima akan kafet din da ya ke shinfide a tsakanin kujeru. Ta fada a bayyane " ina ma qasa ta bude in fada ciki . Da ma ace kwanciyar nan da na yi in tsinci kaina a lahira . Ba na son in ci gaba da rayuwa a cikin duniyar nan da nake ciki. "Allah Ka yafe min, rayuwata ta salwanta. " Hannunta ta ji ya taba wani abu, sai ta hau lalube ta jawo abinda take tabawa. Mujallar dazu ce dan haka sai ta daure ta yaga ledar da aka manne. Ta zaro mujallar ta qurawa hoton bangon ido, tabbas ko sau daya ka taba ganinta a duniya daga ka kalli hoton nan za ka shaida ta. Sunanta baro-baro a qasan hoton, Nihal Nuren Mubin sai aka fadi karin magana mai kama da habaici wanda yayi daidai da abinda ta aika. Zaune ta tashi da sauri hannunta na rawa ta nemo fejin da labarin ya ke. Albishir ake yi wa masu bibiyar abin cewa bayan hotunan da aka saki zaa saki bidiyon a ranar asabar me zuwa, a manya-manyan sinimomin da ke ciki da Kewayen qasar, YouTube, Facebook, Instagram har da ma sauran ababen kallo na social media. Ta zabura ta na laluben wayarta dan ta dakatar da mahunta sakin bidiyon nan, sai ta tuna da cewa ai wayarta ta dade a lahira ba za ta taba dawowa ba . Ta yi magana cikin rawar murya " saboda kudi ne yasa su ka yi min haka ko? To zan biya ko nawa ne." Wayar da take kan tebur wato 'land line' ta jawo ta danna lambobinsu ta ci saa an amsa. Da ta fadi sunanta su ka ji muryar sai suka shaida ta. Ta fara magana cikin fushi da daga murya " ku fadi ko nawa ne zan biya ku amma kada ku tona min asiri . " Dariya ta ji an barke ana ta yi ana qyaqyatawa har da buga qafa. Biliyoyin euro din da aka zaiyano mata zaa iya siyan rabin kasarta Nigeria da shi. Duk tulin dukiyar da take tutiya zuri'arta su na da ita ba zata fanshe ta ba . Ta fada cikin tsawa " kotu zata raba ni da ku muddin ku ka nuna bidiyon nan ." " Shin Nihal kin manta kin saka hannu? Ai da amincewarki aka yi ." Steven ne ya tuna mata . Kafin ta yi magana sun katse wayar. Da ta sake kiran wayar ba su amsa ba . Ta sulale ta kwanta yayin da ta fara tunanin qasashen da baa cika zuwa ba, wadanda ba sa cikin lissafin duniya . Wadanda ba su taba ganin baqar fata ba ma. Wadanda aka ce su na cinye mutane . Tabbas idan ta kutsa cikin qasar har ta mutu babu wanda zai yi tunanin nemanta a can. Idan kuma an ci saa sun cinye ta shikenan ma an huta . Qasashen masu qananan ido cikin kauyukansu da basu da hanyar mota sai gada da kwale-kwale, idan aka ci saa ma Kada ce a cikin ruwa take zama ajalinsu. Ta fada a bayyane " Allah Ya sa idan na je tsallake ruwan kada ta cinye ni in huta." A guje ta tashi ta shiga cikin daki, riga t-shirt da wando Jeans ta saka ta dauki jakarta karama wato puse, abinda ta tabbatar ta saka a ciki shine ATM card dinta da kuma passport dinta. Kanta babu dankwali balle mayafi. Ta saka takalmin shiga bandaki wato silifas. Ta fito da gudu daga cikin gidan bata damu da rufe kofofin gidan ba . Burinta kawai ta matsa daga inda aka taba saninta. Kano Nigeria... Dare yayi misalin karfe takwas, Yayyan Nihal sun hallara a babban falon gidan, fuskokinsu gaba daya a cikin damuwa dan ada su na zaton abin nan wasa ne, yanzu sun tabbatar babbar matsala ce. Sun rasa Nihal a waya da duk wata kafa ta social media. Sun tuntubi duk wanda su ka san zasu sami labarinta a acan, sun duba ta baa same ta ba . General Nuren suka hango ya fito daga cikin dakinsa a sukwane. Ya na tafe da sauri har yana tuntube ya kusa faduwa. A waya yake magana cikin fushi da daga murya . " Ambasador! Ka tura yaranka kowacce kusurwa, boda da filayen jiragen sama da na qasa da suke fadin garin. A hana ta fita daga qasar, Nihal nake so in gani a qasata, a damka min ita a hannuna ko a raye ko a mace. Na sake fada na maimaita a shiga ko ina a fadin kasar a nemo min ita ." Ya harare su ya wuce su ya fita da sauri, dukkansu su ka bude baki su na kallon-kallo . Zabura su ka yi da gudu su ka bi bayansa amma tuni ya shige mota ya fita da gudu, wannan karon ma da kansa yake tukawa baya bukatar direba. Ko ina Zai tafi? oho. Major Abubakar ya daki bango ya fada cikin fushi "me yake faruwa ne? Mu na da haqqin mu sani mu ma fa, amma ake boye mana kamar wadansu bare. Me ya sami Nihal?" Wayarsa ya zaro da sauri ya kira Siyama, bata amsa ba sai ya kira yayanta Muqaddas. Muqaddas ya amsa da sauri. Abubakar ya ce " Ina Siyama? Ta qi amsa wayata . Ka fada mata duk abinda ya cutar da qanwata kwaya daya tal a duniya, ba zan yafe mata ba. Sai na tabbatar na yi mata hukunci daidai da abinda ya sami Nihal." "Malam ka rabu da ni. Ka san halinda muke ciki ne? Yanzu haka za ka ji alamar ina ta nishi, gudu nake da qafata a cikin filin jirgin kano.Ina neman Siyama ance jirginsu ya tashi zuwa Abuja. Ta bar wasiqa cewa ta tafi London su hadu da Nihal zasu shiga duniya ba zaa sake ganinsu ba har abada." Muqaddas yana gama fada ya kashe wayar ba tare da ya jira amsa ba . Tashin hankali ya sa Abubakar ya yi wani qara da kururuwa, shi ya jawo hankalin sauran a guje su na tambayarsa. Ya dago da jajayen idanuwansa ya dube su ya ce komai ya gama dagulewa, Siyama ma ta gudu za su hadu da Nihal su shiga duniya." A tare su ka fada "mu je wajen Mummy ko qofar mu balla mu duba mu gani ko tana raye ma, idan tana raye kuwa yau sai an fada mana mugun abinda yake faruwa ake boye mana ." Da sauri suka isa bakin qofar dakin mahaifiyarsu, Aliyu da Umar sun tukirkire sun yi baya zasu tako da gudu su doka da qafa su balla qofar sai Muhammad ya hana su . " ku dakata Ciwon Mummy baya son hayani da tashin hankali. Mace ce mai saukin kai idan mun lallabata zata fada mana komai ." Su duka suka ja da baya suka bashi waje. Ya qarasa jikin qofar ya qwanqwasa sau daya sau biyu sai ya saka kunne a jikin qofar domin ya jiyo motsin bude qofar bandakinta, yana magana cikin sanyin murya da lallashi. " Mummy 'ya'yanki ne gamu nan gaba daya mu 7 muna cikin tashin hankali. Ki bude mana qofa mu shigo dan mu duba lafiyarki. Mummy ke kadai muke gani mu ji dadi a ranmu, idan damuwa ta taba lafiyarki ko kika rasa ranki na tabbatar mun yi sallama da farin ciki mu ma. Mummy ki yafe mana, ki tausaya mana muna sonki " Gaba daya suka hada baki "Mummy muna sonki ki bude kofar ." Baa dauki lokaci mai tsayi ba su ka ji an bude qofa . Professor Shatu ce ta bayyana a bakin qofar idanuwanta sun yi luhu-luhu abin ka da farar fata. Ta rame ta kuje. Su dukka suka durkusa suka gaishe ta . Ta amsa amma dakyar take magana daga gani bayan bacin rai akwai karancin rashin abinci a jikinta. " Mummy ki fada mana dan Allah me yake faruwa da Nihal? " Usman ne ya tambaya cike da damuwa. Za su yi mata magiya ta daga hannu ta tsayar da su sannan ta daddana wayarta ta miqa mu su. Muhammad ne ya karba ya fara karanta sakon a bayyane . Sakon Nihal ne da ta turo mata wanda take neman gafara daga wajen Allah da iyayenta da Yayyanta da saurayin da zata aura. Sakon qarshen ne ya gigita su da ta ce a daya zaa yi biyu ko ta bar duniya ko ta shiga duniya. Ka da ma su yi wahalar nemanta a London don ta qara gaba . Da gaske babu wanda bai gigice ba su ka fara jejjero mata tambayoyin da ba ta san amsoshinsu ba . "Mummy me aka yi mata ? Me ya faru da ita? Da ta turo miki saqon ke me kika ce mata? Ba ki tsayar da ita ba ? " Amsa daya zuwa biyu ta basu ta ja qofarta ta rufe " Ban san abinda ta aika ta ba gaskiya, mahaifinku bai fada min ba ya ce idan na amsa wayarta bai yafe min ba . Abinda nake so da ku shine ku gaggauta barin bakin qofar dakina kafin ya zo ya tarar da ku yayi zaton wani abu mu ke kunsawa. Nihal kuma ina yi mata addua Allah Ya jikanta ku yi mata hukunci daidai da laifin in har ma ta dawo qasar kenan ." Bayan nan sai ta shige ta kulle dakin da mukulli. Hamza zai sake bugawa Muhammad ya riqe shi ya ce " kada ka buga mata qofa . Ku zo mu fita kawai ," Ya wuce gaba su na biye da shi a fusace kowannensu yake . 11/14/21, 7:19 AM - MY MTN 2: GABA GADI Na Jamila Umar Tanko (JUT) Da su ka isa unguwar zoo road sai Hashim ya kira Darakta Abbas a waya sai ya fada masa inda za su tsaya, zaa zo da mota a dauke su. Ba jimawa wata mota qirar Honda civic ta zo ta dauke su, direban bai tsaya a ko ina ba sai Tiga kwanar dawaki. Sun isa wajen sun iske dandazon mutane ana tsaka da daukar shirin.Nihal na dosar wajen abinda kunnuwanta su ka fara jiyo ma ta shine. "yau ma tsinanniyar 'yar qauyen nan su ka sake kwaso mana." Aisa buzuwa ce ta fada. Yayin da dukka 'yan matan da su ke zaune da ita su ka juyo su ka kalli Nihal. Tafiya su ke yi cikin sanyin jiki kasancewar sun shigo cikin wata duniya da baa qaunar ganinsu. " wannan ce wannan me tsallen?Jin ta ya fi gabinta." Wasu samari ne su ke gulma, maganarsu ta gangaro ta fado cikin kunnuwan su Nihal. Har yanzu dai tafiya su ke su na kutsawa cikin jamaa, fatansu su isa wajen Darakta Abbas wanda su ka zo dominsa. Su ka ci karo da Bash Auta da su ka gaishe shi sai ya amsa dakyar cikin rashin sakin fuska, ya wuce abinsa kamar bai taba saninsu ba. Nihal ta isa in da Darakta ya ke zaune, ya na ganinta ya zabura ya miqe cike da murna. "Yauwa zo nan Nihal." Abbas ya fada . Su ka koma gefe ya na yi mata bayanin abubuwan da ake so ta yi. Ya ci gaba da cewa "an ce baki iya karatu ba kada ki damu da bayan ki da jikinki kawai zamu yi amfani ba magana za ki yi ba." Ta gyada kai ta ce "babu damuwa Darakata." Ya nuna mata wani saurayi mai jar riga ya fada mata sunansa Ahmed Usman ya ce ta je wajensa ta karbi kayan da za ta saka. Cikin sauri Nihal ta nufi wajen Ahmed Usman ta fara yi masa bayani.Ya na ji ya yi kamar bai ji abinda take cewa ba, ya ci gaba da hirarsa da su Aisa. Nihal ta sake maimaitawa "Darakta Abbas ne ya ce ka bani kayan yaqi zan saka." Sai can bayan ta dade a tsaye ya juya ya dube ta sama da qasa. Ya ce " au wai da ni kike? Kamar yaya in baki kaya ban sanki ba." Aisa ta kwashe da dariya su ka tafa ita da Hasiya carkwai su ka ce " kai ma ka fada, kwashe-kwashen Darakta Idris ce shima ya jonawa Darakta Abbas ya kwasa." " Au wannan ce wannan me tsallen da su ka samu take burge su? Ni fa ban ma san haka take ba ." Ahmed ya fada cikin isgili. Su dukka su ka kwashe da dariya su ka yi shewa.Sai da su ka gama isgilancin sannan ya miqa mata kayan. zuciyarta sai tafasa kawai take yi kamar za ta ce ta fasa sai ta daure kawai.Ta karba ta juya za ta tafi sai su ka yi kicibus da wani mutum. Har sai da kayan hannayensu dukka su ka zube a qasa, daga nasa har na ta. A fusace ya dago zai rufe ta da fada sai su ka hada ido, Darakta Tukur ne shima ya qaraso dauke da wasu kayan . " ke! Nan ki ka zo? me na ce miki dazu? Wallahi tunda baki da kunya ki ka yi min rashin kunya ba za ki sake yin aiki ba." Su Aisa su ka taso da sauri su ka zo aka kewaye Nihal kowa yana fadar tasa baqar maganar akanta. Hayaniya ta hargitse Hashim da Najaatu ne su ka fuskanci da Nihal ake sai su ka rugo da gudu wajenta.Ta na tsaye ta sunkuyar da kai qasa hawaye ne ke ta kwaranya. Abbas ne ya qaraso da sauri ya na tsawa" wai meye yake faruwa ne ake ta hayaniya haka? " Tukur ya cije baki ya nuna Nihal da yatsa ya ce "wannan marar kunyar ce ta bangaje ni bayan dazu a Wudil ta gama cashe min da rashin kunya.Na yi rantsuwa ba zan sake saka ta a fim ba kuma duk abokaina ba zasu sake saka ta a fim ba ." "ba ita ce aka ce a hannunka Babanta ya damqa ta ba? Ko rannan ma ai kai mu ka nema da ake nemanta." Abbas ya tambaya cike da mamaki da damuwa. " Tukur ya ce " eh mana da ta daina saka barkakkiyar riga sai ta fara ta kai na. Wato na wayar da ita yanzu tafi qarfina." Aisa ta yamutse fuska ta ce "Darakta ka dai gani da idanuwanka,ka nace sai ka yi aiki da ita.Ba ta da mutunci fa ga girman kai,gaskiya in har da yarinyar nan zaa yi aikin nan ni ba zan yi ba." Najaatu ta ja hannun Nihal ta ce "zo mu tafi Nihal ki daina kuka, rabu da su." Abbas ya zabura ya ce " ku tafi ina? Nihal kin fasa yin aikin ko za ki yi?" Hashim ya zabura ya ce " za ta yi mana Darakta, ai abinda mu ka zo yi kenan." Tukur ya zabura ya kaiwa Hashim mari sai ya tsugunna. Tukur ya ce " ka ji dan iska na ce ba za ta sake yin kowanne fim ba kana cewa za ta yi.Munafuki kai ne ka ke zuga ta ka na fasa mata kai ka na nuna mata ta fi kowa, kana tuttura ta har ta ke ji daidai take da kowa." Hashim ya fusata ya ce " shine kuma za ka mare ni. Me nayi maka?" Nan dai hayani ta kaure tsakanin Hashim da Tukur. Tukur ya na surfa masa ashar Hashim ya na yi masa gargadi akan ya daina domin idan ya gaji zai rama shima. Bash Auta ne ya qaraso ransa a bace ya daka tsawa sai kowa yayi shiru ya nuna Aisa da hannu. Ya ce " ke baki da kirki wallahi kin tsani yarinyar nan.Me ta yi miki? In kin yarda da kanki me yasa kike tsoron wata ta zo itama ta gwada ta ta gwanintar? Ina zaune a can duk abinda ya faru ina gani.Kai kuma Tukur da kake rantsuwa ka daina saka ta a fim na ji na yarda fim dinka ne kana da dama amma baka da damar da za ka biyo ta har wani gari ka ce ba za ta sake shiga wani fim ba." An dade dai ana musanyan yawu qarshe aka bawa Nihal haquri aka ba ta kaya ta shiga wani daki ta canja. Ranta a bace yake matuqa da jikinta take yi amma kowa ya san da zuciya take yi,da alama a fusace take dan haka bajintar da ta yi a yau har tafi ta ran nan.Ta yi sukuwa a doki,ta kai sara da takobi, ta hau tsaunuka ta diro. Har ta yi ta gama bata ce wa kowa uffan ba.Ta na gamawa ta wuce cikin wannan dakin ta canja kayanta ta fito. Ta kalli Hashim ta kama hannu Najaatu ta ce "ku zo mu tafi." Abbas ya zabura ya tari gabanta ya ce " yaya za ki tafi?Ai da saura gobe zaa qarasa, akwai gida na musamman da zaa sauke ku, ku kwana sai gobe ku qarasa. " Ta girgiza kai ta ce " ba na kwana a location a gida zan kwana, gobe ku fada min in da za mu same ku sai mu dawo." Ya gyada kai ya ce "toh babu damuwa, ga kudin aikinki na yau." Ta girgiza kai ta ce " ba na buqata a bawa Tukur domin shi ake bawa." Tukur ya cika da mamaki sai kunya ga nadama su ka kama shi.Ta wuce ta bar shi a tsaye sororo. Abbas ya ce " ka ji ta ce a baka saboda ita har yanzu a uban gida ta dauke ka." Bash Auta ya gyada kai ya ce "kun gani ko? Yarinyar nan ba ta da matsala da kowa amma kun bi kun uszura mata. Ita rayuwarta kawai take bata damu da kudi ko neman suna ba." Mamaki ya hana kowa sakat a wajen gata dai talaka futik amma ba ta da kwadayi,an rasa in da ta nufa ko kuma yadda zaa fasalta halinta. A hanya Hashim ya dube ta cike da takaici ya ce " Nihal kin kuwa san abinda ki ke yi? Rannan Tukur ya cinye miki naira dubu ashirin ya hana ki har yau, kuma yanzu ki kalli duk rashin kyautawar da yayi miki dazu amma kin ce a bashi kudinki dukka, alhali ba mu da ko sisi." Najaatu ta ce " to ai nima kaina ya daure." Nihal ta nisa ta ce "wannan shine maganin maqiyi, shine qarshen gaba da zargi.Idan mutum ya munana maka kai kuma in ka tashi ka kyautata masa. Ka da ku damu Allah Zai ba mu yadda zamu yi." Ita ta biya musu kudin mota har Wudil, ba su isa gida ba, Abbas ya kira Hashim a waya ya shaida masa ya bawa Tukur naira dubu ashirin da biyar na Nihal.Sannan gobe su zo zoo road da wuri qarfe tara ta yi musu acan zaa tafi Kaduna da su. Hashim ya amsa bayan sun kashe waya ya yiwa Nihal bayani.Ta yi kokonton zuwa Kadunar nan amma Najaatu da Hashim su ka yi mata magiya su ka bata qarfin quiwa. Sai a yau Najaatu ta taba shiga cikin gidan Nihal tana ta santin kyawun gidan amma Nihal ta tabbatar mata masu gidan sun yi tafiya ne, su suka bata aro. Ta umarci da Najaatu ta kwana gobe sai su wuce kawai. Daki guda Najaatu ta dauka ta baje ita kadai, Najaatu ce ta yi musu girki su ka ci suka qoshi su ka yi wanka sai kowacce ta shige cikin dakinta ta kwanta.Kafin Nihal ta yi bacci sai da ta rubuce dukkan abubuwan da ya faru a yau a wajen daukar fim.Labarin rayuwarta a duniyar fim take rubutawa, shine Fim din da ta kudira za ta fara yi idan ta zama Ex. producer, producer kuma director.Ta kwatanta tsananin quna da zuciyarta ke yi a lokacin da kucakai su ke wulaqanta ta, babu wanda ya mallaki rabi-rabin abinda take da shi a rayuwa. Asuba ta gari Nihal Nuren!!! Tun daga sallar asuba ba su koma ba, bayan sun idar sai su ka yi karatun Qur'ani, su ka gyara gidan, su ka dafa karin kumallo sannan su ka yi wanka. Qarfe takwas da rabi Hashim ya bayyana a bakin get, sai bugu yake da qarfi tana zaton bacci suke. Nihal ta kalli Najaatu ta yi dariya ta ce " Hashim in maye ne idan ya kama mutum dakyar zai sake shi ya fiye naci.Gashi can yana buga qofa har da kwalla kiran sunana, idan ma makwabta ba su san sunana ba yau sun sani. Ki dauki abincin can ki kai masa ki hada masa shayi ya zauna a farfajiyar get daga ciki ya ci." Najaatu ta yi dariya ta ce " ke kadai yake yiwa haka, cab Hashim baya shiga harkar kowa fa. Jininku ne dai ya hadu." Naja'atu ta tashi ta fita wajen Hashim, sauri kawai yake yi ya na ta azalzalarsu su fito su tafi, da kyar ma ya yarda ya zauna ya ci abincin. Doya ce da kwai da shayi hadin kauri. Qarfe tara da rabi a garin Kano ta yi musu, qarfe goma daidai su na ofishin Abbas har an fara taruwa. A doguwar bus aka dura 'yan camama su Nihal, yayin da Jarumai masu aji irin su Aisa su ke cikin tsala-tsalan motoci masu A.c. "Allah kenan komai da lokacinsa." Nihal ta fada a cikin zuciyarta. Sun isa location a Kaduna amma a wajen gari ne. Anan ma an wuni ana gwagwarmaya, Nihal ta koyawa maza fadan canis da sukuwa a doki gami da wasu siddabarun dubarun fim. Nihal ta burge jamaar dake wajen matuqa. Abbas bai taba zaton basirar ta ta kai haka ba ya ji dadi sosai,sai tattalinta yake yana bata kulawa ta musamman. Ko abinci da aka siyo da kansa ya dauko ya kawo mata. Aisa da tawagarta sun cika sun yi taf kamar za su mutu saboda ana ta yabon Nihal. Sun so ta kula su ayi fada amma ba ta kula su ba, hakan da ta yi ta burge kowa. Kaduna za su wuce su kwana sai washegari su wuce Abuja can ma fim din zaa ci gaba da dauka. Amma ita sinasinan da za ta yi sun qare daga yau dan haka sai Abbas ya sallame su daga nan.Naira dubu ashirin ya qara ba ta, Hashin ya yi sauri ya karba kafin ta sake cewa a bawa Tukur. Bash Auta ne ya yi wata magana da ta bawa kowa mamaki. Ya dubi Nihal ya yi murmushi ya ce " ke 'yar china ki shigo mota in kai ku Kano." Nihal ta girgiza kai ta ce " ka bari mun gode." Zai sake yin wata magana ta bar wajen da sauri har ta kusa isa bakin titi. Hashim da Najaatu ne su ka biyo ta da sauri dan sun ga alamar in har ta sami mota shigewa za ta yi ta tafi ta bar su. Aisa ta qule kamar za ta fashe ashe ita duk duniya babu wanda take so irin Bash, shima ya gane haka kowa ma ya gane amma bai ta taba nuna mata ya san tana yi ba, share ta yake dan ba ta gabansa. Habaici Aisa ta yi masa ta ce " amma an ci baya an fadi babu nauyi tunda kiyashi ya kayar da giwa." Abbas ya dube shi ya yi dariya ya ce " in ba neman magana ba kai da za ka kwana a kaduna da safe ka wuce Abuja. Me ya mayar da kai kano? Da ta yarda ka kai su, yaya za ka yi?" Bash ya yi dariya ya ce "wallahi da kai ta din zan yi har Wudil, in ya so sai na dawo da asuba. Ai mace da jan aji aka santa shiyasa take burge ni ba irin su oooh ba." Shima ya rama abinda Aisa ta yi masa sai ranta ya sake baci. Dan haka ma ta qi shiga motarsa da zaa tafi, haka bata kula shi baya kula ta. A Kano su Nihal su ka tsaya suka yi siyayyar kayan abinci na Naira dubu goma, sannan su ka wuce Wudil da misalin qarfe goma na dare. Tsire da biredi da lemo su ka siya su ka ci su ka sha a falon Nihal. Sai yau Hashim ya taba shiga cikin gidan, ya na ta santin kyawun gidan har da kauyanci ya dinga yi, su na dariya. Da su ka taba 'yar hira sai ya tafi gida, bayan sun rufe gida sai su ka yi wanka su ka kwanta.Yau ma Nihal ta rubuta abinda ya faru a garin Kaduna. Kwanansu biyu a gida ba su fita ko ina ba, zazzabi Nihal take yi saboda gajiya da kuma cizon sauro. Magani Hashim ya siyo mata ta sha. Najaatu ce 'yar zaman jinya ta yi amfani da wannan damar sai ta tafi ta kinkimo gaba daya komatsanta daga dakin su Mami, daman su na ta yi mata ciwon baki akan ba ta biya kudin hanyar wancan watan ba ita kuma ba ta da kudi, dan ba a fim din ake saka ta ba ma. Ta ga fuska a wajen Nihal, ta ga mutunci da mutuntawa, ta ga kyauta ba tare da gori ba, komai na ta ta amince kowa ya ci dan haka ta zabi ta zauna tare da Nihal, duk inda Nihal ta saka qafa za ta bi ta. Bacci ne kadai yake raba Hashim da gidan Nihal ko ya fita sai ya dawo. Aike kuwa ko ina shi ne yake je musu. Nihal ta na jin dadin zama da sababbin qawayenta masu qaunarta. Darakta Tukur ne ya ke sallama da Nihal a qofar gida dan haka sai ta fito ta same shi da sauri cike da mamaki. Bayan ta gaishe shi cikin ladabi sai ta sake cika da mamaki da ta ji ya bude baki ya na bata hakuri akan abinda yayi mata na rashin kyautawa, amma duk da haka ita kuma ta saka masa da alkhairi, ta daga darajarsa a cikin mutane. Sai ta yi dariya ta ce "babu komai ya wuce." Ayyuka guda uku ya kawo mata ya ce biyu na sa ne guda daya kuma na Aliyu zaa fara yi.Ta amsa masa babu damuwa za ta yi. Ya tafi ya na godiya ta na godiya sai yanzu ta sake gasgatawa cewar ka yiwa wanda ya baqanta maka alkhairi, ka da ka rama mugunta da mugunta. Da ta bawa su Hashim labari sai su ka yi ta mamaki su ka sake jinjina wannan halin na ta mai kyau kuma abin koyi. Nihal ita ce Jaruma a dukka finafinan nan guda uku, yayin da ta kutsa Najaatu da Hashim a ciki su ma su ka baje kolinsu. Mami da Amina da 'yan korarsu sun shaqi takaici, sun fusata dan baa basu wasu sinasinai masu muhimmanci ba. Abinda su ke gudu shi yake shirin afkuwa Nihal Nuren Mubin ta fara kwace musu waje. Sun yi kwana goma sha daya su na ta fama sannan aka samu aka kammala dukka finafinan. Ba wani kudin kirki su ka samu ba ma dan Tukur baya biyan Nihal idan ta yi masa fim tamkar ya sami baiwarsa saboda ya ga ba ta damu ba. Aliyu ne ma ya ba ta naira dubu goma ko qirgawa ma ta yi ba ta miqawa Hashim. Su ka taho hanya Hashim ya na ta mita ya raina ita kuwa ko uffan bata tofa ba wannan ba shine a gabanta ba. *** *** *** Bayan wata daya cur sannan Fim din Darakta Abbas ya fito. Cikin ikon Allah bajintar da Nihal ta yi a cikin fim din shi ya jawowa fim din farin jini da kasuwa kuma shi ya sake daukaka darajar Aisa. Ex. producer kuma Daraktan fim din Abbas ya sami kasuwa ya sami kudi, ya sami suna. Abbas da Idris ne su ke zaune cike murna su na ta tattaunawa. Abbas ya ce " maganar gaskiya sai na ke ganin kamar ba mu yiwa yarinyar nan Nihal adalci ba fa. Gaba daya nasarar da na samu a fim din nan a sanadiyyar abin da ta yi ne. Amma ka ga ba ta mori komai ba ita baa bata kudin kirki ba, ita baa nuna ta an san fuskarta ba balle ta samu daukaka." Idris ya ce " na fada ma ka gara da ka yi haka a nuna jikinta a nuna fuskar da aka sani. Kai sai zancen adalci ka ke ta faman yi. Ba dai ka biya ta ba? 'Yar qauye ce ta na can ta na gwaguyar kudinta ta na murna. Aka bibiya ma ba ta taba riqe irin wadannan kudade ba." Abbas ya ce haka ne na ba ta dubu ashirin da biyar sannan na qara mata naira dubu ashirin. Ka san wani abin mamaki kuwa? Yarinyar cewa ta yi in bawa Tukur kudin aikin, bayan zagin da Tukur yayi mata a cikin jamaa bai so ba ma aka saka ta a cikin fim din ba. Ta burge ni matuqa, yarinya ce mai ladabi, kudi bai dame ta ba kwata-kwata ma. Ga hakuri wallahi na dauka zagin da su Aisa suka yi mata za ta yi fushi ta fasa yin fim din sai gashi ta ce za ta yi. Kuma wallahi ta na da kyau in har ta sami gyara sai ta fi Aisa kyau." "Haba dan Allah! kai haba Aisa fa farar fata ce. Yaya ma za ka hada ta da wannan baqar." Abbas ya yi dariya ce " kai ba ka san ma shikashikan kyau ba, ba fari kadai ba ne kyau. Kai ne ka yi mata kallon tsoro amma Nihal ta na da kyau, ga kyan jiki ba za ka hada ta da Aisa ba ma. Ina nan da kai ka bari ta wanke ta fara riqe kudi. Ina so in qara mata wasu kudaden dan gaskiya ita ce ta yi silar wannan nasarar tawa." Idris ya ce " ka da dai ka ba ta ta da kudi, mun sami garabasa yanzu muna bata dubu ashirin ta na murna, in ta saba da kudi fa mun shiga uku." Su ka kwashe da dariya su ka tafa hannu. 11/14/21, 7:19 AM - MY MTN 2: GABA GADI Na Jamila Umar Tanko (JUT) Nihal Nuren Mubin ta kwana biyu baa ganinta a garin Wudil, domin kullum da safe idan ta tashi wajen koyon sana'ar hannu take zuwa a cikin wani qauye da yake kusa da garin Gaya. Anan ta ke koyon yadda ake kwaba qasa (laka) a mayar da ita randar qasa da bankin qasa har da abin d'ana waina na qasa. Bayan an gama akwai wata kwalliya da ake yi musu na zane da fenti duk su take koyo a wajen wasu 'yan uwan Inna kakar Hashim. Ta na jin dadin sabuwar rayuwarta tare da sababbin mutane, ta na jin tausayinsu su na jin tausayinta, su na mutunta ta ta na mutunta su. Riba biyu take samu ga koyon sana'ar hannu ga samun labarun da zata iya zamar da shi fim. A yanzu ta gane matsalolin dake addabar qauyawa, ta san damuwarsu ta san abin da suke fatan su samu. Daman ta gama koyon saqar tabarmar kaba da muhuci a wajen Inna yanzu haka kowacce irin tabarma da muhuci zata iya saqawa in dai na kaba ne. Da la'asar sakaliya Nihal ta dawo daga qauye, ta sauka daga kan babur a qofar gidanta. Ta na tafe ta na layi kamar za ta fadi saboda yunwa da qishirwa, rabota da ta ci wani abu tun ruwan shayi da safe shima rabin kofi.Ta kama gate din gidanta kenan zata bude sai ta ji qarar tsayuwar mota a bayanta, ta juyo da sauri sai ta ga Hashim ya fito daga bayan wata dalleliyar mota ja.Ransa a bace yake ya tunkaro ta yana ta balbalin fada har da kumfar baki, yana tafe yana baza hannu. "dalla malama ina ki ke tafiya ne? Ana ta nemenki an rasa ki tun shekaranjiya. An ce ki sayi waya kin qi, na baki tawa aro kin qi karba. A ina aka taba zama Jaruma babu lambar wayar da zaa same ki? Ga manyan baqi nan daga Kano su na ta nemanki, tun su na kira a waya har sun zo da kansu." Tsayawa ta yi cak tana kallon bakinsa cike da mamaki da takaici. Ta ce a ranta " lallai wannan ya cika dan shishshigi mai daukar matsalar wani ya dorawa kansa, tabbas bashi da aikin yi ne in ba haka ba ina ruwansa da rayuwata? A turai a ina zaa aikata wannan danyen aikin? An bawa kowanne dan adam dama ya zabi abinda yake so yayi a lokacin da yake so." Hashim ne ya katse tunanin da take ya ci gaba da cewa " ki taho da sauri wajen motar can su Bash Auta ne shi da Babban Darakta Abbas.H.Abbas." Nihal ta rasa amsar da za ta bashi dan takaici.Ta juya ta ci gaba da qoqarin bude get, sai Hashim ya zabura ya fusge mukullin daga hannunta. Ya murtike fuska tana zazzare mata ido ya ce " wallahi ba ki isa ba, in kin shiga gidan nan yau Allah Ya tsince min sai kin zo mun je wajensu.Haba Nihal Allah Ya kawo miki daukaka ki na wasa." Ta fusata ta ce "bani mukullina, yau zan ga yadda za ka ce dole sai na yi abin da ba na so." Hashim ya sassauta murya ya na magana cikin rada "ki rufa min asiri ki zo mu je dan na yi musu alkawari zan nemo ki, na nuna musu ke qanwata ce. Sannan in kin samu shiga babban fim nima zan samu ki saka ni. Ki taimake ni Nihal dan Allah." Har wata kwalla ce ta cika masa ido saboda tsananin son sai ta je kiransu. Sai ya bata tausayi ta fara tafiya a nutse ta nufi wajen motar. Gefen direba aka bude sai ga Bash Auta ya bayyana, ya kira sunanta gami da dubanta sama da qasa.Ta yi budu-budu da ita da qura.Qafafuwanta fututu, tun daga nan ya tabbatar wannan ba za ta iya zama shararriyar Jaruma ba a shekaru kusa. Babu alamar wayewa a tare da ita ko ta kwabo. Bash ya yi dariya ya fada a cikin gatsali "Darakta wannan ita ce Nihal Nuren Mubin me abin mamaki." Darakta Abbas ya na zaune a gefen Bash sai leqe yake. Ya yi dariya ya ce "Malama Nihal bismillah zagayo ta nan mana mu yi magana." Ta zagaya ta gefen qofar da ya ke zaune, ta durqusa ta gaishe shi cike da ladabi. Tun daga qafarta har kanta ya kalla, ta yi fururu kai ka ce dambe ta yi a cikin yashi. Ya murmushi ya tambaya "daga ina kike ne haka?" "Daga qauye." GABA GADI ta amsa masa. Ya sake maimaitawa "daga nan qauyen ki ka sake shiga can cikin qasurgumin wani qauyen?Maimakon ki taho gari irin su Kano." "Na fi jin dadin rayuwata tare da 'yan karkararmu." Ta bashi amsa daidai da tambayarsa. "Na ga bakinki a bushe kamar kina jin yunwa da qishir ruwa.Bash bata sauran tsiren nan da lemo ta ci ko ta dawo hayyacinta." Darakta ya fada a lokacin da ya ci gaba da dubanta sama da qasa. Nihal ta girgiza kai ta ce "ba zan ci ba,na gode." Hashim ya zabura ya ce "kawo in riqe mata,kunya ce da ita." Bash ya miqa masa, hararar Hashim kawai take yi. Darakta ya ce " meye abin harararsa dan ya fadi gaskiya?Kowa ya ganki ya san ki na jin yunwa watakila ma noma ki ka yi, ga ki nan kin yi bududu. Ko fadan canis ku ka yi a kan yashi?" Da ta yi dariya sai su ka ga ta qara yin kyau, ga wata siriryar wushirya da dimful a kumatunta sun bayyana. Darakta ya ce " ko ke fa da da ki ka yi dariya kin fi kyau, amma mu zo tun daga uwa duniya Kano ki na ta sha mana kunu." Ya saka hannu a aljihu ya zaro naira dubu biyu ya miqa mata. Ya ce "ki je ki ci abinci. Zan yi magana da Tukur ko wannan yayan na ki Hashim don ya ba mu lambarsa idan buqatar hakan ta taso. Ni Sunana Darakta Abbas dan naga kamar baki san da wa kike magana ba ma." Ta girgiza kai ta ce " ka bar kudinka, na gode sosai." Kafin mamaki ya bar fuskokinsu ta juya ta tafi, ta fisgi mukullinta daga hannun Hashim ta wuce. Sun dade su na kallonta har ta bude get ta shige. Hashim ya na ta bayani akan su kawo dubu biyun ya kai mata ita me kunya ce. Bash ya tamabaya "wannan gidan waye me kyau ta bude ta shiga?" Hashim ya zabura ya ce "gidan 'yan uwansu ne take dan zama kafin mu tara kudi mu kama mata dakin haya." " ko kudin kama dakin haya bata da shi amma ta ke jan aji?Har a bata kyautar kudi ma ta qi karba? Darakta rufe qofar mota mu tafi kawai." Bash ne ya fada cikin fushi gami da jan dogon tsaki.Ya fusgi mota su ka tafi rayukansu a bace.Maganar ta su ke ta yi har su ka iso Kano. Bash ya na ta bambamin fada ya na cewa " ka san mutumin qauye kuma ya hadu da jahilci.In ba rashin wayewa ba ki na kucaka ki kaga danqareriyar mota da manyan baqi. Baqin ma Bash Auta da Darakta Abbas ne da kansu amma ki nuna baki taba saninmu ba kuma baki damu ba. Ka da ma ka saka ta a fim dinka, kawai ka rabu da ita ta qare a qauyen." Abbas ya yi dariya ya ce " nima dai na yanke hukunci ba zan saka ta ba ma kawai a bar maganar ta, amma na yi mata uzuri saboda a galabaice take." Hashim ne a fusace yake ta bugun get din Nihal, sai can da aka jima ta fito ta dube shi ransa a bace. Ya ce " shikenan kin yiwa kanki, sun yi fushi sun tafi." Ta yi murmushi ta ce " ba rabona ba ne idan rabona ne zan samu." Akan dakali su ka zauna Hashim ya na ta cin tsire da lemo saboda baqar yunwar da ta addabe shi.Ya na zaiyano mata wuraren da ya tafi nemanta. Tukur ne ya ja ya tsaya akan babur dinsa har da tayar da qura dan a fusace yake. Ya kira sunanta sannan ya danqara ashar ya dora da cewa " ba na son wulaqancin banza.Mutanen nan tun shekaranjiya suke yi min waya na sa a nemo ki aka rasa ki, ba su haqura ba suka taso da kansu su ka zo, aka dinga nemanki tare da su. Da su ka ganki sai kika yi musu wulaqanci.Ke wacece da za ki wulaqanta babban Darakta? Da me kike taqama? Wannan da baa san asalinki ba ma ba qaramin girman kai za ki yi ba. Kuma da kin yi boko da an shiga uku.Wawuya kawai sai shegen girman kai ba ki da ko sisi.Bari ki ji wallahi in kika sake yi min haka in ga samu na ga rashi, ba zaginki kadai zan yi ba dukan tsiya zan yi miki. Dan haka ki shirya gobe mu je Kano mu ba su haquri." Kanta a sunkuye a qasa zuciyarta na tafasa kunnuwanta na zuqar baqaqen maganganunsa masu muni.Saura kadan ta taka masa burki ta dai daure. Har ya gama ya ja babur dinsa ya tafi ba ta dago da kanta ta dube shi ba.Hashim ne ya karba shima ya ci gaba da zazzaga mata ta sa masifar, shima haushinsa kenan sun ga samu sun ga rashi. Da ya leqa fuskarta sai ya ga hawaye ne yake ta disa daga idanuwanta sai ya ji tausayinta. Ya shiga lallashi "Au Nihal kuka kike yi? Ki daina kuka.Kece da abin haushi wallahi." Ya ciro wani daddaudan hankici daga aljihunsa ya naninqa mata a kumatu. Ba ta san sanda ta rufe shi da duka ba, ta tashi a fusace ta shige gida ta datse get dinta. Hashim ne yake ta shafa wuyansa inda ta mammake shi. Ya yi dariya ya ce "shegiya uwar qarfi, wallahi qashi daya gare ta. Gara in bar qofar gidan nan kada ta sake dawowa ta yi fadan canis da ni kamar yadda ta yi wa Amina 'yar kwalisa." Nihal na shiga gida sai ta barke da kuka me tsanani, ta na takaicin yadda ta tsinci kanta cikin qasqantacciyar rayuwa wacce kowa ke da ikon zaginta da kyara da wulaqanci. Daman Tukur ya saba yi mata irin wannan tijarar, yanzu kuma ga Hashim abokinta kwaya daya kacal wanda take samun sauqi a wajensa shima ya fara kyararta. " Ina zan saka raina?" Nihal ta fada a lokacin da ta kifa kanta a kan filo tana rusa kuka. Da daddare Shazali ya zo ya kwankwasa mata qofa, ta bude da sauri suka tsaya a qofar gida.Bayan ya miqa mata ledar abinci sai ya shaida mata mahaifinta ya ce ya hada su a waya zai yi magana da ita. Da farko ta qi yarda dan bata so su sake jin muryarta a shekaru kusa,sai dakyar ta yarda ta karbi wayar. Da ta ji muryar mahaifinta sai ta ji dadi, wani hawaye mai sanyi ya dinga kwaranya.Amma da ya isar mata da saqon da zai fada sai ta ji tamkar tunda Allah Ya halicce ta bata taba jin labari mai zafi irin na sa ba.Ya fada ya maimaita yau ce rana ta qarshe da zai ci gaba da kashe mata kudi.Ya ciyar da ita har na tsawon watanni uku ya kamata in har aikin take ace yanzu tana da wasu kudaden aikin da aka biya ta, dan haka sai ta fara yiwa kanta komai da su. Ya tabbatar mata da cewa ya janye siya mata abinci, kudin kashewa,da biya mata kudin haya.Dan haka idan bacci take ta farka dan baya ganin finafinata su na yawo a gari.Har Shoprite yake shiga sinima in zaa saki sabon fim amma bai taba ganinta ba.Ya na so ta sani ba bacci ya ce ta je ta yi ba, aiki tuquru yake so ta yi. Ta runtse ido zafafan hawaye ke kwaranya ta fada cikin rugugin kuka ta ce " Daddy! ka yi hakuri ka daina bibiyar rayuwata, ka bar ni zan san yadda zan yi in tafiyar da rayuwata.Ni Nihal Nuren na yi maka alkawari ba zan sake neman komai daga wajen kowa ba. Fina-finaina kuwa zasu cika gari, zasu kai in da ma baka taba zato ba insha Allah, ka bani lokaci kawai kuma ka yi min addu'a. Na gode." Ta miqawa Shazali waya ta shige ciki gida ta datse. Sai a yanzu ta yi kuka na gasken-gaske. Ta ji kamar duk duniya sun tsane ta, bata da kowa kuma. Qarfin zuciya ne kawai yake ta sauko mata.Haqiqi yanzu ne zata fita ta yi gwagwarmaya ta daina bacci.Tukur da Hashim sun fada mata gaskiya cewar tana wasa da damarta, haka ta daina ganin laifin Amina da Mami akan zagin da suke yi mata tabbas su na tsoron kada ta zo ta meye musu wajen cin abincinsu. Gaskiya ne idan aka fito filin daga baa yi da wasa kowa qoqari yake ya kayar da abokin adawarsa. " Ni Nihal Nuren Mubin na yi alkawari daga rana irin ta yau ba zan sake zama koma baya ba." Alkawari Nihal ta yi. Kusan a tsaye ta kwana ta na ta kai kawo a cikin gida har sai da assalatu ta kusa, sannan ta je ta yi alwallah ta dinga jero nafilfili ta na neman tsari daga dukkan sharri, ta na neman alkhairan da suke cikin wannan harka. Ta yi addua Allah Ya daukake ta,Ya cika mata burinta ta kuma cikawa mahaifinta na sa burin.Ta na neman tsari daga jin kunya da dariyar maqiya. Satin ta guda tana wuni a qauye tun daga safe har dare a wajen koyon aikin kwaba laka, har sai da ta tabbatar ta iya sosai. Hashim da Tukur sun neme ta a garin har sun gaji baa ganta ba domin bacci ne kadai yake dawowa da ita ta buga sammako ta sake fita kuma. Kayan abinci ta siya sai ta dawo take girkawa ta ci. A yau ba ta fita ba dan haka Hashim ya same ta a gida, daya kwankwansa sai ta fito. Bayan sun gaisa sai ya ce da ita " fushi kike yi da ni kenan shiyasa ma kika qaura kika bar garin har sati guda. Ran Darakta Tukur ya baci ya ce ki zo ku je Kano mu basu hakuri kin qi zuwa.Ya na ta fada yanzu ma shi ya ce in kira ki. Fim din Darakta Abbas dai kin rasa dan har an fara shooting, jiya ma acan Tukur din ya wuni ya kai musu hayar wasu kayan. Haba Nihal ki na wasa da damar da Allah Ya baki amma ki sani ita dama zuwa take sannan ta wuce dan haka kada ki bari ta wuce ki." Ba ta bashi amsa ba ta shiga ta kimtsa ta fito ta kulle gida suka nufi ofishin Tukur. Daga shigarta ko sallamarta basu amsa ba a fusace Tukur yake yi mata magana ya na tsawa kamar zai mare ta. Amina, Najaatu da Mami ne a zaune a cikin ofishin. Hannu Nihal ta daga ta dakatar da shi ta fada cikin fushi " dakata Darakta ya isa haka.Ka dade kana zagina har kana marmarin kai hannu jikina, ban yarda ba bazan taba daukar wannan ba.Fim ne in baa saka ni ba sai me? Ba rabona ba ne idan rabona ya zo zan yi. Menene damuwarku? Menene matsalarku? Idan na qi yi meye na tayar da hankali dan na qi yin fim? Babu mai ciyar da ni ko biya min haya. Ina ganin girmanka ka tsaya a haka kada ka kai ni bango." "Ke Nihal ki na da hankali kuwa? Da Darakta Tukur kike magana fa." Hashim ne ya fada a gigice gami da tasowa da gudu zai toshe bakinta. Ta tunkude shi gefe. Mami da Amina su ka dauki salati har da mimmiqewa tsaye su na dafe kirji. Tukur ya koma ya zauna ya na shessheqa cewa yake "ku bar ta ta dake ni. Ai na wayar da ita, ta daina saka yagaggiyar atamfa." Ta juya a fusace za ta fita daga ofishin sai ya ambaci sunanta. Ta waiwayo a fusace ta dube shi. Ya harare ta ya ce " ba zan sake saka ki a cikin fim dina ba kuma dukkanin abokaina na nan garin da na Kano sai na tabbatar ba zasu sake saka ki a fim ba. Sai zaman garin nan ya gagare ki wallahi da ni kike zance." " Ina jira." Nihal ta fada ba tare da fargaba ba . Ta fice abin ta. Hashim ne ya durqusa a gaba Darakta yana magiya yana bada hakuri amma kamar zuga shi yake sai fada yake ya na kumfar baki. Amina da Mami sun ji dadin da basu taba ji ba dan haka sai suka baje murya su na sake tunzura Darakta su na qarawa da sharri. Najaatu ce ta fito a guje ta tari Nihal a hanya ta na bata baki tana yi mata nasiha. "Haba Nihal yaya za ki yi haka, ina haqurin nan na ki da juriya? Su Mami ma bazanye suka zage ki kika yi haquri dan Darakta ya zage ki me ya sa za ki ji zafi har kiyi masa rashin kunya?" Ba ta bata amsa ba tafiya kawai take ba tare da ta san in da take jefa qafarta ba. Najaatu bata fasa bin ta ba tana ta bayani har suka isa qofar gidanta. Akan dakali ta zauna tana huci yayin da Najaatu ke zaune a kusa da ita. Sun dade a zaune sun yi shiru. Sai yanzu Nihal ta bata amsa " haba Najaatu, Tukur ya na wuce gona da iri so yake ya fara kai hannu yana dukana bayan zagi.Ni akuya ce ko baiwarsa? Ba zan dauki wulaqanci ba kuma dan adam baya wuce rabonsa." Najaatu ta dafa kafadarsa ta ce " haka ne amma da kin daure musamman da yake a gaban maqiyanki ne, yanzu gasu can su na jin dadi." Hashim ne ya qaraso ya zo gefe ya zauna a sanyaye ya ce " yauwa Najaatu ki taya ni fada mata. Nihal taurin kai ne da ita tanzu,amma da farko zuwanta kamar mai sauqin kai." Wayar Hashim ce ta dauki ruri ya na dubawa ya ga sunan Darakta Abbas, ya zabura ya miqe tsaye yana durqushe-durqushe dan ladabi. " Ina Nihal? Ta na tare da kai ?" Darakta ya tambaya. Hashim ya ce " eh gamu nan tare." Hashim ya naniqa waya a kunnen Nihal gami da yin magana cikin rada "Darakta Abbas ne." Nihal ta ji gabanta ya fadi, ta gaishe shi sannan ta tsaya ta na sauraron abinda yake fada. " ki taho Kano da sauri ki same mu a zoo road zan sa a kawo ki qauyen da muke, akwai wani aiki da zamu yi da ke. Please dole sai da ke zai tafi daidai. Idan baki da kudin mota ki ranta.Tunda baki san Kano ba Hashim ya rako ki." Ta amsa cike da ladabi "gamu nan zuwa." Hashim ya daka tsalle ya dire yana murna ya ce "Alhamdulullah shikenan Darakta Tukur da su Mami sai su mutu. Me ya ce miki?" Nihal ta maimaita abinda Darakta Abbas ya ce sai Najaatu ma ta hau murna ta na magiya itama zata raka su.Hashim ya zabura ya ce ba za ta je ba, amma Nihal ta ce su tafi tare babu damuwa . Ko gida ba ta shiga ba kawai babura suka tare su ka hau suka tafi tasha, su na zuwa su ka hau mota zuwa Kano, Nihal ce ta biya musu kudin motar su dukka ukun. 11/14/21, 7:19 AM - MY MTN 2: Jamila Umar Tanko (JUT) GABA GADI A farfajiyar get su ka tsaya kowannensu zuciyarsa tafasa take huci kawai suke yi ji suke kamar qasa ba Zara iya daukarsu ba. Ji suke dama ace Nihal tana gabansu su yi ta duka, harbin iska kawai suke yi su na ta kai kawo a tsakar gidan daman kowa gwani ne wajen zafin zuciya. babban abinda ya fi damunsu shine rashin sanin takamaiman abinda ya ke faruwa. Tun kafin ma su ji abinda ta aikata, sun qudiri niyyar sai sun casa Nihal, sai ta gwammace ba ta fito a tsatsansu ba . Abubakar ya juya ya dube su ya ce " me ku ke tunani ta aikata haka da har ya tunzura Daddy, ya firgita Siyama ta kasa fada? Ku duba ku ka biyayyar da Siyama ta ke yi min, ta san ba na son karya da boye- boye amma ta kasa fada min har ta gwammace in rabu da ita in fasa auren, har ta gwammace ta gudu ta bar iyayenta akan ta fadi abinda yake faruwa. Ba kwa ganin abin nan ba qarami abu ba ne ? " Usman ya ce " na kasa tunano me Nihal za ta aika da har ya rikita su haka . Kalli yadda Daddy yake magana a waya har yana tuntube saura kadan ya kifa." Mu'awiya ya ce " kalmar a kawo masa Nihal a raye ko mace ta gigita ni ." Muhammad ya dago da jajayen idanuwansa ya dube su ya ce " kowa ya fada min me yake tunanin Nihal zata aikata da zai jawo London da Kano gaba daya ta hargitse haka? " Aliyu ya ce " ko kirista ta zama zata auri kirista. In ba haka ba me zai sa Daddy da Mummy su shiga irin wannan damuwa haka? " Gaba daya suka hada baki "wa'iyyazu billah. Allah Ya kiyaye ." Hamza ya ce " ko wani ta kashe acan ? " Su ka hada baki " A'uzubillahi Allah ma ya kiyaye." Umar ya ce " Allah Ya sa ba cikin shege ta kunso ba . Kun san fa karatun 'ya mace a turai babu muharrami." Muhammad ya cije baki ya daki kansa ya ce " kai haba . Muna raye kanwarmu ta aikata daya daga cikin wadannan abubuwa wallahi wallahi da kuwa da hannuna zan kashe ta kuma na kashe banza ." Abubakar ya ce " abin dai da baa so a fada ne amma na san an yi daya daga cikin abubuwan nan da muka yi harsashe. In ba haka ba me zai tayar da hankalin Daddy da Mummy haka ?" "Mummy fa ta san komai boye mana take yi kawai don girman laifin ba zai fadu ba." Hamza ya fada yayin da kwalla ta cika masa ido . Muhammad ya buga qafa ya ce " daya daga cikinku ya shirya, London din zamu je mu taho da ita. Kamar yadda Daddy ya fada ko a mace ko a raye. Daga ita har kawarta Siyama zasu gwammace dama ba su taba sanin ire-irenmu ba. " Gaba daya su ka hada baki "da ni zaa je, da ni zaa je." Shigowar Motar mahaifinsu su ka hango, yana tsayawa ya fito sai ya gansu sun zagaye shi . "Sannu da dawowa Dad. " Su ka hada baki a lokaci guda. Bai amsa musu ba sai ma guzurin harara da su ka samu. Qoqari ya ke ya keta ta tsakiyarsu ya wuce. Muhammad ya ce " Daddy muna cikin damuwa, muna so mu ji abinda yake faruwa." Daddy ya ce " idan ta yi tsami za ku ji ." Ya wuce abinsa. Abubakar ya zabura ya ce " Daddy mu na da haqqin mu sani don 'yar uwarmu ce ." Daddy ya fada cikin fushi a lokacin da ya bude qofar falo ya na qoqarin shiga ya ce "babu ruwana da dangantakarku da ita." ya barsu a tsaye. Umar ya fusata ya ce " wannan tsohon fa ya manta da cewa yanzu mun girma ne? Mun zama magidanta, mun wuce yara. Yadda yake mana hukunci da horo irin na da kamar a bariki, irin yadda sojoji su ke idan sun kama masu laifi yanzun ma haka yake so ya ci gaba da yi mana." Muhammad a fusace ya ce " ku jira anan bari in je wajensa." ya wuce ya shiga cikin gida Babu jimawa sai gashi ya fito a guje, su ka tare shi cikin dimuwa suka tambaya ko lafiya? Ya na sheshsheqa ya ce " could u imagine da bindiga ya biyo ni." Aliyu ya kwashe da dariya, gaba dayansu su ka yi kansa da tsawa " meye abin dariyar?" Ya ce " hukuncin Daddy ne ya fara ba ni dariya ma." Wannan karon Abubakar ne ya juya da sauri ya shiga cikin motarsa ya fice. Muhammad ya dubi sauran ya ce "kowa ya tafi, mu hadu gobe da sassafe a babban falo." Ya na gama magana ya shiga motarsa ya fice . Mu'awiya ya bi bayansa shima a cikin motarsa. Yayin da sauran su ka nufi bangarensu domin kowannesu ya na da ginin gida a cikin gidan . Toh fa! Kwamacala kenan . Tabbas Nihal ta yi gaskiya da ta ce gara ta shiga kasashen masu qananan idanuwa ta bace, gara kada a cikin ruwa ta cinye ta akan ta tunkari hukuncin da wadannan za su yi mata. Major Abubakar ya kira Engr Muqaddas a waya, Muqaddas ya shaida masa su na filin jirgi har yanzu su na jiran isowar Siyama. Domin sun saka wasu ma'aikatan immigration na Airport din Abuja su hana ta shigewa. Har ma an yankar mata tikitin juyowa kano. Abubakar ya shaida musu gashi nan zuwa Airport din shima zai jira isowarta. Asuba ta gari Siyama Abba Muse !!! Sun hallara da sassafe kamar yadda yaya Babba ya umarce su. Kafin su fara magana fitowar mahaifisu janye da akwatin kayansa ne ya katse musu hazari. Kowa ya bude baki ya na mamaki. " Daddy ina kwana." su dukka su ka hada baki. Gami da tasowa da sauri kowa yana so ya karbi akwatin da yake ja. " ku matsa ku bar min akwatina." Ya fada yayin da yake qoqarin ficewa daga falon . A baya su ka biyo shi ba tare da kowa ya iya qara furta wata magana ba. Habibu direba ne ya iso da sauri ya karbi akwatin ya saka a but gami da bude masa gidan bayan motar, ya shiga ya zauna . Muhammad ya qaraso da sauri ya riqe qofar motar ya dukar da kai ya ce "Daddy mun yanke shawara mutane biyu daga cikinmu zamu je London mu dubo halinda Nihal ke ciki . " "Ka da a kuskura a ayi wannan tafiyar, ban saka ku ba. " "Daddy yanzu ina za ka je? Ko London din za ka bi ta? " Hamza ya tambaya. Harara ya wurga musu ya ja murfin motar ya rufe ya ce da Habibi " Ja motar mu tafi please , suna bata min lokaci." Kowa ya sanqare a tsaye ya bi bayan motar da kallo . Ransu ya sake baci tabbas, a zuciye Conel Muhammad ya juya ya nufi cikin gida sai su ma suka bi bayansa kai kace kaza ce da 'yayanta. Bai tsaya a ko ina ba sai a bakin qofar dakin Mummy . Ya fara bugawa har wasu daga cikinsu su ka taya shi bugun amma bata bude ba. " Mummy ki na da labarin Daddy ya yi tafiya yanzu? Ya fada miki kuwa? " Abubakar ya tambaya. Sun cika da mamaki da su ka ji ta basu amsa. " Eh na sani ." Suka hada ido cike da mamaki . "Ina ya ce miki zai je?" Umar ya tambaya. Mummy ta ce " ban sani ba ." Muhammad ya cije baki ya sunkuyar da kai qasa kamar mai tunani. Sannan ya dago da jajayen idanuwansa ya dubi 'yan uwansa. Ya ce " ku bar ta kawai . Da alama fushi su ke yi da junansu." Mu'awiya ya ce " kin ci abinci kuwa? Ko In kawo miki tea?" Wannan karon bata amsa ba, kuma bata sake amsa musu ba ma, har suka gaji su ka tafi . "Me na ke gani ? Me yake shirin faruwa da rayuwar Nihal 'yar auta 'ya ta guda daya da na fi qauna daga cikin 'ya'yana?" Zuciyar Mummy da Daddy ce ta fada a lokacin da kowannensu ya shiga tunani. BAYAN KWANAKI BIYU Da misalin qarfe hudu na yamma, motar General Nuren Mubin ce ta kutso cikin farfajiyar gidan. Bar.Usman da Dr.Hamza ne kowannensu ya daga labulen wundo yana leqe daga bangarensa. Bayan General ya fito, sun cika da matukar mamaki a lokacin da suka hangi Nihal Nuren na biye da shi a baya, cikin matsanancin firgici ta na tafe ta na sanda. Su ka yi wuf da sauri su ka fito. "Daddy sannu da dawowa." Su ka fada a tare. Ya waiwayo da sauri ya ce " yauwa Hamza ku ce da 'yan uwanku ina neman kowa da kowa gobe da safe a falona. Wadanda basa gari ayi musu waya su dawo. A cewa Muqaddas ya kawo Siyama, domin zuwansu ya na da matuqar amfani. " Cikin damuwa su ka amsa masa, yayin da harararsu ta dira akan Nihal sai ta zabura ta qara sauri a tafiyar da take. Kallo daya zaka yi mata ka san a firgice take kuma a wahale. Ba ka iya hango kwayar idanuwanta saboda kumburin fuska. Habibu direba ne ya zo giftawa ya na janye da manyan akwatunan Nihal har guda uku. Daga nan su ka tabbatar ta qauro gaba daya. Usman ya tambayi Habibu direba daga "London ku ke?" Habibu ya ce " A' a a Abuja mu ka jira isowar Nihal Autan Daddy." Usman ya kalli Hamza, Hamza ma ya dube shi su na cikin damuwa. Usman ya ce " ban ga alamar ciki a jikinta ba fa." Hamza ya ce "daman waye ya ce lallai-lallai ciki ta yi? Mu jira goben mu gani. Zo mu je mu kikkira su a waya, domin Conel yana Lagos, Major ya na Kaduna , Asp Aliyu ya tafi Abuja. A ce duk su juyo su dawo gida kenan." 11/14/21, 7:19 AM - MY MTN 2: Na kudi ne 馃グ馃グ GABA GADI NA JAMILA UMAR TANKO (JuT) Idris ya ce tunda ka na tausayinta ka na so ta daukaka kada ka qara mata kudi, kawai ka sami wani Fim da zaa haska ta sosai ta fito a santa kaga ai ka bata tukuici da shi." Abbas ya yi shiru na dan lokaci ya ce "kuma haka ne fa, idan kudi ne za ta kashe lokaci daya amma wannan taimako ne na har abada. Akwai Fim din da zan fara shooting kwanan nan kawai zan saka ta a ciki ta zama Jarumar fim din." Idris ya girgiza kai ya ce "ka cika gaggawa kada ta zama Jaruma gaba daya ma dau bata roll din da zata taka a ganta sosai ko da a qawar Jaruma ma zata iya fitowa kaga zaa hasko ta sosai nan gaba sai ta haye kujerar Jaruma." Abbas ya ce " me yasa ka ke jin tsoro akan Nijal? Ni kuwa sai zuciyata take bani cewar yarinyar nan fa zata karbu, alamaunta na gani. Ta na da wayo, ga nutsuwa ga, iya magana." Idris ya ce "ka dakata dai ka bi abin a nutse step by step. Zaa zo wajen a hankali." Abbbas ya yi ajiyar zuciya ya ce "haka ne, Allah Ya kai mu." *** *** *** Nihal da Hashim da Najaatu ne ke zaune akan kujerun roba a farfajiyar gidanta da yamma su na shan rake. labari suke su na ta tuntsira dariya.Hashim ya dauko labarin su Mami Harka da yadda yanzu baqin ciki ya ishe su akan Nihal ta zo ta fi su yin suna da farin jini a fim.Najaatu ta na taya shi su ka dinga maganar. Sai yanzu ma Nihal ta ji cewar Amina 'yar kwalisa ta yi rantsuwa in har ta na raye Nihal ba za ta taba zama super star ba. Abin mamaki ko uffan Nihal ba ta tanka musu ba, ta ci gaba da shan rakenta. Su Hashim su ka cika da mamakin game da wannan al'amari. Najaatu ta kalle ta ta yi dariya ta ce " wai! wa ya ga ban san ana yi ba kin ja bakinki kin yi shiru kin bar mu mu kadai mu na babatu." Nihal ta yi murmushi ta ce "wannan shine cin naman mutum ayi maganarsa a bayan idanuwansa bam saba ba kuma ba na yi. Na fi gane in tari mutum gar da gar in fada masa laifin da yayi min." Cikin sanyin jiki Najaatu ta gyada kai ta ce " haka ne wallahi kin fi mu gaskiya." Nihal ta ci gaba da cewa "da sun gane ma da sun daina gasa da ni dan ba abinda ya kawo ni ba kenan. Na yi biyayyar mahaifi na zo in cika aikina in tafi ne kawai." Najaatu da Hashim dai basu fahimce ta ba kuma basu tambaye ta qarin bayani ba. Ta kalli Hashim ta juya ta kalli Najaatu ta ce " abinda ya sa ku ke ganin kamar ba kwa samun nasara a harkar nan saboda kawai ba ku nemi albarkar iyaye ba ne. Ba ku fito da yardarsu ba dan haka ba ku sami addu'arsu ba. Da kun gane da kun je kun nemi izininsu idan sun qi amince ku hakura kawai. Hashim! Inna ta ce a boye ka shiga fim ka na yi mata karya kullum har sai da fim dinka ya fito a gari aka ganka a ka fada mata.Inna ba ta fara yin farin ciki da sana'arka ba har sai bayan da na hadu da kai ta ce min in har haka 'yan fim su ke da sanin darajar dan adam da taimako ta amince Hashim ya yi fim. A gabanka ta fada ko? Alhamdulullah yanzu za ka fara ganin hasken abin. Gyara daya da na ke so ka sake gyarawa shine ka yi amfani da damar da ka samu ko min yaya dai ana biyanka, idan ka yi fim to ka kula da tsofaffin nan sosai. Najaatu! ke gaba daya ma ba ki shigo da yardarsu ba, babban tashin hankalin ma da kika ce gudowa kika yi baa san in da kike ba ma yanzu. Su na can su na kukan zuci da kukan sarari. Wannan bala'in kadai da kika jefa su ya isa ki dinga ganin takaici da wulaqanci. Babban abinda ya bata masana'antar fim kenan ake ganinmu watsatstsu shine na farko, a ta sigar da muke shigowa harkar. Yawanci za ka ga a sanadiyyar auren dole shikenan sai yarinya ta gudo a matsayin ta shiga duniya ta lalace sai ta fado fim ma'ana fim shine qarshen lallacewa alhali ba hakaba ne. Idan mijinki ya sake ki sai ki fado fim shine qarshen cewa kin girmi aure." Najaatu da Hashim su ka zurawa ma ta ido, kansu ya daure ganin yadda take bayani kai kace karantar abin ta yi. Sannan ta manta itama talauci ne ya ishe su ta fito yin fim din. Sai can Nihal ta tuna ashe fa ita baqauyiya ce marar ilimi, sai ta ja bakinta ta tsaya. Najaatu ta yi ajiyar zuciya ya ce "duk abinda kika fada gaskiya ne. Ni yanzu ki bani shawara menene abin yi? Yadda mahaifinna ya tsani fim ba zai taba bani izini in yi fim ba, haka mahaifiyata ba za ta yarda ba. In sun ji labari ma na fara fim watakila su hadiyi zuciya su mutu dan baqin ciki. Ga babban laifin da na aikata sun bani miji na qi yarda, babban laifi da na yi musu shine da na gudo na shiga duniya. Duk duniya babu wanda zai yarda da cewa ba karuwanci make yi ba." Sai ta fashe da kuka. Nihal ta shafa bayanta kamar yadda ake lallashi yaro ta ce " kada ki yi kuka, har yanzu ba ki makara ba . Zan baki shawara mai bullewa insha Allah." Najaatu na jin haka sai ta tsagaita da kukan ta dago da sauri ta kalli Nihal ta ce " ta ina zan fara?" Nihal ta ce ki shirya ki zo mu je garinku ni zan yi musu kalaman da za su yafe miki kuma su janye maganar yi miki auren dole." Najaatu ta ce " amma ko sun yafe min ba zasu taba bari na in dawo fim ba, ni kuwa a rayuwata babu abinda na fi so irin in yi fim." "Sai me in sun hana ki kiyi fim? Sai ki yi zamanki a gida tare da su har sai sun fahimce ki a hankali. Idan su ka qi daman kin yi karatun sakandire, ki koma makaranta kawai ko NCE ki yi. Laifinsu daya auren dolen da su ka yi yunkurin yi miki domin baya cikin tsarin addini da al'ada duk da na san ba zasu zabar miki abinda zai cutar da ke ba. Kuma da kin yi biyayya kin bi zabinsu sai ki ga haske a cikin auren." Hashim ya ce " har yanzu ina nazarin maganar da kika fada min. Gaskiya ne daga lokacin da kakannina su ka ce sun amince da yawun bakinsu in yi fim daga sannan na fara ganin haske da kudi hankalina ya kwanta na daina fargaba, haka da kika ce in dinga kula da cinsu wallahi tun daga lokacin na ke ganin albarka. Gaskiya mun gode da zama da ke, muna qaru sosai." Hashim na rufe bakinsa sai su ka ji hayaniya a qofar gida muryar mata da maza da qarar tsayuwar motoci. A guje Hashim da Najaatu su ka fita amma Nihal ta qi fita, sun dade a waje su na kallo. Hashim ya shigo a gigice ya ce "Nihal ki taso ana rigima a kanki har da 'yan sanda." Ta dube shi sororo kallo na rshin fahimta. Ya ci gaba da cewa su Mami harka ne su ka biya wasu 'yan daba su dake ki, ban san yaya aka yi ba 'yan sanda su ka ji labari su ka damqe samarin su kuma su ka tonawa su Mami asiri." Nihal ta yi shiru ta na tunani tabbas Shagali ya fada mata cewar Babanta ya biya 'yan sanda su na bibiyarta su na gadinta. "Allah gatana. Ya Allah Ka ci gaba da kare ni.Ka dubi kyakykyawar zuciyata." Nihal ta fada a lokacin da ta miqe tsaye ta shige falonta. Hashim ya zabura ya ce "ina za ki je kuma? Ki zo mu je waje ki ga ganewa idanuwanki." Ta bashi amsa ba tare da ta juyo ba "me zan je in gani. Abinda na sani shine ina addu'a kuma ina da kyakykywar niyya akan kowa. Ko an neme ni ka ce ba na nan kawai." Sai washegari da safe Nihal ta amsa kiran 'yan sanda ta je ofishinsu a inda aka garkame Mami, Amina 'yar kwalisa da Iyantu bisa zarginsu da biyan 'yan daba da su zo gida su dake ta. Daya daga cikinsu ne ya tuna da cewa Nihal ce ta taimake shi da kudi a lokacin da ciwo ya kusa kashe mahaifinsa shine ya kai qara wajen 'yansanda asiri ya tonu. Bayan da aka yiwa Nihal bayani aka tabbatar mata zaa kai maganar kotu sai ta ce ta yafe kada a kai su kotu sai dai a rubuta statement a tsakaninsu duk abinda ya same ta nan gaba su ne. Su Mami ne aka fito da su daga bayan kanta sun galabaita Kumar Nihal suke ji babu wacce ta iya hada ido da ita. Dole 'yan sanda suka sa suka durkusa suka bawa Nihal hakuri haka su ma 'yan dabar da suka so yin aika aika suka yi nadama gami da alkawarin ba zasu sake yi ba. Bayan sun fito ne Najaatu ta yiwa su Mami tatas ta tuna musu cewar ta sha fada musu akan Nihal zasu ji kunya dan ita bata da mummunar niyya akan kowa. Hashim ma ya cashe musu yayi musu tatas. Babu wacce ta iya tsayawa ta basu amsa dan kada jamaa su taru aji aika aika da suka tafka amma tuni magana ta cika gari kowa ma ya ji kuma ana ta Allah wadai da su. Tukur da sauran abokansa daraktoci sun ji labarin abinda aka so a yiwa Nihal sun yi Allah wadai da su kuma sun kudiri niyyar ba zasu sake saka su a fim dinsu ba sai kowa ya ji shaawar Nihal ta yi masa fim , wannan al'amari ya sa mutanen gari da masu shirya fim sun qara kaunarta. Allah kenan. Aiki ta ko ina kullum Nihal Hashim da Najaatu su na kan aiki daga sun gama wannan sai su Shiga wancan. Nihal ce kuma tauraruwa a kowanne fim. A jajjere sai da tmsuka Finafinai biyar babu qaqqautawa kuma sun sami kudi sosai hakan kamar darajarta da tsadarta ne ya karu. Kudin yana hannun Hashim Nihal ta kalle shi ta ce nawa ne kudinmu gaba daya ya ce ce kudina dubu ashirin na Najaatu dubu sha takwas na ki dubu hamsin da biyar." Ta yi shiru zuwa wani lokaci ta ce " gaba daya idan aka hada ya kama dubu Casa'in da uku kenan." Hashim da Najaatu suka hau murna. Najaatu ta ce "sai kawai mu kama gidan haya tunda nan aro aka ba mu ko da yaushe zasu iya zuwa su tashe mu. Hashim ya ce ai idan Zaa kama gida sukutum rabin kudin ya tafi gara dai ku kama daki daya dubu ashirin ko sha biyar." Nihal ta ce " Hashim ka ware dubu ashirin ka kaiwa Inna da Baba su yi cefane. Ka ware dubu ashirin Zaa kaiwa iyayen Najaatu. Dubu goma zamu yi kudin mota mu kai Najaatu garinsu. A ware dubu ashirin a siyo kayan abinci da su omo da sabulai. Ka dauki dubu goma ka bawa Najaatu dubu goma." Najaatu da Hashim suma sororo kansu ya daure gaba daya amma tana gama fada ta shige daki ta datse ta ce kanta yana ciwo zata dab yi bacci rana. Najaatu ta kalli Hashim shima ya kalle ta, mamaki a cike a fuskarsu. Najaatu ta ce " wannan wacce irin mutum ce? Ta fara bani tsoro fa kamar ba mutum ba ce normal irin mutane ba. Na kasa gane halinta. Aljanu ne fa aka ce basa kashe kudi ko dai ba mutum ba ce aljana ce ta shigo cikinmu?" Hashim ya yi dariya ya ce "wallahi haka take na rasa me yasa bata son kudi kuma ga talaucin da iyayenta ke ciki ta qi ta tuna da Babanta ta yi masa aike ko ta je ta kai musu kawai sai ta rabar da duk abinda ta samu. Ya zu haka dan Tukur baya nan aka biya ta kudin nan da shi zata bawa ko ta ci karo da almajirai kawai sai ta miqa musu dukka. Mu yinyadda ta ce kawai in ba haka ba wallahi kwashewa zata yi ta rabar idan muka qi." Najaatu ta ce " ina tsoron in koma garinmu a hana ni dawowa da na fara jin dadin rayuwar Fim haduwa da Nihal da kai." Hashim ya ce "ki yi abinda ta fada miki kawai na yarda da kaifin tunaninta kuma tana da ilimin addini sosai." Jikin Najaaatu a Sanyaye ta tashi ta raja Hashim gidansu ya kaiwa Inna naira na dukan Naira jar dubu ashirin ya so ya rage ya basu dubu goma Najaatu ta ce ya basu dukka idan Nihal ta bincika ta ji bai basu dukka ba ranta zai baci. Inna ta fara tsuma hannunta na rawa ta karbi wadannan makudan Kudi kamata a mafarki. Tambayar da ta yi shine " Nihal ce ta ce a kawo min ko ?" Su ka masa mata da "Eh ita ce sai ta rusa kukan dadi ta dinga kwararo mata addu'a da fatan alkhairi marar adadi. Haka tsoho ma ya taya ta yana gefe yana addua har da hawayen dadi. *** *** *** Bayan kwana biyu ne su Nihal su ka shirya tafiya garin Darazo gidan su Najaatu wajen iyayenta domin neman yafiyarsu da kuma yardarsu akan wannan sana'a.Hashim dai an yi masa dole ne kawai ya shirya binsu amma ba don son ransa ba. Ya na ganin kamar wannan shishshigi ne abinda bai shafe su ba ne ta shiga ta yi kene-kene. Da sassafe su ka shirya su ka fito zuwa tasha, sun ci saa kuwa su ka sami mota har garin. Sun isa kafin azabar kwatsam 'yan unguwar su ka ga Najaatu kafin su qarasa gida labari ya kaiwa iyayen Najaatu sai kowa ya tanadi taryarta. Tsoro Najaatu take ji a bayan Nihal take ta maqale yayin da Nihal take bata qarfin zuciya tana tunano mata addu'oin da zata yi ta fada a lokacin da masifa da fargaba ta tunkarowa bawa.Nihal ma Addu'ar take yi Hashim yana ta ya su. Ya ja ya tsaya a qofar gida yayin da Nihal ta fara saka kai a ciki gidan ta yi sallama ta shiga. Aka amsa mata sallama a shelaqe. Gidan yawa ne iyaye da kakanni da facaloli waje-waje sai firfiryowa suke yi ana so a ga yadda Mahaifin Najaatu zai yi da ita. Babu wanda ya basu wajen zama sai kallo sama da qasa ake yi musu. Najaatu ta radawa Nihal ta ce kin ga abinda nake gudu ko? Shikenan yau na mutu dakyar in basu kashe ni ba dan duka." Babu mai dukanki ki kwantar da hankalinki." Nihal ta fada cikin qarfin zuciya. Nihal ta tambaya " ina iyayen Najaaatu? Wajenki na zo ko zaku bawa bakuwarku tabarma ta zauna ku saurari saqon da na zo mu ku da shi?" Ba ki da wajen zama a gidan nan kun je kun gama watsewarku acan me zaku ce mana? Ai mun ganku a fim." In ji ganin mahaifinta Najaatu Najaatu su na Sa'idu. Nihal ta yi murmushi ta ce " Alhamdulullah da Allah Ya sa har kun san inda 'yar ku take. Najaatu ta yi kuskure bata kyauta ba ko daya. Hakan ya sa na kawo ta da hannuna don ku hukunta. Tun daga ranar da ta shaida min ta zo ba da yawun iyayenta ba na kudiri niyyar sai na dawo da ita gida kun hukunta ta." Nihal ta jawo Najaatu ta turo ta gaban iyayenta sai Najaatu ta durkusa ta fashe da kuka. Nihal ta ci gaba da magana cikin sanyin murya zafafan hawaye na kwaranya daga idanuwanta. Ta ce "ku dake ta ku kakkaryata idan ta ji ciwo ku zaku kaita a asibiti idan kuma ku ka kashe ta ku ne dai zaku dauke ta ku binne ta bata da kowa a duniya kamar ku. Idan ta zama ta gari da sunanku Zaa kira ta idan ta lalace da sunanku Zaa kira ta. Jini ba wasa ba ne. Kullum dan adam me laifi ne a wajen mahaliccinsa amma kullum Ya na yafe mana. Ya kamata ku yi farin ciki da ganinta ta dawo kuma duk wani qasqanci da yake samun bawa daga makusancinsa ne. Najaatu ba karuwa ba ce bata ma taba yin saurayi ba tun tafiyarta tana can Kardashian kulawar masanaantar fim. Idan aka ce 'yan fim ba ana nufin sai karuwai ba irin wannan kallo ake yiwa duk wata 'yar fim wannan ba daidai ba ne. Idan ku ka zargi yar ku da cewa ta Shiga fim ta iskance haka jamaar gari zasu dauka kuma idan magana ta fita babu yadda zaku taro ta sunanku ku dukka ya baci. Ku ti mata uzuri dalilinku ta fita aka rasa ta . Me yasa ba Zaa bar yarinya ta zabi mijin da take so ba me yasa Zaa yi yunkurin yi mata auren dole? Iyayen da su ke tilastawa yaransu aka sai sun aikata abinda basa so sukan jefa yaran a cikin matsala. Na kawo muku Najaaatu 'yar ku ko ku karbe ko ku sake nemanta ku rasa kada ku ga laifinta idan ta sake guduwa saboda ukuba. " Nihal ta turawa Najaatu akwatin kayanta ta ce " ki zauna da su ki basu hakuri ki bi wancan shawarar da na baki . Ni zan tafi na barki lafiya ." Najaatu ta zabura ta kama hannu Nihal ta ce "jada ki tafi ki bar ni ba ki tsaya kinga yadda za su yi da ni ba." Mahaifin Najaatu ne a fusace ya yi magana " Najaatu dauki akwatin kayanki ki bi ta ku je can ku karanta na sallama ki." Mahaifiyar Najaatu ta yi carab ya kama hannun 'yarta ta ce " mun Sami ta dawo babu in da zan bari ta sake tafiya sai dai ka kore mu tare ." Ta ja hannunyar ta suka shige daki. Dadi ya kama zuciyar Nihal ta share hawaye ta yi murmushi ta ce Alhamdulullah ta fice ta bar su a tsaye sororo. Sai a lokacin su ka fara magana kowa yana fadar albarkacin bakinsu. Wasu fada su ke yi me yasa Zaa karbi Najaaatu wasu kuma su na fadin maganar Nihal gaskiya ne hannunka ba ya rufewa ka yanke ka zubar. Ta fito ita da Hashim suka dunguma zuwa tasha domin komawa garin Wudil. Hashim yana ta jero mata tambayo Alan abinda ya faru da alama bata son yin magana abinda yake damunsa shi yake damunta. Ta ce masa ya bari zata bashi labari daga baya. Su na zaune a mota sai wayar Hashim ta yi qara yana dubawa sunan Darakta Abbas ne ya bayyana nan da nan ya amsa cikin garin ciki. Bayan sun gaisa tambayar da yayi shine ina Nihal? Hashim ya miqa mata waya da sauri gami da fada mata suna mai kira. Nihal ta yi sallama ta gaishe shi amma tana cike da mamaki da zumudi son jin dalilin kiran. I.sha Allah ta san alkhairi ne. Abbas yana mai farin cikin sanar mata zai fara daukar wani babban fim kuma yana yi mata Albishir da cewa zata fito a matsayin Tauraruwar shirin gaba daya." Sai ta yi hamdala ta yi godiya. Ya ce in da hali ta shigo kano yanzu don su tattauna. Ta sanar2a da Hashim abinda ya fada sai suka bawa masu mota hakuri suka fita suka canja mota mai zuwa Kano. Hashim da Nihal su ka cika da murna sai dai Hashim yana tsoron yadda zata kaya tsakaninNihal da Adnan gaba jaruman birni su Aisa Buzuwa. Amma ya lura Nihal ko aikinta bata kawo wannan a ranta. Ya kalle ta cikin sanyin jiki ya ce " tsorona daya su Aisa buzuwa ba sa kaunarki. " Ta kalle shi ta yi dariya ta ce " baba fargabar hakan karka damu na shirya musu." Kan Hashim ya sake daurewa sai ya bi ta da kallo kawai a ransa yana fadin na yarda da basirarki da jarumtarki Nihal Nuren Mubin. Sun isa kano unguwar zoo road lafiya. A bakin ofishin Abbas idanuwanta su ka yi mata kicibus da a abinda ya firgita ta ya yamutsa tunaninta. Ta yi turismo ta tsaya gami da ja da baya da sauri ya dafe kirji. Kalmar innalilahi wa inna ilaihi rajuun ta ambato yayin da tsakar jikinta ta tashi jikinta ya dauki karkarwa. Hashim zo mi juya Wudil na fasa shiga." Tambayar ta yake " Nihal wai meye? Me yake faruwa ? Me kika Hango? Amsa daya ta gagari fita daga bakinta. Tabbas razana ta kai kololuwar razana gaba daya ya fita hayyacinta. 11/14/21, 7:19 AM - MY MTN 2: GABA GADI Na Jamila Umar Tanko (JUT) Da su ka isa unguwar zoo road sai Hashim ya kira Darakta Abbas a waya sai ya fada masa inda za su tsaya, zaa zo da mota a dauke su. Ba jimawa wata mota qirar Honda civic ta zo ta dauke su, direban bai tsaya a ko ina ba sai Tiga kwanar dawaki. Sun isa wajen sun iske dandazon mutane ana tsaka da daukar shirin.Nihal na dosar wajen abinda kunnuwanta su ka fara jiyo ma ta shine. "yau ma tsinanniyar 'yar qauyen nan su ka sake kwaso mana." Aisa buzuwa ce ta fada. Yayin da dukka 'yan matan da su ke zaune da ita su ka juyo su ka kalli Nihal. Tafiya su ke yi cikin sanyin jiki kasancewar sun shigo cikin wata duniya da baa qaunar ganinsu. " wannan ce wannan me tsallen?Jin ta ya fi gabinta." Wasu samari ne su ke gulma, maganarsu ta gangaro ta fado cikin kunnuwan su Nihal. Har yanzu dai tafiya su ke su na kutsawa cikin jamaa, fatansu su isa wajen Darakta Abbas wanda su ka zo dominsa. Su ka ci karo da Bash Auta da su ka gaishe shi sai ya amsa dakyar cikin rashin sakin fuska, ya wuce abinsa kamar bai taba saninsu ba. Nihal ta isa in da Darakta ya ke zaune, ya na ganinta ya zabura ya miqe cike da murna. "Yauwa zo nan Nihal." Abbas ya fada . Su ka koma gefe ya na yi mata bayanin abubuwan da ake so ta yi. Ya ci gaba da cewa "an ce baki iya karatu ba kada ki damu da bayan ki da jikinki kawai zamu yi amfani ba magana za ki yi ba." Ta gyada kai ta ce "babu damuwa Darakata." Ya nuna mata wani saurayi mai jar riga ya fada mata sunansa Ahmed Usman ya ce ta je wajensa ta karbi kayan da za ta saka. Cikin sauri Nihal ta nufi wajen Ahmed Usman ta fara yi masa bayani.Ya na ji ya yi kamar bai ji abinda take cewa ba, ya ci gaba da hirarsa da su Aisa. Nihal ta sake maimaitawa "Darakta Abbas ne ya ce ka bani kayan yaqi zan saka." Sai can bayan ta dade a tsaye ya juya ya dube ta sama da qasa. Ya ce " au wai da ni kike? Kamar yaya in baki kaya ban sanki ba." Aisa ta kwashe da dariya su ka tafa ita da Hasiya carkwai su ka ce " kai ma ka fada, kwashe-kwashen Darakta Idris ce shima ya jonawa Darakta Abbas ya kwasa." " Au wannan ce wannan me tsallen da su ka samu take burge su? Ni fa ban ma san haka take ba ." Ahmed ya fada cikin isgili. Su dukka su ka kwashe da dariya su ka yi shewa.Sai da su ka gama isgilancin sannan ya miqa mata kayan. zuciyarta sai tafasa kawai take yi kamar za ta ce ta fasa sai ta daure kawai.Ta karba ta juya za ta tafi sai su ka yi kicibus da wani mutum. Har sai da kayan hannayensu dukka su ka zube a qasa, daga nasa har na ta. A fusace ya dago zai rufe ta da fada sai su ka hada ido, Darakta Tukur ne shima ya qaraso dauke da wasu kayan . " ke! Nan ki ka zo? me na ce miki dazu? Wallahi tunda baki da kunya ki ka yi min rashin kunya ba za ki sake yin aiki ba." Su Aisa su ka taso da sauri su ka zo aka kewaye Nihal kowa yana fadar tasa baqar maganar akanta. Hayaniya ta hargitse Hashim da Najaatu ne su ka fuskanci da Nihal ake sai su ka rugo da gudu wajenta.Ta na tsaye ta sunkuyar da kai qasa hawaye ne ke ta kwaranya. Abbas ne ya qaraso da sauri ya na tsawa" wai meye yake faruwa ne ake ta hayaniya haka? " Tukur ya cije baki ya nuna Nihal da yatsa ya ce "wannan marar kunyar ce ta bangaje ni bayan dazu a Wudil ta gama cashe min da rashin kunya.Na yi rantsuwa ba zan sake saka ta a fim ba kuma duk abokaina ba zasu sake saka ta a fim ba ." "ba ita ce aka ce a hannunka Babanta ya damqa ta ba? Ko rannan ma ai kai mu ka nema da ake nemanta." Abbas ya tambaya cike da mamaki da damuwa. " Tukur ya ce " eh mana da ta daina saka barkakkiyar riga sai ta fara ta kai na. Wato na wayar da ita yanzu tafi qarfina." Aisa ta yamutse fuska ta ce "Darakta ka dai gani da idanuwanka,ka nace sai ka yi aiki da ita.Ba ta da mutunci fa ga girman kai,gaskiya in har da yarinyar nan zaa yi aikin nan ni ba zan yi ba." Najaatu ta ja hannun Nihal ta ce "zo mu tafi Nihal ki daina kuka, rabu da su." Abbas ya zabura ya ce " ku tafi ina? Nihal kin fasa yin aikin ko za ki yi?" Hashim ya zabura ya ce " za ta yi mana Darakta, ai abinda mu ka zo yi kenan." Tukur ya zabura ya kaiwa Hashim mari sai ya tsugunna. Tukur ya ce " ka ji dan iska na ce ba za ta sake yin kowanne fim ba kana cewa za ta yi.Munafuki kai ne ka ke zuga ta ka na fasa mata kai ka na nuna mata ta fi kowa, kana tuttura ta har ta ke ji daidai take da kowa." Hashim ya fusata ya ce " shine kuma za ka mare ni. Me nayi maka?" Nan dai hayani ta kaure tsakanin Hashim da Tukur. Tukur ya na surfa masa ashar Hashim ya na yi masa gargadi akan ya daina domin idan ya gaji zai rama shima. Bash Auta ne ya qaraso ransa a bace ya daka tsawa sai kowa yayi shiru ya nuna Aisa da hannu. Ya ce " ke baki da kirki wallahi kin tsani yarinyar nan.Me ta yi miki? In kin yarda da kanki me yasa kike tsoron wata ta zo itama ta gwada ta ta gwanintar? Ina zaune a can duk abinda ya faru ina gani.Kai kuma Tukur da kake rantsuwa ka daina saka ta a fim na ji na yarda fim dinka ne kana da dama amma baka da damar da za ka biyo ta har wani gari ka ce ba za ta sake shiga wani fim ba." An dade dai ana musanyan yawu qarshe aka bawa Nihal haquri aka ba ta kaya ta shiga wani daki ta canja. Ranta a bace yake matuqa da jikinta take yi amma kowa ya san da zuciya take yi,da alama a fusace take dan haka bajintar da ta yi a yau har tafi ta ran nan.Ta yi sukuwa a doki,ta kai sara da takobi, ta hau tsaunuka ta diro. Har ta yi ta gama bata ce wa kowa uffan ba.Ta na gamawa ta wuce cikin wannan dakin ta canja kayanta ta fito. Ta kalli Hashim ta kama hannu Najaatu ta ce "ku zo mu tafi." Abbas ya zabura ya tari gabanta ya ce " yaya za ki tafi?Ai da saura gobe zaa qarasa, akwai gida na musamman da zaa sauke ku, ku kwana sai gobe ku qarasa. " Ta girgiza kai ta ce " ba na kwana a location a gida zan kwana, gobe ku fada min in da za mu same ku sai mu dawo." Ya gyada kai ya ce "toh babu damuwa, ga kudin aikinki na yau." Ta girgiza kai ta ce " ba na buqata a bawa Tukur domin shi ake bawa." Tukur ya cika da mamaki sai kunya ga nadama su ka kama shi.Ta wuce ta bar shi a tsaye sororo. Abbas ya ce " ka ji ta ce a baka saboda ita har yanzu a uban gida ta dauke ka." Bash Auta ya gyada kai ya ce "kun gani ko? Yarinyar nan ba ta da matsala da kowa amma kun bi kun uszura mata. Ita rayuwarta kawai take bata damu da kudi ko neman suna ba." Mamaki ya hana kowa sakat a wajen gata dai talaka futik amma ba ta da kwadayi,an rasa in da ta nufa ko kuma yadda zaa fasalta halinta. A hanya Hashim ya dube ta cike da takaici ya ce " Nihal kin kuwa san abinda ki ke yi? Rannan Tukur ya cinye miki naira dubu ashirin ya hana ki har yau, kuma yanzu ki kalli duk rashin kyautawar da yayi miki dazu amma kin ce a bashi kudinki dukka, alhali ba mu da ko sisi." Najaatu ta ce " to ai nima kaina ya daure." Nihal ta nisa ta ce "wannan shine maganin maqiyi, shine qarshen gaba da zargi.Idan mutum ya munana maka kai kuma in ka tashi ka kyautata masa. Ka da ku damu Allah Zai ba mu yadda zamu yi." Ita ta biya musu kudin mota har Wudil, ba su isa gida ba, Abbas ya kira Hashim a waya ya shaida masa ya bawa Tukur naira dubu ashirin da biyar na Nihal.Sannan gobe su zo zoo road da wuri qarfe tara ta yi musu acan zaa tafi Kaduna da su. Hashim ya amsa bayan sun kashe waya ya yiwa Nihal bayani.Ta yi kokonton zuwa Kadunar nan amma Najaatu da Hashim su ka yi mata magiya su ka bata qarfin quiwa. Sai a yau Najaatu ta taba shiga cikin gidan Nihal tana ta santin kyawun gidan amma Nihal ta tabbatar mata masu gidan sun yi tafiya ne, su suka bata aro. Ta umarci da Najaatu ta kwana gobe sai su wuce kawai. Daki guda Najaatu ta dauka ta baje ita kadai, Najaatu ce ta yi musu girki su ka ci suka qoshi su ka yi wanka sai kowacce ta shige cikin dakinta ta kwanta.Kafin Nihal ta yi bacci sai da ta rubuce dukkan abubuwan da ya faru a yau a wajen daukar fim.Labarin rayuwarta a duniyar fim take rubutawa, shine Fim din da ta kudira za ta fara yi idan ta zama Ex. producer, producer kuma director.Ta kwatanta tsananin quna da zuciyarta ke yi a lokacin da kucakai su ke wulaqanta ta, babu wanda ya mallaki rabi-rabin abinda take da shi a rayuwa. Asuba ta gari Nihal Nuren!!! Tun daga sallar asuba ba su koma ba, bayan sun idar sai su ka yi karatun Qur'ani, su ka gyara gidan, su ka dafa karin kumallo sannan su ka yi wanka. Qarfe takwas da rabi Hashim ya bayyana a bakin get, sai bugu yake da qarfi tana zaton bacci suke. Nihal ta kalli Najaatu ta yi dariya ta ce " Hashim in maye ne idan ya kama mutum dakyar zai sake shi ya fiye naci.Gashi can yana buga qofa har da kwalla kiran sunana, idan ma makwabta ba su san sunana ba yau sun sani. Ki dauki abincin can ki kai masa ki hada masa shayi ya zauna a farfajiyar get daga ciki ya ci." Najaatu ta yi dariya ta ce " ke kadai yake yiwa haka, cab Hashim baya shiga harkar kowa fa. Jininku ne dai ya hadu." Naja'atu ta tashi ta fita wajen Hashim, sauri kawai yake yi ya na ta azalzalarsu su fito su tafi, da kyar ma ya yarda ya zauna ya ci abincin. Doya ce da kwai da shayi hadin kauri. Qarfe tara da rabi a garin Kano ta yi musu, qarfe goma daidai su na ofishin Abbas har an fara taruwa. A doguwar bus aka dura 'yan camama su Nihal, yayin da Jarumai masu aji irin su Aisa su ke cikin tsala-tsalan motoci masu A.c. "Allah kenan komai da lokacinsa." Nihal ta fada a cikin zuciyarta. Sun isa location a Kaduna amma a wajen gari ne. Anan ma an wuni ana gwagwarmaya, Nihal ta koyawa maza fadan canis da sukuwa a doki gami da wasu siddabarun dubarun fim. Nihal ta burge jamaar dake wajen matuqa. Abbas bai taba zaton basirar ta ta kai haka ba ya ji dadi sosai,sai tattalinta yake yana bata kulawa ta musamman. Ko abinci da aka siyo da kansa ya dauko ya kawo mata. Aisa da tawagarta sun cika sun yi taf kamar za su mutu saboda ana ta yabon Nihal. Sun so ta kula su ayi fada amma ba ta kula su ba, hakan da ta yi ta burge kowa. Kaduna za su wuce su kwana sai washegari su wuce Abuja can ma fim din zaa ci gaba da dauka. Amma ita sinasinan da za ta yi sun qare daga yau dan haka sai Abbas ya sallame su daga nan.Naira dubu ashirin ya qara ba ta, Hashin ya yi sauri ya karba kafin ta sake cewa a bawa Tukur. Bash Auta ne ya yi wata magana da ta bawa kowa mamaki. Ya dubi Nihal ya yi murmushi ya ce " ke 'yar china ki shigo mota in kai ku Kano." Nihal ta girgiza kai ta ce " ka bari mun gode." Zai sake yin wata magana ta bar wajen da sauri har ta kusa isa bakin titi. Hashim da Najaatu ne su ka biyo ta da sauri dan sun ga alamar in har ta sami mota shigewa za ta yi ta tafi ta bar su. Aisa ta qule kamar za ta fashe ashe ita duk duniya babu wanda take so irin Bash, shima ya gane haka kowa ma ya gane amma bai ta taba nuna mata ya san tana yi ba, share ta yake dan ba ta gabansa. Habaici Aisa ta yi masa ta ce " amma an ci baya an fadi babu nauyi tunda kiyashi ya kayar da giwa." Abbas ya dube shi ya yi dariya ya ce " in ba neman magana ba kai da za ka kwana a kaduna da safe ka wuce Abuja. Me ya mayar da kai kano? Da ta yarda ka kai su, yaya za ka yi?" Bash ya yi dariya ya ce "wallahi da kai ta din zan yi har Wudil, in ya so sai na dawo da asuba. Ai mace da jan aji aka santa shiyasa take burge ni ba irin su oooh ba." Shima ya rama abinda Aisa ta yi masa sai ranta ya sake baci. Dan haka ma ta qi shiga motarsa da zaa tafi, haka bata kula shi baya kula ta. A Kano su Nihal su ka tsaya suka yi siyayyar kayan abinci na Naira dubu goma, sannan su ka wuce Wudil da misalin qarfe goma na dare. Tsire da biredi da lemo su ka siya su ka ci su ka sha a falon Nihal. Sai yau Hashim ya taba shiga cikin gidan, ya na ta santin kyawun gidan har da kauyanci ya dinga yi, su na dariya. Da su ka taba 'yar hira sai ya tafi gida, bayan sun rufe gida sai su ka yi wanka su ka kwanta.Yau ma Nihal ta rubuta abinda ya faru a garin Kaduna. Kwanansu biyu a gida ba su fita ko ina ba, zazzabi Nihal take yi saboda gajiya da kuma cizon sauro. Magani Hashim ya siyo mata ta sha. Najaatu ce 'yar zaman jinya ta yi amfani da wannan damar sai ta tafi ta kinkimo gaba daya komatsanta daga dakin su Mami, daman su na ta yi mata ciwon baki akan ba ta biya kudin hanyar wancan watan ba ita kuma ba ta da kudi, dan ba a fim din ake saka ta ba ma. Ta ga fuska a wajen Nihal, ta ga mutunci da mutuntawa, ta ga kyauta ba tare da gori ba, komai na ta ta amince kowa ya ci dan haka ta zabi ta zauna tare da Nihal, duk inda Nihal ta saka qafa za ta bi ta. Bacci ne kadai yake raba Hashim da gidan Nihal ko ya fita sai ya dawo. Aike kuwa ko ina shi ne yake je musu. Nihal ta na jin dadin zama da sababbin qawayenta masu qaunarta. Darakta Tukur ne ya ke sallama da Nihal a qofar gida dan haka sai ta fito ta same shi da sauri cike da mamaki. Bayan ta gaishe shi cikin ladabi sai ta sake cika da mamaki da ta ji ya bude baki ya na bata hakuri akan abinda yayi mata na rashin kyautawa, amma duk da haka ita kuma ta saka masa da alkhairi, ta daga darajarsa a cikin mutane. Sai ta yi dariya ta ce "babu komai ya wuce." Ayyuka guda uku ya kawo mata ya ce biyu na sa ne guda daya kuma na Aliyu zaa fara yi.Ta amsa masa babu damuwa za ta yi. Ya tafi ya na godiya ta na godiya sai yanzu ta sake gasgatawa cewar ka yiwa wanda ya baqanta maka alkhairi, ka da ka rama mugunta da mugunta. Da ta bawa su Hashim labari sai su ka yi ta mamaki su ka sake jinjina wannan halin na ta mai kyau kuma abin koyi. Nihal ita ce Jaruma a dukka finafinan nan guda uku, yayin da ta kutsa Najaatu da Hashim a ciki su ma su ka baje kolinsu. Mami da Amina da 'yan korarsu sun shaqi takaici, sun fusata dan baa basu wasu sinasinai masu muhimmanci ba. Abinda su ke gudu shi yake shirin afkuwa Nihal Nuren Mubin ta fara kwace musu waje. Sun yi kwana goma sha daya su na ta fama sannan aka samu aka kammala dukka finafinan. Ba wani kudin kirki su ka samu ba ma dan Tukur baya biyan Nihal idan ta yi masa fim tamkar ya sami baiwarsa saboda ya ga ba ta damu ba. Aliyu ne ma ya ba ta naira dubu goma ko qirgawa ma ta yi ba ta miqawa Hashim. Su ka taho hanya Hashim ya na ta mita ya raina ita kuwa ko uffan bata tofa ba wannan ba shine a gabanta ba. *** *** *** Bayan wata daya cur sannan Fim din Darakta Abbas ya fito. Cikin ikon Allah bajintar da Nihal ta yi a cikin fim din shi ya jawowa fim din farin jini da kasuwa kuma shi ya sake daukaka darajar Aisa. Ex. producer kuma Daraktan fim din Abbas ya sami kasuwa ya sami kudi, ya sami suna. Abbas da Idris ne su ke zaune cike murna su na ta tattaunawa. Abbas ya ce " maganar gaskiya sai na ke ganin kamar ba mu yiwa yarinyar nan Nihal adalci ba fa. Gaba daya nasarar da na samu a fim din nan a sanadiyyar abin da ta yi ne. Amma ka ga ba ta mori komai ba ita baa bata kudin kirki ba, ita baa nuna ta an san fuskarta ba balle ta samu daukaka." Idris ya ce " na fada ma ka gara da ka yi haka a nuna jikinta a nuna fuskar da aka sani. Kai sai zancen adalci ka ke ta faman yi. Ba dai ka biya ta ba? 'Yar qauye ce ta na can ta na gwaguyar kudinta ta na murna. Aka bibiya ma ba ta taba riqe irin wadannan kudade ba." Abbas ya ce haka ne na ba ta dubu ashirin da biyar sannan na qara mata naira dubu ashirin. Ka san wani abin mamaki kuwa? Yarinyar cewa ta yi in bawa Tukur kudin aikin, bayan zagin da Tukur yayi mata a cikin jamaa bai so ba ma aka saka ta a cikin fim din ba. Ta burge ni matuqa, yarinya ce mai ladabi, kudi bai dame ta ba kwata-kwata ma. Ga hakuri wallahi na dauka zagin da su Aisa suka yi mata za ta yi fushi ta fasa yin fim din sai gashi ta ce za ta yi. Kuma wallahi ta na da kyau in har ta sami gyara sai ta fi Aisa kyau." "Haba dan Allah! kai haba Aisa fa farar fata ce. Yaya ma za ka hada ta da wannan baqar." Abbas ya yi dariya ce " kai ba ka san ma shikashikan kyau ba, ba fari kadai ba ne kyau. Kai ne ka yi mata kallon tsoro amma Nihal ta na da kyau, ga kyan jiki ba za ka hada ta da Aisa ba ma. Ina nan da kai ka bari ta wanke ta fara riqe kudi. Ina so in qara mata wasu kudaden dan gaskiya ita ce ta yi silar wannan nasarar tawa." Idris ya ce " ka da dai ka ba ta ta da kudi, mun sami garabasa yanzu muna bata dubu ashirin ta na murna, in ta saba da kudi fa mun shiga uku." Su ka kwashe da dariya su ka tafa hannu. 11/14/21, 7:19 AM - MY MTN 2: Wannan littafin na kudi ne 馃グ馃グ馃グ馃憤馃徎 GABA GADI NA JAMILA UMAR TANKO (JUT) Nihal ta juya da sauri Hashim na biye da ita a baya. "Malam Hashim ! Nihal Nuren Mubin ina kuma za ku je? Ga office din fa." Abbas ne ya fada cikin daga murya sai da kowa ya waiwayo. Cak ta tsaya a tsakiyar hanya ba tare da ta iya waiwayo ba abinda take gudu shine ya afku kuwa, akwai wanda ba ta so ya ganta amma sunanta da aka kira ta san dole sai ya waiwayo. "Hashim ne ya katse tunaninta ya ce "Nihal ki zo mu je ga Darakta Abbas din can ya na kiranmu." Ta na waiwayowa sai ta yi ido hudu da abinda take gudu. Muqaddas Abba Muse ne ya qame qem ya na kallonta. Tabbas abinda ya dade ya na fitowa nema ya samu yau. Ganinsa ya bata mata rai matuqa tabbas barazana ce a gare ta don koma tonar asiri ne. Ta shigo duniyar da baa san ko ita wacece ba ba ta so ta dinga haduwa da mutanen da ta sani a waccan duniyar ta da. Da su ka qaraso in da a Abbas ya ke tsaye sai ya yi dariya ya ce " ai ina zaune ina ganinku ta cikin gilashi ku ka yi kamar za ku shigo sai na ga kin juya. Har kun manta ofishin ne? Nihal duk wannan basirar ta ki ashe ki kan kidime wataran. Hashim kai ma har ka manta ofishina kenan?" Hashim ya yi dariya ya ce" ba mantawa muka yi ba har mun zo sai na ga ta juya ina zaton ko mantawa ta yi ta juya." Muqaddas da yake tsaye a jikin motarsa a daf da ofishin Abbas sai kallon-kallo suke yi da Nihal. Ya fuskanci irin kallon da take yi masa domin ya karance ta tas, ya na gane duk irin yanayin da take ciki. A yanzu dai ta fada yanayin fushi da tsana ne. Abbas ya wuce Hashim ya bi bayansa yayin da ta bi bayan Hashim. Da Muqaddas ya ga zata shige ya zabura ya ce "Baby! tsaya mu yi magana wajenki fa na zo, na dade ina zuwa nan dan in hadu da ke ban taba samun nasarar ganinka ba sai yau." Ta yi sauri ta kalli su Hashim Allah Ya sa sun yi gaba basu ji abinda ya fada ba. A fusace ta juyo ta nuna shi da yatsa ta ce " Kada ka sake, kada ka fara nunawa ka sanni. Ka daina bibiyata ka dauka ranka baka taba sanin Nihal ba, ka dauka a yanzu ba jinsinmu daya ba. Ba na so kowa ya san ko ni wacece a wannan duniyar da na shigo. MuqaddasMuqaddas kada ka bata min shirin da na dade ina yi a lokacin da na yi daf da samun nasara." Hashim ne ya sake fitowa da sauri yana nemanta dan ya ga bata shigo ba har yanzu. Hashim ya ce "Nihal ki shigo mana ana jiranki." Ta juya za ta shige Muqaddas ya kira sunan Hashim, sai su dukka suka cika da mamaki. Sun manta da cewa yanzu Abbas ya kira su a gabansa. Hashim ya washe baki ya zaci a fim ya sanshi domin ya fara saka ran duniya gaba daya ta fara sanin fuskarsa. Nihal ta harari Hashim ta ce " kada ka je ka wuce mu tafi." Abokina Hashim zo mana saqo zan baka." Muqaddas ya sake fada fuskarsa cike da faraa. Kafin Nihal ta sake yin wata magana Hashim ya dire a gaban Muqaddas sai ya miqa masa hannu su ka gaisa. Hashim ya washe baki ya ce "eh kwarai ka gane ni kuwa nine Hashim Ibrahim wudil. A wanne fim ka sanni?" Muqaddas ya yi dibi-dibi ya ce "su na da yawa ai ni Fan dinka ne sosai." Ohoho zo kaga bakin Hashim har kunne yana ta jin dadin da ba zai musultu ba. Ya ce a ransa "ashe har qanqararrun 'yan gayu sun san da zamanna." Nihal ta qi matsawa daga wajen dan kada a tona mata asiri. Muqaddas ya bude mota ya dauko wata leda ya miqawa Hashim sannan ya saka hannu a aljihu ya dauko 'yan dubu-dubu ya sake miqa masa ya ce "kyauta ce na yi mata, ka bawa gwanata Nihal Nuren Mubin nima Fan dinta ne. Kudin kuma na ka ne." Hashim ya washe baki ya na godiya ya dauko kwarababbiyar wayarsa zai karbi lambar wayar Muqaddas, sai ya ji an cacimo shi an hankada shi gefe. Nihal ce ranta a bace matuqa ta fada cikin Fushi "Hashim wuce mu tafi kada ka bari raina ya baci ." Simi-simi ya wuce cikin ofishin Abbas amma fa ya rugume ledar nan da kidinsa ram a hannunsa. Ya na godiya ga Allah da Ya sa sai da ya karba ta koro shi. Ta juya ta harari Muqaddas ta ce " ba da wasa nake ba kada ka sake nemana, gargadi nake yi maka ba neman shawara ba." Kallonta yake yi kallo irun na so da qauna, ya na murmushi. Bash Auta ne da Bilal Sani su ka zo zasu wuce cikin ofishin Abbas sai aka hau kallon-kallo a tsakaninsu. Gaban Nihal ya yanke ya fadi a lokacin da su ka yi ido hudu da Bilal Sani domin ya santa ta san shi amma a intagram ya na cikin manya abokainta na social media. Bilal Sani babban Jarumi ne kuma Ex producer kuma Darakta wanda ya shahara kuma ake ji da shi. "Innalilahi wa inna ilaihi rajuun me yake shirin faruwa da ni ne yau? " Nihal ta fada a cikin zuciyarta yayin da ta yi nadamar zuwanta Kano yau, dama daga Darazo Wudil dinta ta wuce. Bash Auta ne ya tsaya qem yana hararar Nihal da Muqaddas duba na rashin fahimta da alamun kishi. Bilal Sani ne ya zungure shi ya ce "zo mu tafi mana." Dogon tsaki Bash ya ja sannan ya shige cikin ofishin. Yayin da Nihal ta harari Muqaddas itama ta ja na ta tsakin ta wuce ciki. Kalmar Innalilahi wa inna ilaihi rajuun Muqaddas yake ta ambato yayin da ya hau kan motarsa ya zauna ya ci gaba da jira. Ransa ya baci sosai ba dan uba uba ba ne da sai ya kai mutumin da ya jefa Nihal a wannan harkar. Bayan ta gaishe su sai ta sami waje ta zauna daga gani ba ta cikin hayyacinta. Abbas ya fara gabatar musu da juna. Ya kalli Nihal ya ce " kin san Bash Auta ai kun taba yin aiki tare, ga Bilal sani duk duniyar Fim dai an san shi na san kin san shi kema shine dai nake tunanin bai sanki ba. Bilal ga Nihal Nuren Mubin sabuwa ce amma kuma malamarmu ce ita ce wannan me tsallen. " Bilal ya kalle ta sama da qasa ya yamutse fuska ya ce "ban taba jin labarinta ba ma. Wai kana nufin da ita za mu yi fim din ne?" Kowa ya gane dalilin da ya sa ya yi wannan tambayar, raina ta ya yi. Sai Nihal ta godewa Allah dan ta tabbatar bai gane ta ba. Ta ji dadi da Allah Ya sa bata shiga social media da sunanta na gaskiya, ya santa a social media da sunan princess last born. Kamar daga sama ta ji Bilal ya ce " ka ga an nemi princess last born ko sama ko qasa babu account dinta gaba daya ta shafe su, babu number wayarta ko an kira a kashe.Ta yi min alkawari za ta bani shawara akan wani sabon fim dina da zan yi, wallahi na ji haushi wallahi sosai na yi rashi. Na nemi qawarta ma Queen Siyama itama an shafe fejinta. Ko ina su ka shiga oho." Bash Auta ya ce " akwai abar banza irin social media, aka bibiya ma da wani qaton namiji ka ke chating ba mata ba ne" Su dukka su ka kwashe da dariya. Yayin da Nihal ta sake sinne kanta dan kada ya tunano fuskarta domin jifa-jifa ta kan saka hotunanta a dp ko status. Bilal sani ya girgiza kai ya ce " wannan macece kumar 'yar Kano amma ta na zama a London, wato yarinyar nan ta hadu ga kyau ga ilimi ga brain. Wallahi idan ta na turanci ba za ka taba cewa ba da baturiya kake magana ba. Duk turancin nan nawa wani abu sai dai in bi ta da ehh. " Su ka sake kwashewa da dariya suka tafa. " Ita me ta ke yi a London din?"Bash Auta ya tamabaya Bilal ya ce " kai! wata shegiyar attajira ce 'yar gata Babanta ya kai General a soja Yayyanta sojoji ne, mamarta furofesa ce ilimi tana lecturinga manyan jami'oin qasar nan. Ka san me ita ce mace Bahaushiya ta farko da ta karanci fim ta yi degree ta yi masters a London. Ni fa ina ta bincike a kanta aka ce turawa rububinta suke ta yi akan ta yi musu fim. Ka san abinda ya sa suke sonta saboda fatarta ita ce original baqar fata da babu mix bata bleaching sannan ta iya acting na masifa." Bash ya zabura ya ce" Hollywood kake nufi?" Bilal ya ce kwarai da gaske mu kan yi chat da ita a lokacin ta na location amma ina ga baa fara sakin finafinanta ba amma tabbas za ka ga bahaushiya a Hollywood." Bash ya ce " Ah la ce wannan babbar harka ce ba za ta kula ka ba, ina ganin shafe ka ta yi ba account dinta ta shafe ba. Ta raina 'yan Kanywood ne kawai." Bilal ya ce "kuma bata da wulaqanci gata da son ci gaban farfadowar Hausa fim. Gaskiya na yi asarar rasa ta saboda ta yi min alkawarin taimakona da abubuwa da yawa. Ka san wani abu kuwa? wallahi bala'in sonta nake san yadda zan fada mata ba saboda ta fi ni a komai. Ita fa ba ta iya daura zani ba idan ta yi wata shiga cikin Wando oh my God na ce a raina su Aisa Buzuwa su zo su ga 'yar Fim din asali ba kamar su ba." Bash ya ce " ka fada mata kana sonta kawai, shi so ai ba ruwansa da kudi ko wayewa watakila ta so ka yadda ka ke dogo fari santalele, ga ka jinin kudi da sarauta. Aka bibiya ma itama ta na sonka a ranta ta kasa fada maka ka saka kai kawai abokina." Bilal ya yi dariya ya ce " kada ka ingaza ni dan kulanin da take ta daina me jan aji ce bata ma san ina yi ba. An fada maka ta bata ma gaba daya ko sama ko qasa kana yi min wata magana. Ita fa wannan komai bai dame ta ba, ba ta san ma ina yi ba amma dai idan na yi mata tambaya ko neman shawara akan fim ta na bani amsa musamma idan na tura mata saqo ta email dinta. Sunan email din zulaihatshatumubin@gmail.com amma yanzu na tura sakonnin har na gaji shiru ba amsa." Abbas ya yi ajiyar zuciya ya ce " ka ga da ta na kishin yarenta da ta dawo gida an amfana da ita. To irin wannan kuskure mutanenmu suke yi sai su je su farfado da al'adar wata qabilar su zubar ta su mu na buqatar irinsu anan. Ai tunda ta yi karatu mai tsada irin wannan, gida ya kamata ta zo ta wayar mana da kai mu ma mu qaru. Har ta bai haushi ma." Sai yanzu Nihal ta jinjinawa basirar mahaifinta da ya ce ta zo ta yi Hausa fim anan ma ana buqatarta, tabbas haka ne gaskiya. Ta kudiri niyyar kawo agaji ga masana'antar nan kuma kyauta. Akwai himilin kurakurai da ake ta maimaitawa a sanadiyar rashin neman ilimi a harkar. Kowa kai tsaye kawai yake fadowa ba tare da sanin qa'ida ba, shiyasa babu ci gaba har yanzu an barmu a baya. Abbas ne ya katse tunanin da ta tsunduma tana yi ya ce " mu qarasa tattaunawa akan abinda ya kawo mu, ga magruba ta kusa sannan Nihal ba a garin nan suke ba zasu koma kauyensu." Wani kallon banza Bilal ya yi mata ya ce " ah daga qauye ma ta ke? Ai ni ba ni da ta cewa, Fim dinka ne amma ya kamata mu tattauna kafin ka aiwatar da wannan tunanin naka darakta." Kowa ya gane abinda ya ke nufi. Dan gudun kada yayi katobara sai Abbas ya yi sauri ya katse shi. Ya ce "za mu yi wannan maganar daga baya amma yanzu dai nan da kwana uku nake so ku shiryo ku fito, wuraren Nijer za mu shiga cikin sahara. Kowa zan bashi script ya je ya duba sinasinan da zai yi, ba na son a sami matsala kada a yi kuskure." Abbas ya miqawa Nihal na ta himilin takardun, ta karba cike da ladabi tana jujjuyawa. Abbas ya dubi Hashim ya ce "ku je ka dinga karanta mata, ko a sami wanda yayi boko ya karanta mata sosai ta haddace." "Au ba ta ma iya karatun Hausa ba?" Bilal ya zabura ya tambaya. Bash Auta ya qifta masa ido alamar ya yi shiru. Nihal ta zabura ta miqe ta dubi Abbas ta ce "na gode Darakta za mu tafi dan kada mu rasa motar qauyenmu, sai na ji ka a waya." Abbas ya dube ta yayi murmushi ya ce "toh zan tuntube ku a waya zuwa gobe, ki dage a karanta abin nan sosai a gane. Ga kudin mota." Ya saka hannu a aljihu ya zaro naira dubu uku, Hashim ya cafke da sauri dan ya san Nihal cewa za ta yi a bari, ai kuwa har ta kai bakin qofar fita. Sun fito baranda kenan sai ga Bash ya biyo su a baya, ya zaro kudi naira dubu biyar ya miqawa Hashim ya ce " Hashim ga wannan a qara ayi kudin mota. Ko da yake na ga har saurayi ta yi a birni watakila ma shi xai kai ku gida." Nihal ta dube shi kawai sai ta kawar da kai gefe bata ce masa komai ba, gaggawa take ta bar wajen duk da bata hango Muqaddas ba amma ta hango motarsa a wajen. Watqila masallaci ya tafi dan an kira sallar magruba. Nihal har ta kai bakin titi a lokacin da Hashim ya biyo ta da gudu. "mu tambayi masallacin mata ka kai ni in yi sallah." In ji Nihal. Su na tambaya aka nuna musu, bayan sun idar sai suka hau adaidaita sahu su ka nufi tasha. A hanya ne Hashim ya kiyasta maqudan kudaden da Allah Ya basu a yau. Kudin wajen Muqaddas naira dubu ashirin, kudin wajen Abbas naira dubu uku, ga kudin Bash dubu biyar. Naira dubu ashirin da tawas cib. Wani qaramin kwali ne a cikin ledar da Muqaddas ya ce a bawa Nihal amma kwalin an liqe shi ba zai budu ba sai an saka reza. Hararar da Nihal ta wurga masa ita ce ta sa ya fasa kokawar budewa ya Mayar cikin leda ya kunshe. Sun nufi garin Wudil gadan-gadan ba su tsaya a ko ina ba sai a qofar gidan Nihal saboda kafin a kai tasha gidanta yake a bakin titi dan haka su suka fara sauka. Hashim ya raka Nihal qofar gida ya kalle ta yayi murmushi ya ce " Allah sarki yau sai ke kadai Najaatu bata nan. Sabo turken wawa sai na ji babu dadi amma za ki fi ni shiga damuwa." Nihal ta gyada kai ta ce "kamar ka shiga cikin zuciyata wallahi, ban san ta in da zan fara ba na saba zama da ita, ga ta da aiki." Hashim ya harare ta ya ce " ba ke kika yanke danyen hukunci ba. Meye abin Mayar da ita gidansu? Aka bibiya ma ta girme ki kike ganin yarinya ce ta yi kuskure." Ta harare shi ta ce "ba ka da hankali ma kai wallahi, ana yi maka maganar daraja da hakkin iyaye da ya rataya akanmu. Duniya fa ta shigo, su na can su na nemanta dole in mayar da ita." Hashim ya zabura ya ce "kin san Bilal Sani ai ko ? Wallahi in kika samu kika yi fim kwaya daya da shi kin gama hayewa, dan sarauta ne fa gashi ya fi kowa ilimi matakin masters gare shi da. Ga turanci duk wata talla shi yake yi idan ta turanci ce ya na da kudi sosai. Kwanaki ma yayi aure kin ga shagalin da aka yi kuwa. Ya auri 'yar gidan wani gwamna me ci. Amma fa Nihal sai min dage da addua saboda na ga fa kamar so yake ya ce a cire ki ba zai yi fim da ke ba. Saboda ya ganki a kauye babu wayewa. Kin san dan wulaqanci ne fa sosai yana ji da kansa, a junansu ma maganar da ake ta yi kenan. Nihal ta yi shiru ta na tunani, tabbas duk abinda Hashim ya fada gaskiya ne abinda Bilal yake shirin fadawa Abbas kenan, yana nufin bata dace da yin babban fim ba kuma tare da shi. Nihal ta fada a ranta "Bilal Sani ya karkace ya na ta yabo da irin taimako da shawarwarin da princess last born take bashi don ganin ya ginu kuma ya samu ci gaba. Sai gashi yanzu wani yana qoqarin ya yunkura ya tashi amma yana daqile shi baya so. Ba ma fim dinsa ba ne, na wani ne amma yake hassada ba zai bari ba wani ya ci gaba ba." Tabbas gagarumin yaqi ne a gaba domin ba zan bar Bilal Sani ya samu galaba a kaina ba. Zan nuna masa kurensa, zan nuna masa cewar taimakon wani abu ne da idan ka yi shi a gaba za ka tsinta. Zan nuna masa talaka da bakauye ba abin gudu ba ne. Zan nuna masa dan adam ba abin wulaqantawa ba. Kada ka wulaqanta mutum baka san ko shi wanene ba. Har yana maganar so, ashe kuwa ba don Allah Ya ke sonta ba sai don wata manufarsa. Hashim ne ya katse tunaninta ya ce " ga ledarki in kin bude za ki gani ko menene a ciki. Yaya zaa yi da kudin nan?" Ta harare shi ta ce "ka je ka riqe na bar maka dukka." Ta bude gidan ta shige ta datse. Ya san daman zaa runa, hakan ne zai faru. Ya yi dariya ya wuce ya tafi gida su. Ya iske kakannunsa a tsakar gida anan ya zauna ya narki tuwon masara miyar kuka. Inna ta tambayi Nihal ya kai sau goma daga nan Hashim ya tabbatar ba ta da kudi ne. Naira dubu goma ya qirgo ya miqa mata ya ce "ga sakon da ta ce in baki, aiki ne yayi mata yawa shiyasa ba ta shigo ta ganku ba, ta ce in gaishe ku." Sai murna ta rufe su, Nihal na shan yayyafin albarka. Hashim ya yi sallar isha'i da kyar saboda gajiya, ya na layi ya shiga ya kwanta akan ragargajejjiyar katifarsa a cikin daki ginin qasa yana ta juyi, da nan ya saba bashi da in da ya fiye masa wannan katifa dadi. A tsakar gida ya manta ledar Nihal. Asuba ta gari Hashim Wudil. Nihal ta raba dare tana rubutu a laptop dinta domin abubuwa manya-manya har guda uku ne su ka faru a wannan rana ga kai Najaatu gidan iyayenta, haduwa da Muqaddas sai haduwa da Bilal Sani. Sai ta tsinci kanta ta na murmushi domin Bilal ya nuna yadda halin dan adam ya ke, a zahiri bai san ita ba ce yana ta yabonta ya na fatan su sake haduwa a rashin sani, ga ta a zahira amma ya na gyamarta saboda bata da kudi. Sai da ta gama rubutu sannan ta yi wanka ta kwanta sai a lokacin ne ma ta tuna yau gaba daya bata ci abinci ba ga mai girkawa ta yi nisa. Daqyar ta tashi ta hada shayi da biredi ta yayyaga ba dan tana so ba sai don dole. Da ta kwanta sai idanuwan su ke ta haske mata fuskar matsayinta Muqaddas. Asuba ta gari Nihal Nuren Mubin. Kamar yadda Nihal ta raba dare ba ta kwanta ba saboda rubutun abubuwan da suka faru haka Darakta Abbas ya raba dare yana juyi ya kasa bacci ya na tunanin abinda Bilal Sani ya fada masa akan Nihal. Ya bashi shawara akan kada ya yi kasadar saka ta a matsayin Jarumar Fim dan bata dace ba, sannan ya yi rantsuwa shi dai ba zai iya fitowa a matsayin saurayin ko mijin wannan kucakar baqauyiyar nan ba domin ajinsa zai zube. Dan haka sai dai Darakta ya zaba ko Nihal ko Bilal. Abbas ma kunyar Nihal yake ji,ta ina zai fara kiranta ya fada mata an fasa yin Fim da ita bayan an saka mata rai. Bai san me yasa ba ya ji kawai ya na so ya taimake ta ya na da kyakkyawan zaton idan an bata dama zata iya. Tabbas ya shiga tsaka mai wuya . A cikin wannan dare daidai wannan lokaci kuwa Bash Auta ne ke ta juyi ya kasa bacci bai san me ya sa abin nan ya tsaya masa a rai ba, yadda ya ga Muqaddas da Nihal a tsaye su na magana. Me yasa yake jin haushi? Me yasa ya ji ya damu da Nihal? Shi kansa ya rasa amsar wannan tambaya. Haka a bangaren Muqaddas bacci ya gagara ganin Nihal a cikin wannan yanayi ya dame shi. Ko a mafarki daidai da rana daya bai taba zaton zasu kai war haka basu yi aure ba, bai taba kqwowa a ransa zai rabu da ita ba. Gashi abu kamar wasa iyayensa har sun fara maganar ya auri wata a cikin dangi ana ta naniqa masa Samira. Amma babu babban mai laifi sai General Nuren shi ya hargitsa komai. Idan ya duba wani bangaren kuma laifin Nihal yake gani, duk ita ta jawo musu ba dan ta canja course ba da duk haka bata taso ba. Yana jin kamar in ba ita ya aura ba tabbas zai shiga duniya a rasa shi. Ya daga kai ya dubi hotunanta da suka cika bangon dakinsa. Sai hawaye me radadi ya sirnano masa. Asuba ta gari Engr. Muqaddas. ********************** ? ************************** ********** Ai Hausa Novels **************** *************************? ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ? ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ? ************************** *** **** **** Washegari Hashim ya iso gidan Nihal bayan sallar azabar ya buga get ta bude su na hada ido sai ya zabura ya dafe kirji ya ce " na manta ledar nan a tsakar gida bari in je in dauko. Kiransa ta ke amma ina ya fallada gudu, ya tsayar dan acaba ya hau. Ta yi dariya ta koma cikin gida, ya dade sannan ya dawo dauke da ledar cike da murna. A qofar gida suka zauna ya bata labarin irin walagigin da aka sha yi da ledar nan, ya manta ta a tsakar gida, Inna kuma ta share ta zuba a shara aka dauki sharar aka kai juju. A takaici dai a Juji ya tsinto ta kusa da wani gandareren kashi. Nihal ta harare shi ta ce ka tsaya daga nesa ka bude kada ka kawo min kayan kazanta kusa da ni. Ya na gefe yana ta faman farkewa domin bayan kwalin da yake ciki an sami leda mai gyalli an nannade, ya warware ya bude kwalin ya duba. Hashim ya kwalla ihu zabura da gudu wajen Nihal ya nina mata kudin America daloli ne 'yan dari-dari guda ashirin qasan kudin kuma sar1ar zine ce da dankunne da zobe. Ya miqawa Nihal ya ce "taya ni gani wanne irin kudi ne wannan? Kuma sarkar kamar ta qwal." Nihal ta yi shiru tana mamaki amma bata yi mamakin da yawa ba saboda wannan kadan ce daga cikin irin kyaututtukan da ya saba yi mata, sai dai ta fi yin murna a yanzu saboda tana da matukar buqata. Ba ta nunawa Hashim kudi ne masu daraja ba dan kada ya yada haka ta ce masa sarar ba ta gwal din gaske ba ce jabun gwal ne, sai ta sami sauqin suruntunsa. Ta ci gaba da yin kasafin yadda zata yi da kudina nan a ranta . Dallar dubu biyu ta kai naira dubu dari tawas a lokacin sannan sarqar kuwa akwai resitinta da dirham ya saye ta da alama ya yi tafiya zuwa dubai kudinta dubu dari shida da hamsin. Ta yanke hukuncin gara ta siyar ta harhada ta saye gidan da take ciki kawai ko ba komai za ta mallakawa Hashim da kakaninsa su huta da zaman gidan qasa yana rugujewa kullum. Ta dauka ta je ta adana a can qasan jakarta tana jira sai ta ta je kano sannan ta canzar su dawo Naira. Tabbas Muqaddas masoyi ne a kowanne hali take yana tsaye a kanta. Hawayen tausayin su ya sirnano mata ba tare da Hashim ya gane kuka take ba ta yi sauri ta goge. Shi kuwa ya na can yana ta zuba ba tare da bana fahimtar labarin da yake yi ba. Qarya ya shirga mata cewar a tsaye ya kwana ya na salla yana addua kada Allah Ya sa Bilal Sani ya rusa musu budget dan ya ga alama yana kawo musu barazana. Hashim bai rufe bakinsa ba sai wayarsa ta yi qara yana dubawa yaga sunan Darakta Abbas ne sai su dukka gabansu ya fadi. Hashim ya amsa, a sanyaye ya ji muryar Darakta yana magana. Nan da nan Hashim ya yi saranda ya ji a jikinsa labarin babu dadi. Abbas ya ce idan ka na kusa da Nihal ka koma gefe mu yi magana ." Hashim ya zabura ya tashi daga kusa da ita ya koma gefe ya ce " eh ni kadai ne yanzu. " Darakta Abbas ya fara yiwa Hashim bayani saboda tashin hankali sai da Hashim ya sulale ya zauna. Darakta ya roqi Hashim da ya bi duk wata hanyar da zai bi ya fadawa Nihal ba tare da hankalinta ya tashi ba Bilal ya ce ba zai yi fim da ita ba sai dai a zaba ko ita ko shi, shi kuma yana ganin Bilal ne kadai ya dace da fim din. "Innalilahi wa inna ilaihi rajuun". Hashim yake ambato kamar wanda aka bashi labarin mutuwar Inna. Bai san Nihal tana tsaye a bayansa ba, duk da bata ji dukka ba amma ta gane abinda yake faruwa. Sai ta kwace wayar, ta yi sallama ta gaida Abbas. Sai ya ji gabansa ya fadi. "Malam Abbas kada ka damu in ban yi a wannan ba zan samu a gaba. Ai ka nuna min ka na da son ci gabana, kada ma ka ji nauyina." Ya ji kamar zai nutse a qasa dan kunya sai ya sosa qeya ya ce amma in ba za ki damu ba akwai wasu wurare da za ki iya shiga a fim din." Ta gyada kai ya ce " ba damuwa ko ina ne a saka ni zan yi. Na gode sosai." Su ka kashe waya daman a gaban Bash Auta Abbas yake wayar bayan sun katse Abbas ya dafe kai sai gumi kawai yake yi. Ya dago ya dubi Bash ya ce " kai amma yarinyar nan tana da nutsuwa da hankali wallahi ita ce ma take bani hakuri akan kada in damu. Kuma bata yi fushi ba ta ce a saka ta a ko ina ma." Bash ya yi tsaki ya girgiza kai ya ce " mutuniyar kirki ce wallahi na dade da sanin haka, ai kai ka biyewa Bilal shi kadai ne actor, kada Allah ya sa ya yi fim din. Ai tun jiya ya bani haushi mu ka yi kaca-kaca akan yarinyar nan. Ya san ita irin daukakar da Allah zai yi mata nan gaba, yake wulakanta ta." Abbas ya ce don a zauna lafiya ne na bi shi a haka, ka san bai kamata ka bata da mutanen da ka dade tare da su ba, akan sabon zuwa. Amma kamar yadda ta fada din ne zaa hadu nan gaba." Dakyar Hashim ya miqa tsaye daga inda ya zube, hawaye tab ya cika masa idanuwansa. Nihal ta kwashe da dariya ta ce "Hashim har da kuka? Kai da ka kwana kana sallah. Ka ga kenan Allah bai bamu ba kasancewar ba alkhairi ba ne a wajenmu. Baa fushi da hukuncin Ubangiji ka jira ka ga sakayya." Ya matse hawaye ya yi Jugum. Nihal ta ce "zo ka raka ni wani waje, waqila in muka fita ka ga mutane za ka ji sanyi a ranka." Ya tsaya kawai ya na kallonta cike da mamaki saboda yadda ya ga bata damu ba kwata-kwata ma. Su na tafe su na labari ya ce " wallahi da kin yi fim din nan da kin yi suna kuma kin zama mai tsada. Yin Fim da Bilal ma wata daukaka ce shi ba da kowacce mace yake yin Fim ba. Sannan in baa biya ki da yawa ba Allah watakila ki sami zunzututtun kudi naira dubu sabain Wallahi." Nihal ta kwashe da dariya ta ce" har dubu sabain?" Hashim ya zaci tana nufin sun yi yawa ne sai ya ce " bari dai in rage Allah sai ya baki dubu sittin ma." Ta sake kwashewa da dariya ta ce " lallai da mun yi kudi." Ya ce " amma Allah Ya isar mana, Bilal ya cuce mu." Ta yi sauri ta katse shi ta ce "Hashim ba na son irin wannan abin da kake yi fa. Yaushe za ka waye ne? Gaskiya ka koma islamiyya dan ka qara samun ilimi ka san hukuncin yarda da qaddara. Su na isa sai ga Shazali ya fito daga ofis yana ganinta sai ya cika da murna da girmamawa. Ya gaishe ta sai ta shaida masa ko zasu koma gefe ta na da magana da shi. Hashim ya na tsaye a gefe yana kallonsu ya kasa sanin a lokacin da Nihal ta san 'yan garin nan, dan duk in da su ka je sai ya ga ana gaishe ta. Nihal ta dubi Shazali ta ce " maganar gidan da nake haya ne ga shekara ta zagayo amma na ji kamar ka ce sun fi so su siyar. Ina so zan siya." Sai Shazali ya dago da sauri ya kalle ta ya cika da mamaki amma dai ya san daman masu kudi ne dan haka gara ma ya tsagaita da mamakin. Shi dai ya kasa gane abinda ya sa ta kaure garin nan. " Nawa ne kudin? " Nihal ta tambaya. Shazali ya ce " miliyan daya da rabi suke nema amma idan aka zauna zasu rage watakila miliyan daya da dubu dari biyu ko da uku ma sai su bari." Ta gyada kai ta ce " ka je ka zauna da su yau gobe insha Allah sai in biya ." Ya amsa da cewa yanzu kuwa Hajjaju zan je wajen mai gidan duk yadda muka yi za ki ji ni. Har yanzu baki da waya ko?." Ta amsa " eh amma kada ka damu goben da yamma zan zo sai mu tafi mu biya kawai. " Su ka yi sallama tana godiya ya na godiya suka tafi ba tare da Hashim ya san abinda su ka tattauna ba. A hanya Hashim ya ke tambayarta yaya aka yi ta fara sanin mutane a garin nan? Ta amsa masa da cewa "na kusa cika shekara guda fa na fi watanni shida ya kamata daman ace na san jamaa." Ya amsa "haka ne fa. Ina zamu je ne naga kin kama wata hanya ba hanyar gidanki ba?" Ta yi dariya ta ce " Inna da Baba zan je wa hira sai bayan sallar isha'i zan dawo." Hashim ya harare ta ya ce "har wata hira kike zuwa yi ke kwata-kwata ma wannan abinda aka yi miki baki damu ba." Nihal ta yi dariya ba tare da ta san amsar da za ta bashi ba kuma. Ta ce a ranta "da ka san ma kyautar da Allah Ya baka da ba za ka damu akan naira dubu sittin ba." Ba ta bar gidan Inna ba sai da ta yi sallar isha'i su ka yi sallama da su Hashim, ta ce zata yi tafi wani waje gobe kada ya neme ta domin sai da daddare za ta dawo. Da safe ta shirya ta shiga garin Kano bayan ta gama da kasuwar 'yan gwal da kasuwar canjin dalar sai ta boye hamlin kudinta a qasan jakarta ta nufi unguwar zoo road ofishin Darakta Abbas. Abbas ne tare da darakta Idris da kuma Halima Jabir yarinya me tashe da farin jini a duniyar fim. Itace za ta maye gurbin Nihal. Har Nihal ta daga qafa daya zata shiga ofishin sai ta ji ana ambaton sunanta dan haka sai ta ja baya ta tsaya ta kasa kunne ta na sauraro. Tabbas kunnuwanta sun jiyo mata abinda zai hana ta bacci sai ta ji dama bata zo ba. Meye ma ya kai ta ta yi musu labe? Hohoho da sun san Nihal za ta ji da basu fadi wasu maganganun akanta ba. Sai a yau Nihal ta san menene ake nufi da rayuwa, dan ada bata san komai a game da rayuwa ba. Kafin ka ce kwabo ta hada gumi sharkab yayin da hawaye ya gagara tsayawa daga idanuwanta. Ta ci gaba da yin shawara ita da zuciyata. Shin ta shiga ne ko ta tafi ta yi kamar bata ji ba? Anya maganar nan ya kamata ace ta dauke kai akanta kuwa? Gara dai a yi ta ta qare kawai. *** *** **** TALLA! TALLA!! TALLA!!! Me talla shi ke da riba marmaza a garzayo... 鉂も潳鉂も潳鉂も潳鉂も潳鉂� Are you guys looking for where to buy ur skincare product @ mg's skincare is the best plug for you馃 Do you wish to have that flawless skin that's free of all skin prblm Do you wnt to achieve that milky skin that turn heads wherever you go馃槈 Try mg's product nd I assure you you'll never use any other product except mg's product鉁� Mg's will gv you the best out of all With mg's product ur skin is 馃挴 clear,fresh,smooth nd ur skin will absolutely glow all day馃拑 We have herbal whitening black soap now nd beauty set available Nd both the soap nd the beauty set is for all skin type everyone can use it馃 Just gv it a try now nd see wonders鉁� Chat:08062991549 Call:08064532391 Soap price:3k set:11k Follow us on Instagram@glow_with_mgs Facebook:mg's skincare what are you guys waiting for hurry nd grab urs馃拑 now is the time to glow馃鈥嶁檧锔� Pamper ur skin馃Φ Shine like a bride 馃懓 be part of the glow team karkubari abaku lbr Just chat 08062991549 to plc ur orders馃槝 Do not forget to follow us馃憜 Like nd comment pls dearies馃槝 Patronize us馃檹 mg's always serve you the best鉁呪潳锔� 11/14/21, 7:19 AM - MY MTN 2: Na kudi ne鉂� GABA GADI NA JAMILA UMAR TANKO (JUT) Nihal ta na ta dauki ba dadi da zuciyarta wata zuciyar tace ta shiga ciki kawai su san ta ji, wata zuciyar ta ce ta juya kawai kada ta nuna musu ta ji.Daga qarshe ta yanke hukuncin gara kawai ta juya ta tafi kawai babu amfanin ta nuna ta ji, ta bar su da Allah. Dan haka sai ta yi sauri ta juya za ta tafi, da Bash Auta ta yi kicibus saura kadan ta bangaje shi. Ya dago a fusace zai yi ma ta fada sai ya ga Nihal Nuren Mubin ce wato gwanarsa. Yarinyar da take burge shi haka kawai bai san dalili ba. "Ah Nihal ina za ki tafi kuma? Na ga kin yi kamar za ki shiga ba ki shiga ba kika fasa." Kamar daga sama su Abbas suka jiyo sunan Nihal, wannan kalma ta " kamar za ki shiga kika fasa" ta tabbatar musu da cewa ta ji abinda su ka fada shiyasa ta fasa shiga. Bash ne ya sako ta a gaba su ka shigo ta bi kowannensu da kallo yayin da gumi ya fara ketowa kowannensu. " Ah Nihal ke ce a gari? Ga kujera ki zauna." Abbas ne ya fada gami da nuna mata wata kujera dake gefensa. Nihal ta girgiza kai ta ce " A a Darakta babu komai sauri nake, na gode. Sako na kawo zan ba ku in wuce." Ta saka hannu a jaka ta zaro himilin script din da ya bata don a karanta mata. Maimakon ta miqawa Abbas sai ta miqawa Halima Usman gami da cewa " Ga wannan na ki ne shine sina-sinan da kika maye gurbi na." Halima ta sa hannu ta karba a sanyaye yayin da Bilal ya maqale hannu a qirji ya na hararar ta sama da qasa tabbas ya tanadar mata duk wasu shikashikan rashin mutunci a yau muddin ta tare shi da wata magana. Gulma ce ya san yayi kuma baya tsoron masu aji ma balle kucaka irin ta marar gata, marar kudi, marar ilimi. Nihal ta ci gaba da magana da Halima " a zatona ciwon 'ya mace na 'ya mace ne haka duk wanda ya zagi 'yar fim guda daya ya na shafar gaba daya 'yan fim tunda kudin goro ake yi. Tabbas duk wata baraka daga gida ake yaga ta , na waje basu da laifi idan sun ji sun yada sharri akan 'yan Fim. Kin ga baki taba ganina ba ban taba ganinki ba amma kina rantsuwa da cewa Darakta Tukur ya gama yin lalata da ni shiyasa nake fitowa a dukka finafinansa. Wa'iyyazu billah! daga bakin 'yar Fim ce ta furta wannan abu akan 'yar uwarta 'yar fim. Malam Abbas ka duba fa ka gani. Duk duniya akwai wanda ya isa ya wanke wannan maganar. Ai daga gida ta fito daga bakin dangi. Ina mai baki shawara ki guji yarfe da qazafi domin wataran sai ya dawo kanki. Ba sai kin batawa wata suna kafin ki sami wani abu ba, bawa baya wuce rabonsa......" Bilal ne ya zabura ya dakawa Nihal tsawa "dalla malama ki wuce ki ba mu, waje wa'azin ya isa an yi gulmarki din ki yi abinda za ki yi." A fusace Nihal ta nuna masa yatsa ta ce " kada ka sake, kada ka fara yi min tsawa. An fada maka kowacce 'yar Fim wulaqantacciya ce kamar ka." Wannan kalma ta yi masa zafi musamman daga bakin da ta fito, na bakauyiya ma irinta. Zabura yayi ya miqe tsaye watakila niyyarsa ya mare ta. Bash Auta Auta ne ya shiga tsakaninsu. Bash ya fada a fusace "me ya kai ka kaiwa mace hannu? Kada ma ka fara, Nihal mutum ce kamar kowa dole ta ji zafin qazafin da aka yi mata. Kuma a cikin maganarta menene ba gaskiya ba? Baraka daga gida ake samunta sannan 'yan waje su samu su yi gaba da ita. Na tabbatar da zaginta ku ka yi ko kushe ta Nihal ba za ta taba daga ido ta dube ku ba amma wannan qazafin da ku ka yi mata ne yayi mata ciwo shiyasa ma ta yi magana, kuma maganar ma nasiha ce. Ke Halima da kin san halin Nihal ma da ba sai kin yi mata qazafi ba ma. Dan za ki kwace gurbinta da kanta za ta dauka ta baki . To ko manyan Jarumai ma ba sa gabanta balle Tukur, idan ta yi fim a gaban kowa take cewa a bawa Tukur kudin saboda girmamawa shine me gidanta a hannunsaaka damqa ta. Abbas an yi haka ko baa yi ba? Ku ba ku san ta ba kawai kun dauki zargi da yarfe da qage ku na jifanta da shi." Bilal ya fusata ya ce "Bash! babu ruwanka da maganar nan ka ja bakinka ka yi shiru ka barni da ita, daqiqiya ma irinta. " Nihal ta ce " Zaa gane waye daqiqi a tsakanin ni da kai nan gaba." Sai kan kowa ya daure a wajen ke da ko furamare baki yi ba ki na ja da mai masters. Abbas ne ya zabura ya katse Bilal ya ce " A a Malam Bilal banda cin zarafi irin wannan. Tabbas an yi ma ta laifi ba dan kadan ba, dole ta yi magana ta fi mu gaskiya. Nihal ki yi haquri ki yafe mana." Bash ya yi dariya ce " Au Darakta daman har da kai aka yi gulmar? 'yar gidanka ce fa." Abbas ya sunkuyar da kai yayin da gumi ya dinga keto masa. A lokacin ya dinga tunano iya furucin da yayi a cikin hirar. Nihal ta ce " Darakta ka ba ni script din da zan karanta a roll din da ka ga ya dace da ni. Ina son in shiga Fim din nan ko da kuwa zan fito a 'yar aike ne. Domin idan daqiqi ya mu'amulanci masu ilimi jahilcin zai ragu. Darakta ya yi dibi-dibi ya miqa mata wasu takardu ba tare da shi kansa ya san ko wadanne ba ne saboda nauyi da kunya. Nihal da Halima da Bilal ne ake ta kallon-kallo har ta fice abin ta. Bilal ya ce " bata da zuciya ko kadan an kore ka a cikin fim ka dage sai ka yi saboda naci." Murmushi Nihal ta saki ta ce "ga wanda ya san darajar sana'arsa ba ya fushi. Sannu a hankali zai zama mai riba. Domin a haka zan zama Jaruma wataran." Wannan kalma da ta fada ta tuni masa da nasihar da Princess last born take yi masa amma cikin karshen turanci, abu daya su ka fada da Nihal. Princess ta kan ce masa "Bilal in har ka san kanka ba za ka taba yin fushi da sana'arka ba, ko me aka yi maka kuwa. A haka za ka zama Jarumi wataran." Nihal ta fice abin ta yayin da Bilal ya ji kansa ya daure yadda wannan kalmar masu ilimi irin su princess ta fito daga bakin wannan jahilar. Bash ya bi bayanta da sauri su na tafe ya na jero mata tambayoyi ya na so ya ji takamaiman abin da su ka ce akanta. Ba ta da wannan lokacin na nanata magana daya, ko kallonsa ba ta yi ba ta ci gaba da tafiya. Sai ya ba ta hakuri kuma yayi mata jinjina a bisa matakin da ta dauka cikin sanyi. " Na gode." kalmar da ta fada masa kenan ta tsayar da me adaidaita sahu, ko in da za ta je bata fada masa ba, ta shiga ta zauna ta ce su tafi. Bash ya qame a tsaye ya bi babur din da kallo har su ka yi nisa, zuciyarsana sosuwa akan abinda Nihal ta ke yi masa na nuna halin ko in kula. Ya fara jin haushin kansa da kansa akan yadda ya damu da wacce bata damu da shi ba, bata ma kai matsayin ya damu da ita ba din. Sai da su ka yi nisa dan adaidaita sahu ya tuna mata cewar bata fada masa in da zasu je ba. Ta zabura ta dawo daga duniyar tunanin da ta tsunduma. Ta ce "tashar Kano line za ka kai ni." Ya ce " amma kudin drop za ki biya ni ko? Dan ba hanyar zan bi ba." "Nawa ne kudin din?" Nihal ta tambaya . "Naira dari da hamsim za ki biya, wallahi har dari biyu ake biya. Ke ce ma na yiwa ragi dan na ganki da gwanina Bash Auta." Ta yi dariya ta ce "saboda Allah kuma saboda kaunarka da Bash naira dubu biyu ma zan baka maimakon naira dari biyu." Sai ya zabura ya waiwayo ya kalle ta, bai santa a fim ba san haka sai ya zaci 'yar uwarsa ce mai son 'yan Fim ta kawowa Bash ziyara. Ya hau kirari ya na godiya da jinjina. Ya ci gaba da cewa " lallai kin fi ni son Bash Auta tunda kika yi min kyauta domins." Ya shiga ba ta labarun Finafinan Bash da suka fi burge shi, a ciki har da sabon Fim din Idris wanda ta taya Aisa samun daukaka. Ya yi ta koda bajintar Aisa da Bash a fim din nan. Ta na ta dariya ta fada a zuciyarta " an gaida Nihal Niren Mubin." Da ta tashi bashi kudin sai ya ga ta lunka akan kudin da ta yi masa alkawari kafin ya sake yi mata godiya ta bace ya neme ta ya rasa ta. Addu'a ya yi mata a bayyane ya ce "na dade ban ga mai kirki kamar ki ba. Allah Ya ba ki a aljanna Ya biya miki buqatun ki na alkhairi." Nihal ta sami mota qarama a layin masu lodi ta ce ya kara mutane biyu za ta biya sauran kujerun su tafi. A zatonsa iyakacin kujerun da babu kowa ne za ta biya ashe tana nufin har da na wadannan mutane biyu. Mace da namiji ne Namiji ya shiga gidan gaba, macen ta zauna a baya tare da Nihal har za su biya sai direba ya nuna Nihal ya ce "ku yi mata godiya ta biya mu ku." Kallon qurilla su ka yi ma ta su na mamakin wanda yake iya taimako a wannan marar. Sai su ka hada baki su ka yi mata godiya. "Ni kamar na sanki a wani waje." In ji fasinjan da ya ke zaune a gaba. Macen da take zaune kusa da Nihal ta ce " ka santa mana a fim din 'Tsumma' ya fito ita da 'yar kwalisa su ka yi." Sai gaban Nihal ya yanke ya fadi bata ma san finafinan da ta yi har sun fara shiga gari ba. Nihal ta yi murmushi ta sake rufe fuska ta ce " A a sai dai kama amma ba ni ba ce." Matar ta ce " ke yar nan na san ki sosai, ga gidanki nan ma a bakin kwalta. Ke ce qawar Hashim dan gidan Inna Habi me surfe. Ai ki na zuwa gidan Marka mai dinki har kin taba kwana a gidan lokacin da su Mami harka su ka kore ki daga dakinsu." Nihal ta zazzare ido ta cika da mamaki da tsantsan takaici yadda ta zama bata da sirri kowa ya san labarin halinda ta ke ciki ashe. Direba ya ce " oho ko ke ce aka ce su Mami harka sun sa 'yan daba su dake ki asiri ya tonu dan kin zo daga baya kin fi su daukaka?" Nihal ta fada a bayyane ta ce " shikenan ai kun gama magana." Jero mata tambayoyi su ka ci gaba da yi, sunayen 'yan fim din da ba ta taba ji ba ma. Har da Bash Auta da Aisa abin mamaki su ma hirar Fim din nan na Darakta Idris su ke yi yadda Aisa ta yi bajinta. Fasinjan da yake zaune a gefen direba ne yayi magana ya ce " Asiri ai ya tonu an ce duk abin nan da suka yi a fim ba su ba ne wata ce ta yi aka dora fuskokinsu." Nihal ta ci gaba da saurensu ta na mamakin yadda rayuwar 'yan fim ta za ma ba su da sirri, kowanne labari sai da aka kwakwalo shi. Direba ya ce " Haba no fa in ce yaushe muka samu wannan ci gaban haka gaskiya sun yi abin mamaki a fim din. To ita wacce ta yi acting din a fito da ita mana kowa ya santa. Me ya sa zaa boye fuskata a dauki jikinta?" " Allah sarki sannu Nihal Nuren kina da kirki ashe akwai masu hankali da nutsuwa a cikin 'yan fim amma ake yi musu kudin goro ana cewa sun cika wulaqanci. Allah Ya sa ki fi haka kin ji. wallahi haka Marka ta ce min ki na da kirki da hankali. Ki ci gaba da addua dan tabbas su Mami harka ba sa qaunarki." In ji matar da take kusa da Nihal. A qofar gidanta ta ce sauka su na yi mata godiya tana yi musu itama. Gida ta shiga ta yi sallar la'asar ta na idarrwa ta ji ana buga gida, ta fita da sauri sai ta zaci Hashim zata gani ashe Shazali ne.Babta yi mamaki sosai ba, ganin ya na murmushi ya nuna komai ya adaidaita kenan. Bayan sun gaisa sai ya ba ta labarin komai, gami da yi mata albishir akan mai gida ya siyar mata da gida akan kudi Naira miliyan daya da dubu dari biyu da hamsin, sai la'ada Naira dubu hamsin. Ya zaci za ta ce yayi tsada sai kawai ya ji ta ce "ina za mu je mu biya kudin. Amma komai a yi shi a bisa ka'ida. Zaa yi a rubuce a saka lauya a ciki ayi takardu akan qa'ida." Haka kuwa aka yi Nihal ta dauko jakarta wacce ta ke shaqe da kudi su ka dunguma wajen mai gida da mai unguwa. Kafin qarfe takwas na dare gida ya zama mallaki Hashim da sunansa aka siya. Ita kadai ta ke murmushi ta na ta jin dadi a ranta, dan babu abinda ya fi faranta mata rai a rayuwa irin ta zama silar farantawa Musulmi rai kuma ta cire shi daga cikin ukuba da damuwa zuwa ga farin ciki. "Alhamdulullah." Kawai take ambato. Washe gari da misalin qarfe goma na safe Hashim ya bayyana a qofar gidan da yake mallakarsa ne ba tare da ya sani ba. Ya yi ta bugu sai ga Nihal ta bayyana a gabansa ko tantama babu ta san irin bugun Hashim ne. Ya na ganinta sai ya fara murna domin jiya ya wuni shi kadai bai ji dadi ba. "Darakta Abbas ya kira ni daga jiya da daddare zuwa yau ya kai sau goma ya na son yin magana da ke, ya ce kin je Kano jiya. Shine amma baki fada min ba?" Nihal ta dade tana tunani kafin ta san amsar da za ta bashi, ta gyada kai ta ce " eh na shiga kano na je kasuwa." "Me ki ka siyo?" Ya sake tambaya. Wannan karon sai ta cika da mamaki amma da ta tuna da cewa da dan karkara take magana ba da turawa ba sai ta ga normal ne ai. " Malam Abbas ya ce in mun hadu da ke in yi masa flashing." In ji Hashim. Bai rufe bakinsa ba sai ga Abbas ya sake kira Hashim ya miqa mata wayar da sauri. Nihal ta karba ta na magana cikin ladabi. Bayan sun gaisa sai ya qara ba ta haquri game da abinda ya faru jiya. Nihal ta yi murmushi ta ce " haba Darakta da kai ne ka fadi wannan kalma a kaina zan ji haushi amma kai qaryatawa ka ke yi, tabbas na shaide ka ka na qaunar ci gabana kuna da gaske neruda gashi har a bayan idona kana kare ni." Ya ji dadi da jin kalamanta ya tabbatar ta gama jin duk abinda ya faru, ya sake yin godiya ga mai sama da ya matse bakinsa Ya hane shi da aikata mugun lafazi akanta, lallai da anji kunya. Ya ci gaba da ce " mun tattauna da Bash Auta ya ce " a baki roll din qawar Jaruma za ki firfito a wurare kamar guda goma. Ki yi hakuri takardun nan da na baki ba ma fim ba ne ki taho min da su, ranar na rikice ne." " ba damuwa, na gode kwarai Darakta zan dawo.maka.da su. Yaushe ne zaa tafi aiki? " "Jibi ne, da wuri za ki fito." Abbas ya fada cikin fara'a. "Zan iya zuwa da abokina Hashim? Da shi kadai na saba, dan yake taya ni hira." Hashim ya daga hannu sama ya na addua Allah Ya sa Abbas ya amsa. Sai aka ci sa'a ya ce su zo tare babu damuwa. Bayan sun kashe waya sai murna ta kama su biyun suvka shiga tunanin siyo akwatuna qanana wadanda za su zuba kayansu a ciki. Wannan ne karo na farko da za su yi fim a nesa da gida kuma wanda za su kwana a location. *** *** *** Ranar da zaa tafi, qarfe bakwai na safe a qofar gidan Nihal ta yiwa Hashim, ya na ta azalzalar ta, ta zo su tafi. Ko karyawa basu yi ba suka dunguma. Qarfe tara a bakin ofishin Abbas ta yi musu babu ma wanda ya qaraso, har shi kansa Abbas din dan haka sai su ka sami waje su ka zauna zaman jira. Ba su dade ba Abbas ya iso, ya ji dadi da ganinsu. Daga nan aka fara taruwa, motoci su ka cika farfajiyar wajen damqam dukkansu na tafiyar ne. Yawancin kowa motarsa ce kowa da abokan tafiyarsa.amma Nihal da Hashim ba su san kowa ba basu san a in da zaa raba su ba. Abin mamaki sai ga Bash Auta ko kallon Nihal bai yi ba da alama ya ji haushin abinda ta yi masa shekaranjiya. A wata doguwar bus aka dura su Nihal daga ita sai tarkacen 'yan bayan fage da kuma 'yan kan ta waye. Nihal ta juya ta dubi maka-makan motoci masu sanyin Ac, ranta ya dinga biyawa dan ba ta san nisan tafiyar ba, kuma ba ta san irin jigatar da za ta yi ba kasancewar ba ta saba yin doguwar tafiya a cikin kwarababbun motoci ba. Halima Jabir ta hango tare da Bilal sun kame a wata babbar jeep baqa sai nishi motar take saboda tsabagen kyawun inji da sabunta. Su biyu ne kawai a cikin motar kujerun bayan babu kowa, sai dai babu damar ta je ta roqe su cewar su tafi tare. An kama hanya sai Nihal da Hashim su ka yi addua su ka shafa aka ci gaba da tafiya. A cikin motar ne Nihal ta yi qawa me suna Duduwa indiyana. Da ta fadawa Nihal sunanta sai Nihal ta rasa inda aka dauko sunan india aka hada anan, da alama dai ba'a ce ake yi ma ta domin babu abu daya na suffar Indiyawa da ya bayyana a jikinta. Ga ta dai baqa qirin ga rashin gashi, ga rashin aji. Ga ta da yawan magana, har ta fara isar Nihal tun ta na amsa mata har ta daina. Amma da Duduwa ta gangaro kan labarin Nihal Nuren Mubin sai Nihal da Hashim su ka fara marmarin jin kanun labaran. Nihal ba ta san har an santa haka da yawa ba haka an san labaru da yawa akanta. Duduwa indiyana ta shaida ma ta cewar "an ce Bash Auta ya na sonki, kuma Aisa ta na kishi da ke dan babu wanda ta tsana a duniya kamar ke. Aka ce da ke ce za ki zama Jaruma a wannan fim din, amma Halima Jabir ta kwace miki dan Bilal ma ya ce ba zai iya yin fim da ke ba kin yi masa local. An tabbatar da cewa wannan daukaka da Aisa ta samu a sabon fim din da ta yi ta dalilinki ta samu amma ta na yi miki butulci." Nihal ta kalli Hashim shima ya kalle ta suka juya gaba daya su ka kalli Duduwa Indiyana cike da mamaki. TALLA ! TALLA!! TALLA!!! Me talla shi ke da riba. Note: Kada a manta ba JUT ba ce me kaya, talla kawai aka ba ta馃グ馃グ 鉂も潳鉂も潳鉂も潳鉂も潳 Duk wacce ba tayi anfani da sabulun nan ba an barta a baya a can karshen baya ma kuwa. Duk Mai tantama akan sabulai na gyaran jiki cewa basa aiki toh ya cire mg's domin kankat neInsha Allah. Babu Wanda ya yi anfani da sabulunmu ya ce baiyi ba ko yaushe mg's sai san barka. Amare da uwargidaye harda ma 'yanmata ku hanzarta ku samu naku, ba karya domin bama cika baki ku gwada ku bada labari da bakunanku. Sabulu daya tamkar da dubu wadanda ma basa san using cream sabulun 'mg's herbal whitening black soap' ya wadace ku, jikinku zai yi kyau koda yaushe ku kasance clean cikin kamshi Ku na glowing koda bakusa turare ba馃. Kayanmu ba na bleaching ba ne organic ne su na gyara jiki fiye da tsammaninku. Zai fiddobmuku da ainihin 'natural beauty dinki ne Wanda ya gwada shi zai tabbar. Amare ku yi kokari ku mallaki mg's domin ba ruwanku da zuwa andirje muku jiki, za kuga yanda fatarku za ta dinga walwali. Ina masu pimples Tabo(spot), Sun burn dama duk wani matsalar fata?. ku yi kokari ku nemi soap din nan before 2weeks zai share muku hawaye, ku zama abun kwatance. Sisters ma su nankarwa kuma ku nemi soap dinnan Ya na rage nankarwa sosai馃馃徎鈥嶁檧锔廳uk me shakku tanyi kokari ta gwada mg's insha Allah ba za ki so rabuwa dashi ba. Akwai mai saka haske Amma kayanmu na fada ba na bleaching ba ne zai fiddo miki da ainihin halittarki ne ya goge dukkan dattin jiki. Akwai Kuma Wanda zai miki maintaining skin dinki ya saka ki fresh, fatar ki ta zama kalar hutu Sannan mu na da beauty kit馃duk me bukatan (flawless skin/perfect glow) toh yy kokari ya mallaki set dinnan wannan zncn baa mgn馃馃徎鈥嶁檧锔廲uz duk inda kayi se an kalleka馃榾 Buh gsky wnd be son yy haske karyayi using set din cuz gsky yana sa haske buh ba na bleaching ne zai dai murje fata ne nd bring out that hidden beauty in you馃槏 Pls bama cika Baki you HV to try it and see for yourself 100%tested nd trusted Beauty kit: 11k Soap price: 3k Location: kaduna but muna turawa ko Ina Amma delivery is not free Masu so kindly message 08062991549 Call 08064532391 Note: Babu in da zaku sami mg's herbal whitening black soap sai a number dinnan bai riga ya kai market ba in yakai we will let you know but as for now wnn number ne kawai馃檹 Maiso ya hanzarta before ya ji sold out akwai su available now in sunkare you HV to wait a kawo, so mai so ya hanzarta馃檹adade anayi sai gsky馃き馃 Mg's skincare 11/14/21, 7:19 AM - MY MTN 2: Na kudi ne 鉂� GABA GADI NA JAMILA UMAR TANKO (JUT) "Yanzu kenan dan ina yin fim ba ni da sirri ko kadan? Su waye su ke fitar da maganarmu? Ba kowa ba ne a junanmu ne, tabbas mu na da farin jini dan haka kowa ya na son ya san yadda mu ke rayuwa a zahiri abin burgewa ce ace an ji labarin rayuwar dan fim a bakinka dan haka ta ko ina farautar labarin ake yi. Makusantanmu su suke yadawa musamman ma idan abin ba mai kyau ba ne . Mutane sun fi zumudin su yayata sharri fiye da alkhairi. Wacce irin rayuwa muke yi a qasar nan ne? A qasashen da su ka ci gaba abin ba haka hake ba. Tabbas su na da wannan dabi'ar su ma na neman labari a kan celebraties amma da yake acan celebrateties su na da tsaro da kudi baa ganinsu barkatai a fili, ba kamar mu ba." Nihal ce ke tunani yayin da maganar Duduwa indiyana ta katse tunaninta. Duduwa ta ci gaba da cewa "daman maganar gaskiya ke ma Nihal babu yadda zaa yi ace 'yar fim din qauye ta fito kai tsaye ta tari manyan jarumai na birni ta ce za ta fara yin fim da su. Ki dai bari ana sa ka ki a 'yar rawa da 'yar aike a hankali wataran sai ki fito sosai a sanki lokacin kin dan waye kin sami dan kudin siyan mai da sabulu me saka dan farin nan. Kin san 'yar farar fatar nan ake sha'awa mu baqaqe baa ta tamu." Hashim ya yi carab ya ce "in Allah Ya so kwanan nan itama Nihal za ta fara bleaching in dai dan fari ne ya sa su Halima Jabir suke kwace mana waje." Wani takaici ne ya kutso cikin zuciyar Nihal ta harari Hashim ta ce " me ya hada ka da maganar mata ? Me ka sa ni akan bleaching? Allah Ya sawaqe in shafa mai in yi fari saboda wani abu wai shi fim. Kun kuwa san menene illar bleaching? Kun san kallon da masu hankali suke yiwa masu bleaching? Ko ni nan ba na yiwa masu yin bleaching kallon masu wayo, rashin dubara ne da rashin mafadi da rashin tunani. Kun kuwa san menene natural beauty? Kun san yadda irin kalarmu ta ke da tsada a turai?" Jamaa da dama suka dinga waiwayowa su na kallon mai magana domin Nihal ta manta shagalab, ta shiga ingausa wato kalaman turanci da na Hausa take gwamutsawa. Sai ta tuna ashe ba ta taba zuwa makaranta ba dan haka sai ta yi shiru. Har da Hashim a ma su mamakin yadda take magana ta na saka turanci kuma ta na ta bada labarin turai. " A ina ma ta taba ganin turawa balle ta san yadda suke a turai? Turai ta Dan ciyau garinsu ko ta Gumel?" Hashim ya ke tambaya zuciyarsa? Tun daga nan Nihal ba ta sake yin magana ba sai takalo ta su ke da hira dan su sake jin wasu kalaman na ta a hada a yanke mata hukunci amma sai ta qi tankawa. Yunwa da tashin zuciya ne ya dame ta ga qura da ta cika ma ta kunnuwa da idanuwa. Tafiya ta qi ci ta qi cinyewa. Bayan sun iso garin katsina sai aka sake nausawa aka nufi garin Jibiya har sun fara murna sun zaci an zo sai su ka ga an tsunduma cikin bodar Nijer, a wajen Immigration gaba daya motocin su ka taru domin a yi musu kudin goro su wuce akan qa'ida. Nihal ta bude ido tana ta kallon sabuwar duniya,tana son Nijer daman ta dade tana so ta shiga ta gani da idanuwanta. Musamman sahara da rakuma, tabbas ta fara ganin canji da banbanci da qasarta. Sai ta tsinci kanta tana mai murmushi da farin ciki. Yayin da Hashim ya cika ta da surutu wai shi ya taba zuwa daga nan har Niamey babban burninsu. Garin Maradi su ka nufa nan ma ya na cikin manyan biranen qasar. Nihal ta ga abubuwa da yawa da qauyuka da dama dan haka ta haddace su a cikin kwakwalwarta tana da buri ta yi rubutu wataran akan rayuwa da al'adun Africa. Wani gida aka kai su aka sauke su, gidan yana da kyau yana dauke da dakuna da yawa. Nihal sai wurga idanuwa take ko za ta ga sauran manyan jaruman su Bash su Bilal da Halima amma bata gan ba daga nan ta tabbatar nan gidan mararsa galihu ne irinta. Sai ta ji tausayin talaka bawan Allah tabbas a ko ina sai an nuna masa banbanci. A da ba ta lura amma yanzu da ta dandana rayuwar talauci za ta dinga kokarin jawo talaka a jikinta tana daidaita shi da kanta, ya kamata a daina wariya a dinga daidaito a tsakaninsu da su masu kudi. Abbas ne ya zo da kansa ya rarraba daki, dakin mata daban na maza daban, amma a kowanne daki sun kai su uku-uku a daki daya wasu ma su hudu ne. Nihal da Duduwa Indiyana da fati dangerous ne aka hada su a daki daya. Tunda daga jin sunayensu ta san ba za su daidaita ba saboda ba tsarinsu daya ba. Wasu manyan asharai Fati Dangerous ta kwasa ta makawa wani saurayi mai suna Danliti Ado. Nihal ta karbi akwatin ta daga hannun Hashim ta gaggauta barin wajen ta Shiga dakin da aka nuna mata. Ta na shiga ta ga gado ne guda daya sai ta shiga tunanin yadda manya mata guda uku zasu gwamutsa, ga su da qiba duk sun fita qiba. Ta waiga ko ina babu wata katifa da wata daga cikinsu za ta shinfida a qasa. Zuciyarta ce take hautsinawa kamar zata yi amai a sanadiyyar rashin abinci a cikin hanjinta tun jiya da yamma, jiri ta dinga ji dan haka ta laluba gefen gado ta zauna. A bakin kofar dakinsu ta ji ana ta hayaniya data leqa sai ta ga babban daro ne shaqe da shinkafa ana rabawa kowa ya dauki plate din roba kamar wasu almajirai. Hashim ya tabbatar Nihal ba zata fito wajen damben karbar abincin nan ba dan haka sai ya kutsa da qarfin tsiya ya karbo plates biyu. Ya kwankwasa mata kofa sai ta fito, ya miqa mata gami da tambayar ta yaya ya ga kamar bata da lafiya. Dakyar ta bashi amsa ta ce gajiya ce kawai. Ta tura qofa ta koma ta zauna ta kalli qandararriyar shinkafar nan ta hango wani qaramin qashi shine ya nuna an saka nama amma Allah bai sa tana da rabo a ciki ba domin na ta babu nama. Dole ta daure ta luma hannu ta damqo lauma daya ta kai baki, sai yaji da qauri da rashin dandano suka gauraye bakinta har da kunnuwanta. Ta yi juyin duniyar nan ta iya hadiyewa saboda bakar yunwar da take addabar ta amma abu ya gagara. A dole ta tofo ta a cikin kwandon sharar da yake gefen gadon. Bakinta ya hau radadi dan haka ruwa kawai take buqata. Ta suri plates din abincin ta fice daga cikin dakin ta iske kowa ya baje qafa group-group ana ta kai lauma. Saboda dadi Hashim ko hango ta bai yi ba. "Nihal kin koshi ne? Kawo nan ." Fati dangerous ta fada. Nihal ta miqa mata sai ta afka akan babban farantin da suke ci su uku. Ashe anan su ka juye naman dukka dan su ne masu rabo. Ta hango yankan nama sun fi guda biyar- biyar a gaban kowaccensu. "Ku bani ruwa in sha." Nihal ta tambaya a rikice. "Ungo sauran da na sha domin babu wani duk sun wawashe." In ji fati dangerous. Nihal ta tsaya kawai tana kallon bakin da ya sha ruwa ya rage ma ta dargaje-dargaje da shinkafa da wasu jajayen hakora." Nihal ta zabura ta ce "babu wanda baa bude ba?" Domin ita har yanzu bata iya shan pure water ba sai na roba gani take zata kamu da ciwo idan ta sha, amma yau a bisa larura in ta sami sabo za ta sha. Duduwa Indiyana ce ta fusge ruwan daga hannun fati dangerous ta zuqe ta wurgar da leda ta ce " dadi ta yi miki ma da kike neman ruwan da baa bude ba." Nihal ta koma daki ta zauna ta jawo jakar ta ta bude ta dauki alewa bounty da ta siya ta zuba ta sha dan ya shashe mata yajin da ya addabi bakinta. Alamar ciwon ulcer ta fara ji qirjinta yana suya sai ta tabbatar ta yiwa kanta azabar rashin cin abinci kwanan nan, idan bata yi da gaske ba zata kwanta ciwo a garin da bata san kowa ba. Ta shiga tunanin yadda zata ceto kanta- da kanta. Zip din qasan jakarta ta zuge in da take ajiyar kudadenta ta dago da wani kudi bandir guda 'yan naira dubu-dubu ya kama naira dubu dari kenan? sai ta hango wani bandir din shine ta zazzara amma shima ya fi rabi. Ragowar kudin gidan da ta siyawa Hashim ne. Sai ta fara tunani a ranta ina ma ta san wani a garin da zai kai ta ta yi canji ta sami wajen abinci mai kyau ta ci ta qoshi. Shigowar su Duduwa ne ya sa ta yi sauri ta mayar da kudin cikin jaka ta rufe. Hayaniya Su ke ta yi da ihu ba za ka ce mata ba ne, duk magana daya ana rakawa da ashar, ya zame musu ado. Ta bude akwatinta ta dauko tawul da ledar soso da sabulu na wankanta ta fada bandaki, ba laifi a wanke ya ke amma ta cika da kyama kasancewar bata san su waye su ka yi amfani da ita ba.Dakyar ta iya zama akan toilet din bayan data ta yi mata yayyafin dettol dan da shi take yawo. Ta yi wanka ta dauro alwalla ta bude qofa daure da tawul zata fito. Qartan maza ta ga sun shigo Danjuma Ado ne ya daka tsalle yayi super a akan a tsakiyar gadonsu yayin da Duduwa da Fati sun tube daga su sai zani daurin qirji, ga wasu samarin su na tsatstsaye ana ta hira ana hayaniya. Da sauri Nihal ta koma bandaki ta Mayar da qofa ta rufe. Babu abinda ta tuna sai nasihar mahaifiyarta tun tana qarama ta koya mata yadda zata dinga yin kaf-kaf da jikinta a gaban maza. Mazan gidan ma yayyata ne uwa daya uba daya amma kullum ana koya mata yadda zata dinga zama,babu wawan zama, babu fito da hannun rigar nono, babu sakin jiki da gogayya tsakaninta da maza musamman wadanda ba muharramanta ba. A dole ta mayar da rigarta me datti ta fito sai ta iske dakin ya qara cika,ta jawo jakarta ta bi ta bayansu ta fice ba tare da kowa ya ganta ba. Ba ta san dakin su Hashim ba ta dade a tsaye a farfajiyar gidan bata ga fitowarsa ba sai ta fito qofar gida. Ta ga masu adaidaita sahu burjik su ma kamar dai a kano. Ta tsayar da guda daya ta shiga ta zauna ba tare da ta san in da zai kai ta ba. Yaren Hausa yayi mata dan haka ta kwana a gidan sauqi sai ta ce ya kai ta kasuwar da ake yin canjin kudi. Ba tare da bata lokaci ba ya fahimta ya fisgi babur dinsa ya lula. Da la'asar liqis Bash Auta da Bilal ne suka fito farfajiyar katafaren hotel din da aka sauke su sanye da gajerun wanduna da riga mai qananan hannaye. Wajen swimming pool su ka nufa a inda su ka ga kusan duk mutane da suke zaune a wajen turawan faransa ne, faransanci ake yi. Su ka tsinci kansu su na masu nishadi a kusa da fafararen fata tabbas an sami wajen daukar hotunan da Zaa zuba a Instagram. Wayar Bilal ce ta hau qara ya dauko ya duba Halima Jabir ce ta je tasha ta taho da Aisa buzuwa domin ita dazu bata gari ta tafi wani aikin dan haka a motar haya ta taho. Bilal ya ce " ku zagayo ta baya mu na wajen Swimming pool. " Halima ta ce "ai sai mun je daki mun yi sallah mun ci abinci zamu fito Aisa a gajiye ta ke daga Abuja fa ta zarto Maradi." Bilal ya kwashe da dariya ya ce shegiya dole ta daku, ba dai tana so ta zama super star ba." Bai gama dire maganar sa ba sai ya ga wani abu da ya gigita shi har ya gagara qarasa maganar da yake yi a waya. Halima ta gaji da hello hello ta katse wayar. Irin wannan gagarumin tashin hankalin ne ya faru da Bash Auta sai ya zabura ya zare baqin gilashin da yake fuskarsa su ka zunguri juna a lokaci guda. Bilal ya zabura ya dafe qirji ya ce " ka ga Princess last born da nake baka labari rannan, wacce na ce Bahaushiya ce amma tana american fim." Bash ya zabura ya ce " wacce irin princess Nihal Nuren Mubin ce kai." Gaba daya suka bude baki su ka bi ta da kallo sanye take da riga da Wando masu tsada ga wani takalmi mai tsinin gaske kanta babu dankali sai gashi da ya zubo har bayan qeyarta ta na tafe tare da wani bature su na hira abin mamaki yaren faransanci suke yi. Bilal ya zabura ya kwalla kiran sunanta princess bata amsa ba yayin da Bash ya kwalla kiran sunan Nihal Nuren ko waiwayowa bata yi. " Yaya ma zaa ce wannan ba Nihal ba ce ?'" in ji Bash. Bilal ya ce "wai wacce Nihal? Wannan kucakar? ko da wasa ma kada la kawo a ranka Nihal ce, wannan princess ce bari ka gani ma." Ya tashi ya nufi wajensu ya yi sallama amma basu amsa ba.Ya fara magana cikin karshen turanci "Princess za ki iya tuna Bilaliboy abokinki dan Fim a Nigeria? Har kike bani shawara akan yadda zan daukaka." Ina fa? Ba su ma san me ya ke cewa ba suka bi shi da kallo. Bash Auta ne ya qaraso ya ce "ga Nihal ka na gani a zahiri ga dimple dinta nan da wushirya ga irin dariyarta nan. Ke Nihal wai ba ki gane mu ba ne ?" Ta kalle su galala ta juya ta kalli baturen da suke tare cikin rashin fahimta. Yaren faransanci ta yi mu su, daga nan su ka tabbatar bata ma san me su ke cewa ba." "Ikon Allah wannan al'amari ya daure musu kai ga Nihal nan sak, ga princess nan sak amma ba ita ba ce. Su ka koma gefe waya Bash ya dauko ya kira Abbas ya tamabaya "Darakta ina Nihal Nuren Mubin take?: Abbas ya ce yanzun nan na fito daga gidan na raba mu su daki." A' a ka dai sake dubawa ga Nihal anan hotel din da mu ke." Abbas ya yi dariya ya ce " ba dai Nihal ba ce yanzu na bar ta a gida. Amma bari in kira Duduwa in tabbatar ma ka." Su ka kashe waya Darakta Abbas ya kira Duduwa ba ta dauka ba sai ya kira Fati dangerous. Bugu daya ta masa. " ina Nihal Nuren?" Fati ta ce " ta na wanka." Darakta ya kashe waya ya sake kiran Bash ya ce " Nihal ta na gida yanzu haka su na tare da su Fati dangerous. " Sai Bash da Bilal su ka sankare a tsaye su ka ci gaba da kallon wannan baiwar Allah Wacce ta yi mu su kama da mutane biyu mabanbanta. Bilal bai taba karewa Nihal kallo ba dan haka bai santa ba amma babu tantama wannan Princess ce. Har muryar su daya dan sun sha yin magana a waya amma abin mamaki sai ga wannan ko turanci ba ta ji sai faransanci. "Tsarki ya tabbata ga Ubangijin da Ya halicci Nihal Ya halicci wannan yarinya." Bash ne ya fada a bayyane yayin da ya bude baki yana dubanta, ta zo ta wuce ta gabansu. Wajen shan lemo su ka je su ka zauna ita da bature su na sha su na hira da dariya. Ko da wasa ba ta ma kalli in da su ke ba balle ta nuna ta taba saninsu. Bonjour ca va Nihal Nuren Mubin. 11/14/21, 7:19 AM - MY MTN 2: Na kudi ne 馃グ鉂� GABA GADI NA JAMILA UMAR TANKO (JUT) Da daddare ne Hashim ya fito neman Nihal domin kusan kowa na gidan ya fita ganin gari, wasu sun tafi gidan kallo, wasu sun tafi wajen Gala, wasu sun shiga gari kawai don bude ido. A bakin qofar dakinta ya ganta a tsaye rataye da jakarta da alama wani waje take son zuwa itama. Hashim ya dube ta ya yi murmushi ya ce "baccin gajiya na ke ta yi dakyar aka tashe ni na yi sallar magruba. Mu ma ki zo mu fita waje mu ga gari." Nihal ta yamutse fuska ta ce "nina baccin na yi ban dade da tashi ba bana jin dadi ma zuciyata ke tashi kamar ulcer tana son ta kama ni." "Hashim ina Nihal?" Bash Auta ne ya dira a gabansu kamar an jeho shi daga sama. Babu alamar nutsuwa a tattare da shi. Da yake in da suke tsaye babu haske sosai bai gane Nihal ba. Sai su dukka su ka ji gabansu ya fadi. Cike da fargaba Hashim ya ce "ga ta nan ai. Lafiya kuwa?" Bash ya qurawa Nihal ido ya dube ta sama da qasa ita ce dai sanye da kodaddiyar atamfarta leda-leda ta wajen Hashim da ya dinka mata, yarkace-yarkace da ita. Kallon da ya ke yi ma ta yayi kama da na zautaccce. " Malam Bash lafiya kuwa?" Nihal ta tambaya cike da mamaki. Sai ya ji har muryar sak kamar waccan baiwar Allah. Ya zabura ya girgiza kai ya ce "Ah babu komai. Fita za ku yi ne? Yau gaba daya ba ki fita ba ki na daki ko kin je wani waje?" Ta girgiza kai ta ce "ban fita ba, ina kwance a daki bani da lafiya ma yanzu ma chemist Hashim zai raka ni in siyo magani?" Yayi Jugum sannan ya ce " ki na da 'yan uwa a Nijer ko a faransa? Ko ke 'yan biyu ce?" Ta sake cika da mamaki game da wannan tambayar ta ce " ban taba shigowa Nijer ba kuma bani da 'yan uwa a qasar nan. Wani abu ne ya faru?" Hashim ya zabura ya ce "wani sharrin aka sake yi mata? Oga Bash kai ne ka ke kaunar ci gaba Nihal wallahi duk sun tsane ta. Ba ruwanta da kowa ko me aka fada maka qarya ne Nihal a kwance ta wuni ba in da ta je ina tare da ita." Wannan kalamai na Hashim ya sake rikirkita Bash ya sake zunduma cikin wani yanayi. Bash hannu ya ke ta wurgawa ya na magana shi kadai ya juya ya tafi ba tare da ya yi musu sallama ba. Hashim ya dubi Nihal ya ce " wani qazafin aka sake yi miki dan kawai baa so ki yi fim. Na ce miki ai ki zo mu je gidan Malam ya baki maganin farin jini kin ki amma anan Nijer ma an ce garin malamai ne, ki zo a raka mu ki sha rubutun daukaka da farin jini." Nihal ta kwashe da dariya ta ce " ashe baqin jini gare ni kai ne me farin jini ko? Wato ka sami daukaka kenan?" Ya gyada kai ya ce "gashi nan kuwa tun ina zuwa kano har na fara shigo wata qasar yin fim." Nihal ta ce " na dauka ni ka rako ni da bana shan rubutun, ba a dalilina ake dan soka ka a fim din ba? Nan din ma da ka zo kana da tabbacin zaa saka ka ne?" Sai wani tunani mai karfi ya sauko ma sa ya dawo hayyacinsa maganar Nihal gaskiya ce. Ta ci gaba da cewa "ina son duk abinda za ka yi ka riqe Allah Shi kadai ka yarda Shine kadai mai bayarwa kuma mai hanawa. Duk duniya babu mai baka idan Ya hana ka. Haka babu mai kwacewa idan Ya baka. Ban hana ka ka yi addua ba ko ka sa a taya ka ba amma kada ka zaci Malam ne ya baka. Babu wajen Malamin da zan je. Ya kamata ka koma islamiyya Hashim, mu na komawa gida zan sa Inna ta kai ka makarantar Islamiyya." Su ka kwashe da dariya su dukka. Su ka fara tafiya su ka nufi kofar get din fita. Hashim ya ce " na yi makarantar allo Allah sosai ma,da zan bude miki bayana da kin ga shatin duka,har na kusa yin sauka na gudu saboda tafkar da ake yi mana. Ki tambayi Inna." Ta ce "ai karatun allo daban na islamiyya daban. A islamiyya ne za ka ko yi Tauhid , fiqihu, Hadisai da tarihin yadda Annabi Muhammad S.A.W yi rayuwa." "Nihal kin yi bakuwa." In Fati dangerous ce da wata mata su ka diro a gabansu ba tare da sun san ta inda su ka bullo ba. "Baquwa kuma?" Hashim da Nihal su ka hada baki su ka tambaya cike da mamaki. Kafin Nihal ta rufe bakinta sai ta ga bakuwar ta runguma ta. Daga nan ta sanqare a tsaye tana mamaki. Hashim ya zabura ya ce " Lah Najaatu ce ai." Najaatu ta yaye gyalen da ta yi lullubi, fuskarta ta bayyana. Mamaki marar musaltuwa za ka gani a bayyane akan fuskokin Nihal da Hashim. Nihal ta ce " Najaatu daga ina? Garin yaya ? Ta ina ? Yaya aka yi kika san muna nan?" Fati dangerous ta ce "team din Darakta Tukur ta biyo su Mami harka." Nihal ta ji gabanta ya fadi da aka ambaci su Mami. Fati dangerous ta fella da gudu ta bi qeyar Danjuma ta daka. Su ka hau kokawa ta na so ta kwace lemon gwangwani a hannunsa. Nihal ta shiga tunanin yadda wasu 'yan fim su ke irin wannan hali, tabbas su ne wake daya bata gari da suke jawowa dukka 'yan fim zagi. Maganar Najaatu ce ta katsewa Nihal tunanin da ta tsunduma ta na yi. Najaatu ta ce " tare da Tukur da Amina 'yar kwalisa da Mami Harka mu ka taho sai wasu maza guda biyu a motar, dayan ne ya tuqo.Na je gidanki a rufe, na je gidan su Hashim Inna ta ce ke da shi kun yi mata sallama kun tafi Maradi, ba ni da yadda zan yi ga kaya sai na tafi dakin su Mami Harka na tarar za su fito su ka ce min Maradi za su je na ajiye kayanna na zabi kala uku na biyo su. Da suka ce ba zasu zo da ni ba sai na roqi Tukur, dakyar ya bar ni amma naira dubu takwas ya karba a wajena." Hashim ya ce "ai Tukur mayen kudi ne in dai za ki bashi kudi ko abu haramun ne zai aikata." Tukur ne ya dira a gaban Hashim aka hau kallon-kallo babu tantama ya ji abinda ya fada ko kokonto babu yadda suka ga shaida akan fuskar Tukur babu annuri. Hashim ya zabura ya zazzare ido ba shi da mafita, babu wata kwaskwarima da zai yiwa maganarsa ta canja maana akan abinda ya fada. Dan haka titi ya dauka ya dankara da gudu, tun su na hango shi har su ka daina. Tukur ya juyo ya harari Nihal itama ta harare shi. Gefensa Amina 'yar kwalisa da Mami harka ne su ma harar su ke yi mata. " Munafukan banza toh Allah Ya toni asirinku kuma Hashim zai dawo ya same ni. Saboda kun kware da gulma da munafunci har aka dauke aiki baki fada min ba, sai kawai na ji ance kin jawo wancan dankorar na ki kun taho. Zan ga yadda Abbas zai saka ki a wannan fim din." Amina da Mami su ka yi shewa su ka tafa hannu suka hada baki suka " Sai Darakta namu, ka yi min daidai." Su ka juya suka tafi kamar daga sama Tukur ya ji Nihal ta ce " ka shirya kuwa dan za ka sha mamaki." Gaba dayansu su ka jiyo suka bude baki su na mamaki yadda Nijal ta waye har take mayarwa da Tukur magana." Za ta sake yin magana Najaatu ta zabura ta rufe mata baki. Tukur ya ce "haka kika ce ko? To za ki gani." Amina ta ce " na fada maka daman ba ta da kunya." Mami harka ta ce " ah ta fara wayewa har ta fara fita wata qasar yin fim dole ta yi ma ka butulci." Su ka tafi su na ta zagin Nihal. Najaatu ta fashe da kuka ta rungume Nihal ta ce "mutanen nan sun tsane ki tun daga kano gaba daya motar hirar ki ake, su na ta zaginki. Da na fara rama miki ashar Tukur ya cusa min ya ce idan na sake magana zai ajiye ni a cikin daji." Nihal ta yi murmushi ta sa hannu ta gogewa Najaatu hawaye ta ce " kada ki damu, yawan makiyana gwargwadon daukakar da zan samu ne. Zo mu je dakinsu ki ajiye kayan ki mu je mu nemi wajen siyar da abinci mu ci. Nihal da Najaatu suka shiga gida su ka nufi dakinsu Nihal kai tsaye, babu kowa kuwa. Najaatu ta ajiye akwatunta a kusa da ta Nihal ta shiga bandaki ta yi alwalla ta fito ta dinga jero sallolin da ake bin ta, da ta idar su ka fito. Hashim ne a rabe ya na ta boye-boye sai da ya gansu sannan ya taho su ka hadu suka dunguma. Su ka yi ta dariya su dukka. Nihal ta ce " ba ka da aiki sai gulma ai ga irinta nan, ya ce sai ya yi maka shegen duka idan ku ka hadu." Najaatu ta fara bawa Nihal labarin abinda ya faru bayan da ta kaita gidansu. Tabbas an yi tashin hankali ba dan kadan ba daga baya kuma aka sauko aka daidaita. Da kansu iyayenta su ka ce sun amince ta zo ta shiga fim. "Alhamdulullah. Amma wannan wanne abu ne ya kai ga canjawa iyayenki ra'ayi har su ka amince. Naja'atu ta ce "kin san kin bani shawara kada in dinga yin rawa a fim ko? Finafinan duk da mu ka yi sun firfito, sai Babana ya gani kuma ana ta magana a gari, bayan sun gama zagin aka dawo ana yabona yadda na ke acting a nutse na ci saa aka saka ni a mutuniyar kirki a Malama ina ta wa'azi ina jan aya ina fassarawa, na burge sosai daga nan suka ka ce ashe ma wa'azi mu ke yi sannan gaba daya garinmu su ka dinga robubin zuwa ganina, 'yan gidanmu su ka sami daukaka sosai daga sun ce su 'yan gidanmu ne sai ka ga ana rububinsu. Babana rannan mota ya shiga direban ya qi karbar kudin mota ya ce saboda Najaatu an yafe aka ci gaba da yabona sai akwai ya dawo gida da murna ya ce yayi Amanna in yi." Hashim da Nihal su ka cika da murna su na masu godiya ga Allah. Sun zo giftawa ta wani katafaren shagon siyar da abinci, ta cikin galas Nihal ta hango Bilal da Halima da Aisa su na zaune su na cikin abinci. Nihal ta zabura ta ce " ku zo mu shiga nan mu ci abinci." Hashim ya kalli ciki ya kalli haduwar wajen sai ya ce "ba za mu iya siyan abinci anan ba zai yi tsada, ki na ganin wannan wajen kin san na manya ne. An ce akwai wata me tuwo anan gaba, ku zo mu je mu ci abincinmu a acan akan tebura a bakin hanya. Lah kin ga Bilal da su Aisa a ciki su na cin abinci. Na fada miki wajen nan na manya ne irin su Bilal." Bai rufe bakinsa ba har Nihal ta fada cikin shagon su ka biyo ta a baya dan babu yadda su ka iya. Sai ga su a tsaye a tsakiyar haske yarkace-yarkace da su a cikin tsumma. Aka hau kallo-kallo tsakaninsu da Bilal dukka fara'ar da su ke yi ta gushe, bacin rai ya mamaye fuskokinsu. Su ka sha kunu su ka hau harara. Nihal ta tafi gaba gadi GADI ta jawo kujera ta zauna a teburin da ya ke kusa da su saitin Bilal, ta qura masa ido shima ya qura mata ido. Halima ta ce "cabdijam yau akwai drama, za mu ga yadda zasu biya kudin abinci plate daya ma anan. Sun zaci fa irin abincin su ne na kauye na naira hasim." Aisa ta kwashe da dariya ta ce "sun zaci wajen 'yan tuwo-tuwo da ake bajewa a kan tabarma a kofar gida ne. Ba su san har da kudin Ac da suka sha za su biya ba." Farin ciki ya kama Bilal ya yi murmushi ya ajiye cokali ya nade haddu ya ce "ina murna ina jira in ga qarshen wannan fim din, in ga yadda zata kaya tsakanin boss da actor." Sai karaf a kunnen Nihal ta yi kamar bata ji su ba. Dariya su ka kwashe su dukka, su na ta kunshe baki. Najaatu da Hashim sai labe-labe suke yi sun kasa zuwa su zauna, su na tsoron oganninsu da tsoron disgi dan sun san ba su da kudin biya. "Dalla ku zo ku zauna mu zabi abinda zamu ci." Nihal ce ta fada cikin gadara. Hashim ya duka ya gaishe da su Bilal, babu wanda ya amsa masa yana sanda ya ja kujera ya zauna haka ma Najaatu a takure take zaune. Gaba daya 'yan gayu ne a wajen riga da wando suka saka, su kadai ne masu kodaddun atamfofi. Da alama ma ma'aikatan sun raina su sai can a shelaqe wata ta qaraso ta yi musu yaren faransanci. Me zaa ba ku? Su Hashim babu bihim su ka bi ta da kallo kawai, Bilal da su Aisa suka kwashe da dariya . Nihal ta ce " babu me Jin yarenki, hausa za kiyi mana da mu ka shigo nan na ji ku na yin Hausa. Me yasa zaki yi mana faransanci yanzu?" Bilal yayi mamakin yadda har Nihal ta iya yin magana haka cikin qasaita a qasar mutane. Budurwar ta dawo yin magana da Hausa daman rainin ne. Ta miqa musu doguwar takarda na jerin abinci da kudadensu sai Nihal ta hau duddubawa ta na ta zazzaba, abinci kala uku da abin sha ta nuna, ka ji zalla da kifi da dankalin turawa. Ta miqawa Hashim ta ce ya zabi duk abinda yake so ko ya kai kala 10 ne, ya na kallonta yana kifta mata ido. Can ya rada mata ya ce "ba zamu iya biya ba ki zo mu fita." Ta harare shi ta ce "dalla ka zaba kawai ko me kake so." Hashim ya zabi kala biyu shikafa da taliya babu nama. Nihal ta cewa a saka masa kaza guda kada a raba. Hashim ya zazzare ido zai yi magana, ta wurgo masa wata uwar harare, sai ya yi shiru. Najaatu da ta ga haka itama bangaren naman ta fi karfi sai shinkafa aka hada da abin sha kala-kala. Maaikaciyar nan dai rubutawa take amma cike da tsoro, ta sake maimaitawa "dukka zaa kawo muku?" Nihal ta amsa cike da taqama " Eh dukka." Bilal su na jin dadin kallon dramar nan za su so su ga fadan karshe. Su na ta rada su na dariya su na kallo. Nan fa aka dinga jerewa su Nihal abinci kala-kala a gabansu. Da cukula da wuqaqe na turawa. "Ku ci kawai Nihal ta fada a lokacin da ta dauki wuqa da cukali. Haske ta ga gani da alamar an dauke a hoto, a boye Aisa take daukarsu a hoto.Yayin da Halima ta saita wayarta ta na yi musu bidiyo, tabbas social media ta na daf da samun sabon labari. Nihal ta gane amma ta yi kamar ba ta gane ba. Mamaki ya kama su da su ka ga ta iya yankawa da wuqa ta kwasa da cokali mai tsini (fork) ta kai baki ba tare da sun rikito daga bakinta ba. Naja'atu da Hashim ne dai su ka ajiye wuqa suka dauki cokali mai fadi su na kaiwa baka yayin da dadi ya gauraye bakunansu har zuwa kunne. Da abu ya gagara sai su ka kai hannu su ka yagi kaza. Abincin da su Bilal su ka siya bai kai rabin-rabin na su Nihal ba ma amma bill din sai da ya tsorata su. Tabbas su Aisa sun sami abinda ake so, qaryar Nihal ta qare daga yau, za su ga yadda za ta saki jiki ta koyar da tsalle da fadan canis. Fuskar Bilal za ka kalla ta cika taf da murmushi ya na cin abinci cikin nishadi yana kallon kauyawa a birni. "Wato lemo ma ya kai kala goma, tabbas da sun san kudin lemo daya ma da ba su dauki guda goma ba." Halima ce ta fada tana dariya. Su ma ma'aitan maganar su ke yi? su na ta qus-qus-qus a junansu. Su na sake tambayar ma'aikaciyar da ta rubuta order, anya ta nuna musu kudin abincin nan kuwa kuma sun fahimta? Abincinsu kawai su ke ci ba tare da sun damu da kowa ba. Bilal Ya qurawa Nihal ido ta wannan ne karo na farko da ya taba kallon fuskarta a cikin haske tar, tabbas ta yi kama da matar na da suka gani dazu Bash ya dage ya ce ta yi kama da Nihal. Haka a lokaci guda ya ga kamar ta da princess last born. "Rigiji-gafji me ya ke shirin faruwa ne anan?" Bilal ne ya fada a bayyane yayin da ya zabura kamar zai miqe tsaye sai ya fasa. Kansa ya daure sosai ya daina ganin laifin Bash da ya dage ya ce ta na kama da Nihal. Ya ci gaba da kallon sarautar Allah. Aisa ce ta dora hoton su Nihal a Instagram ta rubuta a qasan "some thing big is going to happens." Halima ma ta dora, kalamai daya su ka rubuta. Ashe Bilal ma hakan take ya rubutawa miliyoyin abokansa cewa ga su a qasar Nijer a jihar Maradi, nan da 'yan mintuna za su ji wani labari mai dadin saurara. Ya saka alamar dariya, ya saka alamar gwalo.馃槂馃槂馃槢馃槢. Kafin ka ce kwabo ananta ruwan comments da likes ana ta dokin a ji. Tabbas wannan babban al'amari ne, tunda Jarumai ukun suka saka hoto iri daya suka fadi kalamai iri daya. 11/14/21, 7:19 AM - MY MTN 2: Na kudi ne 鉂ゐ煡� GABA GADI Na Jamila Umar Tanko Su na gamawa ma'aikaciyar ta qaraso dauke da zungureriyar takardar bill ta miqawa Nihal. Nihal ta karba ta duba yayin da ta tuna da cewa ashe da bata iya karatu ba sai ta wayance ta fara jujjuyawa. Ta tashi ta nufi wajen da ake biyan kudi. Ta fara magana da sauran ma'aikatan ba tare da kowa ya ji abinda suke tattaunawa ba. Ta na ta magana an rasa me take cewa. Su Aisa dariya suke ta sheqawa. "Halima ta ce "ta tafi ta roqe su ayi mata ragi, ta dauka a Wudil ne. Yau kam zaa yi ta kenan." Ba su ga sanda ta miqa musu kudi ba saboda ta juya baya, sai dai su ka ga Nihal ta dawo kan tebur dinsu ta yiwa Hashim da Najaatu magana su ka tashi suka bi ta su ka fice. Sai kan su Bilal ya daure matuqa. Mata mai bada bill ce ta qaraso ta miqawa Bilal resit ta ce " Wacce ta fita yanzu ce ta biya muku dukka." Kamar a mafarki, kamar almara, su ka ji tamkar tatsuniya. Aisa ta nuna teburin da su Nihal su ka tashi ta sake tambaya,aka tabbatar masu da cewa ita ce. "Tsarki ya tabbata ga Ubangijin talikai masanin gaibu." Wayar Bilal ce ta ke ta ruri lambobi barkatai ne su ke kiransa. Ya amsawa mutum na farko, na biyu, da na uku dukka abu daya su ke fada cewar su nan su na jira su ji wannan al'amari da yake daf da faruwa fa. Baya bada amsa sai ya katse wayar, saboda bai san me zai ce musu ba, kiran dai ake ta yi ya qi amsawa. Gumi ne yake ta tsatsafowa daga goshinsu su dukka. Bilal ya ji kansa ya fara juyawa ya zabura ya ce " ku tashi mu fita waje. " Su ka fito suka tsaya a waje su na shaqar sanyayyar iska an rasa wanda zai fara magana a cikinsu. Wayar sa ce ta sake yin qara Bash Auta ne ya kira shi ya na fada " wai wannan wanne irin wulakanci ne ku ke yiwa Nihal? Me yasa ku ke so ku tozarta ta ne?" Bilal ya fusata ya yi tsaki ya katse wayar. Wayar Abbas ce ta shigo " ka na ina ?" Tambayar da yayi kenan. Bilal ya kwatanta masa, babu dadewa sai ga Abbas da Bash sun tsaya a cikin mota,su ka firfito suka same su. "Abbas ya ce " mene haka? Wanne irin post ku ka yi? Me yasa zaka biyewa mata ku taru ku tozarta bayin Allah? kawai dan a wulakanta yarinyar nan za ku dauke ta a hoto ku yada? Meye dan sun hau kan teburin cin abinci, su ba mutane ba ne? Dan haka ku gaggauta goge wannan post din dan a zauna lafiya bana son irin wannan. Bash Auta da Bilal ne suka hautsine da fada yayin da Abbas ya shiga tsakiya yana rabiya. Kan ka ce kwabo waje ya cika da mutane musamman da aka gane 'yan fim ne babu abinda yan Nijer suka fi so a wajen'yan Nigeria irin su ga 'yan Hausa fim. Babban takaicin Nihal shine yadda suke da daraja bai kamata su zubar da qimarsu a gaban masoyansu ba wannan shine babbar illar 'yan fim. Sai a lokacin Nihal da su Hashim su ka san an tura hotonsu a social media shine ya jawo fadan dan haka suka labe a lungu su na leqe su na kallo, fadan da babu ruwanka dadin kallo ne da shi. Fada ya koma kan Aisa da Bash tabbas daman tana neman wannan rana da zata yiwa Bash tatas yadda ya ke raragefe akwai alamar yana son Nihal, bayan ya tabbatar da cewa ita ce take bala'in sonsa. Abbas yayi iya kokarinsa wajen rabon fadan domin masu Restaurant sun ce zasu yiwa 'yan sanda waya. Qasarsu akwai doka yanzu nan zaa yi ram da su, 'yan jarida su sami abin bugawa kuwa. Bash ne a fusace ya bar wajen ya koma gefe yana huci, yana waiga bayansa Hashim Najaatu da Nihal ya hango a labe su na shan kallo sai ya sake bude ido ya dube su sosai tabbas su din ne. Abbas na can ya na bada hakuri sai da ya tabbatar Bilal da su Aisa sun shiga mota sun tafi sannan ya dawo ya cewa Bash su tafi. Bash ya shiga mota ya zauna yana huci. Ido su ka hada da Nihal tana kallonsa, wani mugun sonta ne ya ji ya sake sauka a qahon zuciyarsa mai tafe da tausayinta. Abbas ya fisgi mota da gudu suka hau titi ya ce "maganar gaskiya ana caja min kai na gwammace ban gayyaci Bilal ba, ka ga yadda ya saka yarinyar nan a gaba bai kamata ba. Daman can Aisa ta tsane ta kowa ma ya san da haka. Wannan wacce irin rayuwa ce? ka ce wani ba zai daukaka ba sai ka durqushe shi?" Bash ya ce "ka bar ni da su zan koya musu darasi kuma Nihal za ta dauka da babu yadda su ka iya." Da misalin qarfe goma sha daya na dare ne Bilal na zaune a reception din Hotel yana waya ransa a bace yake magana tabbas Bash yake jin haushi kuma ya sha aradu zasu hadu a kano sai nuna masa shi ba sa'ansa ba ne. Wayar da bai qarasa ba kenan princess last born ya hango su na tafe tare da turawa sun zo sun wuce shi, ita kadai ce baqar fata. Ya zabura ya miqe ya bi su a baya yana kasa kunne ya ji me suke cewa amma kash yaren faransanci ne. Kujeru na musamman aka jera musu aka kuma saka jami'an tsaro su na gadinsu a kowacce kusurwa. Dan haka Bilal bai isa ya qaraso in da suke ba. Ta sha riga da wando ta daura dan sirin mayafi a kai, daman haka take yin shigar ta kullum. Gashi yau da ya qarewa Nihal kallo ya ga sun yi kama amma babu tantama wannan princess ce. Ya na daga nesa ya na kallonta, takardu da yawa suka miqa mata ta sassaka hannu. Bilal ne ya kira lambar Bash yaqi amsawa, ba dan komai ba ne sai dan ya zo ya ceto shi daga cikin damuwar nan, domin shine ya san Nihal sosai, shi kuma princess ya sani. Da ta gama saka hannu sai taro ya tashi kowa ya kama gabansa maimakon ta fita waje sai ta haye saman bene inda dakunan suke. A kan matattakala ta ci karo da Bash Auta za ka iya ganin zaburar da yayi ya saki baki yana kallon ta har ta wuce yana.kallonta tana kallonsa babu wanda yayi magana a junansu. Ya bi ta da kallo har ta sha kwana. Ta na shan kwana ta yi kicibus da Aisa da Halima su ma razana suka yi, gabansu ya fadi ko tantama babu wannan ta yi kama da Nihal. Ganin halinda su ka zunduma sai ta gaishe su da yaren faransanci. Su ka bi bayanta da kallo tafiya take ta na rangwada sanye da wani takalmi mai dankaren tsini wanda ko kudi aka ba su ba za su iya tafiya da shi ba. Su ka kalli juna cike da mamaki sai Aisa ta ce " ko dai gamo mu ka yi waccan ta yi kama da Nihal." Da sauri suka sauka qasa suka iske Bash da Bilal su na magana akan abimda idanuwansa suka gani, hakan su Aisa su ka shaida masu abinda suka gani. Waya Bash Auta ya dauko a gigice ya kira Fati dangerous. Ya ce " kina ina yanzu? ki koma gidanku dakinku ki dubo min Nihal tana nan kuwa?" Fati dangerous ta ce "ina qofar gida ne shiyasa ka ji hayani amma ban dade da na na ganta ba ita da Hashim. Amma bari in dubo maka ita. Bayan wasu mintuna ya sake kiran Fati ta tabbatar masa gata ga Nihal tana bacci a daki. Tun kafin Bash ya fada musu abinda Fati ta ce sun ga yadda yanayinsa ya nuna. Ya sake sanar musu da cewa Nihal tana dakinsu. In ba Nihal ba ce wannan toh wacece? " in ji Bash Auta. Bilal ya ce "in ba Princess ba ce wannan toh wacece ita?" 11/14/21, 7:19 AM - MY MTN 2: Na kudi ne馃グ GABA GADI NA JAMILA UMAR TANKO (JUT) Da sassafe misalin qarfe bakwai Bash, Bilal, Aisa da Halima ne su ka dira a qofar dakin su Nihal domin sun kwana ba su rintsa ba, mamaki ya hana su sukuni. Su ka buga qofa sai Duduwa ta bude idanuwanta cike da bacci. Ta zabura ta murtsike ido ta kalle su, gabanta ne ya yanke ya fadi ganin gidiga-gidigan jarumai a gabanta da sanyin safiyar nan. "Ina Nihal Nuren?" Bash ya tambaya a zabure. "Ga ta can ta na bacci. Ke Nihal! Ki zo ana nemanki." In ji Duduwa indiyana. Nihal Nuren ce ta bayyana a gabansu, dakyar take iya daga ido ta dube su saboda baccin da yake cike a idanuwanta. Sai dukkan su suka bude baki su na kallon junansu cike da mamaki marar musaltuwa. " wannan wacce irin kama ce? kuma aca har da tambarin sallar na goshi iri daya? Kai wannan al'amari akwai rikitarwai." In ji Bash. Nihal ta shafa goshinta ta taba tabon sallarta ta ce "me abin sallata yayi? Lafiya? Ku fada min me yake faruwa ne?" Zuciyar Bilal ce ta hasko masa fuskar princess, babu banbanci har da tabon sallar itama. Bilal ya sosa qasumba ya ce " babu amfanin yi ma ta bayani fa ba zata taba ganewa ba. Tunda bata da ilimin da zata gane ma. Ku zo mu tafi." Su ka juya suka tafi suka bar Nihal da Najaatu da Duduwa a tsaye cike da fargaba da mamaki. Najaatu ta ce " me suke nufi? Wani abu aka ce kin yi?" Nihal ta girgiza kai ta ce "ni ma na kasa ganewa tun jiya Bash yake zuwa yana tambaya ta ko ina da 'yar uwa a Nijer? Na ce masa bani da 'yar uwa ." Najaatu ta zabura ta ce "mai kama da ke suka gani kenan sun zaci ke ce. Ai a duniya masu kama daya an ce su bakwai ne ake yinsu haka dai aka ce." Duduwa ta tabe baki ta ce "dama baa hada mu a daki daya ba wallahi, neman rigimarki Nihal ta yi yawa. Tun jiya an hana mu sakat sai a kira a ce ina Nihal ya fi a kirga. Wa ya san mugun abinda kike yi musu, kin hana kowa sakat. Har fada ki ka hada Bash da Bilal, ki ka raba abotar shekara da shekaru. Na rasa dalilin da ya sa ma manyan jarumai kamar su suke kula karamar Jarumar kauye irinki,saboda kawai kin iya fadan canis." Najaatu ta zabura zata mayar da martani, Nihal ta damqe mata baki ta girgiza kai, alamar kada ta yi magana. Duduwa ta warware murya, ta dunkule hannu, ta baje qafa sannan ta ruguzo asharai ta ce " bar ta ta zo mu d'ame, in nuna misali akanta zata tantance ko ni kanwar lasa ce." Nihal ta ja hannun Najaaatu suka fita qofar gida, dan ba zasu koma cikin dakin ba ma balle a ci gaba da fadan, idan ta huce sa dawo. Hashim ne ya hango fitarsu ta wundun dakinsu, sai ya fito ya zo ya same su su ka zauna akan wani dogon benci. Bayan sun gaisa Nihal ta fuskanci jikin Hashim yayi sanyi. Hashim ya yi tsaki ya girgiza kai ya ce " akwai matsala fa, wato fadan Bash da Bilal jiya ya jawo miki zagi a social media, an ce akan ki wata kucaka irinki jarumai biyu sun yi fada. Ali goga ne ya nuna min a wayarsa, hotunanmu ne a wajen cin abinci su Bilal suka dora su na cewa ga wasu kauyawa sun shiga shagon cin abinci mai tsada ba su san yana da tsada ba, zaa ga yadda za su biya kudin himilin abincin da suka yi order. Har yanzu mutane su na jira su ji yadda aka qarke amma basu koma sun ce kin biya ba sun bar mutane a duhu. Sannan Fadan Bash da Bilal ya jawo miki zagi qaton hotonki aka saka dan wulakanci ma baa dauki hoton da kika saka kaya masu kyau ba, aka dauko yagaggiyar atamfa ce a jikinki, hotonki a lokacin da ake daukar shirin 'keke ko Babur' na kamfanin Tukur. A qasan hoton aka rubuta 'Manyan jarumai biyu sun bawa hamata iska a qasar Nijer a sanadiyar Nihal din qauye.' Tunda na ga hoton nan ban iya yin bacci ba wannan cin zarafi ne. Me kika yi mu su ne haka?" Yana gama fada sai wani zazzafan hawaye ya sirnano daga idanuwansa. Najaatu ma ta fara kuka, Nihal ba tausayin kanta ta ke ji ba, ita haka ma ta fi so domin tabbas daukaka ta zo tunda yanzu kowa zai santa. Tausayin qunar zucin da aka dasa akan zuciyar masoyanta sai itama ta fara hawaye. Aka rasa wanda zai lallashi wani a cikinsu. Abbas ne ya dira a gabansu, gaba daya suka dago da jajayen idanuwansu cike da hawaye suka kalle shi. Nan da nan hankalinsa ya tashi tabbas ya san komai. Hawaye ya cika masa ido shima amma sai ya daure ya hana shi zubowa. Ya ce "Nihal sai kun yi haquri sosai wannan ita ce alamar nasara, babu wanda ya taba zama wani abu ba tare da ya sha wuya ba. Ina mai yi miki albishir da samun nasarar da daukaka a cikin wannan harka. Ku tashi mu shiga cikin gida, ku hado kayanku ku fadawa sauran kowa ya shirya nan da awa daya zaa kawo motoci zaa tafi garin da zaa yi shooting." A sanyaye su ka tashi su ka shiga cikin gida, daman sun yi wankansu tun da asuba, kayansu ma a hade yake, suka sanarwa da sauran sakon Abbas. Sai suka fara yin gaba, su ka fito su na jira a qofar gida. Hashim ya ce "yunwa nake ji, gashi basa karbar Naira." Nihal ta bude jakarta ta dauko 'cefa' ta miqa masa ya karba ya tafi wajen me shayi ya hado musu indomi da kwai da shayi ya kawo su ka yi ta ci, har da wasu ma sun samu saboda ashe kudin da ta bayar me yawa ne. Ba su ma san yawan kudin ya kai haka ba sai bayab da suka ga himilin abincin sannan su ka tantance me yawa suka miqa. Sai kowa ya cika da mamaki idan aka ce Nihal ce ta biya kudin abincin da mutane sama da goma suka ci su ka qoshi. " Yanzu wannan bakauyiyar, talakan ce ta iya biyan wannan kudin?" Mutane ne a gefe suke gulma, kasancewar duk an firfito qofar gida. Motocin ne suka iso, sai kowa ya d'uru a ciki, aka fara tafiya cikin qauyuku cikin sahara. Nihal ta waiga ko ina ba ta hango motocin manyan jarumai ba, ta san dai daga hotel dinsu zasu taho. Nihal ta na ta addu'a Allah Ya sa a ba ta roll din da za ta hau raqumi ta yi rawani ta yi tafiya a sahara. Irin wannan al'adu na gargajiya turawa su ka fi so. Tabbas in har ta Samu ta yi zata sami daukaka in har fim din ya fito su ka samu labarin itace. Su ka iso wajen daukar shirin, lallai Abbas ya kashe kudi sosai, gini ya yi na gidajen sarauta. Ga buzaye nan 'yan qasar sun hallara da rakumansu da kaya irin nasu jaka-jaka. Abbas ya ba ta tausayi yadda ya kashe maqudan kudin nan, Allah Ya sa a yi ma sa abinda yake so. Dan ta lura da yadda wasunsu suke yi, ba sa mayar da hankali su yi acting yadda ya kamata kamar da gaske ba sai a tsaya ana ta wani jan aji. A qa'idar fim ana so idan kai mahaukaci ne ka nuna hauka tuburan, idan kai wawa ne ka yi wawancin sosai. Aka ce su bar kayansu a cikin motoci duk su firfito, Nihal na fitowa da hararar basawan qauye ta ci karo wato Tukur da tawagarsa. Gaban Hashim ya yanke ya fadi sai ya zabura. Nihal ta rada masa "ka ka sake ka nuna alamar ka ji tsoro sa, babu abinda ya isa yayi maka kuma kada ka gaishe su." Su ka zo suka wuce ta gabansu ba tare da kowa ya ce da kowa uffan ba. "Munafukan banza kawai." In ji Tukur. Basu kula su ba suka wuce abinsu. Mami harka ce ta ce "babu wacce ta fi bani mamaki ma irin Najaatun nan, a cikinmu fa take amma ta tashi ta koma cikin munafukan can dan kwadayi. Ta zaci wata tsiyar zasu bata su ma ta kansu suke, ana ta yawan neman dakin zama an kasa kama haya. An sami gida me kyau an rabe ance gidan 'yan uwa ne, ina jiran ranar da masu gidan zasu zo su koro su mu ga ta tsiya." Amina 'yar kwalisa ta yi dariya ta ce " yau dai qarya zata qare sai mun wulakanta ta, mun gama magana da su Aisa da Halima Jabir wallahi sai ta raina kanta bata isa ta shiga fim din nan ba." Mami ta ce " da gaske kike kun gama hada komai? Alhamdulullah Allah Ya ba mu saa, yadda ta zo haka zata koma kuwa,shegiya kamar mayya bata fushi kuma." Duk abinda suke fada su Nihal su na ji dan a inda suka zauna babu nisa. Nihal ta yi murmushi ta ce "bai kamata ku damu ba mu da mu ka ce min yarda da Allah ai mun gama samun komai." Najaatu ta ce "haka ne " amma me ya sa kike bari su na zaginki su na hada miki tuggu ba kya ramawa bakya bari a rama miki? Shiyasa suke sake samun damar raina ki." Nihal ta ce " idan mutum yana hali irin na dabbobi bai kamata kai a matsayinka na dan adam mai hankali da daraja ka biye shi ba, sai ku hadu ku zama dabbabin ai." Sai karaf a kunnuwansu Tukur. Ashar Amina ta saki ta kalli Mami ta ce " kin ga yarinyar can 'yar qauye tana kiranmu da dabbobi?" Tukur ya ce "ku ma banzaye ne, na ce ku bar ni da ita na san yadda zan yi da ita amma kuna bata bakunanku." Shalele ya ce " oga da ya gama hada mata duk wani tuggu da ku ka sani tunda ya ce ku yi shiru kawai ku share." Su ka yi shewa suka tafa su ka ce " tuba muke, sai babban Darakta. Hashim ya zabura ya ce "kina ji ko ? Sun gama hada miki tuggu fa suke cewa, ba za ki yi fim din nan ba." Nihal ta fusata ta dakawa Hashim tsawa sai da kowa ya zabura ya waiwayo ya dube su. Ta ce "Hashim na ce ka yi shiru ka kyale duk wanda ya ke ganin zai ja da ikon Allah. Nihal ta dogara da Allah in har duk duniya zasu taru da niyyar su cutar da ni babu abinda zai same sai abinda Allah ya rubuta Ya qadarta zai same ni daman." Aka yi shiru ana gasgata maganarta tabbas kowa ya san tsanar da aka yi mata ta isa. Aka ci gaba da yin qua-qus wasu na yabonta wasu na ci gaba da zaginta. Wannene ne karo na biyu da aka taba ganin bacin ranta Nihal a location, da lokacin da Amina ta mare ta sai kuma yau. Kuma yau din ma Hashim ne ya tunzura ta. Hashim da Najaatu ne suka shiga bata hakuri, huci kawai take yi kamar wata kumurcin muciji ta tashi a fusace ta bar wajen ta tafi can nesa ta zauna ita kadai. Ta na sake zagin mahaifinta da jawo ma ta duk wadannan matsalolin. Ta juya gefenta Abbas ta gani bayan katangar zana shi kadai a zaune a cikin yashi ya dafe kai yana jujjuyawa da alama ya na cikin masifa. Gabanta ya fadi sai ta taso da sauri ta same shi. Sallamar da ta yi masa ne ya tsorata ya zabura ya dago da jajayen idanuwansa ya dube ta, duk iya kokarin da yayi wajen boye mata damuwarsa abu ya gagara ta kasa boyuwa. " Darakta ka fada min damuwarka wataqila in zama silar gushewarta." In ji Nihal. Ya dube ta har takaici ya so ya saukar masa domin maganarta kamar sab'o ce, dan bata san girman damuwar ba ne har take tunanin za ta zama silar warware ta. Abbas ya kasa fada domin ko ya fada mata wannan baqauyiyar babu abinda zata qara masa sai takaici. Da ta dame shi da magiya kuma ya na jin nauyinta ba zai iya korar ta ba sai ya ce " Nihal na kashe kudi mai yawa akan fim din nan sai da na biya manyan jarumai rabin kudaden aikinsu sannan suka yarda suka taho. Ina iyakacin qoqarin ganin kada a sami matsala, tun jiya nake rabon fada tsakanin Bash da Bilal amma yau ma sun sake barkewa da fada. Bash ya yi post akan Bilal da su Halima cewa sun ji kunya sun kasa fitowa su qaryata kansu akan hotunanki da aka saka cewa kun shiga Restaurant kun ci abincin da baki da kudin biya. Aka yi ta zagin su Bilal a social media shine Bilal ya gani ya sami Bash suka yi fada a hotel dazu kafin su fito. Yanzu ni ina ruwana a maganar nan da zai shafe ni? Bilal ya dauke Halima Jabir sun juya kano ya ce a fada min in har da Bash da Nihal a Fim din ba za su yi ba. Dan Allah in shi ba zai yi ba ya kamata ya dauke Halima Jabir? Ita ce fa Jaruma gaba daya a fim din nan, gara roll dinsa zan iya saka Bash in ya so roll din Bash Musbahu ya hau. Yanzu yaya zan yi? Ina ta kiransa a waya yana katsewa ya qi ya amsa min. Da aka jima kuma Bash ya kira ni ya ce Bilal da Halima sun yi hatsari sun ji ciwo sosai, an kira shi a waya an ce ya je ya same su a asibitin Maradi." "Subhanallah! Innalilahi wa inna ilaihi rajuun." Nihal ta fada yayin da ta dafe qirji. Abbas ya ci gaba da magana hawaye ne ya fara zuba daga idanuwansa a wannan karon ya ce "Yanzu maganar a roqi Bilal ma ba ta taso ba dan har na fadawa wadanda suka isa da shi su roqe shi ace ya dawo, sun amince zasu kira shi su yi masa magana kafin su kai ga kira zasu ji mummunan labari. Bash har ya kamo hanya ya nufo nan aka kira shi da wayar Bilal aka ce ya zo waje kaza ga 'yan uwansa sun yi hadari. Ina ga shine wanda su ka yi magana ta qarshe shiyasa suka kira shi. Na ce Bash ya ranta ya biya komai ba zan iya tafiya in bar ku a dokar dajin nan ba. Ga masu raquma na dauko haya babu ruwansu daga yamma ta yi zasu tafi kuma sun ci kudinsu." Nihal ta yi a jiyar zuciya ta sami waje ta zauna tana magana cikin sanyin murya "Allah Ya bawa Bilal da Halima sauqi, Allah Ya sa komai ya zo musu da sauki. Darakta Abbas tabbas ka na cikin damuwa kuma insha Allah babu asara a tare da kai saboda kyakykywar niyyarsa. Ka yarda da Allah ka yarda da ni. In har ka yarda zan iya ni kuwa zan yi maka abinda Halima da Bilal ba za su iya ba. Ka bani wuqa da nama ka yiwa jama'arka nasiha akan su bi duk abinda na ce su yi. Idan an yi haka komai zai tafi daidai, za ka sha mamaki. " Abbas ya tsaya ya na kallonta cike da rashin fahimta da kokonto. "Me Nihal ta iya bare ta koyar? Ina ma zaa hada, yaushe zata iya maye gurbin Halima? Ita da ba ta iya karatu ba ta ina za ta san abinda ya kamata a ce? Ni da zan koya mata a yau bani da qarfin da zan iya kwakwazo, gaba daya ma shirin fim din ya fita a raina." Abbas ne yake tunani. Nihal ce ta katse shi ta ci gaba da cewa " dole kokonto zai addabi zuciyarka saboda kana ganin Nihal 'yar qauye ba za ta iya ba, ba ta iya karatu ba ma balle ta gane. Ina so ka sakar min komai ni ce Darakta ni ce me jan ragama. An karance min tsaf roll din Halima in ba ka manta ba ka bani takardun kafin a canja ni a bawa Halima amma in baka yarda ba, shikenan mu koma Kano in sun ji sauqi sai mu dawo mu yi." Abbas ya zabura ya jingina da jikin katangar zana ya ce " haba yaushe za mu jira su, har sai sun warke? Wannan filin ma hayarsa aka ba ni na sati guda, ginin kuwa na kashe miliyoyin kudi kuma ba ruwansu wa'adina na cika za su rushe. Dan ba ruwan qasar nan da na goro doka kawai suke bi. Nihal.ba ni da wata mafita ki je na ba ki wuqa da nama." Nihal ta ji dadin amsar nan matuqa sai ta miqe tsaye ta karkade baqar abayarta da ta yi fututu da yashi. Ta ce "mu je a fara shooting amma kada ka damu da duk wani canji da zan yi daga masu yin fim din har labarin dan akwai yiwuwar a farke shi tas sannan a dinke. " Wannan karon dubanta ya yi cikin rashin fahimta. Sai kawai aka ga Nihal Nuren da Abbas sun bullo ba tare da an ga sanda su ka tafi ba. " Wai awannan Nihal ce can take tafiya kafada da kafada da babban Darakta, tana masa labari kamar wani sa'anta?" In ji Mami. Amina ta ce " zuwa ta yi ta roqe shi ya saka ta a fim ai ta ji abinda Darakta Tukur ya ce ya gama hada komai ba zaa saka ta ba. Kin san fa makira ce sim-sim-sim da ita kamar wata mumina." Tukur ya juya ya kalli su Nihal sai ya yi qwafa ya ce "ku bar ta duk ta yi ta gama kamun qafarta. Yau dai Abbas ma bai isa ba sai yadda na yi da shi, dan kayan da na kawo masa dole sai da su shirin zai tafi daidai, kome na fada masa zai yarda in ba haka ba, ba zan bashi ba zan juya da su in ya ji haka dole yayi min abinda nake so." Su dukka su ka kwashe da dariya. Talla!! Talla!! Talla!!! Katafaren wajen cin abinci mai suna a qasa: 'JAYROUQ CAFE' Ana daf da bude shi. Akan titin Court Road opp kotun Nafi'u. Abincin zamani irin su: Chinese fried Rice Fried rice Coconut rice Jellop rice. Source: Chiken in sweet and sour source. Stewed Fish Chicken soup Salad: Macaroni salad Chicken Salad Les vagas barbecue chicken salad. Potato salad. Pastries: Shawarma. Burger. Cakes: Birthday cakes Chocolate cake Vanilla cup cakes Red valvet cake Mocktail: Virgin mojito Melonade Lemonade 11/14/21, 7:19 AM - MY MTN 2: Na kudi ne馃グ GABA GADI Jamila umar tanko (JUT) Su na qarasowa Abbas ya daga hannu ya ce "dan Allah a marmatso ku bani aron hankulanku nan, na zo mu ku da babban saqo." Ma su kyamara sun fara hada kyamarori, masu kula da kayan sakawa sun fara warware, masu yin kwalliya su na ta warewa dan haka kowa ya ajiye ya taho. Abbas ya sanar musu da baqin labari cewa Bilal da Halima sun yi hatsari dan haka akwai gagarumar matsala. Sai aka dauki salati wasu na dafe qirji wasu sun dora hannaye akai. "meye abin yi yanzu?" Tukur ya tambaya. Nan dai kowa ya dinga kawo shawarwarin da yake ganin sun dace. Wasu su ka ce a koma Kano kawai a bari ayi wani lokaci, wasu kuma su ka ce a yi fim din kawai wasu su maye gurbinsu. Hayaniya dai ta barke har baa jin maganar wani. Sunaye barkatai ake ta kira cewar sun dace su maye gurbin Bilal da Halima amma babu wanda ya ambaci sunan Nihal ma a ciki.Tukur ya dage Amina 'yar kwalisa ce ta cancanta, da yawa su ka ce Aisa Buzuwa ce ta dace duk da bata qaraso wajen ba amma an ce ba ta cikin motar da aka yi hatsarin. Duduwa ta baje murya ta yi gatsine ta yi fari da ido ta ce "mu kuma kashi muka yi muku a jiki da baa ambaton sunayenmu? Ko mu ba mata ba ne?" Aka kwashe da dariya gaba daya wajen. Hankalin Abbas a tashe yake ya saka tsawa ya ce " wannan fa ba abin wasa ba ne masu raquman nan hayar su na dauko na yini guda,idan ma ba su yi ba su dai kudinsu zan basu. Na yanke shawara Nihal da Bash zasu maye gurbin Bilal da Halima." Shima da ya fada sai da gabansa ya fadi balle ita Nihal din daman tuntuni ta sami lungu ta zauna. "Eh-Eh Darakta ba mu ji sosai ba kamar Nihal na ji ka ambata." Tukur ne ya tambaya. Abbas bashi da tabbacin Nihal za ta iya dan bashi da tabbacin da zai daki qirji ya shaide ta. Ya fada cikin rashin confidence "eh a gwada ta a gani ina ga za ta iya." "Cab lallai akwai matsala." Mami harka ta fada. Hayaniya ta kaure 80% ba sa goyon baya a dora Nihal, irin su Hashim ne kadai ke goyon bayanta. Murna ta kama Hashim da Najaatu har tsalle suke yi sannan arnan gaba su ka hango su su ka fara zagi. Babu wanda ya san Nihal da Najaatu sun sulale sun zagaye baya wajen masu raquma akwai masu jin Hausa kadan-kadan, ta shaida musu zaa fara fim su yi mata shigar 'yayan sarakuna irin na qabilarsu, daman ta iya hawan raqumi a irin qasashe kamar su Dubai da Egypt idan sun je yawon shaqatawa. Amma duk da haka ta ce su koya ma su yadda za su hau, da yadda za ta riqe. Cikin mintuna talatin komai ya kammala. Labari ya kai social media babu tantama akwai wakilin 'yan jarida a cikinsu. Kafin ka ce kwabo duk abinda aka tattauna ya isa ga dinbun jamaa. Idris ne ya kira Abbas a waya, Abbas ya koma gefe ya na amsa waya. Idris ya ce " Abbas ka yi hakuri, ka nutsu domin na san ka na cikin jarabawa. An ce babu Bilal babu Halima sun yi hatsari kana can ka dimauce za ka tafka asara. An ce ka ce za ka saka Nihal a matsayin Halima. Abbas da wata asarar gara wata da ka saka Nihal ka yi asarar Fim dinka gaba daya, gara ka yi asarar wannan rana kafin ayi tunanin wacce zaa saka a madadin ta. Abokan gabarka kamfanin AZ da kamfanin Zubebe su na ta murna wai fim din da kake so ka tsorata su da shi yayi wanwar ya baje. A social media aka dora hotonka a wajen nan da kake yanzu ka yi wujiga wujiga. Ba na bada goyon baya ka saka yarinyar nan ta qauye gaskiyar magana zaa yi ma ka dariya, ni zan taho maka da Salma disco gobe sannan ga Aisa buzuwa a ciki ka zaba...." Iyakacin maganar da Abbas ya fahimta kenan hankalinsa ya koma ga kallon Nihal Nuren Mubin tare da tawagar buzaye akan raquma su na yi mata busa , kida gami da waqoqin sarauta na al'ada. Kidan gwanin dadi haka shigarta ta qayatar a matsayin 'yar sarki ta dawo daga yaqi, gefenta kuwa babbar aminiyarta ce a fim kuma a zahiri Najaatu 'yar mutanen Darazo. Darakta Idris ya ce " yaya na ji alamar ganga ana kida an fara shooting din ne?" Abbas ya ce "Idris katse wayar ina zuwa." Da gudu Abbas ya rintimo ya hadu da dandazo mutanen da kowa ya bude baki yana kallo ba tare da an gane ko su waye ba. Abbas ya cewa masu kyamara ku hasko su daga nesa har su qaraso wannan yana cikin sinasinanmu. "Kamar yaya su dauka? alhali ba ka san ko su waye ba." Tukur ne ya fada a fusace. Abbas bai bashi amsa ba masu kyamara su ka fara aikinsu. Tawagar raquma ta qaraso yayin da gaba daya fadawa su ka fara yiwa gimbiya kirari cikin yaransu na Buzaye. Cikin taqama Gimbiya ta ke jinjina da takofi a hannunta, kasancewar ta sha rawani babu wanda ya gane su. Da gudu aka shinfida mata dardumai abin mamaki sai raqumi ya tsugunna gimbya ta sauko tana tafe tana taqama, qawarta na bayanta itama an koya mata abinda za ta dinga fada cikin yaransu na buzaye. Abin shaawa kowa ya sauko daga kan raquma. raquma guda arba'in ne Abbas ya hayo da buzaye arba'in, sai suka bi layi a saitin qofar shiga gidan sarki.Takofi ta zaro tana yi musu jinjina suna yi mata da tasu takofin har ta shige ciki. "Sin 1 ya kamamala Alhamdulullah." Abbas ya kalli buzaye cike da mamaki ya tambaya "ban koya mu ku abinda za ku yi ba, yaya aka yi ku ka yi tunanin yin hakan?" Nihal Nuren ce tare da Najaatu suka fito daga cikin gidan su ka yaye rawaninsu. Nihal ta ce " Darakta na fada maka ka kwantar da hankalinka ka cire kokonto. Nan da nan yayi amanna ya gasgata za ta iya. Abbas ya zabura ya washe baki ya ce " Ina Baba Shuaibu kai ne sarki marmaza ka zo Buzayen nan su yi maka shigar sarkinsu a ci gaba da dauka. Alhamdulullah komai zai tafi daidai." Tukur da tawagarsa sulale su ka yi su ka zauna, wasu sun dafe kai wasu sun yi tagumi saboda maqaqin hassada da ya mamaye zuqatansu. Ta ina? Ta yaya Nihal za ta ja ragamar wannan babban fim din, su na zaune su na gani. Labari ya canja a social media an dora hoton Nihal da Najaatu akan rakuma a matsayin gimbiya da aminiyarta. Rigijigafji tabbas labarin Nihal ne ke tashe(trending) a wannan satin a Twitter, bloggers su na maganar a youtube, Instagram su na ta reposting, haka ma a Facebook. Sarki ya kame ya zauna fadawa sun yi da'ira 'yarsa Nihal ce a durqushe a gabansa ta na jinjina. Ya daga takofi sama yayi rantsuwa ya ce "na rantse da wanda raina yake hannunsa babu wanda ya isa ya ci mu da yaqi in har Rima 'yata tana raye." Abbas ya dakatar da su ya ce "a cire sunan Rima a saka sunan Nihal kawai. Daman sunan fim din Gimbiya Rima dan haka sai ya koma gimbiya Nihal. "Innalilahi wa inna ilaihi rajuun Amina 'yar kwalisa ta fada yayin da ta yi wuf ta fice waje ta na kuka. Mami ce ta biyo ta a baya anan suka iske Duduwa da Fati dangerous su ma su na tattaunawa, baqin ciki ya wanzu a zuqatansu. Haka Tukur ya dinga gani kamar al'mara kamar mafarki. Labari ya kai social media an shaida musu cewa sunan fim ya canja daga Gimbiya Rima zuwa Gimbiya Nihal. Sai masoyan Nihal su ka hau murna. Baa santa ba sai jiya aka fara ganinta aka ji sunanta a lokacin da su Bilal su ke da niyyar wulaqanta ta ba su san tallata su ka yi ba, a kwana daya kacal Nihal Nuren ta yi suna. Hotonta akan rakumi ta yi shigar sarauta ta daga takobi shine akan status da dp dinbun mutane. Idris ya na ta kiran Abbas amma ina Abbas bai ji ba aiki yayi aiki, fargaba da baqin ciki sun gushe. Ya na karanto abinda zasu ce Nihal na gyarawa,a haka aka kammala Sinasianai masu yawa. Sai ga Najaatu Darazo a tashin farko ta sami daukaka. Basu ji tashin hankali ba ma sai da Nihal ta ce a saka Hashim a matsayin yayanta uwa daya uba daya mai suna Dan sarki Ishaq. Roll din Bash Auta kenan, da Aqilu zaa saka toh bai qaraso ba. Duk abinda Nihal ta nuna masa da shi yake amfani, ya zamanto kawai sai ta zaba ma yayin da kowa ransa ya baci. Mami Harka da Amina da fati da Duduwa dukka a matsayin bororinta su ka fito, daman can ma a haka tsara musu amma yanzu da yake gimbiyar wacce basa qauna ce sai ransu ya baci. Nihal ta dakawa Amina 'yar kwalisa tsawa ta ce " zo nan makira, ban yarda da ke ba. Ke muguwa ce mai mugun hali kina nan aka kashe baiwata fawaza." "qarya kike 'yar talawa Gimbiya Nihal tafi qarfinki." Najaatu Darazo ce ta fada. Amina ta daga hannu ta ce "cut." Ma'ana a tsaya, aka tsayar da dauka. Ya miqe tsaye daga durquson da ta yi a gaban Nihal da Najaatu ta yi magana cikin fusata "gaskiya Darakta ba zan iya fitowa a matsayin baiwar wadannan banzayen ba? ka na jin zagin da suke yi min? Baya cikin abinda aka ce su fada ba." Mami harka ta daka tsalle ta shigo fili ta fara hayani. Abbas ya dakatar da su ya ce maganar su Nihal ta yi daidai? in ba zasu yi ba su tube kayan su kama gabansu, ga dinbun masu so nan." Tukur ya zabura ya miqe tsaye ya fara fada yana fadin gaskiya babu adalci a cikin shirin nan. Kenan an kawo su dan a wulaqanta su ne. Kowa ya shiga tunanin ta in da wulaqanci ya shigo ciki a daukar fim din nan. Jamaa da dama musamman 'yan bayan fage su na son Nihal musamman masu kyamara ta nuna musu makamar aiki sosai, yanzu ba sa shan wahala dauka ba tare da an tsaya ana ta gyare'gyare ba. Buzaye ma su na jin dadin aiki da Nihal tana da faraa gata da mutunta mutane, ga saurin fahimta nan da nan aka yi sinasinai masu yawa. Sin din Bilal, Bash Auta zai hau shi ake ta jira amma hakan bai sa an tsaya ba, an ci gaba da dauka daman Hashim ya riga ya haye matsayinsa. Lokacin sallar azabar yayi kuma an kawo musu abinci da abin sha a cikin manyan Kuloli. Matar da Abbas ya bawa kwangila ce ta kawo daga Maradi ita da ma'aikatanta daman kowa yunwa yake ji an jigata. Hashim ya karbo musu abinci su uku, ruwa da lemo su ka koma gefe cikin wata inuwa su na ci. Hashim ya kalli Nihal ya ce "na gaishe ki 'yar baiwa a she ke ce tsanin da zan taka in hau sama. Na gode da Allah Ya da Ya sa na sanki na hadu da ke domin ke alkhairi ce a rayuwarmu." " Eh dole ka ce haka mana munafuki, in kere na yawo zabo na yawo zaa hadu wataran, sai dai in ba zaku koma Wudil ba." In ji Tukur. Nihal ta giftawa Hashim ido alamar yayi shiru. Najaatu ta fada cikin gadara dan ta basu haushi ta ce "kai daman Hashim sai yanzu ka san muhimmancin Nihal a rayuwarmu? Ai na dade da sanin Nihal alkairi ce, muna godiya 'Gimbiya Nihal." Idanuwan Amina da Mami ta hango, saboda harara kamar zasu fado qasa. Sai ga Bash da Aisa Buzuwa a sukwane wujiga wujiga da su. " A bamu abinci da ruwa mai sanyi." Su ka hada baki suka fada. Aka zubo musu suka zauna su na ci tare a faranti daya. Munafukin da yake yada labari ne ya turawa 'yan Nigeria hotonsu. Nan da nan aka watsa. :Bash Auta da Aisa Buzuwa soyayya ta yi qarfi Allah Ya ida nufi." Abinda aka rubuta kenan. Sai bayan da Bash ya Farfido ya fara gane mutanen da ke gifgiftawa. Ya bawa Abbas labari me dadi cewar an yiwa su Bilal dressing a jikin ciwon da suka ji har an sallame su ma, ya mayar da su hotel anan Maradi da yake babu karaya. " Aisa ta ce " sai dai ayi hakuri a basu kamar sati biyu tabon ya kame sai a fara daukar shirin, har gara ma Billal hannuna da qafa ne ciwon amma Halima a fuska ne duk ta guggurje ko ina duk bandeji. " Abbas ya ce " ah ba zai yiwu mu dakata da daukar shiri dan ba sa nan ba mu tuni ma har mun yi nisa. Yanzu ma break aka tafi zaa ci gaba." " Su waye su ka maye gurbinsu?" Aisa ta tamabaya cike da kidimewa. Abbas ya ce "ku je ku yi sallar ku zo a ci gaba, kada dare ya yi. Da misalin qarfe biyu da Rabi aka dawo bakin aiki sai Aisa ta zabura da ta ga Nijal a matsayin Gimbiya Wajenta kuma har Najaatu ta haye. Wajen Bash kuma Hashim ya haye. "Me yake faruwa ne?" Aisa ce ta tambaya. Yayin da maqiya Nihal suka matso kusa da 'yar uwarsu Aisa maqiyar Nihal su ka bata labari tsaf. Sai ta girgiza kai ta ce "ba da ni ba, wallahi ba zan yi fim da kucakai ba abin ma ya zama shirme." Abbas ya ce "qofa a bude take duk wanda ya ga ba zai iya ba, ya qara gaba." Aisa ta ce " au haka ma ka ce? Ai kuwa zaka san ni 'yar halal ce." Bash ne ya daka ma ta tsawa ya ce ta rufe musu baki. Fim din na ta ne? Ina ruwanta da duk wanda me fim ya saka? Ita ba aiki aka dauke ta ba ta yi abinda ya kawo ta ta wuce kawai. Son sa take yi bata so su sake batawa, sai ta koma gefe tana girgiza kamar wata 'yar tauri. Bash na zaune a inuwa ya na hango yadda Nihal take acting. " kai babu yadda zaa yi a ce yarinyar nan jahila ce, ta san abinda take yi kuma cike da ilimi." Ya na mamakin yadda ta farke fim din nan ta canja masa salo kuma ya tafi daidai. Sai yanzu aka zo kan sin din Nihal da Bash. Bash yayi kyau cikin kayan sarauta amma sarautar Hausawa. Ya taho akan doki ta taho akan raqumi suka hadu a bayan gari daga ita sai shi. Kowannensu na riqe da qatuwar takofi, mai tsanani kyalkyali. Su dukka su ka sauko daga kan abin hawansu su ka hadu a tsakiya kowannensu cike da bacin rai. " ke Nihal! Ke din wacece ne? Ki fada mana asalinki. Qarya kike kin boye asalinki." Baya cikin abinda aka karanto masa aka ce ya fada. Abbas ya tsayar da shirin ya ce "Haba Bash yaya haka? cewa aka yi ka ce ke 'yar sarki ce yadda kike taqama haka nake taqama nima dan sarki ne." Nihal ta ce " Darakta ka bar shi a haka yayi, bari ka ji amsar da zan bashi." Ta dubi bash cikin fushi ta ce "a lokacin da mutum ya shiga cikin abokan gaba ya kamata ya boye kansa. Wanda ya san abinda yake baya nuna asalinsa fa martabarsu domin a lokacin zai gane maqiyansa na asali da masoyansa na asali. Ni Nihal 'yar sarki ce kuma 'yar asali, attajira 'yar gidan altajirai gaba da baya, ni 'yar dangi ce wacce saboda gatana ko quda baa so ya taba ni. Kada ka ga mutum a hanya cikin tsumma ka yi zaton almajira ce qasqantacciya wataqila basaja ta yi." Sai kowa ya fara tsarguwa tabbas a maganarta a kwai alamar tambaya. Bash ya sake fusata fusatar gaske ya dora takofi a saitin wuyanta ya ce "tunda ki ka fito a wannan sigar tabbas ki na da wata miguwar manufa ba abinda ki ke yi ne ya kawo ki ba. Ki fada min me ya kawo ki cikinmu?" "Na shigo duniyarku ne don in san menene rayuwa? In san haqiqanin halin dan adam. Mutum mugu ne kuma butulu ne. Talaka bashi da wani tasiri, dan uwansa talaka shi yake fara kyamarsa, ya tsane shi, ya yi masa sharri. Hakan ya saka ni na sake yin imani, na yi godiya ga Allah mahallicina da a zahiri bai dora min talauci ba. Na sake tausayawa talaka na yi alkawari zan ci gaba da taimakonsa a duk lokacin da na ga alamar yana neman taimako." Nihal ta fada yayin da hawaye ya sirnano daga idanuwanta. Tabbas ta tuna wulaqancin da ta gani. "ki koma duniyarku ki fita daga cikinmu toh. Ke ba alkhairi ba ce a gare mu." In ji Bash. "sai ga shi na saba da ku ba zan iya barinku ba, na zame mu ku qadangaren bakin tulu." In ji Nihal a lokacin da suka kara takubbansu. "Ka matsa ka bani hanya zan wuce duk wannan abinda ka ke yi na riga da na gama jin saqonka na kuma gane da kaina cewar ka na sona ne, wataqila dan ba na kula ka ne shine damuwarka." Ya matsa ya bata hanya, Nihal ta wuce ta je ta hau kan raquminta ta tafi yayin da Bash ya bi ta da kallo a fusace shima ya haye kan dokinsa ya wuce. " cuuuuut." In ji Abbas yayin da ya fara tafi yana daga hannu yana jinjina. Sai 'yan wajen gaba daya su ka hau tafi da ihu. Tabbas sin din nan ya yi masa kyau gaba daya an canja kalamansa amma kuma am fito da sakonnin da ake so a isar ba tare da Abbas ya san abinda suke nufi da junansu ba, domin su na da manufarsu a wannan maganar ta su . Aisa ta fahimci akwai alamar tamabaya a cikin kalamansu sai ta sake fusata. Bayan an yi sallar la'asar aka koma bakin aiki anan ne Nihal za ta kara da Aisa buzuwa. " sarkin garinku ma bawanmu ne dan haka ke ba kowa ba ce illa baiwata wacce ta fito daga tsatson da basu da asali. Ba ki isa ki ja da Gimbiya Nihal ba." Aisa Buzuwa ta tunzura ta ce " Darakta daman haka ka ce ta fada? Na dauka cewa ka yi ta ce "asalin sarkin garinku ma bawanmu ne." Abbas ya yi dariya ya ce "tunda aka ce sarkin garinku ma bawansu ne, kin ga kenan ke ma baiwarsu ce." Aka kwashe da dariya aka kowa ya ce Hausar Nihal ta daidai, dukka abu daya yake nufi. A haka dai dakyar aka qara sin din kamar fada kamar wasa. Dare ya kawo kai don haka aka fara shirin tashi. Garin Maradi zasu koma masaukinsu na jiya sai gobe zaa dawo. Talla!! Talla!! Talla!!! Katafaren wajen cin abinci mai suna a qasa: 'JAYROUQ CAFE' Ana daf da bude shi. Akan titin Court Road opp kotun Nafi'u. Abincin zamani irin su: Chinese fried Rice Fried rice Coconut rice Jellop rice. Source: Chiken in sweet and sour source. Stewed Fish Chicken soup Salad: Macaroni salad Chicken Salad Les vagas barbecue chicken salad. Potato salad. Pastries: Shawarma. Burger. Cakes: Birthday cakes Chocolate cake Vanilla cup cakes Red valvet cake Mocktail: Virgin mojito Melonade Lemonade Contact no. 08065283822 11/14/21, 7:19 AM - MY MTN 2: Na kudi ne 馃グ GABA GADI NA JAMILA UMAR TANKO (JUT) Su Nihal sun nufi wajen doguwar motarsu Bus da ta kawo su za su shiga sai ta hango Abbas ya na yi ma ta dan kira daga lungu, da alama baya so kowa ya gan shi. Ta ce da su Hashim su jira ta bari ta je wajen Darakta ya na kiranta, ta isa wajensa cike da mamaki. Abbas ya ce "ban baki shawara akan ku koma masaukinku zaa iya samun matsala ko su dake ku ko su zage ku. Zan canja muku masauki ku dukka ukun. Yanzu ku yi dubara ko Hashim ya je ya dauko mu ku kayanku daga cikin bus ku kawo motata in sun tafi sai mu tafi. Yanzu kin fita daban da su,kin zama celebrity." Su ka yi dariya ita da shi. Nihal ta kira Hashim da Najaatu gefe ta fada musu saqon Abbas, tabbas ya fadi gaskiya babu abinda zai hana a yi fada yadda kowa ya ke jin haushinsu. Hashim ya tafi da sauri ya fadawa direba cewar ya bude masa but zai dauki kayansu za su canja mota. Ana budewa aka yi yiwa Hashim caaa akai wai kada ya sake ya sace musu wani abu, dan haka duk abinda ya bata shi ne. Mata da maza wasu a waje wasu a cikin mota sai caccakarsa a ke yi, ba komai ba ne illa haushinsu da ake ji sun samu daukaka. Bai kula su ba ya jawo akwatunansu guda uku ya tafi. Anan aka gane cewar an canja musu matsayi sun bar cikinsu sun koma cikin super stars sai ran kowa ya sake baci, Abbas ya na shan zagi daidai gwargwado. Dukka motocin su ka ja suka tafi, Bash ya dauki Aisa su ka tafi. Abbas ne da su Nihal su ka rage, Abbas ya na can su na lissafi da masu raquma ya sallame su. Motarsa ya ce su shiga su tafi, Hashim ya shiga gidan gaba yayin da Nihal da Najaatu suka zauna a baya. Abin mamaki sai ya ga buza daya ya shigo cikin motar. Abbas ya zabura ya tambaya Nihal ta ce ita ce ta ce ya zo su je akwai tattaunawar da za su yi, ta na so ta koyi yaren ko da kadan ne kafin a gama fim din. Abbas ya ji dadi sosai domin akwai hikima a yin hakan. Ya na son Nihal dan komai na ta kamar da gaske take yi ana son actor ya zama haka. Buzu ya na jin Hausa kadan-kadan tun a cikin mota ya fara koya musu ita da Najaatu. Da suka isa Maradi hotel din da aka sauke su Bilal nan ya kai su Nihal da Najaatu ya kama musu daki mai daraja irin na su Bilal. Kai! duniya abar tsoro ce in kai ba kowa ba ne za ka ga wulaqanci. Wato Abbas ko kunya babu har ya daukaka darajarsu. Ya ce Hashim ya zo su je wani gida. Kafin ya bar hotel din sai da Abbas ya wuce dakin Bilal kai tsaye ya je ya duba jikinsa, Aisa ta raka Abbas dakin Halima ya duba ta itama, jikin na su da sauki amma fa za su dauki lokaci mai tsayi kafin su warke gaba daya. Ya shaida musu gobe zaa samo wanda zai tuqa su ya kai su gida. Daga dukkan alamu har yanzu labari bai iske su cewar Nihal ta haye gurbin su ba. Dan a maganganunsu ya ji su na cewa idan su ka warke sai a dawo a yi fim din. Murmushi Darakta yayi a zuciyarsa ya ce " kun makara ai, a wani fim din ma ba zan sake yi da ku balle wannan. Ni da nake da Nihal me zan yi da ku kuma?" Nihal Nuren ce sanye da riga da Wando na Jeans ta na zaune akan kujera a wajen shaqatawa na hotel din tare da bature da buzu su na tattaunawa. Ta bude komfoyutar bature ta na daddannawa email din ta ta shiga ta na karantawa, ta sami dubbunnan sakonni daga masoya da daraktoci turawa da kuma kamfanoni daban daban, ana zawarcinta data zo ta yi musu fim. Da alama an saki wasu daga cikin finafinan da ta yi, duniya gaba daya ta dauka da alama ta karbu. Farin ciki ya ya kama ta sosai musamman da ta ci karo da ruwan alerts zunzutun kudaden da ta samu abin ya firgita ta, ya tsorata ta. Har ta fara tunanin ko mafarki take yi ne, miliyoyin kudin da aka qarasa biyanta ne na fim din data yi, tabbas idan su ka zama naira tana daya daga cikin matasa masu kudin Africa. Nihal ta yi murna sosai tallar da wannan baturen ya gayyace ta kamfanin sun tura mata mail cewa sun dauke ta, domin sun yi bincike akanta sun gano ko ita wacece dan haka za ta yi musu talla akan macemacen mata masu ciki da masu mutuwa a wajen haihuwa a afrika. Za ta yi musu da Hausa da turanci da faransanci. Tashin farko ma miliyan biyar su ka biya ta in ta gama za su cika mata. Ashe meeting din da suka dinga yi kenan da turawa har su Bilal su ka ganta suka zaci ba ita bace. Shi kuwa wannan buzu ya zo ne dan ya karbi kudi, Nihal ta ce gobe su hayo ma ta raquma guda dari da mahaya guda dari da takubba guda dari haka a taho da kayan yaqi guda hamsin-hamsin lallai zaa sha gumirzun yaqi. Da kudinta ta biya ba ta buqatar Abbas ya sani. Bayan bature ya bata takarda ta saka hannu sai ya bata zunzurutun cefa ta miliyan biyu, a ciki ta warewa buzu na sa maqudan kudi ne masu yawa, murna ta rufe shi yana ta godiya. Bilal ne a zaune a gefensu ya na sanye da gajeren wando da riga shimi kasancewar ko ina bandeji ne a jikinsa, sai da ta waiwayo su ka hada ido ta fuskanci ya razana matuqa da ganinta. Ta yi kamar bata ganshi ba, ita da bature da Buzu suka gama kowa ya kama gabansa. Ya bi ta da kallo har ta qure. Abin mamaki bayan ta tafi babu jimawa sai Bilal ya ga Nihal sanye da abaya ita da Najaatu da Bash Auta sun fito su na nemansa. Bash ne a gaba su na biye da shi. Sallama Nihal ta yi masa gami da gaishe shi haka ma Najaatu. Bilal ya saki baki ya na kallon Nihal sama da qasa tabbas yarinyar nan ta na so ta zautar da shi fa. Ya shiga tunani "ashe ba ita ya gani yanzu ta na meeting da bature da Buzu ba kenan?: "Yaya Bilal yaya jikinka? Allah Ya sa kaffara?" In ji Nihal a lokacin da ta katse masa tunanin da ya tsunduma. "da sauki." Ya amsa a fusace gami da kawar da kai gefe da alama baya son ganinta." Da Najaatu ta ga haka sai ta shafawa kanta ruwa, ba ta ma yi magana ba dan ta san ba zai amsa ba. Cikin fara'a Nihal ta dubi Bash ta ce " mu zamu shiga gari wataqila mu shiga cikin wannan qaton wajen cin abincin nan mai tsada na masu kudi, mu sake yin irin na jiya mu ci ko da ba mu da kudin biya Allah Zai fitar da mu, mun ji dadin abincinsu. Ko qawata Najaatu?" Najaatu ta gyada kai ta ce " kwarai kuwa." Su ka juya suka tafi ba tare da sun jira amsa ba. Bash da Bilal suka bi su da kallo har suka qure. Zazzafan tunani ya kece a cikin zuqatan Bilal da Bash sai Bash ya lalubo kujera a kusa da Bilal ya zauna suka ci gaba da kallon masu wanka a cikin swimming pool. Billal yayi a ajiyar zuciya ya ce "ban yarda da Nihal ba, ina zargin fusks biyu ce. Yanzu na ga wannan yarinyar mai kama da ita din nan, ta zauna a wadancan kujerun sun yi meeting da baturen nan da muke ganinsu tare har da daya daga cikin buzayen cikin fim din Abbas. Na gane kayan dan na gansu a hotuna tun kafin mu zo Abbas ya nuna min su. Ta bude laptop ta yi rubutu sosai, da ta shiga ciki sai ta fito sanye da tsohuwar abaya. Anya ba ita ce ba kuwa, take yi mana wasa da hankali ba kuwa?" Bash ya bude baki yana kallonsa ya kasa magana dan kansa a kulle yake. Can ya yi ajiyar zuciya ya ce " ai ta bani amsa a cikin wani sin da muka yi tare da ita dazu. Na ce ta fada da bakinta ita wacece? sai ta ce ita attajira ce mai ilimi, 'yar gata, 'yar sarauta, ta shigo duniyarmu ne dan ta gane masu qaunarta na gaske da maqiyanta na gaskiya." Bilal ya zabura har sai da ya fama ciwonsa. Bash ya riqe shi ya ce "ka da ka tashi tsaye zaka gurde." Bilal ya ce " kada fa a ce Princess last born ce da gaske? Amma ba ka ganin maganarta tana cikin abinda Darakta ya ce ta fada ne?" Bash ya ce " kwarai yana ciki amma ba yadda aka ce ta fada ba ne. Ni dai kaina a daure yake ina mamakinta fa." "Tukunna ma wanne fim ka ke magana, an fara shooting din Gimbiya Rima ne na Abbas?" Bash ya fada cike da gadara " kwarai kuwa mai zai hana an fara. Nihal ce a matsayin Halima Jabir ta sake karbar ragamarta. Kai in takaice maka ma fim ya canja suna ya tashi daga Gimniya Rima ya koma Gimbiya Nihal." Tashin hankali ya kai qololuwa a cikin zuciyar Bilal, sai ya kasa magana. Aisa da Halima ne suka qaraso, Halima tana ta dingishi su ka sami kujeru suka zauna. Bash ya yi zubur ya miqe kamar an muntsine shi, ya ce " zan shiga gari zan ga abokaina." Ya yi gaba ba tare da ya jira amsarsu ba. Bilal ya dago da jajayen idanuwansa ya dubi Aisa cikin fushi ya ce " yau me ya faru a wajen shooting? Labarin da Bash ya bani gaske ne ko dan ya bani haushi ne ya fada?" Aisa ta tabe baki ta ce " bana so in fada muku ne dan kada ranku ya baci, shiyasa ban yi niyyar fada muku ba amma yau kam an yi wani abu wai shi rufa ido. Idanuwan Abbas ya rufe baya ganin kowa sai Nihal, ba ya jin maganar kowa sai ta Nihal da wadannan qazama 'yan korarta." Halima ta zabura ta ce " kina nufin su Nihal ne suka maye gurbinmu?" " sunan fim din ma ya koma sunanta qarewa ma." Sai Halima da Bilal su ka ji hankalinsu ya tashi. Tabbas sun san laifinsu ne, su su ka bawa maqiayar su qofa ta shige. Aisa ta ci gaba da basu labarin wanda tamkar tana caka musu wuqa a zuciya ne. Ta ce " babu labarin da yake trending a social media sai labarin Nihal, ta daukaka kowa ya santa yanzu kuma mu da hannunmu muka tallata ta. Abinda nake gudu kenan, na san idan Nihal ta falle ta shigo aka santa zamu zama 'yan kallo. Dan wayoyinku sun kwankwatse ne ai da kun shiga kun gani, na san ana ta nemanku a waya zaa fada muku wannan labari." Cikin dare bacci ya gagari idanuwan su Bilal, sai juyi kowannensu yake yi saboda hassada da fargaba da nemo mafita yadda zasu dakushe Nihal, har gari ya waye. Abbas ya samo motar da zaa kai su Kano domin ta su ta kwankwatse, wannan kyakkyawar motar da Nihal ta yi ta santi sabuwa fil ita ce ta ragargaje. Allah kenan me yadda Ya so. Sun sha mamaki da su ka ga Nijal da Najaatu sun fito su ma daga cikin hotel, ashe anan suma suka sauka. Wato an daga darajarsu Nihal kenan kafada da kafada suke yi da su. Nihal ta gaishe su ta yi musu sannu babu wanda ya amsa ma ta. Abbas ya ce "yauwa Nihal ku jira ni in sallame su zaa mayar da su Kano ne sai mu tafi da ku a motata." Fuskokinsu Nihal ta kalla tabbas ta san zaa rina wai an saci zanin mahaukaciya tanar sallah, lallai tana shan harara. Ta yi murmushi ta ce "gaskiya ne, su na buqatar su je gida su huta." Maganar nan data yi tabbas harshen damo ce, baqar magana ta fada a takaice amma Bilal ya sha alwashin zai gyara mata zama nan gaba. Kamar wasu awaki haka aka ciccibi qafafuwansu aka zuba su a bayan mota, aka tafi da su. Ashe Aisa ta yi niyyar bin su ta fasa yin fim din, bayan jiya an fara yi da ita. Bash ne ya yi mata gargadi ya ce muddin ta tafi, ba shi ba ita. Ga shi ita take son sa dole ta tsaya, amma ta cika fom kamar za ta fashe. Ta tafi a fusace ta bude gaban motar Bash ta shiga ta zauna, ta na huci kamar kumurci. Bash ma a fusacen yake ya ja mota suka tafi, shima fushin yake yi tun jiya ba tare da kowa ya san dalili ba dan haka babu mai yiwa wani hira a cikinsu. Abbas da Hashim ne a gidan gaba, Nihal da Najaatu ne a kujerun baya suka tafi. Suka isa location su ka iske wajem ya cika tab da mutane dan har motoci sun iso tun dazu? har da qarin wasu motocin daga Kano. Yau ne ranar da zaa ragargaza fim dan na jiya wasa ne. Abbas ya gaisa da kowa a ka shiga ware kayayyaki, masu neman batir na kyamara da sauran abubuwa duk Abbas ya siyo musu ya rarraba musu. Ya bude script ya na karanto in da aka tsaya da kuma ta in da zaa gara yau. Sai su ka hango qura daga nesa, raquma ke tafe himili guda da masu shudayen kaya akai. Su ka juya baya su ka hango wasu tawagar raquman masu jajayen kaya ne akai. Sai kowa ya mimmiqe tsaye ana kallo tun baa ganewa har suka fara matsowa aka fuskanci raquma ne tuli. Sai hankalin Abbas ya tashi ya zabura ya ce "me zan gani? Me yasa raquma suka dawo, bayan na sallame su jiya da kudi mai yawa?" Najaatu ta ce "Nihal ce ta ce su dawo yau ma." Abbas ya daka tsalle ya gigice har sai da wandonsa Jeans ya sulmiyo ya kusa faduwa saboda tashin hankali, Allah Ya sa akwai gajeren wando (boxes) a ciki da an yi tsirara. Abbas a cikin fushi ya ce" ubanta ne zai biya su da ta ce su dawo? Ina Nihal din? Sai ta ci ubanta yau. Wannan yarinya ta cika rawar kai." Aka waiga ko ina babu Nijal babu alamarta Najaatu ta ga Darakta yayi kanta kamar zai sakar mata mari sai ta gudu gefe ta tsaya. Hashim kuwa ya dade da artawa da gudu sai da ya kai wani geji da ya tabbatar ya haye sannan ya tsaya yana leqensu daga nesa. Nan fa maqiya suka samu su na ta caccaka "ah toh ai an fada maka ka qi ji, Nihal sai ta kashe ka tukunna ka ga yanzu ta sa har wandonka ya na shirin fadowa, toh nan gaba ma sai ka yi tunbur? rigar ma sai ta fado." In ji Tukur. Aisa yi take, su Duduwa yi suke, da sauran mata da mazan wajen kowa na zagin Nihal. Amina ta ce "wai ina armurar take ne ko ta gudu?" Daman Nihal sun hada baki da masu kyamara, kawai sai ya fara dauka. raquma su na matsowa hotuna su na sake bayyana. Nihal Nuren Mubin ce a tsakiyar raquma guda hamsin tana cikin masu shudin kaya duk da bata shudin an banbanta shi da na sauran kowannensu takubba manya ne a hannunsu. Su na tafe su na jujjuyawa, ga ganga ga kida, ga busa ga kirari ana yi ta yi ma ta. Daman a sin din yau zaa tashi ne a inda zasu fito yaqi amma a qasa zasu fito ba a kan raquma aka ce su fito ba dan ba zai iya daukar hayar su ba. Da Jamaa suka ga haka sai kowa ya arta da gudu ya zubar da kayan da yake hannunsa suka tafi can nesa suka tsattsaya su na kallon ikon Allah. Buzaye tawa biyu suka hade a tsakiya, sai su ka hau yaqi a junansu. Ana ta karo da tokubba kamar yaqin gaske waje ya kidime da qura. Nihal ma yaqin take yi, gumurzu yayi gumurzu. A can ka hango su Abbas sun sake cillawa da gudu kowa yayi ta kansa. Masu kyamara ne kadai su ka rage a filin daga ashe Nihal ta sake yin hayar wasu masu kyamar Darren fata guda biyu, suma su na cikinsu su na daukar bidiyon. Abbas ya na tsaye kusa da Bash Auta ya ce " Bash na shiga uku, ban taba shiga masifa irin ta wannan fim din ba. Yanzu wadannan su waye? Da ta hayo su kuma sai ta gudu, ko bata nan su dai sun yi aikinsu dole a biya su. Da me zan biya su duk an gama tatike ni. Ashe yarinyar nan haka take har nake goyon bayanta? Nihal ta kashe ni." Ya dora hannu akai kamar mai shirin fasa ihu?" Bash ya ce " kada ka yanke hukunci, bari su gama karon nasu su sauko sai mu ji daga inda suke." An dauki lokaci mai tsayi ana dauki ba dadi da masu Jan rawani da masu Shudi. Ga gawawki nan burjik a qasa amma masu jajayen aka fi kashewa. Su Nihal ne masu shudin kaya dan haka sun ci gari. Sai masu jajayen su ka rage sauran dan haka sai suka ruga da gudu suka yi can nesa. Masu shudaye suka tattare raqumansu suka yi gaba suka bar gawawwaki a zube a qasa. Sai kida da busa suka canja, wannan busar ta alamar an yi nasara ne su ka juyo gida. "Cut." in ji Nihal. Sai masu dauka su ka tsaya. Ta sauko daga kan raqumi ta cire rawani sai ga fuskarta ta bayyana. Ta dagowa su Abbas hannu alamar su taho. Sai a yanzu suka gane ta, kowa ya sake cika da mamaki gami tsananin takaici. Abbas ne a gaba a sukwane ya tunkaro ta ya na fada yana baza hannuwa. Meye hakan? Me kika yi kenan? Kin saka ni a masifa Nihal? Da yawun wa kika aro rakuma, da me zan biya su?" "Ai an biya mu ranka ya dade." daya daga cikin buzayen ya bawa Abbas amsa." Sai ya sankare a tsaye ya na mamaki. " waye ya biya ku?" Bash ya tambaya cike da gigita. Buzu ya daga yatsa zai nuna Nihal sai ta zabura ta ce " Gwanantin Niger ce ta biya har ta bamu turawan faransa masu kyamara guda biyu." Ta nuna turawan. Sai kan kowa ya kulle musamman Abbas ya san dai babu wata gwamnati da take tallafawa 'yan fim. Shi dai koma menene tunda bashi zai biya ba komai ta fancama facan. Sai Abbas ya ji wani sanyi a ransa ya fara washe baki ya na tafi yana yabon yadda sin din ya qayatar. Kwakwalwar Bash ce ta tunano masa maganar Bilal cewar ya ga Nihal da Buzu da Bature sun yi meeting tabbas wannan ne dalilin yin meeting din, ita ta biya babu wata gwamnati. Wannan karon maqiya ne suka fusata su na ta suka cewar "ta yaya zaa bashi gudunmawa amma bata nuna masa bata sanar da shi ba kawai ta yi gaban kanta. Ta shirya komai ba tare da sanin Darakta ba? " Abbas ne mai basu hakuri yana cewa ba ta yi laifi ba a bar zancen kawai." Maqiya sun rasa yadda zasu shiga tsakani Nihal da Abbas duk ta in da sika bi sai a gyaro ta. Mai daukar hoton tsegumi ya tura hotunan Abbas lokacin da wando ya sulmiyo qasa. A ka rubuta Nihal ta cazawa Darakta Abbas kai har wandonsa ya fado qasa. A sake rubutawa Darakta Abbas ya zagi Nihal a lokacin da ta yi gaba gadi ta hayo hayar raquma masu yawa ba tare da saninsa ba. Amma yadda suka kai wancan rahoton haka suka koma suka warware da aka ji cewa an biya kudin raquma tuntuni, Abbas ya na washe baki yana yabon Nihal. Aka dauko hotunan Nihal a yayin da ake gumurzun yaqi a filin daga. Abbas ya tambaya "yanzu Nihal me zaa yi nan gaba?" Ta ce " borori ne zasu saka kayansu su fito a layi dauke da kwaryayyaki mai dauke da alkaki sai su jeru su na jiran isowar Gimbiya daga yaqi. Sarki ma zai shirya ya zauna a fada, Gimbiya za ta wuce ana yi mata jinjina da busa har ta shiga." "Cab ana wani abu wai shi juyin mulli a nan wajen" in ji Aisa. Tukur ya fusata ya ce "na zaci kai ne Darakta ita kuma akta daman akta ce za ta fadawaDarakta abinda zaa yi ko Darakta ne zai fadi abinda zaa yi?" Abbas ya kwashe da dariya ya basu amsa daidai da tambayar su ya ce " Nihal ita ce Actress ita ce Actor ita ce Darakta ita ce mai kyamara." An wuni ana ta daukar fim, sinasinai masu ban sha'awa da abin mamaki. Nihal ta na ta yi musu ba zata musamman yadda suka ji tana furta wasu kalamai cikin yaren Buzaye, ita da Najaatu. Yaya aka yi ta koya? A ina ta koya? Wa ya koya mata? itace tambayar da suke ta yiwa zuqatansu Hashim ya bawa jamaa mamaki yadda shima ya zage ya na acting kai ka ce kwarare ne. Toh ai zama da Nihal ne ya jawo masa haka. Bash Auta da Nihal yau an gwabza yaqi bayan an qare sai aka sauko aka kamu da soyayya mai qarfi a inda iyayensu kuma suka ce basu san zance ba. Sai ga Nihal da Bash su na zubar da hawayen gaske su na ban kwana a biyayya, sai da kukkansu ya taba zuciyar kowa tamkar soyayya gaske. Aisa ta gasgata wannan kallo da kalamai da hawaye ya wuce wasa. Kishi ya tokare ta ta fusata sosai sai da kowa ya gane ta. Tabbas Abbas ya na da tabbacin nasa ba irin na su ba ne, abokan gaba sai su mutu. Idris ya yi saranda ya yarda Nihal ta zama tsanin kai Abbas ga samun nasara, domin ya na ta samun hotuna da labarai kai tsaye daga mahallata wajen shooting. Alhamdulullah an yi wuni guda ana tafka fasaha a wannan waje, haka Nihal ba ta fadawa cewar da kudinta ta hayo hayar rakuma har aka gama, ta ce gwamnati ce ta ba ta kowa bai yarda ba amma an tafi a hakan. Su Mami sun yi saranda cewar Nihal ta girme su a komai sun ba ta girman ma kawai. Fasaharta da wayewarta sun yarda ba za su iya ja da ita ba. Aisa ma fa ta miqa wuya ta yarda Nihal ta gyara mata sinasinanta ko Allah zai sai ta daina kwafsawa. Sai ga Tukur yana shiga harkar Nihal, bata bashi amsa dan shine babban maci amana, ya wulakanta a lokacin bata da tamkarsa. An yi mako guda ana zarya saga Maradi zuwa cikin sahara haka raquma basu daina zuwa ba. Bayan an gama da cikin sahara sai a ka dungumo aka dawo kano a birni zaa qarasa. Nihal da tawagarta su na motar Abbas sun girmi motar su Duduwa Indiyana. Su Nihal basu koma Wudil ba a wani gida qarami Abbas ya sauke ta ita da Najaatu a daki guda Hashim a daki guda. Su dai sun ga in an gama shooting tana fita ta dawo, ba zato ba tsammani sai suka ji ta ce su zo su raka ta wani waje, cikin wani katafaren gida a cikin Nasarawa GRA ta kai su ashe hayar gidan ta kama wanda kudin hayar ya kai a sayi gidan sumunti a qauye, komai akwai a ciki. An yi sati guda ana ci gaba da daukar fim din a cikin garin Kano. Nihal su na zuwa su na dawowa ba tare da an san daga ina suke zuwa ba. Da aka kammala sai Abbas ya sallami kowa ya biya su har Najaatu da Hashim. Sun yi bazata sun sami kudin da basu taba zato ba su na ta murna. Abbas ya shiga jin nauyin Nijal dan ya rasa ma nawa zai biya ta kudin wahalar ta, tabbas ya kamata kudinta ya fi na kowa dan ita ce ma Fim din gaba daya. Nihal ta lura da haka sai ta yi murmushi ta dube shi ta ce " Darakta ni ce da godiya domin ka yi min komai. A lokacin da na buqaci da ka yarda da ni ka damqa min komai, ka amince da hakan ka bani dama. Damar da na jima ina nema baa ba ni ba sai kai. Ka dade ka na cewa ka ji a jikinka zan iya ka na so ka gwada ni. Idan ka yunkuro sai maqiya su danne ka har zuwa lokacin da Allah Ya ce ayi kuma aka yi. Ka gama biya na ba na buqatar naira dayarka ta hada mu. Dan haka kada ka damu kanka a kaina. Bata jira ya bata amsa ba sai ta fice sai dai su Hashim suka same ta a wajen ofis din suka wuce. Hashim dai ya kasa yin shiru sai da yayi magana. Ya ce " yanzu duk wahalar nan da kika sha kin yafe masa komai ya tafi a banza?" Da ya ga babu amsa sai harara, ya ja bakinsa yayi shiru tabbas shi da Najaatu su na tattaunawa sun kasa gane ko ita wacece. Nihal Nuren ve zaune a katafaren falonta da remote Ac a hannunta tana qarawa tana ragewa da safiyar jumaa. Hashim da Najaatu ne zaune akan luntsum-luntsuman kujerun falon, su na zuqar na'ura mai sanyi su na kallon talabijin. Nihal ta jawo jakarta ta dauko mukullin gidanta na Wudil sai ta damqa a hannun Hashim. Ta gyara zama ta ce " ina so Najaatu ta ci gaba da zama a dakinta, ina so ka dauko Inna da Baba su zauna a daya dakin kai kuma ka zauna a dakina." Hashim ya karbi mukulli cike da mamaki musamman da ya ji ta ambaci sunan Inna da Baba. Haka ma ta ga irin wannan mamakin akan fuskar Najaatu. Nihal ta sake bude jaka ta dauko wasu takardu ta miqawa Hashim ta ce "ka karanta da qarfi kowa ya ji ka san ni ban iya karatu ba." Hashim ya fara karantawa ni Alhaji mansur isa Wudil na siyarwa da Hashim Ibrahim wudil gidana da ke unguwar kalau by pass, akan kudi naira miliyan daya da dubu dari biyu, ya biya baa binsa bashi." Hashim ya zabura ya daka tsalle ya dafe qirji ya ce "ni Hashim din ko wani ne? Gidan waye? waye mansur?" Najaatu ta gane sai ta ce "Mansur sunan wanda ya siyarwa da Nihal gida ita kuma ta siya da sunanka, idan na fahimta Nihal Nuren ta siyawa Hashim Inrahim gida sukutum. Haka ne ko Nihal ?" Nihal ta yi dariya ta gyada kai ta ce " Eh an yi haka." Sai Hashim ya barke da kukan dadi ya durqusa a gaban Nihal ya na hawaye ya kasa godiya. Ya ce "daman Nihal ke me kudi ce ki ka shiga cikinmu kika saje da mu talakwa? Ni kuwa wanne irin hallaci na yi miki da har na cancanci ki siya min gida? Duk wahalar da ki ke yi da kakanni bai isa ba sai da kika siya mana gida. Allah ya saka miki da gidan aljanna mun gode." Najaatu ma hawayen dadi ne ya dinga kwaranya ta na ta ta ya Hashim godiya. Nihal ta tabbatar musu ba za ta sake koma Wudil ba, ta dawo kano gaba daya. Daman aiki ne ya kai ta Wudil yanzu kuma ta cika aikinta. Sai jikinsu yayi sanyi su ka ji ba dadi, ta sake tabbatar musu da cewa ta bar musu dukka kayan da suke cikin gidan gaba daya. Laptop dinta ce kadai zasu dauko mata, har kayan sakawa Najaatu ta dauka ta dinga sakawa. Jerin tambayoyi su ka sha jero mata akan su na so su san ko ita wacece amma ta gagara basu amsa ko daya. Sai dariya kawai take yi, Nihal Nuren kenan. Baa son ransu suka bar gida me Ac ba, su ka kama hanyar Wudil da yake kowannensu ya samu zunzurutun kudin da aka biya shi na aikinsa Nihal ba ta qara musu kudin mota ba. Sun isa garin Wudil cike da murna, an kaiwa su Inna albishir mai dadi. Dangi gaba daya sai da su ka ji wannan labarin haka maqwabta. Nihal ta sha addua domin ta dasa murmushi akan kumatun talakawa, kamar yadda ta ke da buri yi a koda yaushe. Bayan kwana biyu su Hashim su ka tare a gidan sumunti tabbas akwai banbanci tsakanin gidan qasa da na sumunti. Ina ma zaa hada. "Tsarki ya tabbata ga ubangijin da ya halicci Nihal. Wannan baiwa mai daraja ce kuma alkhairi ce. Ku kai ni Kano in ga Nihal in yi mata godiya." In ji Inna yayin da ta sake barkewa da kuka, a lokacin da ta ji fanka ta na fifita ta akan katifa mai laushi. Hashim da Najaatu sun zaba celebraties sai Daraktocin wudil ne ke kawo musu hari, su na so su yi musu fim. Hashim ya fara tantama an ya zai sake yin fim a qauye kuwa? Najaatu ta harare shi ta ce " wannan fim din maqiyinmu ne Tukur ka zo mu je kawai mu basu mamaki." Hassada ga mai rabo taki ce sai ga Hashim da Najaatu sun yi wasai sun sake wayewa, kaya masu kyau, wayoyin hannu masu kyau. Su Mami su na ta harare-harare da tsaki,Tukur sai rawar qafa yake yana ambaton sunan Najaatu da Hashim. "Wai ina Nihal take?" Tukur ya tambaya. Amina ta ce "kai ma da bata baki kake. Ai Nihal ta girme ka, yanzu sai su Abbas. Ka na ganin ma an ce ta bar Wudil gaba daya." Ta na rufe bakinta sai su ka ga motocin sojoji da wasu tare da wasu tsala-tsalan jifajifai sun tsaya a gabansu. Sojoji da bindigogi ne suka firfito su ka tunkaro su sai kowa ya gigice suka miqe a tsorace. "Ku dakata kada ku gudu." wani soja ya fada yayin da ya daga hannu ya dakatar da su. Ya taho gabansu ya na magana cikin salama, abin mamakin sojan kamarsu daya Nihal sai kowa ya sake cika da mamaki. Soja daya ya bude daya babbar baqar jeep din sai ga General Nuren ya fito tare da Prop. Shatu mahaifiyar Nihal. Shatu farar fata ce balarabiya sai dai babu wanda yayi kama da ita a cikin 'yayanta su da mahaifansu su ka to kama, sai Nihal ta dauko yanayin jikinta tsab ba su da qiba kuma basu da tsayi sosai kuma ta dauko tsayin hashinta da laushi. " Malam Tukur ni ne Nuren Mubin mahaifin Nihal ka tuna ni ko?" Tukur ya bude baki ya na kallonsa. Tabbas shine wannan talakan da ya zo har bashi da cikon kudin acaba. Yana ku ka yana face majina General ya nuna mahaifiyar Nihal ya nuna Conel Muhammad da Major Abubakar ya sake nuna 'yan sanda biyu Aliyu da Umar ya ce " wadannan officers ne a aikin dammara dukka yayyan Nihal ne uwa daya uba daya. Nihal 'yar gata ce gaba da baya kuma mai ilimi ce, na yi mata haka ne dan ta zo ta ko yi darasin rayuwa kuma ta wayar da kan ku akan yadda za ku inganta sanaarku. Nihal ta yi digiri ta yi masters akan fim kuma ta fara yin fim da turawa ma, ita producer ce kuma director haka Nihal ta goge wajen daukar hoto komai na fim ta karanta. Yadda na kawo ta nan na yankwana ta yanzu na zo ne don in wanke ta da kaina. Na ga fim din Nihal tabbas ta fara kawo canji a masanaantar nan." Kowa ya fara tuni mai zurfi, sai a yanzu suka dinga tunano wasu abubuwan da ta aikata tabbas na masu ilimi ne. Daman nutsuwarta ta isa haka bata damu da kudi ba a she ita a wajenta kudin fim ba kudi ba ne." Tukur ya fara zuga karya ya na nuna yadda ya kula da ita, baya jin kunyar kowa. " yanzu ina Nihal din?" mahaifiyarta ce ta tambaya domin ita burinta ta ga 'yarta. Hashim ya zabura ya ce "nine babban amininta ni da Najaatu, duk garin nan ba ta da kamar mu. Nihal ta tafi Abuja an bata kwangila yin talla, turawa ne suka bata ta ce kada mu fadawa kowa amma ku iyayenta ne dole in fada muku." "Ko kai ne Hashim?" General ya tambaya. Dadi da mamaki ne ya rufe Hashim ya washe baki ya ce " kwarai nine babban amininta. General ya gyada kai ya ce " tabbas haka ne Shazali ya na bani labarin cewa kullum ku na tare. Idan Nihal ta dawo ka ce ta dawo gida wa'adinta ya cika." Kudi mai yawa General ya rarraba musu amma na Tukur da Hashim sun fi yawa. Sannan suka shiga motocinsu suka juya. Su Mami sun yi saranda gami da nadama. Tunaninsu yanzu da wanne ido zasu kalli Nihal su yi qawance da ita dubi irin yadda suka wulaqanta ta. Sai suka fara yiwa Najaatu shishshigi ko Allah zai sa ta san yadda za ta yi ta gyaro musu. Domin sun ga in basu kama qafa da Nihal ba, ba zasu taba shahara ba. Kallon sama da qasa kawai Najaatu ke yi musu babu kunya ba tsoron Allah har sun dawo su na sonta da suka ji asalinta. Tunda Tukur ya zuba kudinsa a aljihu ya damqe, auna tudunsu yake yi yana harsashen za su kai naira dubu ashirin ko talatu. Sai ya ji kawai a dakata da daukar shirin nan sai gobe kuma. Su ka hau yi masa tsiya Tukur da kudi sai Allah. Gaggawa yake ya isa gida ya bawa Sadiya matarsa wannan labarin, ita da ta tsani Nihal, ta wulaqanta ta toh yanzu za ta ji labarin ko wacece Nihal. Su Hashim ma da su ka isa gida sai su ka bawa Inna labarin kowacce Nihal dinta. " Na san zaa rina, saboda yarinyar nan daga gani ta gaji arziki gaba da baya. Duka abin nan da ake yi Nihal ba ta sani ba ta na can Abuja tana ci gaba da aikinta. Bayan da aka gama tsara talla aka gama dauka sai ta dawo kano cikin katafaren gidanta ta yi luf tana hutawa, ta kulle kanta ta na baccin gajiya. A Industry an gaji da nemanta kowa ya na so ta yi masa fim amma an neme ta an rasa don bata da waya. Hashim ake ta damu da kira a waya ana neman Nihal. A dole ya shigo mota ya zo gidanta na Kano, kamar yadda ta ja kunnuwansu kada su bawa kowa kwatancen gidanta ba su fadawa kowa ba. Ta sha mamaki da ta ji ana ta buga get, ta na budewa ta ga Hashim, ta cika da murna shi kuwa har hararar ta ya ke yi sabo ta na jawo musu asara. Akwai fim kala-kala da suke jiranta samunta shine samunsu shi kuma. 11/14/21, 7:19 AM - MY MTN 2: Na Kudi ne GABA GADI NA JAMILA UMAR TANKO (JUT) Ta yiwa Hashim iso zuwa ga babban falonta, abin mamaki sai ya ga ma'aikata inyamurai su na ta jera masa kayan dadi a gabansa. Ya zabura ya ce Nihal "ina ki ka samo wadannan gidiga-gidagan Arnan?" Ta harare shi ta ce "wai kai Hashim baka wayewa ne? Meye kuma gidiga gidagan arna kuma?" Su ka kwashe da dariya su dukka. Nihal ta ce "na dade ban ji wannan kalmar ba ma. Ngozi professional chef ce ma'ana mai dafa min abinci, stella kuma mai gyara min gida. Na dauko wata tsohuwa ma ta na taya ni hira ita ce ta raine ni lokacin mahaifiyata tana karatu kuma tana koyarwa a jamia." Hashim ya zabura ya ce " au na manta mun ga mahaifiyarki ashe farar fata ce jajawur da ita, wayyo Allah na da kin yi farinta da mun sake yin tsada." Sai Nihal ta ji gabanta ya fadi ta dafe kirji tabbas maganar Hashim ba qarya haka prof Shatu ta ke. Kafin ta farfido daga duniyar tunani Hashim ya ambaci sunan Prof. Shatu. Sai Nihal Nihal ta zabura ta miqe tsaye ta tambaya " ka fada min mana a ina ka santa?" Cinyar kaza ya kai bakinsa ya yaga ya kora da ruwan lemo ya lunshe ido ya ce " sun zo nemanki ita da General Nuren da Conel Muhammad da Major Abubakar kai har da yayyanki 'yan sanda biyu a garin Wudil." Nihal ta dora hannu aka kamar mai shirin tsala ihu sai ta fasa. Sai fada take tana nanatawa " Daddy ka kashe ni, ka bata min shirin da na kuaa cimma burina. Me ya sa ka yi min haka? Me ya sa ba ku bari duniya sun ci gaba da daukana a talaka wulaqantacciya ba?" Hashim ya cika da mamakin yadda har yanzu bata so a san a asalinta alhali ga ta da asali mai kyau. Ko basu zo ba ai kowa ya fara zargin akwai abinda take boyewa. Hashim ya sulalo ya sauko daga kan kujera ya ture tebur gefe ya jawo farantin kaji ya fara yaga domin zaman kan kujera da teburi ba zasu isar masa da sakon da yake turawa ciki yadda ya kamata ba. Nihal ta taho da sauri ta dauke farantin ta mayar da shi kan tebur ta ce " wallahi ba ka isa ba, so kake masu aikina su raina baqona. Su ma fa masu digiri ne wayayyu, ka tashi ka hau kan kujera ka ci ga wuqa da cukali dole ka koyi gayu fa ina saka ran za ka zama super star na kwatance." Hashim ya washe baki ya hau kujera ya zauna ya ce " kin katse min jin dadi, ni fa bani na kar zomon ba rataya aka bani. Dan iyayenki sun je Wudil an san kowacce ke sai ki huce a kaina." Nihal ta tambaya " gidan Inna su ka je nemana?" Hashim ya na ta faman dambe da kaza da wuqa da cokali ya girgiza kai ya ce " A location suka zo suka same mu, mutane sun kai guda dari a wajen suka tona. Dadday ya bada tarihin ki ya ce ya kawo ki ne dan ki koya mana sana'armu ta fim saboda shi kika karanta kenan." Wannan karon qudindunewa ta yi akan kujera, dan ta fara jin zazzabin takaici. Hashim ya bata labari daga farko har qarshen abinda ya faru sai Nihal ta yi saranda ta san yanzu kowa ya gama jin komai. Sai da ya cika cikinsa taf sannan ya isar mata da sakonnin producers da Directors da suke damunsa da kira ana nemanta. Nihal ta yi murmushi ta ce " na yi fim na farko nayi na qarshe. Mi Nihal Nuren Mubin sai dai in bada shawara ina gefe." Da alama bai ji dadin wadannan kalamai na ta ba. Yayi juyin duniya akan ta zo su je wajen Abbas shima yana ta kira ta qi yarda. Bai rufe bakinsa ba Abbas ne ya kira, Hashim ya dauka Abbas ya tamabaya ko su na tare da Nihal? Nan da nan Hashim ya amsa " eh gata nan muna tare." Babu yadda Nihal zata yi sai ta karba bayan sun gaisa da babban Darakta nata, mutumin kirki wanda ya qaunace a lokacin da kowa yake hana shi amma bai yarda ba sai da ya farfado da darajarta. Abbas ya ji dadi da jin muryarta dan ya na tsananin nemanta. Ya tambaya "Nihal ina kika shiga ne gari ya dauka ko ina hotunanki a social media da kuma manyan akan alluna na kan titi, ana ta tallar fim din Gimbiya Nihal. Ranar asabar mai zuwa zaa fara nuna shi a cinema a fadin qasar nan. Tabbas ana buqatarki a wajen saboda ke ma jama'a zasu biya su shiga don su ganki. Da fatan za ki yi min wannan alfarmar. Nihal kin yi min komai kin farke labarin kin tsara shi ya tafi daidai,kin qawata shirin da dukoyarki da jikinki dadin dadawa kin yi min duk wannan kyauta ba kya buqatar kudina. Nihal mun sami labarin ko ke wacece tabbas kin fito daga gidan arziki wacce ta gaji arziki." Ta rasa abinda zata ce sai ta yi murmushi ta gyada kai ta ce " ga mu nan zuwa ofis dinka." Murna ta kama Hashim, Nihal ta kira masu aikinta ta shaida musu zata fita, a cikin karshen turanci. Hashim ya sake cika da mamaki ya ce " ka ji wacce aka ce bata iya karatu ba, bata taba shiga aji ba. Amma wallahi kin ba mu wahala." Su ka kwashe da dariya su dukka. Wata lafiyayyiyar abaya ta dora akan riga da wandon da suke jikinta ta dauko jakarta suka tafi. Kallon qafarta yake ta yi saboda ya ga ta saka takalmi cambas fari. Ya na ta mamakin yadda mace zata saka cambas. Bakinsa ya kasa yin shiru sai ya sake tambaya. "Au daman mata su na saka cambass?" Nihal ta yi dariya har sai da cikinta yayi ciwo ta ce " kwarai kuwa, lallai ina da aiki wajen wayar da kai." Ba ta da mota har yanzu a adaidaita sahu suka tafi, sun isa bakin ofishin Abbas sai suka ga wata mota mai kyau an rubuta Bilali 4. Hashim ya zabura ya nuna motar ya ce " wannan na daya daga cikin motocin Jarumi Bilal fa. Ya na ciki ma , amma mun ci saa." Nihal ta harare shi ta ce "kai fa yanzu matsayinka daya da Bilal saboda kai ma super star ne, ina so ka nutsu ka ja ajinka kada ka sake a dinga ganinka kora ko dan maula." Hashim ya gasgata maganarta sai ya nutsu suka shiga a tsanake. Abbas ne kadai sai Editor Anas Bilya yaro mai tashe da ake ji da shi a wajen iya editing. Abbas na ganinta sai ya miqe tsaye dan girmamawa da kansa ya gyara mata kujera suka zauna, bayan sun gaisa sai ya nuna mata Anas a matsayin wanda yake yi masa editing fim dinta. Nihal da Anas suka yiwa juna murmushi suka gaisa haka Hashim ma ya gaishe su. Nihal ta koma kusa da Anas dan taga irin kwarewarsa, tabbas yana qoqari amma akwai kurakurai. Ta tambaya kai ne kake rubuta translation na turanci. Ya girgiza kai ya ce "Bilal ne amma ya tafi dauko dictionary. " Sai ta ji ta raina shi ma ashe turanci na sa kadan ne. Ta jawo kwamfuyuta ta fara dubawa tashin farko ta hango kurakurai a waje uku mabanbanta. Ta gyara su sannannta ci gaba da yi kan kace kwabo ta kusa kammalawa. Har yanzu ya na can ya je ya nemo dictionary dan Nihal ta kusa gamawa. Abbas ya koma gefe yana kallonta cike da mamaki wacce aka ce bata iya karatun Hausa ba ma. Nihal ta dago ta dubi Abbas ta ce " ai bai kamata a yi editing ayi translation ba na kusa ba tunda na yi amfani da wani yare wanda ni kadai na san ma'anar. In ba za ka damu ba idan su Bilal suka gama ka bani in sake bibiya." Abbas ya gyada kai ya ce " ah ai an baki dama ki tafi da shi a yanzu ma." Nihal ta girgiza kai ta ce "bari su gama dai wajen jibi zan zo in karba." Ta tashi ta bar wajen ya koma kan kujerarta ta zauna kenan sai ga Bilal. Bilal ne ya shigo dauke da qaramin dictionary, ya na ganinsu sai ya yi turus da alamar ya razana da ya gansu amma sai ya dake. Ya yi sallama a ciki ciki ya shigo, haka itama ta amsa a ciki-ciki ya wuce yana taqama ya zauna a kusa da Anas. Ya ce " sorry na dan jima ban dawo ba ko? Na hadu da jarumin nan ne na kaduna Iliyas muka dan bata lokacin a studio Silicon. Ina muka tsaya ma?" Anas yayi dariya ya ce "ai mun yi nisa sosai ma." Bilal ya dubi Anas duba na rashin fahimta. Anas ya bude ya nuna masa ce "ka ga in da ya bamu wahalar nan ta yi shi ba tare da ya duba dictionary ba." Bilal ya tambaya cike da fargaba " wacece ?" Anas ya nuna Nihal. Wannan karon zaburar da ya yi sai da ta nuna a zahiri. Ya cire kokonto wannan princess last born ce babu wata tantama. Sai ya qura mata ido kallo na takaici da dana sani da kuma nadama. Ta kawar da kai gefe bata kalle shi ba. Tun daga nan ya ji ba shi da wani qarfin da zai ci gaba. Gumi ne ya dinga tsatstsafo masa domin ya ga samu ya ga rashi. Princess ta yi masa Albishir da alkawura masu yawa tana daf da zata cika masa sai ya neme ta ya rasa. Yanzu gata har gida cikin rashin sani ya wulaqanta ta. Abbas ya ce " Nihal akwai wani sabon fim nawa ko za ki sake taimakawa ki yi min?" Ta gyada kai ta ce " Sai dai ba zan iya ce maka A a ba Darakta." Ya yi murmushi ya ce " amma na gode sosai. Fim din yawanci a Abuja da kaduna zaa yi shi kuma zan so ki karanta labarin na san akwai gyara idan ma zaki farke shi ki wargaza ki dinke irin wancan na baki gari." Su ka yi dariya su dukka. Hashim yayi carafe ya ce " Darakta namu ai kawai ka sakarwa Nihal wuqa da nama. Allah Ya sa in sake samun matsayi in fito a ciki." Nihal ce ta harare shi sai ya yi shiru. Nihal ta gyara zama ta ce " waye Jarumi a fim din?" Abbas ya nuna Bilal ya yi dariya ya ce " a baya kuskure ne, ya yarda za ku yi fim tare yanzu." Hashim ya zabura ya ce "Alhamdulullah fim din zai yi matuqar qayatarwa ga Nihal ga Bilal, wai zaa yi wuta." Allah Ya sani Hashim ya na disga ta kwarai. Ta yi magana a cikin takaici " ah ina kuwa wannan hadi yayi daidai ai bai yi daidai ba, tunda zaa hada Jarumar qauye da Jarumin birni ai sai ta zubar masa da aji. Yayana Abbas ka yi hakuri ba zan iya yin fim da Bilal ba saboda ba matsayinmu daya ba." Bilal ya ji kalamanta tamkar a mafarki, ya ji takaicin furucinta a kansa. Yanzu da ya gane princess ce babu abinda ya fi begets irin yayi fim da ita, tabbas fitowa a fim tare da ita nasara ce babba. Abbas ya shiga bata baki. Kalma daya ta fada ta tashi ta fice shine babu yadda zaa yi ita da Bilal su hadu su yi fim, sai dai Darakta ya zabi daya ko ita ko shi. Hankalin Abbas ya tashi amma na Bilal ya fi nasa tashi. A ka rasa wanda ya iya magana a cikinsu. Hashim ya tashi da sauri ya bi bayanta. A bakin titi ya hango ta, ta na jiran adaidaita ashe Bash ma ya ga wucewarta a fusace, shima ya biyo bayanta. A gabanta ta gansu ba zato ba tsammani, ta daga ido ta kalle su sai ta shaida ashe Bash ne. Ya fada cikin lallashi " ke da ba kya fushi me aka yi miki haka kika wuce a fusace?" Hashim ya ce "ita da mutumin ne Abbas ya ce zai hada su fim da Bilal shine ta ce ba zata taba haduwa da Bilal su yi fim ba, tunda ya ce ba zai yi fim da ita ba a baya." Bash ya gyada kai ya ce "wannan gaskiya ne ta yi min daidai." Nihal ta ji dadin kalaman Bash sai ta saki fuskarta, ya ci gaba da lallashinta akan ta dawo afis din Abbas a zauna a yi magana. Dakyar ta yarda ta juyo, su na tafe Bash yana ta tsokano ta da labari. Aisa ce ta dira gabansu ta kama qugu ta na girgiza ta ce "nan ma location ne da aka fake ana soyayya aka ce a fim ne?" Nihal ba ta kula ta ba dan bata so ya aikata wani abu da zaa buga a jarida. Aisa ta sake tarar gaban Nihal alamar fada ta ke so su yi. Bash ne ya daka mata tsawa " Aisa ki matsa ki bata hanya ta wuce kada ki ja abinda zan wanka miki mari anan." Aisa da Bash suka kaure da Cacar baki, Nihal ta gaggauta barin wajen. Hashim dan shishshigi shine mai rabiya, abin alfahari ne yau a wajensa yana tsakiyar super stars yana raba su fada. Nihal ta isa bakin kofar ofishin Abbas sai ta yi kasaqe tana sauraron abinda suke cewa. Abbas ya ce "ka yi kuskure Bilal, ba kyau wulaqanta dan adam ashe Nihal din da ka tsana ka raina ita ce princess din da ta ce zata taimake ka har kake cewa kana bala'in sonta. Shawara ta da kai shine ka dinga yin komai dan Allah sai Allah ya taimake ka. Ga irinta nan duk wani wulaqanci ka gama yiwa yarinyar nan a niger da Nigeria. Maganar gaskiya ta fi mu gaskiya, ba ni da ta cewa kuma dole in zabi daya a cikinku." Bilal ne yake magana cikin sanyin murya " ni dai a roqe ta ta yi haquri ta yi fim dani wallahi Darakta burina ba zai taba cika ba idan ban yi fim da Nihal ba. Mafarkina kenan a rayuwa, ina son princess fatana in yi fim da ita. Na san ban kyauta mata ba amma rashin sani ne ai. Princess ta so ta taimake ni a rayuwa amma ni ban taimake ta ba, tabbas na yi nadama." Abbas ya cewa Anas ciro min original copy na fim din nan in bata ta gyara, ai yanzu da na san ko ita wacece ba zan yi wasa da damata ba, editin din ta ma na san zai zama special Na gode Allah da na taimake ta lokacin da take neman taimako, ga shi nima tana taimakona." Anas ya ciro ya miqawa Abbas, sai ya fito da sauri sai kuwa suka yi kicibus da Nihal a bakin qofa. Abbas zai yi magana Nihal ta daga masa hannunta ce "kada ka damu. A shirye nake in yi maka komai. " Ya miqa mata CD ta karba ta saka a jaka. Ta ce " jibi zan dawo maka da shi insha Allah idan na kammala." Abbas godiya yake har yana duqawa, Nihal ta zo ta wuce Bash da Aisa da Hashim har da qarin wasu masu sasantawa, ba tare da sun ganta ba ta hau adaidaita ta wuce gida. Ta na isa ta jawo laptop dinta ta fara aikinta a falo. Sai can da jimawa sannan Hashim ya dawo. Har da fada yake yi mata yaya zaa yi ta tafi ta barshi a can yana ta wahalar nemanta? Ta fada cikin gadara "ai in har kai juninka shishshigi wallahi haka kullum zan yi maka." Hashim ya kwalla kiran Ngozi ta zo da sauri ya ce "give me juice and water and chicken." Nihal ta yi dariya ta ce "a kawo musu abinci ma tunda an gama. Akan dining table aka jere musu abinci kala kala, ga farfesun kajin ga shikafa a ga miya. Nihal ta aika a ka kira tsohuwa Baba Balaraba suka gaisa da Hashim sanan suka hau kan tebur suka ci abinci tare. Da yamma Hashim ya ce zai koma gida sai ya zabura ya dauko wata waya mai kyau ya ce in ji Bash ya ce in baki , waya ce da sim dinta. Ya ce ki yi wa Allah dan darajar Annabi ki kunna ku yi magana, ya na son yin magana da ke. Ta harare shi ta harari wayar, Hashim ajiye a kan tebur ya fice ba tare da ya jira abinda zai biyo bayan qarshen hararar ba. Nihal ta fada a bayyane "tabbas Hashim ne silar tona min asiri har sai an san in da nake. Wanna yaron ya qi wayewa." Ta jawo wayar ta kunna tana kunnawa ta samu sakonnin Bash da yawa ta cika da mamaki da ta ji kalaman tsantsar qauna mai hana bacci da ta ginu a cikin zuciyarsa. Ta yi murmushi kawai ta ajiye wayar a gefe. Kira ta ji yana yi data duba sunansa ne ya fito. shine ya yi saving da kansa. Ta yi kamar ba zata dauka ba sai ta tuna cewa ya hada ta da darajar masoyinta shugaba S.A.W, tabbas babu abinda ba za ta iya yi ba in dai ba haramun ba ne muddin aka hada ta da Annabi. Sai ta amsa ta yi masa sallama ta gaishe shi cikin biyayya. Bash ya lumshe ido tabbas ya ji tamkar an yi masa Albishir da aljanna saboda farin ciki. Gaisuwa ce dai kawai suke ta yi su na maimaitawa ya kasa qara furta wata kalma mai kama da soyayya sai yayi mata godiya data kunna wayar ya na fatan ta ci gaba da amsa masa ba dan shi ba sai dan darajar Manson Allah S.A.W. Ta rasa yadda aka yi ya san abinda ta fi so duniya da lahira shine manzon Allah. Ta yi amsa alqawarin zata yi masa hakan saboda darajar ma'aiki. Bash ya kashe waya ya juya ya kalli Bilal ya ce " ka taya ni murna yau Gimbya Nihal ta kula ni." Zuciyar Bilal ta cika da kishi ya ce " ba na tantama Nihal ita ce princess bana ta kokonto yanzu. Saboda yadda na ga turancinta a wajen editing yayi min kama da na princess. Yanzu yaya zaa yi? Bash ka ga kuskuren da na tafka ko? Please ka gyaro tsakaninmu na ga kamar kuna shiri." Bash ya harare shi ya ce "ai ba kama ba ne ba ma, tabbas ina shiri da Nihal kuma har mun kulla soyayya ma." Bilal ya saddaqar ya san ya rasa Nihal kuma ya yi wa kansa. Yayi ajiyar zuciya ya ce " Allah Ya sa ta kula ka, kai din ma. Wai ka san matsayin yarinyar kuwa ?" Bash ya ce "babu ruwana da matsayinta, abinda na sani shine Nihal 'yar qauye ce daga Wudil kuma a haka take burge ni tun ban san ko ita wacece ba." Bilal ya gyada kai ya ce "haka ne. Wai yau ni Bilal har in ce zan yi fim da yarinya ta ce ba zata yi fim da ni ba. Lallai Nihal kin hadu." Bash ya ce " ai bata yi laifi ba idan har zaka iya tuna ranar da na dinga rokqarka da ka daina wulaqanta ta haka, har fada ka yi da ni." Bilal ya gyada kai ya ce "an yi haka sai dai Nihal ta tafka babban kuskure bata san Bilal ba wallahi ko ta halin yaya sai an hada mu a fim. Bash ya fusata da jin kalamansa sai ya diro daga kan mota ya miqa masa hannu ya ce " zan tafi gida umma ta na nemana." "Ok sai anjima" in ji Bilal. Bash ya shiga motarsa ya fara tafiya. Hashim ya kira a waya ya na tambayarsa yadda su ka yi da Nihal. Hashim ya ce " ba ta karbi wayar ba sai kawai na ajiye mata a kan tebur haka bata ce komai ba dai." Bash ya tabbatar yana da babban aiki nan gaba kafin ya samu ya shawo kan zuciyar Nihal. Nihal ta wuni ta sake wuni tana aikin editing da translation zuwa turanci a fim din Abbas. Editing din da baa taba yin irinsa a Hausa industry ba. Ta taso da kanta ta kaiwa Abbas. Ya karba yana godiya itama tana godiya suka tsaya akan sai ranar da zaa nuna fim din a cinema zata je. Dr. Hamza ne ya fito daga bangarensa a gigice ya sami Asp Umar a nasa falon ya miqa masa wayarsa shima kuma a an turo masa a lokaci guda. Hotunan Nihal Nuren ce ya basu ko ina. Wayar Miawiyya ce ta shigowa Hamza ya amsa da sauri. Mu'awiyya ya ce " Hamza shegiyar yarinyar nan fa ta fara wuta a fim." Hamza ya ce "Nihal ko? Ga hotunan ta nan an turo min yanzu muke maganar da ASP Umar. Ance labarinta ke trending a social media." General Nuren ya tara yaransa kakaf a babban falo ya fara magana cikin sanyin jiki ya ce " haqiqa na batawa kowannenku rai ba dan ina so ba sai dan shine kadai hukuncin da ya dace da Nihal. Na fi ku shiga fargaba da tashin hankali a lokacin da na kaita qauye na ajiye ta bata da kowa bata da komai sai Allah. Ta na kuka na juyo na bar ta, na dade bana ci bana sha bana bacci. Kun fi ni kwanciyar hankali dan ba ku san yadda na baro ta ba kuma ban fadawa kowa inda take ba. A lokacin da Ambassador Abba Muse ya kai qarata wajen yayana da sauran abokanmu sun yi min fada sosai sun yi Allah wadai da wannan hukuncin da na yanke. Idan su basu sani ba ku kun sani Nihal daman can 'yar Fim ce, ta riga da ta yi fim dinta a turai. Me yayi saura? Dan haka na ce mu ma ta zo nan ta yi mana mu ma buqatarta. Hakan da na yi na tabbata Nihal ba zata sake yanke wani hukunci Gaba Gadi ba." Ina bibiyar labarunta a industry na ji labarin dukka gwagwarmayar da ta sha har ta kai ga samun nasara. Daga ranar asabar mai zuwa har zuwa wata guda zaa dinga haska fim din Nihal mai suna Gimbiya Nihal. ina so gaba dayanmu mu je mu taya ta murna." "Murna kuma Daddy meye abin murna dan an ga kanwarmu a fim? Ai mu kunya zamu ji ma." In ji Aliyu. Hamza ya ce "mu je mu gani dan kowa sai yabonta yake, an ce baa taba yin bajintar da ta yi a fim ba." Mu'awiyya ya ce " jaridun arewa fa gaba daya labarinta aka buga yadda ta shigo da yadda ake tunanin 'yar attajirai ce." Prof. Shatu ta ce " ina ganin punishment din da aka yi mata ya isa haka a dawo min da 'yata gida. Dazu da safe ma na ji hirarta a BBC radiyo" " This is serious wai daman Hausa fim har sun samu karbuwa a haka a duniya?" Muhammad ya tambaya. Major Abubakar ya ce " ni kuwa Muqaddas ce min yayi ya ganta rannan duk ta rame ta lalace, yararo-yararo da ita a cikin tsumma." Nan dai kowa ya yi ta fadar albarkacin bakinsa. Aka tsayar da shawara Zaa dunguma a je cinema cikin shoprite ranar asabar da yamma. Siyama da Muqaddas sun hada baki sun cewa iyayensu zasu je unguwa sai kowannensu ya fito daban daban a cikin motocinsu. A shoprite suka hadu sai gata ga Major Abubakar, bayan tsawon lokaci ba su hadu ba sai dai a waya, iyayensu sun raba alaqarsu auren da aka dade da tsayawa ya rushe. Major Abubakar ya harare ta ya ce " meye abin zuwa kallon Hausa fim kuma ku da aka ce ku guje mu?" Siyama ta yi gatsine ta ce " na zo na ga qawata ne ba dan kai na zo ba." " fadi gaskiya dai." major ya fada cikin faraa. Cinema ta cika damqam da jamaa jaruman fim kusan gaba daya sun hallara amma kowa waigawa yake ko zai ga Nihal anma babu ita babu kamanninta. Sai ga Abbas ya iso shi kadai babu Nihal. Tawagar Tukur ma sun samu isowa su Hashim, Najaatu, Mami da su Amina 'yar kwalisa. Abbas ake tambaya shima yana tambayar su Nihal. Hashim yayi ta kiran wannan wayar da Bash ya bata amma tana shiga baa amsa ba. Haka Bash ya kira ya fi sau hamsin babu amsa. " Hasbunallahu wa ni'imal wakil" Abbas yake ambato domin duk wadannan jifgin jamaar masu son ganin Nihal ne in bata zo sun ganta ba ba zasu ji dadin kallon fim din ba. Haka su Abbas suke ta bada hakuri cewar Nihal na kan hayar zuwa. Shishshigin Hashim ne ya kai shi wajen mahaifan Nihal ya gaishe su ya gabatar da kansa a matsayin babban amininta. Su dukka suka taru su na jeho masa tambayoyi har ya tsorata, dan bai san in da Nihal take yanzu ba. Ya yi wuqi-wuqi da ido yana kame-kame. " Lah ga Nihal din can." Naja'atu ta fada cikin murna. Sai kowa ya waiwaya ya dube ta. Nihal Nuren Mubin ce ke tafe cikin nutsuwa da Jan aji, ta yi kyau ta bawa kowa sha'awa. General ya dubi Conel Muhammad ya ce " Nihal ta na buqatar security ka tura yaranka su yi mata exco. 'Yan jarida da dandazo Jamaa ne su ka yi kanta tun ana iya hango ta har aka daina hango ta sun kare ta. 11/14/21, 7:19 AM - MY MTN 2: Na kudi ne 鉂� GABA GADI NA JAMILA UMAR TANKO (JUT) Kan ka ce kwabo sojoji sun shiga tsakiyar ta da mutane, camak su ka yi ka yi kwana da ita baa san ma ta qofar da aka shiga da ita ciki ba, sai dai aka fadawa su General su shiga ta baya su ma. Sun Shiga cikin cinema an fara nuna fim din Gimbiya Nihal. Bilal, Halima,Aisa sai suka disashe kai ka ce baa taba rububinsu ba,babu wanda yake ta ta su kowa sai Nihal. Sun yi nadama da su ka qi yin fim din nan, wannan fim ya yi matuqar yin kyau amma sun manta wacce ta sa fim din ya qayatar. Daman masu iya magana na cewa daidai kudinka daidai shagalinka. Nihal ta saki kayan aiki dan haka dole fim ya yi kyau. Sannan acting din da ta yi babu wanda zai iya kwatanta irinsa ma. Bash Auta yana kusa da su sai murmushi yake yi kawai, don yana son irin haka ta faru mutum ya tafka tsiya tun daga duniya Allah Ya yi masa kamun talala. Ya na jin dadin yadda Nihal ta samu daukaka a cikin dan qaramin lokaci ya tuna irin hakurin da ta yi da wulaqancin da ta sha, tabbas mai hakuri shi ke da riba dan bata yin fushi sam. Ya dinga aiyano ranar da Nihal za ta amince da soyayyarsa ta yarda ta zata aure shi. Daman can ya rasa dalilin da ya sa take burge shi gata a cikin tsumma kuma yanzu ma ta ci gaba da burge shi. Aisa ce a kusa da shi ta lura murmushi ne cike da fuskarsa, baya ma taya su takaici ko yayi kishin kansa. Ta kula daga an nuno Nihal aai murmushin ya qaru. Ta yi tsaki ya yi qwafa ta harare shi. Bai kalle ta ba, gyada kai kawai yake ta yi kamar mai jin kida. "Lallai iska tana wahalar da me kayan kara." Bash ya lumshe ido ya ce "Allah sarki Nihal tawa ta gaji arziki, ta gaji mulki, ta gaji ilimi. Allahu akbar. " Bilal ya fusata ya ce "Bash! wannan cin fuska ka ke yiwa Aisa fa, babu kyau." Bash ya ce " ka ji na ambaci sunan wata Aisa a maganata ne?" Halima Jabir ta fusata ta ce "ke ma Aisa kin cika naci ki rabu da shi ya je ya qarata da wannan banzar. Masoyanki burjik wadanda suka fi shi komai, masu kudi ma da kamala." Bash ya tuntsire da dariya ya ce " da ma ya fi wallahi da na huta." Aisa ta fara zubar da hawaye zazzafa. Hasiya carkwai ce a kusa da ita ta yi mata rada ta ce " ki kwantar da hankalinki wallahi sai mun kaita wajen baka anyi ma ta a asirin da ba zaa sake kallonta a industry ba kuma sai mun yi musu farraqu da Bash din, sai ya ji ya tsane ta." Aisa ta yi murmushi ta share hawaye. Bash ya harari Hasiya Carkwai ya ce "in junanki gulma da hassada haka za ki qare babu ci ga, sai dai ki yi ta rakiya gashi dai kina zaune Nihal din da ku ka tsana ta zo ta haye ta barki." Ta fara magana tana daga murya, sai Bash ya tashi ya bar wajen dan ba zai iya zama a kusa da wadannan ba. Hassada ta gama cinye musu zuqata. Wajen Abbas ya koma suka zauna. Tabbas an cika damqar a cikin cinema nan, sai ihu ake ana jinjina. Nihal ta kawo canji a cikin masana'antar nan sai ka rantse ba Hausa fim kake kallo ba, kai ka ce turawa ne su ka shirya komai kamar gaske ga jini nan ga kayan ciki a waje duk Nihal ta tsara kuma ta qara wasu a wajen editing. General da Prof. shatu sai suka zuba ido Prof kallon Nihal a fim, su na fada a zuciyarsa "yanzu 'yar mu ce ta yi wannan bajintar kamar a mafarki? Haka 'yan uwanta maza suka saki baki su na kallo, kansu ya daure yanzu ace Nihal ce ta yi wannan bajinta. Siyama ce kadai ta samu ta kutsa aka shiga da ita wajen da aka boye Nihal daman ita ta san komai ko a turai su na jinjinawa fasaharta. Muqaddas ya zaci zai ganta ta na rawa ko wani shirme a fim, amma bai gani ba fim ne mai nishadantarwa in ka kalli sin din farko ba za ka iya tashi ba sai ka so ka ga me zai faru a nan gaba. Ta yi shigar mutunci ta yi amfani da kalamai masu muhimmanci, ta yi waazi, ta fadakar. Shi dai a yau ya daina ganin illa a fim da har ake cewa ba zai aure ta ba. Toh in haka ne babu illa a fim din Hausa kenan sai dai su 'yan fim din ne suke bata rawarsu da tsalle wajen yin abinda bai dace a zahiri da badini ba. In har zasu kare mutuncinsu da martabar gidansu gami da Addininsu su shirya fim mai ma'ana, Me zai sa a zage su? In har zasu yi qoqarin yin acting kamar na Nihal din nan su fitar da sako da darasi ta sigar wa'azi tabbas zaa daina zaginsu da sukarsu da zargi akan su na lalata tarbiyya. Sai tafa hannaye ake ta yi ana ihu ana kiran " sai Gimbiya Nihal Nuren." Masu kallo sun yi amanna tunda su ke basu taba kallon fim din Hausa mai maana kamar wannan ba. 'Yan gidan su Nihal basu taba zama sun kalli fim din Hausa tun daga farko har qarshe ba sai yau. Sun ga nutsuwa sun ga fasaha ga hikima. Tabbas sun yi jinjina sai suka ji kansu yana fadi yana fashewa saboda kowa a wajen Nihal da Nuren Mubin yake kira, dan haka Nihal ta yi suna, mahaifinta yayi suna, danginka gaba daya sun yi suna. Sai da aka gama aka firfito. Nihal ta fallo da gudu ta rungume mahaifiyarta da 'yan uwanta gaba daya sai hawaye kowannensu yake an tafi shekara guda kenan basu ganta ba. Mahaifinta kuwa yayi-yayi ta zo wajensa amma ta qi zuwa. Da alama tana fushi da shi ne tana zargin baya sonta yanzu tunda ya kai ta ya wutar ya tafiyarsa. Da ya ce ta zo su tafi gida sai ta ce ba zata koma gida yanzu ba don bata gama ayyukan da ta dauki alqawari ba. Nan fa su ka ja itama ta cije sai da ta ga alamar in bata bi su gida da qafarta ba sojojin nan zasu cicvibe ta su saka ta a cikin mota da qarfin tsiya. Kalaman mahaifiyarta ne ya tayar mata da hankali sai ta ji dole ma ta koma gida. Prof Shatu ta matse hawaye ta ce " ni kuma laifin me na yi mu ku da ku dukka ku ke azabyar da ni? laifin junanmu ya na shafa ta. General ya azabtar da ni da ya dauke ki daga gabana ya kai ki in da ban taba sani ba balle na je na nemo ki duk a sanadiyyar ya na so ya hukunta ki. Ke kuma yanzu kin ce ba za ki dawo gare ni ba a sanadiyyar kina jin zafin hukuncin da ya yi miki." Nihal ta goge mata hawayen fuskarta ta ce "Mummy ki daina kuka zan bi ku gida. Shikenan?" Tawagar Bilal da tawagar Tukur da tawagar Abbas da sauran wasu 'yan fim din ma haka suka yi carko-carko a gefe su na kallon 'yan gayu da qarshen gayu wato Nihal da 'yan gidansu. Babu yaren da yake tashi sai turanci, Original turanci ba irin na Lagos ko a Abuja ba. Mami harka ta kama baki ta ce " ikon Allah. wai yanzu wannan Nihal ce da ta zo tana tsamin dusa da hayaqi na dingi cin ubanta ashe kadara ce ba irinmu ba ce. Amma yarinyar nan ta yi mana ba zata, ta cuce mu da bata nuna mana martabar ta ba sai da muka gama tafka kuskure." Asabe da Iyantu suka ce "ai shikenan kashinmu ya bushe babu mu babu wannan tagwamashi da 'yan fim za su samu ta hanyar Nijal." Tukur ya ce :zata yafe mana tana da imani, nima na yi mata rashin mutunci kala-kala wallahi har kunya ta nake ji, nadama nake. Amina ta yi a ajiyar zuciya ya ce "ni ce har da rantsuwa idan ina raye Nihal ba zata zama super star ba a she ma super star ce a turai ba ma a Wudil ba." Aisa kallon Bash kawai take yi ya qurawa Nihal da iyayenta ido ko giftawa baya yi, ta tabbatar ta gama rasa shi don yayi nisa a son Nihal. Bilal kuwa kamar yayi fuffuke ya kamo Nihal saboda tsananin son ya shiga harkarta, shi kula shi ma ko sau daya ne abu ya gagara. Idris ya dubi Abbas ya ce " mu na neman alfarma ka yi mana iso ko Nihal zata yarda ta yi min fim ko guda daya ne. Ashe rabon a wajenka yake nayi-nayi ka bari kada aka saka ta a fim ka qi yarda. Allah Ya sa bata ji labarin yadda na dinga kushe ta ba." Su ka yi dariya su dukka. Nihal ta sa Abbas ya zama shugaba a cikin Daraktoci saboda kowa kamun kafa yake yi da shi akan ya gayyato masa Nihal. Hashim da Najaatu su na ta murna su na kallon kowa daya bayan daya duk me son yin magana da Nihal dole ya biyo ta kansu. Fim ya karbi jamaa su na ta zuwa suna gaisawa suna daukar hotuna da Hashim da Nakaatu abin mamaki babu mai kallon su Aisa sosai. Tsala-tsalan motocin su Nijal ne ke wucewa daya bayan daya sojoji ne a gaba da bayansu suke yi musu rakiya. "Tabbas su Nihal ba dan qaramin kudi gare su ba fa. Masu kudi ne kawai.: In ji Bilal. Tukur ya cusa ashar ya ce "wallahi mun kwafsa da muka bari dama ta wuce mu. Yanzu sai gyaran Allah kawai." Kowa ya tafi da labarin Nihal a bakinsa mamaki ya kasa barin zuciyar kowa. Nihal Nuren ce ta ganta a gida a cikin dakinta tamkar a mafarki sai hawaye yayi ta sirnano mata da ta ga an hada kayanta komai a waje daya kamar wacce ta mutu, komai an kife shi har da hotunanta. Ta bude durowar kayanta ta ga tsala-tsalan kaya na miliyoyin kudi sai ta tuno lokacin da take hada yagaggun kaya tana kullewa. Ta tuna lokacin da Hasiya carkwai da Aisa suka yaga mata riga, su Mami su na yi mata dariya da gori. Ta tuna lokacin da Hashim ya suturta a lokacin da komai ya yayyage ta fada a bayyane ni kuwa da me zan sakawa Hashim da Najaatu a rayuwata su sururta ni a lokacin da maqiya suke so su yi min tsirara. Ta hango wayoyinta da laptops dinta an ajiye su a gefe sai ta dauko ta saka a caji. Da ka jima sai ta kunna. Hohoho jerin gwanon sakonnin ne suke ta shigowana daga turai da na nan gida. Harkar arziki tako ina ake nemanta wasu har sun wuce ta wasu kuma na yanzu ne. Alert ne rututu ke luguden shigowa. Miliyoyin kudin ba zasu qirgu ba, wasu kudin daga yayyanta ne ashe sun ci gaba da bata kudaden da suka saba bata duk qarshen wata. Haka ma Muqaddas ya sha turo mata kudade ya zaci wayarta na hannunta ko Atm card dinta. Kudi me yawa daga Mahaifiyarta. Mahaifinta ne bai tura mata kudi ba dan ya san tsiyar da ya tsula, ya san inda ya kai ta ya zubar ya tafi. Nihal ta san ta yi kudi kudi na kwatance sai ta ci gaba da yiwa Allah godiya ta fara tunanin yadda zata infants rayuwar bayin Allah wato talakawa. Ta dandana yanzu ta san zafin ciwon talauci. Ta ta sami gayyatar wasu Finafinai daga Hollywood tabbas tana shaawar ta je ta yi musu Fim tasan zasu biya ta maqudan kudi sosai ita yanzu ta san darajar kudi. Nollywood ma na nemanta, babbar qawarta Nkechi da suka yi karatu tare ta dawo gida ta bude kamfanin fim dinta ta nemi da Nihal da ta zo ta yi mata fim. Nihal ta kai dare tana bawa kowa amsa sai farin ciki ya kama kowa da aka ji motsinta maimaikon shiru wata da watanni. Ta yi qoqarin dawo da wasu tsofaffin accounts dinta na social media ta goge. Sannan ta bude wasu sabbabi da wannan suna da aka san ta da shi wato Nihal Nuren Mubin. Tun bata bar wajen ba aka dinga adding dinta ana turo mata friend request. Lallai Nihal! Ashe 'yar rigima ce, ta na da waya a boye a jikinta da masu aikinta kadai take waya babu wanda ya san lambarta. Ta kira maau aikinta ta fada musu su rufe gida ba zata dawo ba sai bayan kwana biyu. Wayar wajen Bash kuwa ta bar ta a gidanta har cajin ya qare ta kashe kanta. Bash da Hashim sun kira har sun gaji. An ci saa an ganta a Instagram dan haka duk can suka bi ta su na ta shishshigi, ta hadu da sakonnin Bash da yawa. A wancan account din nata da ta dawo da su na da ta ga Bilal yana yi mata magana, bata amsa masa ba. Ya dawo ya biyo ta sabon account dinta, shima ba ta tanka shi ba. Ta shaidawa iyayenta akwai alqawuran yin fim da ta dauka da yawa dan haka ta na so ta cika ma su alkawura.Sun amince ta je ta yi. Satinta biyu a Lagos ta na fafatawa da inyamurai, su a dole sai dai ta yi abinda suke so ita kuma a dole sai dai ta farke fim din ta sake dan bai yi ma'ana ba, dan ba zata yi abinda zai yaga mutuncinta da na addininta ba. Daga qarshe dole suka bar ta ta yi abinda take so. Sai daga baya suka gane abinda ta ce ayi shine daidai. Kudi me yawa ta samu haka kuma ta samu suna mai yawa da yabo. Ta na dawowa aka fara yin fim din Abbas da ta yi masa alqawari za ta yi masa. Zaa fara yi a kano sai a wuce Kaduna da Abuja. *** *** **** Da yammacin wata asabar Nihal ce ta shigo location cikin tsaleliyar motar ta da ta bawa miliyan goma sha biyu baya. Tun da motar ta tunkaro wajen babu wanda bai yi maganar motar ba sabo da kyawunta. Babu zato babu tsammani motar na tsayawa a gabansu sai ga wata dalliyar budurwa ta fito wato Nihal Nuren Mubin ce. Su kansu producers da Directors ba sa hawa irin ta dan haka kowa ya san ba kudin fim ba ne ya bata. Ta na fitowa sai ta zare baqin gilashin ta dubi kowa tabbas kamar an bi an yado maqiyanta kusan su ne gaba daya wajen. Hashim ya washe baki ya yi dariya ya yi tafi yayi tsalle ya ce "Rangadi. sai aminiyarta wallahi. Yarinya me tashe a fim, mai tashen kudi." Najaatu ce ta taso da sauri ta zo ta tare ta da murna. Nihal ta miqa mata hannu suka gaisa sannan ta qaraso wajen dandazon jamaa. Ta yi sallama ta gaishe su daga dukkan alamu dukka sun amsa har da alakoron fara'a wanda a baya bata samu haka ba. Abin mamaki kujera aka bata da sauri ta zauna sannan Abbas ya fara yi mata bayani. Jigon labarin shine matsalar da take addabarmu ta shaye-shaye da 'yan mata ke yi da samarin har da matan aure ma abin takaici. Shin daga ina matsalar take? Saken iyaye ne ko abokai ko malamai? Talauci ne ko kuwa arziki ne idan yayi yawa yake jawo shaye-shaye?" Nihal ta ce zata fito a mataayin jami'a mai kama 'yan shaye-shaye da ladaftar da su kuma ta yi musu nasiha. Ta ji dadin roll din nan da aka bata. Ba ta yarda an fara shooting ba sai da ta tabbatar babu Bilal a fim din amma akwai Bash kuma daman ta ce lallai-lallai a saka Najaatu da Hashim dinta. Nasir Zakar ne Jarumin fim din shi da Bash. Jigon fim din yayi mata haka, amma ta hango kura-kurai da dama kuma ta na gyarawa. Sun kai dare su na daukar shirin, dan haka ta fara duba a agogo domin a gida za ta kwana. A dole aka tsaya sai kuma gobe. Hashim da Najaatu ta dauka a cikin dandatsetsiyar motar nan ashe ma baa ga komai ba kyau sai an shiga cikin motar. Ga sanyin Ac ga kida mai sanyi daga cikin hadaddiyar speaker radiyo. Kidan buzaye na cikin fim din data yi da busarsu take saurara domin kidan yayi dadi a nutse. Ta kai su Hashim gidanta ta ce su kwana ita a gida zata kwana dan iyayenta ma ba su san ta kama gida ba. Dadi ya kama Hashim da Najaatu su ka ji a wata duniya mai kama da Aljanna. Komai akwai a gabanka Zaa jere maka ga dakuna da garaje na alfarma. Kudi mai yawa na cefane Nihal ta qirgo ta bawa Ngozi. Ta nanata mata ta Kula da bakinta sosai sai gobe zata dawo. Haka ta bawa Baba Balaraba ma kudi mai yawa ko zata aika garinsu. Su ka yi sallama ta fito ta tafi. Tana fita wayar Hashim ce ta dauki ruri bai san lambar ba shima har da irin wulaqancin nan na ya zama celebrity an fara damunsa. Najaatu ta harare shi ta ce " lallai kana daf da daina samun nasara kuwa in har wulaqanci zaka yiwa masu sonka. Ka yi koyi da Nihal mana bata da daga kai kowa na ta ne ko bayan da aka bayyana ko ita wacece. Hashim ya zabura ya masa wayar ce ta sake shigowa. Ya na amsawa kafin ya ce komai sai ya ji wata murya a gigice an ce "Hashim ne ko?" Hashim ya gyada kai ya ce " Eh ni ne Jarumin cikin fim din Gimbya Nihal wato Hashim Ibrahim Wudil. " Ya fada cikin gadara "Nine Jarumi Bilal Sani. Nihal Nuren nake nema." Sai Hashim ya zabura ya miqe tsaye a gigice. Har sai da Najaatu ta razana itama ta miqe da sauri tana tambaya ko lafiya. 11/14/21, 7:20 AM - MY MTN 2: Na kudi ne 馃グ GABA GADI NA JAMILA UMAR TANKO (JUT) Hashim ya gaishe shi cikin murna, babban farin cikinsa yadda yau babban Jarumi irin Bilal ya kira shi. Hashim ya ce "ranka ya dade ba ma tare da Nihal daga location ita gida ta tafi." Bilal ya tambaya "kai yanzu kana ina? Na sami labarin ba ku koma Wudil ba ku na kano." Najaatu wacce ta ke jiyo abinda ake fada sai ta dinga girgiza masa kai alamar kada ya fadi in da suke. Ta rada nasa " mNihal ta ce kada a nuwa kowa gidanta." Hashim ya ce " eh mu na kano amma gidan 'yan uwanmu ne." Bilal ya murmushi ya ce "gani a qofar gidan 'yan uwanku ai, mai gadi ya qi bude min get ya ce bai san ni ba, ka fito ka shigo da ni." Hashim ya hau in-ina da kame-kame. Ya ce "wanne gidan kake magana?" Bilal ya ce " gidan Nihal da ta kama haya a nan no. 1111 Sultan road." Saboda tashin hankali bai san sanda wayar ta katse ba, ya dora hannu a kai. Ya ce " Najaatu na shiga tsaka mai wuya. Me Bilal ya zo yi? Yaya aka yi ya san mu na nan? Ga shi can a qofar gidan nan har ya fadi lambar gidan kuma haka take." Najaatu ta fusata ta ce " ya zo yayi mana me? Dalla ka daina jin tsoronsa, zo mu je qofar gidan." Ta jawo gyalenta a fusace ta yi gaba Hashim na biye da ita a baya. Su na fitowa sai suka ganshi a zaune a cikin mota daf da get. Su ka tsaya a saitin direba, ba sa ganin komai a sanadiyyar ya kulle gilashin wundan kuma baqiqirin ne. Ya zuge gilashin cikin taqama ya dube su sama da qasa ya ce "ku bude min in shiga?" "Ka shiga kamar yaya?" Najaatu ta tambaya cikin fusata. Ya dade ya na dubanta cike da takaici yadda wannan kucakar har ta samu damar fada masa magana. Ya ce " malama ki matsa ba wajenki na zo ba. Hashim bude min get ina da magana da kai amma a nutsu a zaune." Najaatu ta tafa hannu ta murguda baki, ta kama qugu ta ce "abinda ya yi Nihal shi ya yi Hashim kuma shi yayi Najaatu. Dan haka ka fadi komai anan ba sai mun shiga ciki ba. Nihal bata so a san inda take amma sai da aka binciko ta. Tunda aka ce ba ta nan dan me zaa shigar mata gida?" Bilal ya Leqo da kansa ya kalle ta tun daga sama har qasa. Ua ce " haka ne ko 'yar kora ?" Ta harare shi ta ce "fadi ka qara fadi ni 'yar kora ce amma ba ta wani qaton banza ba ta Nihal ce. Ko ba ka ganni a cikin hoton da ku ka dauka ku ka watsawa duniya ba ne? A lokacin da muka ci abincin da muka kasa biya, ai kullum tare muke." "Hashim zagayo ka shigo mota za mu yi magana." In ji Bilal. Najaatu ta tare gaban Hashim ta ce "ba zai shiga motar nan ba fa baqiqirin da ita aje ayi tsafi da shi. Hashim wuce mu tafi gida." A gaba ta sa Hashim su ka wuce cikin get, ta nunawa mai gadi Bilal ta ce kada ya sake ya bude masa get ko ya dawo dan ba mutumin arziki ba ne. Bilal ya dade a zaune a mota ya na jin zafin tsuyuwar da Najaatun qauye ta yi masa. Shi fa a tsarinsa baya yafiya, tabbas sai ya koya mata darasi a gaban nan ba jimawa ba. Dakyar ya iya kunna motar ya ja ya tafi. Ya kwana bai runtsa ba saboda takaici. Da sassafe Hashim ya ji luguden kira Inna ce da tawagarta yau za su zo su yiwa Nihal godiyar gidan da ta siya musu. Hashim ya ce kada su zo Nihal ta ce ta yafe amma ta qi yarda. Ashe ma sanda suka kira shi har sun shiga motar Kano, sai dai daga tasha ba su san yadda zasu yi su zo gidan ba. Da suka iso sai suka kira shi a dole ya katse baccinsa ya fita a cikin adaidaita sahu ya taho da su. Mata biyar ne su da buhun kayan tsarabarsu a daure dadawa ce, kukar kadi, kubewa, fura da man shanu. Hashim an fara wayewa sai ya ji gaba daya warin dadawa suke yi. Ya karbi buhun ya ajiye a bakin qofar shigowa falo ya ce kada su shigar mata falo da kayan wari. Su ka shiga suka zazzauna a qasa. Hashim ya zabura ya ce "ah haba ku zauna a kan kujera ku ji laushi mana, ba ta so inyamurai masu aiki ta su raina baqinta. Kowacce ta saki baki ta na kallon falo dan basu taba ganin irinsa ba. Najaatu ma ta fito su ka gaisa sannan Hashim ya kira Ngozi ya ce ta yiwa baqi abincin karyawa, kakanni Nihal ne. Sai Ngozi ta duqa ta gaishe su, babu abinda yake burge Hashim irin yadda Ngozi ta ke duqawa masa cikin ladabi ta ce yes sir. Sir din nan da take kiransa dadi yake ji. Hashim ya ce " inna ku jira ku ga kayan dadin da zaa hada muku amma fa da wuqa da cokali ake ci baa saka hannu hannu doka ce" "wuqa kuma?" Su dukka su ka hada baki suka tambaya. Najaatu ta ce " ku rabu da shi wai shi dan birni. Ku saka yatsunku guda biyar ku damqo kwai da doya ku kai bakinku." Su ka yi dariya su dukka. "Ina Nihal din ne?" Inna ce ta tambaya. Najaatu ta ce "ta na zuwa , ta na wancan daya gidan na su." Inna ta zabura ta ce "au bayan wannan aljannar duniyar akwai wani gidan kuma?" "Me ku ka gani ma? Ai kyau na wancan gidan." Su inna sai ambato su ke " ikon Allah yarinya marar girman kai." Kayan abinci kala-kala Ngozi ta dinga jerawa akan dining table. Hashim yana yi musu lecture yadda ake hawa da yadda ake ci. Ba a son ransu aka qawaba su akan tebur ba, dan dai Hashim ya yi musu dole ya ce dokar gidan ce gidan sai an hau sama. Nihal Nuren ce ta shigo get din gidanta a cikin luntsumemiyar motarta, yau kuma farar mota ce. Ta cika da mamaki da ta shigo gidan ta ga su Inna sai ta daka tsalle ta rungume Inna su na ta murna su dukka. Da ta juya ta kalli sauran sai ta shaida su 'yan uwan Inna ne na qauye tana zuwa gidansu, acan ma ta koyi ginin randa. Su ma ta gaishe su cike da murna a gigice ya kira Ngozi za ta ce a kawo musu abinci, sai Hashim ya tabbatar mata da cewa sun ci sun qoshi. Sai su Inna suka bude shafikan kukan dadi da godiya da adduoi akan kyautar gida sukutum da ta yi musu. Buhu aka kinkimo a baje kayan tsaraba kan ka ce kwabo warin dadawa ya gauraye falon. Babu yadda Nihal ta iya ta karba tana godiya amma tabbas ta kuaa ta kelayo amai. Ta cewa Najaatu ta karba ta kai bayan kicin dan ta san Ngozi ma bata san wasu irin abinciccikanmu ba. Nihal ta kalli agogo sai Hashim ya ce "Inna mu zamu tafi location ana jiranmu. Ko za ku wuni anan ne da yamma sai a kai ku tasha ku koma gida?" Su ka ce tafiya zasu yi daga nan ma wani qauye zasu je bikin suna. A motar ta Nihal ta dauko su suka fito gaba daya. Ta kai su tasha, shatar mota guda ta dauko musu sannan ta bi kowaccensu da kudi naira dubu goma -goma sababbin 'yan dubu-dubu. Ta basu naira dubu ashirin ta ce su siyo mata kabar da ake saqawa yi tabarma da muhuci, ta ce su hado mata da laka da Fenton da ake yin randa da tulu in sun siyo su turo mata ta tasha gobe, a bada lambar wayar Hashim. Yau Nihal ta sha addua tun tana amsawa har Amin din bakinta ta dauke. A kan hanyarsu ta zuwa location ne Hashim da Najaatu suka bata labarin abinda ya faru jiya tsakaninsu da Bilal.Ta cika da mamaki matuqa yadda ya san in da take ta tabbatar Hashim da Najaatu ba zasu ci amanar ta ba. Babu tantama a baya ya biyo su ko ya sa yaransa suka biyo su a baya aka ga inda suka shiga. Amma koma dai menene ta shirya masa. Sun isa location sun iske kowa ya hallara sai da Nihal ta ga kallon da ake yi ma ta ya yi yawa. Sai daga baya ta tuna da cewa ai irin motar da zo da ita ne. Sai ta ji ba dadi zaa ce fariya ce kiya ta zo da baqa yau ta zo da fara. Wannan motar Mummy ce don ta fito zata tafi ta iske a Usman ya tare ta, an yi ta tashinsa yana bacci bai tashi ba ita kuma zata makara kawai ta dauki ta Mummy. Tabbas kowa zai zaci fariya take yi kullum da sabuwar mota daban. Ta ja ta tsaya a inuwa sannan su ka firfito, yayin da Najaatu da Hashim suka bayyana. Sai kallonsu ake yi duk in da suka dosa sai qamshi me sanyi ne yake tashi ko baka saka turare ba idan ka zauna a cikin motar qamshin 'yan gayu ne yake maqalewa a jikinka. Nihal ce a gaba tana sanye da wani danyen leshi kalar pink an yi yi kwaliyar fulawa da royal blue gown ce mai kyau kuma simple sai ta nade kanta da wani qaramin gyale royal blue. Ta isa wajen mutanen sai ta yi sallama ta gaishe su wasu sun amsa wasu basu amsa ba ashe Aisa da Hasiya carkwai su na wajen su ne basu amsa ba. Ba ta kalle su ba ta isa wajen Abbas aka fara shirya yadda zaayi. Najaatu ce a kusa da su sai suka fara habaici da zagi kai tsaye Nihal suke zagi su na kiran Najaatu da Hashim 'yan kora. Najaatu fa bata shiru bata barin ta kwana bata da tsoro. Daman Nihal ce ke hana ta yau an ci saa Nihal bata kusa dan haka ta cancare musu. Tun ana yi a hankali cikin sirri har na kusa da su suka fara jiyowa, abu yana qara girma har ya fito sannan kowa ma ya ji. Hayaniya ta rikice tun ana yi a zaune har aka miqe tsaye. Nihal da take nesa sai ta juyo luguden ashar, sai ta fahimci da Najaatu ake fadan. Kafin ta qaraso Murtala Dalla ya kai hannu ya dallawa Najaatu mari har sai da ta kai qasa ta kwanta. " Yauwa qarawa shegiya." in ji Hasiya carkwai da Aisa. Hashim ya fusata ya kai hannu zai rama mata Murtala ya daga hannu zai wankawa Hashim mari ta bayansa sai yaji wani wawan mari har guda biyu ta kowanne gefe. Nihal Nuren ce, ranta a bace ta zaro waya ta kira wata lamba. Kalmar farko Major Abubakar ta furta an zo wajen sun san soja ta kira kalamanta yayi kama da kalaman a turo motocin sojoji. "Mun shiga sojoji ne zasu zo wajen nan ai kuwa tattare my zasu yi gaba daya." In ji Danjuma Ado. Mota guda ta ce a kawo sai kowa ya rude. Ta basu cikakken adashin wajen da take. Abbas ya dinga roqonta akan kada a kawo sojoji ta ce ba dan komai ba ne sai dan su sami security, ba zata dinga hulda a cikin maqiya babu security ba. Kowa ya bawa su Murtala rashin gaskiya. Murtala ya rude sai gashi yana tsuma yana ba wa Nihal haquri. Na san wani ne ya aiko ka gara ka fada tun da wuri. Sojoji sun iso sai ta ce tana so a tambaye shi waye ya aiko shi har da zai shiga fadan da babu ruwansa. Kafin ya ji matsa ya fadi gaskiya ya ce Bilal ne ya ce ya ladaftar masa da Najaatu. Haka su Hasiya carkwai ma suka fada Bilal ne ya ce ta yi masa rashin kunya jiya su ladaftar da ita. Nihal ta ce " lallai a nemo Bilal a ja masa kunne l babu duka babu zagi amma a fada masa kada ya kara taka qafarsa kofar gidanta kada ya sake zuwa in da take ma. Aka kira Bilal a waya aka bashi mintuna talatu aka ce ya kawo kansa kafin a kawo shi. Ya ji maganar sojoji sai jiki sa ya dauki rawa kafin ka ce kwabo ya qaraso. Tun daga nesa ya hango Murtala a shanye a rana yana kneel down ya tabbatar yau babu mutunci. Yau dai su Bilal aji ya zube ya na ta bada haquri. Ba dan Nihal ta hana ba da sai yayi tsallen kwado, aka karanto masa karatun Nihal na kada ya sake Shiga harkarsu balle ya taka gidanta sai yayi amanna. Bash ya qaraso ya tarar ana hayaniya a lokacin ya ji labarin abinda Bilal ya aikata sai ya sake jin haushin Bilal . Kowa yana Allah wadarai da wannan abu. Abbas ya sallami Aisa da Hasiya daga fim dinsa aka maye gurbinsu da wasu sabbabin yara masu neman wajen shiga. Bayan sojoji sun tafi a fusace Bilal da su Aisa suka Shiga motarsa ya fita daga farfajiyar a guje ya tayar da qura. 0ho ko ma dai menene dole ka shiga taitayinka. Shooting yayi kyau yayi ma'ana. Da aka tashi daga location Nihal ta kwashi Hashim da Najjatu ta kai su gidanta kamar jiya ta wuce gida. Washe gari da sassafe Hashim ya amsa wayar direba ya ce za su taso daga Wudil ya ce an bashi sako ya zo tasha ya karba su na hanya. Kafin su qaraso ma Hashim ya je tasha yana jiransu su na zuwa ya karba. Nihal ta ji dadin kayan nan sosai dan sun iso a lokacin da take buqata. Hashim da Najaatu dai kansu ya daure sai su ka rasa me zata yi da wadannan kayan, sun tambaya ta qi amsa musu. Ta ce su taya ta zubawa a but din motarta su ka wuce da su location. A sin dinta na yau ne bayan an kama mata 'yan shaye-shaye an kai su wajen hukumar da ta killace su ana kKula su (rehabilitation centre). Nihal ta yi musu nasiha mai shiga jiki sai da koya a wajen ya zubar da hawaye kuka take yi kamar da gaske. Sannan ta fara koya musu sana'oin hannu. Kowa ya cika da mamaki da suka ga ta yi zaman dirshen ta barbaza kaba ta fara dinka tabarma, ta dinka muhuci ta dinka hular maza da zare da allura sai gata tana lailaya qasa tana gina tukunya da tuli har da zancen fentin ta yi kwalliya a bayan tukwanen. An yi kwanaki biyu a wajen koyar sana'ar nan saboda ta burge matuqa. Tun daga nan Abbas ya yi saranda ya gasgata baa taba samun 'yar fim din da take yin komai na ta kamar gaske ba sai Nihal. Ya tabbatar za su sake samun yabo a wannan fim din ma kamar wancan. Bayan kwana biyu aka wuce Kaduna da Abuja aka kammala a sati guda, sannan kowa ya wuce gidansu. Ta tafi da original copy na fim din don ta yi masa editing a nutse da fassarar turanci. Fim ya fito kuma ya sha yabo Nihal ta qara samun masoya abin mamaki kyauttutuka ta dainga samu da tallace-tallace daga manyan kamfanoni irin su mtn, glo, etisalat, maggi, kayan electronic da dai sauransu. Ta yi wa Idris alqawarin zata yi masa fim kuma ta cika masa alqawari maimakon daya ma sai da ta yi masa guda uku domin shima yayi mata halicci a rayuwa. A takaice dai finafinai Hausa guda goma sha biyu ta yi ciki har da guda daya na Bash Auta. Babu fim din data shiga wanda bai yi kasuwa ba, saboda dole ma sai yayi ma'ana. Kasuwar Nihal ta bude a kudancin qasar nan ma, tun da ta yi fim sau daya sai kowa ya yi kanta, sun yi mamakin yadda bahaushi take turanci mai kyau haka da yadda take acting ya burge su sosai. Dakyar ta samu ta gudu bayan da ta yi musu Finafinai guda tara. Ta shiga Amerka ta yi fim da manyan jaruman duniya, haka ta yi wasu Finafinai a kamfaninsu John da Williams wadanda suka fara sakata a fim din farko. Nihal ta yi Fim da indiyawa. Sunan Nihal ya cika duniya dan haka bata sha'awar ta sake yin fim sai dai ta taimaki al'ummarta kuma. Ashe ta gina katafaren industry mai suna N.N Mubin Movies ciki har da makarantar koyar da makamar aikin fim. Akwai bangaren masu koyar daukar hoto da sauti, da masu koyon kwalliya irin ta fim da masu koyon acting , da bangaren koyar da editing. Ta dauki masana malamai daga kudu da kuma turai. 'Yan fim kadai take dauka domin su take so ta ingantawa sana'a dan ta ga kurakurai da rashin wayewar ta yi yawa. A sanadiyyar rashin fita su nemo ilimin da za su inganta sana'armu ne. Kafin ka fara shiga aji sai dole an yi maka lecture sai ka san menene ma shi kansa fim din? Meye asalin samuwar shi kansa fim din? Sannan idan kika tsinci kanki a matsayin 'yar fim me ya kamata ki yi ki kare darajarki da kimarki, da ta danginki da kuma kacokan addininki. Tabbas ta na jin haushin zagin da ake yiwa mata 'yan fim ace musu karuwai, ace masu shaye-shaye, masu bleaching. Tabbas wasu abubuwan an yi amma wasu baa yi ba ma ake qagowa ace an yi. Su waye su ke bada qofar da ake zaginsu? Amsar ita ce su suke bada qofa a zage su. Wasunsu ba sa kama kansu. Nihal ta tantance duk wata matsala da take addabar duniyar fim, ta nemo mafita tsaf. Ta kan Hashim da Naja'atu ta fara, sai da ta samo musu malamai ana koyar da su har na tsawon watanni shida ana koya musu turanci. Sannan ta biya musu suka tafi turai suka yi wasu kwasa-kwasai na share fagen akan koyan aiki. Iyayen Najaatu sun amince da Najaatu ta je sun yarda da kamun kanta kuma sun yi mata addua. Najaatu ta canja rayuwar kowa a danginta sun fita da ga tsantsar talauci. Su Hashim an je London an dawo sai suka shiga wannan kwaleji ta Nihald, su ka fara karatun acting din fim. Mata da maza suka dinga tururuwar cike form neman admission a wannan makaranta amma sai dai kash akwai adadin mutanen da za ta dauka duk shekara dole wasu su jira wasu su gama. Ta bangaren koyon aikin directing ma akwai kwararrun masu koya musu. Ta kan Abbas da Idris ta fara, yadda tsarin yake duk shekara daraktoci guda biyar kacal za ta dinga yayewa dan haka dubbunan masu neman admission dole su saurara. Tukur ma ya nema bai samu ba amma abokinsa Darakta Aliyu ya samu dan haka Tukur ya sha jinin jikinsa ya fara girba zunuban da ya tafka. Bash Auta ya na daga sahaun gaba-gaba da aka fara dauka, a bangaren koyon aikin directing. Ya ce mata Idan ya gama zai koyi acting ma da editing. Ta yi amanna da shi saboda bata manta alkhairi ta daraja wadanda su ka qaunace ta a cikin tsumma. Duk wannan abu da ake yi babu ko sisinsu komai kyauta ne Nihal ta dauki nauyin. Ko ina maganar taimakon da take yi ake ta yi a fadin arewacin qasar nan, har ma da ma kudu, su na fatan ta zo ta musu wannan tagomashi su ma. Maqiyan Nihal sun kasa qarasowa su zo su tare ta su ce su na so. Gashi su na da buqatar Shiga amma kunya, tsoro da nauyin ta suke ji. Ta na sane da su ta yi kamar bata san su na yi ba. *** *** *** Ambassador Abba Muse ya fito takarar gwamnan jihar Kano. Gabansa zakuna, baya kuraye, qasansa kada , samansa damusa ce an saka shi a tsakiya ta ko ina so ake a murqushe shi. 'Yan adawa fa sun hade kai sai sun kayar da shi sun fara siye masoyasa da kudi. Kowa ya tsorata har an fara fitar da rai, gashi zabe ya kusa an rusa dukka kanfen din da ya dade ya na yi na shekara da shekaru. Abba Muse ya hada zufa a falonsa ya dubi 'yan jam'iyyarsa ya ce "an kusa cinmu da yaqi fa. Menene shawararku?" Wasu su ce a saki kudi, wasu su ce a bazama kanfen, wasu su ce a je a ga shugaba qasa. Isa lawan ya ce "mafita daya ce ka je ka sami General Nuren ya ba mu aron 'yarsa Nihal ita kadai wacce talakawa suka sonta suke gane yaronta. Ko ina fostar ce a qasar Hausa har ma da kudu." Nan da nan kowa ya gasgata hakan. Abba ya yi shiru yana tunani can ya ce "Muqaddas da Siyama fa sun dade su na bani wannan shawarar, na zaci dan su na neman shiri da ita ne ya sa suka ce haka. Yanzu 'yar Hausa fim sai ta yi min sanadin cin zabe kuma ta fitar da ni daga wannan gagarumin hargitsin?" Su ka kunna masa fim din Nihal a waya, ya gani suka kunna masa yadda ake dandazon zuwa duk taron da ta shirya na wayar da kai ko na sallah, Har a wasu qarshen ma irin su Nijer Cameroon da Ghana da Lagos. Su ka nuna masa yadda ake ji da ita a amerika har da excot take yawo. " Ta yaya zan tari mahaifinta General in ce Nihal ta zo ta taimake ni bayan saboda fim din na raba auren 'yayansa da 'yayana?" In ji Abba. Qungiya guda aka yi aka je aka sami Geneeal da wannan bukata ta Ambassador Abba. Lallai an zo wajen a lokacin allurar General ta tashi ya goga rashin mutunci ya bada da saqo masu zafi ya ce a kaiwa Abba. Nihal 'yar Hausa fim ce ba zata iya taimakon gwamna ba. Washe gari Genaeral ya ce Nihal ta tashi ta tafi London, ya yankar mata ticket kada ta dawo sai an gama zabe. Kanta ya daure ta kasa gane abinda yake faruwa. Tana da abubuwan da zata koyar a makarantarta amma dole ta bari ta tafi. Abba ya shiga damuwa shi da iyalinsa ne suka dungumo suka zo sai wajen General sai suka iske da gaske ya dauke Nihal ya sa ta bar qasar ma. Babu riqon da basu yi masa ba amma ya qeqasa qasa ya ce ba dai 'yarsa Nihal ba. Wasu daga cikin yaransa irin su Muhammad sun bi bayan mahaifansu yadda Ambassador ya kama hannun 'yayansa ya fice ya ce ba zasu hada zuria da 'yan Hausa fim ba. Dan haka a yanzu ma 'yan hausa fi ba zasu shiga harkar siyayarsa ba. Nuren ya ce "ka kama hannun 'yayanka, matarka ta bi ku a baya ga qofar fita can. Haka aka yi kuwa suka fice fusace. Abubakar ne ya damu saboda kada a kwabe gaba daya ya rasa Siyama ga Muqaddas abokinsa. Major da Miqaddas a boye suka shirya su ka tafi london wajen Nihal sai a lokacin ne ma ta san abinda yake faruwawa Suka dinga shirya shawarwarin yadda zaa shagon kan mahaifinta ya yarda ta yi. Dan sun san ba zata taba yin abinda Daddy bai bata umarni ba. Sun so su dawo da ita Nigeria sai ta zauna a wani babban hotel a ci gaba da magana da Daddy ba tare da ya san tana qasar ba yana amimcewa sai kawai ta fara kamfen. Nihal bata yarda da shawararki ba saboda ta san halinsa zai gane. Su ka taho suka bar ta amma ta yi musu alqawari zata shawo kansa. Ta fara yi masa nasiha a waya "Daddy baa saka tsiya da tsiya kai ka saka masa da alkhairi mana. Abokinka ne, ka yi masa uzuri ka tuna halacci da ka dinga fada yayi maka a lokacin yana Ambassador. Ya hadaka da shugaban qasa an qara maka girma a lokacin ana mulkin soja har sunanka ya bayar aka zabe ka aka nada ka gwamnan Lagos. Jaba Daddy mu na yiwa Allah laifi ma ya yafe mana ka bari in yi masa kamfen in ya so ba sai mun auri 'yayansa ba." Yadda maganarta take shiga haka take fita bai Amince ba. Washegari irin wannan nasiha ta yi masa amma a banza. Sannu a hankali dai ya fara saukuwa, ya yarda ta yi masa kanfen amma ta social media ba ta zahiri ba. Ta ji dadi da hakan ma, ta na fara yi sai ga dandazon comments da likes. "Nihal kema kina yin Abba Muse daman saboda ke mu ma zamu yi shi kuwa." In ji masoyanta. Hashim da ya ga haka sai ya buga hoton Nihal a gefe na Abba Muse ne ya dinga liqawa a ciki da wajen Wudil yana cewa "ku zabi Muse mahaifin Nihal ne." Nihal ta ji labari sai ta bawa Hashim da Najaatu kudi masu yawa suka ci gaba. Sun daukar mata da maza dauke da fastoci aka shiga gari yin kamfen. Zabe ya rage watan biyu Abba Muse ne a waya yana magana da Nihal da alama ma hawaye yake zubarwa. Yana cewa "Surukata ki taimake ni duk wanda zai bani shawara sai ya ce in neme ki, ke ce kadai za ki iya ki taimaka min. Na san halin mahaifinki shine ya hana ki amma ki roke shi ya na sonki ke ce kadai mace yarsa. Zan iya tunawa ya taba fadamin wata magana a lokacin kina yarinya. Ya ce duk duniya babu abinda na fi so irin Nihal gata bata da lafiya babu abinda na qi jini a rayuwarta in ganta a kwance. Ciwonki ya na tayar masa hankali. Kin yi wani ciwo da kike suma. Sai da aka yi miki aiki kika warke. Ina so ki nuna masa bacin rai ya sa ciwonki ya tashi kin suma sai a asibiti kika tsinci kanki. Dan haka ya bari ki dawo gida ki yi min kamfen." Nihal ta sake shiga tsaka mai wuya. Ta yaya zata tayarwa da mahaifinta hankali haka? Ta kira mahaifiyarta ta fada mata yadda suka yi da Ambassador abin mamaki sai ta ji Mummy ta yi amanna. Saboda wannan shawara ita ce kadai mafita. Idan ya ji damuwa ta tayar da ciwo zai saduda dole ya bari. 11/14/21, 7:20 AM - MY MTN 2: Na kudi ne 鉂� GABA GADI NA JAMILA UMAR TANKO (JUT) General da abin qaunarsa Shatu ne ke zaune a falo su na kallon labaran qarfe tara, su na yi su na shan kayan marmari inibi da tofa. Da alama yau General yana cikin nishadi sai hira yake yana zolayarta. Shatu ce farin cikinsa ita kadai take gani yaji sanyi daga ita sai 'yayanta. Major Abubakar ne ya shigo ya gaishe su sai ya fita ya sake shigowa ya fita,ya dawo zai sake fita alamu sun nuna yana cikin damuwa. Prof Shatu ta tambaye shi "Abubakar lafiya kuwa? Wani abu ne ya faru?" General ya ci gaba da kallon talabijin dinsa, ya nuna halin ko in kula daman haka take yi musu. Abubakar ya zo ya zauna a sanyaye ya daga ido da kyar ya kalli mahaifansa ya ce " mummy ba na so in katse muku nishadinku in tayar muku da hankali ne amma ya zama dole in fada muku. Nihal ce ba lafiya tana asibiti ta shide ta sume, likita ya ce damuwar da ta shiga a cikin kwanaki nan ce ta jawo...." Remote din da ke hannun General ce ta fadi qasa dan gigita. Ya zabura ya dubi Abubakar ya fada cikin tsawa " Nihal din ta wa? Wacce damuwa ce kuma?" Abubakar ya jawo wayarsa ya kira lambar waya, baturiya ta dauka wato likita mai da kula da Nihal. Ya saka ta a speaker kowa ya na iya jiyo bayananta. Ta ce sun binciko file din Nihal sun ga tarihin ciwon nan na ta ashe tun tana qarama ta warke bai sake tashi ba sai wannan lokaci, ya kamata a daina takura mata akan wasu abubuwa damuwa da fargaba na damunta. General ya fisgi wayar ya fara magana cikin gigita "Ina Nihal din? Ta farfido ko tana sume? A bani ita mu yi magana." Nihal ce ta karbi waya tana magana cikin galabaita. Ya tambaya "meye danuwarki? Ki fada min ko meye shi zan yi miki." Ta fara kuka sai ya tashi ya tafi can nesa da su yana lallashinta ya na tambaya. Dakyar dai ta ce ba ta da wata damuwa illa ta abubuwan da suke faruwa a kwanan nan, maganar kamfen din Ambassador. Ta shiga tsaka mai wuya tana jin kunya Siyama da Muqaddas za su ga kamar ba ta kyauta ba." Sai ya ji sanyi a ransa da ba wata damuwa ba ce mai yawa. Ya yi tsaki ya ce "wannan ce kadai damuwarki, har kike qoqarin jefa kanki a cikin matsala? Na amince ki dawo gida ki yi masa kamfen. Amma ki bari ki sake jin sauqi nan da sati daya." Murna ta rufe Nihal ya ce ta bawa likita waya ya na magiya akan ta tsaya ta kula da Nijal ita kadai ce 'yarsa mace a duniya. Ya na sonta matuqa. Likita ta yi masa alqawari za ta yi masa hakan. Yayi godiya suka kashe waya. Nijal da ketrine suka yi tsalle suka rungume juna daman ba wata likita ba ce, qawarta ce suka hada baki. General ya dawo wajen da su Abubakar suke zaune ya na fada " akan wani dan qaramin abu shirmen banza zata kashe kanta. Wai damuwarta akan bata yiwa Ambassador kamfen ba ne tana jin kunya su Siyama. ji shirme fa." Su ka dauki salati kamar da gaske nan kuwa su dukka hudun bakinsu daya. "Yanzu yaya zaa yi? Shatu ta tambaya. General ya ce " na bar ta ta zo ta yi in dai dan kamfen ne." Abubakar ya dauki bambamin fadan qarya " ai da ma baka bar ta ba ta je ta kashe kan nata. Meye hadinta da su?" " ka ji shashasha a bar ta ta mutu dan kai ba asararka ba ce? Ciwon nan da ya kusa kashe ta tun tana yarinya shine yake so ya dawo." Inji General ya fada a fusace har da kaiwa Abubakar duka da bayan hannu. Abubakar ya fita da fushi wai shi a dole bai so aka amince ba, nan kuwa dariya ce a kunshe a bakinsa. Shatu ma da kyar ta daure dariya ce ta ke cinta. Zufa kawai General ke yi tabbas ya gigice. Ya jawo wayarsa ya kira Ambassador Abba bayan sun gaisa ya yi masa albishir da cewa Nihal zata yi masa Kamfen. Sai murna ya ke yana godiya. Babu tantama ya san abinda ya shirya mata ne ta bi, ba dan haka ba ya tabbatar in duniya zata hade General ba zai taba amincewa ba, don akwai shi da taurin kai da taurin zuciya. Su na kashe waya ya kira 'yayansa su Muqaddas ya shaida musu, sai aka hau murna. Wayar Muqaddas ce ta shigo wayar Nihal amma number busy dan su na ta waya da Abubakar su na ta tuntsira dariya. Sai bayan da ta gama da Abubakar ne ta kira Muqaddas ya na so ya ji kanun labarai shima. Ta shirya tsaf nan da kwanaki biyu zata iso, kafin kwanaki biyun nan ta shirya komai ita da masu taya ta 'yan uwanta 'yan fim. Ta cika da mamaki duk lokacin da ta dora sabon hoton Gwamna Muse sai ta ga Billal ya yi reposting yayi sharing shima kamfen yake taya ta tun qarfi. Ita kuma sai ta danna masa likes ta yi comment da Thanx. A hakan ma dadi yake ji ya samu ta Kula shi har ta san abinda yake yi. Nihal Nuren ta iso da qarfinta da kuma kayan aikinta wato kudi. An bazama babu dare babu rana, wataran tare da Ambassador da tawagarsa wataran ita da 'yan fim kadai. Sun shiga lungu-lungu, kusurwa-kusurwa ta cikin kauyuka da burane su na ta kamfen. Hankalin 'yan adawa ya tashi tabbas Muse ya biyo ta hannun da zai ci nasara tunda ya hada da su Nihal. Farin jinin 'yan fim shine gaba da kowa saboda hotunansu da bidiyoyin shirye-shiryensu ya kai kowanne lungu so ake kawai a gansu a zahiri kuma kome suka ce zaa yi amfani da shi. Da maqudan kudi su ka so su siye Nihal akan ta juya akalar kamfen din dinta daga kan Muse ta dawo kan dan adawarsa. Tabbas kudin ya na da dinbun yawa in har za ta karba to fa sai dai a saka ta a sahun masu kudin afrika. Allah sarki Nihal ta kau da kai babu ma maganar cewa a bata lokaci ta yi tunani gaba gadi ta ce bata so. Ranar zabe babu ko kokonto kowa Muse ya dangwalawa. Masha Allah Muqaddas da Siyama sun zama 'yayan Gwamna. Muse ya ci zabe. Gari gaba daya ya dinke da murna sai celebration ake yi. 'Yan fim sun fi kowa murna saboda alqawuran da yayi musu in har ya zama gwamna zai tu musu. Saboda ya sun 'yan fim sun yi masa karamci su ma. Ya yi musu alqawarin zai inganta sana'arsu da masana'antarsu. Zai gina musu Fim village wato gari guda zaa dauka a yi fasalin komai kamar na gaske, idan aka yi fim sai a dauka turai ne. Yayi alqawari zai mayar da makarantar Nihal jamiar mai lasisi. Zaa dinga fita da shaidar digiri kamar na kowacce jami'a. Zaa bawa manyan producers da Directors jari na yadda zasu samu su inganta sana'oinsu. Nihal kuwa zai duba Muqami mai girma a gwamnati a bata daga kwamishinan mata zuwa sama. Madalla da wannan gwamnati. Fatan Nihal kawai a taimaki talakawa musamman na qauye tana da littafi guda data rubuta jerin matsalolin da suke addabar suda idanuwanta ta gani ba labari aka bata ba. *** **** *** Bayan zabe kowa ya sami nutsuwa an gama baccin gajiya. Nihal ta sami labarin Aisa Buzuwa ta haukace a sanadiyyar shaye-shaye ba komai ba ne saboda Bash ya qi aurenta. Hankalin Nihal ya tashi matuqa ta nemi adireshin da zata iya samunta. Bash Auta ya cika da mamaki da ya ga kiran Nihal da sassafe. Ya na amsawa ta ce " ka fito qofar gida gani a bakin get din gidanku." "Qofar gidanmu kuma?" Bash ya tambaya cike da mamaki. Ya fito a gigice ya na adduar Allah Ya sa lafiya. Ta yi masa nuni da hannu alamar ya shigo cikin mota ya na shigowa ya zauna baki a bude yana so ya fara tambaya sai ya ga ta fisgi mota ta tafi da shi. Gabansa ya fadi a zatonsa ko wajen sojoji zata kai shi a casa shi a dalilin ya ce yana sonta, ko kuma wasu ne suka hada su aka yi masa sharri. Magiya yake yi mata ta tsaya ta yi masa bayanin abinda yake faruwa bata ce masa komai ba har yanzu. Hankalinsa bai kwanta ba sai da ya ga ta tsaya a qofar wani gida kuma ya san gidan. Yanzu ya gane maganar dai akan Aisa ce. Ya yi tsaki ya girgiza kai ya ce " ban da ke babu wanda zai yi min haka in kyale shi. Meye hadina da Aisa yanzu? Daman can fim ne ya hada mu kuma take haukarta." Nihal ta ce "na sani amma tana buqatar taimakonka. Bash daga yau ina so ka saka a ranka kada ka yi wasa da zuciyar duk wanda ya furta kuma ya nuna yana sonka domin kuwa ba ka san iya gejin da ya kai a qaunarka ba. Za ta iya rasa rayuwarta a dalilin sonka kai kuma ka dauki abin da wasa. Haka kada ka dauki qiyayyar wanda ya ce yana qinka da wasa dan baka san zurfin qiyayyar da yake yi maka ba wataran zai iya halaka ka. Mu je ciki wajenta kawai." Nihal na gaba yana biye da ita a baya a zauren gidan su ka ganta a zaune ta na shan wiwi bayan ta gama da kwalaben kayan maye. "Wa'iyazu billah. Aisa me nake gani? Ki yi haquri ki ajiye ki daina wannan ba ita ce mafitar matsalarki ba. Ga ni ga Bash mun zo wajenki ne don mu yi magana." " Dalla can munafuka ba ke ki ka raba ni da Bash din ba. Yar rainin wayo kawai wallahi sai na kashe ki na kashe Bashir Auta sannan in kashe kai na." Cikin muryar 'yan maye Aisa ta fada. " Subhanallah mai yayi zafi haka? Na zo a sulhunta ne, tashi mu shiga ciki mu yi magana." In ji Nihal yayin da ta kama hannun Aisa zata tashe ta a tsaye. Hasiya carkwai ce ta danno da gudu da tabarya hannunta, ashe har gara haukar Aisa ma sau dubu. Hasiya tunbele take jikinta babu suturar kirki ta kusa yin tsirara. Tabarya ta daga ta kai bugu saura kadan ta sami Nihal a goshi, Nihal ta daka tsalle ita da Bash suka yi waje da gudu. Manyan asaharai Hasiya carkwai ke yi a cikin bayaninta sun take cewa sun yiwa Nihal asiri ne ya dawo kansu. Hankalin Nihal ya yi mummunan tashi daman har qiyayyar da suke yi mata ta kai haka abin har da bokaye? Ta yi mamaki ta yi Allah wadai da wannan halin na su, ba ta taba kawowa a ranta cewar har akwai ranar da kunnuwanta zasu ji irin wadannan kalamau ba amma duk da haka ta sha alwashin sai ta taimake su. Ita da Bash ne a zaune a mota bayan sun yi nisa da gidan Hasiya sai dai su na hango ta daga nesa, ta fito tana jifansu da duwatsu tana tonawa kanta asiri. Waje ya cika da mutane masu wayoyin hannu har sun dauka sun watsa a duniyar social media. An rubuta Aisa da Hasiya carkwai sun haukace a sandiyyar zasu yiwa Nihal asiri ya koma kansu. Nihal ta matse hawaye ta dubi Bash ta ce " sai yaushe zamu ci gaba ne a qasar nan ? Sai yaushe za mu waye? Sai yaushe za mu san da cewa mun shiga sabon cetuary? Wannan abubuwan da suke yi fa tun a zamanin jahiliyya aka yi su. Asiri ba zai kama ni ba tunda ina yin Azkar safe da yamma kuma ban taba cutar wani ba. Me yasa 'yan fim wasu ba sa qaunar junasu? Daukaka ta Allah ce. Me yasa ba zasu saka a ransu cewar kowa iya rabonsa zai ci ya tafi? Da baa matsawa a bawa wasu fili su zasu zo su yi na su tashen ne? Wannan ita ce babbar matsalar 'yan fim. Da gaske dole a zage mu a duniya, kwata kwata wannan ba tarbiyya mai kyau ba ce." Bash ya gyada kai ya ce " tabbas maganarki gaskiya ce gara da kika zo da kanki ki ka gani. Ko na yunkuro zan kula Aisa sai in ga wani mummunan hali a gare ta. Na taba kamata ta na cewa idan ta aure ni sai ta gyarawa ummata zama dan ta fuskanci bini-bini sai ta kira ni a waya ta ce in dawo gida kamar wani yato qarami. Kin ga kenan bukaye za ta bi ta halakar da ni in guji uwata. Nihal ina neman alfarma kada ki tilasta min ki ce sai na auri Aisa na san manufarki. Ni ke nake so kuma ina addua ki amince ki aure ni." Ta zura masa ido tana kallo ta na tunani mai nauyin gaske. Ko me take tunawa? oho. Ta tayar da mota suka tafi, a qofar gidansu ta ajiye shi ba tare da ta sake cewa komai ba, ya fita ita kuma ta qara gaba. Tabbas ta bar shi a cikin dimuwa da fargaba. Maganarsa ba ta da amsa kenan. Nihal ce ta saka ma'aikata suka zo da mota daga asibitin mahaukata aka dauki Aisa da Hasiya carkwai da qarfin tsiya a kai su asibitin mahaukata. Bayan Nihal ta gana da dangin kowaccensu. Ta tabbatar musu bayan maganin asibiti ma su na buqatar addu'oi na warware tsubbace-tsubbace dan shi suka yi ya koma kansu. Ta ji dadi da Allah Ya sa dukka danginsu sun san komai. Ta ba su kudi mai yawa ta ce su tara malamai a taya su da addua. Sun yi mamaki yadda aka yi wacce suka yi niyyar su cutar Allah ya tsare ta yanzu ita take nemo musu hanyar waraka. Sun yiwa Nihal addua da fatan Allah Ya saka ma ta da gidan aljanna tabbas ita 'yar halal ce. Labari ya cika kafafen sadarwa da jaridu da gidajen radiyo cewa Aisa da Hasiya carkwai sun haukace a sanadiyyar su haukarta da Nihal ya koma kansu. Nihal ta dauki nauyin kaisu asibitin mahaukata da kuma biyan malamai su tayi musu addua. Duk yadda 'yan jarida su ka so jin ta bakin Nihal abu ya ci tura ta qi yin magana har da Mu'awiyya yayanta ta qi ta amsa masa. Amma Bash ya tabbatar musu da gaskiyar faruwar wannan al'amari. Sai kowa ya ji Nihal ta sake burge shi,wadanda ma basa sonta a da yanzu sun ji su na sonta haka wadanda ke sonta sun sake sonta. *** **** *** Fim din labarin rayuwar Nihal a duniyar fim mai suna ' A wata duniyar' ya fito kasuwa. Sabuwar Jaruma Fatima Maikudi ce ta fito a matsayin Nihal, Atika a matsayin Najaatu, Tanimu a matsayin Hashim. An sami wadanda suka fito a matsayin su Tukur da su Mami harka. Babu abinda labarin ya rage duk abinda ya faru da ita daga farkon shigarta fim har zuwa yadda take yanzu ta rubuta.Hatta qasar London sai da ta kai Fatima maikuudi aka nuna John da Williams a farkon fim din kenan. Wadanda ba su sani ba yanzu sun san abubuwan da aka yi mata da wahalar da ta sha. An yi kuka a fim din dan tausayi. Sunayen kawai ta canja da kuma sunayen garuruwa. Su Tukur an ji kunya haka ma su Mami harka. A qarshen fim din an nuna sun yi nadama sun sami qarshe mai kyau Fatima Maikudi ta saka musu da alkhairi. An kalli fim din sosai kuma an tabbatar musu labarin gaskiya ne daga baya aka gane labarin ita kanta Producer kuma Director fim din ne wato Nihal. Bayan nan an yi hira da Nihal ta tabbatar da duniya cewa Hashim da Najaatu su ne kadai suka taimake ta sai daga baya Bash, Idris da Abbas sun taimake ta. An sake jin qaunar Hashim da Najaatu a duniyar 'yan kallo kuma ana son kallon finafinansu a yanzu dau babu masu tashe a wannan zamanin irin Hashim da Najaatu. Sun waye sun goge fiye da Bash auta da Bilal da Aisa da Halima Jabir. Motocinsu na farko Nihal ce ta siya musu kafin daga baya suka sake siya da kudadensu. Najaatu ta na yawan zuwa garinsu Darazo, ta bude wajen koyawa mata sana'oin hannu da fadakar da su. Ma su buqatar shiga fim ta hanya mai tsafta da yardar iyayensu take kawo su bayan sun sami horo a makarantar Nihal. Waqa da rawa a fim ya zama sai jifa jifa domin da yawa su na kwaikwayon tsarin Nihal. An sami yawaitar masu rubutun script sosai an yaye su daga makarantar Nihal dan haka an sami labarai masu ma'ana a finafinai haka a wajen editing an sami ci gaba. Nihal ta saye wannan gidan da ta kama haya har da maqwabtansu ma ta mayar da gidan wajen sauke baqi 'yan fim ko wadanda suka zo daga wasu garuwan yin karatu Daya gidan mata daya na maza. Nihal ce da Bash a zaune cikin wani katafaren lambu da yake cikin gidajenta. Ta kalle shi ta ce " ka sha yi min tambayoyi game da aurena da kake so ka yi sorry ba wulaqanci ba ne na kan rasa amsar da zan baka ne. Ina da jin nauyin mai kaunata kuma ina daraja shi, ina girmama shi. Bash na yarda da salon yadda kake sona na yarda ka na sona saboda Allah. Ba dan abinda nake da shi ba ko dan nasaba ta ba. Ka kaunace ni lokacin da ni ba kowa ba ce kuma bani da komai. Ka tsaya min a lokacin da kowa yake kyara ta yana kora ta. Ka hadu da ni a lokacin ina da baikon Muqaddas a kaina." Bash ya zabura ya gwale idanuwa yana fargabar jin sauran kalaman da zasu biyo baya. Nihal ta ci gaba da cewa "kamar yadda ka gani a fim dina a labarin rayuwa ta saura watanni uku bikina mahaifina ya yanke wannan hukuncin kuma aka bata alakata da Muqaddas. Bai daina sona ba ban daina sonsa ba. Amma kalmar da mahaifinsa ya fada ta cewa 'yayansa ba zasu auri 'yar fim ba ita ta tsaya min a rai ina ganin ko sun dawo da maganar aure ba zan amince ba kuma na San mahaifina da wuya ya amince shima, gaskiya zai yi wuya aya amince dan na san halinsa. Idan ba Muqaddas na aura ba tabbas Bash Auta zan aura duk duniya ba ni da kamar ka." Bash ya ji sanyi ya ji dadin da bai taba ji ba. Ya sha ganin alamar kamar Nihal tana sonsa bata so ya gane ne. Yau wannan hira ta burge shi matuka sai ya washe baki yana magana cikin marainiyar murya. Fata yake yana addua Muqaddas ya hakura ya bar masa. Bilal ne ya dira a gabansu ya yi sallama ya ja kujera ya zauna aka hau kallon-kallo. Ya miqawa Nihal da Bash katin daurin aurensa ne shi da Halima Jabir. Su ka karanta sai Nihal ta dago ta dube shi cike da farin ciki ta ce " amma fa na ji dadin wannan al'amari haka ya kamata 'yan fim su dinga auren junansu sai a daina raina sana'arsu ana tsine musu." Bash ya miqawa Bulal hannu su ka gaisa ya ce "congratulations abokina ka ci saa, nima ka yi min addua nawa burin ya cika." Bilal ya yi dariya ya dubi Nihal ya ce " ina yi muku fatan alkhairi a duba maganar abokina Bash kuma a kanku ku manya ya kamata a nuna misali kamar yadda na burge ki dan zan auri 'yar fim ya kamata ki burge kowa ki auri dan fim." Su ka kwashe da dariya su dukka. Nihal na shiga farfajiyar gidansu sai ta iske taron motoci maza ne damqar da ta tambaya sai aka shaida mata cewar kudin aurenta aka kawo daga gidan su Muqaddas basu fada mata ba ne dan ana so a yi mata bazata. Muqaddas ne ya ce a boye mata. Wannan karon gabanta ne ya yanke ya fadi ba kowa ya fado mata a rai ba sai Bash, dazunnan su ka gama maganar nan. Ta san ya na sonta da yawa zai shiga damuwa mai yawa. Ta shiga yi masa adduar samun dangana da canji mace ta gari. Bayan kwana biyu kuma aka kai kudin auren Abubakar gidan su Siyama. Tuwon girma miyar nama bigi sai bigi komai mai yawa aka kai. Kudin aure da kayan sa rana. Bash ya gigice a lokacin da ya sami wannan labari yayi ta kuka Nihal ma kuka take ba tare da ta san abinda za ta ce masa ba, daman can ba ta boye masa ba. Hashim da Najaatu ne ke lallashinsu. Su ma basu ankara ba suka ji sun fara zubar da hawaye. An dade a cikin wannan hali kowa ya kasa lallashin kowa. Nihal ta goge hawaye ta dago ta dubi Bash ta ce " ina so ka auri Najaatu. " Wannan kalma ta firgita dukkansu a wajen.Bash bai ce komai ba ya tashi a da sauri yana share hawaye ya shiga motarsa ya tafi. Najaatu ta dora hannu aka ta ce " shikenan Nihal kin kashe ni, gaisawar da mu ke yi da Bash mun daina." Nihal ta yi dariya ta ce "ki bari ya je ya huce ya dawo zai amsa min ni na sani. Amma ka da ki dauka ban gane kina sonsa ba." Sai Najaatu ta yi wuqi-wuqi da ido Hashim ya hau dariya domin ya san komai. Najaatu ta sha fada musu cewar tana so ta yi fim da Bash ko sau daya ne a rayuwarta a hada su a matsayin mata da miji. Me wannan yake nunawa kenan? Nan dai ta hau musawa su na qwale ta. An dauki watanni sannan aka fara ganin Najaatu da Bash a wasu wurare su na hira hakan ya nuna an fara kulluwa. Najaatu ta waye tana da kyau ashe rashin gyara ne ada fara ce sol ga dogon hanci ga idanuwa gazargazar. Ga ilimi ga gayu ga ta 'yar soyayya. Duk sai yanzu Bash ya lura da hakan a rashin Nihal. Bash ya ziyarci garinsu su Najaatu ya gaisa da iyayenta. 'Yan Darazo sun ga Bash Auta, gari ya dauka ana ta dandazon zuwa ganinsa. Hashim kuwa sun dinke da sabuwar yarinyar nan mai tashe Fatima maikudi tana matuqar qaunarsa kuma har an je gaisuwa a gidansu bayan da aminiyarsa Nihal ta yi amanna da ita. Nihal ce ta cika masa kudi ya sayi katafaren gida a unguwar sharada ana zai tare bayan biki. Bash daman dan gidan masu kudi ne ba laifi gida guda qato a cikin Nassarawa GRA mahaifinsa ya gina masa anan zaa kawo 'yar Darazo. Yayin da Amina 'yar kwalisa ta auri mai trader a Wudil, Mami ta auri mai gurasa da nama a bakin tashar Wudil, Asabe ta auri mai siyar da takalma a qauyen Wudil, Iyantu ta auri Tukur Darakta su na can su na dambe da Sadiya matarsa dambe har qofar gida ake fitowa. Fim yayi gardama an hakura da shi babu kudin babu sunan. Dan inda ake samu a soka su ma kowa ya daina.Rayuwa kenan duk abinda ka shuka shi za ka girba. An sha biki a layi-layi in an gama wannan sai a shiga na wancan. Bilal ne ya fara yi sai na Hashim sai na Nihal sai na Bash da Najaatu. Aure bai hana su ci gaba da gudanar da harkokinsu ba, matan sun daina yin fim amma daga cikin gida su na rubutawa mazan su fim su na kuma yi musu editing su na daukar nauyin fim dinsu da kansu su siyar su sami riba. Bash ya budewa Naja'atu gidan kwalliya da dinki. Hashim ya budewa matarsa wajen gyaran jikin amare da kunshi. Daman sun yi suna a fim dan haka aka dinga tururruwar zuwa wajen dan a gansu ma. Nihal da Muqaddas kuwa sun sha shawaqi (honey moon) a qarshen duniya. Haka Siyama da Abubakar su ma sun kama hanyar su daban kowa da qasashen da yake so. 'Yayan gwamna kenan maganar kudi ma baa magana. Allah Ya bada zaman lafiya Amin. 11/14/21, 7:20 AM - MY MTN 2: Na kudi ne 鉂� GABA GADI NA JAMILA UMAR TANKO (JUT) Gwamna muse ya cikawa 'yan fim alqawuran da ya dauka, duk abinda ya ce zai yi musu yayi har ma ya qara wasu akansu.Ya bawa Nihal kwamishiniyar mata da qananan yara duk da ma da farko ta qi karba amma an matsa mata sai da ta karba dole. Dalili kuwa kowa ya tabbatar ita ce ta fi kowa tausayin mata da qananan yara da kudinta da jikinta ma yi musu take yi balle kuma ta zama hukuma. Ta na yaqi da mata masu shaye-shaye tun daga cikin gida wato 'yan fim har zuwa ga 'yan waje. Amare da angwaye su na zaman lafiya cikin jin dadi da nishadi, arziqi da soyayya. Cikin ikon Allah matar Hashim ta haifi 'ya mace aka saka mata suna Nihal. Watan da ya zagayo Najaatu ta haifi 'ya mace aka saka mata suna Nihal. Major Abubakar da Siyama sun haifi 'ya mace sun saka mata suna Nihal dole su saka sunanta mana dan ita ta hada wannan qaqqarfar soyayyar. Nihal ta yi farin ciki matuqa kuma ta yi wa takwarorinta tara ta arziki. Ita ce dai ba ta sami haihuwa da wuri ba sai a yanzu ta sami ciki qaramin kuma an tabbatar mu su 'yan biyu ne. Ita da mijinta sun yi shiru tukunna basu fadawa kowa ba. Su na a addu'a kada a gane sai ya girma sannan kowa zai sani. Wannan babban abin farin ciki ne a wajensu. *** *** *** Yau ne daren karrama gwanaye(Award Night). Wanda wani babban kamfani da hadin guiwar gwamnati suka hada domin karrama wadanda suka yi wata bajinta a fim da wadanda suka kokari wajen taimaka ci gaban harkar. Daren wata asabar a wani babban dakin taro in ka Shiga sai ka rantse a Amerika kake baa kano ba. Nihal kenan ta kwaikwayo wancan dan haka ta debo turawan ne suka zo suka tsara. Baa taba samun wajen da ya yi kyau kamarsa ba daman ta karantawa 'yan fim yadda ake yin taron da irin kwalliyar da ake yi. Dan haka kowa da kowa ya fito tsaf gwanin kyau. Ta basu shawara mata da maza da su yi Shiga irin ta al'ada wannan shine zai banbance taron Hausa fim da taron igbo fim da taron turawa. Manyan baqi daga turai Hausawa mazauna can da Turawan da 'yan fim din Lagos da Abuja na yarbawa da na inyamurai. Shigar Nihal ta yi kyau sosai dinkin atamfa ne amma fa a turai aka dinka yankan da yadda aka kwalmada zaka zaci English wears ne. Ita da Muqaddas sun yi shiga matching color shima da shadda aka yi masa nasa dinkin aka rasa gane ko menene su ka saka. Nihal ce ta dinkawa iyayenta na su sun fito gwanin shaawa haka Yayyanta guda bakwai gaba daya sun hallara cikin shiga mai kyau kuma su na cikin garin ciki daman don a ranar aka saka musu ranar aure su dukka sun sami matan da zasu aura. Su Hashim da Najaatu da iyalansu ma baa cewa komai, ha Bilal da Halima Jabir sun fito fa an kure adaka an yi matuqar yin kyau. Tabbas babu wasu 'yan Hausa fim da su ka amsa sunansu da basu halacci wannan waje ba daga kowacce jiha. Taro yayi taro kowa ya hallara waje ya cika maqil baka isa ka iya hango karshen hall din ba idan ka tsaya daga gaba. Ayi Hausa ayi da turanci saboda baqi su ma su fahimta. Ga mai gayya mai aiki Gwamna Muse da Justis matarsa a kusa da shi. Qarshen magana kenan, qarshen haduwa, qarshen qarya dan babu abincin da babu da abin sha. Anya an taba yin taro a garin nan ko a ce a duniyar fim din Hausa irin wannan kuwa? Amsar ita ce "A'a baa taba yin kwatankwacinsa ba ma. Masha Allah! Tabarakallah! Alhamdulullah ! Nihal Nuren ce ta karbi kambun girmamawa. Ta daga shi sama ta yi godiya ga Allah, ta yi godiya ga iyayenta da mijinta ta sake yin godiya ga dinbun al'ummar da suke goyon bayanta su na qara zaburar da ita wajen qara qaimi. Nihal ta sharce hawaye ta ce " ina kira ga iyaye su zama masu lura da inda yaransu suka fi karkata. Don da yawan yara tun su na qanana su kan nuna alamar abinda su ka fi so su zama a rayuwarsu. Wasu yaran za ka ga sun fi raja'a a fannin zane- zane, wasu su na yawan nuna alamar su na son aikin labarai a talabijin, wasu su na nuna son gyare-gyare aikin injiniya. Wasu kuma su na nuna aikin likita su ke so. Wasu yanayinsu yana nuna za su iya aikin lauya.Amma sai ka ga iyaye basu kula ba ko kuma ko da sun kula sun rufe ido sun ture ra'ayin yaro sun qeqashe qasa sun zabarwa dansu abinda kwata-kwata ba layinsa ba ne. Daga nan ake fara samun gagarumar matsala, an tilastawa yaro ya je amma baya gane komai ko ya na yi baya murna. Ni Nihal Nuren hakan ya taba faruwa da ni General ka yafe min zan bada misali ne." Kowa dariya da tafi yake har da General, sai ya gyada kai alamar ya ba ta izini ta ci gaba da batunta. Nihal cike da fara'a ta fara bayani ta ce "ya faru da ni ne a sandiyyar hakan ne ma na kawo ga wannan matsayi." General ya kalli Shatu ita ma ta kalle shi, Muhammad ya kalli Abubakar shima ya kalle shi. Abubakar ya ce " yarinyar nan da shegen surutu za ta jawo mana ruwa. " Muhammad ya ce "ka bar ta ta yi misali da iyaye irin su General." Nihal ta ci gaba da cewa "tun tasowa ta na kasance babu abinda na fi so a rayuwata irin in yi wasan 'yar tsana da 'yartsana nake tsara labari in yi kamar wasan kwaikwayo. Ta kai ta kawo ina zana gida da mace da goyo ina tara yara ina ba su labari kamar dirama. Iyayenta sun fuskanci hakan har su kan zauna su na kallona ina yi mu su wasan kwaikwayo a gabansu da ni da bango nake magana su na ta dariya. Ko a makaranta babu club din da nake shiga sai na wasan kwaikwayo kuma idan na shiga drama kowa sai ya yi nishadi kuma ayi ta tafi don ina acting a cikin zuciyata kamar da gaske. Dalili kuwa shine dan ina son abin kuma bana tsayawa akan abinda director ya fada min sai na qara nawa kuma nawan da nake qarawar ya na zama daidai da sakon ake so a isar. Na yi suna a wannan fage da wuya a yi wani wasa baa saka ni ba tun daga furamarehar zuwa sakandire. Ya kamata ace iyayena sun bi nawa ra'ayin ko baa bar ni na zama 'yar fim ba a bari in karanci mass com. Tunda ina shaawar labarai da duk abinda zaa haska ni a talabijin ko a saurare ni a radiyo. Amma aka ce sai na karanci medicine, na fada musu abinda na fi so na karanta cewa ina so in karanci mass communication ina son in yi aikin jarida. Aka hana ni aka hada min da fada da gargadi aka tabbatar min ba shawara ake ba ni ba umarni ake bani. Na tafi raina baya so kuma na tabbatar ba zan iya yi ba dan babu abinda na qi jini irin aikin asibiti. Na zauna da masana da dama a cikin malamanmu na jami'a ina tambayarsu akan maslaha akan wannan matsalar da nake ciki Cesar ga abinda iyayena suke so ga kuma abinda nake son in karanta. A cikin kashi dari kashi casa'in sun ce in bi ra'ayina, wadanda ma basu ba ni goyon baya ba sun ce in je in zauna da iyayena in fada musu zuciyata sun san zasu amince min. Haka suke gani a matsayin su na turawa wadanda suka san cikakken hakkin yaro. Ni kuma na san daga irin qabilar da na fito ba zan iya komawa in isar da buqatata ba, ko da na je ma ba zan sami abinda nake so ba. Gaba gadi na bi ra'ayina na bi duk hanyar da zan bi aka bani course din da nake so, bayan an yi min jarabawa na ci, na ci da yawa ma har sai da suka yi mamaki, rabu da abinda yaro ya ke so. Ina boyewa a gida har na gama digiri na yi masters na hada da wasu kwasa-kwasai domin karatun medicine ana dadewa na riga su gamawa. A wannan zaman da na yi ina jira lilitoci su gama sai mu koma gida tare da su sai aka dinga yi min tayi akan in fara amfani da karatun mana in fara acting a fim. Tsoro nake ji kada a ganni a fim amma a haka na daure na fara yi din. Ina tsoron kuma na yi na san zata fanjama kuma zata yi fanjam da ni. Kwakwalwata ta kasa hango min gejin masifar da zaa tafka. Na san ina cikin matsala sosai idan aka ji wannan labarin a gidanmu. Raina ne kadai ba zaa fitar min ba amma kowanne irin bala'i da ku ka sani na duniya na hango ni a cikinsa. Iyayena sun zo wajen graduation dina na dinga ta kame-kame ba su san har na yi graduation dina tuntuni tare da 'yan ajinmu ba. Sai da aka gama kiran likitoci kakaf amma babu sunana babu ni babu dalilina dan na gudu na buya. Daddy na ya je ya sami malamai aka dubo masa a inda sunana ya fada su ka zauna su ka wayar masa da kai akan matsalata na san su na bata bakinsu ne yadda maganarsu take Shiga ta kunnen dama haka take fita ta kunnen hagu. Wannan shine labarina." Ta gyalgyale da dariya kowa ma dariyar yake yi a wajen. Har da General da matarsa. Gwamna ya yi ta tuntsira dariya dan ya san halin abokinsa, danger kenan. Kowa ya qagu ya ji qarshen labarin nan daman in ta yi magana da Hausa tana maimaitawa da turanci saboda kowa ya fahimta. Nihal ta ci gaba da magana ta ce " Hukunci daya ya dauka akaina kuma wannan hukunci shine labarin da yake cikin fim dina da aka yi mai suna ' a wata duniyar' dukka abinda ya faru da Jarumar fim din shine ya faru da ni." Sai aka kunna fim din aka haska kowa ya na kallo ga wadanda basu taba gani ba, an haska wasu daga cikin sinasinai masu muhimmanci, daman akwai fassara turanci a qasa wadanda ba sa jin Hausa ma sun karanta sun fahimta." Nihal ta ci gaba da cewa na sha wuya sosai, sai na yi taga-taga zan fadi qasa kafin in kai qasa sai in saka hannu in tokare sai in miqe. Sai in sake yin tuntube ina qoqarin faduwa qasa sai in sake miqewa tsaye da qarfi. Har sai da na kai matsayin da ban sake yarda na yi tuntube ba balle in fadi qasa ba. Na tsaya kem da qafafuwana har ma wasu suke dafa kafadata su miqewa tsaye. Alhamdulullah wannan abin alfahari ne a wajena. Babu qabilar da na fi jin farin ciki irin in yi fim a cikin qabilata, ina son Hausawa ina son yaren Hausa." Aka dauki tafi ana ihu ana mata jinjina. General ne ya taso da sauri ya hawo kan stage ya zo ya rungume ta, ya dafa kafadarta sannan ya karbi lasifiqa yayi magana. Ya ce "ni ne Nuren mubin mahaifin shahararriyar 'yar fim din nan Nihal Nuren Mubin. Tabbas labarin nan da ta bayar ya zaburar da ni kuma ya haska min in da na yi kuskure. Ina sane da abinda 'yata tafi so amma saboda wani alqawari da na qudira a cikin zuciyata na manta da na ta ra'ayinta, na manta da walwalarta, na manta da duk bacin ran da za ta sha domin ita ce za ta shiga aji ta sha wuyar yin karatun. Na shiga aikin soja ne don ina so sosai, ba dan iyayena su na so ba. Danginna kakaf ba sa so in zama soja saboda su na tsoron zaa kashe ni. Amma da yake ina so na shiga da qarfina kuma na yi abinda ya kamata, an yi alfahari da ni a qasar nan. Lallai na yi kuskure kwarai da gaske musamman da na qeqashe idona na rufe na qi kallon hawayen da masoyiyata abin qaunata Prof.Shatu Nuren ta dinga zubarwa ta ba ni shawara in bar Nihal ta zabi course din da take so amma na qi. Daga yau ni Nuren Mubin na yi alqawari zan dinga duba ra'ayin iyalina ina ba su dama su yi abinda su ke so na daina zabar mu su kuma na daina tilasta mu su akan abinda basa so. Duk abinda suke so zan basa su dama su yi abinda suka ga zasu iya. Ina neman afuwa ga Nihal da 'yan uwanta maza guda bakwai Muhammad, Abubakar, Umar Usman, Aliyu, Hamza Mu'awiyya da mahaifiyarsu Haj. Shatu Nuren Mubin 'yar Aljanna. Mata ta gari, ta yi hakuri da ni da halayena." Zazzafan hawaye ne ya sirnano daga idanuwansa sai ga Shatu da yaranta maza guda bakwai kakaf da Nihal mace daya tilo ta takwas akan stage suka rungume shi, su ma hawayen suke yi. Sai kowa ya miqe tsaye dan girmamawa ana tafa musu. Bayan su General sun sauka sun koma mazauninsu Nihal ta buqaci da Hashim da Naja'atu su hawo kan stage don ta yaba musu kuma ta karrama su bisa goyon baya da taimako da suka yi mata a rayuwa. Kan ka ce kwabo sun bayyana. Kalaman Nihal sai da ya tayarwa da kowa tsikar jiki aka yi jinjina ga Hashim da Najaatu. kwalla ce take disa daga idanuwansu su dukka, bayan da ta gama na ta bayanan. Hashim ne ya karbi lasifika ya fadawa duniya ko wacece Nihal, kyawawan halayenta da tausayin talaka da taimakon da ta yi masa da iyalansa a rayuwa. Ya tabbatarwa da duniya cewar ko me ya samu ko me ya zama a rayuwa a sanadiyyar Nihal ne. Najaaatu ta karbi abin magana ta yi bayanai masu ratsa jiki akan Nihal, ta na magana tana kuka har sai da kowa ya ji hawaye shima. Ta ce Nihal ce ta tsame ta daga halaka ta dawo da ita kan hanya saboda ta gudo ta afka harkar fim ba tare da sanin iyayenta ba. Nihal ta dauke ta ta mayar da ita gida, ta gargade akan kada ta dawo sai da yawun iyayenta. Kuma sai da suka saka mata albarka sannan ta fara ganin haske. Nihal ce ta hada soyayyarta da mijinta Bash Auta dan haka Nihal ta yi mata komai a rayuwa. Nihal ta karba ta cewa jama'a su taya ta murna da godiya Hashim da Najaatu da Siyama sun haifi 'ya'ya mata sun saka sunanta. Ana ta tafi ana jinjina wannan aminta ta tsakani da Allah. Daga qarshe Nihal ta karrarama Hashim da Naja'atu da kambun kyauta wato awards. Bayan su Hashim sun sauko daga kan stage. Nihal ta gayyaci Siyama da ta jawo kan stage in da Nihal ta gabatar da Siyama a matsayin aminiyar gaskiya wacce ta amince gara ta fada cikin halaka akan ta bude sirrin aminiyarta. Siyama ce kadai ta san ta canza course amma bata taba fadawa kowa ba haka bayan an fara ganewa babu ukubar da baa sakata ba amma bata fada ba. Su ka rungume juna su na hawaye. Nihal ta karramata da kambun girma. Nihal ta sami kyaututtuka da dama a wajen taron daga manyan kungiyoyi har ma da qanana. Gwamna da kansa ya bata kyauta (award) game da yadda take yin aiki tana taimakon mata da yara hakan ya daukaka darajar gwamnatinsa. Taro ya tashi kowa da yabon Nihal Nuren Mubin. Alhamdulullah godiya ga Allah Madaukakin sarki da Ya bani basira, dama da ikon kammala wannan qirqirarren labari. Abinda na kuskure Allah Ya yafe min wanda na fada daidai Allah Ya hada mu ni da ku a cikin ladan. Godiya ta musamman ga Khaleesat Haidar da Aleesa online writers da suka tarye ni hannu bibbiyu suka wayar min da kai akan yadda abin yake. Godiya ga dinbin masoya da su ka sayi labarin nan. Godiya ga wadanda suka bani karfin guiwa akan in dawo rubutu Nura Nasmat da Sumayya Takori. 11/14/21, 7:20 AM - MY MTN 2: Na kudi ne 鉂� GABA GADI NA JAMILA UMAR TANKO (JUT) Gwamna muse ya cikawa 'yan fim alqawuran da ya dauka, duk abinda ya ce zai yi musu yayi har ma ya qara wasu akansu.Ya bawa Nihal kwamishiniyar mata da qananan yara duk da ma da farko ta qi karba amma an matsa mata sai da ta karba dole. Dalili kuwa kowa ya tabbatar ita ce ta fi kowa tausayin mata da qananan yara da kudinta da jikinta ma yi musu take yi balle kuma ta zama hukuma. Ta na yaqi da mata masu shaye-shaye tun daga cikin gida wato 'yan fim har zuwa ga 'yan waje. Amare da angwaye su na zaman lafiya cikin jin dadi da nishadi, arziqi da soyayya. Cikin ikon Allah matar Hashim ta haifi 'ya mace aka saka mata suna Nihal. Watan da ya zagayo Najaatu ta haifi 'ya mace aka saka mata suna Nihal. Major Abubakar da Siyama sun haifi 'ya mace sun saka mata suna Nihal dole su saka sunanta mana dan ita ta hada wannan qaqqarfar soyayyar. Nihal ta yi farin ciki matuqa kuma ta yi wa takwarorinta tara ta arziki. Ita ce dai ba ta sami haihuwa da wuri ba sai a yanzu ta sami ciki qaramin kuma an tabbatar mu su 'yan biyu ne. Ita da mijinta sun yi shiru tukunna basu fadawa kowa ba. Su na a addu'a kada a gane sai ya girma sannan kowa zai sani. Wannan babban abin farin ciki ne a wajensu. *** *** *** Yau ne daren karrama gwanaye(Award Night). Wanda wani babban kamfani da hadin guiwar gwamnati suka hada domin karrama wadanda suka yi wata bajinta a fim da wadanda suka kokari wajen taimaka ci gaban harkar. Daren wata asabar a wani babban dakin taro in ka Shiga sai ka rantse a Amerika kake baa kano ba. Nihal kenan ta kwaikwayo wancan dan haka ta debo turawan ne suka zo suka tsara. Baa taba samun wajen da ya yi kyau kamarsa ba daman ta karantawa 'yan fim yadda ake yin taron da irin kwalliyar da ake yi. Dan haka kowa da kowa ya fito tsaf gwanin kyau. Ta basu shawara mata da maza da su yi Shiga irin ta al'ada wannan shine zai banbance taron Hausa fim da taron igbo fim da taron turawa. Manyan baqi daga turai Hausawa mazauna can da Turawan da 'yan fim din Lagos da Abuja na yarbawa da na inyamurai. Shigar Nihal ta yi kyau sosai dinkin atamfa ne amma fa a turai aka dinka yankan da yadda aka kwalmada zaka zaci English wears ne. Ita da Muqaddas sun yi shiga matching color shima da shadda aka yi masa nasa dinkin aka rasa gane ko menene su ka saka. Nihal ce ta dinkawa iyayenta na su sun fito gwanin shaawa haka Yayyanta guda bakwai gaba daya sun hallara cikin shiga mai kyau kuma su na cikin garin ciki daman don a ranar aka saka musu ranar aure su dukka sun sami matan da zasu aura. Su Hashim da Najaatu da iyalansu ma baa cewa komai, ha Bilal da Halima Jabir sun fito fa an kure adaka an yi matuqar yin kyau. Tabbas babu wasu 'yan Hausa fim da su ka amsa sunansu da basu halacci wannan waje ba daga kowacce jiha. Taro yayi taro kowa ya hallara waje ya cika maqil baka isa ka iya hango karshen hall din ba idan ka tsaya daga gaba. Ayi Hausa ayi da turanci saboda baqi su ma su fahimta. Ga mai gayya mai aiki Gwamna Muse da Justis matarsa a kusa da shi. Qarshen magana kenan, qarshen haduwa, qarshen qarya dan babu abincin da babu da abin sha. Anya an taba yin taro a garin nan ko a ce a duniyar fim din Hausa irin wannan kuwa? Amsar ita ce "A'a baa taba yin kwatankwacinsa ba ma. Masha Allah! Tabarakallah! Alhamdulullah ! Nihal Nuren ce ta karbi kambun girmamawa. Ta daga shi sama ta yi godiya ga Allah, ta yi godiya ga iyayenta da mijinta ta sake yin godiya ga dinbun al'ummar da suke goyon bayanta su na qara zaburar da ita wajen qara qaimi. Nihal ta sharce hawaye ta ce " ina kira ga iyaye su zama masu lura da inda yaransu suka fi karkata. Don da yawan yara tun su na qanana su kan nuna alamar abinda su ka fi so su zama a rayuwarsu. Wasu yaran za ka ga sun fi raja'a a fannin zane- zane, wasu su na yawan nuna alamar su na son aikin labarai a talabijin, wasu su na nuna son gyare-gyare aikin injiniya. Wasu kuma su na nuna aikin likita su ke so. Wasu yanayinsu yana nuna za su iya aikin lauya.Amma sai ka ga iyaye basu kula ba ko kuma ko da sun kula sun rufe ido sun ture ra'ayin yaro sun qeqashe qasa sun zabarwa dansu abinda kwata-kwata ba layinsa ba ne. Daga nan ake fara samun gagarumar matsala, an tilastawa yaro ya je amma baya gane komai ko ya na yi baya murna. Ni Nihal Nuren hakan ya taba faruwa da ni General ka yafe min zan bada misali ne." Kowa dariya da tafi yake har da General, sai ya gyada kai alamar ya ba ta izini ta ci gaba da batunta. Nihal cike da fara'a ta fara bayani ta ce "ya faru da ni ne a sandiyyar hakan ne ma na kawo ga wannan matsayi." General ya kalli Shatu ita ma ta kalle shi, Muhammad ya kalli Abubakar shima ya kalle shi. Abubakar ya ce " yarinyar nan da shegen surutu za ta jawo mana ruwa. " Muhammad ya ce "ka bar ta ta yi misali da iyaye irin su General." Nihal ta ci gaba da cewa "tun tasowa ta na kasance babu abinda na fi so a rayuwata irin in yi wasan 'yar tsana da 'yartsana nake tsara labari in yi kamar wasan kwaikwayo. Ta kai ta kawo ina zana gida da mace da goyo ina tara yara ina ba su labari kamar dirama. Iyayenta sun fuskanci hakan har su kan zauna su na kallona ina yi mu su wasan kwaikwayo a gabansu da ni da bango nake magana su na ta dariya. Ko a makaranta babu club din da nake shiga sai na wasan kwaikwayo kuma idan na shiga drama kowa sai ya yi nishadi kuma ayi ta tafi don ina acting a cikin zuciyata kamar da gaske. Dalili kuwa shine dan ina son abin kuma bana tsayawa akan abinda director ya fada min sai na qara nawa kuma nawan da nake qarawar ya na zama daidai da sakon ake so a isar. Na yi suna a wannan fage da wuya a yi wani wasa baa saka ni ba tun daga furamarehar zuwa sakandire. Ya kamata ace iyayena sun bi nawa ra'ayin ko baa bar ni na zama 'yar fim ba a bari in karanci mass com. Tunda ina shaawar labarai da duk abinda zaa haska ni a talabijin ko a saurare ni a radiyo. Amma aka ce sai na karanci medicine, na fada musu abinda na fi so na karanta cewa ina so in karanci mass communication ina son in yi aikin jarida. Aka hana ni aka hada min da fada da gargadi aka tabbatar min ba shawara ake ba ni ba umarni ake bani. Na tafi raina baya so kuma na tabbatar ba zan iya yi ba dan babu abinda na qi jini irin aikin asibiti. Na zauna da masana da dama a cikin malamanmu na jami'a ina tambayarsu akan maslaha akan wannan matsalar da nake ciki Cesar ga abinda iyayena suke so ga kuma abinda nake son in karanta. A cikin kashi dari kashi casa'in sun ce in bi ra'ayina, wadanda ma basu ba ni goyon baya ba sun ce in je in zauna da iyayena in fada musu zuciyata sun san zasu amince min. Haka suke gani a matsayin su na turawa wadanda suka san cikakken hakkin yaro. Ni kuma na san daga irin qabilar da na fito ba zan iya komawa in isar da buqatata ba, ko da na je ma ba zan sami abinda nake so ba. Gaba gadi na bi ra'ayina na bi duk hanyar da zan bi aka bani course din da nake so, bayan an yi min jarabawa na ci, na ci da yawa ma har sai da suka yi mamaki, rabu da abinda yaro ya ke so. Ina boyewa a gida har na gama digiri na yi masters na hada da wasu kwasa-kwasai domin karatun medicine ana dadewa na riga su gamawa. A wannan zaman da na yi ina jira lilitoci su gama sai mu koma gida tare da su sai aka dinga yi min tayi akan in fara amfani da karatun mana in fara acting a fim. Tsoro nake ji kada a ganni a fim amma a haka na daure na fara yi din. Ina tsoron kuma na yi na san zata fanjama kuma zata yi fanjam da ni. Kwakwalwata ta kasa hango min gejin masifar da zaa tafka. Na san ina cikin matsala sosai idan aka ji wannan labarin a gidanmu. Raina ne kadai ba zaa fitar min ba amma kowanne irin bala'i da ku ka sani na duniya na hango ni a cikinsa. Iyayena sun zo wajen graduation dina na dinga ta kame-kame ba su san har na yi graduation dina tuntuni tare da 'yan ajinmu ba. Sai da aka gama kiran likitoci kakaf amma babu sunana babu ni babu dalilina dan na gudu na buya. Daddy na ya je ya sami malamai aka dubo masa a inda sunana ya fada su ka zauna su ka wayar masa da kai akan matsalata na san su na bata bakinsu ne yadda maganarsu take Shiga ta kunnen dama haka take fita ta kunnen hagu. Wannan shine labarina." Ta gyalgyale da dariya kowa ma dariyar yake yi a wajen. Har da General da matarsa. Gwamna ya yi ta tuntsira dariya dan ya san halin abokinsa, danger kenan. Kowa ya qagu ya ji qarshen labarin nan daman in ta yi magana da Hausa tana maimaitawa da turanci saboda kowa ya fahimta. Nihal ta ci gaba da magana ta ce " Hukunci daya ya dauka akaina kuma wannan hukunci shine labarin da yake cikin fim dina da aka yi mai suna ' a wata duniyar' dukka abinda ya faru da Jarumar fim din shine ya faru da ni." Sai aka kunna fim din aka haska kowa ya na kallo ga wadanda basu taba gani ba, an haska wasu daga cikin sinasinai masu muhimmanci, daman akwai fassara turanci a qasa wadanda ba sa jin Hausa ma sun karanta sun fahimta." Nihal ta ci gaba da cewa na sha wuya sosai, sai na yi taga-taga zan fadi qasa kafin in kai qasa sai in saka hannu in tokare sai in miqe. Sai in sake yin tuntube ina qoqarin faduwa qasa sai in sake miqewa tsaye da qarfi. Har sai da na kai matsayin da ban sake yarda na yi tuntube ba balle in fadi qasa ba. Na tsaya kem da qafafuwana har ma wasu suke dafa kafadata su miqewa tsaye. Alhamdulullah wannan abin alfahari ne a wajena. Babu qabilar da na fi jin farin ciki irin in yi fim a cikin qabilata, ina son Hausawa ina son yaren Hausa." Aka dauki tafi ana ihu ana mata jinjina. General ne ya taso da sauri ya hawo kan stage ya zo ya rungume ta, ya dafa kafadarta sannan ya karbi lasifiqa yayi magana. Ya ce "ni ne Nuren mubin mahaifin shahararriyar 'yar fim din nan Nihal Nuren Mubin. Tabbas labarin nan da ta bayar ya zaburar da ni kuma ya haska min in da na yi kuskure. Ina sane da abinda 'yata tafi so amma saboda wani alqawari da na qudira a cikin zuciyata na manta da na ta ra'ayinta, na manta da walwalarta, na manta da duk bacin ran da za ta sha domin ita ce za ta shiga aji ta sha wuyar yin karatun. Na shiga aikin soja ne don ina so sosai, ba dan iyayena su na so ba. Danginna kakaf ba sa so in zama soja saboda su na tsoron zaa kashe ni. Amma da yake ina so na shiga da qarfina kuma na yi abinda ya kamata, an yi alfahari da ni a qasar nan. Lallai na yi kuskure kwarai da gaske musamman da na qeqashe idona na rufe na qi kallon hawayen da masoyiyata abin qaunata Prof.Shatu Nuren ta dinga zubarwa ta ba ni shawara in bar Nihal ta zabi course din da take so amma na qi. Daga yau ni Nuren Mubin na yi alqawari zan dinga duba ra'ayin iyalina ina ba su dama su yi abinda su ke so na daina zabar mu su kuma na daina tilasta mu su akan abinda basa so. Duk abinda suke so zan basa su dama su yi abinda suka ga zasu iya. Ina neman afuwa ga Nihal da 'yan uwanta maza guda bakwai Muhammad, Abubakar, Umar Usman, Aliyu, Hamza Mu'awiyya da mahaifiyarsu Haj. Shatu Nuren Mubin 'yar Aljanna. Mata ta gari, ta yi hakuri da ni da halayena." Zazzafan hawaye ne ya sirnano daga idanuwansa sai ga Shatu da yaranta maza guda bakwai kakaf da Nihal mace daya tilo ta takwas akan stage suka rungume shi, su ma hawayen suke yi. Sai kowa ya miqe tsaye dan girmamawa ana tafa musu. Bayan su General sun sauka sun koma mazauninsu Nihal ta buqaci da Hashim da Naja'atu su hawo kan stage don ta yaba musu kuma ta karrama su bisa goyon baya da taimako da suka yi mata a rayuwa. Kan ka ce kwabo sun bayyana. Kalaman Nihal sai da ya tayarwa da kowa tsikar jiki aka yi jinjina ga Hashim da Najaatu. kwalla ce take disa daga idanuwansu su dukka, bayan da ta gama na ta bayanan. Hashim ne ya karbi lasifika ya fadawa duniya ko wacece Nihal, kyawawan halayenta da tausayin talaka da taimakon da ta yi masa da iyalansa a rayuwa. Ya tabbatarwa da duniya cewar ko me ya samu ko me ya zama a rayuwa a sanadiyyar Nihal ne. Najaaatu ta karbi abin magana ta yi bayanai masu ratsa jiki akan Nihal, ta na magana tana kuka har sai da kowa ya ji hawaye shima. Ta ce Nihal ce ta tsame ta daga halaka ta dawo da ita kan hanya saboda ta gudo ta afka harkar fim ba tare da sanin iyayenta ba. Nihal ta dauke ta ta mayar da ita gida, ta gargade akan kada ta dawo sai da yawun iyayenta. Kuma sai da suka saka mata albarka sannan ta fara ganin haske. Nihal ce ta hada soyayyarta da mijinta Bash Auta dan haka Nihal ta yi mata komai a rayuwa. Nihal ta karba ta cewa jama'a su taya ta murna da godiya Hashim da Najaatu da Siyama sun haifi 'ya'ya mata sun saka sunanta. Ana ta tafi ana jinjina wannan aminta ta tsakani da Allah. Daga qarshe Nihal ta karrarama Hashim da Naja'atu da kambun kyauta wato awards. Bayan su Hashim sun sauko daga kan stage. Nihal ta gayyaci Siyama da ta jawo kan stage in da Nihal ta gabatar da Siyama a matsayin aminiyar gaskiya wacce ta amince gara ta fada cikin halaka akan ta bude sirrin aminiyarta. Siyama ce kadai ta san ta canza course amma bata taba fadawa kowa ba haka bayan an fara ganewa babu ukubar da baa sakata ba amma bata fada ba. Su ka rungume juna su na hawaye. Nihal ta karramata da kambun girma. Nihal ta sami kyaututtuka da dama a wajen taron daga manyan kungiyoyi har ma da qanana. Gwamna da kansa ya bata kyauta (award) game da yadda take yin aiki tana taimakon mata da yara hakan ya daukaka darajar gwamnatinsa. Taro ya tashi kowa da yabon Nihal Nuren Mubin. ********************** ? ************************** ********** Ai Hausa Novels **************** *************************? ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ? ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ? ************************** Alhamdulullah godiya ga Allah Madaukakin sarki da Ya bani basira, dama da ikon kammala wannan qirqirarren labari. Abinda na kuskure Allah Ya yafe min wanda na fada daidai Allah Ya hada mu ni da ku a cikin ladan. Godiya ta musamman ga Khaleesat Haidar da Aleesa online writers da suka tarye ni hannu bibbiyu suka wayar min da kai akan yadda abin yake. Godiya ga dinbin masoya da su ka sayi labarin nan. Godiya ga wadanda suka bani karfin guiwa akan in dawo rubutu Nura Nasmat da Sumayya Takori.