********************** ⬇ ************************** ************* Ai Hausa Novels **************** *************************⬆ ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ⬇ ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ⬆ **************************  💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 Wa yasan gobe? ▶1⃣ safiya Abdullahi musa huguma 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 Zaune take dirshan bisa carfet din dake mamaye da qaton dakin nata,ta tanqwashe qafafunta yayin data tallafe kumatunta da dukka tafin hannunta,lokaciguda kuma ta zubawa food flask din abincin dake gabanta ido,a zahiri idan ka dubeta zakayi tsammanin flask din take kallo sai dai sam ba haka bane zuciyarta da ruhinta sun lula wata duniya ne ta daban,da yunwa ta shigo gidan saidai sam ta kasa sa koda loma guda ta abincin a bakinta,cikin kwanakin tana cikin wani yanayi wanda ta kirashi da jarraba ko musifa dake tunkaro rayuwarta Wannan ne karo na hudu a rayuwarta da idaniyarta tayi tozali dashi saidai ya zame mata masifa,tun daga ranar da ta dora idonta akansa wani baqon lamari ya ziyarci zuciyarta da gangar jikinta,zata iya kiran lamarin da zazzafan so wanda ya zamto mata tamkar harara a duhu,dalikinta na fadar haka kuwa shine wanda zuciyarta ke budurin a kansa baisan Allah yayi ruwan halittarta ba a doron duniyar subhana,tayi kukan tayi takaicin yadda zuciyarta tayi mata rashin adalci ta hanyar kamuwa da soyayyar wanda batasan koshi waye ba?,meye sunansa?,a ina yake?,taja doguwar ajiyar zuciya sannan ta jawo flask din ta bude da niyyar taba wanu abu a ciki kota tsira daga fadan umminta,ilai kuwa tana loma ta biyu taji sallamar ummin tana daga tsaye ta dubeta tace"yanzu fadila tun shigowarki kika damemu da zancan jin yinwu amma kusan aqalla awa guda banga wani abun kirki da kika ci ba?,tadan yamutsa fuska tace wlh ummi da yunwar na shigo amma kinga na kasa ci"ummi tace ,haka dai kika iya kullum kamar wata qanqanuwar yarinya sai anyi fama dake akan cin abinci ko?,yayi miki kyau ai kinsan ulcer dai ba gidanku daya ba bare kice idan ta kamaki zata miki sassauci,tayi dan murmushi tace kiyi haquri ummi insha Allahu yanzu zan kawo miki flask din empty,ummin tadan harareta tace ai jikina kunne ne,fadila tadan qumshe dariyar da keson subuce mata,har takai bakin qofa ta juyo tace"af na manta ki shirya yanzun zaki kaini gidan alh salim kwana biyu su shiru muma shiru"tadan sosa kanta dake a tsefe saidai ta tufke shi da band tace anya ummi zan gane ma gidan?,ungo wannan ja'ira cewar ummi da ta watsa mata daquwa yace"nima in banda abbanku yace in tafi dake zaki maku siyayyar kayan make up da da driver zanyi tafiyata"tayi ko saurin miqewa tace yauwa ummi dama jiya nayi masa zancen kayan,tace ato minti goma ki sameni ina falo ina jiranki,ta amsa tana qoqarin shiga toilet dinta dake manne da bedroom din ⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜ Tsaf ta shirya cikin abaya baqa mai sulbi saqar qasar dubai wadda aka mata ado da jajayen dutsina masu sheqi,ta nannade tulin gashinta tayi a cuci dashi sannan tayi rolling da wani dan kyakkyawan jan mayafi,simple make up tayi amma kasancewarta tana da wani sassanyan kyau sai ta fito gwanin sha'awa,ta daura agogo na fata ja sai plate shoe da tasanyawa qafarta mai ja ne mai baqaqen igiyoyi,wayar hannunta kawai ta dauka hade da key din motarta ta sake kallon kanta a madubi,cikin zuciyarta ta qaryata masu cewa abu mai duhu baya giwa baqi kyau,duk da cewa ita din ba baqa bace irin matan nan ne masu launin fata(chaculet colour)wasu kuma suce black beauty,fatarta batayi haske can ba kuma kai tsaye ba zaka kirata baqa ba tamkar irin black american haka yanayinta yake,fadila nada wani irin kyau mai sanyi wanda tashin farko bazaka gama tantance kyawunta sai kuna tare wato qananun kyau ne da ita,ba abu mafi daukan hankali a tare da ita irin qirar jikinta cocacola shape,idanunta manya masu dauke da gazar gazar din gashi wanda hakan ke taka muhimmiyar rawa gun tafiya da zuciya gami da ruhin mazaje da dama,goshinta kam irin qananun Gashinnan ne kwance luf wanda ko tayi dauri basu boyuwa,muryarta a sanyaye take cike da wani sirri wanda idan tayi magana take janye hankalin jama'a da dama,fadila tako ina Allah ya bata zubi da tsari wanda yasanya take burge mutane ba maza kawai ba hatta ga yan uwanta mata ma,sai dai gwanar miskilanci ce,sam magana bata dameta ba,tafi ganewa tayi karance karance maimakon zaman tadi,fadila yanzu haka daliba ce a jami'a bayero kano tana karantar mass com,duk da cewa abbanta yayi mata sha'awar karantar medicine ganin cewa mass com bana mutum ne mara son magana ba amma data nuna masa tafi sha'awar mass com din sai ya barta da zabinta kasancewarsa mutum ne mai sauqin kai,sai ya maida zabin nasa kan 'yar uwarta farida,alh abbas ahmad shine mahaifin fadila dan kasuwane mai rufin asiri,domin Allah ya bashi wadata irin wanda ko wane dan adam ke fatan samu ba abunda aka nema a gidansa a ka rasa,asalinsa bafulatanin bauchi ne,yana sana'ar sai da shaddodi da yadiddika cikin kasuwar kwari,yakan tura babban dansa wasu lokutan china ko india domin shigo da kayan su kuma zuzzuba a shagunansu dake cikin kasuwar,ya auri mahaifiyarsu haj amina a maiduguri cikakkiyar shuwa ce wadda Allah ya qaddari aurensu tun bayan da yayiwa manemanta dintinkau a zuciyarta,anan garin kano suka ci gaba da zama tunda anan kasuwancin nasa yake,haihuwar farko suka sami da namiji inda yaci sunan ahmad,baiyi wani tsawon rai ba Allah ya karbi abinsa,shekara daya tsakani suka sake samun wani yaron aka mayar masa da sunan ahmad din,daganan haihuwar tayi musu dif tamkar aun daina,wanda a tsakanin har amina ta soma fuskantar qananun maganganu irin na dangin miji duk da cewar ba a kusa suke ba,sai bayan shekaru goma Allah ya sake qaddara musu samun wata haihuwar,ta haifi 'yar kyakkyawar budurwa taci sunan fadila,shekara biyu tsakani Allah ya sake kawo wani rabon nan ma mace ta haifa aka sa mata farida,kasancewar fadila mara saurin girma sai suka taso kai daya da farida idan ka gansu zakayi tsammanin twince ne don kamarsu daya saidai farida tafi fadila garin jiki da kuma farar fata,tasowarsu tare yasanya komai daya ake musu hatta makaranta tare aka sanya su,sai da suka shiga jami'a ban bancin course ya raba su,shekara shidda da haihuwarsu umminsu ta sake haihuwar da namiji inda aka sa masa muhammad tun daga lokacin kuma haihuwar ta musu bankwana Babban wansu ya ahmad yayi aure tuni da matarsa anty hafiza harsun samu albarkar twince duka mata ,rayuwar gidan rayuwa ce mai ban sha'awa cike take da son junansu suka taso girmama juna da qaunar juna,sai dai tsakanin fadila da farida akwai tsokana fada da wasa na tsakanin sakuwa da sakuwa sai dai duk da haka farida na respecting din fadila 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 S.A huguma [10/16, 12:18 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 Wa yasan gobe? Safiya Abdullahi musa huguma 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 ▶2⃣ Sun fito kenan daga gidan farida ta shigo da motarta layin (da yake ya ahmad yayi qoqari bayan kammala secondry sanda suka samu admission a jami'a ya sai masu yan qananan motoci rio,yace tunda fadila baqace ta dauki fara farida kuma ta dauki marun)farida ce ta soma jan burki ta tsaya don tasan halin mutuniyar zata iya shigewarta tace"ummi ina zaku je?" "Gidan alh salim kwana biyu haduwa tayi wuya shine zanje dubasu"cikin tsokana ta kalli fadila tace "wlh ummi gwara da kika banbaro kifin rijiyar nan kika fito da ita inaga tafi shekara dubu bata je gidan uncle abba ba"fadila ta watsa mata harara tace"ni sa'arki ce"ta qyal qyale da dariya tace sorry yaya fadila"fadila tayi saurin yiwa motar key suka wuce,suna tafiya a hanya suna hira jefi jefi da ummi abinsu gwanin sha'awa har suka isa gidan,gidan na jerin gidajen kundila housing estate dake maiduguri road,gidane irin na masu naira da suka ci suka tada kai,mai kula da qofa ya dage masu wakeken get din gidan cikin fara'a suka shige kasancewar akwai sanayya mai yawa tsakaninsa da ummin Ummi ce a gaba fadila na binta a baya har suka isa tafkeken falon gidan ,haj maimuna na zaune bisa luntsuma luntsuman kujerun dake kewaye da falon kallo suke ita da yaranta sumayy da rabi'ah,sallamar su ita ta dauki hankalin su suka juyo hade da amsa musu,haj maimuna ta miqe cikin girmamawa tana cewa lale marhabin haj kune tafe da yammarnan ,ummi tayi murmushi tace ai kuwa dai kam"ta sake fadada fara'arta tace sannunku da zuwa ai......,maganar haj ta katse ta kama baki tace"a'ah yarannan yau yaushene?,ta fadi tana kallon fadila,dukkansu sun fahimci me take nufi suka qyal qyale da dariya suka ce momi yau laraba,ta gyada kai tana cewa lallai ba shakka ta bawa ranar samu,wlh haj bazan iya lissafa yaushe rabon fadila da gidannan ba,"ummi tace"hmmmm to wlh yauma da qyar na banbarota don taji zamu biya store ne zata kwaso kayan make up shine ma qarfin biyonin"momi ta sake gyada kai cike da mamaki tace lallai yau mun tashi da bismillah haj ku zauna mun tsaya zance na barku a tsaye,dukkansu suka zauna sannan suka fara gaisawa fadila ta gaida momi a kunyace ,ta amsa mata tana cewa"kyaji kunya mana mara zumunci ,sam farida ta fiki zumunci "sumayya dake kusan sa'a ga farida tace"wlh anty fadila faridammu ta fiki zumunci"fadila ta dan harareta da taga idonsu ummi baya kansu tace"ta dai fini qafar yawo yaufa sai da zamu fita ta dawo tun azahar wai ta tafi gidan qawarta "sumayya tace "to ai zumunci taje"fadila ta dan tabe baki tace"ke ni qyaleni yawon farida yafi qarfin qafata ko ina a kano kika kwatanta mata ta sani "sumayya da rabi'ah sukai dariya suka ce "kai anty don dai ke bakison fitarne shi yasa kikace sister ta fiya yawo" Hira suke suka tsinci qanqanuwar muryar yarinyar na sallama ,ta saki hannun wanda ya riqota da gudu ta fado falon,momi ta cewa wanda ya kawota din sannu isah,yace yawwa haj ya juya ya fice,rabi'ah tace oyoyo ifti na,muga kitson,da gudu ta fada cinyarta ta janye hular da ka rufe mata kanta da ita tana nuna mata,kalbace mai kyau twisting wadda aka lafe jelar ta da beads masu kyau,kasancewar yarinyar nada tsawon gashi sai ta kwanta lub tayi kyau har dokin wuyanta,tace anty sumy tayi kyau"sumayya tace gsky qawata ba magana "ta bata hannu suka tafa,ta miqe tayi gun momi ganin ummi yasata duqawa ta gaidata,ummi ta amsa fuskarta dauke da fara'a momi tace"har yanzu fushi ake kenan da ni shi yasa ni baza'a nuna min kitson ba"cikin magana irin tq shagwababbun yara tace "ba cewa kikayi ayimin mai zafi ba"sai kuma ta juya ta koma gunsu sumayya tana bata lbr,ummi ta kalli momy tace"wai iftihal din Aliyu ce wannan?"momi dake tsiyayawa ummi lemo a cup tace"itace mana kinga yadda ta girma ko?"ummi ta jinjina kai tace"ba shakka gata nan kuwa masha Allah,ina zaton ai ba zata wuce shekara bakwai ba ko?"momi tace "idan watan nan ya mutu sabon wata ya kama yakai ashirin zata cika shida",sai bayan sunyi magariba suka fito,tuni iftihal ta maqale wa fadila domin cikin qanqanin lokaci suka saba,don fadila ba daga baya ba gun son yara,bare iftihal yarinya ce kyakkyawa ga wayon tsiya,har bakin mota suka rakosu sumayya na yaba kyawun motocin nasu,fadila tace idan kina so ki amsa mana,sumayya ta kama baki tace rufamin asiri kada kisa yaya aliyu ya babbalani kina ganin abba zai sai mana ma ya hana wai har yanzu bamu da hankali sai randa muka qara nutsuwa?fadila tayi dariya tace "sai kace yau aka haifeku""kema dai kya fada sister cewar rabi'ah,dai dai nan ummi da momi suka qaraso momi ta miqawa fadila baqar leda tace"to ga kayan kwalliyarnan aje ayi tayi ana samo mana sueukai"a kunyace ta amsa tana mata Godiya,momin tace to sai wata shekarar kenan,fadila ta sadda kai qasa tace"a'ah momi insha Allahu zaku dinga ganina"Allah yasa inji momi,ummi tace"wai ni kuwa ina Aliyu ne,na kwana biyu rabon da na ganshi fa"fuskar momi ta canza zuwa yanayin damuwa tace"hmmmm,mtsw,ke dai bari kawai haj kwanan nan zaki jiyomu da shi,Aliyyu fir ya guji aure yaqi fidda mace yayi aure,yafi ganewa kasuwancinsa kawai nayi har na gaji hakanan abbansa kullum zancen kenan amma yaron nan sam yaqi mai dakansa"ummi tace"addu'a kawai zaku ci gaba da yi masa Allah ya kawo ta gari kada a kuma komawa 'yar gidan jiya a bata goma daya bata gyaru ba"momi ta gyada kai tace hakane,Allah ya zaba mana abinda yafi alkhairi"tace amin Daqyar iftihal ta rabu da fadila harsai da ta laluba cikin motarta ta samo mata chaculet sannan ta yarda ta barsu suka tafi,basu tsaya ako ina ba sai a shop rite dake ado bayero mall,ta nufi parking space ta gyara tsayuwar motarta sannan ta kashe,ummi ta zaro kudi cikin jakarta ta miqa mata,tace maza kiyi da jiki ki fito"tasa hannu biyu ta amshi kudin tana qoqarin maida murdin motar ta rufe ne ummi tace"saura ki kwaso kayan zaqi da sanyi ki koma gida ki guji maqiyin naki abinci"tayi murmushi kawai tace baza'a siyo ba ummi ta rufe motar ta shige,cikin nutsuwa take daukar musu abinda tasan suna da buqatarsa ita da farida har ta kammala,har zata nufi kanta ta tuna bata dauki turarenta ba blue lady,cikin sauri ta koma,hankalinta yatafi ga turarurrukan tamkar ance ta kalli gefanta,tsaye yake shima yana zaban nasa kalan,yana sanye cikin shadda dinkin tazarce blue Black ce ta haska farar fatarsa matuqa,ta gefan tana iya hango qaya taccen sajensa dake kwance luf bisa tsararriyar fuskarsa,ga tsinin hancinsa nan yayi das qasan farin qal din glass dake bisa fuskarsa,kyakkyawan idonsa wanda gashin idon suka yiwa rumfa suna juyawa cikin farin glass din nasa yan karanta rubutun dake jikin kwalin turaren,kansa ba hula sai sumarsa dake kwance an dan saisayeta,ya zari turaren kwali uku cikin sassarfa ya juya yabar gun,samun kanta tayi da bin bayansa zuwa inda zai biya kudinsa ,kusan tare suka biya sai dai sam shi bai lura da ita ba ya juya ya fita ta sake bin bayansa,tafiyansa ma abar kallo ce tamkar wani saraki haka yake takawa,daga nesa tadan tsaya a harabar adana motocin don batason ya ganta,cikin aljihunsa yasa hannu ya zaro key ya bude wata baqa sidiq din mota qirar range rover ya shiga yayi mata key ya jata da gudu ya bar gun,jan ajiyar zuciya tayi gamida lumshe idonta hadi da dafe goshinta da tafin hannunta"inna lillahi wa inna ilaihir raji'un allahumma ajirni fi musi bati wa akhlifni khairan minha"abunda take ta nanatawa kenan,wannan wace iriyar musibace zuciyarta ke son jefata ba gaira ba dalili?,ta bude idonta ahankali jikinta ba laka ta soma lalubar inda tayi parking Cikin motar tayi dif zugi da radadi take ji,ba abunda zuciyarta keyi sai zillo cike da dimbin qaunarsa,shi wa?,ita kanta bata sanshi ba,ummi nata mata hira tana cijewa tana amsa mata har suka isa gida,farida na falo ta baje kolin takardu da alama assignment takeyi,batason ta dameta da hira don haka tadan daure fuska,itama faridan data fuskanci hakan bata ce mata komai ba illa sannu da zuwa ya kuka barosu?,ta amsa mata ta haura sama inda dakinsu ita da farida yake,ta watsa siyayyar tasu kan gado zuciyarta cunkushe ta cire kayan jikinta ta fada toilet da niyyar sakarwa kanta ruwa ko zataji sanyin zuciyarta Muje zuwa S.A.M huguma✍🏻 [10/16, 12:19 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍:  🌺🌺🌺🌺🌺🌺 WA YASAN GOBE? ▶3 SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 Lotion kawai ta shafa bayan ta fito ta feshe jikinta da body spray ta lalubi rigar bacci doguwa har qaurinta ta zura don bacci take da muradin yi, ta daura zani a sama ta sanya hijabin sallarta ta gabatar da sallar isha'i, ta dora da shafa'i da wutiri, bayan ta shafa addu'o'inta tabi lafiyar gado, a maimakon bacci yazo mata sai tunani ya mamaye gurbinsa, ba zato ta tsinci kanta da zubarwa kanta da kanta hawaye na tsananin tausayin kanta, a cikin jikinta da zuciyarta take jin ta shiga halin tsaka mai wuya, zuciyarta na bulayi da lalube cikin duhun son wanda bai ma san tana yi ba, farida ta shigo dakin hade da sallama hakan ya sanyata saka hannu tana goge hawayen cikin dabara don bata son faridan ta gani, faridan tadan kalleta jikinta yaso ya bata tamkar yar uwarta na cikin damuwa, don haka jikinta sai ya danyi sanyi ta shigo ne da niyyar tsokana don flask guda ummi ta ciko da abinci tace kada ta sauko da shi sai ta cinye Farida ta ajjiye flask din a gefan gadon ta janyo dressing chair ta zauna tana fuskantar fadilan tace"sister lafiya naga kamar fuskarki ta nuna kamar kina cikin damuwa? ,ta qaqalo murmushi sannan tace"ba abunda ke damuna just na gajine fitar nan da nayi"farida ta girgiza kai ba don ta yarda ba tace"ok,to ga abincin ki nan ,ummi tace " kada ki sauko mata da shi sai kin cinye tana daga kwancen ta zubawa flask din ido tace"har gabana ya fadi wlh, ina zan kai wannan abincin? ,farida ta qyalqyale da dariya tace"ni dai yar aikece kuma na isar da saqo,qafafunta tayi saman tiles din daya mamaye da qaton dakin nata Ta daura zani a sama ta sanya hijabin sallarta ta zari flask din, farida ta kalleta tace " a'ah ina zuwa? "Ba tare data kalleta ba ta juya tana shirin fita sannan tace"jirani ina zuwa"farida ta bita da kallo tana dariya ciki ciki ,ta qofar baya fadila ta fita ta bulla bakin get din gidan,kai tsaye ta nufi gun idi mai gadinsu, mutuminta ne dama da hangota kuwa ya miqe yana cewa " uwar dakina"miqa masa flask din tayi tace"yi sauri ka juye idi"cikin qanqanin lokaci kuwa ya juye abincin ya bata flask din yana zuba godiya Ta tarar da fadila na waya da alama da saurayinta take, ta koma gefan gadon ta zauna tana kallon faridan har ta kammala tsaki fadilan tayi, farida tayi murmushi tana kallon flask din da fadila ta dawo dashi don tasan kwanan zancan, bata son idan zatayi waya tayi mata a dakinta,fadila ta harareta tace"bana gaya miki ki daina shigomin daki idan zaki shirmen wayarki ba? ,tace tana gyara kwanciyarta akan sofa qwaya daya dake dakin " sorry anty na"tana dan murmushi tace kiyi haquri ⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜ Tun bakwai na safe take a kitchen dama haka al'adarta take, idan bata da lecture to Itace mai shirya musu breakfast haka da rana ko da daddare,girki yana daya daga cikin hobby dinta hakan ya sanya ta zama gwana ta fannin abubuwan ci da na sha, Awa daya da rabi ta kammala komai ta koma dakinta tayi wanka ta shirya kasancewar tara da rabi tana da lacture,dakin ummi ta shiga bata nan sai muhammad ta tarar yana kan gadonta yana bacci,dala masa duka tayi tace"tashi malalacin banza eight thirty amma kana bacci ina school din?"cikin magagin bacci yake murza ido yace"wlh nayi wanka bacci ne ya daukeni"tace"oya tashi ka shirya idan zan wuce na sauke ka na baka eight minute"da sauri kuwa ya duro daga kan gadon ya shige toilet Bangaren abbansu ta wuce tare da diba masa breakfast dinsa ta tafi masa da shi,yana zaune kan kafet din falon hannunsa dauke da jaridar daily trust,haka yake a al'adarsa bayan ya dawo a masallaci yakan yi azkar da tilawar qur'ani idan gari ya dan sha kuma sai ya karanta jarida kafin ya fita aiki,fadila ta shigo da sallama, ya masa yana dubanta fuskarsa dauke da murmushi,ta dire kayan abincin ta rusuna tana gaidashi ya amsa yana fadada fara'ar shi yace"sannu fadila da qoqari hala yauma anada da lacture din safen"kanta a sunkuye tana qoqarin hada masa kunun shinkafa da yasha madara tace"eh Abba",ummi ce ta fito daga bedroom din Abban hannunta dauke da doster da alama goge goge ta gama,fadila ta gaidata tana qoqarin tashi tace"abba zan tafi"ya dubeta sannan yace"ai banga kin ci komai ba haka zaki tafi?""abba zan karya a capteria idan na.......... Ummi tayi saurin katse ta da cewa"yi mana shiru wlh abbansu idan taje ma bacin take ba farida ai ta gaya min wai ba zata iya cin abinci a waje ba,wannan yarinya na rasa meke damunki anya lafiyarki qalau kuwa?",abban yayi murmushi yana dakatar da ita"dakata umminsu,fadila lafiyar ta qalau,kin manta yawon asibitin da muka dinga yi da ita tun tana qarama?,haka dai halittarta take"ya juya ga fadila yana tura mata cup din da ta hada masa kunun yace"maza zauna kici wani abu kada ki qara bata ran umminki kinji ko?"tamkar zata sa kuka😟 ta zauna tana cewa"to abba"yaci gaba da cewa"gashinan fadila tafiki abin arziqi shi yasa ta rainaki tana ganin kanku daya,ummin tace sai rawar kai da gwanintar yin girkin amma saidai wasu su ci mata,abban yayi murmushi yana kallon yadda take tura abincin kamar magani😣 Kafin ta kammala muhammad ya shigo don haka abban ya sallamesu suka fita tare,suna mota muhammad ya dameta da surutu,ta daga masa hannu ✋🏻hadi da cewa kaga malam bafa aku na dauko ba🐔idan kuma kai aku ne ka gayan"ya qyalqyale da dariya😂 yace"anty ke dai ba dama mutum yayi hira dake sai kice ya dameki shi yasa yaya farida ke burgeni ke halin ya ahmad kikayo kun fiya kwafsawa wlh,ta harareshi sannan tace"ai da itan da kai duk zamuce ta tadda mujemu idan mutum baiyi surutu ba baya burgeku,kada Allah yasa mu burgekun muyita kwafsawar,idan ka qara magana kuma sai na saukeka anan" take ya rufawa kansa asiri yayi shiru🤐 Taso makara saboda ajiye muhammad da tayi don ita ta saba da wuri take zuwa don ta samu sit din gaba,bata da wata qawa bare ta tarar mata hakan ya jawo batayi parking din motar ta daidai ba ta nufi ajin cikin sauri Lacture din ta daukesu awa uku har da mintina,kanta ya dauki chargy sosai,don haka da fitowarta ta samu wani guri dake nesa kadan da ajinsu bashi da yalwar jama'a sosai yafi kusa da inda suke ajjiye motocinsu idan sunzo,gurine mai wadatar shuke shuke ita kuwa ma'abociyar son tsirrai ce [8/8, 3:24 PM] LOADING...... gun na burgeta saboda son tsirran da take dashi,tamkar a cikin iska ta ke jiyo qamshinsa,gabanta ya tsananta faduwa,ta gefan ta ya wuce saidai bayansa kawai take iya gani,ahigar suit ne a jikinsa masu dan karen kyau da sheqi,kayan baqaqene sai tsintsiyar hannunsa da ta gani wadda yake daure da agogon fata baqi,gefansa wani ne ke biye da shi riqe da takardu da brief case,sam sai ta kasa dauke idanunta daga kanshi👀,hakanan gabanta yaci gaba da faduwa cikin zuciyarta take fadin inna lillahi wa inna ilaihir raji'un"har ya danyi nesa da ita sai taga ya waiwayo,cikin wani irin sauri ta dauke kanta tayi wani sashen da shi zuciyarta kamar ta tsinke ta fado,ganin yayi gaba tayi hamdala da Allah yasa bai lura da ita ba,tana tsammanin jikinsa ne ya bashi ana kallonsa👀,a sace taci gaba da kallonsa har ya bacewa ganinta,taja ajiyar zuciya sannan ta dauke idonta daga kallon hanyar ta jawo jakarta ta zuge ta fiddo da wayarta tana danne danne,ta doshi kusan minti aahirin a gunbtana hutawa sai sannan ta tuna zata fa gidan ya ahmad,da sauri ta miqe tana gyara yafen gyalenta,atamfa ce ajikinta dinkin riga da skirt ne,atamfar England ce dark green mai ratsin yellow,sai mayafinta da takalminta agogo da jakar hannu duk yellow,fadila ba qarya ta iya daukan wanka don duk munin atamfa takai aka mata dinki ya saka komai kushe da hassadarka baka isa kace batayi kyauba haka Allah ya bata wannan baiwar,tana tattare komatsanta tana sanyawa a jaka taji ana kwada mata kira,a nutse ta dago tana neman daga ina wannan kiran mafarautan ke fitowa?,wata class mate dinta ce binta auwal fadila taci gaba da binta da kallo har ta qaraso,"fadila abbas yaufa kinyi tabargaza"abinda ta soma cewa kenan,fadila tace"kamar ya fa?"tana dubanta tace kinyi wrong parking kin toshewa A.s mai tama hanya"ta sake dubanta cikin rashin fahimta tace"waye haka kika bi kika rude?'binta ta zaro ido😳 tace"kar dai kice min baki san a.s mai tama ba,hadadden guy din da duk nigeria bama kano ba ansan da zamansa"fadila ta dakatar da ita ta hanyar cewa"na gode"taci gaba da mayar da kayanta jaka Iya dube dubenta ba wanda ta gani sai mutum daya👀,a tsammaninta idanunta ke mata gizo,sai dai har ta qaraso gun shi din dai ta gani,yana tsaye hannayensa harde a qirjinsa fuskarnan a murtuke,ta qaraso ne da niyyar bashi haquri sai dai lura da irin kallon qasqancin da yake mata mata yasa tayi banza da shi kai tsaye ta nufi motarta ta bude,ta zauna a seat din tana qoqarin jan murfin ta rufe taji an dafe murfin motar,ta dago ta dubeshi,yana tsaye yana mata irin kallon dazun,cikin qasaita taji yace"baki da ladabin bada haquri ga wanda kika aikatawa laifi?"duk da yadda zuciyarta ke sake ninqaya a zuciyarta,muryarsa mai sanyi ta kwanta a zuciyarta,amma ta dake gami da cewa cikin zuciyarta"duk da dumbin qaunar da nakeji taka a zuciyata hakan bazai sa na bada girma da jan aji irin na 'ya'ya mata,ta dauke kanta sannan tace"ai shi wanda akawa laifin baisan darajar bil'adama ba"ya saki murfin motar hadi da watsa hannayensa yace"ok,ba laifi"ya saki murfin motar,cikin wata iriyar gaggawa taga ya amshi key din tasa motar daga hannun wanda suke tare ya bude motar sa ya shiga cikin gwaninta ya take motar ya kurda ya matse motar fadilan ta yadda itama bata isa ta fita ba harsai da ya gogeta,ya kashe motar ya zare maqullin ya rufe motar ya fito yana cilla maqullan yana cafe wa ya danyi tsalle ya haye bayan motar ya zauna,da hannu ya kirashi yadan yi masa rada ya amshi tak ardun hannayensa shi kuma ya juya da sauri ya bar gun Sarai fadila ta fahimci abunda yake nufi saboda haka ta zaro wayarta ta nemi number farida ta kirata"hello farida kin shigo school?"tace"eh ya akayi?""kizo ina parking space ki daukeni mu wuce"farida tace"me ya sami motar ki?""kinga idan zaki zo kawai kizo malama""ok sister gani nan" Cikin 'yan mintina sai ga farida horn tayi mata ta miqe ta fito ta kulle motar ta gabansa ta shige ta nufi farida,dai dai lokacin ta jiyo saukowarsa daga bayan motar,wata yar qaramar mota ce tayi parking a gabansa kusan tare suka shige motocin,ta madubin motar farida suka hada ido ta sakar masa tsaki hadi da murguda baki,cikin zafin nama ya balle murfin motar ya fito da sauri tacewa farida"yi sauri ki bar gurinnan,tamkar kuwa tasan meke faruwa ta figi motar ta bar gun Muje zuwa [10/16, 12:21 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 Wa yasan gobe? Safiya Abdullahi musa huguma 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 ▶4⃣ Sai da motar ta saitu akan titi sannan tace mata"gidan ya ahmad fa zamu"ok" inji farida,"sister wai me ya faru naga kamar wadda aka biyo a guje?"taja tsaki tace"wani dan rainin hankali ne yaso wulaqantani bai san bana daukan wulaqanci ba"ta bata lbr yadda sukayi da shi akan toshe ma juna hanya da sukayi,me farida kuwa zatayi idan ba dariya ba,"kefa 'yar wulaqanci ce shi yasa ban fiya saki cikin lamarina ba,a yar madaidaiciyar harabar gidan sukayi parking,kai tsaye suka nufi falon gidan,ba kowa cikin falon da alama matar gidan na ciki don haka suka dinga kwada sallama,daga kitchen matar gidan ta fito anty hafiza kenan kyakkyawar bafullatana,tana ganinsu ta saki fara'a😊 cikin barkwanci tace"lallai yau baquntar tamu ce"suka saki dariya😀dukkaninsu suka gaidata cikin girmamawa ta amsa musu cikin kulawa tana tana tambayarsu ummi,suka ce tana lpy tana gaidata,fadila ta zaro packet na chaculet tace gashi injita a baiwa twince,wai ni ina suke nema anty?""tace yau ai ranar school ne suna can amma suna hanya don bala ya tafi dauko su,""na manta wlh"ta fada tana qoqarin kwanciya bisa doguwar kujera"anty hafiza tace"ah ya haka ina murna kuku tazo kuma naga tana neman bin lafiyar kujer?"fadila ta dan murmusa 😊tace " anty yau saidai amin afuwa yau kasala nake ji""na miki"inji anty hafiza,farida dake canza tasha a t.v tace"qyaleta anty muje na canjeta yau tsokano fada tayi sauran kadan taci na jaki badan Allah ya kawoni na ceceta ba""tab wucenan wlh wa ya isa yayi gangancin taba mana ita?😳""fada mata dai anty😏"cewar fadila,suka shige kitchen nan suka barta a falon Gyara kwanciyarta tayi don taji dadin yin tunaninsa,shi wa?,idan bata manta ba A.S mai tama binta tace da ita,A.S mai tama ta shiga maimaita sunan ita da zuciyarta,"to me A.S mai tama take nufi?"A dai duk inda aka zaga farkon sunansa ne,to ahmad ne ko ko abubakar ko abdul?,oho itama bata sani ba,wani murmushi ne ya subuce mata😊 sai tunaninta ya dawo kan abinda ya faru tsakaninta dashi dazun,sassanyan muryarsa ta dinga yi mata amsa kuwwa a kunnenta,kyawawan idanunsa yanayin zubinsa da tsarinsa,sai ta tuna sanda ya fito a fusace lokacin data murguda masa baki ta harareshi,nan ma dariya ce ta subuce mata,"lafiya kuwa?"ta tsinci muryar farida na tambayarta,ta hade rai tace"lpy lau me kika gani?"farida ta dan tabe baki tace"hmmm tun dazunfa kike murmushi har da dariya ke kadai kamar wadda ta fara soyayya"da sauri fadila ta kalleta tace"lallai yarinyar ni kikewa wannan titsiyen?to gyada na zama na soye qarewar soyayya"anty hafiza dake zaune saman kujera bata sa baki ba sai yanzu tace"um um yaya fadila wannan fa sign ne na falling in love😜"fadila ta miqe daga kwanciyar tana cewa"kai anty,please kada ki biyewa shirmen farida,ita 'yar sa ido ce komai ta gani idonta na kai,kuma sai ta sanya ma question mark😏",ta gyada kai sannan tace " alright idan tayi wari maji,Allah yasa alkhairi ne""amin amma ba abinda zaiyi wari ma anty",nan gidan suka wuni har 'yan biyu suka dawo suka yini tare da su,suna son yaran sosai ko dan su kadaine jikokin gidan nasu,sai bayan magariba sukayi sallah sukaci abinci har yaya ahmad ya dawo ya tarar da su,bayan sunyi shirin tafiya ne ya ahmad ya baiwa ko wacce 4000 anty hafiza kuma ta basu turarurruka. to daren ranar sam fadila bata samu bacci ba,kusan kwana tayi tunanin A.S maitama,duk da ta danji dadi don aqalla tasan yanzun yasan da fuskarta a duniya,koda bazai iya shaidata ba bare tana tunanin mawuyacine ace yayi saurin manta ta ko dan irin karon da suka yi,har washegari da taje school bai janye motar tasa ba,sun dauki aqalla sati guda a haka sannan taje ta tarar ya cire,a gida tace ne kawai tana tana garage ana duba mata ita ⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜ Cikin wannan yanayin suka soma attachment,ranar laraba aka turasu domin tattaunawa da wani fitaccen dan kasuwa,ita da abokiyar karatunta ne hafsat sai wani ma'aikacin gidan radion khalid da zasu tafi tare qarfe hudu na ranar larabar. cikin yellow din atamfa ta shirya mai zanan blue din qananun taurari,skert ne rafa da riganshi wanda dinkin yayi mata cif a jikinta kamar don ita aka qera atamfar,ta maqala qananun fashion na dutse masu kalan blue,ta daura dan siririn agogo na fata ,qafanta blue din hill shoes ne mai madauri sai mayafi data yafashi a kafada bayan ta soka daurinta wanda ya fito da dogon gashinta ta qasan daurin,jakarta ta dauka 'yar madaidaiciya wadda ake maqaleta a gwiwar hannu ta feshe jikinta da turaren shamsul imarat,shigar ta haska fatarta sosai ta fito dagwas da ita,farida dake nade a tsakiyar gadon fadilan tana charting ta dago ta dubeta"gsky yaya fadila kinyi masifar kyau,tsiyar abun daya da baki kula kowa,sai ance anasonnki kuma ki kama mita bayan laifinki ne saiki yi shiga ta janye hankali kuma kice ba wanda ya isa ya kalaki"banza tayi mata ta dauki wayarta dake kan dressing mirror ta fice,farida ta dan daga murya yadda zata jiyota tace"a dawo lpy antyna Allah ya hadaki da mannau ya biyoki har gida😜"bata dai ce mata ci kanki ba ta wuce dakin ummi don tasan a wannan lkc tana daki tana azkar,daga bakin qofa ta tsaya don ta kusa makara tace"ummi zan tafi""to Allah ya tsare hanya ki kula sosai kuma kuna kammala abinda kukaje yi ki taho gida kada ki yadda kiyi dare a waje"tace insha Allah ummi",acan gidan radion suka hadu,bata shiga ba ta yiwa su Hafsa waya su fito su wuce don a motarta suka tsara za suyi tafiyar,Hafsa na zaune a baya yayin da khalil ya shige gaba,tsaf fadila ta gama karantar manufarsa saidai tayi banza da shi tamkar bata fuskance shi ba,tun zuwanta gidan yake rawar qafa a kanta saidai ya kasa furta mata kamar sauran maza da yawa,tana da wani irin kwarjini ne a idanunsu ita sam baya burgeta,ya fiya surutu shi yasa sam bata son ko aiki ne a hada ta da shi,kamar yanzun ya takura mata sai zuba yake shi ala dole sai ya burgeta,Hafsa na baya tana ta tuntsira dariya 😂don tasan halin kayarta sarai,daqa qarshe c.d plate ta dauka tasa sannan yayi shiru A hankali suke binkwatancen har suka gano gurin,qaton get din gun aka bude musu gu ne a tsare ahankali aka dinga nuna mata inda zata bi har taje inda aka tana da don ajiyar motoci tayi parking suka fito,ta jingina jikin motar tata tana qarewa gun kallo,tamkar ma'aikata gun yake saidai ya tsaru sosai komai neat,khalil ya qarso gunsu bayan yaje yayi tambaya yace muje can sunce mu jirashi yana fitowa,wani dan gune da ka qawatashi da flastic din kujeru da teburinsu kowanne yaja kujera guda ya zauna sun dan dauki mintina har fadila ta soma qosawa da zaman jiran Tun daga nesa da ta hangoshi qirjinta ya hau luguden bugawa,ji tayi tamkar ta tashi ta bar gurinsai kuma taga idan tayi hakan ta bada kanta,don haka sai ta basar ta zarme da bude jakarta ta soma fiddo da kayan aikin da zasu buqata,qashin mayen tutarensa da taji ya mamaye gurin shi ya tabbatar mata da qarasowarsa,sallamarsa ta same tabbayr mata da hakan dukkansu suka amsa saidai ita ta kasa dago ido ta dubeshi ta fake da laluben jaka,ya .iqawa khalil hannu sukayi musabaha hafsat ta gaidashi,sai a sannan ta dago kanta caraf suka hada ido👀 saidai ga mamakinta dauke kansa yayi tamkar bai taba ganinta ba,a hankali ta radawa hafsa"da wa za muyi hirar ne?""gashinan a gabanki a.s maitama "inji hafsat"take taji ta dan rude amma cikin dabara ta gayyato dakiya da nutsuwa ta yafawa kanta,kasancewar Ita ce mai tambayoyin jfsat da khalil na tayata da rubutu dolenta ta jawo kujerarta ta sake matsowa daura da shi ta sanya 'yar qaramar recorder dinta a tsakiyarsu suka sake zama verry close aunyi face to face sosai,wani yanayi ya dinga shiga zuciyarta da gangar jikinta wanda hakan ya haifar mata da kasala,tanason tayi.masa tambaya ta farko saidai ta kasa,har sai da hafsat ta dan dungure sanna tayi ta maza ta dago ta fuskanceshi👀,saidai ga mamakinta hannauensa na harfe ne bisa qirjinsa yana mata wannan salon jallon rainin nasa😏,da fari munason muji ainihin cikaken sunanka,ta fada yayin da ta mayar da dubanta kan radio dinta taga tana nadar sautin yadda ya kamata,shiru taji har yayi yawa ta dago ta sake dubansa a karo na biyu,saia taga ya saki hannunsa ya dauke idonsa daga kanta ya kalli khalil yace"ko zakuyi musayar aiki ita ta ta karbi rubutun kamar ba zata iya aikin ba"khalil ya dan rusuna yave ranka ya dade zata iya haka tsarin aikin yazo"ya kalleta cikin gatsali yace"zaki iya?"batayi qasaaqwiwa ba tave aisai an gwada aknsan na qwarai"ta mayat masa da irin yanayim yadda ya yi mata tambayar,cikin ransa yake jinjina rashin kunyarta tare da fafin nasan maganinki" a zuciyar sa ya fadi hakan Ku biyoni muje......  [10/16, 12:21 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 Wa yasan gobe? Safiyya Abdullahi musa huguma 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 ✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻 ▶5⃣ Ya dan gyara zamansa cikin isa ya amsa mata"Aliyyu salim maitama shine cikakken sunana""sunan ya dace da maishi"ta fadi a ranta,cikin nuna qwarewa da gwaninta ta shiga jefa masa tambayoyi daya bayan daya,sai da suka kwashi kusan awa guda sannan ta saurara masa,ta katse abun recording din nata ta jefa a jakarta,ta miqe tayi gaba abinta,saidai can qasan zuciyarta farinciki ne fal ranta,yau ta zauna daf da shi ta shaqi qamshinsa ta saurari muryarsa son ranta,shi kam bin ta yayi da kallo cike da mamaki da takaicin raininta don a gurinsa wannan raini ne. Zaman ta tayi cikin mota tana dakon zuwansu hafsat ⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜ Dukkaninsu suna gidan alh salim,kasancewar yau ake birthday din iftihal,rabi'ah sumayya farida da fadila anty hafiza sai anty hauwa'u(babbar yar haj maimuna)duk suna bedroom din momi,fadila na kwance bisa gadon momin,dakin ya kaure da hayaniya amma banda ita,sam gun ma baya mata dadi,tun jiya da Abba yayi mata da ya ahmad suka yi masu magana ita da farida kada su kammala attachment dinau ba tare da sun kawo mijin aure ba,farida kam ko ajikinta tunda dama irin wannan damar take jira ita da masoyinta mubarak Ta sake juya kwanciyarta hannun damanta kanta yayi mata gingirin zuciyarta a cunkushe,anty hafiza ta juyo ta kalleta "fadila ki saki ranki don Allah kiyi addu'a shine kawai mafita "fadila ta lumshe idonta hadi da sake qanqame pillow tana sake jin nauyi cikin qirjinta,anty hauwa tace "me ya sameta ne tun dazun na lura bata cikin sukuni",anty hafiza ta gaya mata hadi da cewa"na rasa irin farida kwata kwata bata kula kowa,nan da kika ganta bata da wani gwani"farida tace " anty itama fa da laifinta ya za'a ce duk mazan dake mutuwar sonta ace babu daya da ya mata"a fusace fadila ta kalleta😡"anty kinganta ko ko da ita ake magana?😫"dama zuciya kusa a kusa sai hawaye wani na bin wani😭"anty hauwa'u tace"duk ku tashi ku fita ku bamu wuri"tsam suka fice dakin ya rage daga ita sai fadilan sai anty hafiza,anty hauwa'u taja ajiyar zuciya tace"sai nake gano dacewa tsakanin fadila da Aliyyu Abban iftihal ba don kada nayi muku shishshigi ba da na hada wannan alkhairin"gabanfadila yayi matsananciyar faduwa💔 jin an ambaci Aliyyu,inama ace shine aliyyun da anty hauwa'u ke magana akai?,ina ma ace shine zai taho da neman soyayyarta?,ina ma ina ma.........taci gaba da zancen zuci Anty hauwa taci gaba da cewa"shima anyi anyi da shi ya fidda mata tayi aure ya qi,sai jiya ya kawo wata yarinya mai zubin yare ba alamun tarbiyya a tattare da ita wai ita yake son aura,hafiza yarinyar bata da maraba da matarsa ta farko,amma sai ya kakkareta da cewar wai zaman cikin yare ne yasa aka ganta haka amma da nutsuwarta. Fadila tayi hanzarin tashi don batason zancan da anty hauwa'u ta dauko yayi ma wani nisa,tayi qasa da idonta😪 tace"anty ba wai inason watsa miki qasa a ido bane a'ah,bansan ya Aliyu ba sani na da shi tun ina qarama ne wanda a yanzu na manta shi gaba daya,shima kuma nayi imanin ba sanina yayi ba,ba ta wannan ba anty a zamanin nan auren soyayyar ma ya aka cika bare auren hadi,matar cushe anty ba ta daraja,kawai ku tayani addu'a Allah yayi min zabi mafi alkhairi"suka amsa da amin suka kuma bar maganar suka shiga wata badan maganar ta bar ran anty hauwan ba Kwana biyu da yin maganar anty hauwa na juya maganar cikin ranta sai ta kasa hadiye maganar har sai da ta niqo gari ta dawo gidan don tattatunawa da abba"tana zaune gaban abban bayan sun gama taba hira tace"abba nazo maka ne ne da wata muhimmiyar magana"abban ya bada dukkan hankalinsa kanta sannan yace"uhm ina jinki maijidda"ta dora"abba kasan fadila 'yar abba abbas tafida?"yayi murmushi irin na manya yace"banda abinki maijidda idan ban san su farida ba ai kuma bansan kuba,"tayi dariya ita da momi tace hakane abba"tiryan tiryan take gaya masa halin da yanzu fadila ke ciki game da zancen fiddo da miji,sannan ta dora"abba inason ne na haska muku abinda tuna nina ya hasko min game da wannan lamarin""uhn"cewar abba,anty mai jidda ta dora"abba Ali ya kawo muku yarinyar da azahirin gaskiya baku yadda da halaye da nagartarta ba,ali abba ya riga ya fada soyayyar yarinyar wadda da zarar kunce zaku hana shi auren ta dama ce tq zo masa ta yaci gaba da zama babu zancen aure,zai kafa hujja da cewa ai tun tuni ya kawo ku kuka qi abun"abba ya gyada kai cikin gamsuwa maijidda ta dora da fadin"to abba mai zai hana ku bashi damar ya aureta amma abba ku hadashi da fadila?,abba kai ganau ne ba jiyau ba ka fini sani kasan fadila kasan irin kyakkyawar tarbiyyar da suke da ita,mai zai hana muyi kwadayin hada zuri'a da su abba?,abba kada mu bari ta subucewa family dimmu saboda fadila macace ta gari wadda nake da yaqinin samun alkhairai masu tarin yawa da zuriyya dayyiba tattare da ita?" Shiru sukayi gaba dayansu bayananta na ratsa su tabbas duk abinda maijidda ta fada gaskiya ne,sun gamsu matuqa da bayananta,abba yaji dadi matuqa sosai tare da sawa maijidda albarka gameda zurfin tunanin da tayi akan makomar rayuwar dan uwanta ⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜ Washegari alh salim da kansa ya taka ya nufi gidan amininsa alh abbas tafida,suna babban falon sa bayan sun gam gaisawa alh salim yace"abbas nasan zakayi mamakin ganina ko da daddarennan bayan jiya da azahar ma muna tare"alh abbas yayi murmushi yace ai nasan akwai dalili,kuma ma mene a aciki don dan uwa ya ziyarci dan uwansa aduk sa'adda da yaso?"alh salim ya gyada kai yace"hakane dalili ne kuwa babba ya taso da ni"alh abbas ya vyara zama yace"ina jinka Allha yasa lpy"alh salim yace"danka Aliyyu nazo nemawa auren'yata fadila"alh abbas yace"fadila?"ya gyada kai qwarai fadila ko anyi mata miji ne?"alh abbas ya girgiza kai yana murmushi yace"ko daya wlh,rigimar da nake ma da ita kenan a 'yan kwanakinnan kenan akan sai ta fito da miji,maganarka alh ta yimin dadi sosai wlh,amma ina fatan da amincewar alin?"a'ah ko daya wannan hasashe nayi na son hada zuriyya da aminina"alh abbas ya saki dariya yace"yayi wlh wannan tunani naka yayi kyau qwarai da gaske,domin samun nagartacce kamar Aliyuna a wannan zamanim abune mai matuqar wuya qwarai da gaske,fadila'yar ka ce halak malak kuma ko wani kaso bata wlh zaka iya bashi bate aliyu,na bawa aliyu ita har abada abokina"alh salim yace"a'ah abokina kada kayi saurin yanke hukunci ba tare da kaji ta bakin ta ba ka bari su gana taga idan har yayi mata"alh abbas yace"haba salim Haba salim yaya zaka ce haka bayan kasan yarinya budurwa ubanta ne ke da ikon zaba mata mijin aure ballantana duk yaron da zata zaba mawuyacine yakai nagarta da ingancin aliyyun,ai magana ma ta qare dama dab suke da kammala attachment dinsu nafison ace da zarar sun kammala su tafi dakunansu" Alj salim yaji dadin maganar yace"amma fa wani hanzari ba gudu ba,akwai yarinyar da aliyun zai hada su ya aura tare,to ya kamata a sanar da ita kasan yaran yanzu basa son abokiyar zama kaga ya kamata ta sani kafin ayi"alh abbas yayi dariya yace"shirmen banza ne iri na 'ya'yan yanzu zan sanar da ita kada ka damu,bamu buqatar duk wasu kaya na bidi'o'i"alh salim yace"a'a kaima ka sani momimta haj maimuna ba zata yarda ba yadda za'a yiwa dayar itama sai an mata"suka sa dariya gaba dayansu cikin farinciki,cike da godiya bisa karamcin da amininsa yayi masa"alh abbas yace ka daina godiya da Aliyu da fadila duk daya ne a gurina"alh salim yace"na sani amma duk da haka godiya ta zama dole duk wanda yayi ma jininka kyautar da sukutum da guda ai ba qaramin masoyi bane,cikin girmamawa da mutuntuna juna sukayi sallama Safiyya(mra muhammad bello) [10/16, 12:22 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 Wa yasan gobe? Safiyya Abdullahi musa huguma 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 ▶6⃣ Cikin daran alh abbas ya sanar da mai dakinsa,tayi murna qwarai don tasan amincin dake tsakanin mazajan nasu da irin tarbiyyar dake gidan alhj salim,sai dai tace wani hanzari ba gudu ba alhj ba lallai yaran su so junansu ba fa?,abba yayi dariya yace"duk soyayyar yqnzu shirme ce,ina soyayyar take zuwa?daga anyi auren ta mutu sai ki rasa ranar da tayi musu,wani auren hadin ba yafi qarko da albarka ba,ga auremmu ya isheki misali sai da aka kawo ki muka ga juna ko kin manta,gashinan haryau shekara kusan talatin da biyar ba fada bare yaji"ya dan kalleta ta sigar tsokana yace"nasan dai abu daya kikayimin kin shanye ni na kasa qaro miki abokiyar zama"kunya ta kamata tadan rufe fuskarta da tafin hannunta🙈tana cewa"kai alhaji"shina dariyar yayi😄 yana bude mata fuska yace"ai gaskiya ne" Misalin goma na safiyar washegarin ranar alh salim da kansa ya sanya aliyu a gaba ya tuqoshi zuwa gidan aminin nasa alhj abbas don kawo sadakinsa,aliyun yayi kyau abinsa cikin shadda gezna dinkin tazarce farace qal sai maiqo take,ya saye idanunsa cikin farin glass wanda bai hanaka tozali da farar qwayar idanunsa,takalminsa baqi ne na kamfanin batozi sai baqar hula duk da bai sanya ta ba tana riqe ne ahannunsa,kana nazaratar fuskarsa zaka karanci damuwa a tattatare da shi,sam alh salim bai bi ta kansa ba don yasan kwanan zancan,ya sani cewa gata ne yake son ya yiwa aliyun wanda ko bayan ransa zaiji dadinsa. A nutse yake murza sitiyarin motar har suka iso cikin gidan,alhj abbas da kansa ya fito yayi ma abokin nasa iso zuwa cikin gidan bayan sun gaisa da Aliyu suka barshi cikin motar,ya dan kwantar da kujerar motar yayi rigingine yana kallon yanayin ginin gidan, Alhj salim ya fiddo da daurin bandir na dari biuar biyar rafa daya ya ajjiye a gaban alhj abbas yace "ga sadakin aliyu ga 'yata fadila"alhj abbas yace "amma ai a yimin kara ko ni na biya ai"alhj salim yace"ni da kai ai duka dayane babu komai wlh"alhj abbas yace"Allah to ya yiwa auren albarka yasa ya zamo farinciki a gurimmu da gun yaran gaba daya""ameen"ya amsa masa"auren zai kama nan da sati shida dai dai lokacin da zasu kammala attachment dinsu"alhj salim yace"anya ba'ayi gaggawa ba?""wani irin gaggawa kuma me zasu zauna su yimin agidan ?"to shikenan abbas Allah yasa ayi a sa'a""amin dama ban sanar da yarinyar ba niyyata dama yau ta sani amma munyi zancan da mahaifiyarta,to tunda ga sadakinta ga kuma mijin sai a kirata tasan komai""to ba laifi"inji alh salim Tana ysaka da baccinta😴 taji ana dukan saman qafafunta,ta daga kanta idanunta cime da bacci tana kallon muhammad da ya tashetan cikin jin haushin tashin nata da yayi tace masa"meye?,ba nasha gaya maka idan ina bacci ka daina damuna ba"ya hade hannayansa 🙏🏻yace"am sorry anty,abba ne ke kiranki""abba kuma?😳"ta ta tambayeshi cike da tsoro saboda ta tuna agender su,ya gyada mata kai cike da tabbatarwa,tace jeka ina zuwa"tuni ragowar baccin da take ji ya gudu daga idanunta,ta dirgo daga gadon ta shige toilet ta wanke fuskarta tayi brush sannan ta dawo cikin dakin ta daura zani kan rigar baccin ta ta fesa turare sannan ta zira zumbulelen hijabinta mai hannu,a falo taci karo da umminta tana saka turaren wuta,ta gaidata sannan fuskarta kamar mai shirin rushewa da kuka😟 tace"ummi wai abba ke kirana"ta kalleta tace"to kije mana na ganshi da alhj salim"gabanta ya qara faduwa ta juya ta bar falon A salube tayi sallama a sitting room din,dukkansu suka amsa mata,ta samu gefan kujera ta gaida uncle abba(hka suke ce masa)kasancewar sun gaisa da abbanta tunda asuba,uncle abba ya amsa yana mai qara nazaratar nutsuwa da ladabinta,abbanta ya kalleta yace"fadila ina son ki bani aron nutsuwa da hankalinki "tace"to abba😔""kin sani cewa shekarunki sun isa ace kina dakin mijinki tunda an aurar ma da wadanda basu kaiku shekaru ba,sannan na baki dama ki fito da wanda kikeso kamar yadda qanwarki ta fiti da shi amma har yanzu baki cemin komai ba,na qyaleki har lokacin da nabaki ya qare ban tanka miki ba duk da cewa ina da iko in zaba muku miji amma na baki damarki "ta gayada kai "hakane abba yace"fadila"ta amsa "na'am""abbanki ya nemawa yayanki aurenki kuma na bashi"wata mummunar faduwar gaba ce ta risketa tamakar an daddaure jijiyoyin jikinta taji,hakan yasa ta kasa dago idanunta ta kalli kowa bare su fahimcin halin da ta shiga,ya dora da cewa "yanzu haka ga sadakinki a hannuna"jin hakan yasa ta qarasa rikicewa sauran dauriyarta tuni tayi qaura,addu'o'i ne barakatai suka dinga zuwa bakinta tanayinsu cikin zuciyarta,shikenan na rasa aliyuna?shikenan zuciyata ta rasa muradinta?shikenan mafarkina ya zama hasashe?,abinda take jujjuyawa kenan kawai a zuciyarta,duk maganganun abba ba wanda ta ji ko ta fahimta sai maganarsa ta qarshe wadda sauran qiris ta sa numfashinta ya dauke"kije kuga juna yana falon waje duk da shekarun baya kun sanshi amma saboda tsawon shekarun zaki iya mantashi ya kwana biyu baya qasar"uncle abba ne yayi saurin cewa"a'a saurara✋🏻ina da magana ke fadila gayamin gaskiya idan bakiso kina da wanda kike so"tabbasa da zata iya da ta fayyace musu sirrin dake zuciyarta ko zasu tausaya mata su bar zuciyarta taji ma da masifar da take ciki,amma ko kusa batajin zata iya kunyata abbanta,bayan ya isa da ita yana da iko da ita fiye da yadda take da iko da kanta yayi mata komai a rayuwa ya bata dama masu yawa a rayuwa irin wadda kowane mutum ke son samu,duk ma a ture wannan gefe baza iya daga iso ta budi bakinta tace da aminin mahaifinta wanda yake tamkar uba a gareta cewa batason dansa jininsa ba,hakan yasa tayi saurin girgiza kai tace"ko daya abba na gode da zabin da kukayimin,Allah ya saka muku da alkhairi"ita kanta ta jinjinawa kanta kan namijin qoqarin da tayi na furta haka,uncle abba har zuciyarsa yaji dafi matuqa tare da sake gode ma allah da zata zamo daya dqga cikin ahalin gidansa,albarka suka sa mata sannan abbanta ya umarceta taje su gana Takai kusan minti biyar a qofar sitting room din ta kasa shiga,gaba daya a rude take zuciyarta a cunkushe take,daga qarshe taga tsayuwar batada wani amfani don haka ta tattaro dukka nutsuwarta da dauriyarta ta kutsa kai hade da sallama kanta a qasa😔 ta lalubi kujera daya ta zauna cikin fargabar wa zata daga kai ta gani,muryar da taji ta masa mata ita ta razanata da sauri ta dago kai ta gani ahin da gaske ne ko kunnuwanta da zuciyarta ke yaudararta yadda suka saba?idanunsu suka hadu da juna👀 wanda hakan ya tabbatar mata da tsammaninta,ba qaramar razana tayi ba duk da bata nuna hakan ba,A.s mai tama Aliyyun uncle Abba?,take ta jera sunayan a zuciyarta,komai tsaya mata cak yayi,tunaninta ya kasa gaba ya kasa baya,shiru daki ya dauka ba wanda ya tankawa dan uwansa wanda hakan ya sanya fargabarta daduwa,bata kuma sake kallonsa ba bare taga a wane irin yanayi yake ciki ba,sun jima a haka sannan ta jiyo alamar miqewarsa,har ya kai bakin qofa yayi taku uku ya dawo da baya,kallon nan nasa da ta fari gani a qwayar idonsa ta kuma tsaneshi shi yayi mata sama da qasa sannan yace cikin izza da qasaita"ban iya qarya ba kuma bazan fara taba saboda ke,bazan iya tafiya ban amayar da binda nake ji cikin zuciyata ba,bakimin ba baki dace dani ba,baki ma dace da tsarin rayuwata ba,ke da kanki shaidace ce idan dq zaki iyq yiwa kanki adalci bamu dace da juna ba,baki ma da zubi da tsarin da nake so gun mace,idan banda tsaurin ido ma irin naki taya zaki hada kanki da ni?kinga nayi kala da ke?gaskiya kin cuceni,god forbid ki zama matata,kada kuma ki soma yaudarar kanki ta hanyar zato ko tsammanin nan gaba zan iya sonki harki cuci kanki ki aure ni,wannan maganan daga cikin zuciyata direct take fitowa  Wani mugun takaici da baqinciki ne lokaci guda ya rufeta,tunda take babu wani da namiji da ya taba mata munanan furuci makamanta wannan,ta tuna uawan samarin da ke kara kaina a kanta,samari masu ji da kudi kyau nasaba isa da qasaita,ba wanda ta bawa dama a cikin su,wasunsu dama suke so ta basu koda ta friendship ne amma basu samu ba,samari da dama sun sha kuka a gabanta kan ta mallaka musu zuciyarta,amma yau wani daya daga cikin jinsin maza ke gaya mata wadannan kalaman,ji take a rqntq matuqar ta barshi ya tafi haka ba ta da ta mayar masa da martani ba wanda zai dade yana cizon zuciyarsa ba to ba shakka tayi faduwar baqar tasa"hey🙋🏻"tace da shi sanda ya sanya kai zai gice daga falon,ta miqe tsaye ta yi masa kallon sama da qasa ta yatsina fuska😏 ta tofar yawu a gefanta sannan tace"see you wane mashahurin maqaryacin ne ya gaya maka ina maraba da kai da zaka zo kanata soki burutsu,ni dinma ba yimin kayi ba don baka wuce dan aiken gidana ba a tsarina,amma ni nasan darajar dan adam banga a gidammu ana tozartashi ba kuma na iya darajatta zancan magabata na shi yasa ban tozarta mutumin da mahaifina ya zabamin ba,idan banda qaddar ina budurwa sabuwa dal a leda mai zanyi da bazawari ragowar wata.......... Wata iriyar wafta ya kawowa bakinta wanda ta tabbatr da ya sameta sai lebunanta sun fashe,da gudu ta bude daya qofar falon da zata kaita cikin gida ta baya ta shige ta bankowa aliyu qofar ta batshi tsaye zuciyarsa kamar zata fito saboda fushi,ya ga alamar akwai rainin wayo tattare da yarinyar,yayi qwafa cike da zafin zuciya ya fice,kai tsaye daķinta ta nufa ta kulle qofarta gam tayi zaman dirshan saman carpet dinta,wani irin kuka ta saki😭tayi qasa da kanta😪,ta rasa me zayayi farinciki ne ya kamaceta ko baqinciki?ta jima a zaune tana kukan tate da tambyat kanta da kanta shin dama baqinciki da farinciki na haduwa lokaći guda cikin zuciyar bil'adama?yau kam ta fahimci hakan na faruwa tunda gashi yau ta tsinci kanta a ciki Aliyyunta mafarkinta na kullum?burin zuciyarta muradinta yau shine zai zama mijin aurenta babban burinta kenan dama anan duniya,sai dai kash yazo mata ta wata iriyar fuska da sigar da bata tsammatar mata ba,baya sonta baya qaunarta abin har ya kai tsananin da bazai iya boye qinta a zuciyarsa ba harsai da ya tsaya a gabanta ya fesar mata,baya ga haka ba ita kafaice zata zama mallàkinsa ba?zata yi sharing aliyunta da wata?ga ahi har waya ma ta rigata samunshi(maman iftihal) Da qyar ta iya janye jikinta ta gada saman gadonta,ba abinda ke mata amsa kuwwa akunnenta irin kalaman aliyu,kafin azahar zazzafan zazzabi ya rufeta,sau biyu farida na shigowa dubata tana ganinta a duqunqune tayi tsammanin bacci take,a shigowarta ta uku ne tace"kai yaya fadila wani irin bacci ne haka tun ten o'clock har one thirty?"tasa hannayenta ta janye bargon tana fafin"ba sanyi ake ba ba komai ba kuma kin....... maganar ta maqale mata sanda idonta yakai kan fadila ta zaro ido😳 tana cewa"kinga idonki kuwa?"ta juyar da idonta daya side din sannan tace"kaina ke ciwo" Mrs muhammad bello ✍🏻✍🏻✍🏻📝📝📝 [10/16, 2:39 PM] ‪+234 706 914 1005‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 Wa yasan gobe? Safiyya Abdullahi musa huguma 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 ▶7⃣ Fadila ta juyar da kanta daya barin tace"kaina ke min ciwo"farida ta gefanta ta zauna tace"kinyi dai kuka wanda ya haddasa miki ciwon kai,sis ni 'yar uwarki ce,bai kamata ki dinga boyemin wasu abubuwa da ya kamata ace na sansu ba,yadda nima bana boye miki komai bana boye miki damuwata nake neman shawar warinki akan komai,ko dan tsokanarki da nake ne yasa kikemin kallon am too young?,komai ai da tym dinsa,amma idan kina ganin na takuraki am sorry sister"ta fada tana shirin tashi,sai ta bawa fadila tausayi,farida na sonta sosai,tana damuwa da damuwarta any time,ta riqo hannunta tace"is not lyk dat sister baki takurani ba,I will tell yuh everything,but b4 den bani paracetamol nasha,and kimin alqawarin daga ni sai ke babu maijin wannan sai wanda na amincewa hakan"ta gyada kai tace "I promise sister" To fadila dai sauqi bai samu ba har sai data kwana biyu a kwance tana jinyar jiki da zuciyarta sannan ta samu qwarin jikinta da taimakon farida ta hanyar bata shawarwari da kwantar mata da hankali,ba abinda ke sake daga mata hankali irin lafuzan da suka fito daga bakin abinda tafi so a duniyarta har yau sunqi bacewa daga dodon kunnenta ⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜ Yammacin talata ne wanda ya zamto dukkaninsu suna da abinda za suyi cikin makaranta don haka suka tafi a amota daya suka kuma dawo tare kasancewar lokaci guda kowacce ta gama uzirin da ya kaita,tare sukayi sallama suka shigo suka tadda umminsu a falo ita da muhammad dake gefanta yana ta kumbure kumbure,ta musu sannu da dawowa suma suka mata sannu da gida sannan suka haura samansu kowacce ta nufi dakinta don watsa ruwa,farida ta riga fadila kammalawa har ta sauko ta shiga kitchen ta ciko plate da couscous da vegetable soup wadda ta wadata da hanta,fadila ta sauko sanye da pakistan riga da wando irin shigar farida kenan saidai bambancin colour na fadila dark pink ne na farida kuma light blue Itama kujera ta samu dake kusa da ummin ta zauna,ta dubin sashen da muhammad yake wanda tunda suka dawo ya musu sannu da zuwa bai qara cewa qala ba tace"ummi halan yau akwai abinda ke damun parrot dinki naji yau gidan so silent gwanin dadi ba hayaniya"ummi tace"rabu dashi,haka kawai yazo ya tarar dani ina kallon labarai shi wai dole sai ba canza masa tasha zai kalli qwallo"farida ta kalleshi"meye amfanin t.v din dakinsa"ummi tace"duk yabi ya lalata socket din dake dakinsa wai shi koyon gyara an canza masa wasu ya sake kuncesu to ba sai yaje yayi ta yi ba nidai ba mai takurani ni da falona idan mutum yaji haushi ya tashi ya bani guri"ta fadi hakane don dama ya isheta ta koreahi tun dazun yaqi tafiya,ai kuwa ya tashi ya bar fallon yana shirin sa kuka,fadila ta gimtse dariyar dake son qwace mata don tsakanin ummin da muhammad ba'a shiga tasan kuma nan da anjima shi zata lallabo tace yayi mata tausa,fadila tace"ummi mun hadu da haj barira fa?"ta juyo ta dubeta tace "a'ina?,dama tana gari ne uwar tafiye tafiye?"farida da takai lomar abinci bakinta ta karbi zancan"a danja ummi,danja ta tsayar da mu sai da tasa mukayi parking gefan titi,farida ta qyalqyale da dariya😂 tace"kai matarnan ummi Allah ya zuba mata surutu"ummi ta mata daquwa tace"ungo wannan mamarku ce,da Allah yayi ma ke farida ai da tuni ta zama surukarki"farida ta sake kecewa da dariya😂ta kama haba tace🤔"Allah ya tsare,wai shi abdus-samad ma idan banda abunsa ummi qawata fa rumana yace yqna so amma don ya raina ni yaje ya cewa hajiya ni yakeso,ni bansan ma inda tasan labarin bikimmu ba take tambayata nace mata saura three weeks,ai kauwa har zancan abdus-samad din.ma tayimin wai na dai qishi"ummi tace"ato kunya ma ta isheki" Ummi ta juya ta dubi fadila wadda ta zubawa t.v🖥 ido tayi shiru tana sauraransu ,duk da fadila miskila ce amma ta sake zama so quiet fiye da da,ga wani rama da take dan kumarin da a da take dashi yanzu ya zabge babu shi duk a cikin kwanakin ummin na ankare da ita,abun ya dameta sosai har take sanar da abbansu,ya kwantar mata da hankali ta hanyar cewa"kada ta damu ai dama yawancin 'yammata idam aurensu ya taso gadan gadan hakan na faruwa sai tace amma ai bata ga hakan a gun farida ba yace mata ai kowa da irinshi wani ma qiba yake yi maimakon rama,ummi ta yanke tunaninta tacewa fadila"ki shiga kitchen ki sami abinci ki ci"ta dan noqe kafada "ummi sai anjima"ta bata rai😠 tace"wani anjiman kuma?,kinga tashi ki debo abinci kici tun kafin ranki ya baci"tasan ummi ba wasa don haka a kasalance ta miqe ta nufi kitchen ummi tace mata"ki taho min da kunun aya" Taliya ta zuba da miyar kifi(haka umminsu take gwanar girki shi yasa da wuya kaje gidan ka tadda abinci kala daya a kitchen dinta takanyi kamar kala biyu dai dai yadda zasu iya cinyeshi)kusan sili dai dai fadila ke zara tana ci ummin na kallonta tayi banza da ita,yayin da farida ke mata kallon tausayi😒, Wayar ummi ta soma ruri alamun ana kiranta tasa hannu ta qmsa hadi da yin sallama,"haj maimuna lpy lau........lpy qalau wlh........ah mun gode Allah"fadila dake gefe gabanta ta fadi ta tabbatar kiran daga mahaifiyar Aliyu ne ,ko yaya ta ji wani abu da ya danganci gidansun sai ta shiga fargaba,tana tsoron mai zai biyo baya ne a nan gaba?. Tsinto.muryar ummi tayi tana cewa"yanzu da nufinki haj sai dai naji a gari?ai Aliyu dana ne don zai auri fadila sai na kasa zuwa rakiyar lefansa gidan wasu?ita fadilan ba'a zuwa kaiwa za'a zo kawo nata Wata mummunar faduwar gaba ce ta shigeta,lallai ya tabbata Aliyu nasu ne ita da wata,ji tayi wani daci ya mamaye mata halshenta abincin ya qarasa ficewa a aranta don haka ta zame ta shige kitchen ta maida shi cikin cooler ta rufe,taja plastic din kujerar dake kitchen din wadda sukan ajjiye saboda zaman aiki ta zauna a kai,daganan din tana iya jiyo muryar ummin nata na mata sallama tana cewa"Allah ya kaimu goben,Allah ya nuna ma..........bata qarasa ji ba tayi saurin saka hannunta ta toshe kunnenta qwalla nabin fuskarta😢 ⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜ Washegari gaba daya jikinta a mace yake murus ta kasa fita ko ina tana kwance a daki komai ya cakude mata,har la'asar tayi ummi ta shirya tacewa farida itama ta shirya ta kaita tana jiyo farida na mitar ita fai bazata ba ummi idris kawai ya kaiki,"kinci uwaki ja'irar yarinya to naqi idris din ya kaini ke zaki kaini idan kuma ba zaki ba bani maqullan ni nayi driving din da kaina",haka farida ta shirya babu son ranta suka fita sukabar fadila ita daya a gidan,fitarsu sai taji kamar an qara mata kasalar,kimanin awa guda da tafiyar tasu tajiyo sallama daga bakin falon qasa,ta miqe ta yafa mayafinta ta fito bakin verandar saman benan sani mai gadinsu ne yace"uwar dakina yallabai ne yazo"gabanta yadan fadi saboda wanda zuciyarta ke raya mata shine"wanne yallabai?"ta tambayi malam sani ya saki dariya😃 yace"yallabai Aliyu jan zaki"tayi jim kamar tace baxata ba,sai kuma ta tuna da maganganun da Abbanta yayi mata daran shekaran jiya ta juya ciki tana cewa"kace ya jirani ganinan zuwa"bata wani jima da yin wanka ba don haka body spray ta fesa ta dauki hijabinta ta sanya ta zura slippers din wankanta ta fito,yana cikin sitting room din bakin get,ya dan kashingide akan kujera three sitter waya yake da alamu kuma yana jin dadin wayar don har wani lumshe idanunsa yake,bata ce uffan va ta samu gu ta zauna zamanta da minti biyar ta fuskanci da wadda yake wayar jin zancan wadanda suka tafi kai.lefe da yayi,ya doshi kusa minti ashirin yana wayatsa ba abinda ya shalleshi kamar shi kadai ne a dakin sanann ta jisu suna sallama da juna cike da tsantsar soyayya,wata allurar kishi ce ta soketa ta kauda kanta gefe tayi kamar batasan budurin da yake ba, Bayan ya kashe wayar sai shiru ya baqunci dakin,bakajin motsin komai sai qarar a.c "ke"taji yace,banza ta masa kamar ba da ita yake ba taqi ko da kallon sashinsa,taji ya sake cewa"da ke nake"ta dago ta watsa masa wanu kallo na baka isa ba,bata mai da kanta ba taji yace"baki isa na roqeki ba amma ina baki shawara da umarni kije kice bakya sona,idan ta kama ma zance miki please ko dan nima ki barni in samu peace of mind da wanda nake son aura"sai taji zuciyarta ta karye gaba daya tausayin kanta sai ya kamata lokaci guda,tabbas aliyu baya qaunarta ko qanqani,batasan sanda hawaye ya subuce mata ba,ta sake tabbatarwa da kanta so bala'ine kuma masifane,haqiqa tana cikin jarrabawa mai girma,musamman irin wannan son na SON MASO WANI,sai taji bata da wani zabi da ya wuce ta tashi ta bashi guri,ta miqe tsam ta fice tana lalauben hanya,tabbas ba shakka yau da ita ta zabawa kanta Aliyu ta tabbatar da a yau ta rabu da shi koda sonsa ai zama ajalinta,da kuna zata iya duban mahaifinta ta roqeshi ya janye maganar aurensu da Aliyu da tayi hakan ta jima tana kuka a dakinta sanann daga baya tabi ahawarar da zuciyarta ke bata na ta nemi matemaki mana a cikin lamarinta?,ta wanke fuskarta ta shafa hoda ta zizara kwalliya a idanunta donbta rage musu kodewar da sukayi,after dress ta zira ta dauki key din motarta,tana saukowa taci karo ba daqar leda a falon,bata bi ta kanta ba ta fice,tana bude motar ta ta dannawa mlm sani horn akan ya bude mata qofa sai da tazo saitinsa sannan ta tambayeshi wa ya shigo falo da kaya?"nine yallabai ne yace a kawo miki,inata sallama ma naji ba'a amsa ba sai.........,ta daga masa hannu kawai ta fice Cikin minrina qalilan ta isa gidan ya ahmad saboda gudun da ta tsula anti hafiza na falo ita da biyunta taganta tamakar wadda aka jeho ta zube a kujerar falon tana haki sai kuma qwalla ta fara sintiri a fuskarta,kallo daya anty hafizan tayi mata ta tabbatar ba lafiya ba ta cire yan biyu da suka zube jikin fadilan sunata murnar ganinta ba tare da lura da halin da take ciki ba,ta kiu ra maqociyarta zainab tace ta turo 'yar aikinta ta wuce dasu gidanta tayi baqi Kusa da ita anty hafizan ta zauna ta kamo hannayentabta riqe sannan tace"lpy me ya faru haka?"fadika ta sake fashewa da kuka tana cewa"na shiga uku anty,innalillah,anty zuciyata bata yimin adalci ba ta jefana cikin mawuyacin hali,anty ki taimakamin,me yasa zuciyata ta yimin hka anty?why?why?, Anty hafiza ta dafa kanta tana shafawa tana cewa"calm down ki nutsu ki gayamin meke faruwa?" Tasa bayan hannunta tana share hawayen dake kwararo mata sannan ta saki ajiyar zuciya tace"anty tun kafin na San shi waye zuciyata ta dade da kamuwa da matsananciyar soyayyarsa💘,tun daga lkcn na rasa sukuni a zuciyata kwata kwata,kullum kwanan duniya qaunarsa na qara ninkuwa ne a zuciyata kamar jaraba abun,ina cikin wannan haline muka fara face to face da shi saidai abu na farko da ya fara shiga tsakaninmu fada ne,hakan ya zamana har zuwa lkcn da mahaifin Aliyu salim maitama ya nema masa arena gun abbammu ba tare da nasan shine ba,na shiga matsananciyar damuwa😣 a lokacin da ta bayyana an bada arena ga wani,sai dai sanda nayi tozali da aliyu a matsayin wanda aka bawa ni sai farinciki😊 ya mamaye damuwata Sai dai kuma me?anty ga tarin mamaki na sai kalaman qiyayya suka zamo kalaman farko da na fara samu daga masoyina,kalaman da suka kusa tarwatsa zuciyata💔,qarara aliyu ya nunamin bai qaunata ba nice choice dinsa ba samirah ce muradinsa,meye aibuna naty?wane naqasu nake da ahi wanda ya janyo aliyu ya tsaneni?ban can can ci so bane daga gurinsa bane anty? Aliyu yana sonki zai kuma soki fafila"ta fada tana girgiza kafadarta,kukanta ya tsaya cak sai hawaye dake shatata ta ski baki tana kallon anty hafizan da itama ido ta zuba ma ta tashiga girgiza kai tana cewa"bazai soni ba naty baya kuma sona din ya fada anty da bakinsa fa yace"kada nasan ran wata ran zai soni"anty hafiza tayi saurin tarar numfashinta tace"✋🏻ke da'alla can rabu da shi shike da kansa?WA YASAN GOBE?ai sai allah"ta karyar da kai cike da neman agaji da mafita😧"amma anty haka zamu rayu da shi?rayuwar aurece naty wadda ba yau ko gobe za'a yita a watse ba" anty hafiza tayi murmushi😊 tace"ki kwantar da hankalinki,abu na farko da nake so gareki shine ki miqawa allah lamuranki babu abinda ya gagari allah,abu na biyu ki zamo mai juriya haquri gami da kawaici ki zamo mai controlling din anger dinki ,ni kuma insha 'allah nayi alqawatin doraki akan step na gaba,nayi alqawarin baki shawarwari na gari harsai inda burinki ya gama cika Cikin hikima da dabara ta zauna tana bude mata babi babi na hikima da dabarun zaman tare gamida kwantar mata da hankali har fadila ta ji nutsuwa ta shigeta tace ni anty abinda ke dada tayr min da hankalin ganin yadda nake jin zallar soyayyarsa a zuciyata to shi haka yake jin zallar qiyayyata"tave cool down sister na gaya miki kada ki damu irin wananna ita take fa juyewa wata rana ta zama zazzafar soyayya ke dai ki dinga yiwa soyayyar tasa linzami kada ki bari ya fuskanci akwaita a ranki don kada ya samu jin dadi da sakewa na wulaqantaki harsai lokacin bayyanatan ya yi Daf da sallar magariba yaya ahmad ya dawo bayan sun gaisa yake zolayarta"lpy kuwa amarya nàga tana ta qarewa haka?"tayi murmushin yaqe tace lpy lau yaya"anty hafiźa tayi saurin tare tambayar ta hanyar cewa"abban twince aì kasan fama haka na faruwa ga mutum idan aurensa yazo"ya girgiza kai xikin gamsuwa da bayaninta yace"hakane aure yaqin mata,Allah yasa ayi a sa'a"anty hafiza ta masa amin Bayan isha'i tayi haramar tafiya bayan anty hafiza ta tsareta dole ta sata cin abinci ,antyn ta rakota bakin mota tana sake kwantar mata da hankali fadilan ta dubeta tace"anty unason don Allah ya zama sirei wannan zancan""haba fàfila kada ki damu dake da aysha daya nake daukarku(qanwarta ce aysha)fadila tace anty na gode Tana driving tunani ne fal cikin ranta duk da tana jin ta samu relief sosai cikin ranta,ita kanta mamakin kanta takeyi tasha jin yadda mata 'yan uwanta ke yaba kyau da ajinta👰🏻 bare maza wadanda ita kanta batasan adadin masoyanta na dili da na bòue ba wadanda ke jatumtar sanar da ita da wadanda take musu kwarjini suke batin abuna zuciyarsu,wadanda ke kuka akanta bazata.iya tuna yawansu ba don ita dama Allah bai dora mata kule kulen samari ba amma yau kamar almara sai gata a wata wawakekiyar qofar jarrabawa,ta saki ajiyar zuciya sanda ta iso bakin get din gidan malam sani ya budw mata qofa ta shige ta tsaida motarta bayan ta daidait parking,a gefabta taga motar farida hakan yasa ta gane sun dawo,ta saki doguwar ajiyar zuciya tafito daga motar ta kulle ta tunkari falon nasu MRS MUHAMMAD BELLO ✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻📝📝📝 07066139278 [10/16, 2:39 PM] ‪+234 706 914 1005‬: 8:39 pm 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 Wa yasan gobe? 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 Written by safiyya Abdullahi musa huguma ▶8⃣ Bata nemi kowa ba kai tsaye dakinta ta nufa ta shiga wanka ta hado da alwala ta gabatar fa shafa'i da wutirinta tunda tun a gidan ya ahmad tayi isha,ta dauki kimanin minti goma ta azakar dinta sannan ta ninke sallayar ta sauko qasa ta nufi dakin ummi,ummin ta amsa sallamar bayan ta mata sannu da zuwa ta sanar da ita anty hafiza na gaisheta ummi tace "kinje kenan?"ta gyada kai tace"bayan fitarku ne ummi gidan shiru ba dadi😒shine nace bari kawai na leqa biyu"har ta bude baki zata mata fadan fita ba tare da ta tambayeta ba sai kuma ta tuna fadilan ba gwanar yawo bace banza bata kai zomo🐇kasuwa,ta tabbatar ba'a banza ta fita ba,dama farida ce to tasan hali,sai kawai tace"ina amsawa"fadila tace "ummi bari na wuce na kwanta na gaji"ta dubeta tace"au yau ba zaki jirayi dawowar abban naki ba?"ta gyada kai"um ummi abincinsa na dining area na parlour dinsa ni dai sai da safe"ta miqe ummi tace"Allah ya tashe mu lpy nima wanka zan shiga ki jamin qofar"tana qoqarin fita taji ummi ta kirayeta ta dawo da baya tana amsawa"bayan fitata wa ya kawo kaya a baqar leda suna nan a parlour?",sai a sannan ta tuna da kayan da aliyu ya aiko a kawo mata,ta sunkuyar da kanta😔tace"ummi yaya aliyu ne ya kawo to sai na mantasu a parlour"ummi ta gyada kai tace"yayi miki kyau,fadila ki maida hankalinki fa,gidan kishiyafa zaki,ba ke kadai zaki zauna ba ballantana kice zaki dinga abinda ranki keso......ta danyi jim,jin fadila bata ce komai ba ta Dora"sai kije ki debe tun kafin abbanki ya zo ya gani ranki ya baci"ta qarasa maganar tana shigewa bandaki ,jikinta a salube ta fita,ta isa inda ledar take ta dauke ta tayi sama da ita Hannu biyu ta tallafe habarta da su ranta a jagule,yaushe su ummi zasu fahimci tsananin da take ciki?,har ga Allah tana son ali yana burgeta a rayuwarta komai nasa yana bata sha'awa,yau da za'a ce aliyu yana sonta a sai ta fi kowa farinciki,to su su ummi suna tsammanin ita ke son kawo cikas,ta share hawayenta ta daga ledar tana zazzage kayan ciki Bandir ne na 'yan dubu dubu sababbi fil a miqe💶 guda hudu sai chocolate packet hudu manya🍫,sai turare guda hudu designers,sai awarwaraye banguls da zobensu na gold guda biyu💍,sai agogon hannu na azurfa guda biyu shima,komai tsada ne da tsari,cikin zuciyarta take fadin"yadda Aliyu na ke da kyau da tsari haka everything na shi yake,yadda aliyu yake special haka komai daya dangaceshi yake,komai nashi special one ne hakanan abun ban sha'awa ne,ina ma aliyu zai soni?,ina ma Aliyu zai rufeni da da so da qaunarsa da na zamo daya daga cikin mata masu tsananin sa'a a rayuwarsu"hawayen tausayin kanta suka ziraro mata,ta dauki daya daga cikin rapper din kudin tana shinshinawa,ta lumshe idonta don qamshin turarensa kawai ke tashi a jikinsu(haka aliyu yake saboda yadda turare ya zaunar masa a jikinsa duk abi da yayi gogayya da shi sai yayi qamshin turarensa) Farida ta shigo dakin da sallamarta,fadila ta amsa tana janye mata kayan dan faridan ta samu gun zama,cikin tsokana faridanke tambayarta kayan,tace"duba ki gani ya Aliyu ne ya kawo dazun ki zabi abinda kike so(haka ummi ta koyar da su tun suna qanan idan daya ya samu abu to zai raba tare da dan'uwansa )ta yaba kayan sosai ta dauki turare biyu tace sun isheta,fadila tayi tayi da ita ta qara taqi,ta turo mata kudaden gabanta hadi da yage 'yar paper da taga anyi rubutu a jiki kamar haka"kiyi hidimar biki idan basu isa ba zansa a adado miki"tadan tabe baki ☹cikin ranta tace"nafi buqatarka da su da zaka gane hakan""farida ga kudin hidimar bikinan inji aliyu idan basu kai ba a mishi magana"farida ta dauki kudin tana juyawa tace"har dubu dari hudu😳"fadila tave"hmmm ni da ua ban su nasan mai zanyi ma da su"farida tace"ni da anty hafiza munsan me zamuyi miki da su,ko iya wadannan ma sun isa ya sallameki"ta miqe tana cewa"bari in nunawa ummi,sai da safe sister"ta fita taja mata qofar tana ayyana abubuwan da zasu yiwa fadilan masu amfani ⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜ Duk cikin satittikan da suka biyo baya cikin hidamar shirye shiryen biki suke,ita kam fadila bata da wani zabi na kanta,da zasu yarda ma da sun qyaleta haka don bata da sha'awar yin komai kama daga gyaran jiki zuwa kan duk wasu events da ake yi yayin bikin aure,don duk abinda zatayi wanda za'ayi don shin abun bai dada shi da qasa ba baya gabansa hakan yasa itama ta tsani komai,sai da anty hafiza ta zaunar da ita ta nuna mata duk abinda tayi idanun👀 duniya na kanta,zata tona asirin kanta da kanta ne sannan ta amince da tsare tsaren da suke zuwar mata da su,hatta magunguna tanajin farida na sha da qyar tana mita ita kam nata ido👀karba kawai take ta daddake tunda tana ganin babu wani amfani da zasu yi mata To fa masu karatu ga fadila Abbas na shirin shiga gidan Aliyu salim maitama,gidan da aka gargade ta da shigarsa tun kafin ta kai ga shigarsa,shin mene shawararku gareta???? 10:34 pm 07066139278 ✍🏻✍🏻✍🏻📝📝📝📝 🌺🌺🌺 [10/16, 12:25 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 Wa yasan gobe? 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 Written by safiyya Abdullahi musa huguma 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 ▶9⃣ Ranar laraba 12 ga watan biyu aka soma da kamu👰🏻,ba dan qaramin kyau amare sukayi ba,kai kaso kazo kaga yadda kamun ya qawatu matuqa da gaske,an zubar da dukiya sosai kasancewar wannan ne bikin ummi na farko kuma na qarshe,tamakar tagwaye haka suka zama komai iri daya suka sanya hatta da awarwaro da zobe Kasancewar abban su babar bare umminsu bafulatana sai aka raba abun biyu shigar farko sukayi shiga irin ta bare bari cikin wata lafiyayyar lafaya wadda kudinta ya tasamma kimanin dubu ashirin kamu aka musu irin na bare bari sosai sannan daga bisani kuma suka canza shiga irin ta fulani cikin kayan saqi nan ma aka musu kamun fulani,shida na yamma aka tashi bayan sallar magariba kuma masu kidan qwarya suka zauna zuwa goma na dare Irin cikar da gidan yayi yasa su fadila haqura da zaman gidan su da qawayansu suka koma gidan maman zainab maqociyarsu ce kuma babbar macace don idan batayi sa'ar umminsu ba to zata girmemeta,zainab din yarinyarta ce kusan sa'ar farida ce Fadila nabin kowa da ido don a yanzu kam jikinta ya qarasa mutuwa murus,bata da kuzari ko qanqani komai cikin dakiya da qarfafa mata gwiwa da anty hafiza ke mata take yinsa,ga wani ciwon kai da ya addabeta,ta riga ta saba ita ko da can bata saba da shiga hayaniya ba ko bikin dangi ne bata kwana sai dai farida ta kwana ita kam komai dare zata dawo gida ne,ko hayaniya tayi mai yawa to yanzu kanta zai fara ciwo ko qirjinta ya dau zafi Kwance take kan gadon zainab din ta juya ma tarin 'yammatan dake dakin sunata hayaniyarsu baya ta fuskanci fuskar gadon,yawancinsu duk qawayen farida ne sai 'ya'yan 'yan uwa,farida tayi sallama ta shigo dakin ita da aminiyarta ruqayya hannunsu dauke niqi niqi da ledoji na take away wanda aikin mubarak(angon faridan) ne shi yace a tazo suje tayi musu take away,ta zube musu nan hayaniya ta qaru kowacce tana daukar tata,ta iso kan gadon hannunta da ledoji biyu,ta dan taba qafafun fadilan tace"sister tashi"fadila ta miqe daga kwanciyar ta zauna tsakiyar gadon ta tanqwashe qafafunta tana kallon farida,qasa-qasa muryarta tace "yayaa ga abinci ki daure ki ci sai ki sha maganin ciwon kan ko dan idon mutane ida yaso sai ki kwanta ki huta,"tana maganar tana bude ledar da ta shigo da ita din ta tura mata gabanta,ta sake bude dayar ledar tana cewa"ga dinkimmu na dinner din gobe ta can muka biya da mubarak muka maso"ta soma fito da su Wani dan ubansun material ne mai azabar kyau wanda ko makaho ya shafa yasan cewa ba qananan kudade aka sa aka siyeshi ba,milk ne da ja(milk and red),ita kanta faridan da tunda ma anty hafiza ta bawa ya ahmad da zashi india ya siyo musu bata ganshi ba sai yau da aka karbo dinki faridan ce ke zuzutashi sai yau taganshi yayi bala'in tafiya da ita ,ta jinjina kak tace"an gode miki sister farida"farida tayi dariya tace"ai wannan aikin anty hadiza ne ragowan su earings ma da zamu sa suna gunta"fadila tace"Alla ya saka mata da alkhairi"ta jawo ledar da faridan ta bude mata,gasashshiyar kaza ce🍗 da hanta wadda aka mata gashi mai ruwa ruwa da albasa,shawarma🌮 sai kuma ice cream roba biyu🍧🍧,tayi murmushi ta kalleta kafin tave komai faridan ta rigata magana"ke dai yaya ki ci kawai,kina tsammanin bansan abinda kime boyewa bane a dan qaramin fridge dun gefan gadonki ba wanda ke hanaki maida hankali kici abinci?☺"sai dariya ta kama fadila,lokaci guda kuma tausayin rabuwa da junansu da qaunar 'yar uwarta ya kamata,lallai ne dan uwa rabin jiki,naka nakane qwalla ta ziraro mata ita ma faridan sai ga qwallar,dai dai nan rumasa'u(yar qanwar umminsu ce(ta shigo dakin,ganin haka ta saki dariya"😄a'ah kaga twince sisters wato ku daga fara biki har kun soma gunsheqen kukan rabuwa tun kafin aje ko ina?"yawan hayaniyar da yammatan keyi ya hanasu jin abinda take cewa,farida na dan murmushi ta goge hawayanta,ita kuwa fadila da yake sa'annin juna ne saita harareta"to ina ruwanki 'yar sa ido?"cikin dariya tace"🤗a'ah Allah ya huci xuciyarki bani na kar zomon ba ratayar ma ba'a bani ba ni ummi ce ta turoni tave inzo inga kinci abinci don tasan hali"ta fada tana leqen ledar gaban fadila,fadila ta muwa lanqwashe ledar,tana cewa"kuma duk kwadayin mutum bazaici ba ba?"cikin son zolaya rumasa'u tace"haba aminis ni dake fa bata baci"fadila ta zaro kazar ta nannde mata tace "ungo a banni na hadiyi yawu"tafice tana dariya,farida da tun dazun take ta musu dariya tace"hoo 😂yaya ruma akwai zolaya da abun dariya yanzu fa idan kika bibiya itama bacin zatayi ba baiwa wani zatayi"fadila tayi murmushi tace"ta ji dai Shi dai gundura kawai" Da taimakom farida fadila ta saki jikinta sosai don har ta samu ta shige cikin 'yammatan aka shiga hirar harda ita,hakan ya taimaka mata ta samu sauqin takurar da zuciyarta tayi sosai kafin dare yayi kowa ya kwanta ⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜ Washegari gidan kwalliya anty hafiza ta debesu suka tafi,cikin wasu awoyi aka qalqale wa kowacce fuskarta da kwalliya ta garari dubu ashirin aka ajiyewa matar,itakam anty hafiza tsayawa tayi tana kallon sarautar Allah kyansu ya qara bayyana qarara,daga baya ta kasa ahiru sai da tace"ashe haka kuje da kyau yammatan ummi musamman fadila ashe hasken fata kawai za'a nuna miki?"dariya dukansu sukayi har da ita mai kwalliyar wadsa itama tinda tayi musu take kallo fuskarsu tace"dama ai ba fari ne kyau ba don wani choculet din yafi fari kyau nesa ba kusa ba" sai bayan idar da sallar magariba aka kammala kwashe yammatan zuwa royal tropicana,amare sun gama shirinsu kayan kam sun amshi jikinsu don tamkar saboda su aka halicci yadin da shi kansa dinkin,kiran mubarak ya shigo wayar farida yana sanar mata isowarshi qofar gidan,ta kashe wayar fuskarta na bayyanar da damuwa ta kalli anty hafiza da ta luea tun dazun ta kasa zama sai kaiwa da komowa taketana kiraye kirayen waya ta fuskanci akwai abinda suke boye mata,farida tace"anty ya za'ayi gashi har mubarak ya iso?"hafiza vikin damuwa ta kalli fadika tace"fadila kibi motarsu farida kawai kije"ba abinda tace mata kawai tabi bayan farida suka fice,ko ba'a gaya mta ba itafin ai ba yarinya bace qarama ta sani koda wasa aliyu ba zuwa zaya yi ba,ko da yazo ma tana fargabar kada ya yi mata wani abun da zata kunyata a idon duniya,shi yasa tun usuli ta so su shiryawa farida dinner din ita kadai abunta,mubarak ke driving motar da kansa don haka suna fitowa da kansa ya bude mata kujera mai zaman banza ta kusa da shi ta shiga ya rufe sannan ya koma ya shiga nasa gun,ita kuwa tana baya ita kadai,tunani ya cika zuciyarta tana sha'awar soyayyar farida da mubarak dinta,yana matuqar nuna mata qauna da kukawa ko da a gaban waye,tunda aka fqra hidimar bikinannan kusan tare suke jigilar shi da ita,duk da tana da moyar ta amma ba ruwansa da wannan, da yake basu fito da wuri basun dan bata lokaci gun jira jiran da fadila ta samasa jiran gawon shanu don tasan ba komai bane face jiran tsammanin zuwan Aliyu ya dauketa ita damata ahekara da sanin ba zuwa zaiyi ba,a farfajiyar farko kafin ka shiga tafkeken hall din mubarak yayi parking,saiga anty hauwa anty hafiza da tuni ta iso sumayya rabi'ah da 'yan biyu,fuskar anty hawa da alamun bacin rai ta kalli su mubarak"kama hannunta ku shiga su fadila zasu shigo daga baya"yace "to"ya kama hannun farida su sumayya suka take musu baya su da wasu yammata cikin anko codelace milk dake tsaye bakin qofar ahiga hall din,cikin son kauda ahitun da gun yayi antu hauwa tace"gsky hafiza mun tsinci dami a kala fa,irin wannan tsaleliyar budurwa haka?"duk sai da ta basu daroya,anty hauwa ta budewa fadila motarta gun kujera mai zaman banza tace zauan fadila,wayarta ta zarota shiga kira"muna qofar hall inda ka shanya mu muna jira"ta fada cikin fusata sannan ta kashe wayar,sundebi kusan minti ashirin suna zaman jiran har fadila ta qosa sosai tayi kamar ta nemi alfarmarsu akan su qyaleta ta koma gida tana ahirin yin hakan waau jerin gwanon baqaqen motoci motoci suka danno kai cikin harabar gurin,anty hafiza ta sake feshe fadila da turare sannan duk da qamshin da take zubawa fuskarta fes take kamar yanxu aka gama kwalliyar sai alamun damuwa da suka bayyana a fuskar anty hafiza ta rada mata"be free and comfortable you have to invite happiness in you face even its not true, zaku shiga cikin mutane ke zaki bawa kanki confidences na zaki zaki zama amarya kamar farida da mubarak right?"fadila ta gyada kai tana qoqarin daidaita yanayin din fuskarta,ta maida turaren cikin hamarta tana cewa sai kun shigo "ta wuce ciki,daganan tana hango anty gauwa yadda ta nufesu tana wurwurga hannu da alama masifa take nasa shì kuwa ya yi kicin kicin ya hade ransa sanye yake cikin wata dakakkiyar shàdda milk colour yar ubansu komai na aliyu classic ne yayi wani shegyan kayu dinkin babbar riga da yar ciki ne da wando sai takaminsa half cover na kamfanin mister,daga bisani tafa tana nuno masa ita da hannu itama ta juya tayi shigewarta Duk takunsa daya shike qaŕa bugun da zuciyarta keyi ta dauke idanunta ta ditasu kacokam kan sitiyarin motar kunnanta na jiyo mata takun tahowarsa gun hancinta na shaqo mata daddadan turarensa,sau biyu taji yayi knocking glass din motar bata da zabi illa ta fuskanceshi sabida haka ta dago razanannun idamunta ta saukesu cukin nasa idanunta da nashi suka hadu gu guda👀,zuciyarsa taďan kai ta jawo kadan duk da yaga kyaunda tayi amma sau yaga batakai kyan da samira ta masa ba,cikin halun ko in kula yace mata"les go"fuska a tsuke ya juya😠,ta bude murfin motar tana qoqarin fitowa ta gurde ta tafi luu zata fadi saboda yadda jikinta ke rawa,yasa sangalalun hannunsa na hagu ya tare ta sannan ya miqar da ita tsaye ya saki tsaki yayi gaba,ta yi qoqarin daidaita natsuwarta sannan ta bishi suka jera Shigarsu mawaqin ya sauya kidan zuwa wani take na musamman aka bisu kuma da abin qyalli ana fesa musu🎊 ga gayyar yan rakiya a bayansu da suka sasu a tsakiya,suna zama aka maida waqar da shahararren mawaqin nan yayi musu nura m inuwa(anyi aure biki na'ya'yan girma 'ya'yan alhaji abbas bashir sunyi aure)aka dan cashe kadan sannan m.c ya amshi abun magana🎙ya soma zugasu kamar yadda aka sani sunawa amare da angwàye,lokacin mubarak da aliyu suka gaisa cikin mutunta juna,mc bai qyalesu haka ba har sai da ya samo musu kyautar mota daga gun Aliyu mubarak ya bada dubu dari hajiya shatu yayr alh salim maitama ta basu wata qaramar motaŕ dangin mubarak kuma suka qara musu da dubu hamsin,tunda suka samu abinda suje si suka bude fa bakin gangat zamar da bikin qayatacce a idon duniya,biki kam ya qawayat ta kuma nishadantar musamman farida da angonta,don da aka kira amare da angwaye su shigatsu sukayi filin rawa suka taka sosai itakam ita da aliýu sun tsaya ne kurum suna facing juna ita kanta na qasa ma aka musu ana cikin yi aliyun yaja hannuta suka koma sit din su umarni ma yabi da tafiyarsa zaiyi ya barta ita kàdai tsaye a filin sai akan kujerunsu aka qarasa musu liqin,wayrsa ta dauki wani daddadan ringin,ya daga yar kyakkyawar wayar a kunnensa sannan u yace"oh baby I already told you sai na fara zuwa gun daya dinner din ko idan kuma nabar nan din can zan taho tunda na da wuri zaku tashi ba......ok take care"ya kashe wayar yaja dan siririn tsaki Farida da mubarak ne suka soma yanka nasu cake din sannan dan gaa kadan nasu fadila mai hawa shidda ne milk sannan red milk sannan red haka haka har step shida🎂,bayan su farida sun koma aka kirasu gabanta na ta duka,suka tsaya gaban cake din maimakon ua fara daukar wuqar saboda tsorata ita tà fàra daùka akasa tagi mc yace yau zamuga sabon salon soyayya uwargida zata fara ci da mai gida wata wuta tayi tsiri saman cake din lokacin da tasa yar qaramar wuqar tana yanko cake din hakan ya sake sa jikinta rawa tadan tsorata duk da ta saba gani ammada yake a rude take sai hakan ya sake duburburtata,tayi qasa da idonta sanda ta kai cake din bakinsa ,ya kuwa basar ya sa bakinsa ya karba cikin mugunta ya hada da hannayenta ya datse mata sutaji zafi sosai amma kasancewar tasan da gayya yayi sai ta basar kamar baþa ji zafin ba,bai damu da qanqantar bakinta ba ya yanko qaton cake da tasan yafi qarfin bakinta ya danna mata duk da haka itama tayì namijin qoqarin lalubo yatsunsa ta ganyara masa cizo maimakon ya cire hannun nasa sai kawai ya birkitota ya mannata da jikinsa ya maqure ta sosai duk a zuwan rungumeta ya yi ya sanya bakinta cikin nasa yana tsotse butter din da ta bata dan qaramin bakinta,duk gurin ya dau sowa da tafi masu hotuna📸 da video🎥 suka yo ca suna aikinsu saidai fafila ita tasan azabar da take ji domin tsotsar mugunta ce su kuwa a tsammaninsu tsantsar soyayya ce,ta tabbatar lebunanta idan basu tsage ba to daf suke da au tsage din,kunya da takaici suka dabibayeta cikìn dinbin jama'a saboda rashin kunya irinta aliyu ya mata irin wannan abun?ya saketa sannan ya jata zuwa gun zamanta ya zaunar da ita ya dan ranqwafa mata yace"matuqar idan nayi miki abu kikace sai kin rama u wil b suffer"yana gama gaya mata ya juyà yabi ta cikin mitanen ya bar halla din sai jiyowa tayi ta cikin macros phone mc na sanarwa cewa ango yace a masa afuwa kayansa sun bavi zaije gida ya canza yana kuma yiwa kowa fatan alkhairi godiya da kuma ban gajiya amarya kùma tadan daure taje zasu tafi,kasa tashi tayi kuka kurum take na takaici da kunyasam Aliyu bashi da kunya ya rasa tame zai rama saita irin wannan hanyar?idan su sunsan abinda ke zuciyoyinsu ai ragowar jama'a basu sani ba ko?,harsai da text din anty hafiza ya shigo mata kamar haka sannanta iya tashi"malama kukan ya isa haka ki taahi ki bishi yana wahan hall din yana jiranji isan kùna so kike ki tona abnda muka binne to bismillah"ta miqe tana kare fuskarta da purse👛ta fice Wannan saurayin da ta saba ganinsu ko yaushe da aliyu shi ya fito ya bude mata gidan baya ta shiga sai da ta zauna ta lura da aliyu ahima zaune gefanta bai ko kaeta ba yavi gaba da abinda yake bako motsin mutum cikin motar sai qarar fitar ac har suka qaraso ni'ima guest place,motocin sukayi parking na ciki suka firfito suka tsaya jiran fitowar Aliyu tuni drivan ya fice aliyu ya zube wayoyinsa bayan ya kashesu yà fice shima a motar ya kulleta tare da sa security Wucewarsu cikin hayaniya ta tawagar ango yasanya gun komawa tsit kamar yadda yake ,tun tanajin tsoro har ta dake tana ta addu'o'i,a hankali abinda ke wakana agun ke isowa kunnuwanta ta hanyar lasifiqan da suke amfani da shi,sunan samira da ta ji hade da na Aliyu shi ya tabbatà mata gun bikinsu ne,wani kishi mai zafi ya shaqeta,ta jingina sosai da makarin kujerar tana ambatar sunan Allah tà lumshe idanunta tana ci gaba da sauraren abinda ke wakana cikin gun dinner din,gajiya tsoro kishi da takaici suka mata taron dagi, tun bata gaji ba har ta sare da zaman gashi ba damar fita bare tayi tafiyarta yabi ya kulle matar,zaman jira na kìmanin awa uku tayi a motar sannan ta fara hango tawagar aliyu Mrs muhammad bello ce 📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻 [10/16, 12:29 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 Wa yasan gobe? 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 Written by safiyya Abdullahi musa huguma 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 ▶🔟 Tamakar ya manta akwai wata halitta da ke cikin motar ya shigo abinsa driver yaja motar suka bar gun,ganin haka yasa tayi kamar ta tuna masa su sauketa a gida fa sai taga ai ya ma raina wayonta duk inda zai kaita ya kaita,ganin sunyi hanyar gida yasa ta sake tabbatarwa yana sane kenan A daidai qofar gidansu driver yayi parking yana tsayawa tasa hannu ta bude motar tayi ficewarta ba tare da tace masa kanzil ba haka shima baice komai din ba dama kuma tasan ba cewar zaiyi ba bata kuma dada ta da qasa ba maganarsa,ahankali take tafiya saboda kasala da bacci ga takaici da ya rufeta ya dan bita da kallo yana mamakin haqurin da tayi bata ce masa komai ba ua juya ya bawa nasiru umarnin ya ja motar su wuce Kai tsaye gidansu zainab ta tafi don kwanciya kawai take buqatar yi a halin yanzu,dakin da aka basu ta tura ta shiga wasunsu yammatan sunyi bacci wadanda suka rage kuma kowacce na maqe da waya tana tadi kamar yadda farida tabi sahu itama ganin shigowar fadilan ne ya sata katse wayar ta dubeta tace"ya naga kin jima sosai haka"sai kuma ta danyi murmushi😊 tace"um mace da mijinta meye nawa?",tabe baki fadilan tayi☹ta jawo jakar kayanta ta dauki towel ta kwabe mayan jikinta tadaura ganin haka yasa farida ta gane tambayarta bata da amsa kenan,ta sake dariya bayan taga shigewarta toilet tace"ya fadila tawa......miskili kafi mahaukaci ban haushi Washegari ummi tayi mother's day,cikakkiyar shigar hausawa sukayi ranar don hatta mayafi na atamfa sukayi,kwatsam sai ga momin Aliyyun a gun da mutanenta sunzo wai za ta yi wa fadila nata kamun,gun yayi armashi sosai don kidan qwarya akayi zalla bayan lecture ga amare wadda aka shafe fiye da awa ana musu inda daga baya kuma gun ya karade da waqoqin da irin nasu mamman shata sani sabulu dan qwairo dan indo audu wazirin dan duna da sauransu suma iyaye aka tuno musu da da tunda dama ranar ta iyaye ce, Washegarin ranar sukayi kuma wuni a gida,wata Washegarin kuma ta zamto ranar daurin aure,daurin auren da ya tara jama'a na ban mamaki garin ranar unguwar ba masaka tsinke,jama'a ne tako ina na nan qasar dama maqwaftan qasashe har da na qetare ⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜ Misalin takwas na daren ranar daurin auren fadila da farida na durqushe gaban umminsu sanye cikin atamfa super England lemon grean ce da pink sai adon fari dinkin riga da zani an nannade masu jikinsu da wata danyar lafaya fara tas mai dige digen pink a jiki,dan kunne da sarqa sai banguls duk na azurfa ne ,babu abinda ke tashi jikinsu sai wani rantsatstsan qamshin turaren humra yar gasken ta bare barin usuli Da fari ummi kasa magana tayi saboda tausayi da qaunar yaran nata sai jimamin rabuwa da zatayi da su,daga baya ta daurw ta musu yar tunatarwa saboda ita damacan koda yaushe mai dora yayanta ce kan tarbiyyar zaman gidan aure ce,ta kammala nasihar tata da addu'a da fatan alkhairi a garesu,umma A'i yayar ummi ta leqo tana cewa su fito angwaye nata jira fa,wani kukan suka sake saki suka ruqunqume ummin suna neman yafiyarta,tace ta yafemusu burinta kawai su zauna da mazajanasu lafiya kada taji kada ta gani shine farincikinta,ana riqe dasu amma suna waiwayowa suna kuka idanunsu a kanta kamar zasu qwace su dawo,itama sai ta kasa jurewa suka sata qwalla duk sai suka karyar da zuciyar kowa sai muhammad shima ya dauki masa kukan da ya bawa mutane tausayi kasa zama yayi yabi yan uwan nasa yana ta kuka kowa ya tausaya mai saboda tunda ya taso suna tare da su ya saba su ya saba gani gashi yau an dauke masa su duka biyun Cikin wata arniyar mota qirar sail akace a shiga da fadila suna qoqarin sa farida a dayar ta riqeta gam tace bata yarda ba saidai a hadasu a mota daya,ganin da gaske take yasa suka sasu a mota gudan,lokaci guda motocin suka tashi suka kuma jeru reras bisa titi tamkar motocin rakiyar shugaban qasa,duk da cewar darene amma duk inda suka bi sai sunja hankalin mutane saboda kyawun motocin,kai tsaye yahaya gusau suka fara nufa inda anan gidan farida yake,a nutse suke shiga gidan saboda ba yara ko daya sai manya da yammata tun la'asar aka kai yara suka gama gani aka dawo da su gida tsarin gidan farida gwanin sha'awa ya burge jama'a da dama atsare ginin yake kana kallonsa kasan sai da aka sa nutsuwa aka fidda masa fasali  Sai da suka ajiyeta a bedroom dinta su umman abuja(itama qanwar abba ce)suka sata tayi addu'o'i sannan sukayi haramar tafiya,fadila na nanuqe da farida har yanzu kukan suke sunqi sakin juna harsai da umma a'i tq fusata dama akwai lafiyar fada ta hau sababi tace"ku kunga bamason isknci,kanku aka fara aure ai kowa da haka ya sabatun dazun ake fama da ku ki fito kin noqe to kada ki sake na qaraso dakinann baki fito mun tafi ba"suka sake rushewa da kuka 😩ganin lallai dai rabuwar za suyi,mama sadiya(abokiyar wasan abbansu ce)tazo ta kama fadilan tana rarrashinta tafito da ita tana jiyo kukan faridan kamar yadda itama take jiyo nata  Cikin nasarawa G.R.A motocin suka kutsa qofar wani katafaren gida suka tsaya,kewaye yake da dogayen kuma qawatattun katangu da fitulu masu tsananin kyau makeken get wanda saboda tsananin girmansa sai kayi tsammanin qofar shiga garice suka tsaya,duk yawan motocin sai da kyakkyawar harabar gidan ta lamushe su,sai ma suka tashi yan tsurut harabar wadace ta take da haske tamkar rana sai ka rantse da Allah rana ce ba dare ba "Kai jama'a yanzu kamar ba za'a mutu ba?,wannan gidan dai.....inda ni kadai na shigo wlh ihu zan sak na ce gidan yankan kai nazo,kamar ba mutuwa a duniya?"kakarsu fadila hajja gana mahaifiyar abbansu ke wannan santin,su kam me za suyi idan ba dariya ba😂,sai da suka nufi sashen fadilan masu yaba kyau da tsaruwar gidan suka dadu,ginine wanda kaf garin kano baifi ka qirga masu irinsa da hannu ba,ginin part hudu ne sai boys quarters makeken lambu swimming pool gun wasanni kala kala,basketball table tennis,football boxing,tokwand da sauransu baya ga haraba biyu da gidan ke dauke da shi harabar farko dakin mai gadi da parking space take dauke da shi,sun dan tarad da jama'a a gidan acan part din samira suna jira a kawota,ba abinda ke tashi sai kida da yan uwanta suka ware mai barazanar fasa kunnuwa ganin haka hajja gana ta hana su koda guda suyi ta shiga gidanta da addu'o'i bakinta  "🤔wai ni Allah wannan gida naki fadila idan baka da qarfin imani zai iya saka ka manta Allah "gaba dayasai da hajja gana ta sake sa kowa dariya a gun😂 duk da suma sun lalace ne gun kallon tsaruwar gurin nata falone two in one wanda kan ka shigo main falo akwai varender a farkon sashin sannan ka tadda falon,dukka falukan sun qawatu da kayan qyale qyale na falo babba da qaramim falon kowanne ansa masa abinda falo ke buqata ba abinda aka rage masa,acikin main falon anan daga hannun damanka matattakala ce masu fadi guda hudu zaka taka ka haye gun dining wanda ke daume da wasu hadaddun labulaye masu kacar kacar anan qofar kitchen s dinta take wanda duk wayewarka sai quyancinka ya fito,gaban gun dainin kadan wata yar qoface mai kyau ta glass wadda ke dauke da corridor shimfide da lallausan carfet da hadaddun labulaye dakunan bacci ne guda uku daya furniture ne yan Saudi pink da purple daya dakin kuma yan italia ne ash da pinch yayin da daya dakin kuma aka malaleshi da carfet da manyan tuntuna aka zagayeshi da labulaye masu shegen kyau aka rarrataye mata kayan kaba da kumbuna tamkar jeran qauye sai wani dan gado irin na qauye mai rumfa amma wannan an zamanantar da shi kowanne daki da toilet dinsa sai public toilet dake varender da kuma wani a falo,daga kitchen akwai qofa da zaka zagaua bayan part dinka(ventilation)wanda akayi dan qaramin lambu da wata rumfar bunu sai yar qaramar qorama da aka qirqira da doguwar kujera ta siminti qwaya daya,a falo aka ajiyeta,ido kam ya raja'a da kallom kyawun gidan,sanyi a c da qamshin freshener ya game ko ina ga qamshin sabunta,gidan ya kaure da hayaniyar yammata dake ta zuba santi da yiwa kansu fatan samun koda makamancin wannan gidan ne, Wata hayaniya da suka ji ta kunno kai gidan ya saka su yin shiru suna sauraron daga ina take?,guda ce da aka cakudata da kirari iri iri hafe da habaice habaice"taka lpy uwar gida sarautar mata,isaahshiyar mace a gidan aliyu maitama ,eh anqi Allah yaso,qaryar mahassada ba zasu iya da ke ba wallahi sama ta yiwa yaro nisa saidai ya tada kai yayi kallo,an buga da ke an barki wlh yarinya ko yar sankin santanbul ce kinfi qarfin ta kara da ke saidai tayi iya nata salon ta haqura," hakane ya tabbatar musu masu rakiyar samira ne mama sadiya suka hana kowa fita har suka qaraci ahewarau da shegantakarsu suka shige da ita,zuwa wani lokaci kuma sautin sabon kida na kujerar tsakar gida ya karade gidan tamkar wani club,Allah ya kayuta abinda suka ce kenan  Qarfe tara aka soma kwashe yammatan ana maida su kafin tara da rabi gidanta babu kowa,kadaici ya kama fadila,tsoro ya cikata,bata jin sautin komai sai hayaniya da kidan yan uwan samirah,zuciyarta tayi rauni sosai tunanin irin zaman da zatayi a gidan take,Aliyunta bai sonta,kishiyarta kuwa salon da ka rakota da ahi ya tabbatqr mata ba zaman lafiya tazo ayi da ita ba,hawaye ya balle mata😭 zuciyarta kaar tayi tsalle ta fito saboda zullumi da radadin da take mata Horn din motoci ya sake cika gidan,ta daga kanta ta kalli agogon bangon dake falon sha daya na dare ya nuna mata🕚 ba shakka angone da abokansa suka shigo zuciyarta ke gaya mata haka,sannu taji hayaniyar jama'ar na raguwa hakan ya tabbatar mata ana debe su ne tafiya suke,ga tarin mamakinta sai ta jiyo muryar samira na cewa"ku gaida gida na gode Allah ya huta gajiya,ina jiranku gobe da safe,kuma wlh kada ku yarda sai sun vika muku kudin siyan bakin"fadila ta jinjina kai tana cewa cikin zuciyarta lallai ba shakka kowane tsuntsu kukan gidansu yake Cikin qanqanin lokaci gidan ya sake zama tsit,ba komai cikinsa sai hasken fitilu daya gauraye da kukan tsintsaye da kuma gyare jefi jefi,haka ya sake assasa tsoron dake zuciyar fadila ta runtse idanunta gam😣tana ambaton sunayan Allah hadi da addu'o'in tsari,sannu a hankali taji idanunta da jikinta sun fara nauyi ,gajiyar kwana da kwanaki suka fara sauko mata,taji bata da buqatar komai illa kashingida,ta zame ta dogara gwiwar hannunta a hannun kujerar,tsananin gajiya yasa bacci har ya dauketa bata sani ba💤 ASUBA TA GARI AMARYAR ALY😊😊 Mrs muhammad bello ce  📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻 [10/16, 12:29 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 Wa yasan gobe? 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 Written by safiyya Abdullahi musa huguma 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 ▶1⃣1⃣ Firgigit ta farka kamar an tasheta,ya zame mata jiki tun a gida assalatun farko take tashi tayi yan nafilfilu kafin assalatu na biyu daga nan idan ta idar tayi baccin mintuna idan tana da lacture ta shiga kitchen ta shirya breakfast,yauma gajiyar bata hanata tashin ba saidai ta sabawa lkcn da ta saba tashi sai kiran a kiran sallah na biyu ta tashi,cikin kasala ta miqe don har yanzu tanajin nauyin jikinta tayi miqa hadi da salati idanunta suka kai kan wata farar leda babba mai dan duhu guda biyu tsoro ya darsu a zuciyarta ta katse miqar a iya saninta sanda zata kwanta babu ledar a gun to ya akai ta samu?cikin sanda ta isa inda ledar take kamar wadda akace za'a kama,saidai tunkan ta bude ledar qamshin turarensa ya ziyarci hancinta,hakanne ya bata amsar tambayarta lallai aliyu shi ya shigo da ledar tayi mamakin yadda har ya shigo ya fita bata sani ba, Ta bude ledar gasashshiyar kaza ce wadda akai wrapping dinta guda uku sai ice cream da ya gama narkewa saboda an ciroshi daga ma'ajiyarsa sai fresh milk manyan roba har uku,sai yoghurt shima roba uku tayi ajiuar zuciya ta mayar da kayan,kasala ta sake kamata taja da baya ta koma bisa kujerar ta zauna tana aheqar daddadan turarensa tamkar yanzu yake a gun,ta shiga hasashen fuskan aliyun a cikin wadannan awoyin da yake angon mutum biyu,kishi ya taba zuciyarta,tafan bata waau lukuta a zaune ta kasa tabuka komai sannan ta miqe ta lalubi corridor din nan ta zabi bedroom daya ta shiga,tana alwala tana qarewa tsaruwar toilet din kallo,tabbas dole hajja gana tace kamar ba za'a mutu ba,bayan ta idar sa sallar ma tana lazumi dakin taci gaba da bi da kallo tana yaba irin namijin qoqari da iyayenta da yayansu Ahmad suka yi,bata kammala ba wani daddan bacci ya rinjayi idanunta nan bisa dardumar sallarta Hasken rana da ya soma shigowa ta window yana taba fuskarta shi ya farkar da ita,da addu'ar tashi daga bacci ta miqe a bakinta ta dubi agogon dake ajjiye kan bedside ya nuna mata goma da minti sha biyar na safe batayi mamakin awanni data shafe ba tana baccin ba,toilet ta shiga ta kunna water heater dake manne a kusurwar bandakin cikin mintina qalilan ruwan ya tafasa ta kunna shower ta daidaita zafinsu ta shige kwamin wankan🛀🏼,tsaf ta shirya cikin atamfa mai zanan manyan ganye mai kalolin pink da ja sai light blue,dinkin da ita atamfar kanta tayi.masifar karabarta duk da ba wani make up tayi ba hoda ce kawai sai man lebe da kwalli,dinkin ya lafe mata sai kayi tsammanin fitted gown ce daurinta yayi das wanda ya awa gashinta damar kwanciya bisa dokin wuyanta Ta fito falo ta kwashe siyayyar jiya ta kaisu kitchen,tsayawa tayi kallon kitchen din tana jinjina kai da dan guntun murmushi akan fuskarta😊ba shakka ummi tasan tsarinta game da kitchen kuma ta san maitar kitchen irin tata don haka ta cika mata ahi da dukkan wani nau'i na kayan amfanin kitchen babu ce kawai babu,abun nema ya samu nan ta bata lokaci gun tsara da shirya kitchen dinta yadda take muradi,tana tsaka da aikin ta jiyo ringing din wayarta wadda ita sam ma ta mance da ita ta fito galin tana laluben inda take,tsakiyar filalluka ta hangota tasa hannu ta dahota tana duba mai kiran garida ta gani tayi yar dariya sannan ya daga hadi da sallama,muryar farida a qasa ta amsa fadila tace lafiyanki qalau kuwa?"ta masa mata da "hmmmm,ai dole ki ce min lpy qalau tunda ke naji miryarki garau da ke "fadila da bata fuskanceta ba tace"kamar yaya? Wani abu ya faru ne a gida?"farida ta sake ajiyar zuciya tace"mubarak bashi da tausayi Allah sister fadila jiya kada kiso kiga rashin imanin da ya gwadan,anty hafiza tasan haka amma ta dinga dirka mana magani"fadila data dau haske a zancan nata tace"to Allah ya kyauta""wlh kin ga na kasa tashi sister"ta fada cikim karyewar murya,wani yarrr fadila taji tausayinta da tsoro suka kamata tace"ai ke likita ce saiki kula da kanki Allah ya bada lpy"tace"amin na gode ina ya Aliyu" "Baya nan" Cikin sauri farida tace "kada dai ace samira kika miqawa uwargidan bayan ke aka fara daurawa aure kuma ke aka fara kaiwa?" Fadila cikin son abar zancan tace"ban sani ba 'yar jarida kije ki fara jinyar kanki tukun idan kin warke sai kiji amsa"ta katse wayar,jikinta yayi sanyi sosai a salube ta zauna agefan kujerar,ashe har faahin matsayinta ma sai da aka mata?ita idan banda yanzun ma bata san itace gaba da samiran ba tasa hannayanta biyu ta dafe kanta cikin wani irin yanayi da ta kasa tantance ame take?,ganin ba mafita yasa ta koma kitchen taci gana da gyare gyarenta zuciyarta cike fak da tunani, Da azahar baqi suka soma zuwa mata sallama din komawa gidajensu yan maiduguri ne da yan gwambe,zuwa qarfe uku suka tafi sai su rumasa'u sa'adah minah rahama da hafsah duk cousins dinta ne rumaisa tace'?"wai ke ya ne?"fadila ta kalleta da alamun tambaya ,sa'adah ta karbi zancan "gidan farida muka fara zuwa tana can kwance mubarak nata hidima amma ke gaki dungur gur a zaune"fadila ta juya idanunta🙄tace"lallai yarannan"da yake ta basu tazarar yan kwanaki ta Dora"kuce kawai uawon sa'ido yau kuka fito ko"dukkansu suka sheqe da dariya😄,suka ce"to ai gwara kafin mu wuce muga lamira sun daidaita " tace"to Allah ya qara muku himmar sa'ido"ta fada tana shirin shigewa toilet rahama tace"to ai sai ki kira mana angon mana mu gani ko shi aka dorawa jinyar"ta jiyo ta harareta tace"baki isa ba kuma kwa qaraci zaman gulmarku ku tattara yammatan qafafunku ku koma inda kuka fito"suka sake aheqe mata da dariya😂,ita kuwa ta shige toilet din tana fadi a ranta"koni bancin arziqin samun ganinshi ba rabonku da ganinsa tun a dinner to nima hakan take" La'asar gidan ba kowa duk sun yoye sun mata yan gyare gyaren da suka ga ya dace na game da jere da yan goge goge sukayi sallama cike da kewa tabi kowaccensu da dan dasheshan turare,turaren wuta ta zuba a bin turare mai amfani da wutar lantarki ta daidaita sanyin a.c falon yayi wani dadi qamshi da sanyi auka hafe guri guda,turare na musamman da hajja gana ta musu da kanta kuma ya tsumu sosai don ya jima a ajjiye ta musu tanadinsa,don haka qamshin har farfajiyar gidan,wajajen biyar ta sake gyara fuskarta ta feshe jikinta da turarurruka don dama babdaga baya ba fadila gun qamshi ta gabatar da la'asar da ta kufce mata,tana linke sallayarta tana ci gaba da jiyo hayaniyar dangin samira don tun farkawarta da safe wajan goma da rabi ta fara jin zuwansu,ta gama ta koma falo ta kama mbc bollywood dan ta samu ta debe mata kewa,kafin takai ga zama kan kujerar taji ana knocking din qofarta,ta nufi qofar tana cewa "waye?"saidai shiru ba'a amsa ba,don haka tasa hannu ta bude idanunta a waje don ganin waye,a subhanallah,ta fadi a zuciyarta saida bugun zuciyarta 💓ya dadu sosai fiye da qima,Aliyu ne tsaye a bakin qofar yana sanye cikin wani lallausan farin yadi qal(tissue),yadin nada shara shara don hakka hatta farar vest dinsa kana iya hangota,dinkin yarbawa aka masa(boda)iya gwiwa da dogon wando yana sanye da baqin takalmi idanunsa saye da farin gilashinsa na qa'ida kansa ba hula sai kwantacciyar sumarsa kamar mai sa mata relaxer saidai natural ce haka sumarsa take,qamshin turarensa ke dukan fuskarta,tsintar muryarsa tayi yana cewa"su bar maka a nan ka dinga daukowa kana ahigowa da su"hakan yasa ta tabbatar bashi kadai bane,tayi niyyar yin sauri ta koma ciki don ba hijabi a jikinta saidai ta kasa moysa qafafunta,sai jan jiki da tayi ta rakube a bayan qofa,nasiru n yake shigowa da kayan abinci duk wani dangin abunci da nasha na har ya kammala shigewa da su tsaf aliyi na tsaye tsakiyar falon hannayansa zube cikin aljihunsa yana facing qofar store yayin da ya juyawa qofar shigowa baya,ta haka fadila ta morewa kallonsa ba tare da ya sani ba,ingarman namiji ne wanda siffar qarfi ta bayyana atare da shi bayansa kawai ka kalla zaka fassara hakan,nasiru ya fito yana kade hannayansa ya dan russauna yace"yallabai na gama"yana qoqarin zaro kudi a aljihunsa yace"yauwa ya miqa masa kudin yace"raguna zaka samo guda biyu ka biyaau su gyara komai su wanke acan ka duba motar zuwa kasuwa ka tafi a ita""to yallabai"ya fada yana shirin wucewa"nasir"aliyu ya kirashi a aladabce ya juyo yana amsawa"ka biya ta gidan gona su gyara kaji ka taho da su""an gama sir"cewar nasiru ya fice da sauri Ya juyo yayo tattaki har zuwa bakin qofa,fadila ta saci kallonsa sai taga hankalinsa na waje,cikin sanyin jiki da sanyin mutya tace masa"ina wuni"yqdan kalli sashin da take ya kauda kai,cikin wata dakakkiyar murya yace"kada ki qara zama haka bayan kin san cewa ba ni kadai bane,in kunne yaji......"tace"to"har yasa qafarsa awaje yadan dawo da baya ba tare da ya dubeta ba yave"qarfe takwas ki sameni a gefena"to ta sake cewa,"shikenan babu abinda kike da buqata?"ya fada yana duba agogon hannunsa,"babu"tace "Ok ki duba saman kujerarki"kawai yace yasa kai ya qarasa barin sashin aransa yana cewa"ta wani labe sai kace wadda ake kora" Hannayansa harde bisa qirjinsa yake bin harabar gidan da kallo ,ko ta ina dangin samirah ne kamar wani sabon bikin suke sakewa,ba bainda auke illa aikin dafa abinci da kade kade,shiba wannan ne damuwarsa ba hayaniya ce baiso sam ko kadan,musamman wannan lokavi da tun daren jiya zuciyarsa ke a cunkushe,lamarin na taba ransa sosai yanayin da ya samu samira a daren jiya tun daren bacci ya qauracewa idanunsa,yaja siririn tsaki a ransa yace"wai duk haka matan suke ne?"bashi da mai bashi amsar tambayarsa don haka ya nufi sashensa Damuwa ita ta haddasa masa gajiya da kasala ya zauna bisa kujera ya miqe duka qafafunsa kan kujerar ya hardesu yasa hannunsa na dama yana shafar sumar shi,tunani ya masa yawa ya rasa da wanne zai fara,yana a haka yaji knocking kafin ya nada izini har ta shigo,tafiya take tana wani karairaya kamar mai ahirin tsinkewa ta kafa masa ido tana murmushi,sam ko kusa bata burgeshi ba hasalima wani tsanarta da baqinta yake gani,ta haue kujerar da yake kai kamar zata koma cikinsa"sweet aly ina ka shiga tunda ka kawo kayan abinci ka fice"ya dauke kansa yana qoqarin janye jikinsa yace"na koma kasuwa ne" Ta dan bata fuska ganin yadda yake nuna kamar yana qanqyaminta tace"haba sweet wai meke damunka tun daren jiya fa ma lura da sauyawarka,bayan wannan lokacimmu ne da ya kamat ace mun moreshi,pls kada ka bari wani dan qanqanin abu ya tarwatsa mana jin dadin wannan lokaci da muka dade muna tanadin zuwansakada ka lalata mana suitable moments dimmu"kallon da ya watsa mata shi ya firgitata ya kira sunanta da wata murya da ta qara razanata "Kin dade da wargaza farincikin wannan lokaci tuntuni da hannunki"ta dan zaro ido cikin duniyanci😳 tace "kamar ya wai me ya faru?"ganin tana shirin raina masa wayi yasa ya.miqe gami da jan tsaki yace"ni zaki mawa silly question irin wannan?"ta kama gefan rigarsa tana shirin kecewa da kukan kirsa tave"din Allah ka gayamin me na maka?",ransa tafasa da suya kawai yake,ya dawo da baya yana huci ya ranqwafo kanta tamkar maiahirin fadowa kan nata har tana jiyo hucin numfashinsa,ya ware sexy eyes dinsa soaai a kanta wadanda bata san suna da girma ba haka miuyarsa a shaqe yace"u mean bakisan kinyi loosing virginity dinki ba,u did not know u r not a virgin!! A ina kika bada kanki samirah!!!"ya qaraahe cikin qaraji saboda wani kishi dake sukarsa, Wani kuka ta rushe masa da ahi harda dora hannu a ka🙆🏻 kasancewar tasan halinsa baisan kuka ko da na yaro ne qarami yanzu zai dameshi,gunji take sosai hakan yasa temper dinsa ta fara raguwa,ya koma da baya ya zauna sosai,ta qasqantar da kanta tamkar wadda zata masa sujjada ta muzanta sosai,ta tsara masa qaryar fyade aka mata tun tana qanqanuwa"inna lillahi wa inna ilaihi raji'un"ya dinga mabata ahankali har yaji zuciyarsa ta fara sanyi duk da wani bangaren na zuciyarsa ya kasa gasgata labarinta,ya amince haka qaddararsa take,shi kam ya sani bai taba koda kusantar zina ba bare ya aikata ta amma Allah ya jarabceshi da samun mata har biyu da suka zo masa babu budurci,harda matarshi ta fari "Ya isa,is ok "yace da ita,"hakan baza ta sake faruwa ba"yaci alwashin hakan,ta ruqunqumeshi tqna ta zuba godiya xikin zuciuarta tana godewa allah da asirinta baitonu ba don bazata iya jure rashin aliyu ba,baiga alamun tayi wanka ba don haka ya tambayeta,ai kuwa ta narke murya tave"na manta yadda ka koyan jiya da daddare"cike da madaukakin mamaki yake kallonta mace yar kimanin 25yrs amma ace bata iya wankan janaba ba ya koya mata ta kasa daukewa ?tun asubar jiya kuma tana zaune da janaba ajikinta bata damu ba to ina ga ban sallah kuma?ya jin jina kai yana hamgo girman aikin da ya sameshi,duk kuma yawan yanuwanta da sukazo a rasa wanda zai kwatanta mata harkar gabansu kawai suke,ya fuskanceta sosai ya sake koya mata ,nan toilet dinsa yasa ta shiga bai barta ta fita ba sai da yaga ta kammal ta kuma rama dukkan sallolin dake kanta Tofa masu karatu muje zuwa Mrs muhammad bello 📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻 [10/16, 12:30 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 Wa yasan gobe? 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 Written by safiyya Abdullahi musa huguma 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 ▶1⃣2⃣ Har magariba fadila na bisa kujerar ta kasa tashi,kudin da ya jiye mata na gefanta tafa ce ta dubu dubu guda biyu,tasa hannu ta sake juya kudin a karo na barkatai "nafi buqatarka Aliyu fiye da kudinnan fiye da komai ma,me zaniyi da kudi"ta raya haka a ranta,kiran sallar magariba da aka qwalo a masallacin qarshen layin shi ya kawo qarshen zaman dirshan din da take,wanka ta soma dama ita gwanar sa ce don wani lokacin farida kan tsokaneta da agwagwa sarkin wanka ta hado da alwala bayan ta fito ta sa hijab ta gabatar da magrib sannan ta zauna tana azkar tana kuma jiran kiran isha'i Minti arba'in tsakani ta jiyo kiran isha'in saboda haka ta tashi ta bada ita ta kammala da addu'oi ta shafa sannan ta isa madubinta dake cike da kayan kwalliya,kwalliya ta yi mai qayatarwa bata hauka ba mai cika fuska da yake ba baya bace gurin kyau sai kayi tsammanin bata lokaci tayi gurin yinta ta amsheta sosai ta kuma dave da yanayinta,ta bude duk sif dinta ta zuba mata ido tana tunanin wanne kaya zata saka?,hankali take shafa su har hannunta ya kai kan wani material Pink ne mai adon dark blue da dark green din zare da golden sai wasu dutsuna da aka caba ado da su masu sheqi suma golden colour,dinkin doguwar riga ne da mayafinsa material din yake zuwa,yana da sulbi da taushi ba santsi ba yana shaking kadan a jiki don haka da tasa sai yabi jikinta ya lafe ya kuma haska kyakkyawar chaculet din fatarta fashion na dutse ta dan madaidaici ta maqala a kunnenta sai siririyar sarqarsa data lafe a dogon wuyanta sai zobe blue shima qwaya daya da ta saka a yatsan tsakiuar hannunta,ta shafe jikinta da tutaren asaal da ahlamul arab tame suka gauraya suka bada wani daddadan qamshi mai sanyi ta zura plate shoe pink ta dau mayafin kayan ta nade kanta da shi Sannu ahankali tame ratsa gidan sai yanzu ta qarewa gidan kallo ita kam ya burgeta tsarin sosai,tamkar kana turai,ta sauke ajiuar zuciya sanda zuciyarta ta raya mata dama ita da Aliyunta ne kadai ke rayuwa cikin gidan rayuwa kuma irinta soyayya cikin takun nutsuwa ta nufi qofar da zata sadata da bangaran nasa ido ta saki tana kallon ko ina,tako ina bangaran nasa yafi naau kyau da tsaruwa sosai,tun daga varender dinsa take jiyo sassanyan qamshinsa,ta shiga falon a nitse falone da ya tafi da gaba daya tunaninta tamkar gadar shugaban qasa,haduwarsa da tsaruwarsa tafi gaban kwatance Idanunta suka sauka kanta tana hakimce kan kujera tana fuskantar t.v tana sanye ne da riga body huge da wando na jeans wadanda suka mata dam dam,ta baza kitson attachment din da aka jibga mata aka har gadon baya,fara ce sosai don har wani kore da yalo gefe da gefan fuskarta yake tabbacin kaso saba'in cikin dari na farin nata ya qara shi ne da man kanti,tana da jiki amma ba can ba da alama nan gaba kadan ta samu hutu zata narja qiba ne,tabbas ba don farin da ta aro daga kanti ba kana mata kallon farko zaka saka ta a sahun muna na amma sai farin ya boye kaso hamsim cikin dari na munin nata Fadila ta sake jadda da sallamarta a karo na biyu sai Aliyu ne dake zaune bisa step kan dining ya amsa yayin da samira tayi saurin dago idanunta tana kallon mai shigowar idanunta suka fada kan fadila wani faduwar gaba taji amma ta maze don bata son fadilan ta fuskanci ta razana da ganin da ta mata,maimakon haka ma sai ta mata wani kallon raini na sama da qasa sannan ta janye idanunta ba tare da tace kanzil ba Bata ma lura da kallon ba tana qarasowa cikin falon ta yiwa kanta matsugunni bisa tattausan carfet din da ya malale dakinta jingina jikinta da kujerar dake bayanta,wani abu ke tsunkular zuciyarta game da kishi duk da ta godewa Allah da ta tarar samirah bata fita da komai ba sai farar fata don ta tsammaci aliyu zai so matar da ta fi samira ne ba kamar samiran ba cikin ranta take cewa lallai so hana ganin laifi,to ganin samiran ko sashen da take bata kalla bayasa itama ta dauke mata kai sai ma ta zaro wayarta ta shiga latse latse To shima Aliyun sai da ya kammala abinda yake ya shiga bedroom dinsa ya dan jima sannan ya fito ya samu kujera daya ya zauna ai kuwa tsam samira ta bar gurinta ta dawo jikinsa ta lafe kamar mai shirin komawa cikin sa ta gefan ido take satar kallonsu wani abu mai daci na damunta,amma a haka idan ka kalleta sai ka rantse da Allah batasan Allah yayi ruwansu ba don bata fasa danne danne a wayarta ba Da bismillah ya fara yayi salati ga fiyayyen halitta yaja dogayan addu'oi wandabhar samira ta fara nuna masa tafa gaji,fadila ita mamakin yadfa Aliyu ke zuba addu'a take tamakar ba daga bakinsa suke ba(hmmm fadila kenan bakisan waye Aliyu bane😜)ya kammala sannan ha shafa,ina godiya ga Allah bisa ni'imomi da ya yimin a rayuwata tun daga haihuwata har kawo yau,ya kalli samira yace ga abokiyar zama nan Allah ya qaddara tare zan aureku sai kj zauna lpy bana buqatar hayaniya ko tashin hankali a gidana kowacce ta kama kanta ta tsaya inda Allah ya ajjiyeshi.... Ya dan sarara sannan yace idan da mai magana bismillah ya koma ya jingina da kujera yana jiran cewarsu,samira ta saci kallon fadila tana jiran taga zata tanka sai taga ma Sam idanunta bai kansu ta aza su ne bisa carfet,ta gayara zama cikin iyayi da kisisina tana kuma yatsuna 😏 tace"to nidai bana son shishshigi kuma bana son raini ehe.....kuma kowa ya kwana lpy shi yaso,sweet banji kayi rabon kwana ba?"ya daga kafada yace"its un 2 u ai"tayi wani fari da ido🙄tace"zamu raba kwana dai dai ne yayi aiko?"ta tambayeshi ya sake faga kafada yace taakaninku ai nikam ban iya yawon bin bangare bangare ba,"hmmm shegen girman kan tsiya"fadila ta fada a zuciyarta,duk da idan ka kalleta zakayi tsammanin bata tare da su,yauwa sweet ina kuma da buqatar masu aiki do.....cikin dakiya ya tari numfashinta,ba'a gidannan ba☝🏼,inji aliyu,ta narke murya,please sweet pls mana"bani buqatar roqo✋🏻ra'ayina ne"shiru tayi don tasan Aliyu idan yace eh babu mai sashi yace a'a,bare ita da take lallabawa tasan har yanzu lamarinta bai saki zuciyarsa ba Dakin yayi shiru har ta gama kidanta tayi kuma rawarta ita kadai,ba wanda ya nemi jin ta bakinta Aliyu ya rufe da addu'a,ita din ma bata zaton ko sun ce tace dinma zata tsinka wani abu,suka shafa addu'ar ta miqe ta fice ba tare da ta cewa kowa komai ba,samira ta bita da kallo ranta cike fal da kishi saboda komai hassadarta bata gano abun kushewa tattare da fadilan ba Shima kallon gun da ta tashin yayi yana dan mamakin sauyawarta yayi tsammanin za susha artabu ne kamar yadda suka saba a gida sai kuma yaga b sabanin hakan A bangaranta fadila dana sanin zuwanta tayi gun sosai don bai qareta da komai ba sai hanata bacci da ya yi duk yayin da ta runtse ido da niyyar baccin sai hoton fuskar Aliyu ya bayyana cikin duhuwar idanun nata,wata iriyar soyayyarshi ke mamaye ruhunta cikim tsakiyar daren kewa ta kamata ga kadaici da ya hanata sakat,so ne da bata yaba jin irinsa ba a rayuwarta qauna ce ta musamman,hakanne ya zama sanadiyyar karyewar zuciyarta duj yadda takai ga bawa kanta qwarin gwiwa,kuka ne matsananci ya sarqeta,daren tayi kuka mai yawa a kwancan tana tausayawa rayuwarta da makomarta,tasan tabbasa son Aliyu na daya daga cikin jarabobin rayuwarta,tanajin sa a jiki jini jijiya da ruhinta Cikin taimakon Allah bata manta da ambatonsa ba hakan yasa bacci yayi nasarar daukarta 👏🏻👏🏻👏🏻 ayimin afuwa a danyi haquri da wannan sai Allah ya kaimu gobe Mrs muhammad bello ce ✍🏻✍🏻✍🏻📚📚📚📖 [10/16, 12:31 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 Wa yasan gobe? 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 Written by safiyya Abdullahi musa huguma 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 ▶1⃣3⃣ Kwanakin da suka baya ta yisu ne cikin kadaici da kewa,ita kadai ke wuni a bangaren nata,bata da aiki sai wanka da sallah da shi dama abinci ba gwaninta bane saidai tayi ta jiyo muryar baqin samira da har yau suka qi qarewa,wani lokaci kuma ta kira farida su sha hirarsu Ranar da ta cika kwanaki bakwai a gidan ranar tana kwance a falo hannunta riqe da littafin sahihu muslim mujalladi na daya tana karantawa da yake mayyar hadisi ce ita ta jiyo ana knocking din qofarta ta dora littafim a saman kujerar taje ta bude Anty hauwa ce da yaranta bilkisu kausar Ibrahim sai qaramin su muhammad sai kuma madina qanwar momy da yaronta hamid sai iftihal,farinciki sosai fadila tayi don tasan yau babu wunin kadaici,nan falin ya kaure da hayaniya su suna hirarsu yana na nasu,ta shiga kitchen ta hado musu kayan motsa baki sannan daga bisani ta nufi kitchen don dora girki iftihal da bilkisu suka bita zasu tayata don sune yan manya madina ma binsu tayi aka bar anty hauwa da ragowan yaranta suna kallo fadila tayi tayi madina ta bari amma taqi don haka tare suka kammala komai,tare suka ci a babban plate guda yaran ma aka hada musu anti hauwa ce tace ayi haka kada a bata mata kwanunka,bayan sun gama madina ta hada kan kwanunkan ita da su bilkisu suka gyara mata komai,ganin ba kowa a gun anty hauwa ke tambayarta ina fatan dai baki da matsala da Aliyu ko dan kishiya wannan kam ita ba'a rasa ta da matsala saidai haquri ,dan murmushi fadilam tayi tace"ba wani matsala anty lpy lau muke"ta jinjina kai tace to saidai a yita dai haquri don kinsan zaman aure ya gaji yau fari gobe tsumma,tayi mata nasiha sosai tare da bata shawarwari masu gamsarwa fadila sosai taji dadin maganganunta hakan ya sake qara mata qwarin gwiwa da nutsar mata da zuciya Bayan sun idar da sallah ne ta la'asar wajan biyar da rqbi suka soma haramar tafiya,iftihal tace da naty hauwa mummyn kausar nidai anan za'a barni ko?,antu hauwa ta girgiza kai tace a'ah ai ba haka kukayi da mummy ba,bazan iya da wannan rigimarba tate zamu tafi da ke,ta soma diddira qafa tana maqale kafafa tana cewa nidai anan zan zauna mummyn kausar gaskiya,fadila tace da anty hauwa"anty don Allah ku barmin ita mana dama ni kadai zaman ba dadi wlh"anty hauwa ta zaro ido😳 tace"wai rufamin asiri ai mummy bazata iya zama ba iftihal ba ko na barta da kanta zatq zo ta dauki abarta baki ji yadda aka kafa mana sharadi ba kan a bamu mu taho da ita kamar tasan za'ayi haka"jin haka yasa fadila ta haqura Ta tako.musu har waje bakin part dinta yara nata tsalle kowa da packet na chaculet dinsa a hannu ta bawa su anty hauwa turarurruka da qyar ta karba tace ita lpyrsu kawai ta zo gani,ganin suna shirin yin gaba ba tare da sun shiga gun samira ba tace"antu baku leqa gunta ba kun gaisa"anty hauwa tace o'o'o ni kam tun shigowarmu muka gaisa da ita a harabar gida ta rako baqinta sai dai ko madina ita da yara,madina ta tabe baki tace nima bani zuwa anty ina kallo fa sanda muka shigo tana ganinmu tayi saurin sallamar baqin ta juya ciki kema sai da kika kirata kusan sau uku sannan ta amsa miki,sai dai su kausar maza kuje ku gaidata ku fito mu tafi ungoshi bilkisu ga hamida ma aje da shi ai ya wakilceni Suna tsaye suna jiran yaran sai kuwa gasu jiki a salube sun dawo Ibrahim sarkin zuciya hadda guntun hawaye madina na amsar hamid daga hannunsu tana tambayarsu me ya samesu,bilkisu tace anty koromu tayi wai ba mun gaisa a waje ba meye kuma na wani biyota,ibrahim da ya fisu shekara yana kusan 12yrs yace"har tsawa fa tayi mana wai masu qwala qwalan ido sai kallonta muke wa ya sani ma ko turo mu kayi mu cinyeta"iftihal kam fuskarnan a turbune tqma kasa cewa komai,anty hauwa tace ya 'isa haka is ok bata mata rai baqinta suka yi ku wuce muje,sukayi gaba fadila da mamaki ya kamata tana biye da su mamakin samira take sai kace wata mahukaciya yara zata tsaya tana gayawa irin wadannan magan ganun sai ka ce wasu manya,suna gab da get suka ji ana kwararo horn mai gadin ya tashi da azama ya bude wawakeken get din wata farar motace sol qirar range rover ta shigo ta samu gun parking ta tsaya da gudu iftihal ta kwasa tayi bakin motar Ya bude motar ya fito sanye yake da suit masu bala'in kyau baqaqe sunyi masifar yi masa kyau da kwanciya lif a farar fatarsa tas da shi kamar yanzu ma yake ahirin fita aikin ba wai ya dawo bane,iftihal na qarasawa ya cafeta ya daga ta sama ya jujjuyata yayi kissing kumatunta sannan ya direta ta tsugunna da alama gaidashi tayi,madina tayi dariya😀tace "oh uwar wayon tsiya wai har motocin Abbanta ta sansu wannan yarinya "anty hauwa tace"ke ai iftihal da wayinta aka haifeta don.mummy tace duk cikin jikokinta bata ga mai wayonta ba"da hirar iftihal da suke suka qarasa gurinsu ,cikin motoci fadila ta dan rabe bayan wata mota tana ganinsu tana kuma jina binda suke cewa,ya dago yana masa sallamarsu.lokacin da yake tambayar iftihal"ashe tare kuke mummyn yara"anty hauwa ta mayar masa ta sigar da ya fada"😊mummyn yara tun dazu tazo kuma yanzu zasu koma"ya juyo yana kallin madina yadan hade rai yace"au da waccar kima zo"anty hauwa dake danne dariya tace"eh duk tare muke"tasan yar tsamarsu da Aliyu don tun ranar da take fadin ita babarsa ce tunda qanwar mummy ce bata san yana gun ba suke yar tsama ya daina sakar mata Ya miqawa su ibrahim hannu suna musabaha haka halayyarsa take dama yana dan tsokanar ibrahim din kasancewar sunan kakansu ne shi kuma ibrahim na murmushi ya karbi hamid daga hannnun madina yana duban anty hauwa yace ba wanda ya rakoku ne?,anty hauwa tana dube dube tace tare da fadika muke ina tayi ne?,fadila data dora hannayenta saman motar tana game a wayarta har dankwalin kanta ya zame bata sani ba ta dago jin an ambaci sunanta idanunta suka fara sauka kan aliyu cikin sa'a suka hada ido harara taga ya balla mata wani abu taji ya caki zuciyarta ta lumahe idanunta am ta kasa budesu wani sinsa taji na mamayar zuciyarta da gangar jikinta kamar ana zira ra mata ruwan sanyi bugun zuciuarta ya sake qaruwa,bata san me tayi masa ba yake harararta,sai tq sunkuyar da kanta😔 tana kallon yatsun qafarta dake saye cikin slippers,sai da iska ta watso mata gaahin kanta gefen fuskarta sannan ta gane ma'anar hara rar da aliyu ke mata don bata manta ba rabi'ah ta taba fada mata ya aliyu baison yawo a waje ba dankwali idan ya ganki kuwa kin shiga uku,da sumauri ta jawo mayafin data yafa ta lullune kanta sosai Duk daga idon da zatqyi a rayuwarta ta kalli aliyu sai taji an qara manna mata sonshi ji taje kallomsa ma kawai jaraba yake zamewa rayuwarta sai dai koda tayi niyyar qin kallon nasa sai ta kasa jure haka domin zuciyarta bata lamunce mata ba,ba abinda ke sata nishadi irin kallon kakkyawar qayatacciyyar fuskar tasa To fadila za mu wuce sai an kwana biyu kuma,cewar anty hauwa tana dan murmushi😊 ta taso daga jikin motar da niyyar sake yi musu tattaki suka sake hada ido da shi sanda tayi niuyar satar kallonsa wata hararar mai zafi ya sake watso mata wadda ta sata tsayawa daga nan cak,yaram suka taho suna kama hannunta suna cewa anty bye bye,itama ta daga musu hannu✋🏻 tana dan murmushin yaqe😇 tana cewa"bye"sai kuma iftihal ana su taho ta ja tunga ta tsaya ita allan katafar ba zata bisu ba aliyu dake karbar takaddu daga hannun nasuru ya juyo yana tambayar meke faruwa anty hauwa ta masa bayani,kallo daya tak yama iftihal din tabi bayansu jiki na rawa 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 ▶1⃣4⃣ Bata sake sha'awar kallon inda yake ba don ta gaji da ganin wanna hararar tasa da kallon qiyayya da yake jifanta da su sai ta juya da sassarfa don barin gurin "ke"taji dakakkiyar muryar Aliyu,batason irin wannan kiran sam don haka tayi banza bata juyo ba bata kuma amsa ba kuma bata daina tafiyarta ba ya sake daga murya yace"dake nake"sai ta tsaya cak saboda tsoron da ya bata muryarsa ta canza tayi fakare tana jin yadda zuciyarta ke bugawa,da tsawa yake mata magana bayan ya sha gabanta"ki baki isa a kira ki ba kenan ki tsaya"tamkar tace wani abu sai kuma taga bai kamata ba tunda a harabar gida suke wani zai iya zuwa giftawa ya jisu Aliyu ya kafeta da ido yana huci a zuciyarsa yana fatan ta tanka masa ko zai samu ya huce mata haushinsa amma ko kallon fuskarsa taqiyi hasalima sadda kanta tayi qasa,ganin da ya yi bata da niyyar ko alamun tanka masa sai ya dora mata baqar leda mai dan matsakaicin girma bisa qafarta yaja tsaki gami da hura mata hucinsa akan fuskarta ya wuce,sai sannan ta dago tabi bayansa da kallo tana sheqar iskar wadda ke bada qamshin lemon fresh na mouth fresh,ta kauda idonta sai kuma ta hango samirah na tsaye bisa varender dinta ta zuba musu ido don haka sai ta saki murmushi ta kuma yi saurin dauke ledar tayi bangarenta tana qara hasko fuskar aliyu qamshin turarensa maganarsa komai nashi unique ne mai tsari ba baunda tafi buqata a yanzu irin aliyum saidai tasan samun nasa ba baune mai sauqi ba wanda zata cimmawa cikin qanqanin lokaci ⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜ Kamar ko yaushe a irin wannan lokaci tana kwance kam dogowar kujera a main parlour kunnenta maqale da earpiece tana sauraron suratu baqara cikin qira'ar sheikh Abdurrahman assudais taji ana mata knocking kafin ta bada izini tuni an bude an shigo,ga tarin mamakinta samirah ce ,ta tashi zaune tana qoqarin cire earpiece samirah ta qaraso tana kallon yadda take qarewa parlour din kallo zuciyarta cike da kishin yadda parlour din fadilan yafi nata tsaruwa da kyau,fadilan nata biye wa wanna ba ta nunawa samirah gun zama tace bismilla ga guri zauna😒"ta wani tabe baki tace"ba zama na zo yi ba don nima gidana akwai gun zaman "jin haka yasa fadila ta gane ba mutuncine ya kawota badon haka sai ta koma tayi kwanciyarta kamar yadda take da ta kuma maida earpiece dinta kunne ba tare da taci gaba da sauraron karatun ba Da samira taga haka sai ta yatsine fuska sannan ta fora da cewa"nazo ne don na tuntubeki bakiyi shirya fara zuwa turakar miji bane?,sai tambayar ta bawa fadila mamaki ta kuma ji wani bawai tana daga kwancan ta dubeta"kamar ya?,me kike nufi ne?"samira ta juya ido👀 tace"a....to gani nayi har yau baki fara zuwa ba shi kadai yake kwana nima ba zuwa nake ba tunda lissafe kwanakin amarcinki ne"mamaki ya sake kama fafila don ko a lbr bata taba jin ko ganin raahin kunya irin wannan ba wato ma idonta na kanta kenan Tilas ta miqe ta zauna sosai don nuna wa samira ba ita ce kawai mara munya ba itama ta iya barikancin nan,"da farko baiwar Allah ajiyata aka baki?,ko kuma da mai gidan kukayi maganar bana zuwa gunsa?,to idan ajiyata aka baki ina mai baki shawarar kiyi gaggawar maidawa wadda ya baki ajiyar don wannan aniyar tafi qarfin ki wlh ba zaki iya ba idan kuma shi mai gidanne ya gaya miki bari na sake tambayomiki shi.....,ta fada tana jawo wayarta tana shirin shiga contact cike da barazana don bata tsammanin ko number dinsa akwai cikin wayarta😜 Ganin da samirah tayi da gske kiransa zatayi kuma ta san sarai halin Aliyu bare tana cikin case har yanzu lallabawa kawai ake sai tace"dakata ni ba gangami nace kiyo ba magana ce iya kacina da ke"ta juya tana shirin barin falon fadila ta dan daga murya tace"ai da kin tsaya an sake jin ta bakinsa ko kinga maji dadin qarasa maganar,mu amarci muke mai lasisi ba irin naki ba"bata ce uffan ba ta fice ta ja mata qofa,wani takaici ya kama fadila taja wani dogon tsaki tana cewa"banza ballagaza ko angaya miki ke daya kika iya bariki ne kina ganin kin girmeni ko,da auren so mukai da aliyu wlh kallonki ma kace yayi sai yaji an hada shi da aiki"ta koma tayi kwanciyarta yadda take taci gaba da bin karatunta Kwanaki nata tafiya da fadila cikin gidan,ba wani qiba da zaka ce ta qara sai fatarta da tayi lumi lumi ta sake fresh saboda zaman guri daya Watanta biyu kenan da sati yakwas kwankin da take jinsu kamar waau shekaru saboda zaman kadaici,Allah allah take sakamakonsu ya fito bata da sha'awar komai illa ta fara fita aiki,ta jawo wayarta ta soma neman nafisah classmate dinta ce suna gaisuwar mutunci da fadila don har bikinta tazo tave cikin zuciyarta bari ta kira ta tambyaeta ko sakamakon ya fito saidai nata sameta ba number dinta a kashe don haka ta maida akalar kiran layin anty hafiza sunsha hira aosai ta kuma yi mata qorafin sunqi leqota ba ita ba yan biyu gsky tayi fushi tace tayi hqr insha Allah zasu zo su yinin mata,bayan sun gama sai ta kira hafsah da aukayi attachment tare sun gaisa sosai take tambayar hafsa ko result ya fito tace yana dai hanya da ya fito insha Allah zata sanar mata tayi mata godiya suka kashe wayar ⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜ Zaune take alambun dake bayan part dinta kan kujerar siminti under wear dinta take wake wa su brassiere pant da skert gun tsit yake shima kamar yadda gidan nasu yake saidai ahi akwai kadawar ganyayyaki da kuma kukan tsintsaye jifa jifa wadanda take zubawa gero shi yasa suka dadu kuma suka fi yawa alambun nata fiye da ko ina a cikin gidan tana son gun sosai saboda yawancin lokuta yakan zamo daya daga cikin abinda ke debe mata kewa ko da yaushe gun luf yake dauke da inuwa mai sanyi bata barin undies dinta wanna ma kwana biyu ne da bata jin dadin jikinta dama cutarta ciwon kaine ko ciwon mara shi yasa suka taru haka ita dama can ko a guda da wahala kaga kayanta cikin kayan wanki ko za'a mai saidai kaga na fatida tafi ganewa tana cire maya ta sabesu ta shanya sannan ta shigà wanka,tana cikin shanya ne taji takun taviya sai tayi sak don dai tasan ita kadaice a gun kuma ta kulle sashen nata da idanunta take bin gun da kallo don gane daga ina takun yake,Aliyu ne ke taho wa hannayensa harde a qirjinsasanye yake da jar t.shirtmai gajeran hannu sai dogon wandon jeans mai kalar black blue sau ciki ya sanya balck blue idanunsa saye cikin glass dinsa na qa'ida fari qal zuwa lokacin fadila ta soma tsammanin medical ne bana gayu bane,tayi saurin dauke idonta dag kansa zuciyarta na wani das das das har ya qaraso gabnta ta kasa moysawa tamkar ta nutse saboda irin kayan dake jikinta ta tabbatar babu mai shigo mata ne don ta kulle qofarta shi yasa ta saka su rigane da akery sosai sai dai maau roba ne iya qibarka iya yadda zasu fidda shape dinka gashi gaba daya hannayen ta da skrt din anbi an tsaga ko ina babu inda ya tsira wuyan rigar mai fafi ne son ana hango saman qirjinka sosai kanta kuwa ba dankwali sai tafkeken ribbom da ta saka ta mate gashinta ya sauka mata a kafada duk da ya danyi tauri sabida raahin zuwa saloon kwana biyu A dabarance take duba jikinta tana sa hannu tana gyara inda hannunta fuk yakai saidai ina duk In da ta sa taja ta rufe sai wani gurin kuma ya bayyana shikam hannàyensa na harde ya jinggina jikin qarfen da ta ware tan shanya kayan idanunsa duka ya zuba mata duk dabararta na tattare jikinta sai da ya ganota shi sai abin ma yaso bashi da riya duk da a fuaka sai ka ranyse rufeta ma zaiyi da duka"bari nayi maganin yarinyarnan'ya fadi haka cikin zuciyarsa"ni da waye a gun kiketa wani aikin rurrufe jiki?,gabanta ya fadi kunya ta sake kamata sai taji ya ja tsaki wanda yasa ta dago ta kallo shi ba tare da ta dubi qwayar idanunsa ba don tana kaucewa hakan bataso au hada ido sam don tana tsammanin yana da wani asiri ne cikin qwayar idanunsa aduk sanda qwayar idanunsa auka hafu da nata takan kwana ne ta wuni cikin begensada kuma aAbar aonshi da take ta yaqin ganin ta bunneshi cikin babin rayuwarta,wa ya gaya miki an damu da jikin naki da kiketa qoqarin killaceshi ne?...... Ba wannan ba na duna store naga yadda aka Uba kayan abinci haka suke ba'a taba ba kamar wadda ka bai wa rancansu sannan fridge ma haka yake abu qalilan ne suka ragu mekike nufi? Salon kija min bala'i ko?wannan wankin kuma da kika hafo na meme?duk masu wankin gidannan suma basu miki ba ko gulmar azo a tarar kina wanki ace wuya kike sha?burinki dai kawai na zama mai lafi Ya tsagaita da fadan ya kafeta d ido ko zata ce wani abu amma yaga ba alamu duk da zuciyarta ta baci da yadda aliyu ke mata a cikin gidan ba dama inuwa daya ta haasu sai fada tsakaninta da shi?cikin zuciyarta taja tsaki gami da cewa"shikenan kuma sai akace mutum bàshi da aiki sai dirkar abinci kamar tsohon jaki?kuma ma wane aiki nake don na dwbo yan kayana na wanke da hakan zai zama laifi agun wannan mutumin? Bata tsammci a fìli tayi maganar ba sai da ta ji yace"duk basu zama laifi ba amma ki shirya duk ranar da aka tuhumeni da wani laifi akanki kisan yadda zaki kanki don daukar ki zanyi cancankat nakai musu ke"ya maida kansa gun agogon dake daure atsintsiyar hannunsa 😠 yace"me dame kike da buqata?a gajarce tace masa"ba komai"yayi tattaki ya sake qarasowa gabanta ya ajiiye mata kudi kamar yadda ya saba ya rabe ta gefanta ya wucè tana sheqar daddadan qamshinsa wanda yaja mata kasalar da ala dole ta tattara ragowar da bata wanke ba ta maida ciki Mrs muhammad ce 📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻 [10/16, 12:33 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 Wa yasan gobe? 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 Written by safiyya Abdullahi musa huguma 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 ▶1⃣5⃣ Washegari misalun takwas na dare tana zaune a falo tana kallon wani film gabanta plate ne ta yanka kankana apple da gwanda tana sha dama abincin bai wuce ire ire wadannan qwaqwaso qofar taji anayi ta dauki hijabinta dake gefanta wanda ta idar da sallar isha'i da shi ta zura sannan ta miqe tana tambayar wane?ki bude mana,taji ance bata dau murya ba amma ta gane maca ce,ta bude ba yare da ta kauce daga hanya ba,samirah ce tsaye cikin kwalliya rakacau a fuskarta tana sanye da doguwar rigar atamfa tayi rolling dawani siririn mayafi sai uban turare data bulbule jiki da shi tana taunar chewing gum qas qas qas, tana wani ya tsina fuska tace sweet yace ki fito zamu siyayya,fadila tace😏 waye sweet kuma?,ta wani juya ido tace my aly, Tabe baki fadila tayi tave kice bani buqatar komai,bata jira cewarta ba taja qofarta ta rufe,wani kishi ne ya motsa mata ita kanta tasan tana da tsananin kishin aliyunta amma ya ta iya?,ta jiyo muryar samirah na masifa"aikin banza wa ma ya damu da ke  ?kada Allah ubangiji yasa ki je din dama sho ya takura ayi kiranki waishi mai adalci toga abinda ya jawo mana nan wulaqanci agun wadda bata isa ba"fadila dai murmuahin uaqe tayi wanda akace yafi kuka ciwo,ta dauki plate dinta taci gaba da cin fruit din ta ba tare da tana jin dadinsu ba kamar da Knocking ta sake ji ana mata ta maida plate din kitchen sannan tazo ta bude yana tsaye a bakin qofar hannayensa zube cikin aljihun jeans dinsa fuskarnan kamar hadarin dake shirin zub da ruwa😠ba tare da ya dubeta ba ya kalli agogon hannunsa kana yace"nan da minti biyar ki sameni a mota,abindabya fada kenan ya juya yayi tafiyarsa,cikin qanqanin lokacin kuwa ta shirya kasancewar ita dama koda yaushe bata taba yarda ta zauna babu wanke bare uwa uba qamshi da yariga ya kama jikinta kida muwa bata sanya turare ba,shigar doguwar riga abaya tayi baqa wuluk mai sheqi saqar qasar dubai an mata ado da dutsuna masu kalan sararin samaniya(sky blue)rigar tayi bala'in amsarta musamman da tayi rollinga da wani dankwali madaidaici shima sky blue ta nannde gashinta tayi acuci da shi,ta saka zobe qwaya biyu a yatsunta na tsakiyar hannu plate din takalmi ta saka baqine mai light blue din igiyoyi,ba wani make up tayi ba hodace kawai da weet lips amma kada kaso kaga kyawun da tayi kamar wata baqar balarabiya kasancewarta mai zagayayyar fuska da cikakken gshin gira ga yalwar sumar kai wadda ta bayyana har a gaban goshinta Suna zaune shi da aamirah cikin motar tana ta faman mitan dole wai sai da gadilan za'a tafi ne ya daga mata hannu✋🏻 fuska ba walwala kamar kullum yace"ya isa fa mitarki tayi yawa,for god sake,zaki taimakeni ranar da na tashi barin jiki na ashanye?,anje da ita kamar yadda kaje da ke ruwanta ne ta siyi abinda take ruwanta ne ta barshi fine an fita haqqinta,cikin salon jan hankalinsa tace da tuni ni kadaice taka sweet,an tashi an.manna maka wannan baqar yarinyar,wani kallo ya sakar mata wanda ya tilasta mata tsuke bakinta don kuskuren da taso tafkawa,baya ga haka ma aliyu shi tun usulinsa bai iya yi da mutum ba gaskiya daya ce zai fade ta ne agaban mutumin koda zai mutu ko zai kasheshi Sukayi tsai suna sauraron isowarta aliyu nebya faa hangota ya glass din gefansa,sai ya samu kansa da qarewa shigarta kallo tabbas tana da kyau babban abun ma iya dressing na nutsuwa bana hauka ba fuskarta babu tarin kwalliya irinta ta samira hakanan babu qamshin turare har sai da ta ahigo motar gidan baya ta zauna sannan yaji nata qamshin,shigar tadauki hankalin samirah tamkar ta fito itama ta canza irinta haka ta ji tunda ita fara ce ai zata fi karbarta haka ta gani,amma a fili sai ta wani tsaki,aliyu ya tashi motar ya yi ribas ya nufi get tun kafin yayi horn salisu mai gadin ya dage grmet din gidan nasiru da suke zaune tare da slisun ya taso ya iso saitin da aliyu yake ya fan ranqwafa yace yallabai kai kadai yau zaka fita,ya girgiza kai ina tare da matan gidan ne,nasirun ya dan sake ranqwafawa yace barkanku da dare hajiya an quni lpy,fadila ce kawai ta amsa samirah kam dauke kai tayi kamar batasan yana yi ba takaici ke cin ranta da dab banzan kishi sai tayi banza da shi Aliyu ya qare maganar da suke yi da shi da"sai na dawo kaima zaka iya wucewa gida sai gobe insha Allah"nasiru ya dan ja baya yana cewa to yallabai a dawo lpy Allah ya tsare,har ya saoma jan motar ya tsaya ya dannawa nasiru horn ya dawo da sauri yace masa"nasiru kayi qoqarifa gobe ka fita da wuri ka fara zuwa gunsu haruna ka b tabbata a gobe an gama sa kayan duka cikin store qarfe sha biyu zan qaraso insha Allah ,yace to da yarda Allah goben za'a kammala,aliyu yace sai ka wuce gida ka kwanta da wuri don ka samu tashi da wuri Allah ya bamu alkhairi,ya ja motar suka fice Yanayin tuqinsa salon da fadila bataso ne sau tari sukanyi fada da frida akan haka wato gudun tsiya ne da su,ya iya gudu da keta motoci,motar ta dauki shiru sai sanyin raba dake ratsa kowanansu kowa kuma da abinda zuciyarsa ke saqa masa,a sace fadila ke kallon aliyu ta mirror,fuskar nan ahade tan shaqar qamshin turarensa na chastity sai ta kasa dauke idonta a kansa sonsa na mamayarta,ji take tamkar ta kamoshi ta rungumeshi a qirjinta ko zaiji yadda zuciyarta ke bugawa saboda shi ya tausaya mata,a yanzu ba abinda tane buqata illa soyayyarsa,tana ji ne kamar ta furta masa abinda ke danqare a a zuciyarta ,don kanta ta dauke idonta tana sauke boyayyar ajiyar zuciya Tafiyar mintina qalilan suka isa katafaren kantinnan na shoprite,ya dauki wayarsa iPhone 6 yayi yan danne danne sannan yayi kira da bai wuce na second goma ba ya maida wayar gefensa ya kashe motar minti ashirin na bayar kada kuma a wuce haka,samirah tace cikin murmushi"ok sweet"ya maida mata da cewa"ok dear"wani dadi ya rufe samiran kamar ta taka rawa💃🏽 domin ta dade bata samu hakam daga gareshi ba duk da tsan ba laifinsa bane ita ta barar da damarta,ta kama hannunsa ta masa kiss sannan ta fice,abinda bata sani ba tuni fadilan ma ta rigata ficewa Ta kwashi kusan minti goma bata dauki komai ba tana zaune duniyar tunani sai da taga giftawar samiran a inda take sannan ta ankara ta miqe,wani abu ya darsu a zuciyarta,nana da nan ta soma zabar vest ta maza cotton fala qal mai kyau da taushi ta dauki gajerun wanduna dozen sai hand kerchief dozen agoguna na kamfanin gucci uku azurfa biyu takalma hudu budaddu biyu rufaffu biyu sai turarurruka na kamfanin rasasi sai rezar aski ta maza tare da shaving cream na nair,ta daukarwa kanta turaren blue lady sai relaxer,sannan ta amshi mutuminta wato ice cream manya robobi guda hudu,leda biyu aka mata kayan sai tata ledar ta tashi shafal babu wani abun kirki da ta dauka,kayan basu da wani nauyi don haka da kanta ta dauka ta fito,tana kusantar motar gabantana dada faduwa bata ga alamun samira ta dawo ba don haka ta iso motar ta sanya hannu ta bude gidan baya ta zuba ledojin hannunta sam sai ta kasa zama cikin mitar kasancewar aliyun na ciki don haka sai ta tsaya jikin motar ta jingina da ita ta harde hannayanata bisa qirjita tana bin harabar gun da kallo gamida qare masa nazari na yadda matasan yan birni maza da mata keta kara kainar shigowa gun da motocinsu  Sai fadila ta soma qosawa da tsaiwar gun ganin yadda duk naminin da zai gifta sai ya zuba mata idonsa,taja tsaki tana jin takaicin matsanancin kallo irin na waau mazan,kamar daga sama ta jiyo dakakkiyar muryar Aliyu yana cewa"malama koma.mota ki zauna tun ke bakisan me ya dace ba" a sanyaye ta juya ba tare da ta kalleshi ba ta shige cikin motar zuciyarta na mata quna da jajen yadda aliyu ke mata mu'amala tqmkar wata mara rai kunnuwanta basu taba jiyo mata kyakkyawar kalma daga bakin aliyu ba akanta,zuciyarta ta fara tafasa saidai ta danne bacin ran nata da kiran sunayen Allah,dama ta tsammaci fiye da haka ma daga gurinsa A hankali ta soma jiyo maganganun aliyu dake tsaye jikin mota sai ta tsinci kanta da kasa kunnuwanta cikin qaqanin lokaci ta fuskanci da mace yake hirar,kai tsaye ba zata fassara hirar data soyayya ba amma zaka fuskanci cewa akwai alaqa tsakaninsu ,mai da bayanta kawai tayi ta jingina da makarin kujerar ta lumshe ido tana sauraron bugun da zuciyarta keyi ta dauki tsaqon mintina a haka ba tare da ta tantance halin dabm take ciki ba sai da aka gama zubawa samirah siyayyarta a but qarar rufe buut dinne ya dawo da ita duniyar data Lula Muryar samira ta karade gun cikin tuhumar aliyu da wace yake waya cikin rashin ladabi bai kulata ba sai da ya gama wayarsa tsab yayi sallama dabwadda yake wayar ya kashe bai ko kalleta ba ya bide side dinsa ya shiga itama cikin sauri ta zagayo tana huci ta shiga itama ta bame qofar yana yiwa motar key ta sake jaddada masa tambayarta "na ce ma da wakake waya?"aliyu bai iya qarya ba don haka kansa tsaye ba tare da shayin komai ba yace"da maman iftihal kin gane?"ba samira da tayi tambayar ba hatta fadila da amsar ta daketa,samira ta hadiye abinda ya taso mata don bin qwaqqwafi ta sake jeho masa wata tambayar daidai sanda motar ta saitu akan kwalta"ro mw kake nufi da yin magana da ita gidanka take nufin dawowa koko ya aka soma?""duk yadda ta kama haka za'ayi"ya mayar mata kansa na kallon kwalta,saiga samirah ta dora hannu aka tana shirin zunduma ihu🙆🏻,da sauri aliyu ya sauka gefan kwalta ya taka birki yace"bari na sauke ki idan kin gama ihun saiki tari mota ki biyo ni tunda lasheki nayi ko kuma satoki nayi"ba tare da ta sauke hannun ba ta hau maganganu bai kulata ba ya figi motar ya koma hanya,fadila kam na baya ji take kamar babu jini a jikinta babu abinfa kunnanata da qwaqwalwarta ke ganewa har suka iso gida ita dai taga ficewar samirah fit kamar walqiya bata ma jira motar ta gaa parking ba don saura kadan ta fadi,ita kam bata da kuzarin yin hakan don haka ta jawo ledar da ta yiwa kanta siyayya tabar wadda ta masa,ta fara tafiya ta jiyo maganar sa abayanta yana tambayar ledar meye ta bari?ta sadda kai qasa😔cikim sanyin murya tace kayanka ne,ya sake damqe rai😠 yacekayana?na sanar da ke ne ina da buqatarsu?"dum dum taji atsakiyar kanta wadda tamkar an buga mata guduma a tsakiyar kanta taji,batasan sanda ta isa sashenta ba ita dai ta tsinci kanta ne kwance bisa carfet din falonta Aliyu yabi inda ta wuce da kallo ganin bata tanka masa bailla ma ledar hannunta da ta saka ta wuce tana raba hanya,sai yaji wani iri a cikin zuciyarsa yake jin kamar bai yi abu mai kyau ba ya sunkuya ya dauki ledar da ta saki din ya bude mota ya hada da tasan ya wuce sashensa don ko kusa baiyi sha'awar neman samira ba don yasan bazai tainci komai ba illa qarin damuwa da koke kokenta na tsiya,kai tsaye ya wuce bedroom dinsa ya dora ledojin bisa center table din dake gaban gadon ya cire kayansa ya shiga wanka bayan ya fito ya ciro kayan bacci ya feshe su da turare su haka nan jikin sa,ya shimfida sallayarsa yayi shafa'i da wutiri sannan yayi addu'o'insa ya shafa,ya murzawa qofan dakin key yasa hannu zai kashe wutan dakin din kwanciya idanunsa suka fada kan ledojin da ya shigo da su,bayan ya kashe ya koma ya dauki ledojin ya koma saman gado ya kunna fitilar gefan gado ya zazzage kayan dake ledar farko,daya bayan daya yake daga kayan sannu a hankali yake binsu da kallo,sai yaji kayan aun nurgeshi kamar ta san zabinsa,kayan sun masa sosai ya maida su cikin ledarsu,ya jawo tata ledar ya bude wani dan qaramun murmushi ya saki😊hadi da wani abu mai kamar tausayi da ya kamashi,sam list din siyayyar da aka turo masa nata bai kai daya bisa biyar din siyayyar samira ba,ya tashi ya bude dan qaramin pridge din dake dakin ya debe ive cream din ya zuba aciki ya hade ragowar kayan ya dora bisa bedside Kwananta biyu kenan tana fama da matsanancin ciwon kai da yaqi saukar mata ta wani rame tunani biyu ne ya addabeta,yiwuwar qara masu abokiyat zama wanda take ganinhaka wabi babban qalube ne da zai qara nisanta ta da aliyu sai kuma raahin sauki na qiyayyar ta da take gani qiri qiri atsakiyar idanun Aliyu Mrs muhammad ce 📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻 [10/16, 12:34 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 Wa yasan gobe?....... 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 Written by safiyya Abdullahi musa huguma 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 ▶1⃣6⃣ Yauma tana kwance saman carpet ta kanta bisa pillow kwanciyar rub ciki tayi saboda yadda take jin kan nata kamar zai tarwatse doguwar rigar bacci ce a jikinta iya gwiwa,gashin ta yayi dai dai kan pillow din,idanunta runtse suke ciki n haka ta jiyo sallamarsa,ta kadu sosai wanda hakan ya sake haifar mata da wani ciwon ko motsi ta kasa yi bare tayi yunqurin barin falon,tana jinsa har ya qaraso kanta yana sake maimaita sallamarsa,sai dai dif ta kasa amsawa sai wani bari da jikinta yake yi,yasa qafarsa ya dan bigi gefan pillow din da take kai ga zatonsa bacci take saidai nan ma yaji shiru,hakanne ya danso taba tunaninsa,ya sunkuya a hankali yasa hannayensa biyu ya birkitota gaba daya ta dawo rigingine fuskarta cikin tasa saidai idanunta na runtse don wani tsoron ne ya sake mameyeta,hawaye ya gani sharkaf a fuskarta ga wani dan banzan zafi da jikinta ya yi har haqoranta sun fara haduwa da juna"subhanallah😳"aliyu ya fada,surarta gaba daya ta bayyana har baisan sanda ya fadi hakan ba kyakkyawan gashinta ya sauko ya rufe fiye da rabin fuskarta,sai kuma yadda jikinta yayi zafi da yawa da yadda idanunta suka tasa,ya sunkuceta kamar wanda ya dauki tsinken sakace yana laluben bedroom dinta Saman gadonta ya ajjiyeta ya zuba hannayensa cikin aljihun wadonsa yana kallonta ya rasa mai ya kamata ya yi mata wane taimako ya kamata ya fara bata,don da gaske tanajin jiki rashin lpyr na damunta,a hankali ya bude labbansa yace"relieve ur self and stop d crying "sai da ya kwashi kusan minti biyar sannan yace"already dama baki da lpy?"ta gyada kai ya sake tambaya"meke damunki?"ta nuna masa kanta,bai sake cewa komai ba ya shiga toilet dinta ya hada mata ruwan wanka mai dumi a bathtub sannan ya fito "kishiga ki shirya kanki likita zata zo"daga haka ya fice,ta daddafa bango ta shiga toilet din ta sabe jikinta ta dawo ta saka doguwar riga ta atamfa mai dogon hannu ta fesa body spray ta hade kanta da band qarami ba tare da ta taje shi ba ta koma ta kwanta,bata dade da kwanciya ba taji ana knocking aliyu ne ya tura ya shigo bai dubeta ba taji yana bada umarnin a shigo Likitace sanye da kayan aiki,aliyu dama bai lamunci hurda da likita namiji ba akan matsalar iyalinsa tun usuli tun maman iftihal doctor sa'adah itace family doctor dinsa ta qware sosai akan aikinta tasan me take tamakar mayya haka take akan cuta da maganinta,da sallama ta shigo farar macace dirarriya wadda aqalla shekarunta ba zasu haura talatin da biyar zuwa arba'in ba doctor sa'adatu akwai ta da fara'a don.mawuyacine kaga fuskarta babu murmushi yanzun ma da fara'ar a fuskarta suka gaisa da fadila tana mata sannu yayin da Aliyu ya jawo dresaing chair dinta ya zauna hadi da zaro wayarsa ya soma danne danne,doctor sa'adah ta ajjiye kayan aikinta a gefan gadon ta fara fito da su tana tsokanar fadila"Allah dai yasa qaruwa muka samu madam😃"kunya ta kama fadila don a haife doctor ta haifeta,ta dan saci kallonsa sai ta ga ma sam hankalinsa bai kansu  Cikin qwarewa ta soma aikinta tana gwaje gwajen tana hada mata da tambayoyi,tambayoyinta har suka so rikita fadila domin tamakar doctor na son karanto zuciyarta ne ,fadila tayi ajiyar zuciya lkcn da doctor ta tsagaita da tambayoyin ta zauna a gefan gado yadda zata iya fuskantar aliyun sosai tace"gsky a.s maitama damuwa ce fal a zuciyar madam wadda itace musabbabin wannan ciwon nata wanda Allah ya gani da ace tana fa qaramin ciki da tuni tayi miscarriage dinsa,aliyu ya maida wayar sannan ya kalli😒sa'adatu ba tare da yace komai ba tasan bazaiyi maganar ba don ba komai yake bada amsarsa ba saboda haka sai kawai ta dora da bayaninta"ya kamata ka binciki abinda ya sanyata damuwa mai yawa haka,ya dauke idanunsa daga kan likita yana duba agogon dake daure a tsintsiyar hannunsa yace"doctor iya sanina bata da wata matsala amma gaki gata ai u can ask her"ya dago kyawawan idanunsa masu tafiya da zuciyoyin miliyoyin 'yammata ya zubesu fes bisa fuskar fadila,tayi gaggawar yin qasa da kanta don kada tana fama da kanta ya baro mata wani aikin,tasan cewar a yadda take jinta dinnan matuqar ta yadda suka hada idanu to la shakka qaryarta ta qare domin daga shi har sa'adah ba zasu sja wahalar gano mai ke dawainiya da zuciyarta ba"meye damuwarki?,ya furta cikin dakakkiyar murya ba tare da ya dauke idonsa a kanta ba ,da zata iya ba shakka da tace masa kaine!,kishinka da qaunarka aliyyu sune damuwata!!!,sai fainkash ko kusa bata jin zata iya,abinda take jin zata iya kuma ahi yafi dacewar tayi din shine shiru kuma shi tayi din Shiru din kuwa ya ratsa dakin doctor sa'adah tace"mai tama ba haka ake ba,it can be d screat ne she dnt wanna share it with another person so ka bari idan na tafi ta gaya ma a nutse"ta qarasa maganar tana yago pepper daga memonta mai tambarin asibitinta a jiki ta soma rubutu bayan ta kammala ta ajjiye takardar kusa da fadila da har yau kanta ke sunkuye tace"to madam Allah ya qara sauqi but pls kiyi qoqarin rage damuwa"kai ta daga ta mata godiya,sa'adah ta kalli aliyyu tace ga magungunan da za'a siya mata a nemo.yanzu ta soma sha zata samu relief insha Allah amma ta dan ci wani abu before ta sha din,ta miqe tana hada kayanta tqna musu salllama aliyu yace"thanks sa'adah a gaida yara Mrs muhammad ce 📚📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 Wa yasan gobe? ▶1⃣7⃣ Fitarta da yan mintina aliyu ya dauki pepper din maganin ya fice ba tare daya ce mata kanzil ba,shima ba dadewa da fitar tasa wayarta dake qarqashin pillow ta dau tsuwwa alamun shigowar kira,a kasalance ta daga wayar tana duba mai kiran sister farida ce ta daga hadi da yin sallama farida tayi dan jim sannan tace sister ya naji muryarki ta canza ne?fadila cikin muryar marasa loy ta masa mata wlh bani da lpy ne farida ya gida ya kuma mubarak?cikin yar qaramar dariya farida tace duk muna lpy sister ko ta samu ne?,samuwa kamarbyaya? Ta tambayeta,farida tayi qasa da murya tace ian nufin fa juna biyu,ta dan basar tace abinda kika bugo ki tambaya kenan?,a'ah anty dama ina ceqa ne gibe ki duba haya ina nan zuwa harda result dinki tun last week ya samu,duk da bata jin da lafiya hakan ya mata dadi sosai har ta nuna zumudi,jin bata da lpy yasa farida qyaleta akan sai tazo goben,ta amsa don dama kantabhar ya soma sarawa ta maida kanta saman pillow ta kwantar tana addu'ar Allah yasa ta samu damar aiki Ya shigo hannayensa biyu riqe da ledoji ya shigo ya zubesu kan bedside ya maida hannayanaa aljihu kamar kullum,ji tayi kamar ya cika mata dakin wani kwarjininsa ya cika mata gu jikinta yayi sanyi tanajin kamar ko hannuta ba zata iya dagawa ba ta shiga satar kallinsa duk fa batayi niyyar yin hakan ba zuciyarta ce ta tursasata kansa na qasa ne yana kallon carfet kamar mai nazari,sai ya mata kyau sosai fuskarana fes kama ganinta kasan tasan hutu tabbas maza irin aliyu sai ka tara dari zaka samu biyu cikinsu ga tsawo da qaqqarfan gangar jiki mai murdadden damtse mai cike da qarfi faffadan qirji mai cike gargasa wadda ta bayyana har hannayensa yana da jiki amma ba zaka kirashi mai qiba ba domin tsawonsa ya shanye ta,kusan ko yaushe fuskarsa a haka take ba fara'a sam don ita a iya saninta da shi bata taba ganin haqoransa ba, Saura qiris ya kamata tana satar kallonsa tayi gaggawar janye idanunta daga kanshi a hankali taji yace dazun na tambayeki meye damuwarmk yanzun ma na maimaita karo na biyu"shiru ta sake yi.masa hakan yasa ya kausasa.murya yana sake tambayarta,cikin cool voice dinta tace babu komai,ya dago kamar zai kalleta sai kuma ya lumshe ido ya budesu kan.ledojin da ya shigo da su sannan yace idan tashin hankalinki da damuwarki sun ta'allaqa ne kema kan dawowar maman iftihal to kiyi saurin taimakawa kanki ki nemi sassuci a gun zuciyar ki don zata dawo ne amatsayin mata ta karo na biyu ba wata baquwa bace......sannan ki bawa zuciyar dai taki again shawara da kada ta cika kanta da damuwoyi masu yawa tun yanzun......ya danja fasali sanna ya miqa hannunsa ga wayarta dake gefanta abinka da giant tuni hannun yakai ba tare da ya hau gadon ba ya lallatsa sannan ya ajjiye mata yace"ga abinci nan da magunguna ki sha,then ga number ta if there is any problem contact me"daga haka ya juya ya fita ba tare da Saura ron komai ba Sai abun ya zamewa fadila wani iri ta jima akwancen kafin ta samu damar miqewa zuciyarta na qarfafa mata gwiwa ta tashi ta taimaki kan nata kamar yadda aliyu ya shawarceta,tq shiga toilet tayi fitsari sannan ta daura alwala wai ko zata ji sauqin zugin dq zuciyarta ke mata,ta dawo bakin gadon ta bude ledojin daya magunguna ne a ciki daya kuma gasashshiya,ta dinga zare tsokar tana ci zuciyar ta dauke da addu'o'in samun sauqin daga quncin zuciya(inda Allah ya taimaki fadila kenan bata mantawa da add'a duk irin situation din da take ciki,muyi koyi da ita yan uwa domin hatta qaddara babu abinda yake tareta sai add'u'a,mu dinga tuna Allah a yayin da muke cikin jin dadi da walwala sai Allah ya tuna da mu lokacin da mu kuma muke cikin qunci da neman taimakonsa wannan fadar annabi ce s.a.w,kai ta addu'a da sannu Allah zai isar maka,take note pls!)jin naman take kamar magani mai daci haka taci gabada dannashi har tqji kamar zata yi amai,ta balli.maganin adadin yadda aka rubuta tasha sanna ta dan zauna na mintina don abincin ya fada mata sanna ta ja pillow ta kwanta,cikin ikon Allah ta dinga jin sassuci a zuciyarta,ta jawo wayarta sai taji tana qamshin aliyu ta soma duba contact dinta taga number din da yace yasa mata ai kuwa a rukunin A taci karo da sunansa full name dinsa ya saka mata ta bude numbers din tana qare musu kallo suma special ne don cikin taqaitattun daqiqu zaka iya haddacesu,(mrs muhammad nace ko na sato muku numbers din A.s maitama ne cikin wayar fadilan?to gasu 0803344.......😜😜 to naqi don naga wata har tana saurin kwafa ba ruwana ku da fadila😜)ta zuba musu ido kamar tana son ganin fuskar mamallakin numbobin da ta gaji da kanta ta rufe wayar ta maida ta qarqashin filon ta lumshe idonta tana maida numfashi cikin zuciyarta ta soma tilawar suratu yusuf tana yi tana bin labarin annabi yusuf din da Allah s.w.a ke bayarwa cikin surar,zuciyarta ta mata sanyi damuwarta ta ragu sosai lallai Allah yayi gaskiya da yace(ala bi zikrillahi tadma'innal qulub/ku saurara da ambaton Allah ne kadai☝🏼 zukata ke samun nutsuwa) To fa makaranta na labari yanzu muka soma shigarsa kuci gaba da jumurin bina insha Allah zamu cimma gaci😊 Dumbin godiyata a gareku Mrs muhammad ce 📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻........ [10/16, 12:35 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 Wa yasan gobe? 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 Written by safiyya Abdullahi musa huguma 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 ▶1⃣8⃣ Washegari misalin sha biyu na rana tana kitchen tana tafasa ruwan lipton so take ta dan sha ko zai warware mata ciki don tun tashinta yau ba abinda ta iya ci,muryar farida taji tana qwali mata kira da gudu ta fito suka rungume juna suna dariyar farincikin ganin juna😄,farida ta dan janye fadila daga jikinta tana cewa sister yi a hankali kada ki mana asarar baby,fadila ta ballamata harara tace"wai ke wa ya baki wannan labarin qanzon kuregen?farida tace bayan mun gama waya jiya da ke da daddare rabi'ah ta kira ni take gayan again,fadila na qoqarin komawa kitchen din tace uhm sai ki zauna ai kiyi ta jiran cikin,farida tayi dariya ta bita,maimakon daba lipton sai ruwan zafin ya koma na girki,suna yi suna casar hira,suka kammala suka zuzzzuba su a warmers suka wanke kwanukan hadi da gyara kitchen din Wash! Inji farida bayan ta zauna fadila ta kalleta tace kin canza sister fa sosai kinga qibar da kika fara yi?farida tayi murmushi tace ke dai bari ya fadila ina tsammanin ciki ne fa?,fuskarta cike da fara'a 😄tace ke dan Allah,tace wlh da jibi ko gobe mubarak ya matsa sai naje an min test wai kada na jawo masa asara cikin rashin sani ni sai naga kamar ba shi ba,kasala kawai fa nake da yawan bacci,fadila tace,a'ah nima fa ina bayan mubarak sister kije a dubakin meye amfanin zaman haka,kina likita ai kinfi kowa sanin alfanun abin,tace insha Allahu gobe zamu je Farida ta janyo jakarta ta bude ta miqawa fadila takardunta,cikin zumudi ta buda tana duba result din ba abinda bakinta ke fada sai alhamdulillah,domin kuwa yayi kyau fiye da yadda ta tsammata cikin farinciki tace da farida"burina na gaba farida inga na soma aikin media shine burina tun ina qarama"murmushi ta sakar mata tace"kwantar da hankalinki ya ahmad yana can yana miki wannan aikin don kuwa freedom da express tuni sun karbi takardunki jira yake kawai yaji daga garesu,wani farincikin da qaunar yan uwanta ya sake kamata Tana toilet tana wanka ta bar farida a afalo tana kallin arewa 24 suna haska maimaicin shirin boyle bitmesin wato kyautata rayuwa da yake jiya tace tayi missing bacci ya dauketa bata kalla ba,ta jiyo hayaniya sama sama ta tsinci dai muryar anty hauwa din haka a gurguje ta gama tana fitowa ta shirya kanta cikin shigar doguwar rigace ta shadda wadda aka mata paint work mai tasadar orange ce akayi mata kwalliyar light blue,body spary kawai ta fesa ta daura dankwalinta ta debo magungunanta wadanda zata sha da rana ta fito falon,rabi'ah ce da sumayya da anty hauwa,cikin fara'a suka gaisa suka mata sannu da jiki"tace ai na samu sauqi ina momy da iftihal mutuniyata,anty hauwa tace suna gida gurin momyn nace ne ba da wanda zanzo duk har su kausar suna gunta muhammad ma tunda ba nono yake sha ba acan na barshi don suna zamu wuce dqga nan wata maqwafciyata ce ta haihu to kuma da yake haihuwar ta danzo da matsala a gidan su take acqn za suyi taron,tace eh Allah ya qara mata lpy,amin inji anty hauwa Nan suka shiga hira abinsu minti talatin suka miqe suna shirin tafiya fadila dake ta qoqarin zuba musu abincin tace anty ga abinci don Allah ku tsaya kuci,anty hauwa tace bayan lemo da cake da kika cika mana ciki da shi alhamdulillah wlh,rabi'ah tace nikam anti fa na fasa rakiyar nan gidan sunan kuce da maman hidaya ina mata barka na taho anjima farida ta saukeni a hanya,sumayya tace"dama na sani anti ba rakaki zata yi ba ina ji tana cewa yau ana rana da yawa nasan dama daga nan gidan ba inda zata dara"aishikenan muje mu gaisa da samirah sai.mu wuce,inji anty hauwa,sumayya ta coge😒sannan tace a'ah anty nikam zan jiraki cikin mota ki shiga ki fito tayi saurin yin gaba damma kafa antin ta tsayar da ita,fadila tace "baki kyauta ba sumayya idan kika wuce baki gaidata ba"rabi'ah dake zaune tace wlh anty ko nice ba zan je ba,farida dake ta faman cin abincinta abunta tace qyalesu sister mai daki shi yawan inda yake masa yoyo✋🏻,ai kuwa dai sister farida sai.kaje kayi ta bugu taqi budewa gashi fa kana kallo ta tana kalloka qiri qiri,bayan kuma ta bude sai tayi.bake bake a bakin qofa ta tsare ka da ido tana wani ce maka meye?kamar wanda kazo maula gurinta,duk suka kwashe da diyar yadda rabi'ah ta gwada yadda samiran keyi banda fadila da ta dan murmusa gami da girgiza kai tana mamakin halayya irinta samirah Biyar da rabi farida ta dauki rabi'ah suka tafi suma sashen sai ya dawo sai ita kadai ta so ta yiwa farida zancan dawowar maman iftihal sai kuma taga mai hakan zai dadeta da shi iyaka ta taya ta jimami sai shawara wadda a yanzu ita ma bawa kanta da kanta take,tunanim data fara yin zurfi a ciki ne yasa barin kanta ya soma ciwo bata yada hakan yayi zurfi ba ta tashi ta jona home theatre dinta ta saka cd plate na karatu ya karade falon Takwas da mu mintina na dare nasiru ya turo hancin motar ogan nasa cikin gidan,ya samu parking space ya daidaita tsayuwar motar sanna ya kasheta,a hanzarce ya fito ya budewa aliyu shima ya fito sannan ya miqa masa keys din motar yana fadin gashi sir ya amsa yana cewa debo min files din nan na sit din gaba,ya debosu ya bashi sukayi sallama aliyu ya sallameshi,hankalinsa gaba daya ya yi gaba burinsa kawai ya isa sashen nasa ya watsa ruwa a jikinsa ya samu ya kwanta ya huta,ya soma tafiya idanunsa suka kai kan sashen nata babu wadatar haske kamar bangaren samira dake tarwai da haske harda qarar abin kida ya dauke kai ya shige Yana fitowa daga toilet ya zabi doguwar riga jallabiya fara sol.mai yankakken hannu ya saka ya feshe jikinsa da turarukan baccinsa masu sassanyan qamshi kan sofa ya fada ya miqe qafafunsa sannan ya hardesu ya kansa na kallon sama yasa daya hannun nasa ya shafi cikin sa,yunwa yakeji amma ya rasa inda za shi ya samu abincin da zai gamsar da shi,mutum ne shi.mai tsan tsami ba ko ina yake iya saki jiki ya ci abinscinsu ba sai ya yarda da ingancin tsaftarka hakan ne yasa ya tsani masu aiki hakan yasa tun yana gida ya yi ruwa yayi tsaki ya hana mominsa daukar masu aiki yace meye amfani su sumayya duk da suma bai yarda ko kadan yaci girkinsu sai na mominsa Ya tashi ya qarasa fridge ya bude ya dauko yoghurt na l&z ya hado da fura ya samu cup ya dama ya sha ,ya sake tashi ya maida cup din kitchen sannan ya qarasa window dinsa yana bude glass din don ya bawa iska daman shigowa duk da iskar a.c da ta mamaye dakin kasancewar mutum ne shi maison natural air,idonsa ya sake fadawa kan bangaren nata duk da yaune ya shigo bashi da niyyar ganin kowa bacci yakeso ya samu isashshe don haka har wayoyinshi ya kashe su gaba daya Ya saki labulen yana ajiyar zuciya saboda tunawa da yayi haqqine a kansa ya kula da lafiyarta don rabonsa da ita tun jiya da ya batta da magungunan da ya siyo mata ,ya zari keys dinsa ya zura slippers dinsa ya fice 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 ▶1⃣9⃣ Tana kwance a miqe sambal bisa kujera three sitter don tunda tayi sallar isha'i bata tashi ba agun falon tsit yake ba komai sai sanyin na'urar sanyaya daki wanda ta gauraye da qamshin freshner mai dadi idanunta na lumshe ne tamkar mai bacci saidai ba bacci take ba tayi nisa ne a wata duniya mai wuyar fassarawa duk da ciwon da kan yake mata das das das amma hakan bai dameta baqarar bude qofan falon da qamshim mayen turarensa dake rataye da zuciyarta shi ya dawo da ita,ta bude manayan idanunta akansa yayin da shi kuma ke qoqarin tura qofar tayi namijin qoqarin tashi ta zauna kanta na sunkuye a qasa don ba zata iya jurewa kallonsa ba,hannayensa ya goye a bayansa ya qaraso falin yana kallonta da qayatattun idanunsa ya lura kamar ta dan rame duk da ba sanin ainihin kamanninta ya yi ba"ina yini"tace still kanta na qasa,cike da qasaitarsa da izzarsa ya dauke kai ya maida mata gaisuwarta da tambayar jikinta,da sauqi ta fada cikin sassanyar muryarta data sanya yaji wani dan yam ajikinsa Bata zata ba bata kuma tsammata ba sai jinsa tayi zaune kan kunerar da take kai.kuma dab da ita ya sanya bayan hannunsa a wuyanta da niyyar jin temperatures din jikinta ba komai aransa,sai dai baisan illar da ya sake yiwa fadila ba a zuciya da gangar jikinta ba,kasala mai tsanani tashi guda da kuma wani irin shauqi taji ya saukar mata numfashinta ya tsaya cak na wucin gadi,sam bai kulaa ba yace"still jikinki da ragowar dumi ya kamata ki warke kafin isowar abokiyar zamanku right?ya qare maganar da sigar tambaya,ya.miqe yana cewa babu abinda kike buqata,tamkar ta ce masa"kai nake buqata aliyyu ka qarashe awoyin wannan daren naka tare da ni,maimakon haka sai ta sake gyada masa kai,yace " alright gudnyt"ta bishi da kallo idanunta fal cike da qaunarsa da kewarsa har ya fice daga part din nata ya rufe mata part din,ta koma da baya ta jingina jikinta da kujerar hadi da runtse idanunta hawayen dake maqale a idonta suka gangaro mata wani radadi da zugi zuciyarta ke mata lallai kishi masifa ne Cikin daren bacci gagararta yayi juyi take kawai akan makeken gadonta cike da sha'awar aliyu tunda take bata taba jin makamanciyar sha'awa arayuwarta irin wannan ba ⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜ Sannu a hankali ta miqa dukkan lamuranta ga Allah cikin ikon sa kuwa ta fara samun sauqinsu saidai fa har yanzu babu sauqi ta bangaren soyayyar Aliyu dake maqare cikin zuciya ,cikin lokacin sam ta daina bari idanunta suga aliyyu duk da tarin zugi da zullo da zuciyar keyi na son ganin nasa amma ta danneta Cikin lokacin aikinta ya samu freedom da express din duk suka buqaci yin aiki tare da ita,ya ahmad dinne ya kawo.mata da kansa bayan ya sanar da aliyu da kansa ya kuma amince mata da fara aikin nata,tayi murna tayi tsallae tun a gaban ya ahmad din ya sha godiya sosai har da qwallar farinciki saboda yadda take masifar son aikin jarida shikam dariya yayi yace Allah zata godewa,bayan tafiyarsa ta kira farida dake fama da laulayi suka sha murnarsu tare,nan fa ta zauna ta soma tsarawa kanta yadda zata tafi da rayuwar aikinta ⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜ Cikin satin Aliyu ya shirya musu fita wadda ta farko ce agun fadila don bata taba fita ba wani gu da sunan unguwa ba bayan shopping da suke zuwa duka qarshen wata za suje ne gaida hajiyarsa Tun rana fada ke zumudin fitar tana tunanin mai zata kaiwa momin,akwatunan lefenta dake shaqare da kaya wadanda kamar ba'a taba amfani da komai a ciki ba ta bude ta zabi turarurruka designers guda uku ta warewa abba,ta duba akwatinta da ta adana gift da ta samu na biki ta cirarwa momin atamfofi super Holland da England guda biyu,da kanta ta aiki yaron dake musu gyaran flowers ya samo mata kilishi mai kyau da zuma Tun magariba ta yi wanka ta shirya kanta cikin atamfa dinkin riga da zani kamar light grean da milk sai ratsin baqi dinkin ya mata cas kamar a jikinta aka qirqireshi yari da sarqa ta saka ma dutse masu kalan milk sai farin agogon hannu tq zuba awarwaro mai 24 farare takalmi da jaka milk sai laffaya data nannade jikinta da ita milk ce mai adon baqi ta debi tsarabarta ta dawo falo ta kunna arewa 24 tana kallon shirin matasa at 360,tayi wani masifar kyau ta fito sosai a babarbariyar ta Ya qarashe karin hular sa yana daidaita ta a kansa shaddace fara qal a jikinsa dinkin tazarce sai walwali take ta sake fidda sirrin kyawunsa mutum ne shi ma'abocin iya ado ta wannan fannin kam ko mace haka ta ganshi,komai nashi fari ya sanya hatta da agogo,ya sanya glass dinsa sanna fesa turarensa ya rufe sashen 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 ▶2⃣0⃣ Bangaren samirah ya nufa wanda sai ta kama dole yake shigar sa,ga mamakinsa aai ya taddata sirshan tana zaune abinta zaninta da rigarta daban daban kanta da ta tsefe shi yana tsaitsaye kamar tabarya😜dama ita ba wani tsawon gashi gareta ba sai qarfi da gashin yake da shi,ba abinda falon keyi saiqarnin kifi sardine ta tara gwangwanayen a gabanta ua daurw yadda qarnin ke bugar hancinsa yana tayar masa da zuciya cikin bacin rai yace mata zaman me kikeyi baki shirya ba tun dazun?ta dan yatsina fuska tace qawatace wlh ta kiarani a waya ta kwasheni da jira ya gyara tsaiwarsa cike da qosawa da azababben qarnin kifin yace mata is ok sai ki nemi wanda zaku tafi tare kinsan bana jira yana kaiwa nan ya sanya kai zai fice yana jan tsaki cike da takaici ,ta yi saurin shan gabansa tana cewa haba sweet kayi haquri mana pls ka bani minti uku kaya kawai zan canza,ya kauce ya fice yana cewa wataqila idan kinyi sauri kin tadda ni kafin in ciro mota is ok,ya barta nan baki a sake ta bishi da kallo sai kuma ta zabura tayi cikin daki don ta shirya Knocking taji anayi don haka ta zira hill shoes dinta fari ta rataya jakarta ta dauki ledarta don jikinta ya bata aliyu ne shi dinne kam idonsa na bisa screen din wayarsa yana danne danne bai dube ta ba ya juya taja part din nata ta kulle tabi bayansa tana qare masa kallo"ya gaji da haduwa"ta zanta hakan a ranta,tana jingine da rumfar ajiyar motoce har ya gyara parking qa'idarsa ne indai tare zasu fita baya neman driver duk da dama nasiru ne kawai.ke driving dinsa,wanni dogon hirn ya ja da sauri ta daidaita nutsuwarta ta nufo motar tun kafin ta qaraso taji an bangaji kafadarta da mamaki ta dago don ganin waye samirah tana ta zuba sauri zani a hannu tana gyara daurinsa,duk saurin da take gidan gaba aahe takewa,abun ma sai ya baiwa fadila dariya ta saki murmushi😊 Cikin mintuna da basu gaza talatin ba suka qaraso gidan,harabar gidan tsaf kuma fetal da haske ba kowa sai mai gadi shi da wasu mutum biyu zaune kan benci suna sauraron duniya tumbin giwa suna cin gyada jefi jefi suna taba hira,cikin girmamawa ya gaida aliyu sannan ya gaida su fadila ta amsa masa fuska a sake tunda dama da yar sanayya tsakaninsu ya samirabko kallo bai isheta ba bare tasan yana yi,ya dage masa get din ya wuce ya yafitoshi yayi masa ihsani kamar yadda ya saba shi da wadanda ke zaune a gun suka hau zuba godiya abinsa shi kuma baiso Samira da aliyu suka jera suka fara yin gaba zuwan falon gidan fadila bin bayansu tayi ,sumayya da rabi'ah ne zaune a falin da hijabai ajikinsu da alamar sallar isha'i suka idar,suka juyo suna amsa sallamar sannan suka miqe tsaye cikin farin ciki suna gaida su hankalinsu na kan fadila itama su take kallo suna gaisawa sabanin samirah da ta riqe qugu tana qarewa falon kallo tana yaba tsaruwa da dukiya da ya lashe kamar wadda aka bawa kwangila sannan daga bisani ta zabi kujerar da tayi.mata ta zauna akai,cikin dakiya irin ta babban wa yake tambayarsu ina momy sumayya tace tana sama ya nufi benan taku biyu uku sukayi kacibus da iftihal na saukowa kamar yadda ta saba ta tsugunna ta gaidashi sanna ta daneshi ya sabeta a kafada yana tambayarta momi Tare suka sauko shi da momin yana take mata baya iftihal na hannunshi ganin fadila ya sata ta zille ta diro ta nufeta a guje cikin murmushi fadilan ta tareta ta dora ta bisa vinyarya dukkaninsu suna dariya ta gaisheta,duskar momi washe da fara'a take.musu barka da isowa samira dake zaune dare dare bisa kujera kamar tata tave yauwa fadila dama.na qasa ne kan carpet ta duqar da kanta qasa tana murmushi cike da kunyar momin,gaisuwa aukai da samirah kamar qawa da qawa yayin da fadila ma ta kasa hada ido da ita a haka suka gaisa,ganin taqi sakin jiki ya sa momyn tace su rabi'ah su kaisu dakinsu itama zata gun abbansu yanzu ya shigo gidan,hira suke abinsu da fasika yayin da samirah ta zaro wayarta ta hau danne danne tana ganin duk ta girmesu tafi qarfin zama cikinsu ai,ga takaicin yadda aujewa fadila haba haba itq aunqi mata haka cikin ranta take cewa hmm dangin miji kenan tsinannu(kunji fa?) A haka bacci ya dauki iftihal akan cinyar fadila aliyu ne ya leqo hukarsa a hannu yace ke sumayya ku taho dining"samrah ce ta fara miqewa tana cewa dama yunwa nake ji ta fice,qememe iftihal taqi kwanciya dole iftihal na nishi ta sabota a kafada suka fito su sumayya nata dariyar yadda ta dauki ifrihal din da qyar,momy ce da abba sai aliyu bisa dining din kusa da abban abba na dariya yaceyau ban dawo da wuri ba bare a murqushen tsohon qashi na shine aka rama akanki ko? Duk sukayi dariya kowanne ya samu kujera daya ya ja ya zauna banda fadila dake tsaye sabe dà iftihal wani baccin nason daukarta amma ta qi yarda tayi don kada a sauketa Mrs muhammad ce 📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 Wa yasan gobe? 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 Written by safiyya Abdullahi musa huguma 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 ▶2⃣1⃣ Momy ta kalli aliyyu tace alii rabata da rigi mammiyar yarinyar nan don idan ba kai ba ba wanda zata yarda ya sauketa,ya miqe ya nufesu yanayin yadda ya tsaya gab da ita yana yunqurin karbar iftihal ya haifar mata da wani yanayi cikin jikinta,ya sa hannu zai dauketa cikin rashin sani hannunsa ya shafi qirjinta wani abu taji ya tsirga mata tun daga kanta har tafin qafafunta hakanan shima yaji tsigar jikinsa ta tashi wani shocking yaji kamar an jashi da wutar lantarki,ya sabata a kafadarsa ta miqe zata soma rigima suna hada ido da shi tayi gum da bakinta🤐 ta mayar da kanta kafadarsa ta kwantar ya sauka da ita cikin falom ya kwantar da ita bisa doguwar kujera ya karanta mata addu'o'in bacci na tsari ya tofa mata sannan ya koma Ta tsugunna ta gaida uncle abba ya amsa mata cikin kulawa yana cewa lpy lau diya ta,sannan ta ja kujera itama ta zauna,sumayya tayi serving din kowa🍽🍴 sannan akai bismillah aka fara ci,kwata kwata kasa sakewa fadila tayi ta kasa kai koda loma guda bakinta sai juya cokalin kawai take a cikin abincin ,amma ga tarin mamakimta sai taga samira ta saki jiki tana ta kaiwa uwar hanjinta🍜 harda tsiyaya lemo 🍹🍾da ruwa da kanta,tayi sakewar da ko ita da uncle abba yake kamar uba a gareta ba zata iya irinta ba Abinka da mata momi na ankare da yanayin nutsuwar kowaccensu tana kuma sake godiya ga sarki Allah da ya qaddara fadila ta zamo daya daga cikin family dinsu,afakaice rabi'ah ta qarewa samirah kallo uadda take lodar abincinta ko aliyyu da yake dan gida baiyi haka ba,ki saki jiki mana fadilan ummi kici abincin ki mu fa iyayenki ne ko babu aliyu baki ga yadda yar uwarki ya saki jikinta ba?,cewar ummi,samirah ta amshe cikin tabe baki tace momi kinsan wani akwai qauyanci da rashin wayewa atare da shi"sai kowa yayi dif rabi'ah da takaici ya cikata tace ba rashin wayewa bane kowa dai da irin yanayinsa,ta sake tabe baki tace uhmm,ita kuwa fadila dariya ma ta bata sai daga qarshe ne taga kada suji ba dadi ta kurbi lemon da rabi'ah ta zuba mata Bayan sun kammala momi tasa rabi'ah da sumayya suka gyare gurin suka kwashe kwanukan,suna shirin wucewa don su basu guri momi tace su dau iftihal su wuce da ita,falon yarage daga fadila aliyu samirah sai momi da uncle abba Abba yayi gyaran murya yayi bismillah sannan ya kirawo sunan aliyu ya amsa masa"naam abba"ya dora "aliyyu girma yanzun ya hau kanka duk da a baya kwatan kwacin wannan girman ya taba hawa kanka kuma kayi namiji qoqari wajen riqeshi yadda ya kamata amma bai kai wannan ba,a yanzu dole na sake jaddada maka saboda zama ne da zaka yishi tsakanin iyalinka har su uku wanda ko ni mahaifinka banyi duk da komai tsarin Allah ne Daga samirah har fadila babu wadda gabanta bai fadi ba har sai da samiran yabdaga kai ta kalli abban,uncle abba yaci gaba "lamarin mata ali sai da haquri kawaici da kuma jajircewa halitta ce su maau wuyar sha'ani amma idan ka duba Allah sai komai ya zo maka da sauqi ,aliyyu ina horarka da kaji tsoron Allah ka tsaida adalci tsakanin matanka duk wadda ka cuta wlh wlh sai allah ya bi mata haqqinta sai kuma ya tambayeka,kuma ko ni ban lamunci rashin adalci ba acikin gidanka ka riqe Allah ka kuma ji tsoronsa Ya juyo gunsu fadila da kansu ke qasa kowa da abinda ke cikin zuciyarta yace "dukkaninku ina kallonku ne a matsayin 'ya 'yana na na cikina da na haifa nasihar da zan muku itace kuma ku ji tsoron Allah kuyi zamqn aure a matsayin ibada kuyi biyayya ga mijinku.ku kyautata zamantakewar ku domin kuwa shine muqullinku na shiga aljanna ko wuta idan kuka saba masa Allah ya tsare mu,magana ta biyu kuma na dakatar da shi ne daga gaya muku don inason na gaya muku ni da kaina ta hanyar da ta dace,nasan kowacce mace haka Allah ya halicceta da kishi kuma ba zaku so abokiyar zama ba a yanzu amma ba yanda muka iya da hukuncin ubangiji kuma aure rai ne da shi matuqar bai qare ba komai dadewar zamani sai an dawo anci gaba da yinsa to ina mai baku haquri a madadin aliyyu,mahaifiyar khadija(sunan iftihal na gsky haka abba ke kiranta yawancin lokuta)zata dawo dakun aurenta ina fata zaku hada kanku ku zauna lpy,samirah ta dago kanta a gigice tana fiddo da idanu waje😳tace"abba mai kake fada ne?dama da gaske aliyu yake da yafara zancen?" aliyyu ya juyo ya kalleta wani huci ya saki abba ya lura da yadda yanayinsa ya canza ya san yadda fishin aliyyu yake don haka ya danne shi,cikin tausasawa ya kalli samira yace ki kwantar da hankalinki yata insha Allahu ba zaku fuskanci rashin adalci ba daga gun aliyu ni kaina bazan lamunci hakan ba shiru tayi tana muzurai idonta ya kada yayi ja saboda ganin yadda aliyu ke gasa mata hara ra tamkar zai cinyeta danya,itakam fadila gabq daya jikinta ya saki tunaninta daya ta ina zata samu aliyyu bayan ga wasu na farautarshi ? Jin sunyi shiru dukkaninsu abba yace da momi"kina da magana momin yara?" Ta danyi murmushi tace" aikace komai abban yara,saidai nace aliyu kaji tsoron Allah kamar yadda abbanka yace sannan ku kuma Allah yayi muku albarka kuyi haquri kuma kuyi biyayya sai.kuci riba"suka amsa da amin banda samira da ta kasa furta komai sai tafasa da zuciyarta keyi,abban ya sake basu dama akan idan da mai magana ya yi,ba wadaa tace komai sai aliyu da yace"abba da momi na gode muku kuma insha Allah zaku sameni mai amfani da duk nasihar da kuka yimin zan zamo mai adalci da yardar Allah"Allah ya amince suka ce,fadila ta fito da kayan data taho musu da su ta dorawa abba nasa a gabansa sann ta dorawa momi nata Duk da ranta babu dadi amma ta ji dadin yadda suka nuna jin dadinsu suka sa mata albarka,aliyyu kansa can qasan zuciyarsa yaji dadin hakan don shi mutum ne mai dake qaunar wanda ke kyatatawa iyayensa,haushi ya sake cika samira tayi dana sanin zuwan ta gidan yafi sau cikin carbi bata son taga wani yana yabo ko son fadila kwata kwata Cikin mota ma kowa da irin zaren da yakr saqawa zuciyarsa shikam ya dake abinsa kamar bashi ya sanar da mata har biyu zai qara musu abokiyar zama ba tuqinsa kawai yake a nutse,fadila tata saqar na yadda zata juyo da hankalin aliyu take bata so kuma bazata so ace kishiyoyi har biyu su fuskanci raahin qauna da jituwa dake gudana tsakaninta da shi ba,samira kuwa wani mahaukacin kishi ne ke taso mata zuciyarta namata saqa da baqin zare,tana shirya mata irin mummunan matakin da ya kamata ta dauka abu guda ke taka mata burki idan ta tuno yadda aliyyu ya birkice mata da yanayin da ya sameta a daren farkonsu tasan har yanzu dafin na sukar zuciyarsa somin kuwa duk wani tanadin soyayya da sukayi wa juna tn daga ranar ya rushe,duk kuma waa qauna tata dake zuciyarsa wadda ta rage tuni ta rushe Cikin satin komai ya fara kankama abubuwa suka cedewa baiwar Allah fadila ga zirga zirgar shirye shiryen fara zuwa aikinta ga kuma lamarin na dake mintsinin zuciyarta duk da shiryr shiryenta ya tafi da kaso.mafi tsoka daga damuwar dake cin xuciyarta,tuni tayi waya gidan an ma motocinta service daya tsohuwar tata ce tun ta gida aka sake mata fenti da wasu abubuwa sai ta tashi ta dawo sabuwa dal don tana qaunar motar bata son rabuwa da ita yanzu sai kuma wadda aliyyu ya sa musu a lefe wadda ta sam ira tuni ta dade da cin uban tata ta mora qawaye su ara suma su mora Kira ta dinga samu daga su anty hauwa anty hafiza har da farida kowannan su nasiha ce da jan hankali ne nasa har farida ta so karayar mata da zuciya saidai tayi qoqari matuqa wajen nuna dakiya da mai da komai ba komai ba 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 Wa yasan gobe? ▶2⃣1⃣ Samira kuwa abun nata sai ya zamto tamkar mai qaramin ciwon hauka kamar a kanta aka fara kishiya kasancewar ta samu gudun mawar zuga daga qawaye da yan uwa kala daban daban duk da wasu ba don Allah suke bata basuna baqinciki da rufin asirin kawai da take ciki ne(qalubale a garemu mata sai azo ayita baki shawara akan za'a miki kishiya ko wani harkar wani ahaka kamar mai sonki amma da zaki ga cikin zuciyarsa game da ke tsoronsa ma zaki koma ji,sanin haqiqanin mutum sai Allah,sai ki auna da hankali da Allah ya baki a matsayinki na mutum mai tunani)sai ta sake zama kamar zararriya ita kadai ma abangarenta sai ka jiyota tana bala'i tana zunduma ashariya(wa'iya zu billah)cikin satin baqi ta dinga yi kala daban daban kowanne da tasa guzuri da salon hudubar waccan ta shiga waccar ta fita Tun Aliyu na zuba mata ido idan tana salon rashin mutuncinta da haukanta har sai da ya zamto idan tazo sai dai ta gajibda bugun sashen nasa ta juya da haukanta ta koma inda ta fito,tuni fadila tabgama tsarawa kanta yadda zata tafiyar da rayuwar aurenta ta gama tanadar komai,tana hango cewar itama fa maca ce tana da duk wani abu da da duk wata ya mave maiji da kanta ke taqamar tana da shi,tana da duk wasu qualities da ake buqatar mace da su kafin ta amsa sunan ta na mace,to me yayi saura banda itama ta shiga fagen a dama da ita?? Me zata jira banda ta shiga ta karbo aliyyunta? Ta gaji kuma lokaci yayi da take ganin ya kamata ace ta kasance da da shi ta gaji da dako da rainon soyayyarsa ita kadai ⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜ Biki ya zamto saura kwana uku wanda yayi dai dai da sauran kwanaki bakwai fadila ta soma zuwa aikinta A ranar ne bayan sallar magariba aka shigo mata da akwatina set shida masu matuqar kyau maqarenda kaya nasiru yace mata inji maigida,ta jinjina kai ta rufe qofar sashen nata ta koma kan kujera ta zauna daya bayan daya ta budesu ta zubawa kayan ido duk budurin da ake sai yanzu zuciyarta ta tsinke hawaye suka soma zarya a kuncinta a hankali take sa yatsunta tana sharesu tabbasa an jarrabci rayuwarta da jarabta mai girma ta sani cewa son aliyu jarabta ce daga ubangiji acikin jininta yake kuma bata fatan Allah ya dandanawa wata mace kwatankwacin yadda take ji a zuciyarta,nan saman kujerar ta lafe tana hawaye a hankali take furta HASBUNALLAHU WA NI'IMAL WAKIL har taji zuciyarya ta soma sanyi Haya niya da hargowa take jiyo wa maau qarfi suna karade filin gidan hakan ya sanya kukanta katsewa ta tashi kamar mai sanda ta isa window dinta da yake cikin balcony dinta ta yaye labulen ta riqeshi a hannunta,daga nan tana iya hango dukkq sararin gidan samira ce ke wannan hayaniyar cikin hargowa da babat tanajanyo akwatina irin wanda nasiru ya kawo.mata dazu daga part dinta daya bayan daya tana cillarwa anan tsakiyar filin gidan ko nauyinsu bata ji ,aliyyu na tsaye hannayensa harde a qirji ya zuba mata ido bai ko motsa ba Sai da ta gama lodesu sanna tayi cikin gidan nata a fusace sai gata da gallon da ashana ta daga tana qoqarin bulbula musu fetur din da yake ciki sai a lokacin aliyyu yasa hannu ya fincikota baya a fusace ya nunata da dan yatsa yana cewa kul kada ki soma,ta dubeshi duk da ta tsorata da yanayinsa amma sai ta dake cikin bala'i take cewa" sai na qona aliyu sai na qona wallahi kayan fadar kishiyan wata tsiya ce,sai dai idan na qona idan ka so nima ka qona ni" ta sake zabura tayi kan kayan da nufin idar da niyyarta cikin qaraji da tsawa ya ambaci sunanta wadda sai da hantar cikinta ta kada amma sai ta waiwayo tace"ko kasheni zakayi ba zan fasa ba" tadai sake nufar kayan cikin azama a karo na uku,cikin fusata yasa hannu ya janyota baya harsai da ta zube warwas a gun tamkar ya bita ya tattaka haka yake ji,don da namiji ne ya masa haka to yanajin ba shakka sai ya nuna masa qwarin qwanjinsa Ta sani cewa idan taci gaba da abunda take hukuncin da zai yanke mata ba mai sauqi bane hakan yasa tana daga zaunan ta hau borin kunya cikin surutai da maganganu marasa kan gado daga baya ma da taga ya qi kulata sai ta fashe da kuka Ko kallo bata isheshi ba ya dinga siban akwatunan bibbiyu bibbiyu ya shigewa da au bangarensa yana gamawa ya rufe qofarsa ya barta a nan,data waiga ta waiga taga ba kowa ba wanda ya gansu sai ta goge idonta ta miqe tana kade zaninta tana wa allah godiya da ba wanda yaga abinda ya faru tana yi tana tsinewa hannatu qanwarta gashinan ta jawo mata asarar akwatinan ma dungurun gum dan ita ta bata shawarar tayi haka A falon sa ya zube ya dafe kansa hannu bibbiyu yana tsananin jimanta al'amarin to haka mata suke ne basu da hangen nesa ya jima a haka sannan ya tuno bai ma shiga bangaren dayar ba kamar yadda yake ce mata a ransa"itama idan ka shiga wataqila haukan da zata yi maka kenan"wata zuciyar ke gaya masa,ba yadda ka iya tunda itama aqarqashinka take kuma ka shigarwa 'yar uwarta indai adalcin kake son yin Da sallama ya shiga ta amsa a sanyaye tana zaune ne kan kujera hijabin da tasa ta budewa masu shigo da kaya har yanzu shine a jikinta saidai sabanin da yanzu akwatinan a rufe suke,a fakaice yake dan nazarin falon komai tsaf yake cike da tsafta da qamshi hakanan komai a killace yake a muhallinsa da kyawunsa kamar yau aka jerashi sabanin falon samira da komai ya fita hayyacinsa saboda rashin kulawa duk da dama tsadar kayan ma ba daya bane don iyayenta basu da qarfin iyayen fadilan,kanta na qasa ta dam zamo daga kan kujerar tace ina wuni? Duk da bata sa ran masawarsa ba don bai taba amsa gaisuwarta ba ga mamakinta wannan karon sai taji yace "lpy ga kaya nan abinda babu ko baiyi ba sai ki yi maga ko ki rubuta ta girgiza kai tana cewa😔 komai yayi mun gode Allah ya qara arziqi" ya lumshe idanunsa don har zuciyarsa ya ji dadin addu'ar "madalla" yace ya zaro bandir na dubu dubu guda uku ya dora saman akwatinan ya juya ya fice sai yaji wani sauqi na radadin da zuciyarsa ke masa addu'ar ta faranta ransa don tunda yake bai taba samun kwatan kwacin wannan ba daga bakin wani abu wai iyali ba Muje zuwa yanzu aka soma Mrs muhammad 📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻 12:45 pm 03/11/1437 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 WA YASAN GOBE? 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 Written by safiyya Abdullahi musa huguma 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 ▶2⃣2⃣ Ana ya gobe daurin aure su anty hafiza anty hauwa farida sumayya rabi'ah har da rahama suka zo wa fadila,farida ta zube dinkunan da fadila ta bayar aka mata sunyi matuqar kyau da gaske duk da tana da sababbin din kunan ma da bata taba sa su ba,kala ashirin farida ta zabar mata aka dinko su lace biyar atamfa biyar shadda biyar material ma biyar ne,anty hafiza ce ta taho mata da mai gyaran jiki gashi da lalle takanas sai hade haden magunguna namu irin na mata imgantattun na 'ya'yan itace,anty hauwa sai dariya take tana cewa o'o'o fadila 'yar gata to ai ko kece amaryar sai haka,sai dai tayi dariya ta sunkuyar da kanta qasa cike da kunyarnan ta ta,anty hauwa ta zuge jakarta ya fito da littattafai tace ga saqon momi nan,hannu biyu tasa ta amsa tana godiya litttafai ne kusan goma na addu'o'ine da kuma gyara zamantakewar aure, Zuwansun ya sake debe mata kewa taji dadi nan suka fara tsara yadda za su gudanar da yinin su na gobe wanda ko wacce mace da za'a qarawa abokiyar zama ke gudanarwa,wuni akai ana qalqale mata jiki yayin da su rabi'ah sumayya da rahama suka zage wajen qal canzawa gidan fasali,sune canza labulaye canza carfet goge goge da ahare share duk da komai na fadila tsaf yake sai abinda ba'a rasa ba,cikin qanqanin lokaci kuwa gidan nata ya canza kamar ba shi ba,hatta qamshinsa sai da aka canza kalarsa ya zama na musamman abinka da diyar bare bari Rahama ke tambayar fadila samirah fa?fadila tace wlh tun safe dai naji tashin motarta amma ban sani ba ko qunshin itama ta tafi "Allah ya kyauta inji anty hauwa ,bayan isha'i komai ya kammala anty hauwa tace zasu wuce sai gobe kuma idan Allah ya kaimu anty hafiza da yake kwana za suyi ita da farida tace"dama kwanciyar ku muka yi maman kausar wlh ,a'ah hafiza na bar yara su daya a gida daga su sai Abbansu wunin yau fa duka?"anty hafiza tace to don Allah ga laila(mai qunshin da ta dauko)ku sauke min ita a dorayi Suna kan gado duk su ukun sunyi shirin yin bacci hafiza ta zubawa ido dake qoqarin shafa addu'a tace wai yau wa kuka barwa mijin ne?samira fa bata dawo gidannan ba haka kuke masa?"cikikin son rufe sirrinta da son gyara rayuwar aurenta ba tare da taimakon kowa ba tace "girkin samira ne anty bana son neman rigima da tashin hankali me zani in masa tunda ba girkina bane?salin inje mu raba dai abun fada?"daga haka suka qyale zancan ⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜ Washegarin aka zo akawa salima jeranta da yake aikin maza ne nan da nan yayi sauri amma akwai wasu daga cikin yan uwanta mata da suka zo da su,girkinsu su fadila sukayi sosai suka zuzzuba a manyan warmers suka aikawa yan uwan salima da wani wasu kuma suka barshi nan cikin kitchen dinta saboda mutane yan uwa da maqota da keta zuwa Allah ya sanya alkhairi har a lokacin sashin samira na kuelle ne alamar bata dawo ba kenan hakan yasa kowa ya shigo gun fadila yake yowa idan suka tambayeta samira sai tace ta tafi gidan qunshi Ba qaramin kyau fadila ta zuba ba tamakar ita ce amaryar daga wayewar garin zuwa yanzu ta sanya kaya kusan kala takwas kenan har harabar gidan jama'ace don babu laifi yan taru duk da ba wanda suka gayyata 💔💔💔💔 Qarfe sha daya da rabi na rana aka daura auren Aliyyu salim maitama da salima tukur Abubakar,kasancewar gidansu salima na na unguwar dake daura da g.r.a ne yasa yanuwan fadila na jiki da suka halacci daurin auren suka dinga zuwa ana gaisawa suna tafiya ciki kuwa harda abbanta da muhammad da ya ahmad taji dadin zuwan hakan kuma ya faranta mata ranta don tun da aka daura aurenta rabonta da taga abban nata kuma shima yaune zuwansa na farko gidan nata,ya mata nasiha sosai da ta qara mata nutsuwa ta kuma sata kuka ta sake tabbatar da cewa ba qaramin zumunci bane tsakanin abban nata da uncle abba mahaifin aliyyu tabbas babu abinda zata wa abban ta aduniyar nan fiye da ta jure zaman aure da aliyyu,anan suka bar mata muhammad zuwa yamma abban zai turo a daukeshi Qarfe sha biyu da rabi ta sake wanka ta sanya wani Swiss lace pink ne mai dan turuwa kadan sai kore aka masa da ratsin silver din zare sai manyan dutsina masu walqiya sarqarta abun hannu da dankunne mayafi da takalmi duk silver ne dinkin riga da skert aka mata skert din eight pieces ya bude daga qasa sosai ,yayi matuqar karbarta ya haska chaculet din fatarta gashinta mai tsawo da santsi da baqi ya sha parking da pink and green din ribbom sai ya kwanta a bayanta sai sheqi yake tayi daurinta das wanda ya ta qasansa gashin nata ya fito,ta dauki turare tana fesawa taji ana kiranta maqotanta sun shigo kuma wasu na nemanta a harabar gidan saurin da take yasa ta manta bata dauki mayafi ba,suka gaisa da baqin tasa aka kawo.musu abinci sannan ta qarasa harabar gidan, nasiru ne da wasu mutane suke neman gun jibge abincin da ake ta shigowa da su,ta nuna musu store dinsu dake harabar gidan ta farko kusa da parking space Tana shirin shigewa ciki motocin suka soma danno kai suna parking daya bayan daya,bata fuskanci su waye a ciki ba sai da suka cika harabar gun dukkaninsu cikin fararen kaya suke,Aliyyu ta hango a tsakiyarsu fuskarsa nata fitar da wani annuri cikin wata rantsatstsaiyar shadda babbar riga da yar ciki sai wando zata iua cewa bata taba ganinsa da irin wanna shigar ba ya qara wani kyau da kwarjini sosai ta shagala da kallonsa har suka hada ido Haushi ne da takaici suka cika shi ganin yadda tayi kwalliya kuma ta fito har kusa da get a haka na tare da tayi lullubi ba,yayi mata kallon nan nasa data tsana wanda ya saba yi mata hakan yasa ta tuna a uadda ta fito fa tayi saurin shigewa cikin jama'a ta bacewa ganinsa Tana zaune cikin baqinta sumayya ta shigo tace anty kije inji yaya sai taji maganar banbarakwai gabanta kuma ya fadi tace yana ina?yana cikin garden,dakinta ta shiga ta sake fesa turare sannan ta lulluba mayafinta,tunda ta nufo lambun zuciyarta ke dukan uku uku a haka har ta cimmasa,yana tsaye ya goya hannunsa a baya ya juyawa qofar shigowar baya,batasan yadda akayi ya gane ta shigo ba don gurin gaba daya grass carfet ne bare tace yaji takun tafiyarta ne sai ji tayi yayi gayaran murya gayaran muryan sai ya zamo kamar ya mata luguden guduma a qirjinta🔨,me ya fito dake harabar gida babu lullubi?shiru tayi muryarta na dan rawa tace ka.....kay......kayi haquri"ya dan dauke wuta na dan lokaci kana ya juyo da azama kar mai shirin waftar wani abu,hakan ya sa tayi tsammanin duka zai kawo mata tayi baya da sauri cikin tsautsayi ta taka wani dutse sai kuwa ta tadeta tayi baya luuu zuciyarta na bugawa da sauri don ta gama saddaqarwa sai ya sha qasa,sai kuma ta jita jikin mutum aliyu ne ya sa singalalin hannunsa ya tallafeta ta bude idonta data lumshe tana jiran ta jita ta sha qasa sai ga idonta cikin nasa,ya tsuke mata fuska 😠kana yace meye haka tashi" tayi azamar zare jikintata tana cewa kayi haquri,sai ya harde hannunsa aqirji ganin yadda duk tabi ta duburburce yabi gashinta wanda ya bi wuyanta ya dawo kafadar ta ta dama da kallo lace din ya zauanar mata caras cas yabi lafiyayyar fatarta chaculet,ya dan dauke kansa yabi gefansa da kallo yana jan tsaki a fili 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 WA YASAN GOBE? ▶2⃣3⃣ Sai da ya gama shan qamshinsa sannan yace ina da baqi dame dame kuke da shi a kitchen?cikin dai rawar muryar tace akwai sinasir masa funkaso da miya fried rice sai white rice da miya,ya danyi shiru sanna yace cikin sweet a bamu sinasir da masa sai a hado da white rice tace to har ta juya yace hey! Tadan waigo idonta na kallon qasa yace idan min kawo kiyi knocking kawai ki barsu a bakin qofa ta gyada kai ta wuce Bayan isha'i gidan ua dade ba mowa sai anty hafiza da farida suma suna gama kintsa mata ko ina suka turare shi sannan sukai haramar tafiya,godiya ta musu mai yawa su kuma suka cikata da nasiha ta rakosu tana bawa naty saqo don allah ki kawo min yan biyu tunda kika kaisu gida yaye anty minqi karbosu tace yayanku ma mita yake amma shekaran jiya munyi waya da mama sun kusa dawowa insha allah da haka suka rabu ta dawo ta koma bedroom dinta ta hada ruwan wanka wanda ya wadata da turarukan wanka,bayan ta fito ta shirya kanta ckin wani lafiyayyen material kalar qwanduwar qwai wanda aka masa ado da qyalli silver da ratsin fari kadan kadan ,shima yana daya daga ckikim dinkunan da aka kawo mata jiya riga ne da skert amma wadannan sun kamata sun muma fito da shep din ta sosai,tana gyara kayan kwalliyar dake kan madubin nata ne taji gudar yan kawo amarya jikinta ya saki ta zauna bisa dressing chair Tana kwance bisa kujerar qaramin falonta agogon bango ya kada qararrwar qarfe goma tayi ajiyar zuciya ta gayar kwanciyarta goma da ashirin da biyu qarar intercome ta tada ita daga bangaren aliyu ne hakan yasa ta fahimci hadasu yake sonyi kamar yadda al'ada ta tanadar gabanta ya tsanata faduwarsa💔,cikin nutsuwa ta sake feshe jikinta da turare turare ta lulluba mayafi a lallausan gashin kanta wanda bata daura dankwali ba Da sallama ta tura qofar falin nasasu biyun ne suka amsa amaryar na tsaye gaban fridge tana ciro ruwan roba da lemo yayin da gogan ke hakimce bisa kujera two sitter shigar jikinsa ta yanzu ta babbanta da ta dazu duk da dai babbar riga ce yanzu ma a jikinsa ta shadda milk colour ya ajiye babbar rigar a hannun kujerar da yake kai,salima ta dan zubawa fadila ido na yan sakanni sannan ta dauke kai ta dauki plate saman fridge din ta dora kayan fadila ta samu one sitter dake gefansu ta zauna ,saluma ta janyi centre table dan madaidaici gaban aliyun ta dora masata tsiyaya ya masa ta jiye ta koma kusa da shi kan kunerar da yake kai ta zauna,fadila ta saukar da idanunta qasa tana cewa cikin ranta "ni kadaice bani da irin wanna damar me yasa why Aliyu?,na kusa samota na kusa da qarfin zuciyata insha Allah" muryarsa ta jiyo yana fadin kefa mume jira ko?,shiru na yan mintina sanna ya qara cewa"yayi miki kyau" ya ajiye wayar ,saluma tace kawai ka qyale ta ni na gaji bacci nake so nayi,fadila ta dago kai suka hada ido sai kuma kowacce ta dan saki fuskarta fadila tace sannu amaryarmu"itama da dan murmushin a fuskarta tace sannu kuna lpy"a taqaice fadila ta amsa mata da" lau"ta dan saci kallonsa shi lemonsa ma yake kurba idonsa na kan qofa Banko qofar akayi aka shigo samirah ce sanye da baqar doguwar riga babu ko alamar hida bisa fuskarta sai dan kwalun atamfa da ta dauro a kanta wanda tayi masa daurin ture kaga tsiya,ta kama qugu tana cuno baki gaba tace da aliyu "gani" wani banzan kallo ya jefeta da shi sanna yace "ga gurin zama nan ko ina idan kuma bai miki ba.....ya nuna mata qofa da hannu👉�,sai da ta qarewa ko ina kallo sanna ta nufi kujerar da aliyun ke kai kusa dashi a daya side din ta dora qafa daya kan daya tana girgizata harara salima ta makawa samirah itama kuwa batayi jinkiri gun ramawa ba,taja tsaki sanna taci gaba da jijjiga qafarta,hara rarta aliyu yayi ya kalli qafar da take jijjigawa ta fuskanci abinda yame nufi kuma tasan ba magana zai.mata ba don haka ta sake zumbura bakinta sannan ta sauke qafar tata Godiya ya far yiwa Allah sanna ya dora dukkaninku a qarqashin iko na kume kuma tsarin Allah ne shi ya tsara hakan kamar yadda yame da ikon tsara rayuwar ko wane bawa nasa to ma gode masa akan duk yadda yayi da tawa rayuwar "daganan ya dora da yi musu gargadi da jan kunne sannan ya tunasar dasu tsarinsa na zama a bangarensa mai girki ta biyoshi"salima ta kanne masa ido tave" dear ani dama na nasan da wanna tsarin naka tuntuni saidai kawai ya zamto kamar tunasarwa a gareni"murmushin shima ya mayar mata yace "yes" Zuciya ta kawowa samirah iya wuya sai da ta tanka" a banza ai wai talaka ya girmi sarki dolen mutum yanzu shinr qarami ko yaqi ko ya so"cikin fusata salima tace "👉�ke nifa ba dake nake ba,ban gayyatar irinku a zancena don ni idan banda qaddara ba ma baki kai matsayin ma ki zama kishiya ta ba wlh don ko yar wanke wanken gidammu ta fiki kwarjini sai kuwa samira ta nuna ta da yatsa tace"👉�don kutumar uban mutum ya qara gaba mana don ni duwa wuce dole ne a zauna da ni zama daram wlh "sai suka so su kacame Cikin wata gigitacciyar tsawa aliyu ya dakatar da su sannan yace kowacce ta bace masa agun ba zasu haddasa masa ciwon kai ba haka kawai"salima ta miqe ta shige bedroom dinsa samira kuwa ta fice tana gungunin a qyaleta wlh taci uwar mata,ita kuwa fadila abun nasu tsorata ta yayi don bata taba ganin fadan kishiyoyi ba hasaluma ma ba'a taba yiwa umminta kishiya ba gidansu daga ita sai farida sai muhammad ko a tsakaninsu ba fada suke ba don haka tun ma kafin ya kammala bada umarni su fice din ita tuni ta riga su fita yana juya lamarina ranta Ransa abace ya shiga dakin duk yadda taso lallashinsa yayi banza da ita ta san halinsa tun ba yau ba kuma bata manta da shi din ba don haka da taga yayi banza da ita yana shirin shiga wankà sai ta qyaleshi sai da ya fito yana shirin kwanciya sanna ta langabe a jikinsa tana bashi haquri,ya dan kalleta ya basar sannan yace matuqar kika ce haka zaki dinga biye mata kunayi a cikin gidana to na rantse babu wadda zan saurarawa acikinku,idan banda raini ma a gabana? Ta sake marairaicewa tana cewa "Allah na lura ita wannan kanta na hayaqi ne da kamar dayar ce da babu ruwana da ita,su auremin mijin kuma suce bazanyi kishi ba" shi sai a lokacinne ma ya tuna da fadila baima san sanda ta fice a dakin ba donsanda yake musu jawabin ka ta na sunkuye ne sai ya tuna rana shigen irin wanna da ya hadasu ita da samirah ba wanda ta kula a ranar ma ahi ko samiran harta wuce" ya kauda wannan yace mata" am telling uh indai kina son zama da ni cikin kwanciyar hankali" "baza'a qara ba dear" Ganin yadda yaqi sakin jiki da ita yasa ta dinga masa wasu abubuwa wanda suka sa ala dole ya ajjiye fushinsa abinka da dama wanda yake cikin wani hali nan ya bada kai bori ya hau aka tuno da tsohuwar zuma don salima dama idanunta a goge take ta wannnan bangaren to haka shima aliyyun yake dalilin da yasa saliman ma ta kasa auren kowa kenan tayita naci har sai data dawo masa Mrs muhammad 📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 WA YASAN GOBE?....... 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 Written by safiyya Abdullahi musa huguma 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 ▶2⃣4⃣ Cikin kwanakin amarci kawai ake ta ballewa a gidan ,salima wayayyar gaske ce ko da wani lokaci tana manne da A.s maitama samira kuwa ta kasa tsaida hankalinta gu guda,yiwa salima itada da aliyyu labe kuwa ya zamo.mata kamar ibada mintina kadan sai ka hangota tana ta safa da marwa tsakanin sashenta da na Aliyu,fadila baiwar Allah lissafinta yafi ga kwanakin da zata soma shiga office da kuma ranar da zata zamo itace ranar girki a gareta Kwana uku kenan da tarewar salima fadila ta soma zuwa aikinta ya kama ranar laraba,shiga tayi ta hausawa atamfa ce dinkin riga da zani wadatattu yayin da tayi lullubi har kanta cikin yalwataccen mayafi komai nata cikin kamala yake da nutsuwa haka nan halittarta take kamar wata babbar mace duk da shekarun nata qana na ne,ta bude sabuwar motarta fara qal wadda bata taba shigarta ba saiyau,ta zauna a sit din zaman driver ta kunnata ta wana ta sosai sanna ta sauke hannunta daga kan key din ta hada tafukanta ta soma addu'a🙏🏻,sai da ta gama tana shirin tasar motar ta tuna da hand bag dinta data manto kan gadon ta da sauri ta bude motar ta koma ciki A hanyar dawowa ne sukayi kacibus da shi kasancewar ta gefansa ne zata wuce din sai tayi tsammanim bai ganta ba don haka ta dauke kanta cikin sauri ta wuce don ta kusa makara ta ajjiye jakar a asit din baya tasa hannu zata kunna motar taji an janye hannun gami da zare key din ta daga kai tq bishi da kallo bai ko kalleta ba ya zagayo sit din mai zaman banza dake kusa da ita ya zauna sosai sannan ya maida qofar ya rufe,ta dan sunkui da kanta😔 ya dan kalleta sannan ya basar don ya lura kamar al'adarta ce hakan,ya tabe baki cikin muryar nan tasa ta isassun maza mai cike da izza ya soma ce mata"ko banza a qarqashin mulki da ikona kike saboda haka u must obeying my statute and order if kina son aikinki,ya dan qara tsuke fuska 😠duk da yawancin lokuta haka fuskar take ya dage kafadunsa sannan yace" I don't know why aka wani tsiri yin aikin bayan ban gaza komai a gidana ba...... Ya dan sha qamshi sannan ya dora firstly ya zama dole kanki shiga ta kamala idan kin tashi fita,sannan ban lamunce da yawace yawace abu na gaba kada ki kuskura na ganki da number din wani qato a waya ko receiving calls ba and d last one kuma mafi girma wanda zai iya causing loosing din aikinki mu'amala da maza,kada ki dauki damar da na baki na fita aiki lasisi ne da na baki da zaki dinga ganin kina da right na yin duk abunda kika ga dama,take note👉,yana qoqarin ficewa tace insha Allahu zan kiyaye"duk da ranta a abace yake da irun dokokim da yake kafa mata da ita a karan kanta ai tasan ya kamata,baice komai ba ya cilla mata key din yaja qofar ya fice ya tafi abunsa,ta miqa hannunta ta rufo qofar sannan tabi bayansa da kallo yanayin yadda yake taku kamar zabar masa inda zai taka ake,ranta babu dadi ta ja motar ta fice a gidan ,yanayin motar yana da dadin tuqi hakan ya taimaka mata wajan dawo mata da walwalarta,a hankali temper dinta take sauka sai ta dora da fadin la'ilaha illa anta subhanaka inni kuntu minazzalim cikim zuciyarta,da haka har ta qarasa gidan radiyon freedom don can ta tafi sha'awa amma duk da haka akwai wasu privet ayyuka da zata dinga yi da express radio din Yanayin yadda ta samu karbuwa ya sake sa mata interest akan aikin sosai,su biyu ne kawai a office din ita da wata fauziyya kusan za tayi sa'a da fadilan amma ita nada yarinya daya iman,fauziyya shekararta uku da soma aiki da tashar,sosai fadila taji dadin samun fauziyya da tayi wayayya mai faran faran da son jama'a duk da ita miskila ce,wunin ranar tayi shine tare da managing director da wasu ma'aikatan tana arranging din ayyukanta ciki harda tsara sabin shirin da suka qirqiro wanda za'a fara gabatar da shi a asabuwar shekara wanda itace mai gabatar da shirin da taimakon fauziyya ta sake fuskantar yadda abubuwa suke duk da dama tasan da wasu lokacin attachment dinta Kwana biyu tayi tana tsara komai ta mai da kanta busy sosai ta hana kanta sukuni hakan yasa bata da wani lokaci na tunani ,da ta koma gida tayi wanka tayi sallah sai ta samarwa kanta abunci simple ta ci sai kwanciya idan da wuri ta dawo kuma takan yi tilawar alqur'ani tunda dama ta jima da kammala haddarsa tun lokacin da tayi candy,idan ta gama taga tana da wani lokcin sai ta dauki wani aiki da zai taimaketa a office ta yi ko tayi amfani da laptop dinta tayi research na wasu abubuwan masu muhimmanci,a rana ta uku ne da taga komai ya kammala ta nemi hutu na kwana biyu ba wani matsala suka bata tunda dama bata soma gabatar da ayyukan ba cikin shirye shirye dai take,tayi hakanne don a lissafinta ya bata yau itace zata karbi girki ,kuma dama tuni ta shiryawa zuwan ranar Da wuri ta koma gida ruwa kawai ta watsa ta zura doguwar riga har qasa mai hannun shimi ruwan hoda ta saka,ta taje dogon gashinta ta daureshi da ribbom shima ruwan hodar ne,farin hijabi ta saka wanda iyakacin qirjinta kawai ya rufe,ta wuce locker dinta ta lalubi inda ta adana muqullan da bata amfani da su ta debesu gaba daya ta zira farin silifas na fata ta fito,a falonta ta soma tsayawa ta bude fridge ta dauki lemon chi exotic nectar na pineapple da yayi sanyi sosai ta sha ta maida sauran ta rufe sashen nata, TO FADILA SAI INA?🤔 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 ▶2⃣5⃣ Kai tsaye sashen Aliyyu ta nufa gabanta na dan faduwa kadan kadan har ta isa qofan,addu'a fal bakinta ta ke sanya muqullan daya bayan daya take gwadasu har ta dace da na qofar,ta tura babbar qofar ta shiga sanyin a.c ne da daddadan turaren aliyyu ne yayi mata maraba,ta dan lumshe ido kadan sannan ta waresu sosai kamar mai neman wani abu,a hankali take bin kowane sashi na falon da kallo tabbas yana buqatar gyara,bata shakka cewa har bedroom dinsa ma na buqatar a kintsashi,ba tare da tsayawa wani dogon nazari ba ta dauko dust bin dake falon ta ajjiye a tsakiyar falon ta zare dan hijabin nata ta jefashi kan kujera ta fara tattare ta fara tattare leda takarda gwangwani da duk wani abu da ya zama datti ne tana jefashi cikin kwandon sharan Tana tsaka da aikin ne taji ana taba qofar alamar an shigo a tsorace ta dago tana tsammanin aliyu ne sai dai kuma maimakon haka sai taga ashe salima ce tayi tsaye a abayanta tana qare mata kallo ,fadila ta tsani yadda matar me mata naci nkallo haka,dama ita tun da can ta tsani mutum mai azabar kallo,to haka saluma ke mata a duk sanda hanya zata hada su ,abinda ita fadila bata sani ba shine kishine taf cike a zuciyar saliman don so tayi ta samesu gaba daya babu mamora kamar yadda taga samira bata da qira sam,saidai ance gwano baijin warin jikinsa ne ita dinma da tayi dogon nazari da tsinkaye da ta fahimci yadda tata qirar take irin matan nan ne masu azabar tsawo da sirantaka sai wani azababben fari da take da shi irin me gauu din nan to duk da babu laifi tafi samirah amma ko kusa bata kamo qafar fadila ba,tsawonta da azabar sirantaka su suka sata take a miqe kamar number 1 ba wani shape sai tsabar iyayi da yauqi Ta kau da kai.daga kallon fadilan ta tabe baki sannan tace"oh nayi tsammanin mai gidan ne ya dawo da naga gun a bude" a taqaice fadila ta amsa mata da"A'a" taci gaba da aikinta,sai kawai salima ta bude fridge ta dau maltina hadi da kunna t.v ta nemi gu ta hakimce,sarai ta gano ba abinda yasa saluma zama a gun banda bin qwaqawafin taga me take yi hakan yasa ta sa key ta bude bedroom dinsa ta shige tare da rufe qofar da muqullin ta ciki,salima tabi qofar da kallo cikin takaici don ba haka ta so ba,nan ta zauna tana ci gaba da shan maltinan tana dakon fitowar fadila wadda batasan ma tana jiran ba Ta qarewa shima bedroom din kallo sannan cikin nutsuwar nan tata ta fare tattare shi shima tana kintsa komai a muhallinsa tanayi tana mamakin kamar babu wasu mata dake kwana a dakin komai a yamutse?towel ne underwear ne comb ne mayuka ne turaruka ne kai tarkace dai wanda da alama a safiyar yau kafin ya fita yayi amfani da su warwatse bisa gadon bedsheet din kansa duk da babu datti amma ya yamutse,kowanne abau ta maidashi inda ya kamata cikin qanqanin lokaci dakin yayi fes komai ya dawo cikin hayyacinsa ta kunna kaskon turaren wuta electric ta zuba irin turaren wutan da take amfani da shi a bangarenta sanna ta wuce toilet Toilet ne qaton gaske wanda yakai girman ciki da falo na mata da yawa yana dauke da duk wani kayan amfanin toilet na zamani,cikin lokaci qanqani shima ya dau haske komai na cikin sa farine sai da ya dawo daidai tamkar ka zuba abinci a qasan ka ci,sai da komai ya mata yadda take so ya wadatu da sanyayyan qamshi sannan ta bude qofan ta koma falon don ta qarasa aikinsa Salima ta bar falon saidai ga gwangwani nan da tasha malt cups da qarin ledojin cake da na wasu tarkacen ciye ciyen nata watse a agun da ta tashin,baki ta tabe cikin ranta tana cewa"Allah ya sawwaqe an san yadda za'a bata amma ba'asan yadda za'a gyara ba sai kace ba mata ba,tana wanna zancan zucin tana kammale falin duk da girmansa kuwa,har kitchen bata barshi a baya ba sai da ta gyareshi ,"haba duk kyan abu ai yana buqatar gyara"inji fadila tana riqe da qugunta ta fada bayan ta gama aikin tana qarewa bangaren kallo yadda ya koma tamkar ba shi ba Aikin ya ja mata lokaci sosai kuma ya gajiyar da ita,tana kimawa bangarenta nan ma dai ba zama din kitchen ta shiga ta kama habarta🤔 cikin tunanin me zata girkawa aliyyu wanda zata iya kammalashi kafin kiran sallar magariba ganin gashi hudu tayi har da rabi,abu mafi muhammancin ma bata san choice din aliyyu ba ,sai ta yanke a ranta bari ta fara gwadashi da tuwo ta gani din ta fuskanci wasu mazan ba sonshi suke ba in yaso idan yayi masa shikenan an wuce gurin Tuwom shinkafa ta daura miyar danyar kubewa wadda ta dagargaza mata zallar tsokar kaza sanna ta sa tantaqwashi ya wadatu a ciki,misalin qarfe shida komai ya kammala ta soma mulmula tuwon da yayi fari sol cikim farar leda ya tuqu sosai ya hada jikinsa,sababbin warmers masu kyawun tsari ta dauko ta jerashi a ciki,ta gama ta gyara ko ina kamar bata yi aiki a kitchen din ba,ganin tana da ragowar lokaci yasata ta dora farfesun danyan kifi ragon ruwa maimakon zaman jiran dahuwarsa sai ta hada zobo wanda ta markada wadatacciyar abarba ta zuba a ciki ta hada da citta da kanunfari ta dafa,shima ta zubasu a mazubi ta wanke tukwananta,cikin azama ta shiga toilet ta silla wanka 😂😜 na gano su maman sa'ida fa na son jin qwaqwaf an baza👀👂🏻👄 anason aji ya aka kaya ko To🤔🤔🤔kada dai ku gaji ku biyo safiyya insha Allah don jin kanun labaran Mrs muhammad dinku ce 07066139278 📚📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻 [10/16, 12:38 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 WA YASAN GOBE? 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 Written by safiyya Abdullahi musa huguma 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 ▶2⃣6⃣ A bakin mudubi ta yada zango ta fara shafe loko da saqo na jikinta da turare dama ta saba da yin hakan kwalliya irin ta zamani mai tsari ta shiryawa fuska fuskarta bata cikata da jagwalgwalo ba ta taje gashinta mai tsaho da sulbi ta daureshi da ribbon ja swiss lace ta saka orange mai adon ja riga da skirt dinkin rafa wanda yayi masifar fito da sharp dinta,ta bata lokaci tana zana dauri a kanta ya zauna gwanin sha'awa fashion ta saka na dutse na sarqa da dan kunne sannan ta cika hannunta da awarwaro irin na india ja mai ashirin da hudu ya ahmad ne ya taho musu da tsarabarsa sati biyu da suka wuce,plate shoe ta saka orange and red ta sake feshe jikinta da turaruka sanna ta kalli kanta a mudubi,masha Allah ta fadi ba tare da tasan ta fadi ba sai murmushi ya subuce mata ita kanta yau ta sake gasgata kyawun da ake fadar tana da shi,kiran sallar magaribar da taji shi ya sata saurin fitowa ta shiga kitchen ta shirya kayan abincin ta kulle sashen nata ta fito tana tunanin qila ma aliyyu har ya dawo,ta cikin balcony din ta ta isa sashen ba alamun ya dawo don haka ta sa key dinta ta bude tana shirin shiga tajiyo alamun tsayuwa mota ta waiwaya sai taga samirah ce ke shirin fitowa daga motar tata wani irin kallo samiran ta watso mata wanda fadila ta gaza gane mai take nufi,dauke kanta tayi abinta ta shige don ba ita bace a gabanta tana mamakin masifaffen yawo irin na samira Cikin qwarewa ta shirya table din sannan ta sauko cikin falon ta kunna tafkekiyar t.v plasma din dake manne a bango cikin sa'a kuwa malaminta ne ke karatu a saudi qur'an ta dan qaro volume matsakaici ya game falon ta koma gefe ta tada sallarta cikin nutsuwa bayan ta idar ta koma ta zauna tana kallon yadda mahajjata ke dawafi Mintina biyar da zaman nata taji ana bude get jikinta ya bata Aliyyu ne jikin window taje ya dage labulen tana kallonsa har ya fito daga motar dukkan alamun dake nuna gajiya ga mutum sun bayyana a tare da shi,duk da ya gajin amma a nutsenshi yake kyawunsa na nan saidai fara'a da tasake yiwa fuskarsa qaura hirar da fadila keyi kenan ita da zuciyarta nasiru ne ya kulle motar bayan yafito sanna ya miqa masa kayayyakinsa da muqullan cikin rusunawa kamar ko yaushe aliyu ya karba yana cewa👉kada kowa ya jirani gobe ka sallamesu don bazan fito da wuri ba idan ka sallamesu sai kuci gaba da list din suna yan wadanda suka karbi kayan amma a cire sunan alhaji hamza wannan mun gama da shi✋🏻,nasiru yace ok insha Allahu ya juya yana shirin wucewa yace Allah ya tashe mu lafiya,ameen ya amsa masa Burinsa ya isa gida yayi wanka ya samu abinda zaici ko da tea ne donshi kam har yau cikin matan gidan babu wadda zai nuna👉�yace girkinta ya masa har gwara salima yakan qoqarta yaci indomie dinta don kore yunwa,yayi mamakin ganin qofar tasa a bude amma sai yayi zaton ko salima ce,ba wani dadi da yaji don ason ransa so yayi ya zauna shi daya ya samu hutu Saidai yana tura qofan wani daddadan qamshi ya daki hancinsa wanda ya tilasta shi lumshe ido kasancewarsa ma'abocin son qamshi sai ya shiga tunanin inda ya taba jin qamshin amma ya kasa cankowa idanunsa suka sauka a kanta bata anakara da ya shigo bane ko tsorone ya hanata motsi?ya dan tabe bakinsa 😠yana tunanin mai ya kwao ta kuma? Ya qarasa shiga falon yana sallama a nutse ta dago tana amsawa ya dan zubawa fuskarta ido zuciyarsa na son yaba wani abu amma ya rasa meye shi?ita kuwa gabanta ke faduwa cike da fargabar kada ya wulaqanta aniyarta yadda ya saba ganin yaddda ya hade rai kamar ya ga kashi,sai kuma taga ya dauke kansa ya nemi kujera can gefe ya watsar da kayan hannunsa sannan ya zauna har baisan sanda yace wash! ba ya sake lumshe ido yana ci gabada sheqar qamshin da ya ji yayi masa har cikin zuciyarsa ya rasa kuma ta Inda ya samu don dai shi har ya bar falon baiji qamshin ba sai yanzu da ya dawo 📚📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 ▶2⃣7⃣ Sannu da zuwa tace cikin cool voice dinta,ya bude idonsa tana durqushe gabansa riqe da cup da jug na glass baice komai ba yabi hannun nata da kallo dake riqe da cup din tana tsiyaya masa lemon zobon dake ta tsatstsafar sanyi da qamshin abarba ta janyo center ta dora a kai sanna ta balle murfin gorar ruwa na c'bon ta cika masa shima cup da shi ta ajjiye masa duk baice komai ba cikin dari darin kada ya gwasaleta ta miqe ta dauki briefcase dinsa safa takalmi key dinsa da duk ya wurgar din ta yi cikin daki da su Tana shiga tayi maza ta maida qofar ta jingina jikinta ta dafe qirjinta tanajin yadda yake bugawa da sauri da sauri idanunta a lumshe tana dan murmushi☺, cikin zuciyarta tana cewa wai Allah na! Sai da ta dan nutsu sannan ta ajjiye kayan a inda ta tsara musu kai tsaye ta wuce toilet ta kashe makunnin heater din don har jar danja ta kama alamar ruwan ya tafasa ta hada masa ruwan wankan a bathtub ta saisaita shi ya zamo mai dumi sosai yadda zaiyi saurin saukar da gajiya sannan ta zuba masa turarukan wanka a ciki A hankali yasa hannu ya dauki cup din zobon yana tunanin meye wannan? Ya kai bakinsa da niyyar dandanawa sai gashi ya shanye har da qari sai da yasha cup uku sannan ya saki ajiyar zuciya saboda yadda dadinsa da sanyinsa ya ratsa shi sai yaji kaso goma na gajiya da qishirwarsa har ma yunwar sun fara sakinsa ya samu relief har a qwaqwalwarsa ya jingina bayansa da makarin kujera Sai a yanzu ne ya lura da canjin da falon ya samu ko ina tsaf tsaf kamar yadda yake so,tunanin wa ye yayi aikin yake don shi kqm daga samira har salima yasan cewa matane masu azabar ganda da ko ruwan sha sai ya tambaya ake iya tashi a dauko masa,ga ruwan wanka can a toilet ko kana da buqatar yin wanka,ya dago da kansa tuni har tayi hanyar kitchen fadila tayi hakanne don gujewa baqar maganarsa ko da ziyi mata ta maqale a window din kitchen tana leqensa Sai da ya bata lokaci sosai har fadila tayi zaton bazaiyi wankan bane ta soma dana sanin shishshiginta sanna ta hangoshi yana kwance agogon hannunsa hadi da cire suit dinsa ya riqesu a hannu ya shige dakin tabi bayansa da kallo,ta janye idanunta hadi da lumshesu ta dafe goshinta da tafin hannunta tana cewa a can qasan maqoshinta"wo hoho Aliyyu badai miskilanciba?.... sai kuma ta sake sakin murmushi tana cewa"Allah ka mallakamin Aliyyu"tayi saurin dafe bakinta tama zare ido saboda ta fuskanci maganar zuci ce ta fito fili Sak yayi ya tsaya yana kallon dakin baccin nasa komai kamar yanzu aka jerashi ko tsinke babu a farin tiles din dake mamaye da dakin ya jinjina kai ya ajjiyr kayan hannunsa a gefan gado ya fara binciken inda ya ajjiye rigar wankansa sai ya bude wardrobe donnya dubata a ciki,canji idanunsa suka masa karo da shi,wardrobe ce ta jikin bango mai hangar komai ya canza bangaren shadda daban yadi daban suit dinsa haka kai hatta socks dinsa da handkerchief an masu nasu tsarin bai san sanda ya saki murmushi ba don tsarin ya burgeshi kasancewarsa dan gayu ya tabbatar babu tsarin rigar wankansa a gun don haka ya haqura ya wuce toilet cikin ransa yace wonderful cikin wani glass dake manne a kwanar bandaki ya hango rigunan a tsare jikin hanger bai bata lokaci ba ya shige cikin ruwan wankan duminsa da qamshinsa suka ratsashi sai yaji kamar kada ya fito,ya shafe kusan minti talatin sannan ya sabe jikinsa ya dauraye ya fito bisa gefan gadon ya zauna ya tsane jikinsa ya nemi farar jallabiya yasa don yafi son sata idan ya dawo daga aiki ya taje kansa ya feshe jikinsa da turare sanna ya bude jakar computer dinsa ya cirota yayi waje da niyuar shiga kitchen ya tafasa ko tea ne ya sha Ganin ya zauna yana aikinsa ya sanyata debo kayan ta shimfida babbar ledar cin abinci a gabansa baisan me takeyi ba sai da yaji qamshin abinci nata shiga hancinsa sanna ya dago kansa ya dubi gabansa ta jera tuwon a farin kyakkyawan plate miyar na wani dan kwano na tangaran shima fari ne tasha man shanu ta cika wani plate din da farfesun ragon ruwan ta zuba ruwa na sha da na wanke hannu ta tsiyaya masa lemo sanna ta janyo tissue box ta ajjiye masa tace bismillah ya kalleta 😠yace " ce miki akayi da yunwa na zo? Ko an baki labari ina buqatar abincinki kinga malama kwashe abincinki ki ban wuri, Ba qaramin sosa mata zuciya maganganun suka yi ba bata san sanda hawayen da take boyewa suka silalo mata ba😭karo na farko kenan tun sanda ya fara mata cin kashi,batayi qoqarin maidasu ba ta barsu suka ci gaba da zuba Cikin zuciyarsa addu'a yake allah yasa kada ta kwashe din don tunda yaji qamshin sha'awar cinsa ta kamashi ai kuwa aadu'arsa bata karbu ba don a zuciye ta soma maida abincin cikin warmers din  😜😜😜 Kuyi haquri da wanna yau bani da chargy wadatacce Mrs muhammad na muku fatan alkhairi👏🏻 📚📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻 [10/16, 12:39 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 WA YASAN GOBE? 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 Written by safiyya Abdullahi musa huguma 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 ▶2⃣8⃣ Sai da yaga da gaske take cikin daurarriyar fuska yace kinga malama zuba kada a qarani gaba ace bani da adalci tunda kin kawo kanki" ya fadi kamar wanda da gasken tilastashi akayin,kalmar tunda kun kawo kankin tayi matuqar bada gudun mawa wajan qona mata rai don haka hawayen da suke zuba suka qara gudu😭 Malmala daya ta saka masa da miya ta miqe wata zuciyar na zugata kiyi tafiyarki kawai wata kuma na lallashinta da hanata tafiya tana gaya mata saurin fushi ba nata bane yanzu da sauran lokaci dai,kujerar da ta tashi a kai can ta koma ta zauna tana qoqarin maida kukanta ta canza tasha zuwa mbc boollywood ta tarar suna film din kuch kuch hotahie tsohon film ne amma bata gajiya da kallonsa Ta kasa hankalinta kusan gida uku kason farko na kan aliyyu ne da taga ya ci gaba da danne dannensa a computer ya shanya abincin,na biyu na kan matan gidan da ta ga har yanzu ba wadda ta leqo da niyyar yi masa barka da dawowa ashe haka suke masa har ita din?,na uku kuma ta dorashi kacokam ne bisa t.v dake gabanta sai ka rantse da Allah ta bata hankalinta ne gaba daya Ta gefan ido taci gaba da satar kallo da nazarinsa sanda taga ya rufe computer din ya sauko qasa mamakinta zaman da taga yayi zamane irin wanda annabi yake yayin cin abincinsa mamakinta ya sake qaruwa ne sanda taga yayi bismillah ya sa hannunsa ba tare da ya nemi cokali ba A hankali taci gaba da bi biyarsa da idanunta,yanayin yadda yake cin abincin a nutse yq burgeta tana ankare da shi har sanda ya cinye ta biyu ya soma cin ta uku,ranta yayi mata dadi ganin yadda yake cin abincin bisa dukkan alamu yayi masa dadi Hankalinsu dukkansu ya kai bakin qofar jina naturo ta,saluma ce ta shigo da yalwar fara'a a fuskata amma sai taja tayi turus ganin fadila a falon,cikin iya tsabar duniyanci da iya waskewa ta gayyato fara'a fuskarta ta dubi sashen aliyyu tace" a'ah dear inacan ina zullumin yau ka jima baka dawo gida ba"ya miqamata hannu sanda ya sa lomar tuwo a abakinsa yana mata nuni alamar ta taho ,ta taho din kuwa ta zauna kusa da shi sai da ya hadiye sannan yace almost one hour da wani abun da dawowata na gajine shi yasa ba wanda na nema"da ido ta nuna masa fadila tana masa nuni da ita ya akai tasan da dawowarsa har ta rigata zuwa?,dauke kai yayi kamar bai fuskanci abinda take nufi ba don ba'a haka shi da shi,itama tasan hali don haka ta bar maganar Murya a anarke tace dear dama zancan ankon lubabatu ne qawata da nayi maka,kudin nakeso na karba don banason in zama a qarshe saboda baka fiya samun mai kyau ba"ya gyada mata kai yana ci gaba da cin abincinsa,ta tsare shi da ido ganin baice komai ba bayan gyada kan sai tace sake cewa naji kayi shiru baka"ya dago cikin qosawa yace ba munyi maganar ba tuntuni ba kuma ana amsa miki kuma yanzu baki ga abinci nake ci ba" tace cikin son wayancewa ok takai dubanta ga abincin gaban nasa sannan tace" dear yaushe ka fara cin tuwo?"kai tsaye yace "yau"cikin mamaki ta maimaita yau" ya gyada kai yace "yes"sai kuma tace ammafa nima abincin ya burgeni bari muga"ta tsoma hannu a plate din nasa,aliyu ya tsaida cin abincin ya bata fuska ya dago yana dubanta "repeatedly am telling you duk sanda kika soma cin abinci ba tare da kinyi bismillah ba kina cine tare da shaidan ko?" Ta dan dafe kai tace oh sorry na manta bismillah amma fa abincin nan dear yayi sosai a wane restaurant ka siyo" na gida ne ya bata amsa ya dan dubi sashen fadila wadda idan ka kalleta a zahiri zakayi tsammanin kallin film dinta takeyi haiqan sai dai duk tana jinsu tayi kunnan uwar shegu da su,salima ta fuskanci abinda yake nufi don haka ta tsuke bakinta😷tana da na sanin yabawar da tayi wa abincin din bata yi tsammanin fadilan ce tayi ba Salima na ta zubawa aliyyu surutu jefi jefi yakan tanka mata har suka kusan tashi da abincin gaba daya har farfesun kifin,suka gama aliyyu ya koma kan computer dinsa ya ci gaba da lissafe lissafensa na kayyayakin dake cikin store da wadanda za'a zuba sababbi da kuma wadanda ya saba rabawa yan kasuwan Har kusan tara na dare salima na zaune taqi tafiya,cikin haka saiga samira itama ta shigo yanayin samira ne yasa sauran kadan farida ta tuntsure da dariya duk da quncin da zuciyarta ke ciki,nikam safiyya kasa daurewa nayi sai da na dara😂😂 har sai da maman walid ta rufemin baki don kada su ganni Zanin shadda ne a jikinta rigar atamfa dankwalin material,har abada ba zaka ga kwalliyar samirah cikin gidanta ba idan har kana son ganin kece ado tofa saidai idan fita zatayi cikin qawaye takan ce kada a raina min wayo ina gidan nera dole na dinga keta shiga da kowacce mace zata kiyayi kanta tasan tana tare da matar Aliyyu salim maitama(kunji wata toshewar basira fa) 📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻 03:15 pm 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 WA YASAN GOBE? ▶2⃣9⃣ Salam! Samirah tace cikin daga murya tana tafiya tana wani budewa babu wanda ta kalla direct ta wuce gun maigidan hannunta dauke da zungureriyar farar takarda,ya dan bar abinda yake kana ya dubeta yana masawa,ta qaraso inda yake ta zauna hannun damansa yayin da salima ke hannun hagunsa takardar ta miqa masa ya amsa kafin ya duba yace" kada ki sake min irin wannan sallamar da kikamun yanzu don ba sallama bace take note,ok?"ta gyada kai tana buntsuro baki,ya bude takardar yana dubawa,ya qare dubawar sannan ya dago kai yana kallon fuskar samiran idanunsa da alamun neman qarin bayani,ta dan yatsine fuska sannan tace"eh abu uwan amfani ne da suka qare nake da buqatarsu" ya dan gayara zamansa ya jingina da makarin kujerar ya sanya idanunsa sosai cikin nata,sai ta kasa kallonsa ta dan soma rikicewa tana son janye idonta ta kasa tasan shi tamkar maye yake wajen naqaltar mutum tasan yanzun nan ba qaramin aikinsa bane ya harbo jirginta,da zarar aliyyu yayi ma irin wannan kallon yake gamawa da kai,sai da yayi shiru na muntina sannan yace"ina zaton yau ko sati biyu ba'ayi ba na karbi list na dukkan abunda baku da shi na kawo.....ya akqi naki ya riga na kowa qarewa bayan ko sati biyun ma ba'a cika ba?" Ganin tayi shiru ta kasa bashi amsa yasa ya maida kallinsa ga salima wadda tayi kasaqe tana sauraronsu zuciyarya cike da farinciki tana mai addu'ar Allah yasa a ci mata mutunci"nawa ne kudin naki ankon"tawani yi fari da ido sannan tace😊 atamfa dubu arba'in ne lace dubu sittin aai gudun mawar da zan bata dubu dari"(kunji tsabar rashin hankali irin na wasu matan mutumin da duk qarshen wata yake fita da su suyi siyayyarsu idan akwai abinda sai anshiga kasuwa ake samu zai sa su su rubuta ya bayar a akawo musu haka nan kayan abinci da na ciye ciye zaisa a sabunta miki koda basu qare ba kuwa ruwanki ne kisan yadda zakiyi da su shi dai duk qarshen wata zai miki haka,hakanan zai kawo kudi masu kauri ya baki bayan wanda kullum zai baki koda ba ranar girkinki bace )baiji komai ba kasancewarsa mai hannun kyauta ne koda ba ga iyalinsa ba,amma ya lura barnar ta soma yawa don haka ya sake waiwayawa ga samira yace"uhm....am waiting for d answer Ta yatsina fuska tace" kasan ni maca ce mai jama'a 'yar dangi kuma duka dangina anan garin suke ba baquwar haure ka auro ba wannan ya shiga ne wannan ya fita"salima tasan da ita take kasancewar iyayenta da danginta ba a garin suke ba a hannun qanwar mamanta take anan kanon amma ba yan garin bane,cikin hasala tace "da uban wa kike?"kamar dama jira samiran kuwa take tace da ubanki nake👉,kinji na kasa da ke ne bare ki dauka banza kawai😙 mtswee!"ai kuwa salima tayo kukan kura tayi kan samira da niyyar shaqota dama da qullin samiran a ranta Wata gigitacciyar tsawa ali ya daka musu wadda hatta fadila dake gefe sai da ta miqe tsaye saboda razana bare su salima da suka koma sukayi zamqn dirshan ba tare da sun shirya ba,ran 'yan maza ya baci fa zuciyarsa ta tabu take idanunsa suka kada Cikin tsananin bacin rai ya kallesu "wadanne irin mahaukata ne da baku da burin da ya wuce kuyi kokawa?"salima da ta shaqa da yawa ta nuna kanta👆🏼 tana cewa aliyyu nice mahaukaciya?" Ya dora da cewa "kun wuce hakanne?bai sauraresu ba ya murza yatsunsa suka ce das das das ya nuna su👉� sannan yace dis is d last worning kunyi na farko kuma kunyi na qarshe dambe a agabana.....☝🏼bazan dauka ba don ni ba shasha sha bane" salima da idonta ya ciko da qwalla😢 tace"amma fa kana gani fa tana shigowa ta hau habaici daga qarshe ta hau zagina.....samirah ta tari numfashinta da cewa"tambaya kimayi na baki amsa daidai da tambayarki" shut up!" Ya sake dakawa samira tsawa ya nuna mata qofa😡👉� sannan yace da ita get out of my room,jiki a salube ta juya zata fita ya ce hey🖐🏽ta juyo ya nuna mata paper dinta👉� take your rubbish neman tashin hankalinki ya siya miki ya bita da "stupid" wani takaici ya sake turnuqeta ai kuwa buguzum buguzum ta qarashe ficewa Ya dawo da idonsa kan salima yace"ni bani da kunne sanda tayi zagin ba zaki bari kiga hukuncin da zan dauka ba sai ke sarkin iya hukunci?,sai kuma alokacin ta soma shagwabe masa da sunan bashi haquri ya dakatar da ita ta hanyar daga mata hannu"🖐🏽dont disturb me please leave me alone"ta san bacin ran aliyu bashi da dadi do haka ta ja qafafunta ta fice cikin takaicin asarar da sira ta jawo mata na kudaden da take son karba a gunsa,yaja tsaki mai qarfi cikin ransa yace"silly girl" ya juya a hanzarce ya shige bedroom dinsa Ransa ya baci sosai mutum ne da baison hayaniya yanzu haka qirjinsa zafi yake haka yake ko hira yayi mai tsaqo yanzu kansa zai fara ciwo shi yasa ko musu bai iya ba,ba ruwanshi da shiga wata harqalla ko abokai bai fiya tarawa ba baifi ka qirge abokansa ba da hannu,to da shi da fadilan bansan wanda yafi wani ba🤔 Mrs muhammad dinku ce [10/16, 12:39 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *wa yasan gobe?* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 Writting by safiyya Abdullahi musa huguma 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 ▶3⃣0⃣ Kai tsaye bedroom dinsa ya nufa ya canza kayansa zuwa na barci farare ne sol masu taushi mutum ne shi ma'abocin son fararen kayan amfani ya fada bisa gadon yayi rigingine qafafunsa na qasan gadon ranshi a cunkushe yake Fadila da ke tsaye sai yanzu ta motsa ta saki ajiyar zuciya gami da fadin Allah ya kyauta ya iya mana abinda ba zamu iya da shi ba,ta isa inda suka baje kolin abincinsu suka ci suka tashi bar kwanukan ta tattare su ta gyara gun kamar ba'a yi hada hadar abinci ba agun Ta isa kitchen ta zubasu cikin sink ta kunna gas ta hada ruwan bununsa wanda ya wadatu da citta kanunfari da lemon grace ta saka lipton daya sannan ta rufe tukunyar,ta koma ta saki fanfo ta wanke duka kwanukan ta adanasu sannan ta juye mishi tea din cikin wani dan qaramin flask mai kyau ta dauki cups guda biyu na tangaran ta dora a saman plate ta hada masa da spoon,ta rufe qofan kitchen din ta doshi bedroom din nasa Ta tura qofar tana dar dar don tana tsoron kada ya maimaita mat abinda ya mata dazun,ya canza kwanciyar tasa zuwa barin hannun damansa yayin da ya juyawa qofar shigowa baya,qafarshi da yake dan kadawa kadan kadan shi yasa ta fahimci idanunsa biyu a hankali ta ajjiye tire din a asaman bedside sannan ta koma saman kujerar madubi ta zauna tana fuskantar bayan nasa,dakin ya yi tsit kamar ba wata halitta a dakin sai qarar agogon bango dake maqale a abangom dakin yana ta aikinsa,ita batace komai ba bareshi da tasan dama ba maganar zaiyi ba Zuwan can ta dan ja numfashi sannan ta tattaro dukka dauriyar da ta rage mata bayan ta gama wassafa da tsara maganar da zata fito a bakinsa,tayi yar gajeriyar gyaran murya a dan tsorace sanann tace" nazo ne baka haquri game da bata maka rai da mukayi dukkaninmu mu ukun,zan ari bakin yan uwana na ci musu albasa ince kayi haquri da mu baki daya,idan ban manta ba haka Abba ya gaya maka a ranar da mukaje masa _lamarin mata sai da haquri da kuma jajircewa halitta ce maau wuyar sha'ani amma idan kasa Allah a gaba sai komai ya zo maka da sauqi_"kayi haquri da mu Allah kuma ya huci zuciyarka😔,ga black tea nan ko kana da buqata sai da safe Ta miqe tana barin dakin ya dan waiwayo yana dan kallon ta har ta fice,yana cike ne da mamakinta dama tana da saurin sauka a fishi ne?,at least ya samu relief ainun daga damuwarsa,hakan ne ya bashi dama har ya jawo flask din ya murda murfinsa ya bude qamshinsa ya taso ya mamaye hancinsa ya dan lumshe idonsa take kwadayin tea din ya kama shi,yasa kofi ya tsiyaya ya sanya zumarshi ya kurba qamshin cittan da kanunfarin da lemin grace suka hadu a abakinsa suka masa dadi ⚜⚜⚜⚜⚜⚜⚜ Tana idar da sallar asuba bayan kammala al'adarta ta kullum wato azkar na sabahi wal masa wanda annabi ya koyar ta koma ta jingina da gefan gadonta idanunta a lumshe ta soma tilawa kamar yadda ta saba cikin sassanyar muryarta,sai da tai izifi biyar sannan tayi addua ta shafa,ta linke sallayarta sannan ta soma gayara bangaran nata duk da ba datti ko kadan sai 'yar qura da ba'a rasa ba wadda hadarin da ake tayi kwana biyu idan ya hado sai kuma ya zama iska mai sanyi wadda ke tashi hade da yar qura,tana kammalawa tayi wanka sannan ta shirya cikin doguwar rigar yan kanti mai roba roba red ce ta sauko mata har qasa ,daga gaban rigar wajen qirji an kamata an mata tattara yayin da ta bude sosai daga qasan aka jera wasu irin dutsuna manya guda uku masu garai garai da qyalli hannun vest ne da ita saboda haka ta sanya long sleeve shirt fara ,tayi rolling da farin mayafi wanda acucin da tayi da gashinta ta mai doughnut ya taimaka wajan qarawa rolling din nata kyau iya kafadunta mayafin ya tsaya,qananun fashion na barima farare ta saka sannan ta jawo takalminta slippers na fata shima fari ne,wayarta ta dauka ta kulle bangaran nata Yauma da keys dinta tayi amfani ta bude gurin,shiru yake ba motsin komai hakan yasa tayi tsammanin bacci yake,hakanne kuwa ta gani sanda ta leqa bedroom din nasa cikin sanda,yana kwance tsakiyar gadon duqunqune cikin farin lallausan bargo ,gefansa daga qasa dardumarsa ce qur'ani da kuma carbi 📿akai,yayi mata kyau sosai aliyyi gwanin kyau kome yakeyi kyansa fita yake,baccinsa yake verry calmness fuskarsa tayi fresh,sai ta lumshe ido tana tuna da yadda daren jiya tayi nata baccin cike da kewa da azaba,amma shi yanzu gashi yana nasa hankalinsa a kwance har da qarin wani na bayan sallar asuba kenan,ta dauko wayarta ta kashe plasher dinta tayi snapshot din fuskarsa,ai kuwa ta fito shar zara zaran gashin idanunsa sun kwanta luf,tayi kissing din hoton sannan ta juya ta yi kitchen *mrs muhammad ce* 📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *wa yasan gobe?* ▶3⃣1⃣ Chips ta soya hade da wainar qwai sannan ta dama masa kunun gyada da ya sha madara yayi fari qal sai zuba qamashi yake,sannan ta bare indomie ta yi masa awarar indomie,nan fa qamshin abincin ya karade gaba daya falon har cikin gidan to wani ma yayi rawa bare dan makadi,fadila gwanar girki ce mayyar kitchen ce tun tana gida ma,tana saitin window inda kan famfo yake tana wanke kayan da ta bata ta ke jiyo motsi kadan kadan,windon na cikin lambun bangarenshi da ke bayan part din kowa,tana daga kai ta hangoshi qarfe yake dagawa🏋🏼ya hada gumi sosai,armless riga ce a jikinsa da shortnekeer damtsensa cike da qwanji a murde,ya ajjiye qarfen ya dau dan farin towel dake gefansa yana sharce gumin kana ya dauki bottle na ruwa ya daddaka ya rufe ya koma kan keken training kuma🚵🏻 Ta saki murmushi ta kada kai,da azama ta hada komai ta koma bedroom ta gyara masa ta wanke toilet ta hada masa ruwan wanka,ta budade ko ina da qamshin nan nata sannan ta dawo parlour ta zare rolling din kanta ta fara gyare falon shima ,yana daga can yake jiyo qamshi kala kala na shiga hancinsa da fari qamshin girki ya fara jiyowa ya bude dogon hancinsa yana shaqar sa saboda ya masa dadi daga bisanai kuma ya jiyo wani qamshin qamshin da ya kwana jiya yana sheqa,ya sauka daga kan keken shima ya dauki wayarsa da towel dinsa ya bude qofar bayan ya shigo ta cikin kitchen wanda yasa sauran kadan suyi karo,ta ja baya da sauri tana gaidashi kanta na duqe a qasa kamar kullum bai amsa mata ba dama ta zaci hakan ya dai daga mata hannu🖐🏽ya wuce A bandaki ya tarar da ruwan wankan nasa,ya dan yi dam domin bai saba ganin hakan ba a tarihin rayuwar aurensa ba ganin tunanin zai bata masa lokaci yasa kai tsaye ya shige cikin ruwan🛀🏼yana sheqar qamshin da yake Cikim suit ya fito baqaqe masu sheqi sunyi masifar fito da ainihin kyawunsa,takalmi ne half cover dan hasken marun kamar yadda tie dinsa yake marun da jakarsa a hannu fuskarsa saye da fari qal din medicated glass dinsa wanda bai hanawa mutum ganin kyakkyawan qwayar idanunsa,sumarsa a kwance luf baqa sidik sai sheqi take ita ba mai yawa ba kuma ba a aske ba qamshin nan nasa na musamman ke fita a jikinsa,ya dan zauna a hannun kujera yana qarasa taje sumarsa da brush dake hannunsa 👏🏻👏🏻👏🏻👏🏻👏🏻 Afuwa afuwa  Nayi rubutu mai yawa zan turo muku na ajjiye wayar ina dan wani uziri kafin na dawo ya goge,chargy kuma ya riga yayi halinsa,kuyi haquri da wannan ku bini bashi da yardar Allah Na gode Mrs muhammad ce 📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻 [10/16, 12:40 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *wa yasan gobe?.....* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *written by safiyya Abdullahi musa huguma* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 ▶3⃣2⃣ Ganin wannan dama ya sanya fadila tayi saurin sauko da kayan breakfast din gabansa duk da cike take da fargabar kada ya gwasaleta,tayi saurin hada masa tea☕ ta daidaita masa zafinsa ta ajjiye masa sannan ta sa masa wainar qwai🍪 da farfesun kayan ciki🍲,taji dadi da baice komai ba ya sauko ya karya,bayan ya kammala ya dauki jakar laptop dinsa💼 ya ciro yan dubu dubu guda uku ya ajjiye mata kamar yadda yake ajjiye wa sauran matan ranar nasu girkin duk da kuwa babu abinda zasu siya komai diba za suyi yana ajjiye,ya yi gaba ta biyoshi a abaya gabanta na dukan uku uku bangaren samira ta ga ya shiga don haka ta ja tunga ta tsaya baifi mintina biyar ba ya fito ya shiga gun salima mintina takwas sai gasu sun fito yana gaba tana biye da shi ganin fadila na tsaye da alamum jiran fitowarsa take sai yanayin fuskarta ya sauya😠 take ta juya ta koma ciki Har sai da ya shiga mota ya zauna sannan tace a dawo lafiya tayi saurin juyawa ba tare da ta jira cewarsa ba don tasan bazai ce din ba ma idan ma ua fadan to ba mai dadi zata ji ba,tana hango salima da ta yaye labulen falonta tana kallonsu don haka sai fadila ta qorqiro murmushi ta dora bisa fuskarta Ta rasa hali irin na salimar mutum ce mai tsananin qyashi da hassada ga azabar sa 'ido komai idanunta na kai kamar wadda aka bata aikin yin hakan ita dai samira barta da kishi masifa da tsokalar rigima kuma kana tabata za kuyi uwar watsi agun shikenan duk da haka kishin salima har yafi na samira ita kawai tanada duniyanci da yasa take iya boyeshi ba kamar samira da ba ruwanta ko a gaban uwar waye ayita ta watse ba munafunta ⚜⚜⚜⚜ Haka fadila taci gaba da tsara rayuwarta duk ranar da take da girki zata shiga bangaren ta gyara ko ina da ina,tana kuwa fama da aikin domin tsakanin samira ko salima babu mai iya yin cangal kowacce haka take fita daga girkin ta tabar sashen a ahautsine Tsakaninta da aliyyu sai girki ta shirya masa daddadan abinci ta zuba masa ya ci idan ya kammala ta kwashe ta wanke kana ta ja qafarta ta bar sashen sai kuma washegari idan ta shigo hada masa breakfast,da zarar kuwa kwanakinta ya qare bata bi ta kan kowa da zarar ta taso a aiki ta shiga sashenta ta qulle qofa tofa sai washegari zata sake fitowa Wai inji hausawa sunce jiki da jini kuma mutum da zuciya cikin lokacin sai sai qyamar girkin su samira ya fara kama aliyyun ransa ya soma sosuwa da ganin sam gyara bai damesu ba,har gwara ma.salima tunda at least akwaita da son ado da kwalliya zata yi wankanta tayi kwalliyarta hakanan zata qoqarta ta dafa masa koda jallop ce albarkacin masifar son sa da take duk da bata taba girki a gidansu ,amma samira kuwa babu daya qanwar biyu daga ciki Cikin harshensa da zuciyarsa yana jin dadin girkinta sosai dandanon da bai taba jinsa ba gun kowa ba baya ga mominsa,miskilanci irin nasa yasa ko a fuska bata taba ganin alamun haka ba,takan tattare masa socks singlet handkerchief three quarters da duk inner wears dinsa harda jallabiyoyinsa da yake sawa ta wanke su tas ta goge su sannan ta feshe su ta turare ta jera masa su to ammafa insha Allahu bayan kwana hudu ta karbi girki zata zo ta tarar da su kamar kamar ba su ba komai an hargitsa shi sai ta soma fuskantar wani abu akwai gayya a ciki ta kuma san bazai wuce su salima ba don adawarsu gane da aikin nata a fili yake qara ra wani lokacin takan jiyosu suna yan qana nan maganganu takan sharesu taqi tankawa don basu tari gabanta sun gaya mata ba bare ta kula da shashancinsu Abu daya ke qona mata rai aishi aliyyun na gani suke batawar shin bazai tsawatar musu ba idan su basu da tunani? Ga misali a farkon fara aikin nata kafin su soma adawarsu takan tsince kayan aliyyu ne kawai a dakin a watse takan gyara ba tare da ta damu ba tunda tasan aikin ta ne dama,da tafiya ta soma nisa sai suka dinga barin brassiere panties sleeping dress underwear 👙👗musamman salima wadda kullum sai ta tsince nata tunda samira ke fara girki sai ita wanda a qa'ida fadila ce ya kamata ta zamo mai girki a farko amma suka maida ita ta qarshe ta qyalesu duka ta zuba musu ido ,tasan da gayya take zub da kayan,zuciyar fadil na matuqar baci da hakan,a duk lokacin da ta tsinci kayan takan bata lokaci mai yawa tana qissima dalilin barin kayan daga jikin mai su wanda hakan ke qara ta'azzara kishinta ga aliyyu Wani sabon rainin hankalin kuma sai ta fuskanci ya shigo ta soma gyaran sai ta shigo tace"☺sorry fa don Allah,jiya na mance kayana akan gado wallahi dear ne ya rudani daren jiya shi yasa da safe na manta da su ban dauka ba,kinsan shi akawai nacin abun,sai dai fa ba sauqi shima fa gwani ne😉"wannan ya bata ranta fiye da abinda tayi mata,har ta soma hasashem anya basu da masaniyar babu abinda ya taba gilmawa tsakaninsu? Akwai lokacin da ta zube har da magungunan mata maau dauke da hotunan banza,wannan fadila maganinta tayi ta dauko mata wasu wanda wata maqociyarsu a acan gida ta bata ita basonsu take bame ma zatayi da su tunda ta bata ta jawo locker ta watsasu sai yau ta tuna da su ta qara mata tace ga wasu sai ki qara naga naki basu kai wadanan tsada ba ni kinsan bana amfani da su halitta ta bata buqatarsu komai nawa yaji ba sai da kwaskwarima ba"jiki a salube ta karba duk da bata nuna mata hakan ba,ai kuwa da ta karanta kwalin sai taga tabbas sun fi nata kyau to tun daga ranar bata sake bari ba samira nata rashin mutuncin yafi ysakanin falo da kitchen parlour zuwa kitchen,zata dauko plates ne🍽 kofuna ne🍶 da su spoon tayi ta batawa wani abun plate din ma leda ce ta chewing gum ko biscuit zata dora akai kuma ta barshi a nan tunda ta sani cewa babu mai aikin gyara gun sai fadilan,duk da wannan neman masifa da suke ba wadda ta isheta kallo a cikinsu Su kansun so suke ta kulasun amma ta qi basu wannan dama Mrs muhammad 📚📚✍🏻✍🏻✍🏻 01:18 pm 05/11/1437 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *wa yasan gobe?* ▶3⃣3⃣ Lahadi daya daga cikin ranakun qarshen mako ne wanda yake zama ranar hutu ga ma'aikata to haka ne ya zama ga fadila hutun ya zame mata double babu zuwa office kuma bata da girki,la'asar sakaliya ta ranar ta shirya tsaf cikin doguwar riga shigar da tafi so kenan ta material ce ruwan qwaiduwar qwai dinkin rigar ya bude sosai dga qasa an mata dogon hannu tayi rolling dinta kamar yadda ta saba da jan mayafi,takddunta ta diba 📄📉📈 na aikin office da takeson dubawa zata yi wani aiki a kansu ta dauki yar madaidaiciyar dadduma da daya daga cikin matashin kujerarta ta zira takalminta ta firo harabar gidan,sai ta tarar da saluma da samira zaune kowacce a harabar sashenta bisa farar kujera plastic,novel a hannun salima📖 samira kuma na riqe da wayarta📱 tana tana ta faman danne danne,tun kafin fadila ta kai ga zama ta fuskanci zaman nasu ba na Allah da annabi bane don kuwa taba fitowa ta fara cin karo da baqaqen maganganun da auke jifan juna da shi a fakaice ba tare da kowa ya kalli dan uwansa ba kamar ta koma ciki sai kuma ta duba agogon wayarta📱taga biyar harda rabi da minti uku bata da wani lokaci na duba takadddun idan ba yanzu ba cikin gidan kuma zafi yayi yawa sanadiyyar hadarin da keta hadowa ana yin yayyafi dan kadan wanda ke qara tada zafin garin,ga injinsu yayi tsiya yaqi tashi tun wajen uku bakaniken ke kansa yana fama da shi kasancewar ba dan qarami bane yana daukar dukka freezers dinsu heater a.c da sauransu sun riga sun saba da wuta ko yaushe 24 hours,sai kuma ta ahimfida dardumarta cikin ranta tana fadin _ina ruwan biri da gada?_,tayi bismillah ta zauna ta soma aikinta,ashe duk suna ankare da ita,minti goma bai cika ba da zaman nata samira ta soma receiving call "shegiya kina duniya?......heeeee wlh gamu a cikinsa muna gogawa.......hahahahahaha aike kinsan fa hali tun ba yau ba"ta danyi shiru sanna ta sake kecewa da dariya kamar wani gardi tace"a haba haba ke sai kace ba nice samira ba?.....k kinsan saidai a gaji aqyale mana,kowacce qaramar shegiya sai ta kama gabanta da qafafunta🏃🏽 ,salima ta bude shafin gaba na littafin dake hannunta tamkar da gsken karatun take tace"qaramin dan iska ma yaci uwatar ai yasan kansa,samira ta sake kecewa da dariya "wlh har mai share share da goge goge ita wannan ai ba wahala zata bani ba.....yo hannatu yar anacen ma ba komai bace a guna wallahi duk hasashen da take na ita wata ce a gunsa Sarai fadila ta san da ita take amma sai taga ba mutuncinta bane tsayawa tana cece kuce da wadda batasan ciwo mutunci da kuma darajar kanta ba ,kan ta qare wannan tunani sai ji tayi tas! Da sauri ta dago idanunta don ganewa kanta wanda ka zubawa wannan lafiyayyen marin,aikin salima ne tana tsaye a gaban samiran bayan ta kwasheta da marin tana huci,tuni samira ta katse wayar hannunta na kan kumatunta ta miqe tsaye salima ta dora mata da bayani👉shiru shirun da kike ganin ina miki ba fa tsoronki nake ba ki bar ganin kina min kina samun nasara wallahi kin kaini bango nifa ba sa'ar yinki bace don uwarki"tasa yatsanta tan nuna qirjinta👆🏼 tana cewa"ni kika mara?"😁an marekin kadan ma kika gani wata rana zaki ga abinda yafi marin ma,kina tsammaninke kaďaice tantiriyar karuwa ko?💁🏽to 👆🏼nima karuwace nayi nayi kuma yaqon duniya fiye da naki ke da kika local ma 😳😳mamaki da tsoro suka kama fadiladama har akwai abun tutiya gun mace don tayi yawon karuwanci?wannan wane irin zama nine da Allah ya kwomù da har karuwanci ya zama abun ado?ita takaici ma sai ya sata ta maida kanta kanrubuce rubucenta📝taqi kola kowaccensu tana jinsu cacar baki mai zafi ta barke tsakaninsu tamkar zasu cinye junansu 🎭 Duf taji gun yayi shiru kamar an sanya musu kwado a baki🔐,ta dago da hazari don ganin mai ya sanya su yin shirun ba tare da kowa ya raba su ba?,aliyyu ne ashe ya ahigo kuma baau ankara da shigowar tasa ba sai da ssuka soma daga hannu da niyyar kaiwa juna duka👊🏻,kowaccensu tayi sak saluma ce ta fara cewa 😢wallahi tallahi ban kulata ba itace ta fara takalatakuma ka tambayi fadila"jin sun sanyo sunanta cikin sha'aninsu ya sanyata azamar taahi ta soma linke sallayarta,daidai lokacin da ya kai dubansa😒 gun da fadilan take da salimar ke nuna masa,ga mamakinsa tana gama ninke sallayar a nutse ta duqa ta mwaahe takardunta ta juya ta shige sashen nata ba tare da ta kalli ko da daya daga cikinsu ba cikinsu ba sai aliyyu ya bita da.kallo👀 karon farko wani abu daga garetà ya fara burgeshi nutsuwarta ,sai da ta shige ta kulle qofarta sannan ya dawo da idonsa kansu tuni samira har ta gudu🏃🏽ta rufe itama qocarta cike da fargaba da tsoron fushin Aliyyu😡 a akanta don ta tabbatar In dai ya bincika ya tarar bata da gaskiya to la shakka fa kashinta ya bushe,ta ruwan sanyi yake ma hukuncin da zaka raina kankà babu duka ba zàgi bà baqar magana,ya juyo ya dubi saluma da jikinta ke rawa sai kawai shima ya gewayeta ya shige nasa part din ⚜⚜⚜⚜⚜ Kwana uku tsakaniya kamaqarshen wata ne,kamar yadda ya zama al'adar gidan fita aiyàyya a iřin lokacin don sabunta abu uwan buqata na amfanin yau da kullum Yaune za auyi fitar farko tun bayan dawowar salima gidan gidan Fadila ta shiryq cikin shigarta ta bare bari tana nannade cikin lafayarta ,ta kammalà komai ta kira umminta don su gaisa,hira suke sosai ta jiýo tashin horn ta tabbatar aliyyu ne don bai son jira kuma baya jira saboda haka shima bai bari a jirashi tayi saurin maqale wayar a kafada tan ci gaba da hirarta da ummin tasa daya hannunta dauki jakarta🎒ta sa mèy ta kulle sashin,ta qarasa jikin motar tana sallama da ummin ta ciro wayar daga kafadarta tana kashewa sai ga salima da samira tamakar an jehosu kowacce na qoqarin bude gidan gana ta shige don badon fadila tayi azamar matsawa ba da daita zasu yi awon gaba,ta rufe bakinta da tafin hannunta🙊 dariya na shirin subuce mata😂,cikin zuciyarta tana cewa sunan wani film *qauyawa* Allah kayi mana magani wannan ai kishin jahiliyya ne 😂😂😂😂😂 Ku biyo *mrs muhammad* 📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻 [10/16, 12:41 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *wa yasan gobe?* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *written by safiyya Abdullahi musa huguma* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 ▶3⃣4⃣ Allah ya sawwaqe tace,ta bude gidan baya ta shiga tana kallon drama,aliyu ne ya juyo don ganin meke faruwa haka ake shirin cire masa hannun mota?cikin tsawa musu su matsa masa daga jikin mota,bai wata wata ba ya figi motarsa ya barsu a gun sake da baki😦,gudu yake zubawa abinsa bisa dukkan alamu ransa ya baci,duk sai fadila tayi tsuru-tsuru don da irin wannan gudu da yake zabgawa gwara ya sauketa salun alun , Qiiiii...taji ya taka burki,ya gangara gefan titi ya faka motar cikin shaqaqqiyar murya taji yace"fito ki dawo gaba don ni ba driver din gidanku bane😠"bata ce kanzil ba ta dawo gaban Yanayin zaman yayi wa fadila kusa sosai,mayen turarensa ya soma raba mata hankali,lissafinta ya soma qwacewa take kasala ta saukar mata,wani shauqin aliyyun ya mamayeta duk da azahiri idan ka kalleta zaka yi tsammanin ko inuwar sa bata gabanta Sun isa shoprite inda suka saba siyayyar duk qarshen watan,ta san tsarinsa bai shiga yana tsayawa ne a waje yayi zamansa cikin mota,da sun gama siyayyar ayi masa total a turo masa list da amount,da yake yana harka da su akwai kamfaninsa dake india wanda akwai hurdar kasuwanci tsakaninsu,"u have twenty minutes idan kima gota haka so sai ki nemi motar mai da ke gida"ta jinjina masa kai duk da idan da sabo yaci ace ta saba don duk sanda ya kawosu mintina ashirin din yake basu basa kuwa darawar domin dukkaninsu sun san halinsa yana iya tafiyarshi A nutse ta shiga ta duba muhimman abubuwan da take buqata don tana lisaafin jibi ita zata karbi girki duk da ba wani tsiya bane a ciki banda tsabar bauta ta gyare gyare da dafa masa abinci wanda sau da yawa tare suke cinyewa da samira da salima ,sukan daidaici lokacin cin abincinsa ne su shigo da nufin sun zo taya shi hira sai kuma su taya shi lamushe abincin A gurguje ta kammala zabar duk abinda tasan bata da shi ba wani kaya ne mai yawa ba tunda bata iya gama amfani da siyayyar tsohon wata suke sake sabuwa saidai ma wani abun ta bada shi,sai ta soma dibarwa salima da samira abinda ta lura sunfi siya yawancin lokuta idan suka zo,Allah ya taimaketa minti goma sha takwas ta gama komai,ta riqe leda daya ragowar aka biyo ta da su  Tana fitowa suka yi kacibus da shi yana tsaye a hanyar wucewar tata,shi da wata matashiya ce wadda a qalla shekarunta ba zasu gaza ashirin da shida ba,abunda ya bata mamaki shine ganin hawaye bibbiyu bisa fuskarta😭,ta maida dubanta garesu a karo na biyu daidai lokacin da aliyyun ya nuna ta da yatsansa yana cewa "👉 this is d last warnings da zaki sake bina wani guri ki kama kanki tun kafin ya gudu ya barki and respect ur self" 😳Sai taga kawai ya sa hannu ya rungumota kafadarsa sassanyan qamshinsa ya buwayi hancinta suka bi ta gabanta suka wuce,cikin mamaki fadila ta waiwayo still tana tsaye tana binsu da kallo hawayen na bin fuskarta😭,ta sake fashewa da kuka a guje ta nufi motarta ta fada ciki🚗🏃🏽, Daf da zasu qarasa cikin motar wadda tuni an kammala zuba kayan taji ya tureta daga jikinsa ,ta tsaya a baya sai da ta bari yayi gaba sannan ta biyoshi,zaman kurame suka sakeyi cikin motar har suka isa gida Ta kammala shirin baccinta ya sanya night gown sannan ta dora dogon hijabinta mai hannu da ya sauka har saman qafafunta ta sanya sannan ta kwashi ledojin da ta yima su salima ta su siyayyar ta nufi sashensu,saidai ta tarar dukkaninsu basa nan don haka zuciyarta ta bata amsar ba zasu wuce sashen aliyu ba Can kuwa ta tarar da su kowacce ta debi fushinta akan ya wulaqantata ya tafi ya barta taje masa da shi ,basu san ya fisu fushin ba don haka ci kanki ba wadda ya gaya mawa a cikinsu ya watsar da su a falo ya shige dakin barcinsa ya shiga wanka,sun sani ba wadda tayi gigin binsa ciki tunda suka ga ya musu banza to da tashi da su nan suka jibge a parlour zaman jiran sa,har ya fito ba wadda ya kalla ya haye dining yana fama da girkin salima wanda,farar shi kafa ce tsura babu salad ko cabbage bare akai ga batun nama,cikin qufula ya kira sunan salima da suke zaune suna fama da 'yar harare harare,bisa kansa ta tsaya ita dole wadda akayiwa laifi ce tace gani😼,ya dora gwiwar hannunsa saman table din ya hade yatsunsa cikin juna ya dora habarsa a tsakiya sannan ya kalleta yace"😒 sau nawa nake gaya miki I don't like such cooking?,ko kayan cefanenki sun qare ne?ko sun qare ba zaki iya sanarmun ba kenan?,ta tabe baki ta kawar da kai tace "kayi haquri "ya danyi shiru ya dafe kansa kamar ba zaice komai ba,har ga Allah ba don yunwa ba baiga dalilin da zai sanya shi cin wannan abincin ba,ya shiga tuna irin dandano mai gansarwa da yake samu duk ranar girkinta,ya dago kai yace bude fridge dina ke debi cabbage da cucumber ki yankamin ki hada min da dafaffen qwai tunda yau ban isa naci nama ba"ba tare da ta amsa ba ta juya Mrs muhammad👑👑 📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻 5:44 pm 5/11/1437 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *wa yasan gobe?......* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 ▶3⃣5⃣ Da sallamarta ta shigo falon sam bata ma lura da shi ba bisa dining,ta dan dora murmushi bisa fuskarta🙂,salima ce ta masa sallamar itama ciki ciki kamar wadda aka cusawa tsumma a baki,ta qaraso gabansu ta direwa ko wacce ledarta🛍 a gabanta tana cewa"sannunku,ga siyayyarku nan Allah yasa na haso muku da abubuwan da kuke buqata " salima shiru tayi saboda tafasa da zuciyarta keyi,yayin da salima yar takife tace" waye ya saki sarauniyar masu shishshigi ,kina murna kina rawar kai an koro mu ke an tafi da ke,shine don digimi da neman gindin zama harda wani yi mana siyayyar kaya ko?to ahir dinki wlh ni ba'a shiga gonata don kiji na gaya miki,har wata fada ce dake a gunsa banda ta shara da zaki mana rawar kai?ko an gaya miki sonki yake?" "Hmmmm matar cushe kenan"cewar saluma da bata tofa ba sai yanzun,cikin wani irin mamaki da al'ajabi ta dago tana dubansu,meke faruwa?a ina suka san wannan ?haka aliyyu ya gaya musu cewar ba aonta yake ba?,wannan wane irin kwance zani a akasuwa ne?,wanne irin cin kashi ne haka yayi mata?"take idanunta suka sauya launi,wani irin fushi da bata tsammaci tana da shi ba ua sauko mata😡😣,kamar hadin baki suka miqe suna shirin barin dakim don dama haushin kaza ne huce kan dami,tunda sunsan ko giyar wake suka sha basu isa su juye haushinsu ba kan wanda ya musu laifin sai suka juyeshi kanta,suna shirin ficewa suka jiyoshi cikin lion voice dinsa yana kiransu "😠ku kwashe kayan nan daga gun nan ku bace min da gani"kunnen uwar ahegu sukayi niyyar yi a zafafe yace da su"👉�billahil azim duk wadda tabar ledarta a nan tamu ce ni da ita"tilas kowacce ta waiwayo ta dauki tata tabar sashen Cikin matsanancin bacin rai ta dago kantasai suka hada ido,wani baqinsa ta gani wanda bata taba ganin yayi makamancin haka a idanunta ba,kafin ya janye idanunsa ta fara janye nata tayi azamar juyawa ta bar sashen Kusan kwanan zaune tayi ,babu abinda ranta bai gaya mata ba,abunda take ta qoqari da fadi tashin bunneshi ashe ya dade da yin tsiro har yqyi yabanya?tabbasa aliyyu ya cutar da zuciyarta ya cutar da zuciya da ke cike da qauna gami da begensa cikin kowanne fitar numfashi na dan adam,tabbas a ayu badon mutum bai da ikon cire son wani daga zuciyarsa ba da itakam ta ciro har zuciyar ta wurgar ta huta ma gaba daya,ranar idanunta basu ga bacci ba sai tunani data takurawa.kanta da shi wanda ya haifar mata da da ciwon kai da zazzafan zazzabi,ba ita ta samu kanta ba sai washegari da la'asar bayan ta takurawa kanta ta cire damuwar ta ajjiyeta gefe ⚜⚜⚜⚜⚜ Cikin qyanqyami yake shiryawa,gaba daya dakin ya hargitse sun kuma barshi kamar yadfa suka saba,sai dan yakanji relief idan ya tuna zaije ya dawo ya tarar da komai ya zama neat,da hanzari ya kammala ya dauki jakarsa💼 ya fice ba tare da ya saurari breakfast da salima ta hada ba ruwan tea ne fari sol babu citta bare kanunfari sai soyayyen qwai wanda qarninsa ke hanashi hadiyarsa,shi kuma akwai qyanqyami yayin da su kuma basu maida tsafta 💄👠👒💅🏽da gyara wani abu mai muhimmanci ba Sanda ya dawo ya tarar da sashen nasa yadda ya barshi yayi matuqar mamakin hakan,don bai saba ganin haka ba,yasan ranakun girkinta zai tadda komai a kintse hakanan yaji ransa ya baci da ganin haka,ya zube anan saman kujera yana fitar da iska mai zafi daga bakinsa,ya dubi agogon hannunsa qarfe shida da arba'in har da hudu,mintina qalilan suka rage a shiga masallaci sallar magarib,a kasalance ya duqa yana zare sau cikin qafarsa👞hadi da sabule safar,wata bahaguwar yunwa ke rarakarsa,yinin yau gaba daya ba abinda yaci banda maltina mai sanyi da ruwa da yake ta dirka,saoda yana da yaqinin zuwa ya tadda abinci mai kayau🍛, Kai tsaye ya shige toilet ya dauro alwala ya dawo falon yana goge ruwan jikinsa da handkerchief,gidan🏛 tsit sai hasken fitilu da ya gauraya da duhu suhun magariba da ya soma kawo kai ,ya dan lumshe idanunsa kewar qanan yara na shigarsa👫,ya tabbata da yana da su da zai dinga jin koda hayaniyarsu ce da gilmawarsu ,ya riga ya saba da tsabar qwarewar.matan gidan wajen iya rashin kula da miji,ya katse tunaninsa sanda ya jiyo kiran salla a masallacin dake can farkon layinsu ya sanya silifas ya fice yana maìmaita abinda liman ke cewa kamar yadda annnabi ya horemu idan munji kiran salla A can ya zauna ya jira sallar isha'i sannan ya dawo gidan,still gidan dai na nan kamar yadda ya barshi kowa na kulle a sashensa,ya dauki wayarsa ya kira nasiru ya gaya masa inda zaije ya samo masa masa da miyar ganye,cikin lokaci kadan saiga nasirun ya dawo ya amsa ya koma ciki yayi wanka ya sauya kayan bacci,ya zuba masar ya ci sai da ya qoshi sannan ya jawo computer💻 dinsa ya soma shigar da lissafinsa na yau,hankalinsa ya kasu kashi biyu,ko alama zaman gun ya gundireshi sabo da tsaftar gun bata masa ba,shigowar saluma ce ta saka shi tsai da abinda yake ,ba laifi salima indai ta bangaren qalqale jiki ne salima ta iya wannnan kam,yanzun ma ashirye take cikin dinkin lace baqine mai adon ja,ya sauke biron dake hannunsa Mrs muhammad ce👑 📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻 [10/16, 12:42 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *wa yasan gobe?*....... 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *written by safiyya Abdullahi musa huguma* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 ▶3⃣6⃣ Ya sauke biron dake hannunsa🖍yana dan binta da kallo,tayi masa kyau sosai,fuskar sa ta dan sassauta daga dauretan da yayi ganin yadda take masa murmushi😃,gefansa ta zauna cikin salon kissa take cewa"barkanka da warhaka ranka ya dade"yadan janyota jikinsa yana cewa "barka kadai......sai yanzu aka ga damar zuwa yimin sannu da zuwan?"ta san tabe baki tace"girki na ne da zan taho daga dawowarka?" "Ko ba girkin ki bane ni ba mijinki bane?" "To ayi haquri ko" yace "ya wuce"ya maida kansa kan aikinsa tana tayashi da hira jifa jifa yana amsa mata Samira ce ta shigo wannan karan harda sallama,abun arziqin nata yau yana da yawa🤔 don ba'ayi wari da.wari ba riga da zani ta saka na atamfa,kanta tsaye ta zauna daf da shi tana mata sannu da zuwa ba tare da ta nuna ma ta san da zaman salima ba agun,ya dan saki fuska bayan ya ja yatsun hannunta da nashi zara zaran yatsun yace"bana amsawa tunda kema sai yanzu" "bana shishshigi ne sweet kuma bana son maiyi shi yasa"ya dade da haddace wannnan kalma daga bakin samiran,don haka ya mele baki gefe sannan yace"lallaikam,da kun bani babies ai da sai nace kusha zamanku ni kuma insha hira da yara na ko?" "Nikam ai na riga nabada tawa baby din"cewar salima"no she is belongs to momy,u already know...sabuwa nake so"cikin shagwaba ta dan bata rai sannan tace"haihuwa is not easy dear"samira sai ta tabe baki hadi da cewa"mukam ai ba yanzu ba,tunda sauran quruciyata🤔"aliyyu ya jawo ragowar takardunsa yaci gab da rubuce rubucensa ,kowacce yasan inda tasa gaba dama salima d tasu ai tun shekarun baya,shikam idan da abunda ya rage masa yanzu shine tara family babba Cikin kwanakin fadika ta watsar da duk wata harka data danganci aliyun ta koma rayuwarta irin ta da,idan gari ya waye tayi ayyukanta na gida ta fice office sai ta dawo tan dawowa ta shige to sai washegari idan ta gaji sai fa kira farida ummi ko anty hafiza su sha hirarsu,ko muhammad yazo mata su wuni tare abinsu Gaba dayan bangaren ya fita daga ran aliyyun saboda tsabar kacamewar da yayi,ko ina ba kyawun gani a hargitse,ranar da salima ta fita daga girki yaga tana shirin kulle sashen ta wuce nata sashen,cikin takaici ya kalleta ganin bata da niyyar kawar da ko cup din da ta hada masa tea bare akai ga batun gyara "jimana!" Yace da ita a zafafe ta dawo tace gani"bai ko kalleta ba ya daga intercom ya kira sashen samira ,sai da ta qara wasu mintina kana ta iso hakan ya sake hassala shi,ya dubesu cikin bacin rai yace "Anya kuwa ky mata ne cikakku?ba ko wani jinsin bane ku?"a mamakance suka dago suna kallonsa,"kamar ya?"inji samira,da hannunsa ya soma yi musu nuni da falon suna binsa su kuma da kallo,"ku duba....dubi......haka ya kamata ace ya kasance?haka sauran mata suke barin turakar mazajensu?....abun naku ba ya yi yawa na lira ba hankali a ciki,ba tsafta ba iya kula da miji?kuma ni kuna son kyautatawa daga gareni?....it cant abun yayi yawa na gaji da tolerating bad attitude dinku....👉as from today ya zama dole a kanku kowacce kafin ta bar nan ta tabbatar ta gyara duk inda ya kamata ba ruwana da qazantarku ruwanku ne ku gyara naku ko ku barshi haka is not my own business..... Ya suri briefcase dinsa ya fice,da kanshi yau zaiyi driving kasancewar nasiru baya nan ya tafi ganin gida ,ya juya kan motar ya danne horn yana jira a bude masa,ta kalli gilashin mudubin dake gefansa da niyyar gyara zamansa don ganin wanda kebin bayansa sai yaga wata motan na jira ya fita itama ta fita,ya duba sosai sai ya hangota zaune hannun ta saman sitiyarin fuskarta tayi fresh cikin safiyar,agogon dake daure a tsintsiyar hannunta take kallo da alama ta kusa maka rane don sai yatsina fuskarta take,material ne ajikintan yellow mai adon coffee,ba makeup ko kadan a fuskarta banda powder data shafawa soft chocolate skin dinta,sai lips balm data shafawa lips dinta sirara masu taushi,tayi lullubinta na mutunci har saman ka,ya dan tabe baki ya dauke kai itakam bata san ma yana yi ba,duk da ta ganshin Ayimin afuwa kasancewar yau ina da uziri irin wanda ke kama ko wanne irin dan adam na turo muku shi late kuma ba yawa amma zamu hadu insha Allah,ina godiya a gareku👏🏻👏🏻 Mrs muhammad ce 📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻 [10/16, 12:42 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *wa yasan gobe?......* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *written by safiyya Abdullahi musa huguma* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 3⃣7⃣~3⃣8⃣ Fisgar motar yayi ya ficee daga gidan sannu sannu take binsa a baya har suka bar cikin layin suka hau babban titi,yana hangota ta qarawa motar gudu tayi over taking nasa ta wuce shi ba tara da ta dubi koda sashen sa ba,ya daga idanunsa yabi motar da kallo yana dan gyada kai cike da mamaki da jin izza shi zata nuna wa iyawa da qwarewar sarrafa mota?,yaushe ma ta fara kama sitiyarin Wani girman kai ne ya kamashi,ya qarawa motar shi speed cike da qwarewa da gwaninta shima ya mata over taking,ta lura sarai da shi amma sai ka rantse da Allah batasan da wanzuwarsa akan titin ba,ta dan cije lebenta sannan ta dan daki saman sitiyarinta cikin zuciyarta tana dariyar mugunta,sai da ta barshi ya sakankance sosai ta take motar ta qara maya gudu sai ji yayi fit ta wuceshi ,cikin zafin nama da mazantaka ya qara wa tashi shima wutar don ya nuna mata bata isa ba saidai kafin ya qaraso har ta qaraso kwanar freedom ta sanya signal ta shige,ta morrow din gaba suka hada ido yana wucewa amma sai ya wuni mugun dauke kai kamar ma bata sanshi ba Ya girgiza kai ya miqe kasancewar b.u.k zai shiga hanyar ta rabu cikin zuciyarsa yana fadin"zan koya miki hankaline kin maida ni abokin wasanki kenan Qarfe biyu ya baro b.u.k din bayan ya kammala abinda ya kaishi,kai tsaye ya tashi motarsa ya bar makarantar,biyu da rabi ya iso freedom hakanan bai taba zuwanta ba koda hira suke son yi da shi yana basu appointment ne,ahankali ya gangara layin ya qaraso bakin gidan radio din ya yiwa mai tsaron bakin qofa horn ua taso don yaji me ke tafe da shi,da ganinsa ya fara fara'a cikin mutunci suka gaisa ba tare da jiran komai ba ya bude masa qofa yana jira ya shiga,da hannu aliyu yayi kiransa ya qaraso saitin window ya ranqwafo yana saurarensa,"wata sabuwar ma'aikaciyar ku nake nema ina fata bata fita ba"cikin tunani yake kalleshi,aliyu ya gyada masa kai da son tabbatar masa,sai kuma yadan saki murmushi yace "oh ko haj fadila?"aliyu ya gayada kai yace"yes itace"😃 tana nan ciki kuwa bata fita ba mutuniyar arziqi kuwa ranka ya dade.....ko kira maka ita za'ayi"aliyu ya dakatar da shi"✋🏻a'ah barshi zan dan jirata ba matsala"ya tada motar ya shiga security suka nuna masa gun parking"ya daidaita motar qasan bishiyun dake gun ya kasheta,ya miqar da sit din nasa ya kwantar da shi yadda zai masa dadin kwanciya,yayi sama gaba daya da glass din motar kasan cewarsu akwai (tinting)jikinsu,yasa hannu ya qaro qarfin a.c dake jikin motar ta gauraye masa ko ina ya kashe dukkanin wayoyinsa ya watsa su sit din gefansa,ya maida bayansa ya kwantar jikin kujerar yana fuskantar ginn gidan idanunsa akan reception,lokaci lokaci kuma yana bude mujalla yana dubawa Zaman minti ashirin yayi ya ganta ta fito gefanta wata yar matashiyar ce sabe da baby girl a kafadarta ,ita tayi hanyar waje ita kuma ta nufi inda tayi parking tasa maqullinta ta bude motar tashiga,ya miqe ya gyara zaman kujerarsa ya jawo belt ya daura,ya kunna motar ya biyo bayanta sanda take ficewa daga ginin gidan radiyon Ko kusa fadila bata lura da shi ba don bata kawowa ranta ba,cikin kwanciyar hankali take tuqinta,wani mahaukacin horn taji ana mata kafin ta ankara motar ta zo daf da ita tana shirin gogarta a gigice tayi gefe da motar tana ci gaba da kallon motar da ta kasa tantance waye a ciki?,kafin ta gama wannan tunanin har ya dawo daya side din data koma ya sake matsowa daf da ita yana shirin gogarta,sai ta tsorata 😳kasancewar titin da ta biyo ba mai yalwar jama'a bane bugu da qari kuma rana ce babu gilmawar mutane sosai a gun Cikin lokaci qanqani ya gama rudata gaba daya ta tsorata dama da hugunta ya dinga komawa,tuni lissafinta ya qwacr tama manta sitiyarin na hannunta ne,sai ta taji motar ta soma yawo da ita saman titi idanun aliyu na kan motar,ya zubawa motar ido ganin ta soma yawo bisa kwalta a hankali yana nazari,ya saki ajiuat zuciya sanda yaga ta daidaita ta daina tangal tangal din da takeyi,ya qaraso saitin window dinta sai ya sauke glass ta juyo idanunta cike da taf da tsoro suka hada idanu,ya dauke kansa ya qarawa motar speed yayi wucewarsa,wani abu ya daki zuciyarta sai ta kasa tuqin,ta sauka a hankali ta gangara gefan kwalta ta kashe motar ta jingina da makarin motar idanunta a runtse😣 zuciyarta na ci gaba da bugawa💓,sai hawaye ya biyo rufaffun idanunta ta saki kuka silently,sai da taji don kanta ta samu nutsuwa sannan ta kunna moyar taci gaba da tafiya slowly a gefan titi don gaskiya ya dauki haqqinta Tana isa parking space taga motar tayi tsammani ya shge cikin gidan saidai tana gama kulle motar ta ganshi tsaye jikin motar yana amsa waya,idanunsa suka shiga cikin nata wadanda suka dan kafa alamar tayi kuka takaici yasa ta sakar masa harara🙄 hadi da murguda masa baki😙ta shige jin alamun taku tayi ana bin bayanta,tana juyawa taga kuwa shi din ne,tasan mai yasa ya biyota cikin azama ta qarasa shigewa bangaren nata daidai lokacin da yakai hannunsa zai fincikota,tayi saurin sanya maqulli ta qulle qofar hadi da jingina a jiki,tana kallonsa ya juya ya koma" kawai"ta fada a hankali Zaune take tana kallon wani Indian film hum dil de chuke sanam tana ganin son maso wani tamkar nata da aliyu,ta bada hankalinta kacokam bisa t.v din sai tsintat qamshinsa tayi yana yawo bisa hancinta,ta dago da sauri yana tsaye bisa kanta hannunsa harde a qirjinsa shima idanunsa na kan t.v din sai a lokacin ta tuna da abinda ta masa dazu da hanzari ta miqe ta jawo hijabinta ta zira tana neman guduwa sai alokacin ya dawo da idonsa kanta fuskarsa a dinke tsaf,da baya da baya ta soma tafiya yana binta har ta dangane fa qofar bedroom dinta ta fafa ciki tana shirin danno qofar,yasa hannu ya kare ta,yaci gana da binta sai da ta dangane da sif dinta ,qwalla ta cika idanunta idonta tuni ya raina fata,girgiza kanta ta soma yi tana cewa cikin tawar murya"donA....Allahh kay......yi...yih.....haquri...."yasa yatsansa ya dalle mata baki,taji zafi sosai ta sanya hannunta ta dafe bakin🙊,ya zare mata ido sosai yace"wa kika harara? Ni sa'anki ne?kin raina ni ko?,still tafin hannunta na dafe da bakinta ta girgiza kai tuni hawaye ya balle mata😭,ya saka hannunsa ya kama gashinta💆🏼 da ta tufke cikin hijabin har sai da tace "wayyo Allah na!......,hadi da wani dan guntun hawaye da ya silmiyo mata,ya saketa yana sake matsota har tana jin hucin numfashinsa,ta runtse idonta gam tana jiran jin hukunci na gaba,ta yarda aliyyun mugu ne,tasan yau Allah ne kawai zai qwaceta Shirun da taji yayi yawa ya sata bude idonta,ba kowa a dakin hasalima an ja mata qofar dakin sai ita kadai dake tsaye jikinya na kakkarwa,ta sake sakin kukan ta kifa kan gadonta ⚜⚜⚜⚜⚜ Cikin kwanakin gaba daya ya gama tsanar bangaren nasa,bedroom sin da suke cikin corridor din wadanda bai amfani da su duk sai da ya budesu yayi amfani da su ,duk da alokacin su su samira suna ganin suna qure adaka gun gyaran amma shi sam bai masa ba,don ba wani qwarewa sukayi ba kamar na fadilan,yakan daure ne kawai ya nuna yabawarsa,ya tabbatar wa ransa nata yafi wannan kimtsuwa Kowanne dan adam wani lokacin kakan tsinci kanka cikin rashin jin dadin rai hakanan to haka yau aliyu ya tashi,alhamis ce wadda aka wuni garin lullube da hadari da iska mai cike da qamshin qasa,mutane da yawa yanayin yayi musu amma banda shi,biyar saura yama yi dawowarsa gida,yayi cilli da jakar tasa a falo,gidan dai na nan a yanayinsa na kullum wato shiru,toilet ya shiga ya watsa ruwa ya fitar jallabiya mai sulbi irin ta maza milk colour mai dogon hannu ya saka,ya feshe jikinsa da shamsul imarat ya hada da turaren chastity ya dawo parlour ya fitar da computer dinsa ta tafi da gidanka(laptop)ya jona mata chargy ya jawota har kan kujerar da zai zauna ya dora ta a saman kujerar,ya daddanata ya bude bayan komai ya gama daidaituwa ya soma aikin da ya dawo da shi Munti biyar goma sha biyar sai aikinbya soma gagararshi saboda yunwa,ya dafe kansa da hannu daya yasa dayan ya lallatsa comouter din ya kasheta,ya zubawa fridge dinsa ido yana nazarin me zaici a ciki?komai dai na nau'in ciye ciye akwai aciki🍏🍎🍐🍊🍋🍌🍉🍇🍓🍈🍒🍑🍍🍅🍆🌶🍠🍤🍟🍔🌭🍕🌮🌯🍕🍘🍦🍧🍨🍺🍷🍾 Saidai gaba daya sun gundireshi babu abinda yagi buqata sai abinci mai nauyi da gishiri,gaba daya taste din girkinsu salima bai gamsar da shi bare yasa su dafa masa wani abun,koda ranar gikinsu ne yana yin kawaici ne kawai yaci don kada suga rashin kyautawarsa A nutse ya isa gaban freezer din ya bude yana sake kallonta kamar baisan meye da meye a ciki ba,hannunsa yakai kan madarar fresh yo da tayi sanyi sosai tanata fidda tsatstsafar sanyi yasa daya hannun ya maida murfin freezer din ya rufe,ya maida kallonsa kan robà dake riqe a hannunsa yana jujjuyata tamkar mai karanta rubutun dake jikinta Ya saki tsaki hadi da cillar da robar kana yayi tattakì ya isa bakin window dinsa yajanye labulayen jiki gefe daya ya dora idonsa a harabar gidan,idanunsa suka sake kaiwa kan bangaren nata a karo na barkatai,tarwai yake da haske alamun tana nan,ji yayi yà gaji baAi iya jutewa ba sole ne yazo tayi masa aikin da tasabar masa idan yaci gaba da jurewar yana jin qila yunwa da tsantsami na iya illatashi,ya juya ya zira slipper dinsa ya fito.... Mrs muhammad ce👑 📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻 [10/16, 1:41 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *wa yasan gobe?.....* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *written by safiyya Abdullahi musa huguma* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 3⃣9⃣~4⃣0⃣ Ya juyabya zira slippers dinsa ya fito Gaba daya tana ma gida babu inda ta fita saboda ba ba abinda zatayi a gidan radiyon shi yasa bata shiga ba,zamanta tayi ta dinga bacci abunta sallar azahar kawai ta tashi tayi ta dan sha yoghurt ta koma baccinta Qarfe hudu da rabi ta farka tayi wanka,tq gabatar da sallar la'asar din da ake binta,riga da skert ta saka hade da mayafinsu sannan tayi kitchen da azama saboda wata hadaddiyar yunwa dake sakadarta A tsaitsaye ta hada jallop din taliya🍜 da tasha kifi ta watsa mata carrot piece da grean beans,da zaman jiran dahuwar abincin da zata yi sai taga gwara ta hada lemo,cikin lokaci kadan ta hada lemon kwakwa da yasha madara ta bude freezer din kitchen din ta sanya ta a ciki,bayan ta kammala ta juye a plate ta kalli plate din tana murmushi hadi ya tsina fuska don ita kanta tasan ba iya cinyeta zata yi ba ta mata yawa"let me try"ta fada tana gyada kai ta hado da lemonta dake cikin jug din ta taho dashi parlour ta zabi kujerar da zata zauna akai don haka ta jawo centre table ta dora su a samansa Ta juya ta koma daki don daukar wayarta ta tashi ne ta tarar da missed call din fauziyya colleague dinta ta barshi da niyyar idan ta gama abinda take ta kirata Ya kama handle din ya murda hadi da tura qofar ta bude ya shiga,qamshin freshner din parlour hadi da qamshin jallop din ya dunqule ya daki hancinsa wanda hakan ya sake haddasa masa yunqurowar wata matsananciyar yunwa,idanunsa suka kai kan plate din dake dauke da jallop din🍝😋dake ta tururi da qamshi, Fadila ta fito hannunta dauke da wayar tana duba missed calls din data tarar ciki harda na rumasa'u da farida,,sam bata lura da shi ba agun sai da yayi gyaran murya,adan furgice ta dago don bata zaceshi ba,a dinke fuskarsa take kamar kullum ya cillo mata muqullai suka sauka a kusa da qafafunta,yayi gefe da kansa sannan cike da ginshira yace"ki gyara min bangarena sannan ki sama min abinda zanci yanzun nan tunda sai an koya muku abinda ya dace" ya nemi kujera ya zauna hadi da jawo wani dan qaramin table din na glass ya miqe qafarsa akai A hankali ta sunkuya ta dauki muqullan,cikin zuciyarta tace"ka gama qunbiya qunbiyarka ka ma,mutum sai shegen jin kai ka fito kawai kace kazo neman taimako guna,ki banza dai ina da muhimmanci tunda.duk cikinsu babu mai iya maka haka sai ni duk da dan banzan jin kanka"ta shiga daki ta canza mayafin zuwa hijabi sannan tazo ta wuce shi yana zaune yadda ta barshi Kamar jira yake ta fita din ya jawo abincin gabansa,ya dauki cokali mai yatsu yana jujjuyata yana qare mata kallo,a zahiri shi taliya bata dameshi ba don haka ya ture plate din gefe sai kuma qamshin ya addabeshi don haka dole ya jawo yakai loma daya bakinsa🍜 Lumshe ido yayi dadin na zagaya kunnensa👂🏻,ya tabbatar wannan ne taste😋 din da yayi missing kwana da yawa kuma shi yake nema wasa wasa saiga gashi ya tashi da plate din gaba daya,ya shafa cikinsa take yaji yana buqatar qari bai qoshi ba, ya miqe ya nufi kitchen kasancewar tsarin ginin nasu daya ne shi yasa ya fahimci inda yake,ya daga tukunyar gaba daya ya juye ta ciki ya cinye ya dawo falon dauke da ruwan roba na faro a hannunsa ,sai yaji ya samu nutsuwa ba shakka yunwa bata da hankali inji dan almajiri Ya miqe a kan three sitter🛋saboda yanaji har cikin zuciyarsa yanayin qamshi da tsaftar falon sunyi.masa,idanunsa a lumshe yana tunane tunane har aka fara kiraye kirayen sallar magariba sannan ya miqe ya bar sashen,kafin ya qarasa nasa suka ci karo da samirah na shigowa da motarta,ya tsaya qam yana dakon qarasowarta hannunsa zube cikin aljihun wandonsa,tunda ta hangoshi tace da qawarta sa suka shigo tare "na shiga uku kubra mai gidan nan ya dawo"kubra da hankalinta ke kan waya ta ja tsaki tace"mtswee to sai me?ni wlh samira mamaki kike bani tunda.kika yi auren nan duk kin canza komai adarare duba fa dazu da zamu fita fitted gown fa kawai nace ki saka amma kika qi bayan kinsan gun manyan mutane zamu ji,tsoron mutumin nan kike ji kamar wani Allahn ki ke yadda ma kike tsoronsa baki tsoron Allahn naki ma,nidai gwara ma dai yau naga wanne dan mulkin nan ne wannan da.kike masa biyayya haka kamar shi ya tsuguna ya haifoki Cike da gadara da rashin kunya kubra ta fito yayin da samira keta.rabe rabe don kuwa riga da skert ne a jikinta na shadda kana kallon shaddar kasan an kashe mata naira mai tsada ce saidai anci mutuncinta ta wajen kacalcalata da yi mata matsatstsen dinki,ga mayafin jiki ta sai kace wadda aka yiwa gorin lullubi Kallo daya ya yiwa kubra da ta tsareshi da ido duk wata rashin.kunya da ta fito da ita tayi nata gun,hakanan aliyu yake Allah ya bashi baiwar kwarjini masifa,ta sake kallonsa karo na biyu"wow"ta fadi a hankali don gaba daya ya tafi da tunaninta,sai ta mance mission din ta fito da shi,ta zuba masa ido gaba daya,sai a lokacin idonsa ya kai kanta bayan ya dauke kansa daga samira,takaici ya kama Aliyu ganin irin kallon qurillar da take masa ya sake dinke fuska tamau,sai lokacin ta kula da ta bada kanta fa ashe, Ta dauke kai cike da duniyanci da niyyar bin bayan samira dake ta zuba sauri jiki na rawa,tsawa ya daka mata😠 hadi da nuna mata qofar get sannan yace"get out of my house idiot kada na kuma ganin wadannan lalatattun qafa fun naki a gidana"murmushi ma ta saki ta juya ta fice cikin karairaya wai ko zata janyo hankalinsa, bata san wani takaicin ne ya sake qumeshi ba yaja wani dogon tsaki ya juya ya nufi sashen samira Mrs muhammad👑 📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻 3:37 pm 8/11/1437 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *wa yasan gobe?.....* 4⃣1⃣~4⃣2⃣ Kubra ta tsaya a bakin get din tana jinjina kai ita daya take sumbatu"kut lallai yarinyarnan dole ta matowa gayen nan shi yasa take ta faman rawar qafa?ai kuwa wlh baza'ayi bani ba"tayi qwafa sannan ta ja qafa tayi gaba, samira ta kasa zaune ta kasa tsaye tasan halinshi sarai yarjejeniya kuma suka qulla tun kan aurensu kan shi baison wadannan kwashen qawayen nata gashi yau ta saba yarjejeniyar,tana shirin guduwa dakin gadonta ya damqota ya maidata kan kujera,ya kalleta sosai sannan ya jefo mata tambaya"ina kika samo waccar shedaniyar?"ta dake duk da tsoro ne fal cikin idanunta tace"qawata ce fa"ya gane mai takeson yi duniyancin nata data saba don haka ya shirya nuna mata nasa salon,don haka sai ya saketa daga riqon da yayi mata,ya saki fuskarsa ya daga kafadarsa hadi da watsa hannayensa na nuna alamun rashin damuwa da abu kana yace"good....verry good tunda qawarki ce kinga abun zai zo min da sauqi kenan ko?,dama gani nayi tamun inason aurenta aikinga zaman naku zai miki dadi tunda kun fuskanci juna, bata san sanda tayi zumbur ta miqe ba tana zazzare idanu ba baki na rawa tace"iyi...mme...me kace"ya daga mata gira sannan yace"abinda kunnen ki suka ji shi nace"ya juya yana niyyar barin dakin,hankalinta a tashe ta riqoshi kasancewar tasan halinshi *fada da cikawa*ya dubeta fuska a turbune yace"meye haka"don Allah ka rufamin asiri wlh bazan qara ba kasan wace kubra kuwa?"ya sake dage kafada hadi da cewa"ni ina ruwana da koma wace ce tunda kin kawo min ita har gida ni kuma na gani kuma ta yimin"ya zare hannunsa yayi ficewarsa,yana jiyo kururuwarta sai ya tuna haukan da tayi masa sanda zai dawo da salima,murmushi🙂 ya subuce masa ba tare da yayi niyya ba,yasan cewa shikenan yayi abinda zai rabasu kenan har abada ba tare da ya wahal da bakinsa ba,(samira irin mai rawar kan tara qawayace ko wa qawarta ce kare da doki ga son birga da burgesu ita dole sai an san mijinta wani ne,kaya komai tsadarsa suka gani a gunta tofa take zata basu ko nawa aka siya musu ko na aliyyun ne kuwa,indai zata burge tofa magana ta qare,gata da saurin daukar maganarsu don yadda take jin zancansu nata jin na mahifanta haka ne yayi silar lalacewarta,wannan ne yasa aliyu ya rabata da kowacce qawa amma da yake akwaita da kafiya taurin kai da naci sai ta sake wasu sababbi wadanda aliyyun bai sansu ba) Kai tsaye ya wuce sashen sa tun daga falin ya ga canji komai fes ya koma hayyacinsa,daddadan qamshin girki ya cika falon nasa,bedroom ya zarce ya daura alwala ya nufi masallaci,kan ta kammala aikin ta gama gajiya tubus don kuwa aikine ya gama taruwa ya cakude ita kanta wani gun cike da qyanqyami ta daure ta gyarashi to ina kuma ga aliyyu Take tasha alwashin zata yiwa tufkar hanci don badaqalar data tarar a bedroom din tasa ta isa,tuni ta gane cewa fushinta bashi da amfani don yadda komai ya qazance ta sani cewa da duniya zata gani ba iya su samira kawai za'a zaga ba harda ita,don ba wanda yasan mekw gudana tsakaninsu,ta sake gayawa zuciyarta lallai ibada tazo yi ibada kuma mai wahala wadda itace tafarkin shiga aljannarta kuma ta dade da sani aljanna bata samuwa daga zaune ba tare da ka tashi kayi aiki tuquru ba kuma dole ka ninka haqurinka(wannan sune daya daga cikin lafuzan umminsu garesu ko yaushe,uwa ta gari kenan) Aliyu bai shigo ba har sai da yayi sallar isha'i don haka tuni ta gama komai har ta jere a dining taje tayi wankanta ta shirya tsaf cikin dark blue din shadda doguwar riga wadda aka mata surfani mai kyau tun daga sama har qasanta ,hankalinta dai na kan taliyarta don haka ta nufi table din saidai wayam don ko plate din babu,ta juya ta shiga kitchen acan ma a bude ta tadda tukunyar wayam Ta san babu wanda ya cinye abincin sai shi don ba wanda ya shigo din,wata dariya😂 ta subuce mata data tuno yadda ya shigo dazun rai a hade yayi wani kicin kicin da shi😠 ashe harda yunwa itama ta taimaka wajen dinkewar fuskar tasa,ta hade kwanunkan ta dauraye ta maida su muhallinsu cikin ranta tana cewa"babu rabona nasha ice cream🍧 Tana bisa carfet ta bude babbar robar ice cream din tana diba a hankali tana kaiwa bakinta lumshe ido take don babu abinda take jin dadin shansa kamarshi din,wayarta ta duba jin qarar shigowar text _kizo ki bawa mutane abinci_"haka taga an saka,ta duba sunan Aliyyu salim maitama kamar yadda yayi mata serving din ta ranar da bata da lafiya"ta miqe hadi da dauke ragowar ice cream din ta maida cikin fridge ta koma daki ta fesa turarenta na blue lady ta hada da asaal brush perform ta nade kanta da da farin hijabi ta zari wayarta ta fito hadi da kulle gun ta,a hanya suka hadu da salima ta rako baquwa suna tsaye da alama magana suke ganin fitowarta duk sai sukayi shiru suka bita da kallo ganin haka yasa tace musu salamu alaikum sanda zata giftasun,baquwarce kawai ta iya amsawa itama can xiki kamar wadda akayiwa dole,suka ci gaba da kallon nata har ta shige bangaran aliyun sai a sannan suka dauke idonsu baquwar ta saki ajiyar zuciya tace "tab gaskiya salima tahir na janjanta miki don wannan kam banga ta inda zaki ci nasara akanta ba,saidai ban sani ba ko ta bangaren farar fata"salila ta kai mata duka hadi da cewa"banason iskanci sadiya kota farar fatar ai sai na yi yaqi da itan ,dadin abun ma miskilancin mai gidan bai bari ki gane wa yafi so cikinku ai da tuni inaga na dade da kamuwa da ciwo yanda nake bala'in a son my dear💘 "ta fadi tana dafe qirjinta"(abunda bata sani ba aliyyun irin mazan nan ne wadanda ke nunawa mace qauna wadda kan bawa mutane mamaki har adinga zaton kunya ce basu da ita ko mallakesu akai sunyi sake da damar da ya basu tun farko har ta subuce musu)sadiya ta dafa kafadarta tace"to Allah ya bada sa'a don ko nice a matsayinki gaskiya bazanyi wasa da aliyyu ba"salima ta juya ido tace "ashe kin fara gano gaskiyata🙄 " Mrs muhammad ce 📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻 [10/16, 1:42 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *wa yasan gobe?....* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *written by safiyya Abdullahi musa huguma* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 4⃣3⃣~4⃣4⃣ 😳 '' |👙 | / \ 👠 👠 Ku tayani duba jama'a na taho da sauri na ina neman littafina na *wa yasan gobe*zan muku typing na nemeshi na rasa 😜😜😜😜😜😜😂 Just for fun ga wadanda suka ji haushina *wa yasan gobe?....* Loading..........👇🏼 *WA YASAN GOBE?....* *PART 2* 🌺 1⃣~2⃣ Sadiya ta dafa kadar salima tace to Allah ya bada sa'a don ko nice a matsayinki gaskiya bazanyi wasa da aliyyu ba"salima ta juya ido tace ashe dai kin fara gano gaskiya ta🙄" Sanda ta shiga yana zaune gaban na'urar tafi da gidanka yana qarasa aikin sa da dazun yunwa ta hana shi yi,sallama tayi ya amsa kansa na kan allon computer din,kujerar dake gefansa ta samu ta zauna,kusan mintina sama da ashirin bai ce mata kanzil ba don haka itama ta bude wayarta ta soma register din watsapp saboda yanzu as journalists tana buqatar wadannan kafofin sadarwar, duk da basu dameta ba don ba yadda farida batayi da ita tun a gida ta bude koda watsapp ne kawai ba amma taqi tafi ganewa karance karancen magazines da wasu rubuce rubucen Cikin yan mintoci qalilan ta kammala da account dinta na watsapp ta soma qoqarin hada na facebook,falon yayi tsit kowa ya sanya na'ura a gaba,lokaci lokaci takan daga ido ta saci kallonsa,qayatacciyyar fuskarsa da hasken screen ya sake hasketa tayi fresh,ta zubawa hannayensa ido yadda yake sarrafa computer din cikin qwarewa da da gwanancewa typing yake cikin sauri tamkar shi ya qera computer din yasan madannin kowanne abu abun sai ya burgeta sosai Wayarsa ta soma ringing ya dauke kai daga kallon fuskar computer din ya maidaa idonsa kan wayar ba tare da ya daga ba,baquwar numbace kuma bai dagawa,kira aka ci gabaa da yi akai akai har ya gaji ya danna ok ya dora ta bisa computer ya sanya ta a hands free Muryar mace ce "hello ranka ya dade" "salamu alaikum wake magana?"ya fada hannayensa na saman laptop dinsa yana aikinsa,"daga daya bangaren aka sake maqe.murya"suna na nadiya ina kiranka ne daga unguwar rijiyar zaki kano"bai maida hankalinsa ba kan wannan yace"me kike nema?"aka danyi jim har yana shirin kashewa sannan akace "don Allah ka rufawa zuciyata asiri kada ka kashemin waya domin kashe wayar tamkar kashe ni ne"ya tsayar da abinda yake sannan yace "uhm go on" aka saki ajiyar zuciya sanna tace "maitama Allah ya jarabceni da tsananin qaunarka wadda tasa na kasa jure hakan cikin zuciyata har sai bakina ya furta maka,ina roqonka don Allah ka taimakeni ka so........" "hey!"ya daka.mata tsawa "stop that,rubbish!"tsit tayi,ya ware idonsa kamar tana gabansa yace"ke baki da ajine irin na mata?" Shiru ba amsa don haka ya dora "let me tell you baki da shi,and inason gargadinki wannan ya zama na qarshe da zaki kira numberta,I hope kin fahimta ko"ya katse kiran hadi da jan tsaki,fadila tayi saurin dauke kanta lokacin da ya dago kansa taga tamkar ita zai kalla zuciyarta na wani irin bugu,kishi ya tokare mata qirji,ta lumshe ido bugun zuciyarta na qara sauri....... Mrs muhammad dinku ce😘 [8/25, 3:44 PM] ‪+234 812 673 9684‬: 5:55 pm 16/8/2016 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *wa yasan gobe?...* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *written by safiyya Abdullahi musa huguma* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *PART 2* 3⃣~4⃣ Kusan kimanin minti biyar idanun nata na lumshe ta kasa budesu saboda wani abu da takeji a jikinta wanda tasan baya rasa nasaba da tsan tsar kishi,ta sauke boyayyar ajiyar zuciya sannan ta bude idonta ta dora su bisa screen din wayarta tana ci gaba da qoqarin kammala bude account nata na Facebook duk da wani bari na zuciyarta na ci gaba da mintsininta,cikin zuciya lallai ta godema Allah da bai qaddara ta zubda ajinta ta bayyana abinda ke zuciyarta ba har ta kai aliyyu ya fuskanta bare ta samu nata kason cin zarafin kwatankwacin wannan wanda it may break her heart Tabbas ta sake yarda cewa so masifa ne musamman son da hausawa kema laqabi da son maso wani,babu irin baiwar da tabbas bata da ita iya kyau Allah ya mallaka mata shi ilimi hankali da nutsuwa,tasha jin mata yan uwanta da yawa na yaba ta bare tarin maza dake kara kaina a kanta Ta sake satar kallon nasa wannan karon maimakon ta tadda shi yana aiki kamar dazun yanzun takardun na watse ne a gabansa ya jingina kansa harda bayansa a jikin kujera dukkanin tafin hannunsa ya tallafe bayan kansa da su idanunsa na rufe,gashin idonsa yayi ma idon rumfa tamkar an jera su "Bani abinci"ya fada idonsa na a rufen,ta miqe ta shirya masa komai still dai idanunsa na arufen har ta gama ta koma ta zauna,a hankali ya bude idonsa ya kalli warmers din"u mean ni zan zuba kenan da kaina?"😒 ta girgiza kai sannan ta taso ta zuba masa white rice ce da miyan kaza sai hadin coleslaw tana kammalawa ta miqe da niyyar fita "ina zaki je?"ya tambayeta cikin izza,ta kawar da kanta sannan tace "sashina zan koma" yaci gaba da cin abincinsa sai da ya mula don kansa sannan yace "ban baki izini ba"cike da haushi da takaicin irin mulkin da yake mata ta koma da baya ta zauna kanta a qas Cin abincinsa yake with calmness ba abunda ya dameshi ya shanyata abunsa,har ya kammala bai dubi sashenta ba already ta soma gundura da zaman ga bacci ya soma mamayarta ga kuma fita office gobe early,sai da ya kammala duk abinda yake har ayyukan da yake shigarwa cikin laptop dinsa apple sannan ya tattare kayayyakinsa ya maida jakar laptop din yana shirin shiga bedroom dinsa yace da ita"ki hadomin coffee ki kawo min" Kamar zata fashe da kuka☹ ta shiga kitchen cikin mintina biyar ta hada masa ta juye cikin cikin wani set din butar shayi irin na larabawa na silver da cups dinsu yake hade da tray Hade da sallama ta shiga dakin yana cikin lallausan bargonsa cikin shirin bacci ba haske a dakin sai na fitilar gefan gado,yana receiving call har ta shigo ta isa bed side ta dora plate din daidai lokacin da ya kammala amsa wayar ya kasheta gaba daya ya cillata bayansa tana tsaye har ya kammala addu'o'in bacci sannan ya juya mata baya yana gyara kwanciyarsa hadi da jan bargonsa "kina iya tafiya" dama a gundire take Allah Allah take ta bar masa dakin ta juya ta fice abinta Tana shiga bedroom dinta nightgown kawai ta sanya ta fada gadonta tana addu'o'in kadan kadan har ta gama,a hankali ta lumshe idonta tana da muradin yin bacci amma ina sai tunanin da akullum yake zame mata na qarshe a rayuwarta shi ya lullube qwaqwalwarta,duk yadda taso bacci yayi awon gaba da ita abun ya faskara har sai da ta dade tana ninqaya a duniyar qaunar aliyyu haidar sanan baccin yayi awon gaba da ita bacci ne mai cike da mafarke mafarken aliyyun ⚜⚜⚜⚜⚜⚜ Cikin hukuncin ubangiji rayuwar ke tafiya da bawa wani lokaci ta zo maka uadda kake so kake tsammaninta wani lokacin kuma ka samu akasin haka yau fari kenan gobe tsumma jibi nasara gata asara duk cikin hukuncin ubangiji ne da yadda yaso rayuwar bayinsa ta kasance,to bawa mai cike da tauhidi da imani sai ya godewa masa don kamar yadda haka yake ga fadila,shekararta guda kenan cikin igiyar auren aliyyu,shekarar da ta ga abubuwa daban daban ta fuskar qalubale da nasara Zamu iya cewa babu wani abu da ya sauya dangane da salon mu'amala da alaqa dake gudana tsakaninta da shi baya ga wadda muka riga muka sani,nasara daya ce zata iya daga hannu🙋🏻 ta fadeta cike da alfahari shine duk cikin samira ko salima babu wadda take iya sarrafawa aliyyu girki da tsaftar muhallinsa kamar ita Abunda suka fi qwarewa ciki sune kowacce ta fito tana tunqaho da hura hancin Aliyyu yafi sonta akan sauran 'yan uwanta,takan kau da kai cike da yakanah tayi kamar bata san abinda suke yi ba,wani lokacin kuma sukan bata dariya har ma ta murmusa takan daukesu ne a matsayin wadanda basu san mai ya kamacesu ba duk da kuwa duk sun bata wasu shekaru sun kuma girmemata sosai tana ganin tutiya bata kamacesu ba a irin wannan rayuwa da suke,ta sanu da gayya suke mata wani abun ganin cewa bata taba daga ido ta kallesu ba bare suyi 'yar tankiya So suke ta zamo daya daga cikinsu domin kuwa fada tsakaninsu sun koma tamkar 'ya'yam tumaki har bangarenta tana jiyo hayaniyarsu,sukan ji kasiririt ne idan aliyu yana gida don ko giyar wake suka sha a yanzun basu fada gabansa tun tuni yayima tufkar hanci ya kuma tauna tsakuwa don aya taji tsoro ta kuma ji din saidai su yita 'yan habaice habaice wadanda shi da yake namiji me bai ma fuskantar me suke Ta riga tuntuni ta saddaqar da cewa soyayayyar aliyyu wani gine ne daga Allah cikin zuciyarta,tayi imani koda bai sonta ba koma zai sota din ba kamar yadda yayi mata tunqaho Allah bazai taba wofintar da ita darajar biyayyar aure da take hidima a gareshi da kayutata gami da girmama buqatunsa,duk da babu wani sauqi da take ganowa a tattare da aliyyun amma har kulluma tana bawa kanta confidence kan hidimar da take masa especially a duk sanda haduwa ta hadasu da uncle abba momi abbanta ko umminta taga yadda suke nuna jin dadinsu har yau da wannan aure nata sai taga zata iya ci gaba da faranta ransu indai hakane Saidai abinda bata sani ba shi kansa yakan samu kansa cikin nutsuwa a duk ranakun da suka zamo nata ne ko banza ya san yana sakewa yaci abincinsa cikin nutsuwa da kwanciyar hankali kuma cike da gamsashshen dan dano irin wanda yake so duk da babu ruwanshi da ita,some times ma kafin ya dawo ta hada duka abinda yake so ta bar masa bangaren,mutum ne aliyyu maciyin abinci bao wasa da cikinsa ko kadan hakanan halittarsa take,duk qwaqwar mutum bai isa yayi indication wasu sign da zai nuna yana jin dadin hidimarta ba Mrs muhammad dinku ce😘😘😘 📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻 [8/25, 3:45 PM] ‪+234 812 673 9684‬: 5:08 pm 20/08/2016 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WA YASAN GOBE?..* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *written by safiyya Abdullahi musa huguma* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *PART 2* 5⃣~6⃣ Cikin watannin da basu gaza biyar zuwa shida ba fadila ta samu gagarumar nasara ta bangaren aikinta,nasarar da bata taba tsammanin zata sameta in a few months ba,ta soma aikine cikin sa'a,farin jini sosai take da shi,sunanta ya fara fantsama cikin al'umma shirye shiryenta sun samu karbuwa matuqa da gaske,ki ina ka zaga zancan matashiyar 'yar jarida fadila Abbas wakili ake,ita kanta tana mamaki with her few age ta samu daukaka haka,saidai da yake mai hankali ce takan godewa Allah domin tasan babu wanda ya isa yayi mata haka sai Allah,hakan yasa ta sake daura damarar riqo da aikinta cikin qwazo amana da kuma gaskiya da kuma manufa kyakkyawa da zata kawo gyara da ci gaban al'ummarta,bata mantawa da ya ahmad da abbanta wadanda su suka jagoranci samuwar ci gaban nata Bayan ta kammala duk wasu ayyukanta kamar yadda ta saba,ta shirya masa komai hatta da tissue bata barta ba,sauri take ta yi ta fice daga gun kafin dawowar tasa,saidai kash bata ci nasarar hakan ba don kuwa a bakin qofa suka yi kacibus kadan ne ya rage basu bige juna ba,da sauri taja da baya tana shaqar numfashin ta dake gudu sakamakon tsoratar da tayi,qasa tayi da kanta tana murza tafin hannunta gami da cewa "sannu da zuwa" Kusan minti biyu taji shiru shi bai wuce ba ba kuma alamun juyawa yayi,ita kuma ya bashi dama ne ya fara wucewa duk da sauri da take ta koma bagarenta ta cire pad din jikinta ta sauya wata,ta dago kanta don taga me yakeyi ne haka yana tsaye hankalinsa kwance kamar bai tsarawa kowa hanya ba don bashi da wani alamu na matsawa hasalima tie dinsa da coart yake cirewa a nutse Ganin haka yasa ta raba gefansa don ta shige ashe bata sani ba ya sanya mata qafarsa dake saye cikin sau ciki👞sam bata lura ba don hankalinta yayi gaba,luuu tayi baya ya goce sai kuwa ta bugu da qofan falon ,cikin azabar radadi ta dafe gun ta dago a hankali ta kalleshi sai taga tamkar ma baisan mai yayi ba agogon hannunsa na gucci yake cirewa,malolon takaici ya kama mata maqogaro tuni kuka ya kufce mata tasa kai tanashirin bar masa gun tana dafe da goshinta Ji tayi ya jawota baya ta dawo tayi kamar zata sake faduwa Allah ya taimaketa ta tsaya da qafafunta bayan taga tagar da tayi "sama fa qasa ya kalleta sannan yace "😠baki da kunya ko?,ni zaki buge ki wuce kenan?"tafin hannunta tasa ta kate fuskarta tana ci gaba fa kukanta shi kuwa ya zuba mata ido ba tare da ya sake cewa komai ba, sai da ya gama ikon nasa don kansa ya kauce tare da wucewa ya bar gurin Da gudu ta fice tana ci gaba da kukan ta wuce bangarenta,dispenser ta kunna tayi heating gurin sannan ta koma bisa gadonta ta kwanta tana maida ajiyar zuciya,me ta masa?ma ta tsare masa banda tsabar cin zali kawai don ta rabe zata wuce sai ya mata wannan muguntar?" Ta danyi qwafa kadan a ranta tana ayyana zata rama ⚜⚜⚜⚜⚜⚜ Su biyar ne zaune cikin office din fadilan sai fauziyya fa'iza aisha da halima dukkaninsu abokan aikinta ne matasa ne son saidai duk sun girmemata aqalla zasu bata shekaru uku zuwa hudu,amma nutsuwa da kaifin hankalin fadila yasa ta saje cikinsu suna jin dadin zama da ita sosai duk da miskilace saidai akwai karamci da mutunta mutum Hira suke gaman da zamantakewar aure irin hirarmi dai mata da aka sani wadda matuqar mayan aure suka wuce biyu aka hadu sai an yita,hira ce ta qaruwa ba banzar hira ba wadda bata kamata ba,duk da haka fadila na gefe don bata da abun fadan saidai jifa jifa takan ce wani abu Hira tayi nisa fa'iza ke basu labarin wata maqociyar yayarta 'yaf nijar dake saida magungunan mata masu kyau na gargajiya wadanda basu cutarwa,dukkansu suka ce ayi kiran matar suna so fadila kawai ta rage,fa'iza ta kalleta"ke ba ki siya fadila wlh maau kyau ne"murmushi tayi tana neman qaryar da zata gilla musu,don ko ta siya me zata yi da su,ta kalli fa'iza "to a hado da ni ga nawa kudin"ta nude zif din jakarta ta fito da kudin,fa'izan ta kuma cewa idan ma bakiso akwai wani hadin tutare mai tada sha'awar mai gida sai a kawo miki shi"cikin basarwa fadila tace"a hadomin duka kawai"(kaji fa mai karatu kamar gasken tana da buqatarsun 😜😜) Take fa'iza ta kirata ta sanar mata,ta kaahe wayar tana dubansu tace kun taki sa'a don gata nan ma anan kusa don tana ja'en,cikin minti talatin sai gata kowacce ta karbi nata ta sanya ajaka Qarfe biyar ta soma hada kayayyakinta tana sallama da su zata wuce gida don ta kammala aikinta ,wayarta dake aljihun bayan jakarta ta dauki qara alamun ana nemanta *sister ta* ta gani bisa screen din hakan na nufin farida ke kiranta,da sauri ta daga hadi da yin sallama,"sister ki taho kiga baby girl mai kama da ke kamar copy naki akayi na haihu yanzu haka ina gida"wani tsalle fadila tayi hadi da qaramin ihun farinciki sam ta mance a office take ba a gida ba sai da taga su fauziyya sun taso suna tambayarta mai ya faru sannan ta tuna ta maida wayar tana dariya cikin doki tace junior sister na ce ta haihu wlh"suka mata barka hade da dariya suna cewa saura ke kenan,murmushi 😊kawai ta musu ta saba jakarta tana cewa"Allah ya bamu alkhairi"ta kama kumatun yarinyar fauziyya tana mata wasa har ta fice yarinyar nata kuwa bangala mata dariya don fadila akwai son yara yarinyar ta soma sabo da ita yauma sa'a akaci bata sa kuka ba da zata tafin Da dokinta ta shiga motarta da niyyar wucewa gidan farida kai tsaye,har ta kunna motar ta tuna cewa sai fa ta sanar da aliyyu,take murnarta ta ragu tamkar an zare mata laka ta kashe motar,ta jawo hand bag dinya dake kusa da ita ta ciro wayarta ta bude sannan soma searching number'n sa cikin contact dinta wadda yayi mata serving da kansa ranar da bata da lafiya,tayi attempting din kiransa yafi sau goma ta kasa,sai ta fara dialing sai ta katse da kanta,bata san answer da kuma result da zata samu ba Daga qarshe taga hakan bazaiyi mata amfani ba sai kawai tayi shahada ta kira din,yadda wayar ke qara yin din din haka zuciyarta ke bugu,idanunta a rufe gam tana jiran wayar.... Mrs muhammad dinku ce👑👑👑 📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *written by safiyya Abdullahi musa huguma* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *PART 2* 7⃣~~8⃣ "Assalamu alaikum" dakakkiyar muryarsa ta doki dodon kunnen fadila,numfashinta ya dan dakata na wucin gadi,komai da ya danganci aliyyi jinsa yake har cikin jininta da bargo komai qanqantarsa kuwa,"hello waye ne?" Ya sake maimaitawa, "idan mai kira baida abun fada zanyi rejecting I have a lot to do"dadi muryar tasa ke mata har can qasan zuciyarta,zata so ta dawwama tana sauraren muryar idan da halin hakan,din din din da taji sau uku shi ya tabbatar mata ya katse wayar kamar yadda ya fada tun farko,ta saki wani dan murmushi da ya tsaya a kuncinta tana kallon fuskar wayar tata,tazarar minti biyar ta bayar sannan ta redial din number tasa Tana daf da tsinkewa ya daga wannan karon ita ta fara yin sallamar ,yayi dan dum sannan ya masa a daqile sanan ya dora da "who's on d line?"cikin in ina ta soma magana don gaba daya dakiyarsa ta rudata "nice" "kewa"ya maida mata da tambaya,"fad...fadila"ya sake shiru na yan sakanni har tana tsammanin ko baya kan layi ta duba wayar sai ta ga yana nan "What's going on?"ya sake tambaya,wani abu ya dan taba ranta da gaske bai ganeta ba har sai da yayi analysing a qwaqwalwarsa,"sister farida ce ta haihu" "uhm labari kike ban kenan?"ya fadi cikin watsar da muhimmancin batun a gunta,tambayar ta quleta hakan yasa tayi shiru,"me kike buqata ne ina fa da aikin yi"ta daure tace "baby nake son inje na gani" "ban amince ba"ya fadi kansa tsaye,din din ya katse wayar,wani hawayen takaici ne ya sulmiyo mata,tayi wurgi da wayar kujerar gefenta,cikin takaici ta figi motar sai gida Danja na tsaida su tana ganin wani wani saurayi dake gefan tata motar yadda ya zuba mata ido da alama yana mamakin me ya sanyata kuka ne,ta kawar da kanta gefe cikin zuciyarta tana ayyana in banda babu kyau fita babu izini tabbas da sai tayi wucewarta gidan farida saidai aliyyu yayi tsirenta,ta share hawayen sanda danja ta sake su ta sake figar motar,tana kallon yadda saurayin ke sa mata signa yana son tsaidata tayi banza da shi ta qarawa motarta speed,ita kanta bata san tayi gudu haka ba sai da ta iso gida agogon wayarta ya harba taga yan taqitattun mintocin da suka kawo ta gida,tana qoqarin shiga gidanne bayan mai jire bakin qaton get din gidan ya dage mata qofa ta soma shiga taji wani horn din,ta glass ta hangota motar samira ce wadda take cin ubanta da hawa ta tabbatar da motar mutum ce da tuni ta dade da guduwa,ba samiran ba hatta qawayenta sai suzo su ari motar su wuni sur suna cin ubanta ko a daddoke mata ita su kuma dawo su yasar mata ita ce mai kudin banza ta gyaro ta zuba musu mai gobe su dawo su sake ara ita kuma ba lissafi ta basu saboda tsabar neman suna irin na samira,shi uasa tayi nacin aliyyu ya canza mata mota qememe yayi buris da ita don yana sane da abinda takewa tatan Mrs muhammad ce 📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻 12:36 pm 22/8/2016 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WA YASAN GOBE?..* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *written by safiyya Abdullahi musa huguma* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *PART 2* 9⃣~~1⃣0⃣ Ta ajjiye motar a parking space ta kashe ta tana mai dauke idanunta daga kansu samira zuciyarta na tur da irin halayen mutanen da samiran ke mu'amala da su,hakanan ko yaushe zaka gansu cikin shiga ta banza da rashin da'a,yanzun ma qawayenta ne su uki ta dauko cikin motar kowacce kuma cikin shigar tasu dai ta dabi'ar da suka dorama kansu ,tana jin shewarsu sanda take rufe motarta kasancewar suna bayanta ne tsaye jikin motar samiran su basu shige ba hakanan basu komacikin cikin motar ba,sun saba yi mata haka tun ba yau ba kula su ne sam bata taba yi ba don bata kallonsu ma a matsayin cikakkun masu hankali,tana ganin idan ya kula su ma tamakar ta basu wata martaba da daraja ne,kallon tsiya ma basu isheta ba bare su sa ran wataran zasu samu na arziqi bare fadilan dama miskilar kanta ce sai ka gama cin kashinka a gabanta idan bata ga dama ba quda bazata kore maka ba Kamar ko yaushe yauma har ta bawa banza ajiyarsu tayi gaba abinta maganar da ta jiyo suna fada ita ta sanyata dawowa da baya ta tabbatar ya zama dole yau ta yiwa tufkar hanci bare yadda take cikin takaicin hanata zuwa gidan farida da aliyyu yayi shewa suka yi sanda take yin gaban sannan daya daga cikinsu tace"badi'a (sunan daya daga cikinsu ta kama)saiki dinga fakewa da fita aiki ana yawo a kwararo Da baya ta dawo sannan ta fuskancesu,dubansu tayi daya bayan daya up to down ta saki wata 'yar siririyar dariya tace "😏 ai karuwanci iyawa ne kuma karba karba ce,💁🏽wata hajar sai ta qaraci zamanta a kasuwa tasha qura tayi futu futu kullum kuma sai an fito da ita an kasa amma sai kiga ko kallonta al'umma basuyi bare su baqaci siya,kinga kenan inda wani yayi rawa aka bashi kudi wani idan yaje yayi dan banzan duka zaici Ta sake watsa musu kallon raini sannan ta dora"ku ba abokan yina bane don ban hada sabga da ku ba wannan.....ta nuna samira da key din mota dake hannunta "itace abokiyar yina,ita din ma zata gaya muku inuwarta bata isheni kallo ba bare zahirinta,but.... well zan baku shawara guda daya hade da gargadi mai kama da jan kunne,shawara ta farko itace ku rufawa kanku asiri ku samu ku raba jikinku a dakin aure kafin a rasa mai kwasar ragowarku......😂🙊 au am sorry na manta yanzun ma fa hakance ta faru da ku fa shi yasa kuke gararamba da yawon kwadayi da maula agidajen matan wasu And gargadina shine kada wadda👉 ta sake bude rubabban bakinta da niyyar shiga gonata don nikam duk cikinku babu wadda tayi isar da zan shiga gonarta,saboda haka nima akiyaye shiga tawa gonar👉"ta kama kunnenta daya da hannunta tace"idan kunne yaji......gangar jiki ta tsira"ta saki hannunta ta juya da niyyar shigewa dukkansu sunyi mutuwar tsaye don nasu taba tsammanin ta iya magana haka ba a yadda samira ke basu labarinta,samiran ce tayi yunqurin nuna jarumtarsu tasha gabanta ta kama qugu tana cewa"ke qaramar 'yar iska mu kike nufin zakiyi wa rashin mutumci?" Murmushi fadila tayi tace"🤗 a'ah sanin kanki ne fa ni ban iya hayagaga ba ke zaki fara baiwa wanda bai sani ba labari ,to kuwa akan wadancan👈🏼 shashashan bazan fara ba"ta gewayeta tayi wucewarta,tana jiyosu suna ci gaba da kuri da cika baki kala kala akanta har suka wuce sashen samira,cikin ranta take fadi Allah ya bawa daya daga cikinsu sa'a tace zata biyota taga yadda ake rashin albarka Wanka tayi don taji sanyin zuciyarta tuni ta watsar da batun su samira don basu gabanta hasalima bata daukesu wani abu ba don tasan baya ga tsabar jahilci dake damunsu rashin tarbiyya na bibiyar rayuwarsu,tana mamakin tsarin rayiwa irin tasu sam basu damuwa da yanayin da rayuwarsu ke gudana,falo ta dawo ta hada yoghurt mai sanyi da fura ta dama ta koma saman kujera tana diba da cokali a hankali tana sha zuciyarta sam bata gidan,kira ne na anty hafiza ya soma shigowa wayarta tana neman farida ne tayi ta kiran wayarta busy shine ta kira ko suna tare ta bawa faridan,nan da nan ta tabo mata miki basu gama sallama ba ta kashe wayar don bata son taji kukan da ya qwace mata,kamar kuwa hadin baki yan uwa ke kiranta suna cewa ita zasu yiwa barka itace uwar 'ya,hakan ya raunana zuciyarta sosai tasha kuka,sister faridanta guda amma wai a hanata ganin 'yarsu? Har magariba jikinta amace yake,sai sannan ta tuna bata kira umminta ta mata barka ba,jin muryar ummin bayan ta daga sai ya karyar mata da zuciya kuka ta saki,a tsorace ummin tace "meye haka lafiyarki kuwa?"cikin kukan tace "ummi ya hanani zuwa ya hana ni inje inga baby ummi"ummin ta saki ajiyar zuciya sannan ta ja tsaki"wlh harkin tayarmin da hankali na zaci wani abune ya faru ko ya sameki?" Ta sake marairaicewa cikin muryar kuka tace "ummi wani abune mana sister farida fa ummi" "to sai me idan baki je din ba?,idan kinje ma me zakiyi mata iyakaci kije kuyi ta surutu,tunda Allah yasa an sauka lpy bashi kenan ba abunda dama ake buqata kenan"ta sake sakin kuka tace "ummi ki masa magana don Allah idan ba haka ba baza ni ba"kama haba ummin tayi kamar fadilan na gabanta tace"🤔lallai bansan haryau quruciya na damunki ba fadila,to ba da ni ba wannan shiriritar,bana som sakarci ki maida hankalinki fadila kada na soma jin wani abu kuna jina ko?" A sanyaye ta gyada kai ta sani ummin bazata so ace bata je ba amma bazata taba bata goyon baya ba,halin ummimsu ne a gidan aure maca ce mai tsananin biyayya ga abbansu ko layi uaja yace kada ta tsallake to insha Allahu ba zata tsallake din ba hakanan kaf yaran babu wanda zata bari ya tsallaka hakan ne yasa har yau har gobe har ma jibi inji shi abban nasu yake alfahari da kuma ji da ita ********************** ⬇ ************************** ************* Ai Hausa Novels **************** *************************⬆ ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ⬇ ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ⬆ ************************** Ta saki ajiyar zuciya bayan ta kashe wayar tana jan majina hadi da son maida kukan ta,alwala ta daura tayi sallar magariba ta zauna kan sallayar tana jiran a kira isha,hakanan fadila take tana da kwadayin wannan garabasa da ake samu ga duk wanda ya idar da salla bai kuma tashi daga gurin ba,jira ne baifi na awa daya da rabi ba aka tada isha'i ta gabatar da ita duka harda shafa'i da wutiri sanann ta sake zama ta karanta subhanallahi wa bi hamdihi subhanallahil azim,don kanta ta gaji da zaman ta ninke abun sallar ta maida shi muhallinsa ta baro dakin sa hijabinta a jiki don dumin cikin hijabin ya mata dadi Cartoon ta maida tana kallo kan tashar m.b.c 3,lokaci lokaci tana sakin ajiyar zuciya saboda kukan da tayi,sannu a ahankali ta soma jiyo qamshinsa ,ta daga fararen idanunta ta maida su bakin qofar shigowa falon,cikin nutsuwa da sallama ya shigo yana sanye da jacket black blue sun haska farar fatarsa,sunyi amsarsa matuqa da gaske adorable structure dinsa ta fito sosai,sassanyan kyawunsa din nan ya bayyana cikin kamilalliyar tafiyarsa ya qaraso falon hannayensa sarqe a qirjinsa,can qasan maqoshinta ta amsa sallamar carelessness ya samu hannun daya daga cikin kujerun ya zauna ba tare da ya dubeta ba With bounded face yace"ki fito na miqaki kiga baby"tamkar tayi banza da shi ko tace ta fasa sai taga idan ma tayi hakan ai kanta ta yimawa ba wani ba don shi kam bashi da asara,ta miqe kamar marar laka ta shige bedroom dinta tana qunquni qasa qasa"sai an ma gama qonawa mutum rai sannan za'a wani tasa shi a gaba akaishi kamar wani dan qanqanin yaro" "idan baki zuwa ba saiki zauna ba ke ya shafa"ya fada a tsawace,baki ta rufe da sauri ta qarasa shigewa bedroom din don batayi tsammanin ya ji ba,lallai shi kuwa wane irin kaifin ji gareshi take mamaki cikin zuciyarta *NOTE*: assalamu alaikum masoya littafina saqonninku nata isheni da maganganunku game da littafina,duk da cewa na sani nayi muku bayani tun a farko na yadda rubutun zaici gaba da kasancewa sakamakon shirin fitar da shi kasuwa,na dauka tuni mun wuce gun saboda banyi zaton zanci gaba da baku shi littafin ta watsapp bama amma yanayin yadda kuke nuna qauna gameda da shi din yasa naci gaba da rubuta mukun duk da na rage yawansa kamar yadda na fada, To amma naga rashin fahimta na son shiga ciki,na farko har ga Allah yadda wasunku ke min bana jin dadi yana bata zuciyata,saboda bani da wani uziri da zai taso min a matsayina na yar adam a gunsu abunda kullum suke buqata shine nayi musu kawai typing na turo musu,sannan wasu babu yabawa saidai qorafi da zarar sun gama karanta wanda na samu na turo,hakan da suke yana kashemin gwiwa ne,maimakon suyi abinda zai qarfafa min gwiwa ko saboda gaba kada ku manta hannu ne keyi ba fada muke wayar na rubuta mana,kuma yau da gobe ai sai Allah,ni 'yar adam ce gsky da bana son abinda zai dameni ko ya samun damuwa a zuciyata nakan haqura da abubuwa da dama matuqar zasu jawomin damuwa,don Allah ina roqonki ku tsaya kuyi duba na fahimta game da ni,ni ba budurwa bace matar aure ce ku duba kuga yanayin hidimomin gida na kullum dake kan matar aure baya ga wadanda ka iya taso mata wadanda bata tsara da su ba a rana,ku dinga adalci kuna hukunci na gaskiya,mu fahimci juna don Allah wannan shi zaisa ni daku muci gaba da jin dadin alaqar dake tsakaninmu,wlh akwai abubuwa masu yawa da muhimmanci a rayuwata da nake yi kulluma da kafin fara muku rubutu amma a yanzu sun gagareni yi saboda rubutunku,na sani harka ta mutane sai kayi haquri tunda yadda muka banbanta a halitta haka Allah s.w.a ya ban banta mu a halaye da dabi'u,na gode Allah yasa mu dace👏🏻👏🏻 Na biyu kuma masu ganin abunda aliyyu yake yayi yawa kada kusa gaggawa a lamarinku kuma kada ku manta shi haquri shine jagoran kafatanin lamuran mu na duniya bare haquri ga 'ya mace kuma acikin gidan aurenta hanyar shiga aljannarta riba ce ba kadan ba,ina so ne yan uwana mata muyi koyi da halinta koda cewa ba irin auren ta kikayi ba amma nasan baza'a rasa matsala daya ko biyu da kike iya fuskanta ba daga mai gida wadda shigen halin da aliyyu ya taba nunawa fadila ne to ga yadda ta shanyeta ga kuma ribar da ta samu,na godewa masoyana gana daya ,Allah yayi mana sakamako agidan aljanna ya hadamu dukkanmu a cikinta in kuma ci gaba da zama marubuciyarku ta gidan aljanna 😜😜😀😀👏🏻 Mrs muhammad din[truncated by WhatsApp] 4:50 pm 23/8/2016 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WA YASAN GOBE?..* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *written by safiyya Abdullahi musa huguma* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *part 2* 1⃣1⃣&1⃣2⃣ Powder kawai ta shafa a fuskarta ta shafawa kyawawan labbanta lip glosses,atamfa ta zaro cikin kayan nata dinkin doguwar riga ne mai umbrella ta bude sosai an mata dogon hannu simple style ne,ta ware dan madaidaicin mayafinta ta yafa shi har saman kanta kamar yadda ta saba yafenta sannan ta fesa turare ta fito Yana tsaye a wajen motar yana amsar calling yayin da salima ke tsaye kusa da shi hannunta harde a qirjinta tayi kicin kicin da fusaka,sallama fadila tayi mata sai taga ta dauke kai don haka sai ta ja tunga itama tayi banza da ita,ya gama amsar kiran ya kashe wayar hannunsa na kan mabudin motar salima ta kalleshi tace"please dear"kai ya gyada yana cewa"dont mind" ya bude gidan gaba kusa da kujerar mai tuqi ya zauna ta bude baya itama ta shige,nasiru ya gaida ta cikin girmamawa a mutunce ta amsa sannan ya tada motar suka fice Tafiya ce kamar ta kurame sai ka rantse bata cikin motar sai shi da nasirunne ke hira jefi jefi galibi ma bai wuce zancan kasuwa,idanunta na kan titi yayin da zuciyarta ta lula duniyar tunani A bakin get suka dakata bayan mai gadin ya dage masu get aliyyu yasa nasiru yayi masa magana ya rufe ba shigowa za suyi ba,fadila ta tabe baki cikin ranta tana gulmar aliyyun,nasiru ya gyara parking din sannan ya fice daga cikin motar,fadila ta sa hannunta a kan mabudi zata fice "twenty minutes"haka ya fada cikin carelessness,ba abunda tace da shi tayi ficewarta "ko baka gaya min ba ai na sani uban masu tsari da qa'ida na duniya😙"tayi zancan cikin zuciyarta Da yake takwas na dare ma ta dan gota gidan ya samu sararawa daga cincirundon 'yan barka mutum hudu ta tarar Amina da mariya qannan mubarak ne sai maqociyarta guda daya sai kuma wata dattijuwa inna jummai wadda mahaifiyar mubarak ta kawo mata ita saboda kula da mai jegon da kuma jaririyar,alokacin da ta shiga ma tana kitchen tana kwashe tuwon da ta yiwa faridan,fadila nata qyalqyala dariya ganin inna jummai nata loda tuwon a flask tana ce mata"inna zanso naga dambarwar ku kam da farida don ba abincin da taqi jini irin tuwo,dama dai ni kika baiwa"innan da yake macace mai kirki da saurin sabo da jama'a tace"ai duk qinta kuwa da tuwo yanzu ya zama abokinta dole ta cishi tunda jego ya zo" Tayi sallama ta shiga falon faridan dukkaninsu suka amsa mata cikin fara'a suna dariyar hirar fadilan da inna jummai,farida kam ture kayan jarirai dake gefanta take tana cewa sister taho nan daya hannun nata kuma cup ne cike da tea tana sha sai hada gumi take inna kuma taqi ma a kunna fanka bare a.c saboda wai jego faridan zatayi irin na da,fadilan ta qaraso tana cewa "🤔sister farida mai tsokana da yawon gidan qawaye yau gata dq baby" dariya ta basu dukkaninsu harda faridan,idanu fadila ta baza tana neman baby tace nifa baku nazo gani ba wlh ina 'yata ku bani ita naji duminta"yarinyar na hannun maqociyar ta ta nannade cikin farin shawul mai taushi ta miqe tana miqawa fadila ita hadi da yi misu sallama ta ajjiyewa faridan 1000 kudin barka ta mata godiya ita kuma ta fice Ta kammala shanye tea din tas ta dire cup din tana kallon fadila tace "sister da fa har nayi fushi kece ta farko da kika fara sanin haihuwarnan baya ga abbanta amma sai yanzu zaki zo mana tun dazu baby ke son ganin mummynta bata zoba sai da aka rigata gane mata ita" "hmmm lallai yarinyarnan kukan dadi fa kike da yaya yanzun ma ya barni tare ma fa muke"cikin zolaya wadda attitude din farida ne tun usulinta tace "wow kice har an fara boyonki lallai soyayya ruwan zuma"fadila ta harareta tace "wlh badan kin mun abun kaiba kin bani baby mai kama da ni ba da sai na bubbuge bakinki"su amina suka qyalqyale da dariya sannan suka miqe suka ce bari dai mu baku guri kada a buge mana anti a gabammu"dariyar suka bawa fadila su kuma suka fice kitchen gun inna jummai Fadila ta sake zubawa yarinyar ido tubarkallah masha Allah qatotuwa da ita lallai kam wannan photo copy dinsu ce ta kalli farida tace sister sannu"farida ta ya da kai gefe tana tuno wuyar da ta sha"hmmm ke dai bari sister ansha gwagwarmaya ni kam dan ba qara"fadila ta sake rungume yarinyar a qirjinta tana sake jin qaunarta na shigarta bata qi ace tata bace,ta saki dariya tace "yanzun fa aka fara farida me akai da maza daga ihu daya sai kuma murya ta dashe?😜"ta qarashe ta sigar tsokana yau dai ta maida raddin tarin tsokana irin na farida da take mata ko yaushe,ko da can dama fadila Allah ya zuba mata son yara,sanda suka tashi muhammad ne kawai yaro a gidansu to har gidan maqofta take shiga dauko yara duk da yanayin unguwarsu irin unguwan nin nan ne da ba ruwa na da kai kowa na qulle shi da ahalinsa cikin gida amma haka fadila ke shiga ta taho da su,miskila ce ako ina magana bata dada ta da qasa ba amma banda kan yara hakanan zaka ga ta sasu a gaba suna ta wasansu,farida kam dama idan taga dama idan suka zo neman anty fadila sai ta korasu tace bata nan zasu zo su dameta ne Farida ta girgiza kai da sauri tana juya ido tace "kai sister is hardly in sake ko zan qara sai after five to ten years,nikam na barmiki ki taba kiji"dariya ma ta bata ganin duk yadda tayi laushi duk rashin tsoro da dakiya irin na farida,murmushi fadila tayi tana ci gaba da kallon yarinyar tayi kissing dinta agoshi,"ina aliyyu ne sister?"🙄af yana waje " farida ta miqe daga kashingidar da tayi tace "kada dai kice mun kuna tare yaushe ya aliyyu boss ya fara kai matarsa unguwa"fadila tace"saboda ya bata min ya fara ta kaina yau kina gani fa kamar gidqn nan yace min wai twenty minutes?"farida tace "wlh am serious ya aliyyu ko salima matarsa ta farko bai taba kaita wata unguwa ba idan ba monthly shopping naku ba(farida ta fi fadila sanin halinsa ne kasancewar tq fita shiga jama'a hakanan ta fita zuwa gidan uncle abba)kuma shine kika barshi a waje ga sitting room nan"fadila ta tabe baki tace "oho masa har get malam salisu ya bude masa yace a maida arufe ba shigowa za su yi ba" "gashi mubarak yanzu ya fita maida hajiyarshi gida da ya shigo da shi"farida ta fada tana lallatsa wayarta,"zancan kike so ki bar mubarak kada ki taso shi idan da rabon zasu hadu zasu hadun don ko mubarak ya zo idan bai ra'ayi ba bazai shigo din ba" Minti goma sha biyar ta shude suna ta hirarsu farida na cin tuwonta a sake kasancewar su mariya sun bar masu dakin,dahiru yaron dake wa farida aike aike ne ya shigo karbar abincinsa bayan ya miqawa inna jummai kwanon ya tsaya bakim falon faridan yace"anty wai baquwa ta fito za su tafi"fadila ta bata rai don tasan aliyyu ne yayi aiken kuma aqa'ida tana da sauran minti biyar Ranta a bace bayan ta bude camera din wayarta ta yiwa baby pic ta sake sumbatarta ta ajjiyeta gefan faridan ta dubeta tace sister zan dawo insha Allah me kikeson na kawo miki"murmushi tayi tace"sister fadila nayi missing din wainar shinkafarkin nan da kike mawa dady,idan zan sameta inaso"dariya fadilan tayi saboda ta tuna mata lokacin da suna gidan idan tayi insha Allahu kan ta gama shiryawa Abban a warmer taci na ci kuma ta bi ta har falon abban suci tare da shi tana hara rarta tana komai amma sai tayi biris,"insha Allah kamar kinci waina ta kin gama"sukayi sallama tamkar kada su rabu Tana fita taga motar mubarak fake kusa da tasu shi dinne kuwa da alam yanzun ya iso don lokacin suke gaisawa da aliyyun ta qaraso suka gaisa ya juya yayi cikin gida yana cewa bari ya dauko ma aliyyun babyn ,hannu biyu yasa ya dauki babin mubarak na gyara masa riqon don da gani bai iya ba,ya riqe ta sosai yana kallinta hadi da fadin"masha Allahu la quwwata illa billah"(yan uwa gaka annabi ya horemu da fada a duk lokacin da muka ga wani abu da ya qayatar da mu to ko kana da kambun baka bazai kama abun ba domin wasu ma auna da shi amma basu san suna da shi din ba,sai kaga abu kayita kodashi ba tare da ka fadi hakan ba daga qarshe sai wani ibtila'i ya saukarwa abun ya lalace don Allah mu kula da wannan) Fadila na satar kallonsa kadan kadan tana kallon yadda ya zubawa yarinyar ido ya lumshe idanunsa daga baya ya budesu ya sumbaci goshin yarinyar sannan ya miqawa mubarak ita yana sake cewa Allah yayi mata albarka,ya amsheta sukai sallama ya shige gida da babyn Aliyyu ya yafito qasimu dake fitowa fitowa daga gidan hannunsa da robar abinci qasimu ya qaraso hadi da rusunawa aliyyu ya amshi bandir din kudin dake hannun nasiru ya miqawa qasimu yace ka kaiwa maman baby ya zaro 1000 daga aljuhun trouser dinsa ya bashi ya shige motar yabar qasimu nata zuba godiya yare da komawa cikin gidan don sada saqon aliyyu ya bawa nasiru umarni ya tada motar suka bar layin fadila nata satar kallonsa don kiwa dubu dari ce ya bayar a kaiwa babyn Mrs muhammad ce 👑 📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻 2:08 pm. 24/08/2016 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 WA YASAN GOBE?.. 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *written by masoyiyar buk din wayasan gone..* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *Part 2* 1⃣3⃣&1⃣4⃣ Fadila tacigaba da sake2 azuciyarta bata ankaraba taji ana bude get tana dago kaitaga harsun iso gida ashe,parking space ya nufa ya kashe motar,fadila dakekokarin bude motar setaji ya kulle motan ta waiwayo tadubesa suka hada ido tayi saurin dauke kanta zuwa gefe,shiko gogon sebinta ya ke da kallo can yace wai meye kiketa wani bata rai tamasa banza yacigaba damagana ,inatambayarki,kaikidanayine nayi lefi koso kike danabarki kikwana? nan ma shiru yaharzuka cikin tsawa yace wai badakenake maganaba salan wulakanci, Se asannan fadila tadago kai da fuska cike da hawaye tace wulakanci? wulakanci yawuce wulakantani dakakeyi Wanda haka har matanka suka sami damar gorantamun,Aliyu nayi nadamar aurenka auren bakinciki Inatabbatarma dabadan mahaifinaba dana dade dabarin gidan nan,cikin kuka takemaganar yayin da Aliyun yatsinci kansa da tausayinta Yakuma kasa cewa kome illa binta da kallo. Fadila tacigaba kodan matanka da ni ba irin su naso nayi kishi dasuba,naso ahadani da wayanda suka San mesukeyi😭 bawadannan da kake kallo amataba nibanga mata anan ba kuma duk ajin naka akan salima da samera yakare ragowar wasu,cikin bacin rai yadakamata tsawa,itako ta dannan motar tabude tafita da gudu tanufi sa shinta,tana shiga tafada kujera setaji ya akayi tayi wadannan magana,setaji kamar bats kyautaba cankuma wani bangaren zuciyarta tacemata garadakika masa haka yasan fa kinsan mekikeyi kuma yasan badan shikike gidanba Dan biyayyar iyayankine,tamike tashiga toilet tayi alwala ta fito ta tada sallar isha dabata samu tayiba. Can Aliyu kuma kasa futa yayi daga motar jikinsa duk yamutu zuciyarsa ta cunkushe abinda yafi damunsa shine kalmanta datayi kansu samira da salima domin yakaratunawa da yanda yasamu samira adarensu nafarko,sannan Salima bayan rabuwarsu itama ba agida tayi rayuwaba,yadafe kansa karo na farko da naga A S metama na kwalla daya nazurarowa daya bayadaya😰 yace inna lillahi wa inna ilaihirraji un.tabbas jidakai bekama ceniba domin ina tare da wadanda basu cancanci suzama iyayan yayanaba,gashi inakallo se haihuwa ake Wanda akai bikinmu tare duk sun haihu,su naji kowacce tace batashiryaba itakuma wanan yarinyar banashiga harkanta,gashi du k ta gane kome,Aliyu yacigaba da hawaye yana maibakkincikin abubuwa kala kala yadaure ya fita daga mortar jiki akasalance yanufi bangaransa yanashiga ya kulle kofar yabar makullin ajiki sabida bayasan ganin kowa domin koda sunzo sunyi amfani da makullinsu bazebuduba.yashige bedroom yafada gado yacigaba da tunani aranar dai Aliyu beruntsaba Dan maganganun fadila kemasa yawo akwalkwaluwarsa, Itako fadila cikin nishadi tayi barci domin tafidda wani tabo da kedamun zuciyarta. *amun afuwa Mrs Muhammad nayi muki shishshigi amma haka mukeson buk yadawo munakara mikamiki godiya dayabawa Allah yakara basira kidora saga inda natsaya domin zansamu goyon bays amma kitambayi friends sunyarda kidora😀*bye nabarki Lfy Wanda sukaji haushi suyafemin kar azagen nima wlh soyayyar buk din yasa nayi👍🏻 Ba Mrs Muhammad bace👑 📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻 [10/16, 1:46 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WA YASAN GOBE?..* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *written by safiyya Abdullahi musa huguma* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *part 2* 1⃣5⃣&1⃣6⃣ Qarfe tara fadila tayi wa iftihal wanka itama ta shirya cikin riga da skert na atamfa a cikin qana nun kayanta ta cirowa iftihal wasu riga da skert dama sun mata kadan jajayene in and top ta raba mata gashinta gida biyu ta tufke mata da ribbon sosai iftihal tayi kyau suka yi break sannan ta soma gyara part dinta kafin ta isa ga na aliyyu don duty dinta ne duk inda ta shiga yarinyar na biye da ita ita ala dole sai ta taya ta aiki sai da fadila ta bata mopping din kayan kallo sanna ta rabu da ita Fadila ta fito tana goge hannunta da duster bayan ta gama aikin ta iftihal dake ta fama da chocolate tace "anty ina daddy na?"murmushi fadila tayi ta kama kumatunta tace"kwantar da hankalinki 'yar daddy yanzu zaki ga daddy shiga daki bakin gado ki dauko min hijabina"da gudu kuwa ta shiga sai gata da shi a hannu ruwan madara ne iya qugu wanda ya shiga da atamfar jikinta sosai,ta kama hannun iftihal din bayan sun rufe qofan Tana sa kai falon taji hayaniyar sama sama muryar salima ke a sama,tana tsaye hannayenta harde saman qirji kan aliyyu shi kuma na zaune kan kujera yana sanye da kayan bacci na maza ruwan madara shima hannun nasa harde a qirjinsa😠,shigowar su yasa salima yin dif daga maganar da take yi din gami da sakin fuskarta daga tsukewar da tayi tana dan binsu da kallo(salima akwai duniyanci)sam bata lura da iftihal ba da suka shigo tare sai da yarinyar ta zame hannunta daga na fadila wadda ta shige kitchen ta ruga a guje tayi gun daddynta tana cewa"daddyyyy daddyyyy...."kamar yadda ta saba ta durqusa a agabansa kafin ta haye cinyarsa tana cewa"morning daddy sabahul khair",murmushi ne sosai dauke a fuskarsa wanda bai bayyanar da haqora😊yasa hannu ya dagota yana kallonta yace"sabahun nurrrr my lovely khadija"tayi tsalle ta dane cinyarsa abinta tana wasa da maballan gaban rigar baccinsa tana cewa"daddy tunnjiya nazo da daddare kaqi zuwa na ganka" "wonderful,anan kika kwana ke da wa?""ni da anty fadila tare ma yanzu muka taho"ya daga kansa yana nemanta da idanunsa sai dai tuni ta jima a kitchen bata a gun sai salima dake tsaye ta zubawa 'yar tata ido Kallonta take tana jin wani alfahari na shigarta tana godewa Allah da bai bata damar rasata ba,wani dadi ne ke cikata ganin gudan jininta ita da halitta mafi soyuwa a gareta wato Aliyyu salim Abdallah maitama,tabbas iftihal abar alfaharinta ce yarinyar bata debo kammaninta ba ko kusa babu wani abu nata data dauko illa farar fata wadda aliyun ma na da ita,kowa ya ganta ya san jinin su ce family din alhaji salim Abdallah maitama ce jininsu ce Ta dawo daga duniyar tunaninta hadi da miqawa iftihal din hannu alamar ta taho sanda suka hada ido fuskar salima dauke da murmushi,da taga kamar yarinyar bata fahimta ba sai tace"come on baby na come on my dear " yarinyar ta noqe kafada tayi luf jikin mahaifinta kamar mai tsoron ta babu sabo ko kusa tsakaninsu,wani kishi ya kama salima don taga yadda suka shigo da fadila yarinyar a sake take kana ganinsu kasan akwai sabo mai yawa tsakaninsu Ta sake gwada sa'arta ta miqa mata hannunkaro na biyu tana sake cewa"come on mana mai dear kin manta mominki ne iftihal? Me yasa baki zo guna kin kwana ba ina da chocolate da biscuit da yawa da zan baki"ta sake noqe kafada tace "um um nafison na kwana gun anty fadila she's nice like daddy"sai salima ta maida hannunta ta rungume cikin jin haushi Aliyyu na ankare amma yayi kamar baiga abinda ke faruwa ba,sai da yaji tana jan qwafa sannan ya tanka mata"duk uwar da bata yi showing mercy akan yaronta ba tayi abandoning duk wasu duty nata akansa no need to deceive her self akan shi zai iya jin qanta ya kuma ji tausayinta"idanunta sun kada sunyi ja kadan take jira ta fara malalar da hawaye tace"aliyyu abinda ya wuce ya riga ya wuce please"ta juya cikin zafin nama ta bar part din nasa kamar zata rushe da kuka 🔱🔱🔱🔱🔱 *TUNA BAYA*👈🏼 🔱🔱🔱🔱🔱 Aliyyu da salima sunyi aure ne irin auren da zaka iya kiransa na soyayya,karatu shi ya fara fitar da aliyyu india cikin garin mumbai dake qasar india,ya karanci fannin kasuwanci da masana'antu ne tun usulinsa,kusan binda ma ya zaunar da shi kenan a qasar bayan kammala karatunsa kafin daga bisani ya soma kai kawo tsakanin nijeria da indian Tun kafin aliyyu ya kammala degree dinsa na farko yake siyan kaya yana turawa uncle Abba yace a siyar masa tun uncle abban na dariya yana dauka wasa ne abun nasa yakance"alii rigima idan banda abinsa mai ya nema ya rasa da zai takurawa kansa sai ya fara kasuwanci tun kafin ya kammala karatunsa?"shi kama aliyyu ya dage aiko kaya yake tun daga lokacin da uncle abba ya fuskanci son kasuwancin a jininsa yake sai ya qyaleshi ,sai gashi tun kan ya kai ga kammala degree dinsa na biyu ya mallaki kudade masu tarin yawa na qashin kansa tsantsar guminsa,sam yaqi amsar tallafin sisin kwabo dag dukiyar da Allah ya horewa mahaifinsa,kwata kwata aliyyu ba cima zaune bane akwai zuciyar neman na kai tun yana qaraminsa,bai damu da arziqin da mahaifinsa ke da shi ba Wadannan kudade yaci gaba da juyawa har kawo yanzu matsayin da yake kai na mamallakin companies da share shares a gida nijeria da wadansu maqwaftan qasashen,aliyu ya zamo daya daga cikin matasa masu tarin dukiya mutumne shi da Allah bai bashi dagawar son a san wayeshi ba,yasha gayawa abban nasa tun kafin zuwan wannan lokacin shi yafison yasan ya san zafin neman na kai,sai gashi burinsa ya cika don ya tara dukiyar da shi kansa bai sa ran samun kamarta ba,darajar addu'ar mahaifa riqon gaskiya da amana tausayi da taimakon na qasa su suka kaishi ga wannan matsayin da yake kai Haduwar su da salima ta kasance ne sanadiyyar hutun qarshen zangon karatu da daliban instute din pashwar suka samu ciki harda,wadanda ba 'yan qasar ba kuma suke da sha'awar zuwa qasashensu hutu nata shirye shiryen zuwa gidan ciki kuwa harda saliman,wasunsu na ahiga kasuwannin dake cikin mumbai don yiwa yan uwa tsaraba Cikinsu harda salima su hudu ne ita sai wata qawarta 'yar nijeria sa'adiyya abikan karatunta biyu 'yan qasar data nemi rakiyarsu don qasarsu ce sun fita sanin kan farashin kayayyakin shruti da arohi,sun ahiga shagon a sanda aliyyu ke ciki yana zaune kan daya daga cikin kujerun dake ajjiye a shagon suna lissafi ne shi da mai mai shagon kan wasu kaya da aliyyun ya sara a gunsu alokacin tun kafin ya bude kamfaninsa Abu na farko da ya fara kama jan hankalinta game da aliyyun shine baiwar tsantsar kyau da Allah ya bashi da daddadan sauti ,abu na biyu ya bata mamaki jin yadda yake hira tar tar da indiyanci tamkar haifaffen can,tunda suka shigo shagon daga kallon farko na amsa sallama bai sake duban sashin da suke ba ya mai da kai yaci gaba da abinda ya kawoshi shagon Ita din ma azahiri idan ka kalleta sai kayi tsammanin hankalinta bai kansa saidai duk siyayyar da take yi kusan qani abun ma bata san me zatayi da shi ba data dauke shi don hankalinta na kan alin Tuni ya kammala abinda yake yayi sallama da raja ya wuce,sanda yake fita ashagon garin karkatawa ya wuce taga silmiyowar wani abu daga aljihun trouser dinsa ma baya amma bata zaci wani abu mai muhimmanci bane sai da ta sake matsowa ta sa idonta sosai sannan taga ashe wata 'yar kyakkyawar wallet ce ,da sauri tasa hannunta ta bude ciki,rupees(kudin india) ne masu yawa aciki a miqe,sai dan qaramin hotonsa wato passport,sai kuma wasu kati guda uku biyu na wasu shaguna dayan an rubuta *adishwar garment* shagon na cikin *janta cloth market hawkers plaza*ta maida shi ta duba dayan shi kuma na shagon *ajmeri fashion* shagon shi kuma na *hazarat abbas road Samuel street*,duk cikinsu babu shagon da ta taba zuwa tunaninta na kan yadda Atayi masa da wallet da kuma yadda zata sake samun damar hanawa da shi,tana duba kati na uku uku na dauke da sunan hotel din da ya sauka haka jikinta ya bata tunda su muta nene da komai ka siya ko kayi mu'amalar ciniki da shi sai sun baka rasit ko card nasu,tasan hotel din tunda takan ziyarci cikinsa lokaci bayan lokaci nan kusa da makarantarsu yake Ta maida duka kayan ciki tana sauke ajiyar zuciya,bayan sun kammala siyayyar suka koma cikin makaranta,da daddare ta canza shiga irin tamu ta hausawa atamfa ce saidai dinkin riga da skert ne tayi kwalliya sosai a fuskarta,ba wata tafiya ce mai nisa sosai ba tsakaninsu don haka irin keken nan nasu ta hau ya qarasa da ita,bata sha wahalar samunsa ba saidai da yake hotel ne na manyan mutane akwai tsaro sosai da kuma tsari duk magiyarta basu yarda sun bata number din room din ba sai da sika kirashi suka sanar masa,duk da yayi mamakin mai neman nasa kuma sunce mace yace a bata number din baisan me ya kawota ba ko da taimakon da zai iya bata Ku biyo Mrs muhammad👑😘 📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻 [10/16, 1:47 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WA YASAN GOBE?...* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *written by safiyya Abdullahi musa huguma* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *part 2* 1⃣7⃣&1⃣8⃣ Sai da tayi knocking sama da sau biyar sannan aka bude mata,fuskarta ta wadatu da murmushi😃 yayin da tasa take a tsuke😠 kamar hadari,"sannu ko?"tace da shi cikin fara'a"yauwa sannu" ya fadi adan dake yayi bake bake abakin qofar babu wata hanya bare ta sa ran shiga ciki don ko kalan labulen bakin qofan ba zata tantancewa ba,cikin qosawa ya gyara tsaiwarsa ganin tayi shiru yace "I hope lafiya dai ko?"ta sake yin murmushi a karo na biyu ya zaro wallet din daga cikin yar purse👛 dinta dake damqe a tafin hannunta sannan ta dubeshi tace"wannan ka yar dazun a mall din paras mahal collection"ta miqa masa tana dan murmushi,ya sa hannu ya amsa yana cewa"thank you verry much"ya juya yana qoqarin mai da qofarsa ya rufe Da sauri ta dakatar da shi ta hanyar cewa"haaabaaa haabaa malam babu ko goron tsintuwa?😊" a qagauce ya dakata ya juyo yana cewa"nawa kike buqata?"t saki wani mayaudarin murmushi"ba kudi nake so ka bani ba,kawai passport nake so na cikin wallet naka sai kuma phone number dinka shikenan abunda nake buqata🤗" Girgiza kai yayi hadi"it can't ki zabi wani abun dai daban banda wadannan"ta kanne ido daya😉 tace"ni su din dai nake so"kafewa yayi kai da fata bazai bata ba"i told you ba zaki samu ba"itama kafewa tayi akan shi take so indai alherin da tayi masa yake son rama mata,daya lura tana da yawan taurin kai sai ya bude wallet din ya zaro rupee dubu daya kwatan kwacin kudin nijeria a yanzu naira dubu hamsin ya ajjiye mata saman qafarta ya juya karo na biyu yana shirin sake rufe qofarsa Ta tabbatar idan ya subuce mata a yanzu mawuya cine ta sake samun dama kwatan kwacin wannan don haka cikin zadin nama ta tattara kalmomin"idan kamin haka baka min adalci ba zaka kashe min gwiwa ne na aikata aikin alkhairi,ni bana buqatar kudinka Da haka ta kashe masa gwiwa don bazaiso ta zama mara kirki ba ta sanadinsa ya sani idan har hakan ta faru yana da tagomashi a agun Allah,dole ba dan yaso ba ya bude wallet din ya bata passport din hadi da karanto mata numbobinsa ta kwafe tsaf bisa wayarta tayi serving,tun daga lokacin hotonsa shi ya zama abokinta da zarar ta kadaice shi take sawa a gaba tayi ta kallo,kyan Aliyyu na qayatar da salima ya tafi da imaninta 100% Takan bata lokaci tana gurin kiransa amma ba zai daga ba,ta jure hakan ba tayi zuciya ba tana ci gana da kiransa,yau da gobe tafi qarfin wasa har takai da idan ta kirashi sau goma zaoyi qoqari ya daga mata ko sau daya ne shima daga gaisuwa bai bari a wuce haka,an halicci zuciya abisa son mai kyautata mata to hakan yake don kuwa kulawa sosai salima ke nunawa aliyyun mutum ne dama da bai taba budurwa ba samun hakan yasa ta shiga cusa masa ra'a yinta sannu a hankali har ya minta da ita ya bada amannar zata zama abokiyar rayuwarsa Asalin salima 'yan katsina ne mahaifanta,yan boko ne na bugawa a jarida irin mutanen nan ne da ake cewa"yan boko aqida"wato ga karatun bokon ga kuma bin duk wasu aqidu nasu, bokon suke da gaske babu sirkin addini ko kada cikin mu'amalar rayuwarsu ta yau da gobe bokon kawai akasa agaba shine madubi,hakan yasa tun a nijeria salima ke alalace don babu kwaba balle hantara da zarar kin kai shekaru goma sha takwas a gidansu to kina da yancin yin komai da kika ga dama,iyayenta na da arziqi daidai gwargwado don su suka dau nauyin karatunta ta fita indian Mutum daya ne salima ta yarda da shi ta sallama masa jikinta a nijeria suke harkarsu duk da tana bawa wanda taga dama kanta yayi tabe tabensa don a cewarta ita babbar harka take,sai kuma zuwanta india ne wani abokin karatunta rahul,shima din tunda ta hadu da aliyyu tayi mishi fata fata sukayi handing over don kuwa tunda ta ga aliyyun tayi amanna ta samu kalar namijin da take so ya zama miji a gareta ya hada komai hundred percent Cikin lokaci qanqani salima ta dage a tada maganar aure don kuwa tsoron take kada ta rasa aliyyun saboda tana ganin yadda mata jinsin qabilu kala kala dake indian mazauna can yan asalin indian da kuma baqin haure ke kara kaina akansa abunda ya sauqaqa abun ma babu fara'a ma bisa fuskarsa ko yaushe tana daure ne tamau balle kice zaki kawo masa wargi Bai damu ba suka koma gida nijeria aka gama komai sannn ya dauko ta suka dawo indian saboda business dinsa ita kuma ta samu ta kammala karatunta,dole salima ta yakice duk wani abokin shashancinta saboda matsananciyar qauna da take ma aliyyun Ba qaramin tashin hankali aliyun ya shiga ba yadda ya sameta ba budurwa ba duk da bai san ya budurwar take ba hakanan tasha stitches duk don ta matse,yafi aqalla sama da wata abun ma dukansa amma kasancewar sa mutum mai tsananin kishi da baijin zai iya auren mace ya saketa wani ya aureta yasa ya qyaleta,bugu da qari tsantsar qauna da take masa tamkar ta fidda ranta ta bashi,yayi imanin idan ya rabu da ita mawuyaci ne taci gaba da rayuwa parfectly Cikakkiyar kulawa aliyyu ya dinga samu sosai daga farkon aurensu duk da ya fuskanci qalubale da dama na wasu ayyuka na cikin gida wanda ya zama dole kowacce *cikakkiyar mace* ta iya su,kama da girki zuwa tsaftace gida amma sai yayi haquri da hakan yake koya mata wasu abubuwan da niyyar idan sundawo gida nijeria zai turata makarantar koyon irin wadannan abubuwan Abu na farko da ya fara kawo babbar baraka a zamantakewarsu wanda shi ya zama sila kuma sanadiyyar barkewar alaqar dake tsakaninsu shine,wata uku da yin aurensu ta soma rashin lpy,tuni suka yiwa mumbai general hospital tsinke sabodancita take sosai ,ba bata lokaci likita ya fara aikinsa cikin dan taqaitaccen lokaci sakamako ya bayyana sun samu qaruwa Allah ya albarkaceta da samun juna biyu Ba qaramin tashi hankali da razana aliyyu ya tsinkaya ba kan fuskar salima shi da ya tsammaci ganin farinciki,tun acikin asibitin take kuka wi wi har suka iso gida,duk da ya kawo abubuwa da dama cikin ranta game da kukan da take sai dai ya hani zuciyarsa da yanke hukunci bisa zato da zargi,don ya tabbatar ya matsa mata da tambayar mekw faruwa? Bata yi qasa agwiwa ba kuwa budar bakinta tashin farko ta ce masa"gaskiya darling ban shirya haihuwa ba yanzu babu abinda ke cikinta banda wahala da tsofar da mutum,just shekarata ma nawa da zan fara shiga rayuwar raino da wahalar 'ya'ya?,am just 25 fa"ta qaraahe maganar idanunta na malalo da hawaye Da fari ua dauka rashin fahimta ne saboda boko da ya dabai baye rayuwarsu don haka sai ta ma bashi dariya ya murmusa idanunsa akanta yace"that's my salima,wannan tunanin naki fake ne it's not real,haihuwa ai ni'imace daga Allah wanda kudi ko mulki ko wata isa basu isa su baka ita ba,tsufa kuma ai lokacine,idan yazo babu abinda ke tareshi,bama haka ba idan kika ga haihuwa tasa mace tsufa ya danganta ko daga gareta ne rashin gyara ko kuma daga yanayin kulawar da take samu daga mijinta,ke kam baki da wannan matsalar ko daya,come on baby dont bother your self kinji,I promise I wil be with you cikin ko wanne irin yanayi" Wannan duk baiwa salima ba tun aliyyu na rarrashinta har ya gaji ya sanya mata idanu,daga qarahe ma ganin ya zuba mata idanu sai tayi tsammanin ko ya haqura ne gaba daya?,sai kuwa ta fito masa da aniyarta na son zub da cikin wai ko don ta samu taci gaba da yin karatunta cikin kwanciyar hankali da nutsuwa tunda tana final year dinta watanni kadan suka rage mata zata fuskanci exams A ranar taga bacin ran aliyyu irin wanda bata taba ganin irinsa ba,yayi mata kaca kaca ta inda ya shiga ba ta nan yake fita ba ya mata jan kunne mai zafi akan kada ma ta yarda koda mistake wani abu ya samu cikinsa bazai lamunta ba bare kuma intentionally,ta tsorata ainun amma duk da haka ta kafe ta turje akan bata ga abunda zai sata zam da cikin ba tunda bata so ai ba'a dole shi kuma yace zai mata dolen kuma zata gani,kamar ta haqura amma zugar qawaye na sake tunzurata,cikin rikici ta dinga rainon cikin ji take kamar tasa hannu ta fisgo abinda ke cikin ta jefar ta huta,wani takunkumi ya kafa mata ya hanata fita ko ina hakanan ya hanaduk wani mai zuwa zuwa gurinta,makaranta ma shike daukarta ya kaita ya kuma tsaya a bakin inda da zata dau lecture din har sai ta kammala ya daukota ya maidota gida ya kuma kulleta sannan ya fice sabgoginsa Da wannan rikici ta kammla karatunta yayi clearing din komai nasa ya dawo Nigeria shi da ita gaba daya sai dai idan wani abu ya kamashi na yaje indian sai ya tasata agaba suje tare su dawo tare don kada ma ya barta tsautsayi ya gifta tayi abinda ranta ke raua mata,don baijin idan ta aikata hakan zai iya qyaleta ko ya daga mata qafa, Ita kuwa ta samu sake rigima harda mara dalili yinta salima take dom dai taga duk ya dora burinsa kan cikin,ya zuba mata ido ne saboda albarkacin yaronshi da take dauke da shi gashi mai tausayi ne qwarai da gaske kan mace mai ciki,hakanan tsakiyar dare sai ta tashi ta zauna ta kuma taahi aliyyun suyi kwanan zaune ta kuma kwana tana rusa masa kuka da ihu ita wai cikin ya dameta ya hanata sakewa Cikin haka ne ranar wata juma'a aliyyubya fito a masallaci aka masa waya asibitin doctor sa'adah yazo salima ta haihu,yayi matiqar mamaki don kuwa cikin watansa takwas da sati biyu kuma lafiyar Allah ya fita ya barta a gidan babu wasu alamun naquda tare da ita don baccinta ma take shirga,baiyi qasa agwiwa ba ya isa asibitin cike da murna doki da koma mamaki,yana zuwa ya samu qarin bayanin zuwa tayi aka turo naqudar ta qarfin tsiya wai ta gaji da zaman cikin ajikinta don lafiyarta lau ta iso asibitin,yayi fada sosai don sunga doctor sa'adah bata nan ne da ko bakin salima zai cire don roqo bazata yi mata ba har sai da yarda da kuma izinin aliyyun Ransa yayi mummunan baci saidai yana yin tozali da santaleliyar baby girl din da Allah yayi masa kyautarsa sai farin ciki ya mamaye gurbin bacin ransa tuni yama mance da abunda ya faru,sak kamammin family dinsu tayo ya rungume yarinyar tsam tsam a qirjinsa qaunarta na mamaye jinin jikinsa,ya dinga kissing din yarinyar da tofeta da addu'o'in tsari kala kala,tuni gidansu ya cika da yan uwa mominsa farin ciki tamkar akan yarinyar ta fara jika,duk wani uatsina da salima keyi da daga kai ita da yam uwanta hakan bai dami yan uwan aliyyu ba domin su gadon arziqi ne ba taka shi sukayi suka haye ba rana tsaka,harkar girma kawai sukeyi Suna akayi na tserewa sa'a,yarinya tayi albarka sosai don daga salima jar aliyyin babu wanda bai ga hakan ba,khadijatu shine sunan da ya mominsa ta zaba mata don abba ya bawa zabi shi kuma yace ya bawa momin ta zabawa kishiyarta sunan da kanta tayi murmushi tace ta bata khadijatu tana fatan Allah yasa ta yi gadon hali irin na mai asalin sunan,salima dama wannan bai dameta ba ita dama ta rabu da cikin shine agabanta alaqaqai kamar yadda ta laqaba masa Aka gama wannann ta wuce salima ta sake qirqirar matsala ta biyu wadda ta tunzurashi ta koma jawo igiyar aurensu ta guntule Mrs muhammad ce👑 📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻 [10/16, 1:48 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WA YASAN GOBE?...* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *written by safiyya Abdullahi musa huguma* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *Part 2* 1⃣9⃣&2⃣0⃣ Yadda abun ya faru shine salima sam taqi shayar da iftihal,anty hauwa ita ta gani ta yiwa salima magana cikin nasiha da kuma fadakar da ita illolin dake tattere da qin shayar da yaro nonon uwa indai ba lalura ba mai qarfi wadda zata jawo hakan koda hakan ta faru wasu basu yarda da madarar suna kai dansu ne ga wata wadda suka amincewa halayenta ta shayar musu da yaro balle ita da lafiya lau ne babu wata lalura,qememe salima tayi da ranta taci gaba da dirkawa iftihal baiwar Allah madara ba tare da masaniyar aliyyu ba Ranar da lamarin ya faru sati biyu ne da yin haihuwar cikin yan suna wata ta sanar da ummi halin da ake ciki don haka ta aiko anty hauwan takanas da roqo da kuma lallashin salima tayi haquri ta shayar da iftihal don abun ya daga hankalin momin tace ko lafiya ce bata da ita tayi magana sai a a samo mata magani cikin tsiwa da rashin kunya salima tace"ita momin ce ta aiko ki?to ki gaya mata babu dan iskan da ya isa ya jawomin abinda zaisa jikina ya lalace lafiyatq qalau saidai tun farko na gayawa ubanta ban shirya haifarta bane,don da na samu dama da tuni tabi rariya ba zata ma zo duniyar ba bare azo ana min iyayin banza da wofi akan........... Bata qarasa ba taji saukar lafiyayyun mari hagu da dama na kumatunta,da sauri ya daga kai din taga wanda yayi mata irin wannan aika aikar,aliyyu ne tsaye bisa kansa cikin matsanancin fushi fuskarsa tayi jajur😡 abunka da fari huci kawai yake fitarwa kamar wani zaki ya dora da cewa"bansan baki da mutunci ba sai yau ashe ke 'yar iska ce ban sani ba? Mahaifiyata kike fadawa wadannan mugayen kalaman?.....to bari kiji salima.....👉har yau ba'a haifi yarinyar da zata ci mutuncin iyayena ba wallahi duk son da nake mata,yarinyata kuma daga kin bar bata madara indai ni ke aurenki" Cikin hasala ta miqe tana nuna kanta tace 👆🏼ni ka mara aliyyu?....ni ka mara?,to an fada din yarinya kuma wallahi ko sama da qasa zasu hadu ba zata sha min nono ba,ai kana da yan uwa mata kana iya basu ita su shayar maka ko ka samar mata wata uwar ko kuma ka maidata cikinka ka sake haifeta"ya harzuqa matuqa ya daga girarsa yana kallonta "oh haka kika ce! Indai kuwa haka ne baki da wani amfani" "to ba sai ka yiwa tufkar hanci ba"a zafafe ya gyada kai yace "ok,well kije na sake ki saki daya" Maganar tayi matuqar girgizata tayi zumbur ta miqe ta dangwarar da iftihal da da take riqe a hannunta tace"tafi nono fari ai" ta shige bedroom dinta,yarinyar tamkar kuwa tasan meke faruwa ta tsandare da kuka,ko waiwayo ta bata yi ba,anty hauwa tuni ta qame hannunta aka 🙊🙆🏻saboda sakin da aliyyun yayi Ta fito dauke da akwati tana shirin fita,sai lokacin anty hauwa ta samu bakin magana "kiyi haquri don Allah ki dauki yarinyar nan"ta juyo a fusace sannan tayi murmushin takaici ta dubi anty hauwa"ai burinku ya cika ko?kuma ina tsammanin kema macace akwai nono a qirjinki kamar nawa to kina iya bata naki"a fusace aliyyu ya sake tasowa da niyyar kai mata wani marin anty hauwa ta tare gabansa "a'ah aliyyu kada ka sake dole taji haushi its our fault dont beat her again mu lallabata ta dauki yarinyar dai"cikin harzuqa da tsawa wadda baisan yayi ba yace da anty hauwan"ni👆🏼 ni zan lallabata don ta dauki iftihal god forbid anty"ya fada yana kada kai"ko zata nemi hakan ba zata samu ba"bai san ya sake tura ma salima wani baqincikin ba da sauri ta ja akwatinta ta fice,a sanyaye anty hauwa ta juya ta dauki baiwar Allah iftihal dake nannade cikin showel tana ta tsanyara kuka kamar tasan abunda mamanta ke yi ,sanyata tayi a kafada tana jijjigata tana kallon aliyyu dake zaune saman kujera dafe da kansa idanunsa alumshe jijiyoyin kansa sun fito sunyi rada rada tasan alamun tsananin fushin aliyyu kenan tun yana yaro ,a hankali tana shafa bayanta har yarinyar ayi shiru da yake mai haquri ce bata da rigimako kadan matuqar ta qoshi Zaman sukayi tamkar na makoki na kusan minti talatin sanann tace"aliyyu tashi mu wuce gida dole su abba suji irin aika aikar da kayi,ya kada ki bayan ya bude idanunsa da suka koma ja ya kalleta"ban yi laifi ba wannan shine hukunci da yafi dacewa da ita,ni nasan me dame salima ta yimin bayan wannn tun alokacin ta cancan ci narabu da ita amma na daure"ya maida kasa kujera yana maida numfashi ya daga mata hannu alamun ta tafi kawai Ta girgiza ki tace "a'ah bazaiyi na qyaleka ki kadai ba kana cikin irin wannan mood din"ita tayi driving shi kuma ta bashi iftihal din ya riqe,ido sosai ya zuba yana kallon yarinyar tausayinta matuqa ke shigarsa yana tausaya mata na rashin dacen uwa da bata yiba ya rungumeta tsam tsam a qirjinsa cike da qaunarta Fa babu irin wanda momi bata yi ba tamkar ta ari bakin wasu,kamin abbansa ya dawo ya dora da nashi,ce masa auke ai haquri shine mafita ba saki ba,shi dai uffan bai ce ba don baijin koda salima ta dawo tofa ta rasa shi shi da 'yarsa har abada To kuma sai aka taki saa ko rashin saa zance ne?uncle abba me ya nuna dattako da kansa ya taka gidansu salima don yin bikonta,qara ra a gabansa abban ta ya nuna masa shifa ba ruwansa bazai tursasawa 'ya 'yansa ba don suna da 'yancin yin duk abinda suka ga ya dace da rayuwarsu,amma zai kira salima atambayeta idan zata koma to,da yake a cikin zafin kanta take a lokacin bata ji kunyar budar ido tace da uncle abba ba itafa ba zata koma ba"abban nat ya kalleshi yace"to kaji mai zaman tac3 bazata iya ba"abba bai sake tofa kanzil ba ya bashi hannu sukayi musabaha ya dawo gida Lamarin rayuwar gidan nasu yayi matuqar bawa uncle abba mamaki,rayuwar'yancin kai suke irin ta mai jan kunne?ba rayuwa ba irin ta addininmu wadda fiyayyen halitta ya koyar da mu ba?,wanna wane irin masifane da a yanzu muka qaqabawa kanmi?,bayan ya dawo ya sanar da momin yadda sukayi,ita kanta da ake mace abun ya daure mata kai amma kasancewarsu iyaye masu dattako da basu so dansu yayi saki sai ta nemi izini gun uncle abban akan ita ma zata je ko za'a dace"uncle abba bai hanata ba yadda mai akai da mahaifin salima exactly haka akayi da mahaifiyarta don aqidar duka iri guda ce Saidai ita an samu dan bambanci kasancewar salima tafara saukowa har ta fara kewar aliyun sai mamarta tace wa momi saidai aliyyun yazo da kansa,nan momi ta saka shi gaba akan lallai lallai ya shirya yaje,shi dai kullum yana binta ne da to don kuwa ya riga ya gama yankewa ransa cewq ko itace autar mata yq haqure mata don gaa daya ta qarasa ficewa fit daga ransa,bata da wani abu a yanzu da zata burgeshi da shi Ganin momi ta soma tsanantawa a al'amarin sai ya soma shirin komawa indiyarshi ba tare da sanin kowa ba bai so ba ba kuma a son ranshi ba don baiso yayi nisa da yarinyarshi sai da ya kammala ne suka sani,momin taso ta hana abba yayi mata magana aka ta tsagaita hakanan da Maganar dole sai salima ta dawo idan da rabo zaman bai qare ba zata dawo ne,aliyyu mai tsananin biyayya ne bashi da tarin kunne akan duk wani umarni da iyaensa suka bashi,yana dai da zurfin ciki ne da nauyin baki,tun yana yaro idan suk ce yayi abu ya kafe baiyi ba to yanada dalilinsa ne mai qwari wanda sai daga qarshe idan suka bincika sai suga lallai yana da gaskiya Momi ta gamsu da bayanin abban ta kuma yiwa aliyyun fatan alkhairi da samun dacewa,aliyyu ya bar nijeria 🛫cike da kewa da qaunar 'yar diyar tashi tsoka daya a miya khadijatul iftihal,ya tanadar mata duk wani abu da zata buqata daki guda ya ware mata yajibge mata komai hatta da ruwa da zata sha ya tanadar mata bai bari ya dorawa kowa wahalarta ba harda kayan banza ma da wofi wanda bata buqatarsa,hakanan ya bude mata account duk wata yana saka kudi a ciki yace da momin aje a cira ayi mata abinda tale da buqata,to kawai take cewa kamar yadda uncle abba ya umarceta don shi tuni ya karbe ragamar komai din kudin da aliyyun keta aikin turowa uncle abba yace abarshi cikin account din ta amfanesu idan ta mallaki hankalin kanta Wata shida kacal salima taji ajikinta qaunar aliyyu da yarinyarta tamkar zata zautata cikin begensu take kwana take tashi,yayin d iftihal ke cikin walwala da samun gamsashshiyar kulawa gata da soyayya ta qannen uba kakanni na gun uba da kuma dangainsa,tayi bulbul abinta madarar dai ita taci gaba da karba don itama taqi nonon kowa zakaran da Allah ya nufa da cara sai gashi cuta mai taba yaro bata taba samun yarinyar ba don ko haqori tashi sukayi suka ganta da shi ya soma fitowa,ga wayo a gunta gane mutane da kaifin basira Shekara daya da rabi salima ta kasa daurewa,ido ta rufe ta soma neman aliyyun,saidai ya riga ya toshe duk wata kafa da zata sada shi da ita,sai daga baya ta samu labarin ya koma india,ba bata lokaci tayi visa ta bishi don zamanta da aliyyu ta samu dukiya sosai kasancewarsa mai sakin hannu shi yasa hatta zaman gidansu take jin bai mata ba Acan din ma bata sameshi da wuri ba don ya canza gari ma gaba daya sun zauna a mumbai ne shi kuma ya koma new Delhi taci wuya ka su hadun saidai haduwar tasun mabata haifar mata da d'a mai ido ba,kaca kaca yayi mat irin wanda bata tsammani ba ya kuma jamata kunne da idan har ta sake suka kuma hada hanya sai ya wulaqantata,ta samshi qwarai idan ya fusata baida dadi iya kuma qurewa ta sani ta qureshin don haka bashiri ta tattara ta dawo nijeria ba tare da ta cimma nasara ba Aliyyu bai waiwayi nijeria ba sai bayn shekaru uku cike da nasarori da budi masu tarin yawa wadanda bai taba tsammatar samunsu ba,company nasa ya bude babba acan hadi da qulla harkokin kasuwanci kala daban daban da wasu manyan kamfanonin,yazoya taras salima naci gaba da bibiyar rayuwarsu shida yarsa taqi aure sam duk wadata tsaya da shi sai taga ba namiji bane ganinsa take kamar mace yar uwarta taqi sauraron kowa da komai,itace kira saqonni na email sms duk wata kafa da ta samu ya rabu da duk wasu layukansa saboda ita amma ya rasa yadda take samun sababbi,sunzo don a basu iftihal yafi sau hamsin tun yana india suke da muradin haka ya gaya masu su da iftihal saidai su ganota daga nesa don bata buqatarsu 🔱 🔱🔱🔱🔱🔱 *samira* 🔱🔱🔱🔱🔱🔱 Shekarunsa hudu da dawowa ya hadu da samira gun bikin abokin kasuwancinsa,tunda ta qyalla ido a kansa ta qwallafa ranta,ta rasa ta inda zata samu shiga domin kuwa baida walwala ko sakin fuska shi yasa take fargabar tunkararsa,da yake tare yake ta hidimar bikin abokin nasa da iftihal dinsata lura da yadda yake ta nan nan da yarinyar ta samu kuma information kanncewa 'yarsa ve da yake tsananin qauna sai itama ta jata ajiki sosai tattali take nuna mata kamar babu gobe,shikam mai son wanda ke son iftihal dinsa ne don haka ya sakar ma samira duk da ya ja jikinsa sosai da fari saboda yakan tuna yadda ta kasance masa a baya tsakaninsa da salima Itama tazo akan gaba don lokacinne tsananin ya sake aure ya masa yawa a gida ahi kuma a zahitin gaskiya a wannan lokacin bai da time na duba mace,ganin ya samu maison iftihal dinsa yasa ya amince daga qarahe ne ma momi ke masa albishir din itafa ba zata bashi iftihal ba donnta riga tazo kenan,ba yadda ya iya duk da son da yake wa yarinyar tasa Sai da salima ta gasu sosai fiye da tsammaninta wanda tadinga jelen kamun qafa da momi da abban da a baya ta watsawa qasa a ido kullum tana cikin gidantana magiya sannan ta samu dawowa gidanta,gidan da ta tarar ya kubce mata har wasu biyun sun samu mazauni cikinsa,ya ta iya da ranta son da take masa yasa bata ji wani abu ba tayi zamanta duk da a baya tana daga cikin matan dake iqirarin basu ba kishiya don ba zasu iya zama tare da ita ba 🔱🔱🔱🔱🔱🔱 *_dawowa labari_* 🔱🔱🔱🔱🔱🔱 Washegari tun qarfe tara fadila ke shirin fita suna,tayi wanka ta shirya tsaf cikin shadda dinkin doguwar riga ne yasha aiki daga sama har qasa butter colour ta debi wadanda zata sauya a can kala biyu ne da tayi musu anko ita da faridan zasu sa tare ta shirya iftihal cikin itama doguwar rigar yan kanti wadda ajiya ta bada aka siyo mata hade take da takalminta da ribbons dinta red ce in and top ta tsaya mata iya qauri takalmin boot ne na yara fari qal tayi ma gashin yarinyar ado da fararen ribbon tayi kayu matuqa kasancewar yarinuar mai yalwar gashi mai tsawo da santsi Hat ta tada motarta iftihal ta hango abban nata ta balle murfin motar ta fice aguje,bayan ta duqa ta gaidashi ya dauketa yana wulla ta a sama shiko nauyi bata yi masa"cewar fadila cikin ranta tana satar kallonsu,tana ganin iftihal na nuno mishi ita,ya juyo ya kalleta suka hada ido tayi maza ta sunkui da kai don kada qwayar idanunsu ta hadu ya saka mata dafin da ya saba jefa maya cikin zuciyarta na qarin qaunarsa,"verry neat ya fada sannan ya dauke kai"iftihal ta leqa fuskarsa "daddy munyi kyau kuwa"yayi kissing kumatunta yace kinyi kyau sosai my dear"tadan bata fuska tace "anty na fa?"yayi yar qaramar murmushi yace "both of you""thank you daddy"ya sauketa bayan ya sake kissing dinta tana daga masa hannu ta zura aguje ta dawo cikin motar tana dariya Mrs muhammad ce👑😘 📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻 [10/16, 1:50 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WA YASAN GOBE?..* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *written by safiyya Abdullahi musa huguma* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *part 2* 2⃣1⃣&2⃣2⃣ Fadila tayi murmushi sannan ta tada mota iftihal tace "anty Abba yace munyi kyau wai na zama 'yar gatan anty ni 'yar gatanki ce wai anty?"ta shafa kanta da daya hannun nata tana murmushi tace"iftihal ke 'yar gata na ce mana" Minti arba'in suka qarasa gidan da yake safiya ce babu yawaitar mutane sai 'yan uwa na jiki sosai,su hajja gana(kakarsu ta gun uba) umma a'i anty hafiza rumaisa da sauran 'yan uwa na nesa da na kusa,Fadila ta fada jikin hajja gana tana cewa bari na more cinyar 'yar tsohuwa" hajja gana ta sa dariya da yake sunfi shiri da Fadila fiye da farida"more abinki kafin kema Allah ya kawo miki masu more taki"murmushi fadilan tayi sannan suka soma gaisawa da yan uwan hajjar na tambayarta mai gidan tace lpy lau yana ma gaisheki Kafin azahar gidan ya tumbatsa da jama'a,ko ta ina,bayan azahar kuma da kadan sai ga family din aliyyu momi ce kawai banda ita,cikin bedroom din farida sukayi zamansu anata karbar baqi Rabi'ah ta kalli fadila lokacin da take canza kaya su anty hauwa na sallah tace "ni dai anty idan kuka tafi chinan nan qana nan kaya kawai nike son tsarabata"fadila ta dago ta dubeta bayan ta gama zuge zif din rigarta tace"wace china kuma rabi'ah"dariya rabi'an tayi"kai anty ko baki son asan zaki ne?"cikin rashin fahimta take dubanta tana qoqarin daura dankwalinta"wai wa yace miki zani china rabi'ah?"ta sake qyalqyalewa da dariya tace"tun last week fa yaya aliyyu ya gaya ma momi an gama ginin sabon company dinsa da zai bude zai wuce china cikin satin nan ke da shi,shekaran jiya kuma sai ga shi ma da visa dinku a hannu ta fito jibi zaku tashi da daddare amma anty kice baki sani ba?😀" A badini zancen yayi matuqar kidima fadila ya daketa sosai amma sai ta dake don kada ta bada satar amsa ta qago murmushin yaqe"kinsan halin yayanku akwai lafiyar miskilanci dazun dai yake cemin idan na dawo zai min wani albishir to ina tsammanin shine"sumayya da a lokacin ta sallame sallarta tace "har Allah Allah nake na idar kinga haukan da salima ta dinga yi wai da ita za'a tafi?"su sumayya suka kwashe da dariya rabi'ah tace"qara fa ta kawo gun momi sai gata tayi tsuru tsuru da ya aliyyu yake fadin babu abinda suka iya ba inda zai je da su su zamar masa nauyi"sumayya ta dora "qarshe ma momi da yake zayyano mata matsalarsu kunya ce ta isheta ta bar falon ba shiri tace suje gida su shirya kansu mu dai bamusan ya aka qare ba bata sake tada zancen ba ma"anty hauwa tace"ku kuma gaku sarakan gulma ba,kwaci qaniyarku da ya kamaku kuna labe ai" Duka wunin ranar bunda ke cin zuciyar fadila kenan zancan tafiyar yayi masifar daga mata hankali,sai ta rasa nutsuwarta gaba daya,lokaci lokaci qwalla kan taru a idonta ta faki idon mutane ta matse ta,gaba daya sai kuzarinta ya ragu,Allah Allah take su kebe da farida,bata tsammani alkhairi aliyyu ke nufi da tafiyarsa da ita,nufinsa ma fa kenan gaba daya tabar aikinta da take masifar so ta kuma fara jin dadinsa yake kuma debe mata kewa?sam ba zata iya wannan tsari nasa ba Sai bayan sallar isha'i ta samu nasarar tadda farida cikin bedroom dinta zaune gefan gado tana canzawa baby da taci sunan maman mubarak wato(aisha humaira)pampers ta zauna itama a gefan gadon tana duban pampers din da faridan me sawa humairar ,da fara'a farida ta juyo a fuskarta tana duban fadila zata dan tsokaneta sai fara'ar ta janye sakamakon qwalla da ta gani tana bin kumatun fadila tayi hanzarin sauke humaira da ta aza akafadarta tana cewa"lafiya sister?"tamkar ma ta tunzurata sai hawayen suka dadu Tafin hannunta take sawa tana share su da nufin tsaidasu saidai turereniyar fitowa ma suke abinsu,sai da farida tasa hannayenta ta kamo hannayen fadilan ta sa cikin nata sannan ta sake tambayarta,da qyar kuma cikin muryar kuka fadila ta bude bakinta tace"yanzu tsakani da Allah abinda aliyyu kemin yana kyautawa?"tayi tambayar wasu hawayen sabbi na shirin sake zubowa,farida ta sake fuskantarta a dan kidime tace"meke faruwa sister me ya miki?"ta girgiza kanta cike da damuwa"wai china zai dauke ni mu tafi har kuma na tsawon wata hudu Sai farida ta sake ta hadi da sakin dariya tana tafa hannu"🤔yanzu sister fadila wannan abun farincikin kikewa kuka kamar wata teddy?"fadila ta katseta"ba zaki fahimta ba farida kwata kwata wata na nawa da soma aikina?"farida ta sake dubanta"😏aikin banza sister fadila,ga inda zaki samu aljannarki kike zancan wani aiki"sake girgiza kai fadila tayi"still farida baki fahimceni ba,zan gaya miki abunda babu wanda yasan yana faruwa sai ke,har yau sister aliyyu bai sona,aliyyu bai qauna ta kalma mai dadi bata taba hada ni da shi ba kallon arziqi bai taba shiga tsakanin mu ba amfani na daya agunsa shara da girke girke tamakar wata 'yar aikinsa tun muna kusa da iyaye kenan tun muna qasarmu kena ina ga nabishi can wata uwa duniya mai kuma kike zaton zai faru a ni?" Ga mamakin fadila sai taga farida tayi murmushi mai kaa da dariya sai fadila ta saki baki tana binta da kallo tan tsammanin farida bata damu da halin da zata tsinci kanta ba kenan ko yaya?,sai da ta gama dariyarta sannan tace"☺👏🏻bravo! bravo! bravo!,wallahi aliyyu yayi miki gata ba da qarami ba"zaro ido fadilan tayi har ya mamakin bai sake ta ba😳,ganin haka yasa farida ta kama kafadar fadila ta sake juyowa da ita ta fuskanceta sosai,ganin yadda fadilan ta tsure sai ya sake bawa farida dariya daga baya kuma sai ta dawo serious dinta ganin kallon sakarcin da fadila ke mata,ta kuma kama hannunta sannan tace"ni na gano abinda qila ke baki gano ba,kuma ba zaki gano shi ba yanzu,sister duk abin ya aliyyu koya nuna ko kada ya nuna ko ya yarda ko kada ya yarda kina da muhammanci da wani tasiri a rayuwarsa komai qanqantarsa koda kuwa ya qaryata hakan da bakinsa,sister a iya hangena da tunani na na fuskanci cewa don kada ya aliyyu yayi missing girkinki ne baya so yayi nesa da abincinki wanda yasan zaiyi wuya ya samu kamarsa nima shaida ce"ta qarashe maganar cikin sigar tsokana wadda ta zame mata jiki Ta nuna fadila da yatsa 👉�sannan ta dora ke zaki canza wannan manufar ke zaki sauyata da kanki,ke zaki canza wa aliyyu wannan lafazin nasa na bazai soki ba har abada ki qaryata lafazin nasa ta hanyar nuna masa ba wanda *_yasan gobe_* sai Allah,sosai ta gamsu da maganar farida dari bisa dari kaso sittin cikin dari na damuwarta ya tafi,ta jinjina kai hadi da sakin ajiyar zuciya sannan tace"batun aikina fa sister?" "So easy"inji farida ta gada tana murmushi😊"k8na iya daukar excuse a gurinsu ki musu bayani tafiyar gaggawa ce ta sameki zuwa china zaki ajiye aiki amma da manufar zaki je course ne na wata hudu,idan hakan bai samu ba su barki a matsayin wakiliuarsu ta qasar china ta tsawon wata hudu" "great sister!"fadila ta fada cike da farinciki,tabbas dan uwa na gari dadi ne da ahi gashi xikin 'yan mintina qalilan ta warware mata damuwarta,ta rungume faridan tana cewa"thank you sister ya barmu tare ya raya mana humaira"tace "amin Allah yasa kema ki samo mana tsarabar dan china nan da wata tara ko goma mu dauki sabon baby " dariya sosai ta bawa fadila tana jinta ne kawai Sanda ta dawo gida yana zaune cikin balcony dinsa,tayi maza ta dauke kai gami da qara sauri don ta shige shi ⚜⚜⚜⚜⚜⚜ Washegari qarfe 6:40 pm ta dawo daga aiki sun gama settling komai da managing director na express da freedom sai damuwarta ta sake raguwa qwarai da gaske,tana toilet din falo tana wanka taji moysi kadan kadan a falonta,da sauri ta kammala tana son taga waye don a bude tabar bangaren nata,kacibus sukayi da shi tsaye yake tsakiyar falon yana sanye da kufta dark coffee wadda tasha aikin sarauta sai hukarsa baqa abinka da fari sai yayi matuqar kyau kyansa da jaskensa ya sake fitowa shigar ta amshe shi sosai fadila ta lumshe idonta tana jin wani abu na zagaya jikinta"ki shirya na kaiki gida ki masu sallama,gobe zamu bi jirgin yamma insha allah zamu wuce china"duk maganar nan da yake idonsa na kan wayarsa dake hannun hagunsa damansa kuma cup ne cike da maltina mai sanyi🍺,ta dan langabe kai kamar bata ji mai yace din ba"ina zamu je?""kaiki zanyi na siyar"ya fada yana ci gaba da danne dannensa ta faki idonsa ta manna masa harar ta zagayeshi ta wuce zuwa bedroom A sanyaye ta kammala shirinta cikin atamfa dinkin riga da zan8 simple style hakanan fadila take bata fiya son abimda ya cika ado da yawa ko daukan hankalin jama'a ba yadda take bata da hayaniua haka dabi'unta suke saidai idan ta so,ta lullube kanta da wadataccen mayafi kalar kayan,ta jawo locker dintabta debo kudaden da suke ciki ire iren kudaden da aliyyun ke basu ne duk qarashen wata da kuma na cefane acewarsa tunda komai suna da shi a ajjiye hatta magi ba zasu buqata ba ta watsa su cikin jakar sannan ta rataya ta ta fito,yana zaune a mazaunin driver tasan bata isa ta shiga baya ba ko ya shiga zai maidoto ne gaba don haka ta bude gaban ta zauna,yadan kalleta hadi da dauke kai ya daga glassan motar gaba daya samà ya rufe su ruf hadi da kunna a.c,wani irin tuqi yake slowly tamkar baza'aje ba tayi tsammani zaiyi irin tuqin nan nasa mai gudun tsiya,a hankali suke ratsa titi nan har suka qaraso cikin anguwarsu fadila Muje zuwa masu karatu🚶🏻🚶🏻🚶🏻🚶🏻 Mrs muhammad ce👑 📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻 [10/16, 1:50 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WA YASAN GOBE?...* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *written by safiyya Abdullahi musa huguma* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *part 2* 2⃣3⃣&2⃣4⃣ A qofar gidansu yayi parking,bata ce masa komai ba kamar yadda bai tsinka mata ba,ta bude murfin motar ta nufi bakin get din gidan cikin doki ta dan tsaya suka gaisa da malam mai bude masu qofa idan zasu shige da motarsu Parlour din babu kowa sai qamshin fresher da ya gauraye da na girki ,murmushi fadilan tayi kai tsaye ta nufi kitchen cikin zuciyarta tana cewa"ummi na bakya tsufa kullum gida kamar na budurwa" (haka haj amina take ma'abociyar tsafta ce da gayu,don bata yarda wai don tana da manyan yara harda jikoki ta zauna haka ba,baka raba qafarta da hannunta da jan lalle mai ado irin na yanzun wanda akeyi,hakanan kullum kalolin girkinta daban ne masu dannkaren dadi hakan ne yasa yaranta sukayi gadonta suma,tun aurensu ita da alhj abbas koda wasa bai taba tunanin qaro aure ba donba cewarsa ta isheshi duk dashi qarin aure qaddara ce rubutacciya idan Allah ya qaddaro maka sai kayi Muhammad ta tarar ciki riqe da babban spoon na qarfe yana ta faman juya fried rice,dariyar da fadila ta tuntsure da ita ita ta saka shi juyowa don bai ankara da shigowarta ba sai lokacin,ya saki murmushi yace"anty fadila yaushe kika zo?" Ta kama baki"🤔ina zaka san na shigo ka taqarqare kana ta jagwal gwalawa ummi abinci,wai yaushe ma ka fara shiga kitchen?"ya saki spoon dinnyana share zufa a goshinsa"😊 ni wallahi ma gwara da Allah ya kawomin dauki ,please anty karbi girkin nan,haka yanzu ummi kemin ko ta daina sona ne ma oho?,amma don Allah anty fadila ina ni ina wani kitchen?,wai gwara na iya tunda ku kun tafi saura ni da ita kawai a gidan"dariya fadila ta sake saki ,ta qaraso kan girkin tana gyara wasu abubuwa sai da ta hada komai ta rufe ta rage mata wuta don ta turara sannan ta tambayeshi ya haye saman freezer yayi zamansa"ina ummi" "tana gun Abba yanzu ya dawo daga kasuwa ne amma tunda an fara kiran sallah yanzu zaki gansu" Yana rufe baki kuwa saiga dariyarsu cikin falo,da hannu Muhammad yayi mata nuni da falon cikin salin gulma,dariya ma ya bata ta miqe da sauri ta isa falon,ita da abban ne kuwa yana tsaye riqe da abun sallah ummin kuma na dauke da hularsa,da murmushi suke kallonta ta durqusa ta gaida su abban na tambayarta yanzu take tafe?,ta gyada kai yace masha Allah ya mai gidan?,tace abba tare muke yana waje,"ashshsha banda abin fadila shima ai gidansu ne amma don sakarci kika barshi a waje "ummi tayi saurin qwalawa Muhammad kira tace ya zo ya shiga da shi,abba yace barshi naje na sameshi in yaso idan mun idar da salla sai mi shigo tare,a shirya mana abinci kafin mu shigo din Ummin ta dan rusuna tana miqa masa hularsa tace"insha Allah abban Muhammad a dawo lafiya"ya karba yana dora ta a kansa yace "Allah yasa Allah yayi miki albarka" cikin dariya yaran suka taya ta amsawa da amin Sai da fadila ta taya ummin suka shirya komai kan dining sannan suka tafi yin sallah ummi ta ahige dakinta fadila ma tsohon nata dakin ta bude ta shiga,bin dakin tayi da kallo komai yana nan kamar yadda yake,dan fridge dinta na boye ice cream 'yar kwanar da take ibadunta,inda take boye kanta idan zatayi kukan Aliyyu,sai komai yake dawo mata"Allah sarki" ta fada a fili tana shafa filonta da take cusa kanta a qasansa ,qwalla ta dan taran mata a ido ta sa yatsanta ta dauketa,toilet ta tura ta shiga ta daura alwala ta dawo inda ta saba yin sallarta tayi,bayan ta idar ta duba kan mirror dinta powder ce kawai akai ita ta dauka ta sake gyara fuskarta sannn ta mutstsika turare ya sauka qasan Muhammad ne kawai zaune kan table din yana buga game a wayarsa ta zauna kusa da shi hadi sa dan dukan kafadarsa,ya dago ya dubeta yana murmushi, "ka shiga aji nawa ne har ummi ta yarda aka baka waya,cikin dariya yace "haba anty nafa zama senior ina s.s one fa,kuma ma yanzu nine babba a gidan nan"dariya ya bata sosai tana cikin darawar ne ummi ta fito,tuni har ta yi wanka ta canza shiga tayi kyau duk da ba make up take yi ba,fadila na shirin tsokanarta tace tayi kyau sallamar abba da ta aliyyu ta karade falon wadda ta yake hirar da suka so farawa Abban ne a gaba aliyyu na biye da shi har suka qaraso dining space din abba ya fara cewa da aliyyu bismillah kai tsaye taga yaja kujerar dake kusa da ita ya zauna sai tayi duru duru har rudewarta taso ta fito,ji tayi ya take mata qafa ta danji zafi ta dago kai suka hada ido yayi mata alama da ido na ta nutsu,sannan ya duqar da kansa ya gaida ummi cikin girmamawa,ita kuma ta amsa masa cikin kulawa tana tambayarsa mutanen gidan Fadila ita tayi serving kowa banda ummi don tasan ba zata ci ba,tazo kan aliyyu sai ya rasa mai zata zuba masa idonta na kan warmer tace "mai zaka ci?" "Zuba min duk abinda zaki ci" ya fada abunsa tamkar ba shi yayi maganarba,da sauri ta dago kai ta kalleshi saboda wata kunya da ya bata amma sai taga shi ko ajikinsa,ta saci kallonsu ummi sai taga hirar su ma suke da abba kamar basu san da su agun ba,sai kawai ya zuba masa fried rice da farfesun naman kaza mai yawa tana son qureshi taga zai cin? Sai kuwa ya shayar da ita mamaki don abincinsa yake ci hankli kwance duk da baici da wani yawa ba yafi shan lemo,bayan sun kammala ita ta kwashe kayan ta kaisu kitchen ta hada ta wankesu kamar yadda ta saba tanayiwa ummin tun kafin tayi aure,tana aikin cikin ranta tana gulmar aliyyu bai da kunya Saman kujera ta tadda su ta parlour ta samu gefan umminta ta rakube,aliyyu ne ya dora kan maganar da sukeyi da abban "sallama mukazo yi muku abba saboda gobe insha Allah zamu wuce china" abban yace "zancan bude kamfanin ne ya taso kenan munyi maganar da abban naku ai wancan watan yake gayamin an dan samu tasgaro ne da tuni cikin wannan watan company n ya fara aiki" aliyyu ya gayada kai yace "eh abba insha Allah wanna karon za'a kammala komai a budeshi daman cike ciken takaddu ne na yarjejeniya tsakani na da gwamnatin qasar ya kawo tsaiko amma yanzun al'a muran saun daidaita Mrs Muhammad ce 👑 📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻 1:41 pm 29/8/2016 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WA YASAN GOBE?..* 2⃣5⃣&2⃣6⃣ Abban ya jinjina kai yana cewa "kasan qasa ce mai tsari da doka ba irin namu qasaahen ba da sai dai muce inna lillahi wa 'inna ilaihi raji'un,Allahbya taimaka ali ya kuma yi jagora yasa a budeshi a sa'a,Allah yayi ma jagora a dukkanin lamuranka"ummi na amsawa da amin yayin da shima yayi qasa da kansa yana cewa "ameen ameen abba na gode Allah ya qara girma" yana shirin miqewa yasa hannu cikin aljihun kuftanshi na riga ya zaro turare yan ubansu designers ya ajjiue wa abban,albarka yasa masa tare suka qarasa miqewa abban zai masa tattaki kasancewar alhj abbas mutum mai sauqin kai ba ruwansa da wai shi mai shekarune babba ne kowa nasa ne Sai lokacin fadila ta janye idanunta daga kan aliyyu kallonsa tayi sosai don bata taba ganin sa yayi doguwar magana irin haka ba,yanayin yadda yake maganar cike da girmamawa sai ya sake burgeta ta sake lafewa jikin ummin tana saukar da ajiyar zuciya,ummin ta kalleta sanda suka gama ficewa "au sake ma wani rabewa kike ajikina ke da ake jiranki?" Dama mai neman kuka ne aka jefe shi da kashin awaki sai kuwa ta saki kuka,ummin ta saki baki tana kallonta "wai wannan wane irin sakarci ne ko wata matsala kike da ita?" Kai fadilan ta girgiza,ance tsakanin d'a da uwa sai Allah hakanan sai tausayin gadilan ya kama ummin don yasan duk mace kimai jin dadinki baki rasa matsala ta zamantakewar aure,a da rance take mata nasiha hadi da lallashi Ganin hankalin ummin ya tashi sai tace cikin son kawar da hankalin ummi daga tunanin ko tana da wata matsala tunda tasan halin iyaye yanzu sai ta fita shiga damuwa"ummi bana son na barku ne har wata hudu" ta saku ajiyar zuciya tana godewa Allah "idan banda quruciya irin taki fadila ko kina nan din ma basai ki kusa wata biyu ma baki gan mu ba ummm.....kiyi addu'a kinji Allah ya kaiku lpy ya dawo da ku lafiya kawai" tace amin tana share hawayen cikin dakiya Ta zuge zif din jakarta ta fito da kudaden nan ta dorasu cinyar ummin,ummin ta kalli kudin sannan ta dubeta "wannan fa na meye?" "Naki ne ke da abba" "ina kika samo su fadila?yaushe kwata kwat kika soma aikin? Ina fatan ba roqonsa kike ba dai ko?", ta girgiza kai "a'ah ummi shi yake bamu kullum idan zai fita" ta dauke kudin ta ajjiye a gefe tana cewa "za'a dai juya miki zan bawa abbanki ko yayanki zasu san inda zasu sa miki su" ta langabar da kai tace "don allah ummi to ko dan wani abu 👌🏼 ne ki cira aciki ke da abban ku samin albarka" ta bita da "to naji" Idonta fal da hawaye zuciyarta a raunane ta fito ,suna tsaye jikin motar aliyun ta qaraso ta tsugunna har qasa idanunta rau rau muryarta na rawa tana yiwa abban sallama "to fadila Allah yayi muku albarka ya kaiku lafiya ya dawo da ku lafiya,ki zauna lafiya agidanki bana son fitina kada na ji kada na gani" tuni kukan ya qwace mata "insha Allahu abba"kasa tashi tayi har sai da abban ya daga ta da kansa,aliyyun ya zuba musu ido wani abu yaji ya taba ransa shi ya bude mata motar Abban ya sata ciki da kansa,aliyun ya rufe qofar sukayi sallama da abba ya zagaya ya shiga gun zamansa ya tada motar Shiru cikin motar sai sautin kukanta danke tashi kadan kadan hadi da sheshsheqa,burki taji yaja bayan ya gangara gefan tati ya kashe motar sannan ya dan kwantar da kujerar da yake kai din ya kwanta rigingine idanunsa alumshe yana sauraran sautin kukan,sai da suka kusan kwashe awa guda ahaka lokacin tuni har kukan nata ya tsagaita,ya miqe a kasalance ya gyara zaman kujerar baice uffan ba ya tada motar suka wuce Cikin daren bata kwanta ba sai da ta hada duk abinda take da buqata cikin babbar trolly dinta sannan ta kwanta zuciyarta fal da saqe saqe kala kala ⚜⚜⚜⚜⚜⚜ Cike da kasala take janye da akwatin nata har ta iso bakin motar qirar sienna dake fake a harabar gidan,yadine a jikinta mai sulbi blue 🔷 tayi rolling da red din mayafi🔴🔵,sosai rigar ta bude daga qasa takalminta red ne hill sosai 👠,motar na bude duk suna ciki nasiru na mazaunin driver aliyu na kusa da shi sai salima dake sit din can baya bisa dukkan alamu ga fuskarta nan ta sha kuka,fuskar samira ba yabo ba fallasa tana sit din tsakiya,yayin da fadila ta zauna a sit din farko nasiru ya karbi troly din nata ya sanya a baya Cikin hanzari nasiru ke ruqin aliyyu ya sake duba gaogonsa yace "nasiru qara sauri zamu iya missing flight" ya sake qarawa motar gudu don bin umarnin ogansa Ba dadewa suka isa aminu kano international airport nasiru ya ajjiye motar inda aka tanada don ajiyar motoci,dukkaninsu suka fito daidai lokacin da airport din ta karade da sanarwa neman masu tashi a jirgin ethopian airline,hakan ya tabbatar ma da aliyu sun kusa makarar kam,tuni nasiru ya ciro musu jakankunansu,ya dubi samira da salima da fuska take adinke musamman salima da takejin kamar ta dora hannu aka ta zunduma ihu,"sai na dawo" yace kamar mai jira salima ta fashe da kuka ta taho a guje ta fada jikinsa,ya saki dan qaramin murmushi hadi da sa tafin hannunsa yana dan bubbuga bayanta alamar rarrashi,ya miqawa samira daya hannun alamar ta taho,dauke kai tayi tana turo baki zuciyarta babu wani takaici sosai Idan ta tuna da maqudan kudaden daya barwa kowaccensu tasan zasu sha bushasha don ma yayi misu gqrgadi da jan kunnen akan fita"sai ka dawo"tace kawai,ya dan janye salima daga jikinsa sukayi sallama da nasiru,ya wuve fadila ta rufa masa baya saluma ta bita da harara kamar ta fincikota,batasan itama fama take da fargabar bin aliyyun ba Reception suka wuce suka qarasa departure ta farko suka shiga layin screening,aka kammala da su aka basu boarding pass suka qara gaba,immigration suka sake duba visa dinsu suka buga musu stamp suka shiga dan dakin jiran jirgi,mintina qalilan jirgi yayi ready suka bi layin shiga jirgi tana gabansa yana tsaye a bayanta Mrs muhammad ce😘 📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻 [10/16, 1:51 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WA YASAN GOBE?...* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *written by safiyya Abdullahi musa huguma* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *part 2* 2⃣7⃣&2⃣8⃣ 25 and 26 ne number din sit din nasu don haka sune maqotan junansu,aliyyu ya daga yar trolly din da aka barsu suka shigo da ita saboda kilo din ba wani mai yawa bane ya sanyata a inda mayafiyan ke ajjiye jakankunan nasu,yan kallo fadila nata kiciniyar sanya tata saboda ta dan yi mata nauyi,sai da ta soma gajiya sannan ya sa hannu ya janyeta ya fada kan kujerarta ya daga trolly din tata ya sanya mata ya koma sit dinsa ya zauna yana gyara zaman suit din jikinsa Kowa ya zauna a mazauninsu,fadila na bakin window ta zubawa filin airport din ido tana fargabar yadda jirgin zai Lula da su sararin subhana duk da yawansu kasancewar wannan shine shigarta jirgi na farko a arayuwarta A hankali aka zare matattakalar aka maida qofar jirgin aka rufe bayan sun gama duk wasu yan tsarabe tsarabensu suka bada sanarwar daura belt,fadila ta jawo belt din saidai bata san yadda zata sata ba,tana satar kallon aliyyu ta gefan ido yana daura tasa,ya kammala ya fito sa laptop dinsa ya dora bisa cinyarsa A hanakali jirgin ya soma qugi hadi da shawagi a doron qasa na kimanin minti goma sha biyar sannan ya yunqura don rabuwa daa doron qasa,fadila ta runtse idonta saboda wani tsoro da ya kamata,ta qanqame belt din dake hannunta wadda ta kasa daurawa jin jirgin na niyyar dawowa qasa ya tarwatse da su😂😂😜😜 lol har naga idon masu karatu aliyyu salim mai tama da fadila zasu mutu😂😂 Ta qanqame belt din dake hannunta jin tana niyyar subucewa daga kan sit din ta,cikin zafin nama aliyyu ya kareta da hannunsa sannan ya amshe belt din ya zagayeta da hannayensa ya daura mata hadi da cewa "silly girl" ya gama ya koma kan danne dannen da yake kan laptop abinsa ba tare da ya sake dubanta ba,a dan sace ta harareshi gami da jan dan siririn tsaki ,ya juyo da sauri don tsakin kunnuwansa sukaji kamar tayin da azama ta dauke kanta ta maida window Allah ya taimaketa basu hada ido ba sai ta waske Tafiya ce ta awa hudu ta saukesu a *ethopia* don musayar jirgi cikin babban birnin na *ethopia* wato *addis ababa*,ba kwana zasuyi ba amma saida aliyyu ya kama one room apartment cikin hotel din dake kusa da airport din,tamakar kazar da qwai ya fashewa a ciki ta nemi gefan kujera qwaya daya dake cikin dakin ta zauna a takure,sallar magariba da isha'in da bata yi bane ke damunta amma duk a takure take bare tayi azamar tashi Tana kallo ya dora jakarsa💼 kan gado ya tube takalminsa 👞 da socks dinsa ya shige toilet,motsin ruwan da ta ji yasa ta raya alwala yakeyi Kusan minti arba'in ya fito sanye da rigar towel mai budadden qirji👘,kallo daya ta masa ta dauke kai tsigar jikinta na tashi 😣,gashine kwance luf a qirjinsa baqi sidik tamakar wanda ake sawa relaxer kamar yadda na hannayensa da qafafunsa suka kwanta saboda ruwan da suka sha,ta sake runtse ido gabanta na dan faduwa💔 da alamu ma shi ko ajikinsa don goge sumar kansa yake da dan qaramin towel dake riqe a hannunsa Ganin ya soma kunce dan zaren da ya taimaka wa rigar ta rufe jikinsa ya sata yin azamar afkawa toilet,ta dade numfashinta na kaiwa da kawowa wani abu na mata yawo a jiki sannan ta iya daura alwalar ta fito,ta cimmasa tuni ya har ya tayar da tasa ta koma gefe ta kalli inda taga ya kalla ta tayar da alama nan ne alqibla har ta kammala tata ta zauna tana lazumi lokaci lokaci tana satar kallonsa har ya sallame Shirye yake a yanzun cikin jacket masu kalar green da black sabanin dazu da yake sanye da suit baqaqe kullum aliyyu cikin sa kaya yake sabanin wadanda ta sanshi da su,kusan ma zata ce bata taba ganinsa yayi maimaice ba,yana zaune saman qafafunsa ya kammala addu'arsa ya shafa ya miqe tayi saurin yin qasa da kanta don kada su hada ido tana yiwa Allah tasbihi saboda kyawun da taga yayi mata har ya juya ya fice Fitarsa ba dadewa daya daga cikin ma'aikatan hotel din yayi knocking ya shigo mata da abinci fried spaghetti ce da roosted chicken sai drink da ruwan gora mai sanyi duk da cewa akwai su cikin fridge dake dakin,babu abijda ta iya ci sai lemon da ta sha Saman kujera ta nade ta janyo wayarta ta kunnata wadda tun shigarsu jirgi ta kashe,babu service da ya hau saboda ya fita daga inda yake da amfani ,ta danna power off ta kashe don bata da wani amfani ta maida kanta ta kwantar a hannun kujerar A hanzarce ya shigo ya dauki jakarsa 💼 ya juya yana cewa "let's go"ta miqe ita ma ta dauki tata👜 ta bi bayansa 🎊🎊🎊🎊🎊🎊 *_CHINA (SIN)_* *_guangzhou airport_* Qarfe hudu ⏰ na yamma da minti ashirin a agogon qasar china qarfe sha daya da minti ashirin agogon Nigeria suka sauka a qasar,iyakar gajiya fadila ta yita,tafiya ce ba kadan ba tamkar ta yada shege zama ne na awanni kimanin goma sha biyar a jirgin wadda bata taba tafiya makamanciyar ta ba Da qyar take daga qafarta da tayi mata taruwar jini saboda tsabar zama,suka sake bin layin screening immigration suka karbi passport suka kuma duba visa dinsu don tabbatar da cewa sun samu izinin shigowa qasar tasu,bayan sun tabbatar da ingancinta suka buga musu stamp suka wuce Sauran kadan aliyyun ya bace mata saboda ta lura cike yake da kuzarinsa tafiyarsa yake kamar baiyi wata doguwar tafiya ba bisa dukkan alamu ya saba da irin wannan tafiyar,motar ce mai azqbar kyau da daukan hankali tayi parking gabansu mutum uku ne suka fito dukkaninsu sanye da coart baqaqe baqin space da baqin sau ciki😎,cikin girmamawa suka iso inda aliyyu yake biyu daga ciki suka miqa masa hannu sukayi musabaha,cikin harshen nasara suka fara gaisawa dayan dake gefe ya dauki akwatinansu ya sanya a bayan motar Bayan ya ruge boot suka dunguna gun motar fadila ta bisu a baya,ita da shi na sit din tsakiya biyun kuma na sit din can bayan driver din kuma ya shiga mazauninsa ya tada motar,hira suke abinsu da aliyyu yayin da hankalin fadila ya kasu biyu,daya ta dora shi ne bisa ga aliyyu yadda yake turanci kai sai ka ranyse [10/16, 1:52 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WA YASAN GOBE?..* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *written by safiyya Abdullahi musa huguma* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *part 2* 2⃣9⃣&3⃣0⃣ Yayin da hankalin fadila ya rabu gida,daya ta dorashi ne kan yadda aliyyu ke turanci kai ka rantse da Allah cikakken buture ne gaba da baya,babu tuntuben harshe ko kuskure ko qanqani,daya kuma ya tafine kan kyawu tsari gami da tsaftar garin ,garine mai azabar kyau da tsari,yanayin gine ginensu sun burgeta matuqa da gaske,saidai abu na farko da ya daga mata hankali dan banzan sanyin da suka tarar ana danawa a garin🌫,taji daya daga cikin yan chinan na sanar da aliyyu yanzu ma aka shiga cikinsa wanda irin wannan sanyin a Nigeria shine wucewar jaurarmu A hankali motar taci gaba da kutsawa cikin cikin kyakkyawan shimfidedan titin har suka shigo cikin wata kyakkyawar unguwa mai tsafta da tsari wanda tafiyar fadila tsakanin airport da inda suke yanzun ta fuskanci haka unguwanninsu suke,basu yi wani nisa a layukan da suke wucewa ba suka sa signal suka gangara wani layi,sun kusa kaiwa qarshen layin driver ya faka qofar wani dan kyakkyawan gida dake yanyame da shukoki daga gaban gidan kuma grass carfet ne to kusan ko wanne gida dake layin haka yake left to right Driver din ne ya fito ya bude musu qofa sannan ya bude boot din ya fitar da kayansu,Aliyyu ya ciro keys daga aljihun cikin rigar suit dinsa ya miqa masa ya sa hannu ya karba ya nufi gidan ya bude,ya shigar da kayan sannan daga bisani shima ya shiga Tun fadila na tsaye har ta gaza jure tsaiwar ta maida bayanta ta jingina jikin wata 'yar bishiya dake dashe a gun,shi kam tsaye suke qyam jikin motar shida lukas da andi suna ci gaba da hirar kasuwancinsu cikin harshen nasara,jifa jifa tana tsintar wani abu wani abun kuma ya kuce mata idan tunani ya rinjayeta,tsayuwar awa guda cif sannan ya fito ya qarasa shigar da ragowar kayan da bai dauka ba ya kaisu ciki,ya dawo cikin girmamawa ya ya miqawa aliyyu maqullan ya karba yana tambayarsa "have you finished?" Ya gyada kai gami da cewa "yes sir everything is ready"ya girgiza kai yana cewa "well done"ya juya gunsu andi da lukas ya basu hannu sukayi musabaha gami da sallama ya juya ya nufi cikin gidan su kuma suka shige motar driver ya jasu suka bar gun a kasalance ta rufa masa baya zuwa cikin gidan Falone wanda ba za'a kirashi qato can ba hakanan ba zaka kirashi da qarami ba,saidai yadda ya tsaru dole ya qayatar da kai ta yadda zaka iya fin sha'awarsa ma fiye da wani qaton,kujeru ne set guda yan madaidaita masu azabar kyau sai labulaye na alfarma da suka kewaye falon ta yadda baka iya bambance ina qofa take center carfet center table da wasu yan qanana dake maqale tsakanin kujera da kujera tafkekiyar plasma TV da home theater dining area mai dauke da dining table mai kujeru hudu komai na falon fari ne tas sai wasu abubuwan masu sirkin baqi kadan,qofofine hudu cikim falon daya kitchen ne sai store sai public toilet sai bedroom,komai tsaf yake kuma qal qal ta tsammaci hakan dama idan tayi la'akari da dan karen son tsafta irin na aliyyu Fadila ta zabi daya faga cikin kujerun tayi saurin zama saboda yadda take jin gajiya na nuqurqusarta har cikin qashi ji take tamkar ba zata iya daga koda yatsanta ba,tana nan takure kan kujerar tana satar kallonsa,gaba daya sanyin garin ya soma takura ta tun yanzun,ga bashin sallah dake damunta tunaninta daya ta ina zata soma iya taba ruwa da wannan azababben sanyin? Key yasa ya bude dukkanin qofofin ya tura daya wadda a samanta aka rubuta da wani dan siririn katako mai kyau *bedroom* ya shige,ta miqe itama a gajiye ta shiga public toilet cikin sa'a ta tadda a kwai heater kunna ta tayi ruwan ya dan yi zafi sannan ta kunna famfo na zafin da na sanyin ta saisaita su yadda zai mata dadin alwala,falon ta dawo saidai bata san ina ne gabas ba don haka ta kintaci inda taji hankalinta ya fi karkata ta tada salla Minti goma ta kammala magrib da isha'i har ma da shafa'i da wutirinta,batabar kan carfet din ba tana duqunqune cikin hijabinta wanda dama yana cikin jakar hannunta haka al'adarta yake ko ba zata sanya hijabi ba to bata rabo da shi cikin jakar ta,a hankali tana duqunqunen idanunta suka soma mata nauyi da radadin bacci tamkar an watsa mata tsakuyoyi a cikinsu gajiya da bacci suka yi mata tarom dangi suka murqusheta bata san sanda ta bingire da bacci ba agun Cikin sabon shiri yq fito yana sanye da jibgegiyat rigar sanyi mai gashin dabba daga ciki trouser ne da long sleeve shirt duka baqaqe kansa hular sanyi ce ta gashi mai azabar kyau qafafunsa boot ne mai dan tsawo 👢ya sanyawa hannayensa safofin hannu ya saye idanunsa cikin gilashin nan nasa na ko yaushe👓 cikin hanzari ya fito da niyyar fita don sama musu abinda zasu ci idanunsa ya sauka kanta tsakiyar centre carfet din dake tsakiyar falon ta cure guri guda Ya san sanyin garin ne ya soma addabarta shi kansa da ya saba zuwa abroad cikin irin wannan yanayin wannan karon sanyin ya dameshi balle ita da bai tsammanin ta yaba zuwa,ya dawo da baya a hankali ya isa ga makunnin na'urar dumama daki ya kunna ta ya sake juyawa ya zuge gami da rufe duk wasu qofofi windows da labulaye dake abude na gidan sannan yasa kansa ya fice hadi da sa key ya kulle gidan A hankali ya soma bude idanunta tanajin yanayin dakin ya sauya mata,sanyin da ya takura mata dazu da zata kwanta ya ragu sosai da sosai,ta kasa tashi illa idanunta dake bude tayi zuru tana jin yadda cikinta ke qugin yunwa,idan bata manta ba rabonta da abinci tun a nijeria sai drink da take ta sha har acikin jirgi Wanka a qa'ida take da buqatar yi da ruwa mai zafi don ta samu ragowar gajiyar ko zata sake ta amma rashin ganinsa afalo yasa take tsammatar yana bedroom din,kasa kunnenta tayi sosai bata jo motsin kowa ba don haka ta miqe akasalance,cikin sanda ta tura qofar bedroom din ,babu kowa ciki daki ne babba yalwatacce ba wani tarkace cikinsa cupboard ce sai dressing mirror hadi da dressing chair sai sofa qwaya daya madaidaicin gado ne mai rumfa wanda aka kafashi daga jikin window sai center carfet da center table daga gaban gadon kenan,komai na dakin shima farine kamar dai falon hatta da kalan furniture din zuwa ga bedsheet Ta sako kanta ciki bayan ta tabbatar babu kowa akwatunansu na saman gadon a ajjiye nashi akwatin ne ta gani a bude kayan sun dan hargitse kadan da alama ya bude ne ya debi wasu abubuwa,gefe ta zauna ta fiddo da duka kayan nasu ta shirya su cikin cupboard,nashi ne auka cinye fiye da rabinta ta tsaya tana kallon yadfa kayan suka tsaru ita kanta sun burgeta ta karkade hannayenta ta rufe qofofin sannan ta shige toilet din bayan ta ciro kaya kala daya da zata sanya Ta fito daure da towel wanda ya sauko mata qasan gwiwarta yayin da ta yafa qaramin saman kanta tana goge ruwan da ya dan taba mata shi da wanda ya shigar mata kunne,sam bata yi tsammanin ya shigo dakin ba shi din ma haka yana zaune ne kan bedside hannunsa riqe da lemon kwali yana dan zuqa kadan kadan ,gabanta ya fadi sosai don ta tsorata da ganin nasa,da azama ta juya don komawa toilet din garin haka towel din kata ya zame ya fadi qasa kanta zuwa kafafunta suka fito sarari,gashinta ya kwanta luf bisa dan dogon wuyanta zuwa gadon bayanta wanda ruwan da ya tabashi ya sake sashi kwanciya,da sauri ya dauke qwayar idanunsa ita kam ko ta kan towel din bata bi ba ta koma hadi da tura qofar Ta hudar dan maqulli take leqensa tana gani ya daga lemon maimakon shan ganin dama irin na dazu dai taga ya daga kwalin bai sauke ba saida ya daddake shi tas sannan yayi cilli da kwalin yayi qas da kanshi yafi Minti guda ahaka sannan ya miqe da sauri ya five a dakin,sai da tabbatar ya fita sannan ta fito da sauri ta sawa qofar key sannan ta shirya cikin doguwar riga mai dogon hannu cotton ce sosai ta yane kanta da mayafi ta duba jakarta don dauko turarenta na shamsul imarat da blue lady Kaf jakar ta lalube da hannunta ta nemi su sama ko qasa ta rasa,cikin shakku ta zazzage jakar gaba daya babu babu blue lady din babu shamsul imarat din sai wani da ta gani cikin kwalba cikin takaici take kallonsa tasan dai ita ta sayeshi amma ta manta a ina?,ta zumbura baki tana maida kayan da ta zazzage din cikin jakar,ta dauko shi shima zata maida saita shanshana"ba laifi shima qamshinsa"ta fadi haka tana ajjiyeshi a gefanta Kuyi haquri da aliyyu kudai kuci gaba da bina komai daki daki yake a rayuwa😂😂😂 Na gode🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻 Mrs muhammad ce 👑 📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻 [10/16, 1:53 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WA YASAN GOBE?...* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *written by safiyya Abdullahi musa huguma* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *part 2* 3⃣1⃣&3⃣2⃣ Ta dade a tsaye tana takaicin rashin sako turaren nata da batayi ba don gaba daya tayi tsammanin ta sako su,taja tsaki yafi a qirga ita ba sanin gari tayi ba hasalima yau ta soma shigowa qasar ko da ta sani din ma ai dole sai dai ta yiwa aliyyu magana wadda ita kuma hakanne bata so,to idan kuwa haka ne bata da zabi illa saka wannan turaren tunda sam bata son zama a rayuwarta ba tare da taji jikinta na tashin qamshi ba haka take qamshi a jininta ya ke,ai shima wannan din turarene,sam fadila ta mance aikinsa tama manta a inda ta sayeshi tunda abun bai gabanta tunda ta wulla shi a jaka ta manta da babinsa Ta kammala shafawa tana lumshe ido gami da cewa "hmmmm" saboda yadda qamshin nasa ya yi mata dadi sosai,qanshi ne mai sanyi ya karade jikinta da ma dakin gaba daya,ta maida shi cikin jakarta ta rataye jakar a abun rataye jakankuna ta jawo qofar dakin ta dawo falo,yana zaune a gaban laptop dinshi 💻(agogo sarkin aiki😏)cewar fadila cikin zuciyarta,aliyyu hardworking person ne komai yasa a gabansa yakan zama serious akai har sai ya kai ga cimma burinsa,yana jin fitowar tata amma bai daga kai daga abinda yake ba bare ya dubi sashenta Sannu a hankali qamshin ya soma karade falon ya soma kuma fisgar hankalinsa,ya rasa daga inda qamshin ke fitowa,sannu sannu kasala ta soma rufeshi idanunsa suka soma lumshewa,ya daga kansa ahankali ya dubi sashen da take waya ce a hannunta📱 tana danne dannenta saqonni take dubawa da suka shigo mata,ya maida ido runtse sosai yana qaryata kanshi game da feelings din da yake ji,ya sani tun usul haka halittarsa take yana daga cikin mabuqata,gaba daya ya mance da wannan matter din sanda zai taho aiki ne kawai a gabansa da kuma tsaftar inda zai zauna da abincin da zaici Cikin lokaci kadan mood dinsa ya canza sosai he needs something really, idanunshi sun jima a rufe aikun da yake ya gagareshi saidai still mood din da yake ciki bai canza ba,ya sake kallonta karo na biyu bata san ma me ake ba har yanzu wayarta na hannunta tana latse latsenta,"take dis bags ki samin nawa a plate ki dauki naki Juyowa tayi don jin muryar tamkar ba tasa ba,amma sai taga latse latse yake bisa laptop idanunsa na bisa screen din,bata ce komai ba ta ajjiye wayar a gefanta ta debi kayan ta shiga kitchen,shawarma ce da Chinese spaghetti sai roasted chicken ta saka kowanne a aplate din ta hada masa da ruwa da lemo ta jawo dan side table gabansa ta dora masa akai,zuwanta gabansa ya sake sa qamshin ya cika masa hanci,ya sake runtse idonsa hadi da qanqame hannayensa gu guda cikin wani irin lust moode,sam bata lura ba ita dai ta kammala hada masa ta dauki tata ledar ta koma mazauninta,duk yadda ya kai ga son cin abincin haka ya dinga tsakurarsa a kasalance girman kai kuma ya hanashi ya sake koda duban sashen da take 🔅🔅🔅🔅🔅 Ta sake duban agogo karo na uku kenan sha daya da rabi na dare🕦,tuni bacci ya sake cika mata idanu kamar ma batayi shi dazun ba duk da dama ba wani jimawa tayi ba ta farka,tunaninta daya ko ina makwancinta? Tasan dai ko giyar wake ta sha bata tafiya kai tsaye su hada dakin kwana da aliyyu ba bare ya yarfata kasa daurewa baccin da take ji tayi saboda haka ta ware mayafinta ta lullube kafadarta zuwa qafafunta ta ja filin kujera qwaya daya ta tada kanta da shi tunda shi kam lura aikinsa yake tuquru hadi da amsa kiran dake ta shigo masa wanda dukka da harshen turanci yake maganar hakan ya tabbatar mata yan qasar ne masu kiran,batasan yayi hakanne bane ko zai samu feeling da yake ji ya sake shi shi uasa ya takura kansa da aiki,ba abunda yake sai faman dirkawa cikinsa coffee flask guda ta hada masa amma ya kusa tafiya abun har yaso bata tsoro Tsaye yayi a kanta baccinta take sosai,bai taba qarewa fuskarta kallo ba irin yau,gashin gaban goshinta ya sake kwanciya kamar relaxer ta shafa masa komai nata medium mai kyau tamkar ma ba baccin take ba,a hankali abun nan da yake son ya danne ya ci gaba da taso masa,ya tabbatar idan yaci gaba da kallin nata a yanayin da yake ciki din nan zai iya aikata abinda yame ganin ita din ta masa kadan ta iya daukarshi gane yake zai iya nakastata,ya janye ida nunsa daga kan fuskarta yana maida numfashi,yasa hannunsa ya zare filon da take kai kanta ya sauka saman kujerar Firgigit tayi ta farka don ta dan tsorata ya kalli idanunta wadanda bacci da ta soma da tsoratar da tayi yasa su sukai wani kyau ya dauke kansa gefe guda zuciyarsa na dan bugawa da sauri, ganinsa tsaye bisa kanta yasa ta dan sukuyar da kanta "idan kinga dama ki koma bedroom ki kwanta"ya fada yai gaba hannunsa dauke da cup da flask din tea Ta dauki a qalla minti talatin a zaune tana doubting din aliyyu ne kuwa ma ya tasheta?idan shi din ne ma ya zata iya kwana daki guda da aliyyu? Aliyyun da yaqi jininta? Bai sonta bai qaunarta?,wani benefit nata kawai yake so tayi masa girki da shara ba wai ainihin ita fadilan ba,ganin babu mafita ga wani sanyi da yake sirarowa falin saboda kashe na'urar falon da yayi ya sanyata miqewa jiki a salube ta njfi bedroom din Kamar wata munafuka ta tura ta shiga,ga mamakinta yana kwance ne aqasa saman dan qaramun carfet din nan na gaba gado mai dauke da center table ya sauke center din shi kuma ya maye gurbinsa,trouser ne kawai ajikinsa da singlet,yayi ruf da ciki,hannun hagunsa da damansa duka pillow ne ya jajjerasu ya kuma matsesu ajikinsa,faffadan bayansa mai cike da siffar qarfi ya bayyana,ta dauke kanta cikin sanda ta zagayeshi gami da hayewa kan gadon tana mamaki cikin ranta shi kam wannn baijin sanyin garin nan ne? Ga kuma sofa a dakin doguwa amma bazai hau kai ba?bata da courage din da zata magana don haka ta maida gulmarta ciki ta tattara tafukan hannayenta tayi addu'ar bacci ta shafe ilahirin jikinta da ita ta jawk bargon ta rufa tayi matashin kai da hannunta kasancewar duka filon dake kan gadon aliyu ya kwashesu zasu taya shi kwana😜😜 Idanunta fes a kansa tana gain yadda yake ta mutsu mutsu cikin ranta take munafuncin haka yake wai baccinsa ne shi,tun tana kallonsa har bacci ya rufe idanun nata,taso tayi daddan bacci mai tsawo a a lokacin saidai saidai hakan ya gaza samuwa don ta tashi yakai sau nawa saboda rashin sabo duk kuma tashin da zata yin idanunta na kan aliyyu sau uku tana ganinsa yana canza gurin kwanciya ana hudu ne ta ruskeshi yana qiyamul laili tuni ta miqe don ita din ma lokacin tashi yin tata sallar yayi Aliyyu na bisa darduma yaga tashinta a zatonsa fitsari zata yi sai yaga bayan ta fito ta tayar da sallah shi da zuciyarsa yaje gulmar isha'i ne bata yi ba kota tsammaci asuba ce tayi?,shi kadai ke kida da rawarsa ita kam ta kafu gaban ubangiji,har ta idar idanunsa na kan fejin qur'anin dake hannunsa yana karantawa yana shafin qarshe ne cikin suratu anbiya'i,kusan yare suka sake miqewa suka tada sallar asuba kowa yayi tasa,yana so ya samu falalar jam'i sai dai girman kansa bazai barshi yayi mata tayi ba,bata jima da soma azkar dinta ba bacci ya sureta ko gamawa bata yi ba 🔅🔅🔅🔅🔅 Sanda ta farka ta duba agogon dake ajjiye kan side drawer tayi mamakin yawan baccin da tayi,ta yunqura da niyyar tashi sai ta ganshi shima kwance kan abun sallarsa yana baccinsa cikin nutsuwa da alama shima surarsa yayi bai shirya ba kamar yadda yayi mata,ta dan zubawa kyakkyawar fuskarsa ido wanda da idonsa biyu bata isa ba🙊,fuskatsa tayi mata kyau tayi wani fresh,ta dan girgiza kai ta miqe tsaye ta soma gyara gadona a nutse cikin taka tsantsan don kada ta sheshi sai da ta kammala tayi mopping ta wanke bandaki duk da baiyi komai ba ta sake kintsa falo,ta koma ta buda jakarta ta fiddo da turaren wuta ta jona abun turaren wuta mai amfani da wutar lantarki ta zuba cikin qanqanin lokaci gidan ya dumame da qamshi har ya leqa moqata ma,cikin sanda ta koma dakin gadon tayi saurin shiga wanka tun kafin aliyyu ya farka ta kasa sakewa Shigar shadda tayi pink dinkin riga da skert ne sun mata cif sun zuna das ajikinta babu inda yayi kwarara kai ka rantse a jikinta aka dinka su,hida lip glosses sai kwalli kawai ta saka ta taje dogo kuma baqin gashinta ta kameshi da ribbon pink,ta ware dankwalinta tayi daurinta na zamani wanda ake sokeshi(ture kaga tsiya)hakan ya bawa jelar gashin nata damar zubowa ta qasan daurin,rigar sanyi ce wadda ko ciki bata rufe ba mai gashi dogon hannu ne da ita ita ta sanya light blue,ita kanta sai da ta juya ta sake kallin kanta duk da ba wani make up tayi ba amma ta zuba kyau ta dauko turarenta ta shafe lungu da saqo na jikinta,har ga Allah tana jin dadin qamshin turaren yayi mata ta maida shi sannan ta koma kitchen din shirya break Mrs muhammad ce👑 📚📚📝📝✍🏻✍🏻✍🏻 [10/16, 1:56 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WA YASAN GOBE?..* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *written by safiyya Abdullahi musa huguma* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *part 2* 3⃣3⃣&3⃣4⃣ Tun acikin baccin ya soma jin qamshin na ratsa qofofin hancinsa,duk zuqar numfashi daya da zaiyi yana zuqarsa ne tare da qamshin,qamshin yayi masa,tun yana tsammanin ko amafarki ne har ya soma gasgata cewa a zahiri ne ido biyu ne,sannu a ahankali idanun suka ci gaba da buduwa ya soma zagaye dakin da idanun nasa 👀,ko ina fes sai qamshin turaren wuta ke tashi da na wannan turaren nata da har yanzu ragowar qamshin bai bar dakin ba Komai na dakin a kintse neat " I like it" ya fada can qasa,hakan yakeso ko da wani lokaci area din da yake rayuwa ta kasance,ya dan miqa hannunsa ya jawo wayoyinsa da ya dora kan center ya duba agogo,lokaci ya gani ya ja sosai din kuwa qarfe goma sha daya agogon china qarfe shida agogon gida nijeria,ya duba call logs nan ya tadda missed call na mr lin,babban dan kasuwa ne dan qasar china saidai sananne ne a qasashen duniya hakanan yana da companies anan gida nijeria sai missed call din andi biyu sai na salima guda biyar da ya biyo baya,duka baiji ba don a silent wayar take mantawa ma yayi bai kasheta ba don baya kwana da waya a bude saida babban dalili A hanzarce ya miqe ya watsar da fulallukan da yake kai ya nufi toilet,as usual tun a gida a nan ma haka ya tadda ruwan wanka ready cikin bathtub shigewa yayi kawai abinsa,mintina talatin ya kammala wankan a gurguje ya fito ya shirya kansa cikin baqaqen suit harda baqar safar hannu saboda sanyi sunyi matuqar haska farar fatarsa yayi kyau kamar wani bature tabbas aliyyu badai kyau ba Da hanzarinsa ya wuce kitchen kai tsaye kamar yadda ya zame masa aladarsa shan ruwa cup guda da safe kafin yaci komai,tun daga falon qamshin girki ya marabceshi,hancinsa ya bude sosai yana sheqar qamshin son ransa👃🏻😋,cikin kuzari ya qarasa kitchen din tana tsaye gabn gas tana kwashe chips don shi kadai ya rage mata dama ta kammala,bayanta yake bi da kallo tayi kyau kamar wata 'yartsana don kayan sun mata cif cif ajiki ya bi gashinta da kallo wanda ke reto a bayanta sai ya tsinci kansa cikin birgeshi da hakan yayi don shi kam ma'abocin son gashi ne tun yana qarami,ya dauke idonsa ya maida kan freezer bayan ya budeta yana jawa kansa kunne Sam bata san da shigowarsa ba qarar rufe freezer din ita ta ankarar da ita,ta dago ta dubeshi yana shirin ficewa ya dan lumshe idanunsa sanda yake qoqarin barin kitchen din saboda feeling da yake ji sosai irin na jiya da ya hanashi sukuni da bacci mai dadi,bata ce komai ba ta biyo bayansa,har ya samu hannun kujera ya zauna numfashinsa na fita da sauri da sauri,cikin hanzari ya balle hancin gorar ruwan ya kai bakinsa ya soma daddaka Bai ajjiye ba har sai da ya shanye tas ya wurga robar cikin dust bin dake kusa da shi yana maida numfashi bayan ya rufe idanunsa "Your breakfast is ready"yaji muryarta kusa da shi tana fada,a hankali ya bude idonsa bai ganta ba don tuni ta wuce sai ragowar bayanta da ya gani sanda take qarasa shigewa kitchen,bai sake komai ba illa wucewa dining da yayi don gwada cin abincin Ta zuba masa komai hatta tea ta hada masa a cup ya sanya cokali yana motsa shi,mamakin kanshi yake yana kuma tambayar kanshi *meke faruwa?* da shi,ta fito daga kitchen hannunta dauke da dan qaramin cup data hada black tea☕ta zauna cikin falon tana kurba a hankali qamshin ne yaci gana da buwayarsa ta hanyar iska dake kado mishi shi Ya maida hankalinshi kan tea dinsa yana kurba kadan kadan,comfortably yake jin zamansa kan dining din shi daya,ya debi chips da pork ya kai bakinsa yana ci gaba da monitoring movement dinta da idanunsa,"hey" taji yace ta dago da kanta ya dan dago hannunsa ba tare da ya dubeta ba"come here"ya kirata sai taji ban barakwai,ta ajjiye cup din hannun nata a hankali ta qarasa dining din,ya sake kurbar tea din idanunsa na kan ruwan tea din da yake sha "sit" yace da ita,ta ja kujerar gami da kasa kunne tana sauraran mai zaya ce mata Bai ce komai ba har ya kammala breakfast dinsa,qamshin da yake ji ne ke rudashi ya rasa wanne irin mayen turare take amfani da shi ya zaro tissue daga cikin tissue dice box yana dan goge hannunsa inda ya bacin "as from today kada ki sake kawomin abinci ki bar gun har sai na kammala understand?"(nikam cewa nayi hmmmmm,fadi gaskiyarka na daure.......) "mutum sai shegen mulkin tsiya ba haka nake masa ba a nijeria wani lokacin bai taba cewa don me ba sai yanzu?wato zai fara fidda sabon salo don yaga ba'a gida muke ba"cewar fadila ita da zuciyarta,a fili kuwa gyada kai tayikata na a qasa "hey" ya sake cewa ta dago ta dubesa ta sake sadda kai "open ur mouth u r not a bruise" to tace masa cikin qosawa da zaman Har ya ja kujerarsa baya yana niyyar tashi don ya tabbata ya sake qara wasu mintina a gaba bai bar gun ba tabbas bazai iya mallakar kansa ba,abunda yake ji a cikin gangar jikinsa is very strong feeling,yana so yace ta daina amfani da perfume nata amma girman kai ya hana, yana ganin idan ya fadi mata zatayi tsammani ya damu ne da wani abu nata,he feel he can sustain whatever zaici gaba da ji,wayarsa da ta soma kadawa cikin tattausan ringing ita ta dakatar da shi daga tashin da yayi niyya Mrs muhammad ce 👑 📚📚📚📝📝✍🏻✍🏻 [10/16, 1:57 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WA YASAN GOBE?..* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *written by safiyya Abdullahi musa huguma* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *part 2* 3⃣5⃣&3⃣6⃣ Ya ciro wayar ya duba mai kiran ya dan saki ajiyar zuciya kadan sannan yayi pressing ok,sunan da taji ya ambata ya sata gane da wadda ya ke wayar,salima ce,hira take yi masa sosai yana dan biye mata,hirar da tasa fadila kasa jure zaman gurin ,satar kallonsa take ta qasan ido gaba daya launin idanunsa sun canza muryarsa ta sake zama so cool Idanunsa na kan fadila lokacin da ta miqe don basu guri don zuciyarta ta samu salama daga mugun kishin dake taso mata,ya dan daki table din da hannunsa wanda yasa fadila daje shirin sauka juyowa suka hada ido da shi,fararen idanun nan nasa da sukayi returning zuwa ja ya lumshe su sannan yayi mata alama ta koma ta zauna,kamar ta zura da gudu tabar gurin haka taji saidai ba yadda ta iya ta koma din Minti biyu tsakani yayi sallama hadi da kissing wayar sau uku,lumshe nata idanun tayi tanajin wata dalmar kishi na digar mata cikin zuciyarta,bata bari shaidan ya kitsa mata komai ba ta soma karanta *hasbunallahu wani'imal wakil*,wani gumi ta gani yana tsatstsafo masa ya maida jikinsa ya jingina sosai da makarin kujerar idanunsa a rufe wani weakness yake ji sosai cikin jikinsa ya dauki aqalla minti goma sha biyar a haka kafin mood dinsa ya dan saisaita ya dinga sakin 'yar qaramar ajiyar zuciya a jajjere,har a lokacin fadila na satar kallonsa tana mamakin meke damunsa haka mood dinshi yayi bala'in canzawa within few minutes,ya sauke doguwar ajiyar zuciya lokacin da yake bude idanun sa,caraf ya kamata tana kallonsa sai yayi wani kicin kicin da rai yana ganin kamar tasan meke damun sa,sunkuyar da kai tayi shi kuma ya zark handkerchief ya share ragowar zufar fuskarsa Sauka yayi a ahankali daga dining area din ya shige bedroom,tana zaune a gun ya sake fitowa wannan karon yellow and coffe din suit ne ajikinsa da alama kaya ya canza koma wanka yayi ne oho wa yasan masa😜😜😜,hannunsa riqe da brief case yana amsa wayar mr lien a hanzarce yake tafiya ya sanya hannu ya bude pocket din sa ya zaro yuan dari ya ajjiye mata(five thousand kudin naija) kana ya dago suka sake hada ido dukkaninsu sunji jiki ita ta sunkui da kai shi kuma ya fice a hanzarce,ta kalli kudin ta tabe baki "ne me zanyu da kudin qasarsu?tabdijan" ta fada a fili amma qasa qasa kamar mai gunguni Yana fita lukas da andi na qofar gida cikin motar kamfaninsa da yake shirye shiryen budeshin *maitama group of companies* haka yake kowa yasan da su,da fitowarsa suka sara masa kamar wani soja sukayi handshake kamar yadda yake a al'adar sa don dabbaqa value ba addininsa a ko ina yake,lukas ya bude masa qofar zungureriyar motar ya shiga suka rufa masa baya Driver din ya bawa umarnin yabi ta lujing road huangtian street zasu fara shiga yueyang hotel yana son ganin ramzan dan india ne wanda yana daya daga cikin wadanda ya bawa contract na ginin factory din nasa,factory ne babba na qashin kan aliyyu wanda ya narkar da maqudan kudade gurin samar da shi,factory ne da zai dinga manufacturing kayan babies blouses na maza da mata Wunin ranar cikin zirga zirga mai yawa yayi ta ahiga can fita nan,hakan ya taimaka masa sosai gurin rage masa abinda yake ji cikin jikinsa,yayin da a daya bangaren fadila ta wuni kwanciya sai bayan ta idar da sallar la'asar sannan ta shiga kitchen,pepe chicken couse couse da miyar qwai sai mutuminta lemon kwakwa da ya wadatu da madara da flavour wannan shine jadawalin abincinta na dare Nan da nan ta gama kasancewar gas din nata mai hudu ne,ta turare gidan nata da turaren wutanta bayan ta zuge duk wani glass da window dake gidan,sai gidan yayi wani dumi mai dadi daya gauraye da qamshi,cikin ruwa mai zafi sosai tayi wanka saboda sanyin dake damunta na garin,riga da wando tayi shirya kanta ciki wandon dogone har qas pencil rigar kuma da kadan ta rufe cikinta jacket ta saka mai kauri ta mata wanda ta sauko har qasan gwiwarta tana da dogon hannu sai manyan maballai guda shida masu fadi da aka jera daga gaban rigar kusan sune kadai adonta,rigace da yawanci a turai matansu ke amfani da ita musamman lokacin sanyi Gashinta ta gyara sosai ta kamashi da band ta saya socks qafa da hannu ko zata samu sauqin sanyin,da turarenta ta shafe jikinta ko ina ciki da waje,ta maida ta tattare abinda ya dan yamutse a dakin ta gyara shi sannan ta ciro jakar laptop dinta da sam ta manta da ita ta cirota tasan saqonnin email na nan na jiranta jingim ta dauki wayarta ta dawo falo Sai da ta zauna sannan ta duba agogo don ganin ko lakacin sallah yayi don bata tsammanin akwai masallaci anan inda suke tun da tazo bata ji kira ba da agogo kawai take amfani ko dazun ma sauran kadan sallar azahar ta qwace mata,lokaci kadan ya rage lokacin sallar ya shiga don haka sai ta jona chargy na laptop din nata sannan ta zira hijabi ta shimfida dadduma ta tada salla Bayan ta kammala ne ta ninke hijabin hadi da daddumar ta maida daki sannan ta dawo kan computer din tata,aikam ta tarar da saqonni masu yawa anty hafiza sumayya rabi'ah na sister farida ne akan gaba harda pictures din baby humaira masu yawa har da na ya ahmad ragowar kuma duka na masoya ne na gari dake qaunarta ,na 'yan uwanta ta soma dubawa kowanne na tambayarta ne sun iso lafiya? Da makamantansu,dai sai taji kewarsu ta cikata take ta shiga maida masu amsa lallai duk wanda yabar gida gida ya barshi,sai data gama da su sannan ta soma duba na sauran jama'a wanda ke da muhimmanci ta maida masa amsa mara amfani ta goge shi A hankali ta daga kai karo na farko ta duba agogo,tara da mintina goma sha biyar,duk da cewa unguwar da haske ta dan soma duhu alamun dare ya soma kenan wasu sun kashe qwayayensu "me ya tsaida shi tun safe har yanzu?" Fadika kewa kanta wannan tambayar da ita kanta bata san amsarta ba,fargaba ta dan soma shigarta da tsoro lokacin da idanunta ke ganin kamar ana gilmawa ta cikin balcony dinsu,ta miqe a dan tsorace ta maida hijabinta bayan ta zare computer din daga jikin socket ta maida daki ta dawo falon ta tayar da isha'i Har ta idar babu aliyyu ba alamunsa,zama tayi kan daddumar jiki a takure,kewa ce sosai ta kamata,ita ba layin qasar cikin wayarta bare tayi kira,a gogon ta sake kalla ya nuna mata qarfe goma da minti biyu,tsoro ya sake shigarta musamman da taji unguwar ya sake yin shiru ba komai ke tashi sai haushin karnuka🐕da keta kai kawo Dif wutar gidan ta dauke gaba daya,gabanta yayi wani matsanancin bugu yadda duhu ya mamaye gidan ko tafin hannunta bata iya gani,tuni jikinta ya soma rawa ta dunqule guri guda tsoro ya mamayeta haushin karnukan sai take jinsa kamar a qofar gidan Bata san sanda ta wuntsila tayi bayan kujera ba jin haushin karen a bakin qofar falon hadi da tsaiwar mota wadda aka yiwa full light aka dallare gidan gaba daya daga baya aka kashe,ai bata san sanda ta saki kukan tsoro ba dumin hawayen kawai itama taji,cewa take shikenan na banu,kusan minti biyar sannan ta daina jin motsin karen,zama tayi dabas a qasa hadi da dafe goshinta da tafin hannunta,kuka sosai ta saka,tana bala'in tsoron kare arayuwarta,don duk gidan da zata matuqar suna da kare to komai mutuncin da kuke tafa bar zuwarmuku kenan daman yaya lafiyar kura,yana daya daga cikin abinda yasa bata saba da gidansu aliyyu ba bata zuwa kenan da can suna da karnuka har biyu kafin daga bisani uncle abba yasa aka fita da su Sam bataji shigowa ba sai takun sawaye ta ji,a guje ta miqe tana neman mafaka a rude ,ji tayi an cafkota cikin duhun,ihu ta bude bakinta da niyyar yi ko da wanda Allah zai sa ya kawo mata dauki sai taji ansa hannu an toshe mata baki dai dai lokacin wutar ta dawo,fuskarsa cikin tata yake kallonta ya zuba mata qwayoyin idanunsa,fuskarta tuni tayi jage jage da hawaye jikinta sai bari yake don sai da wutar ta dawo ta gane ashe tuni har hular kanta ma ta cire saboda tsabar rudewa😂 Ita ta fara janye idanunta hadi da kawar da kanya gefe ganin shi bashi da niyyar janye nasa sexy eyes din da ya zuba mata,qoqarin zame hannunta take har a lokacin kanta na gefe tana kuka mara sauti don iya tsorata ta tsorata,jikinsa a mace yake murus ga gajiyar zirga zirga da ya wuni yana yi tuni rigarshi ma ta saman ya cireta a hannu ya shigo da ita,yaqi sakin hannun nata yayin da yake qara zuba mata wani dafin mai illa ga ruhinta har cikin qwaqwalwarta don baisan me riqe mata hannun ya jawo mata ba,ta kuma rasa me yake yi a tsayen har lokacin don qeya ta juya masa idanunta bai kansa ta kuma qi kallonsa Gashinta yake kallo dake ta sheqi shigar ta karbeta sosai kamar yasa hannunsa ya shafa gashin saboda sha'awar da ya bashi sai kuma wata zuciyar ta gargadeshi "zaka jawowa kanka raini" a hankali qamshin turarenta ya ci gaba da sakar masa da gabobi da qyar ya Iya dauke idanunsa yana jan tsaki cikin ransa yana jin haushin kansa Mrs muhammad ce😘 📚📚📚📝📝✍🏻✍🏻 [10/16, 1:58 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WA YASAN GOBE?..* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *PART 2* 3⃣7⃣&3⃣8⃣ Ji tayi an janyota baya an zaunar da ita saman kujera ta dago kai suka hada ido fuskarnan tasa kamar dai koda yaushe,ta sunkui da kai hawaye naci gaba da zuba,tana jin tausayin kanta ne cikin zuciyarta soyayyar aliyu ta gama yi mata illa,yana tsayen dai yayin da ya sauke dukka qwayoyin idanun nasa a kanta yana kallonta ita kuma kukanta take haiqan mara sauti lokaci lokaci tana sa tafin hannunta tan rage ruwan hawayen ta hanyar sharesu hadi da jan majina Kusan minti biyar sannan taga ya dora mata handkerchief saman cinyarta qamshin turarensa da yake jikin handkerchief din ya daki hancinta,briefcase dinsa ya dauka ya wuce daki,saman gadon ya fada yayi rigingine yayin da qafafunsa ke qasa hadi da cewa *"ya Allah"* Lokaci sosai ya bata yana maida numfashi tukun kafin ya miqe ya cire kayan jikinsa ya sanya rigar wanka ya wuce bandaki,ko cikin toilet din ma haka ya dade cikin bathtub kafin ya cude jijinsa ya fito,jallabiyya ya gani saka da short nikker gefan gadon a ajjiye bai kawo komai cikin ransa ba bayan ya tsane jikinsa ya shafa lotion dinsa sannan ta taje soft sumarshi ya feshe jikinsa da designers turarukansa ya jawo kayan ya sanya Har yanzun tana bisa kujerar saidai yanzu har jingina tayi lokaci lokaci ta na dan saki ajiyar zuciya irin na wanda ya sha kuka,kallo daya yayi mata ya dauke idanunsa ita kam dama ko sashin da yake bata kalla ba don haushinsa take ji,sai da ya fara zuwa gun makunnin t.v ya kunna ya dauki remote ya qaro volume gidan talabijin dun qasar ne ke labarai ya maida remote din ya wuce dining,da kansa wannan karon yayi serving din kanshi sannan ya soma cin abincin,yaci abincin sosai ba tare d shi kanshi ya san yaci haka ba Tuni bacci ya dauke ya dauketa kafin ya kammala,ta takure kan kujerar kamar kwanciyar jariri cikin mamansa,ajiyar zuciya take saki kadan kadan cikin baccin,a hankali ya qaraso gabanta ya tsaya bayan ya kammala duk abunda zaiyi,ya zuba hannayensa cikin aljihun short nikker dinsa ya zuba mata ido "sleeping beauty" yaji zuciyarsa na fada,wata sha'awa matsananciya ta taso masa har wani yarrr yaje ji cikin jikinsa,ya tabbata da da salima yazo kai ko samira ce da tuni an wuce gun Itama ita gani yake kamar bada kaine ya tunkareta tunda dukkansu sun fita shekaru,ta sake jan wata doguwar ajiyar zuciya cikin baccin nata harda juyawa,ya kalli hannunta handkerchief din da ya bata ne duqunqune tsakiyar dogayen yatsunta,karo na farko wani abu mai kama da tausayinta ya ratsa zuciyarsa,ya tuna yadda ta tsorata dazun ya tabbata rashin dawowarsa ne da baiyi da wuri ba da kuma dauke wuta da akayi wanda qarewar kudin wutar su ne daga can company din ya jawo haka,yasa hannunsa ya danyi mata baya da gashinta da keson shigar mata ido Da sauri ya janye hannunsa kamar wanda wuta ta ja,ya daga kai ya kalli lokaci sha biyu na dare saura minti shida,yasa hannu a ahankali kamar jiya ya zare filon nata,a tsorace kuwa ta tashi don har sai da yasa hannayensa ya tareta don kada ta fado,sai bayan ta nutsune suka hada ido ya janye hannunsa tayi qasa da kanta,tana jin takunsa sanda ya shige bedroom,sai da ta tsaya ta tattare kwanukan ta mada kitchen dare ya riga yayi ga dan Karen tsoro wanda ya hanata gyare gun kamar yadda ta saba Tamkar jiya yauma kwance yake saman center saidai yau lullube yake da wani qaton lallausan farin bargo ba irin na kan gadon ba,saidai ya debe gaba daya filallukan kamar jiyan blanket din kawai ya bar mata Again yauma dai sallar ta tarar da shi yana yi saidai ita bayan sallar asuba bata koma bacci ba breakfast ta hada masa don taji da yana waya kamar yana cewa zai fito da wuri zasu Beijing ⚜⚜⚜⚜⚜⚜ Washegari maqociyar ta ta hannun hagu mr lin ta shigo mata 'yar asalin qasar china dince tana da yara uku,sosai fadila taji dadin kulawar da ta nuna mata sun dan jima suna taba hira har daya mqociyar tata ta shigo,sunanta nadiyya 'yar asalin alqahira ce sai fadila tafi farinciki da nadiyya fiye da mr lin saboda addini da suka hada duk da cewar itama mai kirki ce,saidai ita nadiya yaronta daya mashkur sai mai gidanta abdul-basid karatu ne ya rabosu da qasarsu,sunyi hirarsu da ita sosai cikin harshen larabci don ta nan bangaren ma ba'abar fadilan a baya ba 🔅🔅🔅🔅🔅🔅 Rayuwa aqasar da baka da kowa ba wanda ka sani bata fiya dadi ba ba kamar idan kana qasarka ta gado ba,to hakanne ya kasance ga fadila da zarar aliyyu ya fita ta kammala aikace aikacenta sai ta koma kan waya ko computer ta duba saqonni,idan ta gaji sai ta sanya hijabinta ta dawo balcony ta zauna tana kallon masu shige da fice,duk da cewa unguwa ce da bata da yalwar jama'a amma ba'a rasa masu wucewa jefi-jefi har wasunsu kan tsaya suyi mata magana ganinta baqar fata mutanen qasar mutane ne masu so da girmama baqo hadi da mutunta shi 🔅🔅🔅🔅🔅🔅 A irin wannan ne ranar bayan ta kammla aikinta da wuri ta hau social media dinta ta gaji ta dawo balcony kamar yadda ta saba,saidai yau da gobe sai Allah sai zaman nan din ma ya gundireta,wasu 'yammata su uku ta gani sunzo wucewa dukkaninsu akan kekuna suna tafe ajere suna hirarsu abinsu🚴,sai taji tana da sha'awar zaga koda layin sune zuwa qarshensa Cikin zumudin tunanin da tayi ta zqro wayarta ta dan yima aliyyu text, _*please zan dan fita qarshen layi*_ Mrs muhammad ce👑 📚📚📚📝📝✍🏻✍🏻 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WA YASAN GOBE?..* *WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* *PART 2* 3⃣9⃣&4⃣0⃣ Ta kalmashe wayar a hannunta bayan ta tabbatar saqon ya je,ta miqe ta saya qofar don bata damu da sai ta kulle ba ta san qasa ce mai cike da tsaro A hankali take ratsa layukan duk da dan banzan sanyin dake bugarta amma yanayin yayi mata dadi sosai,tana tafiya tana cilla hannayenta gaba da baya fuskarta qunshe da murmushi ,unguwar ta burgeta matuqa babu yawan jama'a tunda dama can ita bata son hayaniya,sai yara jefi jefi dake wasa wasu cikin balcony dinsu wasu kuma a qogar gida duk wasannin nasu baya wuce tseran keke da buga qwallo(football) Abinda ta lura da shi shine su kamar ma sanyin bai damesu ba ba mamki ko don qasarau ce sun saba,har ta fita daga layin da shiga second street bata sani ba,yara ta gani su hudu babbar ciki ba zata wuce shekaru tara ba ma bi mata ba zata wuce takwas ba ta ukun kuma ba ta gaza uku qaramar ce mai alamun biyu amma da yake yanayin qasarsu ya bam banta da namu buka buka da su masha Allah,ball suke bugawa suka bugo mata saidai a qafarta ta sauka basu sameta ba Babbar cikinsun ce ta fara lura da wadda suka bugawan ta tabo mai bi matan tana mata rada akunne tana kallon fadila duk sai suka juyo suna kallonta,fadika ta sunkuya ta dauki ball din ta nufi inda suke fuskarta dauke da murmushi suma murmushin suke saboda ganin baquwa,ta ajjiye ball din agabanta tabuga ta ta tafi gabansu ai kuwa suka hau ysalle da murna suka dawo mata da ita,duk da bata jin yarensu amma ta gane dadin hakan sukeji A nan gurin yaran ta bata lokaci sosai ba tare da ta sani ba,yaran sun sake sosai da ita nan ta hada su dukkaninsu ta shige tsakiyar su tayi musu hotuna,suka shige gidajensu suna daga mata hannu,sai alokacin ta duba gari taga ya soma duhu hankalinta a taahe ta juya ta soma laluben hanya garin haka sukayi kacibus da mutumin nata (kare)shaf ta manta kare baya son gudu don a rude take tuni ta takure ta sheqa a guje shi kuwa ganin haka ya rufa mata baya Motar kamfanin ta ajjiye aliyun a qofar gida yayi sallama da su yana jaddadawa wanda ke gaban motar su tabbatar gobe early in d morning sun kawo engines din nan an qarasa kafasu agurarensu,ya amsa masa cikin girmamawa,suka ja moyar shi kuma ya juya ya shige gidan Qwan lantarkin na kashe yasa hannu ya kunna haske ya gauraye falon,neat yake kamar ko yauahe cike da qamshi ya jefa rigar samansa da ya cire hade da jakarsa kan kujera shima ya zauna,a gajiye yake tubus ya soma zare takalminsa da safarsa sannan ya kalli inda ta saba ajjiye masa ruwa da lemo wandayake fara sha da zarar ya dawo,wayam babu sai abincinsa dake jere saman dining,yanmiqe ya bude freezer wanda basu kunnata sosai yanzu saboda yanayin sanyin garin ya ciro ruwan roba,ko cup bai nema ba ya balle murfin ya kafa kai sai da yasha kusan fiye da rabi sannn ya maida ya rufe Bedroom ya nufa don yin wanka hadi da alwala cikin zuciyarsa yana mamakin rashin jin motsi ko yaya cikin gidan,mamakinsa ya dadu ganin babu ita a dakin ya bude toilet babu ruwan wankansa wanda ya riga ya saba ya tadda shi yana jiransa,tunaninsa sai ya tafi ga ko tana kitchen,ya nannade hannun rigarsa ya daura alwala idan yayi sallar daga baya yayi wankan tunda yau bai samu ruwan ba,har ya shimfida abun sallah zai tayar sai kuma ya fasa zuciyars ta kasa samun nutsuwa,sai yakejin wani irin rashin ganinta amma sai ya alaqanta hakan da sabawa da yayi da ganin nataidan ya dawo Kitchen din ya nufa kai tsaye bata nan,wani dim yaji zuciyarsa ta harba💓,ya riga ya sani tunda auke da ita bata taba fita koda qofar gida ne ba tate da izininsa ba,a hanzarce ya koma bedroom inda ya ajjiye wayarsa saman madubi call logs ya shiga da sauri da sauri yana dubawa dinta ko Allah zaisa yaci karo da number dinta,tsaf ya gama bincikensa bai ganta ba,ya saki ajiyar zuciya hankalimsa amatuqar tashe,sai sannan ne ma idonsa ya kai kan 'yar qaramar envelope dake maqale saman wayarsa wanda ke nuni akwai sabon saqo a wayarsa, Har zai maida wauar aljihu sai ya fasa ya jawo saman wayar ya shiga gun sms,numbers ne guda biyu daya ba suna daya kuma ta mr jake ne,yana gama karanta tex din ya tabbatar ita ta turo masa shi baisan sanda ya juya ba ya zira silifas ya fita a sukwane ,da sauri yake daddanna numbobin jumong daya daga cikin direbobin kamfaninsa wadanda suka fi kusa da unguwar da auke ciki yave ya kawo masa mota yanzu yanzu,bai iya ysayawa jiran mitar ba ya fita da qafafunsa yana ji ajikinsa cewa hanyar dawowa ta rasa A hanzarce yake tafiya,kasancewarsa giant ma'abicin kuzari sai gashi yayi tafiya mai dama kafin isowar jumong din Ta waiwayo cikin gudun dai bata fasa ba taqin dake tsakaninta da karen dan kadan ne,ta saddaqar cewa ta gama yawo,tuni tayi surrender ta tsaya cak lokacin da taga ya daka tsalle tana jiran taji ya yago ta,qyam tayi jinin jikinta adaskare,rungumeta taji anyi yayin da qamshin turarensa ya mamaye mata hancinta,tsawq taji ya daka wa karen ta bude idanunta ahankali yayin da dumin jikinsa ke ratsata,sum sum taga karen ya juya cikin sassarfa ya bar gun,sai da ya bace alayin sannan ya juyo ya kalli qwayar idanunta,idanunsa fal da fushi sai huci yake,hannunta ya fincika ya bude bayan motar ya sanyata sannan shima ya shiga jumong ya tada motar Bai ce mata uffan ba kamar yadda bai sake kallonta ba idanunsa na bisa titi har yanzu kana ganin fuskarsa kasan cikin fushi yake,kuka take kanta na qasa ita kanta ta rasa kukan kuma na mene tunda Allah ya taimaketa,sai da suka qaraso gidan sannan ta tabbatar aahe tafiya tayi mai yawa bata sani ba irin haka? Ya bude side dinsa ya fito sannan ya bude nata ya damqo hannunta ya fito da ita,jumong nata cewa"gudnyt sir" amma baibi ta kansa ba,saman kujerar ya cillat yana huci,shi kansa bai san me yasa yake jin wani fushi ba don ta bata hakanan yake jin wani tashin hankali da bai ganta ba,cikin jikinsa yake ji kamar *ZATA IYA GUDUWA* wataran tace zata barashi, Saman kujerar ya dora qafarsa yayin da ya sauke dayar a qasa yana tsayw gabanta,kukanta har yanzu take ci gaba da yi harda dan sautin sheshsheqa,hankalinsa gaba daya ya rabu biyu ,hukunci sosai yake son yayi mata saboda kada ta sake fita har ta bace agaba,yayin da qamshin turarenta keta rarŕaba masa hankali,ya kasa komai kukanta na ci gaba da shiga kunnuwansa,hannu ya dunquke ya daki kujerar da suke kai "keep quiet"ya fadu cikin tsawa,hannu tasa ta rufe bakin nata hawaye naci gaba da silalowa🙊,ya dage girarsà yana fadin"kiwa mutane laifi kuma ki sasu a gaba kina masu kuka?ko don kinga bakinki yafi nawa iya kuka?"ya qarashe maganar da sigar tambaya Ita dai babu abinda tace,kusan minti biyar shiru ya ratsa falon hawayenta naci gaba da silalowa shi kuma yan ci gaba da kallonta yana jin 2ani abu kamar ya zaqe da yawa why?,a hankali ya juya yana barin gurin hadi da cewa "silly girl" Abincin da bai iya ciba kenan a ranar ita da kanta kuma sai taji bubu dadi,koma mene tasan batan ta ne ya bata masa rai shi kuma ya jawo mishi,da bacci ya dauketa ma kan kujera da asuba anan ta farka ta ganta bai tashe ta ba kenan *mrs muhammad ce*👑 📚📚📚📝📝✍🏻✍🏻  [10/16, 1:59 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WA YASAN GOBE?..* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *PART 2* 4⃣1⃣&4⃣2⃣ Kwana uku tsakani tana zaune ya kawo mata foam🗞,gefan ta ya ajjiye bata san na mene ba sai da ta bude sannan ta duba sosai ta gani ashe na wata instute ce, sabon corse ne kan aikin jarida zasu fara wata uku ne kacal za'a kammala,daga qarfe goma na safe zuwa daya na rana,zaka iya attending classes dinsu kokuma ka dauki lecture din online kana daga gida Tsalle ta dinga yi cikin murna bata san aliyyu na tsaye ba qofar kitchen ashe ita ya zubama ido,a hankali suka hada ido tayi saurin komawa ta zauna kunya ta kamata shi kuma ya ya dauke kai ya shige kitchen din,a nutse ta dinga cike foam din har ta kammala da maida cikin envelop 🔅🔅🔅🔅🔅🔅 Sosai fadila ta soma jin dadin karatunta duk da online take daukan lecture ko yaushe tana gaban computer din ta,koda ta kammala daukan lecture sai tayi zamanta tayi ta research,tun daga lokacin da abin ya faru itama bata sake gigin fita ba,iyakacinta gidan nadiyya ita din ma ba sosai don gidan mr lin ma sau daya ta taba leqa mata,sai dai su turo mata yaransu suyita taya ta hira don ma bata gane yaren nasu tafi hira da mashkur don ya iya yarensu na larabci sosai 🔅🔅🔅🔅🔅🔅 Zaman garin yanzun bai fiya takurata ba sosai tun lokacin da ta fara daukan lecture dinta,sosai computer din ta sake zama abokiyarta shi kansa uban tafiyar ya lura da yadda gaba daya walwalarta ta koma kan laptop dinta,haka nan sai ya soma jin haushin computer din gani yake kamar ta tsare masa wani abu da ya rasa mene shi gaba daya bata da wani sukuni sai ta zauna a gabanta Shi yasa wani lokacin da zarar yaga ta dauko da niyyar yin karatu sai ya tsiro wani aikin na babu gaira babu dalili,cikin zuciyarsa yake gulmar "reading like machine"karatu kamar ranta,(hmmm kaji fa gwano baijin warin jikinsa shi da yake wuni zirga zirga da kai kawon bude company dinsa) 🔅🔅🔅🔅🔅🔅 Kamar kullum yauma tara daidai ta kammala dukkanin ayyukanta sabida goma zata zauna lacture,tana sanye cikin kayan sanyi na turawa ta yane kanta da dan qaramin hijabi fari tas iya kafada,shigar orange and white 🔶⚪tayi sai ta haska chocolate colour skin dinta,tana tsaye a dining area tana zuba masa farfesun kan rago cikin plate ta hada masa tea cikin cup☕ don ya dan sarara kafin ya fito Taa cikin rufe flask dinne taji takun tahowarsa ,a dabarance ta saci kallonsa ta gefan ido cikin rashin sa'a ya kamata,da sauri ta dauke idonta ya qaraso dining din ya jawo kujera daya ya zauna hadi da dora briefcase dinsa a dayar ya ajjiye wayarsa kusa da cup din tea📱☕,itama kujerar ta ja ta zauna kamar yadda yakeso kenan idan zaici abinci(🙄🙄🙄 hmmmm) Ta sake satar kallonsa a karo na biyu suka sake hada ido "hold on ur sight"ya fada yana kai cup din bakinshi,sai ta danji kunya ta kamata duk da shi din ma tasan satar kallon nata yayi har suka hada idon,tsakanin jiya da shekaran jiya zuwa yau gani take mood dinshi ya canza,duk da dama bawai mai fara'a ne ba amma taga sauyi cikin walwalarsa da kuzarinsa,hakanan ayyukan da yake tahowa da su yayi ta lodawa cikin laptop dinsa ya ragu sosai Haka nan cin abincinsa ya ragu daga kusan kaso saba'in cikin dari,cikin ranta take ganin bata da wani matsayi gurinsa bare tayi gigin binciken meke damunsa,kamar yadda ta zata kuwa tea din kawai ya shanye ya miqe yana rataye jakarsa ya kuma ajjiye mata yuan 100 kamar yadda ya saba,a hankali yake saukowa daga daga step din dining area din kamar mara laka Tuni qamshinta yayi masa rugu rugu da gangar jiki da kuma zuciyarsa,babu abinda yake buqata a yanzun idan ba mace ba koda samira ya samu ayanzun zai iya maleji da ita,har sai da ya fice sannan ya kauda kanta daga kallonsa ta maida idonta kan table din inda ta hada kayan break,tea kawai itama ta iya hadawa ta sha ta kwashe kayan ta gyara gun takai kitchen ta wanke ta dawo kan computer dinta don yin karatun Qarfe daya da mintina goma sha biyar ta kammala ta rufe laptop din,ta danyi miqa irin ta gajiya tana yar hamma,ta jawo wayarta ta dan duba saqonninta na watsapp na tsawon minti arba'in sannan ta sauka,sallah ta soma yi don biyu tayi sannan ta kwaba alkubus don shi ta shirya yi yau Tana tsaka da aikin nadiya ta shigo nan ta zuba ido tana mamakin me fadilan ke hadawa haka?,dariya fadila tayi tace irin abincimmu ne Sai qarfe uku nadiyan ta tafi fadilan ta rakota bakin qofa tana gaya mata idan ta gama zata ta turo mashkur ya karba mata taci taji,ta saye qofar falon ta koma kitchen din fara aikinta,ta kammala komai da wuri ta gyara gurin ta koma bedroom don daura alwalar sallar la'asar don har tana qoqarin subuce mata Turus ta ja ta tsaya ta kuma saki baki,jakarsa da rigar suit dinsa na watse saman sofa shi kuma na kwance saman gado ko takalmin qafarsa bai tube ba,cikin mamaki take satar kallonsa tana mamakin yaushe ya shigo gidan don ko alamunsa bata ji ba,kuma ma mainya dawo da shi gida a wannan lokacin Rabawa tayi ta shige toilet ta dauro alwalar ta fito ta dauki abun sallarta ta koma falo,bayan ta idar ta koma saman kujera ta zauna sai dai hankalinta ya kasu rabi na kan t.v rabi na bakin qofar bedroom din don har yanzu bata ji motsinsa ba Hankalinta ne ya gaza kwanciya cikin sanda ta miqe ta tura qofar tana leqen saman gadon,har yanzu a kwance yake kamar yadda ta barshi,ta qarasa bude qofar gaba daya a hankali cikin sanda ta qarasa bakin gadon ta duqa ta kama qafarsa a hankali ta zame masa takalman bai motsa ba har ta gama cire masa sai tayi tsammanin bacci yake ta sabule masa socks din ta cusa cikin takalmin ta kwashe su ta maida su muhallinsu Ta juya zata fice ta sake waiwayowa kalleshi idanunsa na lumshe kan hancinsa yayi wani ja irin na farin mutum kamar an murza gun,ta kauda kai ta fice daga dakin,duk abinda take yana kallonta idanunsa biyu,matsanancin zazzabi da yake ji da ciwon ciki mai azaba wanda ya jima rabonsa da shi shi ya hanashi koda yin motsi,yasan yadda ciwon cikinsa yake idan ya kamashi baya masa ta dadi,sai yaji dadin yadda ta sake dawowa ta dubashin ganin bai fito ba,ya tabbata kasa nutsuwa tayi da rashin ganin bai fito din ba Sai da ta shigo daura alwalar sallar magariba sannan ta ganshi zaune kan abun sallah a side din gado duk da bata ga fuskarsa ba kansa na aduqe,ta sake wucewa tayi alwalar Qarfe tara na dare zaman falon ya gundireta ita daya kamar mayya,sabo mugun abune zaman da sukeyi tare duk dare shi ya sanyata kewa ganin yau babu shi duk da ba wani zaman da za'a fadeshi bane kowa harkar gabansa yake duk da da zarar daya yayi wani motsi mai qarfi zaka ga hankalin dayan yayo kansa Sai da ta hada masa coffee ta hada harda abincin cikin babban tray guda daya don har lokacin bai ko leqo koda falon ba bare yaci abincin nasa,ta dauka bayan ta gama shirin kwanciyar ta cikin night gown riga da wando ne wandon har qasa rigar iya gwiwa cotton ne very soft sai hijabi saboda sanyi *Mrs muhammad ce* 👑😘 📚📚📝📝✍🏻✍🏻✍🏻 3:54 pm 5/09/2016 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WA YASAN GOBE?..* *WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* *PART 2* 4⃣3⃣&4⃣4⃣ Ta ajjiye tray din kan bed side tana tunanin ina ne makwancinta yau kuma?,saboda aliyyu na kwancene a kai crossing gadon,bata jin kuma zata iya kwanciyar qasa yadda shi yakeyi domin matsanancin sanyin garin ya girmi qashinta,ta kuma kallinsa karo na biyu yana duqun qune cikin bargo gaba dayan jikinsa kansa ne kawai a waje Sai ta rasa ta yadda zata tada shi tafi qarfin minti goma ahaka kafin dabara ta zo mata,gyaran murya ta taqarqare ta ja har aai da maqogwaronta yayi mata zafi,a hankali ya bude idonsa ya zubesu fes kan fuskarta tsakiyar qwayar idonta,fadila ce ta soma janye nata qwayar idon tana jin wani magnet na fusgarta,tabbas ba don aliyyu mutum bane zata iya cewa wani mayen qarfene cikin idonunsa da duk sanda ta kalla yake fusgarta,cikin ranta taje mamakin yadda fareren qwayar idanun sa kar suka rine zuwa ja Cikin jikinta ta soma jin anya lafiyar aliyyun qalau?,ta kawar da wanna tunanin tana ji a jikinta har yanzu ita aliyyu yake kallo, "na zuba maka ne abincin?" Can qasa ta jiyo shi yace " I don't need",ya maida idanunsa ya lumshe,ta kuma kallon nasa tace "but...." "leave me "ya fada can qasan maqoshinsa cikin katseta,ta ga alamun bai da lafiya ne don haka bata yi zuciya ba tace masa "please ko coffee ne kasha mana" shiru yayi kusan minti uku baice komai ba,hakanne yasa ta gane ya yarda Ta jawo flask din ta tsiyaya masa rabin cup din sannan ta sake matsowa kadan yadda zataji dadin miqa masa "take it pleas",da qyar ya iya miqewa ya jingina da makarin gadon,ta sake miqa masa yasa hannunsa zai amsa ya hade da hannun nata,kamar bashi ya riqe mata hannu ba bai saka ba bai kuma ce komai ba Wani shocking take ji ga kuma dumin zazzabin jikinsa da yake ratsa ta itama,sai lokacin ta sake tabbatar da ashe bai da lafiyar,a hankali ya zame mata hannun sannan ya riqe cuo din sosai ya sale maida idonsa yaumshe kamar ba zai sha ba,illar da turaren ke masa nada yawa haka yake rayawa cikin zuciyarsa,ya sashi cikin wani yanayi nason kasacewa tare da ita fiye da tsammaninsa, Bai damu da dan banzan zafin coffee din ba ya daga kai ya kwankwade tayi saurin amshe cup din ta hada kayan ta maida kitchen ta dawo dauke da cup da gorar ruwa ta dora kan bedside,sai ta tsinci kanta cikin damuwa da cutar yasa duk da bai buda baki yace mata komai game da lalurar tasa ba tasan yana jin jiki,tuni ya kwanta a daya side na gadon ya juya wa ragowat sararin dake bayansa baya A hankali ta haye gadin gami da debe qafafunta ta maida su saman gadon ta rungume gwiwoyinta da hannayenta tana kallon bayansa,tana iya ganin yadda numfashinsa ke sauka a hankali,jikinta ya soma saki bacci ya kamata batasan sadda ta zame ta kwanta ba _*2:30 pm*_ Can cikin tsakiyar baccinta taji ayi mata wani irin mugun riqo,nishi take ji cikin kunnuwanta sama sama dumin numfashin na dukan wuyanta,a firgice ta farka amma ta kasa tashi sabida namijin riqon da yayi mata gaba daya ya cukuikuyeta,da qyar ta samu ta juya tana fuskantarsa,murqususu sosai yake yana hada gumi numfashinsa ke fita da sauri da sauri,tuni ta gigice ganin yadda yana yinsa ya sauya gaba daya,ta tashi ta zauna dirshan hannunsa na riqe da cikinsa idanunsa adamqe daya hannun kuma ita ya zagaye da shi,sosai ta rikice babu abinda yake fadi sai *"ya Allah"* Kimanin minti goma ta shude a haka ta rasa ya zatayi,tunaninta suna da first aid kit a gidan?to koda ma akwai din bazai qyaleta ta tashi ta dauko ba don gaba daya a kanainaye yake ajikinta,dabara ta zo mata da sauri ta miqa hannu ta dauko robar ruwanan da cuo din da dazu ta shigo da su,ta tsiyaya ruwan sannan ta sa bakinta ta tofa masa ayatush shifa ta hada masa da _*allahumma rabbin nas,azhibul ba'asi,wash fi antash shafi,la shifa'u illa shifa'uk,shifa'an la yugadiru saqama*_ Ta dan kalli fuskarsa da tayi ja har yanzu idon ke rufe yana hada gumi "pls can you take it?" Ya dan motsa kadan tasa masa cup din abaki yasha kuwa fiye da rabi Cikin ikon Allah da taimakon ayoyin al qur'ani sai mutsu mutsun da yake ya soma raguwa,riqon tsaurin da yayi mata ya fara sassauta,sai ajiyar zuciya da yakej saki kadan kadan,bata samu sukuni ba sai da taji numfashinsa ya soma daidaita,a hankali jikinsa yayi weak bacci sosai ya daukeshi Ta saki ajiyar zuciya tana kallin irin yanda ya zagayeta da hannunsa,ta tabbatar da a hayyacinsa yake bazai yi hakan ba,gumin fuskarsa har yanzu da saura,tasa lallausan tafin hannunta tana share masa kadan kadan gami da bin fuskarsa da kallo ganin yadda tayi ja alamun wahala,tayi tayi ta janyeshi daga jikinta cikin dabara saidai abun ya faskara yayi mata nauyi ahaka itama baccin yayi awon gaba da ita *THIS IS THE BEGINNING OF*............ *mrs muhammad ce* 📚📚📚📝📝✍🏻✍🏻 [10/16, 1:59 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WA YASAN GOBE?...* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *PART 2* 4⃣5⃣&4⃣6⃣ Yau kam sun makara sosai suka makara don ko sallar daren babu wanda yayi a cikinsu sakamakon bacci da basu samu ba jiya,shi ya fara farkawa ganinta cikin jikinsa ya bashi mamaki,kamar ta san me yake faruwa ta farka itama fuskarsu cikin ta juna,kamar hadin baki da sauri kowa ya janye jikinsa suka miqe a tare,shi ya fara shigewa toilet ita kuma ta shiga na parlour Ta rigashi idarwa tana zaune tana azkar har ya idar,tana zaune har ya kammala nasa addu'o'insa, tadan waiga kadan tana duben gefansa tace "ina kwana" kamar yadda ta saba ba tare da neman amsa ba tunda ta sani ba masawar zaiyi ba don bai taba amsawa din ba,saidai idan yaga dama ya daga mata hannu kawai,saidai yau ga tarin mamakinta karo na farko sai taji ya amsa da "lafiya",ta sake cewa "ya jiki?" Kai ya daga mata,ta tabe baki ta miqe cikin zuciyarta tana cewa"hmm an ma yi yau abun arziqi" tana kallonsa ya sake komawa gado ya duqunqune Bai dade da kwanciya ba wayoyinsa dake gefan gadon suka hau ruri,hannu yasa ya debo su bai daga kiran ba hakanan ba tare da ya duba mai kiran ba ya kashesu duka sannan ya maida su kan side drower hadi da jan bargonsa ya sake rufa 🔅🔅🔅🔅🔅 Tana kitchen tana hada breakfast tajiyo muryarshi cikin parlour yana amsa waya,saidai muryan tayi qasa sosai alamun bai cikin jin dadinsa don bata iya jin abinda yake cewa,cikin rarraba hankalinta da takeyi ne ta yanke hannunta da wuqar🔪 da take rarraba kazar da take so tayi masa pepper chicken ba tare da ta sani ba,wuqar ta shigeta sosai don yankan ba qarami bane,zafin ya ratsa ta har cikin qwaqwalwarta batasan sanda ta saki razananniyar qara ba,jini ne sosai ke zuba ta runtse idonta tana jin azabar yankan Ta bude idonta a hankali suka sauka kansa lokacin da yake shigowa kitchen din cikin sauri,hannun nata da yake digar jini yake bi da kallo,da sauri taga ya ajjiye wayar saman freezer,hannun nata dake digar jini ya riqe yana kalla,wani yarrr fadila ke ji har cikin jininta,shi din ma haka,lallausan tafin hannunta yaso haddasa masa wata sabuwar fitinar cikin jikinsa,yayi saurin sakin tafin hannun nata ya kama tsintsiyar hannun Janta yayi zuwa gaban sink ya kunna famfo ya tara hannun sannan ya barta gaban famfon ya fice da sauri,cikin 'yan sakanni sai gashi dauke da first aid kit,abunda tayi ta tunanin ina yake jiya,spirit ya fito da shi ya janye hannunta daga famfon ya dangwala a auduga ya soma wanke mata kan yankar,zafi sosai take ji yana ci gaba da ratsata ta runtse ido 😣 tana dan yin baya da hannun,cak ya tsaya da wanke matan da yake don spirit din baya samun inda yake so,fuskarta da idanunta ke rufe ya zubama ido har wani abu yaso shagaltar da shi Jin shiru ya daina sawa ya sanyata bude ido,idonta ya shiga cikin nasa suka hadu,wani magnet ya hadu da qamshin turarenta yaso rikita aliyyu ya manta da abinda yake,amma sai yaso nuna mazantaka ya dake har da qarfin halin kaurara muryarsa "stop it,idan baki buqata zan hada kayana,kau da kai tayi don bazata iya jurar kallon qwayar idanunsa ba,ya duqar da kai yaci gaba da wanke mata daga bisani ya rufe mata da bandage don kada datti ya dinga shiga Yana maida kayan cikin akwati ta dan motsa labbanta tace "thanks" "for what" ya fadi ba tare da ya dago kai ba bai kuma tsaya da rufe akwatin ba,she became speechless don haka ta zabi yi masa shiru kawai,haka shima bai sake cewa komai ba har ya kammala rufe akwatin ya dauki wayarsa ya fice Da hannu daya ta qarasa aikin don haka kafin ta kammala duk ta jagwalgwale hannun jinin da ya tsayar mata tuni wani ya soma tsatsatsafowa ta bandejin da ya sa mata,sai da ta gama serving dinsa sannan ya ankara da girkinta ashe ta ci gaba da yi,ya dago ya dubeta tana ta faman hurawa yatsan iskar bakinta,baice mata komai ba ya tashi ya sauka a dining din sai gashi dauke da first aid kit,ta zaro ido cikin tsorata😳 tana tunanin mai kuma zai mata yanzu Sosai ya riqe hannunta gam tana qoqarin zamewa saboda azabar yadda yake daye bandage din da ya sa mata dazun zai canza mata sabo,sai da ya cire tas ya sake wanke mata ya saka mata sabo sannan ya maida kayansa ya kwashe mai jinin ya sauka da su Ya dawo ya soma cin abincinsa yana kallonta time to time yadda take ta qwalla "ko da yaushe kina acting kamar baby" hakanan taji ya fada can qasan maqoshinsa,sai da ya kammala cin nasa taga ya ja plate ya zuba mata komai ya tura mata gabanta, "oya" yace hadi da yi mata nuni da plate din da ido fuskarsa a hade,ta dan langabar da kai gefe don bata marmarin cin komai yanzu sai ta tashi a lecture "am ok,na qoshi" kallon nan nasa ya tsareta da shi cikin tsare gida,ta fuskanci hukuntata yake sonyin da ido,tayi saurin janye idanun ta hadi da sake jan plate da cup din gabanta ta soma ci tana yamutsa fuska cikin zuciyarta tana mitar "ya wani tsare mutane sai sunci abinci sai kace wani abbana lokacin da ina gida" "Good haka abban ke miki saboda baki jin magana kan cin abinci ko?"ya fadi yana fuska a hade yana daga girarsa,da sauri ta dago ta kalleshi batasan sanda tea din da ta kurba a bakinta ya dawo ba,batasan ya akayi yaji abinda take fada ba,anya wannan mutumin ba maye bane?, "am talking to you kin qwalalomin idanunkin nan masu girman tsiya"(lol aliyyu 😜😜😜😜😜) ya fada cikin dan daga murya,kai kawai take girgizawa don babu bakin cewa wani abu,minti biyu tsakani yace "shi yasa kullum store da freezer dinki ke acike kenan basuyin qasa ko?good.....to ni a gidana dole adinga cin abinci.....oya....bismillah ina son naga plate empty" Daga haka ya maida kansa gun wayarsa dake ruri ya fara amsa wayar mr lien,ci take amma sam bata so,da zarar kuma ta tsaya suke hada ido dole take ci gaba da ci,sai gashi taci abinci mai yawa wanda ita kanta ta jima rabon data ci,ta ture plate din tana dan taba cikinta da taji yayi fam tana yatsina fuska yayi mata wani irin qabe qabe babu dadi, "I think u filled your stomach,let me see" ya fadi yana qarashe kashe wayar"qwalalo 😳 ido tayi tana tunanin anya kan aliyyu daya?ciwon cikinsa na jiya kodai ya taba shi?,she dont know why he behaving like dis?,cikin nata zaya ce ta ta yaye rigarta ta nuna masa?,ta dawo cikin hayyacinta lokacin da ya zare mata ido yace "aha show me" ba shiri cikin sanyin jiki ta dage rigar sanyin hadi da shirt din dake ciki,cikinta ya bayyana, ashafe yake tamkar zai hade da bayanta,ya zuba mishi ido,soft skin tata ta bayyana kanta ko ba'a fada maka,wani irin magnet ke fusgarsa,ya dubeta ta tsira mata ido duk a rude take,muryarsa can qasan maqoshinta yace "up" yana ci gaba da kallon cikin,a zaton ta bai gani bane sosai ta dan sake janye masa rigar "up again" ya sake fada,sai ta tsorata don dukka cikin nata ya fito waje da zarar ta sake janye rigar qirjinta(breast) ne zai bayyana Ganin bata sake dagewarba yasa ya dauje idanunsa daga kallon cikin ya maida qwayar idanun nasa cikin nata,ya karanci ta tsargu don haka sai ya waske ya bata rai hadi da janyo warmer yana budewa gami da cewa "no ni banga yayi full ba,don banga ya daga ba" ta marairaice tuni qwalla har ta cika mata idanu "I swear idan ka qaramin zanyi amai wlh Allah haka cikina yake" da mamaki can qasan ransa ya tsaya da abinda yake din,dama akwai mata masu irin wadannan halittar cikin?,ya riga da ya saba da matansa masu tumbi Ya koma ya jingina da kujerar da yake kai yana cewa "ok remove dis items,but be careful with your wound,dama neman mafita taje don haka da rawar jiki ta tashi ta soma gyara gun ,cikin kitchen kitchen tafi minti biyar tana dafe da qirjinta idanunta a lumshe kafin yanayinta ya daidaita "me ya sauya shi haka" can qasar zuciyarta take tambayar kanta *Mrs muhammad ce* 📚📚📚📝📝✍🏻✍🏻 [10/16, 2:00 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WA YASAN GOBE?...* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *part 2* 4⃣7⃣&4⃣8⃣ Ta dade kafin ta baro kitchen din har yanzu yana dining area bisa kujera yana danne dannensa a waya,a falon ta tsaya ta jawl computer din ta ta tafi da gidanka(laptop) ta bude tana shirin kunnawa "hey stop" taji ya fadi cikin wata iriyar murya mai kama da ta mai jin kasala,kasaqe tayi tana jira taji mai zaice "shutdown ur system yau ba daukan lecture,kin mance wound dake fingers dinki ne?" Sai ta rasa mai zata ce tana ganin ai hannunta bazai hanata lecture ba koda guda daya zata iya yi,amma da yake mutum ce ba mai son jayayya ba don haka ta kashe din ta koma ta zauna hadi da zubawa sarautar Allah ido Tana zaune ya shiga ciki yayi wanka ya shiryo cikin kayan sanyi,kan kujerar dining din dai ya koma ya zauna,babu dadewa kuma door bell ta kada,ya dubeta sannan yace "put your hijab" mayafine yafe a jikinta bayan kayan sanyi masu kauri da tasa,nan ma dai bata tanka komai ba ta koma daki ta dauko hijabin,ko da ta dawo su biyu ta tarar shi da doctor yungpho,ta samj kuje daya ta zauna doctor yungpo mutumin china na gaidata cikin harshen turanci Suna gefanta doctor ya gama duk hwaje gwaje da tambayoyinsa,ya dago yana duban aliyyu "sir,sanyin garin mu na son taba ka gashi kana kwanciya a inda zai iya affecting health dinka,ya kamata ka kula saboda kada yayi maka yawa ya zamarmaka illa" "ok" aliyyun yace, "sannan ciwon cikinka ciwon marasa aurene me yasa ya taso maka a yanzu bayan kana da aure?...." da sauri aliyyun ya katseshi yana satar kallonta duk da kanta baya fuskantar gun amma hankalinta na gurin haka nan kuma ta dago wani abu duk da ya katse doctor din Magunguna doctor yungpo ya bashi yana shirin hade kayansa aliyyu yace ya bashi pain killers" ya hada masa duk cikin magungunan,fitarsa babu dadewa aliyyu yasa ta bashi ruwa yasha magungunansa,tamiqa masa ita kuma ta wuce kitchen da zummar dora abincin rana tunda taga alamun da qyar idan yau zaya fita Sai tsintar aliyyun kawai tayi cikin kitchen din ya damqota yayo waje da ita,saman kujera ya zaunar da ita yana ware mata sexy eyes dinsa kamar wata qaramar yarinya "idan kika sake jangwale ciwonki I will wash it again budewa zanyi in sake wankewa no pity ok?" Tayi qasa da kanta tana kallon yatsan nata mai ciwon,muryarta so cool tace "lunch zan hada mana ne" "we don't need" ya fadi yana juyawa "wo hoho Aliyyu.......Aliyyu...." fadila ke fada cikin zuciyarta,ya sata hutun dole kenan?....... Babu karatu babu girki?.....fine" ta fadi tare da yin kwanciyarta saman three sitter Wunin ranar tana zaune ita dai sai gani tayi an kada qararrawa da rana an kawo musu lunch hakanan da daddare,coffee kawai ta faki idonsa ta hada,shima tana dire masa ta bar bedroom din don kada yace zai mata fada,sai da ta kintaci kamar yayi bacci sannan ta koma,cikin sanda ta salallaba ta hau daya side din tana jan bargon zata rufa taji ance "good" ta zaro ido tana shirin sake jin mai fada,jin yayi shiru bai sake cewa komai ya sanyata jan bargo ta lulluba tana addu'o'inta cikin zuciyarta tana yiwa kanta dariya,wato ita mai wayo taqi shigowa ta gudu sai yayi barci ashe idanunsa biyu,ta saki ajiyar zuciya wadda ba don kwanciyar kai da qafa sukayi ba da zai iya jiyota Yafi awa biyu yana yaqi da zuciyarsa,qamshin turarenta ke ban banta masa tunani,ya rasa wace iriyar masifa ce,sosai ya san yana cikin wani hali amma baisan me yasa ta sanadiyyarta yake samun kansa cikin wannan halin ba,sunsha zama haka shi da salima idan ta masa laifi don ya hukuntata,suna daukan tsawon lokaci a haka ba tare da kuma ya damu ba,saidai ita ta gaji ta hanyar gyara laifin da kuma bashi haquri,ya runtse ido,da qarfi yake son tilastawa kansa sai yayi bacci,da qyar wani wahalallen bacci mai cike da mafarkai yayi awon gaba da shi 🔅🔅🔅🔅🔅🔅 Kwana uku tayi babu cas babu as,duk abinda ta dauka zata yi sai yace "stop it,hatta da shara kuwa kawai akan dan yatsanta guda daya,saidai ta faki idonsa ta kimtsa inda taga bai dace ace ana barshi haka ba,da zarar kuwa yazo yaga alamun hakan zai zuba mata ido wanda ta fassara shi da *eyes punishment*,sai ta sunkui da kanta kawai ta wuce sum-sum-sum ta bar gun,kwana biyu yana gida yana jinya babu inda ya fita,sai a rana ta ukun ya koma kan ayyukansa Sosai itama ta rungumi karatunta tana jin dadinshi matuqa ta bashi mahimmanci mai matuqar tasiri don ta sani zai sake jawo mata qwarewa da kuma daukaka ta fannin aikinta,hakanan tana sake samun goyon baya da qwarin gwiwa daga gidajen rediyoyin da take mu'amala da su,su kansu ko yaushe suna fadi mata yadda sukayi missing aikace aikacenta masu cike da inganci da juriya 🔱🔱🔱🔱🔱🔱🔱🔱 _*SANADI*_ 🔱🔱🔱🔱🔱🔱🔱🔱 Cikin nasarori masu tarin yawa dukkan wani shirye shiryen bikin bude kamfanin suka kammala,cikin watansu na uku da sati na uku a qasar ta sin,wanda cikin lissafin da fadika keyi kwanaki goma daka iya zuwa a gaba koma sati guda wato next week zasu iya komowa gida,tun sati uku da suka gabata ta kammala naga coarse din ta kuma fita da sakamako mafi kyau duk cikin daliban Tuni ya sayi injina masu kyau ya aiko da su gida ta container din max air wanda na wasu kamfanoni ne da yakeson budewa idan ya dawo gida a kano cikin rukunin kamfanoni dake sharada industrial area 🔅🔅🔅🔅🔅🔅 Tsaye take a kitchen sauri sauri take ta kammala girkinta saboda yau tayi late sosai,sanye taje cikin trouser na mata sai rigar sanyi in and top ta saqa ce irin saqar turawa,yar cikin har gwiwa take mai gajeran hannu ta saman ce iya qugu mai dogon hannu,wuyan rigar yankan *V* shape ne,ta taje baqi sidik din gashinta mai sheqi ta sake shi ya sauka gadon bayanta,kanta na saye da hular sanyi na mata mai wadda a jikinta yaje saqale da teddy's qananu,shigar dark pink tayi tayi masifar yin kyau kamar wata black American Hankalinta sosai yayi gaba,ta bada duk wani attention nata kan girkinta don hatta dan siririn mayafinta da tadan yafa da hular kansu sun zame don haka ko shigowarsa bata ji ba,fresh milk shi din ma ya shigo dauka hade da ruwa don busy din da tayi yau ya sanya ta mance bata ajjiye masa ba yadda ta saba,wani strong abu yaja hankalinsa sosai game da ita,sai ya koma jikin freezer din ya jingina ya harde hannayensa saman qirjinsa kamar yadda ya harde qafafunsa yana bin duk wani moments nata da kallo Sosai ta tsorata lokacin da ta juyo zata dauki ragowar markadaddun kayan miyan da ta sanya a fridge saboda ganin mutum a tsaye unexpected,tsananin tsoro ya kamata tayi baya zata qwalla qara don rudewa ma bata barta ta kalli fuskarsa ba sai kuma ta taka bawon doya ta zame tana shirin shan qasa saboda santsin tiles da doyar ga kuma ruwa Gaba daya taji ya rungumeta tsam cikin jikinsa yayi hada bakinsa da nata don hanata yin ihun,zaro ido tayi,cikin yan sakanni ya soma kashe mata jiki saboda yadda yake sarrafa bakinsa cikin nata tamkar ya samu sweet qamshin turarenta na dada ingizashi,cikin lokaci qanqani ya soma burkice mata har ya fara bata tsoro duk da ita din ma tana cikin shauqin abinda yake matan,wannan shine karo na farko da ta soma hada jikinta da wani da namiji a rayuwarta Caraf tayi qarfin halin riqe hannunsa jin yana qoqarin shiga wani fage,sai lokacin da ta hada hannuntabda nasan sannan ya soma dawowa saitinsa,cak ya tsaya da abinda yake yi din,cikin sauri ta 6ashi daga jikinsa tana maida botiran rigarta hadi da maida gashinta baya wanda tuni ya hautsine,kunyan da tsoro suka hanata tsaiwa ina zata boye?,bedroom nasu ne su biyu duka,kitchen gashi a ciki,gudu gudu sauri sauri ta nufi qofar ventilation da niyyar ficewa "Hey you" taji aliyyu wanda ke jingine jikin kantar kitchen yana maida numfashi yace "cak ta tsaya ita bata qarasa ficewa ba hakanan bata juyo ba "duba girkinki it burns",sai a lokacin ta tuna doyarta data dora *mrs muhammad ce*👑 📚📚📚📝📝✍🏻✍🏻 [10/16, 2:02 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WA YASAN GOBE?...* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *part 2* 4⃣9⃣&5⃣0⃣ Verry slowly ta juyo kanta a qasa ta kashe gas din ta sulale ta fice ya bita da ido,sirrintacciyar ajiyar zuciya ya saki jikinsa a mace ya juya ya dauki abinda ya kawoshi Tamkar sirikinta haka ya koma mata gaba daya taqi koda kallonsa a haka ta zuba masa abinci ta miqa masa taja kujera ta zauna tana wasa da nata abincin sai jagwalgwalashi take da spoon baice da ita komai ba har kammala nasa,sai da ta miqe tana shirin hade kwanukan ta maida kitchen taji yace "baki isa ba sit and eat" ya tabo mata abinda taqi jini wato ace taci abinci,ta langabar da kai cike da fargabar ya za'a yi ta iya cin abinci yanzu?,ita hasalima tun abin nan da ya mata dazu taji cikinta ya cike amma taga ma shi ko ajikinsa tamkar bashi yayi ba,tamkar ba aliyyun nan ba kamar kullum canza shi akeyi Da qyar tayi spoon biyar ta fara yunqurin amai "stop don't vomit,go" hakan dama takeson ji saboda haka da sauri ta kwashe kayan ta maida su,sai ta kasa zama afalon tayi komawarta daki tayi shirin kwanciyarta ta nade abinta a gado duk da a lokacin bata jin wani bacci,a hankali ta dinga tuna yanayin da suka kasance dazu da aliyun moments din yaqi bacewa daga kwanyarta,unforgettable ta fadi hakan a hankali can qasa,sai kuma wani murmushi ya subuce mata ta cusa kanta tsakiyar filo tana jin kunyar kanta da kanta,qaunar aliyun take ji na sake linkuwa cikin ranta,wannan shine karo na farko da suka taba body contact yana cikin saninsa,ta dinga tuna yanayin qamshi da laushin jikinsa,kamar yadda shi dinma yana zaune a falon ya kasa hasala komai ga ayyukansa nan a gabansa amma ya kasa koda sa password ya bude computer din bare akai ga batun yin aiki,tun barci ma fisgarta a hankali har mai nauyin ya saceta A hankali ta soma ware idanunta saboda jinta da tayi tamkar tana rungume jikin mutum,qamshinsa ne ya bata amsar,a hankali zuciyarta ta tsananta bugu💓 sosai ta gwada yunqurin miqewa saidai ina ya zagayeta ne da hannayensa,ta tsammaci bacci yake ko magagin bacci ne ya sashi yin hakan saidai sanda ta sake yunqurin zare jikinta karo na biyu sai taji shi cikin soft voice can qasan maqoshinsa yace "relax,relax,am not going to do anything with you....just am feeling like am going to froze,I need to warmth my body ar you clear?" Bata ce komai ba ta maida kanta ta kwantar idanunta kan ribbon da hular sanyinta dake watse a gefe da alama shi ya zare mata su don kanshi ya tura cikin gashin yana saukar mata da dumin numfashinsa tsakiyar kanta Ta lumshe idanunta sanda ya sake janta jikinsa sosai ya nutsa zara zaran yatsunsa tsakiyar gashin nata yana sake sheqar daddadan qamshin turaren gashi data ke fesawa kanta wanda ya cakude da na jikinta yana rarraba masa hankali,turarenda bai taba jinsa kan matansa ba,hucin numfashinsa da ta ji ya dawo sauka bisa dokin wuyanta shi ya sake rikita ta,cikin rawar murya tace "a....a....am" tsayawa yayi cak "is there any trouble?" "N....noo" bata san sanda bakinta ya fadi hakan ba,sake matseta yayi cikin faffadan qirjinsa a hankali dumin jikkunansu ya soma ratsasu,sanyin nan mai ratsa qashi ya ragu matuqa,a hankali takejin wani calmness da bata jin irinsa ba na shigarta,hakanan 2ani daddadan barci mai cike da nutsuwa ya saceta Ya saki ajiyar xuciya jin saukar numafshinta alamun bacci ya dauketa,ya ciro daya hannunsa yana sake shafa gashin,sam ya kasa daurewa gashinta na burgeshi matuqa kasancewarsa mai son gashi,yaci gaba da shafa shi yana jin dadin santsinsa cikin tafin hannunsa har shima nasa daddadan baccin yayi gaba da shi cike da mafarkai kala kala 🔅🔅🔅🔅🔅 A hankali ta bude idanunta tadan juya bayanta ba kowa sai qarar saukar ruwa da taji cikin toilet,qarfe biyar na asuba,ta zubawa qofar toilet din ido lokacin da taji an bude ta,aliyyu ne ya fito sanye da rigar towel nan tasa mai budadden qirji,gashin qirjin san nan ya kwanta luf baqi sidik da shi,suka hada ido da shi kansa akwai moisture da alamu wanka yayi na ibada,ta lumshe ido hadi da cusa kanta cikin filo ganin yadda ya kamata dumu dumu tana qare masa kallo,shi kam kau da kansa yayi baiso ta kamashi da yin wanka ba ya dauki jallabiyarsa cumb da perfume nashi ya fice falo,sai da taji ya fice sannan ta zuro qafafunta ta sauko ta shiga toilet din don dauro alwala ta bada nata faralin 🔅🔅🔅🔅🔅 Kamar kowacce safiya tana kitchen tana hada masa break,tayi wankanta ta shirya kamar yadfa ta saba saidai yau ta gaji da sa kayan nasara din haka atamfa ta saka dinkin riga da skert da suka mata cif suka bi shape din jikinta,tana jin shigowarsa lokacin da take juya chips cikin frying pan,addu'a ta dinga yi Allah yasa wani abu yazo dauka yayi ya fice a kitchen din Saidai addu'arta bata samu karbuwa ba don kai tsaye ya nufi ma'adanin plates ya dauki qwaya daya hadi da jawo plastic chair guda daya daga cikin biyun dake ajjiye a kitchen din ya dawo opposite dinta ya zauna, Plate din hannun nasa ya hau miqa mata yana yamutsa fuska cikin shirin fita yake "pls help me kada yunwa ta yimin illa" sai yaso bata dariya yadda yake ta faman turo mata plate din idanunaa kamar zasu fada cikin frying pan din,tuni ta gama karantarsa akwai shi da ci ta amshi plate din ta cika masa shi da chips din sannna ta dora masa waina,dayar kujerar ta jawo gabansa tayi masa table da ita ta hada masa tea ta dauko masa ruwa da drink ta dora mishi gaba daya,ta gama hada tea din ta ajjiye masa ta miqe zata gudu don duk a atakure take jin ta don ta kasa hada ido da shi gaba daya ,rashin kunyarsa ma ita take gani kamar baiyi komai ba harkarsa ma yake free "Thanks" taji ya ambata,cike da shakku da dimbin mamaki ta tsaya cak tana doubting anya su biyu ne kuwa cikin kitchen din nan,don bata gasgata cewa aliyyun ne ya fadi haka ba,don kawai ta hada masa break?,wace irin hidima ce mai tsauri wadda tafi wannan batayi masa ba bai taba yabawa ba ko a ido sai wannan?,sai ta yanke shawarar juyawa don ta tabbatar suka hada ido kuwa lokacin da yake kai chips bakinshi,sai ya tsaya ya fasa kaiwa bakin nasa tare da daga mata gira "yes thank you" da sauri ta juya zata fice don tana tsammanin aliyyu na karantar zuciyar mutum ne "come back,zaki broking rules dina,sai na gama kya fita"kanta a sunkuye ta dawo ta jingina jikin kantar kitchen din tana jira ya kammala 🔅🔅🔅🔅🔅🔅 Yadda wasu lamuran na aliyyi ke sauya salo ke bata mamaki idan yayi wani abun sai ta dinga tambayar kanta anya aliyyu ne?,shi kansa baisan ya canza ba ,sau tari sai ya tsinci kansa cikin sa'ido akan duk wani abu da ya shafeta duk wani movements nata,shi da kansa sai yayi wani abun sai ya koma yana tambayar kansa how comes?,sai kuma ya koma nazarin halaye da dabi'u nata shi kadai idan yana zaune perfect attitude nata,yakan daga kafada yace "perhaps she concern about me I think shine dalili na nima,true?"hakan zaita tambaya da baiwa kansa amsa Sosai aliyyun yayi wani fresh yayi wata 'yar cika data qara masa kyau da kwarjini,ya gama zirga zirgarsa ya dawo gida ya tarar da lafiyayyen abinci da tsaftataccen muhalli kamar yadda yake so,ita din ma yanayin garin ya amsheta sosai don fatarta ta sake yin kyau da santsi ainihin chocolate clour mai kyau, Tun daga ranar sai kwanciyarsu ta koma haka,koda tana wani aikin bata shiryawa kwanciya ba dole sai ta taho don yace mata umarnin likita ne ya dinga samun dumi sosai a jikinsa(lol aliyyu 😜😜),ita din ma bata damu sosai ba duk da yana sata a wani yanayi saboda tana samun dumi sosai wanda ke sata tayi bacci nutsatstse kuma mai tsawo ba kamar da da sanyin ke hanata wani baccin arziqi ba _*ta faru ta qare*_ *to be continued*....... *Mrs muhammad ce*😘 [10/16, 2:00 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WA YASAN GOBE?...* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *PART 2* 5⃣1⃣&5⃣2⃣ Qarfe bakwai na dare ya shigo gidan bayan kammala sallar magariba da kadan tuni ta kammala komai zaune take kawai tana duba saqonninta na email,kamar kowanne lokaci da sallama ya shigo hannunsa daya riqe da rigar saman kayanshi da briefcase dinsa daya hannun nasa kuma leda ce mai dauke da tambarin wani shago da suke sayar da kayan sawa na mata,ta dago idanunta don amsa sallamar qwayar idanunsu suka hadu,ita ta fara janye idanun nata don tasan idan bata janye din ba bazai fasa kallon nata ba, "wani kallo ya koya" haka fadilan ke fada ko yaushe cikin zuciyarta duk lokacin da yayi mata hakan,har wata rana bata sani ba zancan zuciyarta ya fito fili "see you tell me what you think,me zan kalla a jikinki?" Hakan ya fada still kuma yana ci gaba da kallon nata Cikin falon ya qaraso ya zube kayan hannayen nasa saman kujera ya zauna hadi da fadin "ya Allah" sannu da zuwa tace hadi da miqewa don zuba masa ruwan sha kamar yadda ta sabar masa,baisan yadda akayi idanunsa suka bita da kallo ba,material ne ajikinta dinkin riga da skirt,sosai dinkin ya fiddo duk wani sharp na jikinta,yau babu rigar sanyin saboda yanayin sanyin da ya fara ja baya a qasar sai kawai ta kunna na'urar dumama gida ta yafa dan qaramin dankwalin a kanta,tana tsugunne gabansa ta cika cup din da lemo ta miqa masa 🍺 Maimakon ya amshi cup din sai ya hade hannayenta duka biyun da nashi hannayen,dumin tafin hannun nasa ya ratsa har ta qwaqwalwar ta,sosai yasa taji wani na yawo cikin dukkan sassan jikinta,ta miqe da alamun tafiya zatayi ko zai sakar maya hannun maimakon haka sai taji ya finciko hannunta ta fado jikinsa gaba daya tayi dirshan kan cinyarsa,suka saki cup din duka su biyun ya tarwatse saman tiles din yayi pieces Sosai ya matseta tsakiyar faffadan qirjinsa yana cusa hancinsa lungu da saqo na jikinta yana sheqar ni'imtaccen qamshin dake fita ta jikin nata,yamutsa ta yake son ranshi sosai qamshin ke rikita shi,ya dora hancinsa bisa wuyanta hucin numfashin sa ya daketa tsigar jikinta ta tashi,a hankali numfashin nasa ke kaiwa da komowa,tuni ya soma birkita mata lissafi itama kamar yadda shi ya dade da fita daga nasa hayyacin,qirjinta ke bugawa kamar tayi tseren gudu,tuni jikinta ya mutu murus ta kasa wani motsi Qarar wayarsa ce ta katse masa hanzarinsa,duk da haka bai bata damar tashi ba ba tana jikinsa,yayi qoqarin daidaita nutsuwarsa sannan ya daga wayar "I will call you back" kawai yace ya katse kiran tare da jefata kujerar gefansa,yakalli fadilan da idanuwansa da suka canza launi kanta na sunjuye sai maqyarqyata take,sake matseta yayi a jikinsa yana ci gaba da cusa kansa jikinta kamar zai maidata cikin hancinsa,cikin kasalalliyar murya yace" da wanne perfume kike using?"karo na farko da tambayar ta silmiyo daga bakinsa ba tare da ya shirya ba, "am.....amw.....wan"jin gaba daya a gigice take yasa ya saketa, "shiryomin abinci zanyi wanka" a hankali ta zame daga cinyarsa cikin gudu gudu sauri sauri ta fada kitchen ya bita da kallo Gaba daya jikinta rawa yake yana zaune shima a gun har ta soma debo kayan abincin yana lure da ita,ruwanshi yake sha yana bin ta da kallo,sai da ya kusa tashi da roba biyu,har barin miya tayi ta kuma taka ta santsin ya kusa dibarta kadan ya rage tasha qasa sai da ya dan riqeta hadi da cewa "take it easy"sai da ta gama jera abincin sannan ya miqe ya shiga wankan Saman kujerar ta fada tana haki kamar wadda tayi tseren gudu,mirgina kanta kurum take,ta rasa wanne tunani zatayi daga cikin tuna nukan da suka cushe a qwaqwalwarta,me yake son canza aliyyun?ko kuma me ya canza shi din ma? Aliyyun da yace bai sonta?aliyyun da yace bazai taba qaunarta ba koda wani lokacine a anan gaba?me yasa yake son jikinta koda yaushe?bata da amsar kuma babu mai amsa matan Sai da ya ritsata taci abincinta kamar yadda yake mata ko yaushe,ya jawo ledar da ya shigo da ita ya tura mata" I think jibi ne bikin bude company,ga kayan da zakiyi amfani da su nan" "thank you ta fada cikin sassanyar murya kanta a qasa don kallon da yake mata yana takurata matuqa 🔅🔅🔅🔅🔅🔅 Da qyar yake iya jan numfashinsa saboda azabar da yakeji yana ciki,ji yake idan bai kasance da ita ba kamar zai iya mutuwa,shi kansa yaga matuqar qoqarinsa a yadda yana yin halittarsa yake,wata hudu babu wani abu yana cikin matsananciyar sha'awa?,yana cikin matsanciyar buqata mai tarin yawa,baisan sanda ya sanya hannunsa ba ya janyota a gigice ya matseta gam wanda hakan shi yayi sanadiyyar farkawarta,tayi tsam tana jin yadda yake nishi numfashinsa na kaiwa da kawowa da sauri da sauri tamkar yana shirin kufce masa,bata kawo komai ba cikin ranta illa tunanin ko ciwon cikin sa ne ya tashi? A gigice ya birkitota sukayi face to face,lullubeta yayi cikin ingarman qirjinsa,saqonni ya soma aika mata masu zafi da tafiyar da hankali wanda shi kansa ya manta da wasu sai a alokacin,tuni saqonninshi suka girmi hankalin fadila,ganin yana neman wuce gona da iri ta soma yunqurin qwatar kanta cikin kasala saidai sam ko motsawa ta gaza yi ya aza mata nauyinsa,loko sa saqo ya dinga bi yana lashewa hadi da rabata da duk wani abu da zai raba tsakaninsa da fatar jikinta Tamkar a mafarki take gani,sosai taga lamarin na aliyyu da gaske yake gaba daya kamar baya duniyar ya gama fita daga ainihin aliyyun ya burkice mata baya ji hakanan baya gani,tabbas yana so ya mata abinda ta dade tana tsoro da fargabarsa,ganin dan qarfinta bazai amfana mata komai ba sai ta koma magiya da roqonsa yayi haquri,tamakar da dutse take magana ko wani kurman bebe,tuni ya gama rabata da komai na jikinta sai 'yar mitsitsiyar vest da ta rage ajikinta wanda ita kadai dama ta sanya don bata kwanciya da brassiere sai tasa vest mai dame jiki, "pleeeeaaaaseeee aliyyu zaka jimin ciwo,pleeaasee kayi haquri don Allah" hannu tasa tana rufe qirjinta saboda babu wani abu da vest din ta kare na surar qirjinta,dukiyar fulaninta ta cicciko cikin vest din sunyo Da hannunsa daya yasa ta riqe hannayen nata biyu yasa daya hannun ya tsarge vest din gida biyu ya zareta ya wurgar,tuni dukiyar fulanin ta bayyana,wani iriyar gigicewa yayi laushi da santsin fatarta ya kusa zautar da shi,bai taba karo da qirar da ta taba tafiya da imaninsa ba irin ta fadilan tuni ya sake haukacewa kamar mayunwacin zaki,kamar akuyar da ta shiga garken tumaki,magiya da roqon taga sunqi tasiri gaba daya akan aliyyu sai ga barke da kuka,a hankali ya dinga lashe duk wani hawaye da ya biyo kuncinta bai bari ko guda ya diga a aqasa ba,sannu a hankali ya dinga kashe mata duk wata gaba ta jikinta da wani irin salon soyayya da bai taba gwadashi kan wata diya mace ba,komai nata ya saki ya zare mata duk wata ragowar qarfi da kuzari da ya rage mata Sai da ya soma aiki tuquru sanan ta soma gane kurenta,ihun kuka ta soma saki a maimakon hawaye zallah,kuka take mai hade da ihun,hawaye da majina kuwa tuni suka hada kogo bisa fuskarta,cizo da yakushi kuwa har sai da ta gaji don kanta,tuni yayi nisa cikin duniyar da bai taba koda giftawa ta kusa da ita ba,ya shiga wata duniya mai wuyar fassarawa a gareshi,tuni sukayi hannun riga da wani abu da ake kira hankali,tun fadila na fahimtar halin da take ciki har ta soma gane komai a hankali idanunta suka rufe duhu ya mamaye mata idanu,dif komai ya dauke mata ba tare da aliyyu ya sani ba Gefe ya koma ya yashe tare da matseta gam cikin jikinsa ji yake kamar ya tsaga qirjinsa ya maidata ciki,sosai ya rushe da wani irin kuka tamakar qaramin yaro,karo na farko sa hawaye ya zuba a idanun Aliyyu haidar ta silar fadila tun bayan da ya mallaki hankalin kansa,tuni hawaye sukayi male male bisa fuskarsa fadi yake a zuciyarsa har ma a fili "alhamdulillahil lazi bi ni'imatihi tatimmus saalihat (godiya ta tabbata ga ubangiji wanda da ni'imarsa ne abubuwa masu kyau suke cika)ashe har yanzu akwai mata masu kai budurcinsu gidan mazajensu?ashe zai samu wannan abun mai daraja?ashe dama babbar kyauta Allah yayi masa?ashe baiwa ce babba a cikin gidansa bai sani ba?ashe gata abbansa yayi masa?ashe soyayya abban nasa ke masa ta gaskiya?....ashe din ta aliyyu a lokacin mai dama ce,nadamarsa mai tarin yawa ce,kuka yake sosai da hawaye masu tarin yawa kwance bisa fuskarsa Wani abu mai girma yaji yana ratsa shi game da ita wanda tunda yake bai taba jin makamancin hakan ba,ya dago da fuskarta yana kallonta,wani tausayi so da qauna girmamawa da kunyarta suka rufeshi masu tsananin tasiri,ga shatin hawaye nan bisa fuskarta da suka bushe sukayi alama,sai a lokacin yaji baijin sukar numfashinta,yatsunsa ya sanya saman hancinta yaji dif babu alamun fitar numfashi,a gigice ya zareta daga jikinsa ya wuntsulo daga kan gadon da gudu yayi parlour,freezer ya bude ya dauko ruwa,jikinsa na rawa ya balle murfin ruwan ya kwarara mata kan fuskarta,wani dogon numfashi ta ja hadi da saukar da ajiyar zuciya mai nauyin gaske,muryarta can qasa qasa yadda bi jiyota sai da ya zauna tsakiyar gadon ya dagota ya mannata da jikinsa yaji tana fadin "please kayi haquri kada ka qara" qwaqumeta yayi ya dora habarsa tsakiyar kanta "relax am not going to repeat it" jikinsa shi kansa rawa yake har yanzu,ajiyar zuciyar yake saki shima a kai a kai tamkar marayam da ya ci kuka ya qoshi,kana kallonsu a lokacin dukkansu sai sun baka tausayi dukkansu sun koma kalar tausayi Azabar da fadilan keji ya sanyata sakin wani sabon kukan mai ban tausayi,radadi sosai take ji kamar ana yankarta a gun,sake rufe ta yayi ruf da qijinsa yana cewa cikin rawar murya da ta jiki "am sorry fadila am sorry please" Duk da tana jin jiki kalaman sun bata mamaki,aliyyu?,aliyyu ne?"a hankali yake dauke hawayen nata da harshensa yana shanayesu gami da shafa kanta zuwa bayanta alamun lallashi yana fadin "am sorry...am sorry"abunda bakinsa kawai ke iya nanatawa kenan kamar karatun sallah,sunfi minti arba'in a haka dukkansu suna sakin ajiyar zuciya,ita bacci ya fara dauka don shi kam ko alamaunsa bai ji,a hankali ya zamar da ita ,ido ya zaro ganin yadda jini yayi face face kan farin bedsheet din,tausayinta ya sake kamashi,shi kansa yasan bai mata kadan ba,ya riga ne ya fita daga hayyacinsa,hannu yasa ya yaye shi gefe ya kwantar da ita a ahankali don kada ya tasheta yaja mata bargo ya lullubeta,yasa hannunsa ya kama mata gashinta da ya yamutse gaba daya ya daure mata shi guri guda,fuskarta da tayi fayau ta bayyana a dan hasken fitilar gefan gadon Zaman dirshan yayi yana gadinta duk wani motsi nata na kan idonsa,ranar duk qwarewar bacci kan iya sata haka ya haqura yabar aliyyu,har asuba yana zaune dirshan idanunsa na kanta tana wani wahalallen bacci *mrs muhammad ce* 📚📚📚📝📝✍🏻✍🏻 [10/16, 2:03 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WA YASAN GOBE?....* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *PART 2* 5⃣3⃣&5⃣4⃣ Jinta kawai ruwan zafi na ratsata,a gigice ta farka saboda azabar zafi,a rude ta qwalla wata gigitacciyar qara duk da muryarta a da she take,ta riqe hannunshi sosai tana sheshsheqar kuka "calm down please,u wil get fine,pain din da kike ji zai ragu" ya fadi cikin taushin murya da kwantar da kai,ba yadda ta iya haka ta maida jikinta tayi laqwas tana jin yadda zafin ruwan ke ratsata har gun ciwonta,a hankali ta dinga jin zafin na dan raguwa sai a lokacinne kuma ta fara lura ashe haka aliyyun ya sunkutota babu komai a jikinta,hannu tasa tana kakkare qirjinta Shi din ma tun dazun yake qarewa halittarta kallo tana ci gaba da attract nashi ji yake kamar ya maidata ruwa amma raunin da yayi mata shi kansa ya san yayi barna,hankalinsa ya bar jikinsa ne however ma baiyi zaton zai sameta da virginity dinta ba,sai da yayi matuqar kai zuciyarsa nesa kan fadilan saboda yadda surarta ke fusgar hankalinsa,ba halitta ce da zaka iya kalla sau daya ka kau da kanka ba,wanka yayi mata ya nadota a towel kamar wata baby ya maidota daki,kunya babu kalar da fadila bata jita ba yau,shi yasa mata pant har da brassiere tana ta ture hannunsa kan ya qyaleta zata sa saidai yace "am sorry ki barni kawai,ba zaki iya komai ba" ta rasa wacce iriyar rashin kunya ce da aliyyun,doguwar riga ya zira mata harda hijabi ya shimfida mata dadduma sai da yaga ta hau sallayar sannan ya shiga nasa wankan A kwance ya dawo ya taddata kwance saman abun sallar,komawa taga yayi ya ciro wasu capsule ya zaunar da ita ta sha sannan ya tayar da sallah,tuni bacci ya sake dibarta kafin ya idar nan kan abun sallar ko azkar din ma bata samu tayi ba,cak ya dauketa a hankali don kada ya yada ta kan gadon ya maidata ya zare mata hijabin sannan ya ja lallausan bargon ya rufeta zuwa wuyanta,zaman dirshan yayi kusa da ita yana kallonta tamkar an bashi assignment a kanta,wani abu ke ci gaba da ratsa zuciyarsa,sosai baya ga qauna yake jin qimarta da darajarta na sake linkuwa cikin zuciyarsa,tunaninsa mai zaya mata a duniya tukuici zuwa ga tarin kyautatawarsa gareta?,me zaya mata wanda zai saka mata kan wannan baiwa tata yau da ta masa kyautarta dungurun gum,kyautar da bai taba katari da makamanciyarta ba?,dame zai faranta ranta da shi a fadin duniya?,she deserve anything Qarfe takwas na safiya a gogon garin har lokacin baccinta take gashi fitar dole ta kamashi saboda yau baqinsa zasu soma isowa,dole shi zai kama masu hotel da zasu zauna andi kuma aikin da ya basu yayi yawa bare ya hada masu da wannan,ga mukhtar (abokinsa ne na kusa)bai qaraso qasar ba bare ya hada shi da aikin,don haka fiya ta kamashi dole,idan banda wannan dalilin kam baijin akwai abinda zai fidda shi daga gidan yau,ya gama shiryawa tsaf cikin suit kamar yadda ya saba sai da ya shiga kitchen ya hada mata tea ya zuba cikin flask ya soya mata chips da qwai ya hada da cups yayi dakin don kada ta tashi babu abinda taci,ya qaraso bakin gadon bayan ya ajjiye tray din kan 'yar locker din nan ta bedside yana sake kallonta,baccin take kawai ko motsawa batayi,shi kansa yasan dole ne kam tayi bacci,ya zira hannunsa a hankali ya sake maida mata gashinta gefe,karon farko cikin nutsuwarsa ya sanya tattausan lebensa ya sumbaci goshinta sannan ya maida leben nasa saman nata leben masu taushi da siranta,ya dan jima yana sheqar hucin numfashinta dake shiga hancinsa yana masa dadi yana jin kamar tana qara masa wata ruyuwar ne ta musamman Hot kiss ya bata wanda sai da yasa tadan motsa kadan ya miqe yana sake kallonta tare da hade tafin hannunshi da nata,baya son fitar ko kadan,ya sani tana da buqatar kulawa,sai da ya qoshi da kallon nata sannan can qasan maqoshinsa yace"i will back soon" tamkar yana magana da wadda ke idanunta biyu,ya fice a dakin yana waiwayenta hadi da ja mata qofofin gidan Cikin ayyuka yake da mutane saidai duk wani motsi da zaiyi qwaya daya tana manne cikin zuciyarsa,kaf hankalinsa na gida gangar jikinsa ce kawai a nan,har wasu abubuwan mancewa yake maimakon ya fadi sunansu sai yace "fadilah",sai kuma yace musu "am sorry I mean kaza.....",Allah Allah yake ya kammala abinda zaiyi ya koma gida saidai yana murna ya kammala sai kuma wannan ya bullo dole haka yake sake zama yayi settling Da kanta taji ta qoshi da baccin ta farka bakinta dauke da addu'ar tashi daga bacci *"Alhamdulillahil lazi aa faani fi jasady waradda alaiyya ruhi wa'a zina li bizikrihi"*,tayi niyyar miqewa kamar yadda ta saba saidai jin yanayin jikinta da ya canza shi ya tuno mata abinda ya faru da ita jiya tsakaninta da aliyyu Daki daki komai ke dawo mata,tana tuno moment din tar cikin kwayarta *"wanne turare kike amfani da shi?"* tambaya daya da ya maimaita mata ita sau biyu kenan a jiya,sannu a hankali tunaninta game da turaren ya soma dawo mata *"hasbunallahu wa ni'imal wakeel"* ta fadi cikin zaro ido da matsananciyar faduwar gaba,da sauri ta diro a gadon tuni ta mance wani ciwo da take,kai tsaye gun jakarta ta nufa inda taje rataye,tasa hannu ta cirota cikin rawar jiki ta soma laluben turaren ta ciroshi hadi da zuba masa ido tamkar yau ta saba ganinsa Da sauri ta daga jakar ta zazzage ta kafataninta,dukkayan ciki suka zubo,tarkacen magunguna da suka siya ne gun fa'iza,wannan turaren da nake shafawa shine?shine wannan turaren mahadin magungunan?" Jakar ta saki qasa hadi da komawa baya ta zauna kata ta dafe hadi da sakin wani irin kuka mai cin rai, _*"saboda sha'awa aliyyu ya tara da ita ba don so ba?turare shi ya ja hankalinsa kanta ba qauna ba?me yasa nayi gaggawar baiwa aliyyu kaina ne?me yasa na amince na yaudari kaina? Tabbas aliyyu bai sona kuma ta yarda bazai taba sonta din ba"*_,jikinta ne ya burgeshi ko me? Ta ci gaba da fada cikin zuciyarta,tuni ta gama sarewa,ta gama yankewa kanta qauna da zama tare da shi,babu irin abunda bata gwada ba amma babu nasara to sai yaushe?sai yaushe nasarar zata zo mata ne? Da gaske kenan hasashen anty hafiza na zai soki fadila wataran son da bai taba tsammani anawa wata diya mace irinshi ba,ai babu *wanda yasan gobe sai Allah* ya zama mafarki........?,tana jin wannan karon ya zama dole ta zare aliyyu daga cikin tsarin rayuwarta,ya zama dole ta rabu da shi haka nan ya zama dole ta nisanceshi,ta gama yin duk abinda ya kamata tayi.....ta gama duk abinda zata iya....ta gama bashi kuma duk wani abu da take da shi,kulawa.....tattali....tausayi da soyayya......kai harma da jikinta da zuciyarta gaba daya amma aliyyun ya gaza samuwa,to me yayi saura?,bata da wani ragowar abun bashi banda ta bar masa sararin rayuwarsa itama ko ta samu salama? Cikin azama tamkar ba mai ciwo a jiki ba ta hada kan kudaden(yuan) da ya jima yana bata su har take ganin basu da wani amfani a gurinta,ta bude locker da ta ajjiye passport dinta ta dauka,har ta juya tana shirin fita sai ta dawo da baya a hankali,ta yagi paper cikin takaddunshi ta dauki biro ta ja dressing chair ta zauna,tafi minti biyar da dora alqalamin kan takaddar saidai hawayen da ya cika mata ido ya soma diga kan takaddar ya hanata ganin komai,ta miqa hannunta ta yago tissue ta tsane hawayen sannan ta samu damar ganin ta,cikin kasala kamar mai ciwon 'yan yatsu hannayenta suka soma rubuta abinda ke qunshe qasan zuciyarta *amincin Allah a gareka* *duk da na sani cewa saqona ba wani abu bane da zai dameka ba,domin kuwa ina tsammani irin saqon da ka dade kana tsammani daga gareni* *aliyyu na soka irin son da ban taba yiwa wani halittar da namiji ba a duniya ba,na soka tun kafin na gama sanin wane ne kai,na soka son da ban yiwa kaina shi ba,na soka a fili na soka a boye* *saidai kash! Aliyyu ka qini qin da ban taba ganin ka yuwa wata halitta shi ba,ka tsaneni tsanar da na gaza canko mai na maka da zafi haka a rayuwa?,ka qinin ne kamar yadda ka fadamin gaskiyarka tun farko kace baka sona kuma ba zaka taba sona ba hakanan kada nayi tsammanin kuma cewa wata rana ko anan gaba zaka soni* *A lokacin na dauki zancan tamkar tatsuniya,na dauki zancen tamkar wani labari da wata rana zai iya shafewa ya gushe,ashe na tafka kuskure,nayi kuskure ba dan qarami ba,nayi abinda ni zan gushe ba zancanka ba,ashe ba zaka sonin ba har abada kamar yadda kace din,naji...na gani na kuma gamsu aliyyu...dama hausawa sunce jiki magayi,haka din ne ni ganau ce ba jiyau ba* *a yau na rabu da kai aliyyu kamar yadda kake bege....na fita a rayuwarka kamar yadda kake muradi.....,wata qila lokacin da kake karanta wannan saqo na dade da fita daga rayuwarka,kuma na yima alqawarin fita fita ta har abada.....koda sonka zai samo sanadiyyar daina numfashina a duniya,I promise I leave yiu forever.........😔* *na sani ko ban roqeka ba abu ne mai sauqi in samu sakina daga gareka,to ina fata zata zamo rubuce jikin takarda don samun shaida ta kuma samu isuwa zuwa ga magabata na,na gode da jurar zama da kayi da halittar da baka so cikin inuwa guda.......na gode da da ci...sha.....suttura da ka dinga bani ba tare da zulunci ko gajiyawa ba thanks for everything,na gode na gode....🙏🏻* *fadila Abbas bashir* Ta ninke wasiqar cikin wani irin kuka mara sauti mai azabar cin zuciya da azabtar da rai,gefan pillow din da ta tashi ta ajjiye ta,cikin azama ta rataya jakarta ta fito hadi da jan qofar gidan,tana son koda sallama ne tayi da maqotan arziqi nadiya da mr lin amma bata son su fahimci wani abu har suyi yunqurin tsaidata,zuciyarta ta riga ta qeqashe duk radadin da ciwonta ke mata hakan bai dameta ba burinta kawai ta baf qasar,burinta ta fice a qasar ta china da take kallonta baqiqqirin Tana bayan taxi din ta ciro katin tana dubawa ta fada masa address din inda zai kaita branch ne na kamfanin ethopian airline taje ta fara rage bucking tunda tim din fitarta a qasar bai cika ba,cikin lokaci qanqani suka qaraso tace masa ya jirata yanzu zata fito Tana tsaye a gabansu cike da matsananciyar damuwa tana ta sharar qwalla,tsananta adsu'arta take ya Allah yasa ayau ta samu damar ficewa a qasar,burinta kawai ta nisanci aliyyun,bata son ta ganshi bare sonsa yasa ta karaya ta ci gaba da zama da shi,ma'aikacin dan qasar sin din na sake sauri gun duba mata jirgin da zai tashi yana sake bata baki cikin yaren English kasancewarsu masu girmamawa da tausayi ,cikin sa'a aka samu saidai zai sauka a ehopia kamar yadda aka saba sanann ya qarasa da su nijeria garin *kano*,sit daya ne ya rage suka gaya mata kudin da zasu cajeta suyi mata printing ticket?,cikin sauri ta gyada masa kai tun kan ya kammala printing din ta fito da kudaden ta ajjiye masa a gabansa,yana miqo mata da rawar jiki ta karba tana duba time da jirgin zai tashi awa guda ta rage mata *mrs muhammad ce*👑 📚📚📚📝📝✍🏻✍🏻 [10/16, 2:04 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WA YASAN GOBE?...* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *PART 2* 5⃣5⃣&5⃣6⃣ Da sauri ta koma gun mai taxi ta shige gidan gidan baya tana bashi umarnin su wuce airport,koda suka je kasa zaune tayi babu abinda take banda duba agogo hadi da sharar qwalla 🔅🔅🔅🔅🔅🔅 Da qyar aliyyu ya samu ya yage aiki da kuma jama'ar dake dakonsa,ya bawa jumong umarnin ya maidashi gida,cikin motar ya zaro wayoyinsa ya kira lukas yace kada a nemeshi ko menene ya taso shi ko mukhtar yayi handling dinsa,ya wuce gida ne madam ba lafiya,cikin girmamawa ya amsa masa,ya cire wayar daga kunnensa ya hada da wadda ke ajjiye kan cinyarsa ya kashe su gaba daya,ya zuba su cikin 'yar jakar laptop dinsa Jumong ya tsaida motar aliyyun ya fice,jumong din nata yi masa sallama amma hannu kawai ya iya daga masa ya shige gidan,fuskarta kawai yake da muradin kallo,ita kadai yake son gani,ta bashi wani abu mai tsada muhimmanci da daraja agun 'ya mace,ta bashi abunda ya kasa samu shekaru masu dama,abinda ya debe tsammanin ana samunsa gun matan yanzu,yana jinta sosai cikin jikinsa zuciyarsa ruhinsa...yana kuma jin wani matsayi da daraja mai girma nata cikin idanunsa Wullar da jakar tasa yayi kai tsaye ya nufi bedroom don yafi tsammanin samunta a can,yanayin yadda dakin ya dan yamutse ya danji mamakin ganin hakan,saboda bai saba gani ba ko tsinke bai taba katarin tsinta cikin kitchen dinta ba ballantana bedroom,to amma bai kawo komai cikin ransa ba sai ya dan ganta hakan da yanayin raahin jin dadin jikinta,saboda haka ya juya ya koma ya duba kitchen,shi yana nan kamar yadda ya barshi da safen babu wani abu da ya canza,sai ya sake komawa bedroom din yana bawa ransa tana toilet to Gefan gadon ya zauna yana zaman jiranta wanda daidai yake da a kirashi da zaman jiran gawon shanu,har sai da ya dan soma qosawa ya miqe bayansa sama gadon fuskarsa na kallon ceiling,sai yaji qayau qayau kamar ya kwanta kan wani abu,yasa hannun nasa qasan bayansa ya zaro ta yadan jujjuyata sai ya wullata daya gefan gadon,ya mirgina kansa da niyyar duban qofar toilet din sai idanunsa suka sake kaiwa kan takaddar,sai ya tsinci kansa da son budeta yaga mene a ciki don bata barin komai saman gadonsu Yana daga kwancen ya jawota ya warwareta yakai idanunsa ciki ganinta cike taf da rubutu ya bashi mamaki,paragraph din farko kawai ya karanta sai gashi zaune dirshan tsakiyar gadon ba tare da ya san yaushe ya tashi ba,kafin aliyyu ya kammala karanta saqon tuni ya jiqe da gumi duk da ragowar sanyin dake qasar ta sin,ya kammala karanta layin qarshe na takardar gami da cukuikuyeta cikin tafin hannunsa da qarfi,rawa kawai jikinsa yake tamkar sojan da aka bugawa kugen yaqi,launin idanunsa tuni sun canza daga ainihin fararen nan qal masu haske zuwa jajaye,babu launin na alamun tashin hankali a lokacin da bai bayyana bisa fuskarsa ba,tsananin tashin hankalin da yake ji a lokacin bazai misaltu ba "why?why fadilah?me yasa kika yimin gurguwar fahimta?,me yasa kika fahimceni a abaibai?,ina zaki tafi?ina zaki tafi ki barni?,ba haka bane fadilah....ba haka bane abinda kike zato"shi kadai keta wadannan sumbatun ya dunqule hannayensa cikin junansu takardar na tsakiya Wurgi yayi da takardar,tamkar an zungureshi ya fice daga dakin cikin matsanancin sauri,"ina zata yanzun?batasan kowa ba cikin qasar? " Tambayar daya takura yake ta faman nanatawa kansa ita bayan yasan shi kansa ba sanin amsad yayi ba,yana gab da fita a gidan wani tunani ya fado masa,cikin zadin nama ya juya ya koma ,kai tsaye inda yaga passport dinta shekaran jiya ya nufa ya hau dubawa wayam baya gurin,cikin zafin nama ya juya ya fice daga gidan,taxi ya tsayar ya shige shaf yama manta da cewar ana gayawa mai abun hawa inda za'a,gani yake ma tamkar taxi driver din yasan inda zai kaishi,saida yayi ta nanata Tambayar inda zai kaishi sannan ya tuna ya gaya masa airport zasu je Safa da marwa take cikin departure din,hankalinta a tashe yake gani take tamkar aliyyu zai biyota ne ya hanata tafiya,wani bangare na zuciyarta ke tunatar mata babu yadda za'ayi aliyyun ya biyota,abunda kake qauna shi kake nunawa kulawa da damuwa da halin da kake ciki,koda sace ta akayi bata tsammanin aliyyun zai biyo sawunta bare tafiya tayi da qafafunta,duk da haka hankalinta bai kwanta din ba sai da suka hau layin shiga jirgi,ko anan din ma bata fasa sharar hawaye ba,sam bata damu da yadda jama'ar keta kallonta ba har wasu kan gaza shiru suce mata "sorry" kallon da suke mata bai dadata da qasa ba don ji take tamkar ansa mata wani hijabi ne cikin zuciyarta,tuni kowa ya kama sit din sa ya zauna tana sit 34 A,sanarwar daura belt ta biyo baya bayan an rufe qofar jirgin,a lokacin ta tuna tahowarsu da aliyyu qasar ranar da ta kasa daura belt dinta,kuka ne sabo ya sake qwace mata *kukan baqincikin rabuwa da shi ne ko kuma na farincikin rabuwa da shi ne?kukan shaquwa ne ko kuwa na kewa ne?* oho ita kanta bata sani ba,ita dai kawai ta tsincin kanta tana yinsa,a hankali jirgin ya soma qugi yana motsawa sannu sannu har ya ware sosai ya fara shawagi kan kwaltar dake doron qasa Ko ta kan security dake ta tareshi da tambayoyi bai bi ba har sai fa ya dangane da inda yake son zuwan,duk ma'aikatan gun suka miqe saboda girmamawa don tuni garin na guangzhou ya soma gane wane aliyyu cikin qasar ta sin,sanarwar bikin bude katafaren kamfaninsa ya riga ya karade ko ina cikin qasar,cikin sakanni qalilan ya basu umarnin duba masa list na sunayen mutanen da suka tashi zuwa Nigeria tun daga safe zuwa yanzu,girmansa yasa suka masa haka don kuwa ba kowa ke samun haka ba sai idan jami'in tsaro ne da kyakkyawar shaidar neman wani mai laifi Tafi yafi har suka zo list din qarashe wanda suka sanar masa jirgin yana daf da cillawa sama,daga qarshe sunan fadila Abbas Bashir ya bayyana,cikin azama ya dakatar da su yana fadin"mai wannan sunan nake nema" "ai tana cikin wadanda jirgi zai daga da su nan da yan sakonni" cikin sauri ya tashi yana fadin yana son a dakatar da tashin jirgin,cikin girmamawa yace "sorry sir bazai yiwu ba mun riga mun gama handling din komai,duk ma'aikatan mu sun san da tashin nasa,haka na qasar da zai sauka" da qarfi ya doki sama table din cikin zafi yace " I said stop the flight now!!!" Ya sake rusunar da kansa yace "sorry sir it can't,but idan kana buqatan tafiya zuwa nijerian ne sai amaka printing ticket" Ya harde hannayensa a qirji ya lumshe ido yana maida numfashi,shi kadai yasan yadda zuciyarsa ke masa zafi da quna,shiru yayi tamkar baza ya furta komai ba "hasbunallahu wa ni'imal wakeel" yake karantawa cikin zuciyarsa,a hankali ya soma jin temper din na nasa na raguwa,still idanun nasa na alumshen yace"ok ina son jirgin da zai kuma tashi anjima" "sorry sir yau babu jirgin da zai kuma zuwa nijeria" "gobe da safe " "sai da yamma sir" "noooo!!!" Ya fadi sa qarfi hadi da bude idaunsa wadanda suka kuma zama manya ya ware su sosai kan ma'aikacin,ya sake dan rusunar da kansa gami da cewa"sir sai da yamma kayi haquri"shirun ya sake yi yana ci gaba da kallonsa,cikin ransa yake dana sanin rashin mallakar jirgi na kansa da yaqi yi a baya bayan yana da damar hakan,sai da ya gaji don kansa sanan ya sanya hannu cikin aljihunsa ya fito da kudi wanda baisan nawa bane ya ajjiye masa,ya miqa masa ticket sannan cikin sauri ya irgi kudin su ya muqawa aliyyun sauran saboda gudun kada ya karya dokar qasarsa,wani irin wawan kallo aliyyun ya watsa masa wanda ya sashi janye hannunsa shi kuma ya fice abinsa Tafiya ce mai tsawo tamkar a zuwan ta kawosu airport din addis ababa,hamdala tayi da taji cewar nan da awanni biyu jirgi zai sake kwasarsu ya miqa su nijeria kanon dabo babu batun kwana kenan a ethopia,hakan yayi mata dadi sosai don burinta kawai shine ta bude idanunta ta ganta cikin nijeria zuwa lokacin idanunta sun sake yin luhu luhu saboda kuka wanda ta kasa tsaida shi 🔅🔅🔅🔅🔅🔅 Qarfe takwas na dare agogon nijeria jirginsu fadila ya landing cikin aminu kano international airport,sannu a hankali passengers suka soma saukowa,tun sanda suke kusa da sauka ta soma tunanin ina zata nufa?gata dai a nijeria?,ba zata nufi gidansu ba ko giyar wake ta sha,ta sani idan dai har taje din babu shakka babu ruwan abbanta ko umminta zasu maidata ne gidan aliyyu hankali kwance,ta tabbata ko ta bakinta ba zasu buqaci ji ba,bayan ta riga ta yiwa aliyyu da ita kanta alqawarin yanke zamansu,ta masa alqawarin yin nesa da rayuwarshi,a yanzun bata da muradi ko digo kan ci gaba da zama da shi *"ta inda aka hau ta nan ake sauka"* haka zuciyarta ta gaya mata,take ta amince da batun zuciyar tata,ta yiwa daya daga cikin direbobin airport din magana kan inda zaya kaita,take ya amince tare da tsula mata kudi,bata damu ba ko a duska din ita ba wannan ne a gabanta ba,ba ta wannan take ba ta kanta kurum take yi Har a lokacin hawaye bai daina bin fuskarta ba kamar yadda bata fasa gogeshi ba,har ta soma jin babu dadi saboda kukan da take,har qofar get din gidan mai taxi din ya ajjiyeta,ta fidda kudinshi ta bashi,unguwar ba kowa shiru kasancewar haka yanayinta yake koda da rana ma balle dare,ta qarasa ta qwanqwasa get din,mai gadin ya yaso yana tambayar wane? dare ya soma a lokacin don tara ma ta gota,"nice" ta amsa masa bai dai gane wace din ba har sai da ya leqo ta 'yar qaramar qofar dake maqale jikin get din,cikin rawar jiki ya soma ture wagegen get din yana fadin sannu da zuwa hajiya,ga tsammaninsa a mota take,shigewa kurum tayi ta ajjiye masa dari biyar canjin da mai mota ya bata bisa bencinsa tana cewa "rufe get dinka bada mota nazo ba"yawan kyauta da fadila ke dashi yasa yake daukin zuwanta din bata taba ahiga ta fita bata yi musu ihsani ba Tana shiga anty hauwa na fitowa daga kitchen da yake qofar shigowa falon opposite qofar kitchen din ta ne na qasan,hannunta dauke da food flask guda biyu,baki ta saki galala bayan ta tsaya cak tana kallon fadila,har ta bude baki zata yi magana sai ta lura da yanayinta a hargitse taje ba kamar yadda ta santa ba ba lamaun nutsuwa tare da ita,mamakinta yaushe suka dawo daga china babu labari?,kan tace komai din fadilan ta share wani qwallar "subhanallahi" anty hauwa tace ta qaraso da sauri ta dire flask din saman kujera ta kama hannayen fadilan tana fadin "lafiya fadilah?"a rude,"daga ina haka?" "Daga airport nake anty" ta bata amsa murya a dashe Bata kuma cewa komai ba don tasan ba lafiya ba ta ja hannunta suka bi ta wani dan madaidaicin corridor dake hannun hagun falon,dakunan bacci ne ciki guda uku,daya na baqi wadanda baza'a kaisu boys quarters ba daya na yaranta wanda du sun kwanta bacci kasancewar da wuri take sasu suna yi saboda makaranta,daya kuma nata ne duk da ba kwana take ciki ba sosai ko yaushe suna sama a tare da mi gidan ta saidai idan yayi tafiya ne,ta tura qofar dakin suka shiga tare,daki ne mai kyau kamar sauran dakunan bakin gado ta zaunar da fadilan hadi da cewa"kiyi wanka kiyi sallolinki,nasan cewa ba lafiya ba lo baki gayamin ba"ta miqe ta fita jim kadan ta dawo dauke da wani cooler madaidaita guda biyu na baincin daya hannun nata kuma sabuwar abaya ce ta ajjiye mata,"ga abinci kici,ga kaya ki sauya don kifi jin dadin jikinki,zani na sallami abbansu kausar right?"ta qarashe da tambayar fadilan,kai kawai ta gyada mata kamar qadangaruwa a sanyaye anty hauwan ta juya ta fice Cikin abinda anty hauwan tace tayi abu uku ta iya wanka canza kaya sai sallah,tana zaune akan darduma tana share hawayen dai nata,ta yanke hukuncin da taga shine daidai saidai ta rasa me yasa zuciyarta ke son bijere ma umarninta?,anty hauwa ta turo qofar ta shigo ,a sanyaye fadilan ta dago kanta tana masa mata sallamar sai kuma wani dan kukan mai dan qaramin sauti ya kubce mata ta sunkui da kai,dirshan anty hauwan ta zauna gabanta ta riqo hannayenta "cool down fadila mana,ki nutsu ko gayamin me yake faruwa?,ni kuma na miki alqawari tunda kika zabeni kika kawomin matsalarki zanyi qoqarin warware miki ita"cikin sigar lallashi har anty hauwa ta ciyo kanta ta tsagaita kukan duk da hawayen dai basu bar zuba ba Ta danja majina irin ta mai kuka tace "anty so nake na rabu da aliyyu"zaro ido antyn tayi har da sakin hannun fadilan,daga bisani ta tattro kalaman tambayarta "saboda me fadila?,me ya shiga tsakaninku haka bayan kowa na ma ali murnar morewa aure yanzu?kowa sha'awar zamanku yake?,"murmushin takaici ne ya kama fadila ta girgiza kai "anty zaman mu abun sha'awa ne ga wanda baisan halin da nake ciki ba,ni da nasan me nake ciki banga abun sha'awar ba,banga sha'awa ga tilastawa wanda bai sonka ya zauna tare da kai ba,kin taba ganin inda anty wuta da ruwa suka hadu suka cakuda suka zauna kuma suka rayu suka wanzu gu daya?,banga abin shaawa ga zamantakewar auren da babu soyayya cikinta ba sai zallar qiyayya,anty aliyyu na cutar da ni ta hanyar rashin samun soyayya da kulawarsa,hakana ina matuqar cutar da shi ta hanyar tilasta masa zama da ni baya baya so,baya sona,ina cutatsa ta hanyar sashi kallona a matsayin matarsa,bayan ya gayamin baya sona bakuma zai taba sona ba,don me zan zauna anty allah ya kamani da haqqin cutar da shi?" Ido ta kuma zarowa tace"kamar yaya fadila,kimin gwari gwari ki daina min zancen kurma da bebe" Ta dago tsaf tana kallkn antin don mafita yanzu take nema,so take ta canza rayuwarta yanzu,so take ta bude sabon babin rayuwa ta manta komai,rayuwartatake so ta maida ta ta mafarki ta fara ta gaske,tana so ne ta manta da aliyyu ta manta ta taba sonsa,baya sonta(a zatonta) itama ya kamata ta qishi(nikam nace hmmm zaiyiwu kuwa????)hmmmmm muje dai zuwa ga *part 3* 🎊🎊🎊🎊🎊🎊🎊🎊 *alhamdulillahi rabbil alamin,wassalatu wassalamu ala man talaqqal qur'nu mi ladun hakimul khabir* 🎊🎊🎊🎊🎊🎊 *godiya ga mahaifana* *sannan godiya ga dukka members din group dina huguma novels readers da dukkan wani masoyi na wa yasan gobe,Allahbya bar qauna ameen summa ameen* 🎊🎊🎊🎊🎊🎊🎊🎊 *kuci gaba da bina da jin yadda wannan rikita rikita zata kasance,meye ra'ayinku game da jaruman wannan littafi?ina saurarenku ta number wayata* *na gode* *mrs muhammad ce*👑 📚📚📝📝✍🏻✍🏻✍🏻 [10/16, 2:08 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WA YASAN GOBE?...* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 WA YASAN GOBE?....**WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HIGUMA*👉 🏼*PART 3*👈🏼0⃣1⃣ A hankali ta bude bakinta tace "anty *ta inda aka hau ta nan ake sauka* ,kece silar qulluwar igiyar aure na da aliyyu,ranar wanka kuma ba'a boye cibi"............A nutse cikin hikima ta soma labarta mata tun ranarhaduwarsu da aliyyu,ta fara sonshi tun kafin tasan waye ne shi,hakanan tun kafin shima ya san tana yi,ta rufe da cewa "sai ajiya na sake tabbatarwa aliyu ba sona anty yake ba bisa wani qwaqqwaran dalili nawa"(ta rufe ba tare da ta gaya mata ba),tayi shiru hawaye na diga a fuskartaShuru anty hauwa tayi don ta kasa cewa komai,ta jima cikin jimami,ta jima tana gyada kai kafin daga bisani ta saki nanauyan ajiyan zuciya "fadila sannunki da qoqari,ba shakka ke din jarumar mace ce mai son farincikin iyayenta,kin cika 'ya ta gari kuma 'yar halak,dama wannan zaman kike amma bamu taba gani ko a fuska kin nuna alamu ba?,tabbas aliyyu zaici qaniyarsa duk hukuncin da kika daukar masa ya dace da shi,wanne taimako kike da buqata a guna fadila fadeshi,kowanneiri ne zan iya miki shi,nayi da na sanin zamowa silar hada aurenku,na zamo silar xamanki cikin qunci bayan ni ima zaune cikin walwala"anty hauwan ta fadi cikin takaiciGirgiza mata kai fadilan tayi "kada ki soma dana sani anty,domin kuwa qaddarar Allah ce,ya hukunta hakan dole sai ya faru koda babu ke anty......alfarma daya nake so anty....bana son kowa ya san ina gidan nan koda kuwa 'yan gidan mu ne,bana son in sake tozali da aliyyu har sai ya ban sakina,rabuwa nake son nayi da shi saboda na barshi ya sake yayi rayuwarsa ba takura,in barshi ya rayu da masoyansa don rayuwa tare da miqiyi cikin inuwa guda ciwo ne da ita"ta fadi maganar tana jin wani daci har kan harshentaSosai anty hauwa taji wani tausayi nata har cikin ranta ta girgiza kai gami da kama kafadarta"indaiwannan alfarmar kawai kike nema fadila baki da matsala,kin samu dari bisa dari,amma in one condition.....sai kin min alqawarim cire wannan damuwar daga zuciyarki,kin bar wannan dan banzan kukan da kike,ba lokacin ki bane na kuka yanzu lokacin aliyyu ne har taya shi ya kamata ayi saboda asarar mace irinki da yake shirin yi,asarar da bazai taba maye gurbinta ba,dubi fuskarki yadda ta canza saboda tsananin kukaMurmushin yaqe tayi"insha Allahu na bar kukan anty daga yau,bazan sake zub da hawayena ba akan aliyyu,yadda bay sona ni din ma na bar sonsa kenan har abada" "good" anty hauwa tace tana dariya hadi da girgiza hannayen fadilan,sai kuma kunya ta dan kamata yadda ta taqarqare tana gaya mata bata son dan uwanta ita kuma ta kuma tana bata goyon baya ba tare da son kai ko zuciya ba ta sunkui da kai,Murmushi anty hauwan tayi "kada ki ji kunyata fadila gaskiyarki kike fadi,kowanne hukuncikuma da kikayi yayi daidai,don wallahi kinji na rantse miki mace dai dai ce zata iya irin zaman da kikayi ba"🔅🔅🔅🔅🔅Ya sallami mai taxi din da kudin da shi kansa baisanyawansu ba sannan ya shige gidan,bisa kujerar falo ya zube yana maida numfashi,wani azabar ganinta yake son yi ,a hankali ya kai idonsa inda ta saba ajjiye masa ruwa da drinks wayam gun yau ba komai,ba qamshin girkinta babu na freshner dinta,sai yaji gidan tamakar kango garin ya koma masa tamkar maqabarta,burinsa kawai gobe tayi yafice ya bar qasar,wayarsa ta soma karadi ya cirota don takaici bai san sanda ya bugata da qasa ba ta bude komai ya tarwatse a saman centerA sanyaye ya zauna gefan gadon hadi da zubawa farin bedsheet din nasu ido yadda ya baci da jini haryanzu yana bisa gadon,bai son tayar da ita ne a jiya shi yasa ya tureshi gefe ya kwantar da ita,idanunsa suka sake kaiwa kan tray na breakfast da ya hada mata tun safen kafin ya fita,yana nan yadda ya shigo da shi dai dai da cup ba'a juya shi yadda ya saka shi ba da alamun babu abinda taci kenan?Ya daga zanin gadon yana qarewa jinin jiki kallo,shi kansa bedsheet din wata qimarsa yake gani,daga qarshe ya duqunquneshi a qirjinsa da dukka hannayensa biyu idanunsa na a lumshe,wata mahaukaciyar soyayyarta ke ratsa shi,baisan lokacin da ya kwanta saman gadon ba,fuksarta ce kawai ke masa yawo cikin idanunsa,zanen fuskar yake gani sanda suka kasace a lokaci mafi tsada dadaraja a rayuwarsa,lokacin da bazaya taba barin tunaninsa saidai mutuwa ta cire masa shi,lokacin da bazai taba daina ganin darajarsa ba saidi mutuwa ta hana shi,qamshinta ya dinga ji sosai kan pillow din da ta kwata tamkar tana gurin,da sauri ya bude idonsa,vest din ta ce ta jiyan daya yaga saitin hancinsa,da sauri yasa hannunsa ya dauko ta yana sake mannata cikin hancin nasa,tamkar zai shide tamkar zai zuqo fadilan daga jikin vest dinJuyi yake sosai cikin wai irin shauqin qauna da soyayya da bai taba zaton akwai makamanciyarta ba a duniyarmu "why u leave me?why?,I cannot sustain missing you,I can't,me yasa sai da kika mun kyautar abu mai tsada da daraja baki tsaya kin karbikema abu mafi tsada da daraja aguna ba kika barni?,me yasa ba zaki tsaya na saka miki dimbin kyautatawarki gareni ba?,why baki sanar da ni sirrin zuciyarki ba sai lokacin da kika barni why?....." shi kadai qwal cikin gidan harma a dakin yake ta wadannan sumbatuSam ya kasa hassalawa kansa komai,koda suit dinsaya gaza cirewa bare akai ga yin wanka ballantana kuma batun abinci,koda yana da buqatarsa bazai iya ci din ba don harshensa bai gamsuwa da girkin kowa idan ba natan baSai yanzu ya soma tantance son da yame mata ashe yafi wanda yake ma girkin ta?,sai yanzu ya fara ankara da dalilin da yasa yake hasala da yawa idan bata gyara masa part ko bata masa girki ba fiye da yadda yake jin zafi yake hasala fiye da su samira?,sai yanzu ya gane dalilin da yasa yake jin haushi idan ta kammala girki ta bar masa bangarensa kafin ya dawo?,sai yanzu ya fuskanci dalilun da yasa yake qin cin abinci har sai ya tilasta ta ta zauna by his side har sai ya kammala?,ashe sone hakan?,wani irin salon sone wanda bai farga da wane lokaci da kuma yaushe ya shiga zuciyarsa ba sai yanzu?,ba abun mamaki bane don bai taba kamuwa a akaran kansa da *SO* din ba sai a kanta,tamkar ya taso ne ya saba da cusa masa shi ake ta qarfin tuwoKamar ya jawo goben haka yake ji,daren gaba daya ji yayi yayi wani mugun tsawo a gunsa kamar jansa aka dada yi,gani yake kamar gari bazai waye ba,kayanta dake cikin cupboard gana daya ya watsosu ya barbazasu kan gadon ya kwanta akai yana shaqarsu ko zai samu sa'idar zugi da zillo da zuciyarsa ke masa game da ita,saidai inaa....kama da wane bata wane,tamkar wani zautacce haka ya koma idanunsa jazur bashin baccin jiya da yau gabadaya kuma bacci bai ziyarceshi ba sai gab da suba🔅🔅🔅🔅🔅🔅Kiran wayarsa su mr lun ke tayi amma gaa daya layukan switched off,suna baqatarsa sosai don awanni uku kacal ya rage a soma gudanar da bikin,baqi masu zuwa nata tambayarsa,hakan yasa andi da kansa ya taho gidan takanas ba shiriCikin bacci yaji anataba qararrawa da alamun neman izinin shigowa ake,tsaki yaja ya maida kansasaman filon hadi da maida fuskarsa hannun hagu maimakon dama a yadda take dazu bashi da ko niyyar tashi,saidai mai danna qararrawar yaci gaba da matsata kamar babu gobe har sai da mijin nadiya ya fito abdul basid,hakanne ya sashi miqewaa fusace ya zare rigar saman ya cire tie din ya wurgar ya bar 'yar ciki ya fito cikin haushin kaza huce kan damiSuna hada ido da andin yasan cewa babu lafiya fa,don kalli daya zaka yima aliyyun kasan ya koma wani hargitsatstsen aliyyu,cikin tsawa yace "what doyou want?!" Cikin girmamawa yace "sir d time is passing,u have to prepare........." "leave me alone!" Aliyyun ya dakatar dashi ta hanyar daga masa hannu cikin wata tsawar,ya ja qofarsa garam ya kulleta ya koma cikiSaman kujera ya koma ya zauna yana nishi,sai a alokacin idanunsa suka sauka kan wayarsa da ya tarwatsa jiya,yasa hannunsa ya tsince ya maida layukan ya sanya batirin ya kunnata,servicena gama hawa massage suka yita shigowa sun kusa hamsin,ko guda baiyi sha'awar budewa ba bare ya karanta,hasalima hankalinsa bai kanta nashi tunanin daban,cikin haka kira ya shigo,bai ko kalli wayar ba bare akai ga batun dagawa,sai da tayi ta katse har sau biyu,cikin jan tsaki ya sanya hannu ya janyo wayar da niyyar kasheta,number din uncle abba ya gani,bau damar kashewa kenan,luguden bugu kawai zuciyarsa ke masa,ya danna ok,ya gama bada amannar cewa fadila taje musu ne,ba qaramin rudewa yayi ba saboda sanin halin abban nasa sarai bashi da sauqi kan wasu lamuranYa kara a kunne jiki a sanyaye,tambayar da abban nasa ya masa ta sake sashi cikin wani halin ha'ula'in"me kake yi haka ne aliyyu?,lafiyarka kuwa qalau?" Cikin rawar murya yace "abba...wallahikuskure ne....kuskure aka samu kuma....."ya dakatar da shi"ya isa bana son jin komai maza ka tashi ka shirya,mr lin ne ya kirani ya gaya min komai har mutum ya aiko maka ka koreshi,damar da ka ka jima kana jira yanzu don ka sameta shine kakeso kayi wasa da ita?,maza ka ahirya kafin lokacin yayi kamar yadda aka tsara"wata boyayyar ajiyar zuciya ya saki ya maida bayansa jikin kujera "to abba inshaAllahu" suka qare wayar yana masa addu'ar samun nasara tare da sanya masa albarkaYa kashe wayar sannan ya zuba mata ido,yana ji a jikinsa da zuciyarsa bai kyautawa abban nasa ba ma,bai san da qanne ido zai kalleshi ba,cikin kasalartasa ya miqe ya shiga toilet ya hada ruqan wankanshi da kanshi don cika umarnin abban nasa,awanni biyu ya dauka ya kammala shiryawa,komai da yakeyi babu walwala a fuskarsa,dama yaya lafiyar kura bare tayi hauka? Hakanan babu kuzari ko qanqani tattare da shi,shigarsa ta suit yayi saidia wannan ta musamman ce 'yar ubansu,wadda dama an tanadeta ne domin wannan rana,maqudan kudade aka kashe gun siyan nata,kai da kanka idan ka kalleta ba sai angaya maka ta lashi kudi ba zaka baiwa kanka amsa ash ce mai cakude da yarfin baqi rigar ciki kuma da tie dinsa kuma light pink ne,agogo da ya daura da takalmi na qafarsa ma kawai abun kallo ne,sumarsa tayi kyau sosai kamar yasa mata relaxer,sosai aliyyun yayi kyau tamkar balarabe,yaya dama mai kyau yasa abu mai kya?,saidai cikin zuciyarsa sam babu nutsuwa ko farinciki ko dayaSuna waje suna jiransa cikin dalleliyar sabuwar baqar mota,sabuwar qira ce don a shekarar aka farahawanta,yana daya daga cikin kutane na farko da suka mallaketa ko a qasar chinan,mutum uku ne suka miqe ya watsa musu harara don yana ganin susuka takurashi zuwa gurin tamkar su suka yi laifin,dayan ya bude masa inda zai zauna yayin da ragowar biyun suka bishi da gaisuwa,baiko kallesu ba sun san ba lafiya son haka basu sake cewa komai ba suka shiga mai tuqi ya tafa motarTafkeken dakin taro ne dake cikin ginin kamfanin*maitama factory*,hall ne da yaci sunan hajiya*maimunatu ibrahim muhammad* mahaifiya gareshikenan,cike yake da al'umma mahalarta taron,sosai aka qawata gun,decoration aka masa mai azabar kyau da tsari,kowanne table kujeru hudu ne suka zagayeshi,kusandukka mahalarta taron sunyi shiga ne ta baqaqen coat kamar masu ashobi,maza ne damata jinsin yarw da qabila daban daban,kowanne zaune gurinsa a nutse cikin tsari suna sauraran bayanai daga bakin mai gabatarwa duk cikin dakon isowar aliyyu,babu wata hayaniya kai sai ka rantse babu mai numfashi cikin hall dinShigowar tasa ya sanya duk wani dake dakin taron miqewa tsaye cikin girmamawa,tafi ya cika hall din raf raf raf,tamkar ya zura da gudu ya bar hall din haka yake ji don tafin nasu wani kuda yake masa akunne,sai da ya hau step din da ka tanadar musu don zama gefan hannun hagunsa mr lin kusa da shi miss sisineo ce hannun damansa kuma ramzan ne kusa da ramzan kuma mukhtar ne,sai da auka kmmla zama sanna kowa ya koma.mazauninsaya zaunaDakin taron ya sake yin shiru,mai gabatarwa ya yi wa aliyyi barka da isowa,sannu a hankali aka ci gaba da gabatar da taron yadda aka tsara daki daki,duk anun nan da kae maganar minti biyu aka ritsa aliyyi da bindiga aka ce ya maimaita saidai a harbeshin don baya gurin *gangar jikinsa* ce kawai zaune,hankalinsa na kan fadila da agogo,duk bayanminti guda sai ya duba lokaci,jawabai masu muhimmanci da ka tsara shi zai gabatar babu ko daya da ya iya yi,sai ya bada uzirin baijin dadi sosai,drinks da kayan ciye ciye da ka cika gaban kowa da shi babu qanda ya iya kalla balle ya tantance yana sha'awarsu ko baya yi bare akai ga batun zai ci ko zai shaAwanni biyu aka dauka sannan aka zo gangara,su mukhtar suka tilastashi kan dole ya karba yayi jawabin godiya ga dimbin al'ummar da suka.tako gari ya gari suka zo masa,yana ture lasifiqar yana komai haka mukhtar ya manna masa ,idanu da sukamasa ca yasa ya sa hannu cikin kasala da rashin sanin a halin da yake ciki ya amsa"Fadeelah!" Abinda ya soma mabata kenan cikin bututun maganar,tsit suka yi fiye da wanda sukai dazun tamkar wanda yayi calling attention nasu,ido kowa kr binsa da shi don dai sun san suna.ya ambata "fadeelah ta soni matuqa cikin rayuwarta.....na zauna da ita cikin boyayyen nuni gairin tawa kalar soyayyar gareta",ya danyi jim sannn ya shaqi numfashi ya dora "fadeelah ta barni a lokacin da ya bayyana gareni na dade nima ina sonta ba tare da nawa sanin ba....ta barni a lokacin da nake da buqatar yi mata mafificiyar soyayyar da ba'a taba gwadawa wata 'ya mace irinta ba......ta barni da wani nauyi mai azabar nauyi cikim zuciyata ba tare da na samu na sauke mun raba tare ba......fadeelah ta zama ruhina da gangar jikina"dora hannun sa yayi saman qirjinsa saitin zuciyarsa "fadeelah ta mallaki nan ba tare da saninta ba,ya dade da zama mallakinta ba tare da sanin ku mu duka biyun ba""Na tsinkayi fushi fusata da rashin fahimta masu tarin yawa qunahe cikin kalamanta,qunshe cikin takardar da ta zamo baqa aguna,cikin saqon dake bayyana bankwana da abinda zuciya ke so,cikin shafin takarda qwaya daya tal saidai sun yimin nauyi fiye da littattafai dari masu shafuka dari dari"ya hade tafukan hannayensa guri guda yana yinsa ya sauya soaai da alamun abinda yake fadi din na taba zciyarsa sosai,da alama zancan daga ainihin zuciyarsa yake fita ba daga harshensaa yakeba "ku yimin alfarmar sani a addu'o'inku....ku yimin alfarmar roqa min Allah ya huci zuciyarta,na gode muku baki daya...."ya fadi yana qoqarin komawa ya zauna,gaba daya suka.miqe suna tafi,yanayin salin ne ya burgesu,fuskarsu da zuciyarsu cike da tausayinsa,abunka da mai jajayen kunnuwa akwai girmama soyayya komai tsufanta,miss sisineo ce tabude 'yar jakarta ta fiddo da bangles na gwal guda biyu danqara danqara ta ajjiye gaban aliyyu tace ga kyautar ta a isar da ita ga fadilaSosai abun burgeshi ta yima fadilansa kyauta duk da yana da arziqin da zai siya mata ninkin wanann amma ayi kyauta wa masoyinka ma abun faranta ranka ne,yasa hannu ya dauke yayi masu kyakkyawar ajiya..........*mrs muhammad ce*👑📘📘📘✍🏻✍🏻✍🏻✍? 👉🏼 *PART 3*👈🏼 3⃣&4⃣ Bayan ciye ciye da akayi a gun suka soka fita gun ainihin ginin kamfanin wanda aka zagaye shi da wani yadi mai kyau aka daure bakin qofar shigar da shi,aliyyun ne a gaba a tsaye andi ya miqo masa qaramin almakashi ya amsa ya dora saman yadin ya datse,tafi aka saki sannan suka dunguma gaba daya sukayi ciki,guri guri suka dinga shiga daya bayan daya cikin kamfanin,sosai ginin ya tsaru yayi kyau matuqa da gaske,komai cikin fasali gwanin sha'awa Ba qaramin qaguwa yayi ba,duk bayan minti daya idanunsa na kan agogo,gani yake kamar yanga lokacin yake masa,binsu kawai yake ba tare da fahimtar abinda suke yi ba,sam hankalinsa bai tare da su,cikin dabara ya zame jikinsa ya koma office dinsa wanda aka tanadar masa ko da zai zo wani lokacin,yasa key ya bude ya shiga sannan ya koma ya kulle ya koma saman kujera ya zube,awoyi uku ya rage jirgin nasu ya tashi,baya tsammanin zai iya zaman jira,ya zaro wayarsa cikin hanzari ya kira jumong da mukhtar Tare sukayi knocking ya tashi ya bude musu,kan kujera mukhtar ya qarasa ya zauna yayin da jumong ya rusuna yana jiran jin umarni,"ka shirya mota zan fito yanzu zaka kaini airport" "ok sir" ya fadi hadi da juyawa cikin hanzari ya fice,yayin da mukhtar ke kallonsa yana son tambayarsa me zaya yi a airport?,bai bashi wannan damar ba ya soma masa bayani da kansa ba tare da ya tambayeshi ba "nijeria zan wuce mukhtar nan da awa uku,ina son na bar komai a hannunka kayi handling dinsa,bazan yi sallama da kowa ba its urgent,ka wakilceni please"cikin rashin fahimta yake dubansa "like how aliyyu baqin naka zaka bari ka wuce nijeria?" "Pls mukhtar if u cannot help just tell me directly" yasan halin kayan sa sarai saboda haka ya gyada kai "is ok,is ok I will" ya miqe tsaye ya sake duba passport nashi da ticket dake cikin jakan sa,yaga komai na nan yadda zai buqace shi,ya dauka gami da zaro master card platinum ya ajjiyewa mukhtar din sukayi hand shake "thanks" aliyyun ya fada a gaggauce sannan ya bude qofar ya fice,mukhtar da mamaki ya cika shi yabi aliyyun da kallo galala,gaba daya aliyyun ya fita daga hayyacinsa sam ya fice daga nutsuwarsa Ta get din baya ya fice don baison kowa ya tsaidashi,don kuwa baiga abinda zai tsaida shi daga tafiya nijeria ayau din nan ba saidai ikon Allah,ko cikin motar ma gani yake jumong baya sauri laqaqai laqaqai kawai yake,gaza haquri yayi har sai da ya soma masa maaifa kan ya qara gudu "sorry sir ida mukayi gudu ya wuce qa'ida camera na kallon mu za'a iya kama mu" sai a lokacin ya tuna ba'a nijeria yake ba dole ya haqura a haka har suka isa airport din,ko jirgin ma gani yake ba sauri yake ba shirme yake(hhhhhh),da suka sauka ko a ethopia aka basu dakunan kwana kan sai gobe zasu qarasa nijeria jinsa yayi kamar a saka shi a kurkuku,masifa kawai yake yana fadin dole ya sayi private jet nashi,dole yana ji yana gani ya haqura har sai washegarin 🔅🔅🔅🔅🔅 Qarfe goma na safe a garin kano tayi masa,tuni nasiru yazo da mota don daukarshi,gidansu yace ya wuce da shi kundila maiduguri road,yana shirin fitowadaga cikin motar saiga sumayya ta fito cikin shirin tafiya school,da sauri ta sauya akalar tafiyar tata ta nufo gurin motar fuskarta qunshe da fara'a"sannu da zuwa ya aliyyu" ta fadi tana leqa cikin motar cikin neman fadila,"yauwa" yace yana sanyo qafarsa waje,ya dubeta cikin dakiyar nan tasa "ke,me kika bani ajiya kikemin leqe leqe cikin mota" sai ta dawo ta tsaya dai dai cikin fara'a "anty fadila nake leqe ko zan gani yaya,surprising din mu kuka so yi shi yasa ko a waya bata gaya mana ba,kwananta biyu ma bata kira mu ba ashe kuna hanya"da sauri ta juya tana shirin komawa ciki tace "bari na fara yi mawa momi albishir"sosai jikinsa ya mutu basu da labarin ma ta dawo to me yake faruwa ne?"maida qafar tasa yayi cikin motar ya rufe ya bawa nasiru umarnin ya kunnata su wuce sani mai nagge(unguwar su fadila) Har cikin gidan malam ya bude musu suka shiga,ya fito ya ningina jikin motar bakinshi fal addu'a,yana tunanin yadda zai shiga gidan ne,sai ga muhammad ya fito daga inda suke ajiyar motocinsu hannunsa dauke da qaton almakashi irin na yankan shuka,nasiru ne ya qwala masa kira,da sauri ya juya ganinsu yasa shi nufo gurin yana fara'ar ganin aliyyun,"sannu da zuwa yaya"muhammad ya gaida shi ya amsa masa "kai da anty ne yaushe kuka dawo amma bata gayama ummi zaku dawo ba"ya fadi yana washe baki da son jin amsar inda yayarsa take,innalillahi wa inna ilaihi raji'un"aliyu ke fada cikin wani irin hali,muhammad ya juya yana fadin "bari nakira abba bai fita ba"aliyu na shirin hana shi saiga abban ya fito ummi na riqe da jakarsa Sosai abban ya nuna jin dadin ganin aliyun,yasa muhammad ya bude sitting room suka shiga,maganar da abban ya qara fadi ita ta sake tabbatarwa da aliyyu fadilan bata zo gidan ba"ina mai kukan tafiya yanzu dai ai kuka ya qare ko tunda gashinan anje lafiya an dawo lpy"aliyun ya sunkuyar da kai wata fargaba na shigarsa "tana lafiya abba" abinda ya iya fada kenan,to shima abban bai takura masa da wata doguwar hira ba ya sallameshi shima ya fice kasuwa Gidansa kawai yasa nasirun ya kai shi don bai san kuma me ya rage masa ba,tunaninsa ya tsaya cak,a harabar gidan ma'aikata ne kowa na masa barka da dawowa,baijin ma me suke fada hannu kawai yake daga musu,ya sallami nasiru ya fito daga cikin motar yana shirin shigewa ciki aka sake dage gate din gidan,tsayawa yayi hadi da juyowa don hajin wanda aka bude mawar,motar samirah ce wadda ta sake cin ubanta,su hudu ne cikin motar,wata dabance ke driving din samirah na gefanta sai wasu su biyun a baya,dariya suke ta sheqawa sam basu ma kula da wani aliyyu ba har suka yo parking,har ta fito tana sheqa dariyarta kamar wadda aka yiwa albishir din ba zata mutu ba,cak ta tsaya tana kallonsa kamar yadda shima ya zuba mata ido,suma qawayen dariyarce ta tsaya cak,sun san halinsa sarai baya da kyau,sum sum daya bayan daya suka fice daga gidan,kai kawai ya gayada ba tare da yace mata komai ko ya sake kallonta ba ya shiga bangaransa Yafi mintin talatin a zaune kafin ya miqe yaje yayi wanka,kafin ya kammala shiryawa anyi kiran sallar azahar,duk wani motsi da zaiyi tana manne cikin ransa,duk wani tunaninsa na ina zai sameta?ina zai ganta?ina kuma yanzu zaije nemanta?,cikin yadin tissue fari tas ya shirya,yayi kyau sosai duk da kana kallonsa zaka karanci bai cikin walwala duk da kusan hakan yanayin fuskarsa yake amma wannan karon ya ninka yadda yake da,ficewa yayi kansa tsaye ba tare da ya nemi kowa ba da kansa ya ja motar ya bar gidan Sai da ya fara tsayawa a masallacin bakin layinsu ya bada faralin sallar azahar dinsa sannan ya wuce,kai tsaye yahaya gusau ya wuce gidan farida,ya dan jima a tsaye a qofar gidan baiga gilmawar kowa ba har yana shirin komawa sai ga dahiru almajirin faridan,da sauri dahirun ya qara so inda aliyyun ke tsaye don ya ganeshi,cikin girmamawa ya gaida aliyyun,ya amsa masa yana tambayarsa matar gidan na ciki?,ya amsa masa da "eh alhaji ko a kira maka ita za'ayi?" "A'ah tambayarka dai nake so nayi"aliyu ya fda yana gyara tsaiwarsa "to..Allah yasa na sani" "tayi wata baquwa tsakanin jiya da shekaran jiya da yau?" "Kai gaskiya a'ah,don suma jiya suka dawo daga lagos ita da mai gidan"ya fada masa cikin bashi tabbaci Idanunsa ya rufe yana jin wani abu sannan ya bude,ya saki qaramar ajiyr zuciya sannan ya ciro kudi ya bama dahirun ,cikin murna ya amshe yana zuba godiya,bai bi ta kan godiyarsa ba ya shige motar ya tasheta ya bar layin Har la'asar aliyyu salim na bulayi bisa titunan kano,shiga wancan fita wancan,ko manshi da yake qonawa bai damu ba,ya rasa inda zai zauna bare yayi tunanin mafita,gaba daya feeling kansa yake a matsayin guilty,cikin rudanin inda ta tafi yake,ina ta boye kanta haka?,duk da yana ji daga can cikin wani sashe na zuciyarsa na gaya masa she is safe and she is in safety place Sai da ya soma ganin gurare daban daban na ta alwalar sallar la'asar sannan ya samu ya kashe motar a bakin wani masallaci ,ya daura alwalar ya bi jam'i,sai bayan da ua idar ne yaji cikinsa na qugi sannan ya tuna rabonsa da abinci har ya mance,ya miqe ya koma cikin motar tasa ba tare da yabi ta kan yunwar dake sakadarshi ba,sai da akayi sallar magariba yana bilayin yawon titina sannan ya gano cewa wannan fa ba mafita bace,tunanin matsalar itace zata samar masa mafita da gano masa inda fadilan ta boye,ya juya akalar motarsa ya nufi gidansu dake kundila. ....... *mrs muhammad ce*👑 📘📘📘📚📚✍🏻✍🏻  [10/16, 2:09 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WA YASAN GOBE?...* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 👉🏼 *PART 3* 👈🏼 5⃣&6⃣ Yana shiga ya tadda rabi'ah kan dining area ita da iftihal momy na kitchen,da alamu su din ma zaman na cin abinci ne,da gudu iftihal ta gangaro tana ihu "yeyyyyyy daddyyyy"kamar yadda ta saba ta duqa ta gaidashi,ya amsa mata maimakon ya dauketa ya shilla sama yadda suka saba wannan karon sai taga kawai ya shafa saman kanta yayi hanyar kitchen din,ta tabe baki kamar zata saki kuka Tana kiciniyar rufe warmer taji an rufe freezer,ta dago kai da sauri aliyyun na tsaye yana daddakar ruwan mai azabar sanyi,sai da ya shanye robar guda momin na kallonsa ta zuba mai ido,ganinsa take a wani birkice duk da jikinsa fes yake kuma ya yi kyau da 'yar cika(sakamakon kulawar da ya dinga samu a china)amma abunka da mahaifiya kallo daya tayi masa t gano akwai damuwa a ransa Yana qare shanyewar suka hada ido da momin,sai ya kautar da kai ya sanya robar cikin dust bin yana cewa "momi barka da dare ina wuni"bata dai daina kallon nasa ba tace "lafiya lau Ali kun dawo lafiya?" "Lafiya qalau ha fada yana jan kujerar plastic dake kitchen din zai zauna "mun sameku lafiya?" Ya sake tambayar momin yana dauke kai don baya son irin kallon nan na momi,nan da nan take naqaltar mutum,itama sai ta dauke kan tana ci gaba da rufe warmer din tace"lafiya lau,tun safe sumayya tace min gaka,shiru shiru baka shigo ba ko da aka leqo kuma ba kai a gun"ta qarashe maganar idanunta a kansa kamar tana son jin amsa kenan Ya basar da zancan ta hanyar cewa"rabu da wannan shirmammiyar yarinyar momi,makaramta fa zata tafi amma don gulma ta koma,gida muka qarasa kawai"ta dire warmer din tana cewa"ina 'yata fadila" gabansa sai da ya buga "lafiya"kawai ya iya furtawa tare da miqewa don kada ta sunkuto masa wata tambayar da zai gagara kubutar da kansa,ta waiwayo tana cewa "a'ah ina zuwa kuma?" "Zan wuce gida ne momi" "baku gaisa da abban naka ba,yana gida fa,kuma ma na zaci tare zamuyi dinner ko?" Abinda momi bata sank ba bazai iya jiran abban nasa ba don gani yake kallo daya zai masa ya karanto abinda ke faruwa,karo na farko da aliyyun yayi ma momin qarya a rayuwarsa "Zani gida ne momi za muyi magana da mukhtar,na baroshi ne da mutane a can wadanda ban sallamesu ba na taho" to da yake ma qaryar bata karbeshi ba sai ya jada harda subul da baka ba tare da ya ankara ba "ya zaka dawo bayan baka sallami baqi ba ali?,wai meke damunka ne haka?,a kunnena fa abbanka ya tursasaka zuwa bikin bude kamfani,yanzu kuma ka taho ka bar jama'a acan,baqonka annabinka fa ali"yayi saurin dosar qofar fita yana cewa"momi ai ba matsala mukhtar zaiyi komai kamar ina nan,sai da safe momi idan abban ya sauko ki gaida shi ina hanya goben"baki sake ta bishi da kallo tana ayyanawa tabbas akwai abinda ke damun yaron nan,gashi da shegen zurfin ciki kamar mace,idan kaji cikinsa to ya ciyoshi ne,ta dan daga murya tana cewa"ka gaida mutan gidan" "zasu ji momi" ya fadi yana barin falon cikin sauri don kada suci karo da iftihal ta tsaida shi Har ya koma ya bude sashensa ya shiga yayi wanka ba wadda ya gani,shi yama fi son haka din ma,yasa koda sunzo babu abinda.zai samu sai qarin tension,shi kuma yanzu abinda ke damunsa yasha kansa fiye da komai,sai da dibi kusan awa daya da wani abu sai ga salima,fuskarsa ta zubawa ido tana murmushi saboda sosai aliyyu ya canza,ya qara ja sumarsa ta sake baqi sidik,gargasar jikinsa kamar an dada mata baqi laushi da yawa,ya sake kyau,badon fadila da ta hargitsa masa lissafinsa ba da abun yafi haka,hakanan shima ya sakar muta fuska don ya zama dole haqqinsu ne don bazaya yiwu haqqin wani ya danne na wani ba,kuma matsalarsa yasan ba tasu bace indai ta wannan bangaren ne Da sauri ta qaraso ta zube ajikinsa tana fadin "oyoyo welcome my dear"yadan karata ajikinsa yace "thank you ya muka sameku?" "We are fine but I miss you" yadan saki fara'a "ok,to ai yanzu gani mai zan samu?" Ta tabe baki sannan tace "ba komai tunda ai ba yau kace zaka dawo ba ganinka kawai mukayi tsakar rana,ni ta window ma na hageka ka fice" "ni din ma haka dawowar ta zo min" cikin son bin qwaqwafi tace "ko fadilan ce ta takura sai andawo?" "Eh"kawai yace mata cikin som kashe maganar don tamkar allura ce akan qurji idan aka tada masa da zancan fadila, "but ban gata ba kuma ma bangaren ta akle yake" "eh"ya kuma cewa dai bai buqatar taci gaba da yin maganar Shiru ya dan ratsa dakin kanta na jingine a kafadarsa,kishin fadilan duk ya cikata gani take kamar wani gun ya kuma kaita don ta huta,samira ta danno kai harda sallamarta kamar gaske kai a sunkuye,duk da haka saboda tsabar neman bala'i sai da ta gasawa salima hara ra,ai kuwa itama bata yi qasa agwiwa ba ta rama don ba qaramin adashen tsiya suka dinga shukawa ba sanda baya nan,kullum sai an raba gari a gidan saidai idan garin Allah bai waye ba,amma kwana suke su wuni suna abu guda kamar karnuka,suna hada ido da aliyyu ya bata tasa hararar tayi saurin sadda kai qasa,gefansa ta zauna cikin tausasa murya tace masa "sannu da zuwa an dawo lafiya?" "Lafiya"yace mata a taqaice,duk sai taji ta muzanta,tafi kowa sanin laifinta,gargadi mai zafi babu irin wanda bai musu ba kafin ya tafi kan fice fice,duk da yau ma tsautsayine amma ta kwan biyu bata saci fita din ba,wannan ne satar fitarta ta hudu salima tayi biyu tana tsammanin tayi na qarshe tunda ya kusa dawowa qasar bata san yau ya dawo ba Shiru ya gauraye falon kowa da abinda yake saqawa cikin zuciyarsa,aliyyu yafi kowa nisan kiwo cikin duniyar tunani,"dear ya kamata muje ku kwanta ko?"salima ta fada tana kashe masa idanu,da sauri samira ta dago "kamar yaya?"cikin daga murya samira ta tambayeta,itama ta dubeta ta mayar mata "kamar yadda kika kunnuwanki suka ji nace"da sauri ta nunata da yatsa "baki isa ba wallahi kinyi kadan don yadda kike buqatarsa nima hakan take.....ke bari ma nayi miki dalla dalla...yadda kike a matse ni nama fiki matsuwa"ta fada tana wani gayara zama,sai kuwa cece kuce ya barke dama kadan kowacce take jira 'yar uwarta ta tabo ta,sak yayi yana kallonsu,sai ya zama kamar wani mutum mutumi,babu wadda tayi masa wani abu na azo a gani a matsayinsa na matafiyin da yayi wata judu bai cikin iyalinsa yanzu ya dawo musu,shegiya shinkafa fara sol da yaji babu wadda ta turo masa tace gashi,amma aqalla ai ko tsakar dare ya dawo idan da tunani sa tashi su sama masa wani abu ko drink ne,to amma ga drink din ma jibge a freezer dinsa su dauko ma su hada masa da cup suce masa gashi babu wadda ta iya yin hakan,babu wani welcoming na arziqi,amma ko wacce burinta ya kwanta da ita ya biya mata buqata kamar wani inji Ganin abun nasu ma shirin wuce makadi da rawa don har an fara 'yar lakace lakacen hanci yasa ya dakatar da su ta hanyar daka musu tsawa don idan ba tsawar ya musu ba yadda suka kacame babu wadda zata iya jiyo shi"bana buqatar kowa cikinku,duk ku tashi ku bani waje,tunda ku baku iya kwantarwa da mutum hankali ba saidai ku tayar masa,ko kwana daya banyi ba cikin gidana amma kun fara samin bacin rai?" Tuni samira ta miqe,salima ta rausayar da kai tana cewa "amma aliyu ......." "amma me?Please stay away" ya fada yana nuna mata hanya,samira ta sheqe da dariya tana cewa "ato saiki taso ai mu daye,ki daina naci haka kowa sai ya riqe kwadayinsa tunda yace bai yi" wani banzan kallo alin ya watsawa samiran yana cewa "kin sanni,kada ki bari muyi arangama dake bani da kyau!"tasan hakan kuwa tuni tayi gaba salima ta bita a baya,yan jiyo kici kicin kokawarsu a bakim part din nasa,yayi banza da su _*12 PM*_ Sha biyu na dare ya dinga gwada maqullan hannunsa a qofar har ya samu na qofar tata,ya tura ya shiga ya haska makunnin fitila ya danna dukka qwayayen suka kama bangaren ya cika da haske,qamshi falon yake tamkar tana nan,kamar bata yi tafiya ba na tsawon watanni hudu ba,hakanan komai akillacensa,kai tsaye ya shige bedroom dinta,shima dai kamar falon cikin qamshi yake da tsafta,gadonta a dame yake komai ajere,pant da brassier dinta ne kawai a gefan pillow,ya qarasa ahankali ya haye gadon hadi da kwanciya pillow din ya janyo hadi da rungumeahi tsam tsam a qirjinsa,qamshi pillow din yake kamar a shafa masa turare ne,ya sake miqa hannu ya dago pant and brassier din farare qal ya zuba musu ido,a hankali ya mannaau a hancinsa yana sheqar qamahin turarenta na shamsul imaraat A hankali ya shiga sosai cikin zurfin tunani,yanayinta,halayenta,dabi'unta,haquri irin nata kawaici da yakanah,bai taba ganin ta tana fada irin nasu samira ba,bai taba ganinta tana koda sa'insa da daya daga cikinsu ba,duk wata sabga tasu bata ciki,shi da kansa alokutan baya har haushi yake ji idan yaga bata damu da fadan kishi ba,ashe so ne?,ashe haushi yake ji yana ganin kamar bata sonshi ne? Juyi kawai yake samar gadon,jinsa yake tamkar wani maraya,wani irin kewa yakeji mai zafi da radadi tana kamashi,ya riga da ya saba da kwana jikinsu na gogayya da na juna,ya saba da sheqar qamshinta,sosai ya sake rungume pillow yana sakin numfaahi sama sama,yafi awa biyu kafin wani wahalallen bacci awon gaba da shi ,ko cikin baccin ma bata qyaleshi ya huta ba sai da ta jawo masa yin wanka,ya dawo bakin gadon yq zauna yana tsane jikinsa da towel dinta,idanunsa ya sauka kan wani dan kyakkyawan madaidaicin frame da yake zaune dirshan bisa side bed,yasa hannu a hankali ya dauki hoton ya zuba masa ido yana kallonta,murmushi take yi sosai,fararen haqoranta jerarru reras sun bayyan,yar lobawar dake tsakiyar habarta ta fito sosai,ya sanya bakinshi saitin lips nata yayi kissing,murya qasa qasa yace "I love you"ya dan manna hoton a qirjinshi Sai da yayi sallar asuba sannanya baro bangaren har ya fito ya manta bai dauko hoton ba ya koma ya dauko abinsa,kan side drower dinshi ya kafa sa,yana shiryawa yana kallon hoton har ya kammala shirinsa tsaf cikin shadda fara tas mai asalin tsadar sai maiqo take da daukan idanu,yayi masifar kyau saidai fuskarnan na kirtibe,qarfe bakwai ga fito ya soma da sashen samira don itace a damansa,yana tura qofar ta bude alamuna bude ta kwana,kai tsaye ya zarce bedroom din ta don yasan tana ciki,yana tafiya yana bin falon da kallo tamkar dakin ajiyar shirgi haka ta maidashi Dai dai ya sameta saman gado hannu can qafa can,gajeran gashinta maras tsawo wanda bai hadu da mace mai gyara ba duk ya hautsine ya tashi yayi cako cako kamar bishiyar qaya(don ko baki da tsawon gashi matuqar ke mai gyara ce to zai bada sha'awa,amma komai tsawonsa indai ba gyara abin qyamata zai zama),sosai iyyu ya tsani irin wannan kwanciyar tata,don kuwa insha Allahu kuka hada gado daya da samira to ranar fa ka shieya zaka daku da hannu da qafa,haka kullum yake fama da ita,shi yasa ya gwammace ya matseta a jikinsa ayi baccin haka Ya dan taba qafarta yana kiran sunanta,saidai kamar gawa ko motsi bata yi ba bare yasa ran zata tashi jan minsharinta kawai take,yasan hali dama bata motsa din ba kuwa har sai da ya dage ya daki daki qafar da hannu sannan ta miqe a zabure tana cono baki gami da mutsitstsika ido,sai da ta gama mutstsike idanun sannan ta dubeshi,ganin aliyyu a tsaye ya sata shiga taitayinta,addu'a take cikin ranta Allah yasa maganar laifinta yazo yayi mata,don tasan halinshi shirunsa ba abu mai dadi yake haifarwa ba,fuska a murtuke yace "hala ko sallar asuba bakiyi ba?" Nan ta hau kame kame "zan....zanyi....yanzu ne na tashi ai..." "good" yace da ita cikin takaici yana gayada kai,ya juya zai fita "zan fita sai na dawo" "to" tace kaar wadda aka tilasta ta sai ta fadi hakan,Allah Allah take ya fitan taja bargo ta koma barcinta,bata sani ba shi din ma Allah Allah yake ya bar dakin,don zarnin bandakinta dake cikin bedroom din shi ke busowa har cikin dakin gadon,sai taga kuma ya juyo hadi da cewa "bani key din motarki da wayarki" cikin marairaita tace "don Allah kayi haquri bazan sake ba" a zafafe ya kalleta "will you keep quiet or not? Da baki iya bada haqurin ba kenan sai yanzu?common bani key da phone nace"nuni tayi masa kan hargitsatstsen dressing mirror dinta,ya juya ya kalli kan madubin saboda hargitsewarsa ma shi bai hango wata waya ba ballantana maqulli "ok...ni zanje ma na dauko miki ko?" Dolenta ta sauka daga kan gadon ta dauko ta miqa masa tamakar zata yi ihu,ya amsa ya fice da sauri ba tare da yace mata qala ba don zarnin sake busowa yake,kuma ko yace ta gyara ba zata yi din ba don sau nawa yana fama da ita kan hakan sai tave masa yau fa sati daya kacal da wanke shi ba wani dadewa yayi ba Salima ma na bisa gadon a nade bacci na dibarta sama sama,ita din ma sai lokacin bakwai da wani abu ta yi tata sallar,saidai yana sallamar ta amsa gami da miqewa zaune kan gadon,murmushi take masa wanda hakan ya sanyashi rage daurin fuskarsa"kar daiace har ka fito" ta soma cewa,ya kalleta yace "eh"yana mamakin yadda basu iya gaisuwa wa mijinsu ba,babu wadda ta fado masa sai fadilan,duk safiya sai ya gaidashi kamar yadda ya zame mata qajibi sannu da zuwa da adawo lafiya duk da sai yaso yake amsawa amma hakan bai dameta ba haqqinta take saukewa, "amma yaci ace yau a gida zaka wuni ko" ta sake shigowa da wani qorafin "a hakan kuna batan ran babu wani caring bare a faranta maka"yayi zancqn cikin zuciyarsa,a fili sai yace "maiduguri zani zuwa anjima zan dawo insha Allah"cikin tuhuma tace "maiduguri?gurin wa?...." "stop your suspicion,sai na dawo" ya katseta, "madalla"tave tana binsa da cike da kishi har ya fice Cikin motarsa qirar 4matics fara ya zabi yin tafiyar shi kadai,bayan yin addu'o'in matafiyi ya kunna motar ya fice daga gidan cikin tsammani mai yawa da fata na gari akan kanshi *mrs muhammad ce*👑 📘📘📘📚📚✍🏻✍🏻 [10/16, 2:10 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WA YASAN GOBE?...* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 👉🏼 *PART 3* 👈🏼 7⃣&8⃣ Cikin kwankin kullum cikin kuka take kwana take wuni,a haka ma an samu sauqi saboda takan kaucewa idon anty hauwa don kada ta dinga jin ba dadi,damuwa sosai ta yiwa zuciyarta yawa,tana jimantawa kanta yadda soyayyar aliyu ta gama illata ta,saidai bata barin damuwar ta tsawaita mata da yawa ba ta tsananta yin addu'o'i,da taimakon hakan ta soma samun kyakkyawar nutsuwa cikin ranta,koda yaushe cikin kula da ita anty hauwa take bata barinta ta zauna ita daya bare ta damu sosai,sau da yawa anty hauwan idan tana bata haquri kunya fadilan keji "nifa babu wanda yayimin laifi don Allah anty ki daina bani haquri,kunya hakan yake bani wallahi" Yara kam murna suke anty fadila ta dawo gidansu sunata tsalle,idan akace babu makaranta to suna liqe da ita wani lokacin har sai anty hauwan ta kore mata su tace su barta ta huta,ita kam dadi take ji idan tana tare da yaran saboda dama can mai son yarance ita,sosai mamansu taja kunnensu da kada su sake su gayawa kowa cewa anty fadilan tana nan gidan saboda yadda taga suna rawar qafa zasu iya subul da baka Ita kanta tayi mamaki qwarai yadda ta soma ragewa kanta damuwa kan aliyun duk da yake ba abun mamaki bane addu'a ai tafi qarfin wasa,sosai tayi yaqi da zuciyarta,bata bari bacin rai ya rusata ba,da zarar ta soma tunane tunane zata datseshi ta hanyar daukan qur'ani ta karanta,idan ta gama kuma ta shiga shafukanta na sada zumunta,komai anty hauwa ta hanata yi,duk da hakan fadilan taqi yarda don kullum tare suke shiga kitchen yin lunch ko dinner,wani lokaci kuma ta shirya mata yaran da safe 🔅🔅🔅🔅🔅🔅 Gudu sosai ya dinga yi shi daya cikin motar,cikin ikon Allah ya sauka lafiya,saidai tun daga yadda su ya gana ke faman tambayar fadilan ya sare da al'amarin ya tabbatar bata garin ma baki daya bare gidan,sallah kawai yayi ya baro garin,bai damu da yawan tafiyar da yasha ba bare ya nemi hutawa har yaci abinci,juyin duniya ya gana tayi ya tsaya yaci abinci amma qeme me yaqi,ya bata haquri bayan ya ajjiye musu kudade masu dama yace yana da abubuwan yi masu yawa a kano,haka ya kamo hanya ya taho,gudu na ban mamaki ya dinga shararawa ba qaqqautawa,sai da yaji tuqin na neman gagararsa sannan ya samu wani shago kam hanya ya siyi yoghurt yasha,bai fasa gudun nasa ba wanda ikon Allah ne kawai ya kawoshi garin kano lafiya 🔅🔅🔅🔅🔅🔅 Kwana hudu bai cikin daidanshi,matansa mata ne marasa kulawa,tabbas sunga canji sosai tattare da shi amma babu wadda ta damu da tambayarsa mene damuwarshi,momi kam ganin baice komai ba yasa ta tsuke bakinta ta qyaleshi don ta sani ida dai ya soma zurfin cikin nan nasa bai gayawa kowa komai sai lokacin da yaga dama *G*idan anty hauwa shine gida na qarshe da hankalinsa ya kai kai,anan ya tattara dukkanin fata da tsammaninsa,duk da wata zuciyar na tantamar mai zaya kaita can bayan ko gidansu bata je ba?,qarfe biyar da shirin na yamma ya gama shirinsa cikin qananun kaya da sukayi matuqar yi masa kyau Suna kitchen ita da fadilan suna hada abincin dare sunayi suna hirarsu,yara suka jiyo wadanda suka bari a falo suna kallo da yake alhamis ce suna cewa "ina wuni uncle....ina wuni uncle" gaban fadila yayi mummunar faduwa ta saki mirfin hannunta da take shirin rufe miya da shi,"shikenan yau zan amshi takardar rabuwa da shi" abunda zuciyarta ke gaya mata kenan "anty aliyu ne"ta fada tana kallon anty hauwa dake tace shinkafa "aliyu?" Ta fada tana kallon fadilan cikin kasa kunne,"ina zuwa" anty hauwa fada bayan ta ajjiye tukunyar hannunta ta fice da sauri,komawa fadila tayi jikin drawer ta jingina bayan ta hatde hannayenta a qirjinta tana jiyo sweet voice din sa,batasan me yasa take jin qunci a qirjinta dalilin gaya mata da zuciyarta ke yi takardar sakinta aliyun ya biyota da ita Ruwa aliyun yace ma anty hauwa ta bashi,duk ruwan dake freezer din falonsu ya qare sai lemo,da hanzari anty hauwa ta miqe ta hau sama ta dauko masa a parlour din abban kausar don bata son ya shiga kitchen din,ji yayi bazai iya jiranta ba don haka ya miqe ya shige kitchen din,a hankali fadila ta bude idanunta da a da ke a lumshe,cikin jikinta take jin tahowar tasa,nan da nan tayi wuri wuri da ido tana neman maboya,a asukwane ta shige bayan qofar wadda a kusa da ita freezer din take Kai tsaye ya qaraso ya dage freezer din ya sunkuya yasa hannunsa ciki,cak ya tsaya da qoqarin ciro ruwan da yake yi,sai yake jin qamshinta cikin hancinsa,irin qamshin da ya ji cikin bargo pillow da undies dinta,sakun murfin yayi ya soma kallen kallen kitchen din yana neman ta inda qamshin ke fitowa,ko ina ya kai idanunsa sai yaga babu kowa,tuni fadila tayi surrender bayan qofa numfashinta kamar zai dauke musamman da taji ua jingina a bayan qofar ya kuma qin barin gurin,yafi minti uku cikim kitchen din yaqi fita din qamshin turarenta na ahlamul arab kawai yake ji,hat sai da anty hauwa ta shigo hankalinta a tashe tana tsammanin ya ga fadilan,sai ta tadda shi a tsaye kawai jingine jikin qofar hannayensa harde a qirjinsa,"ina ka shiga ga euwan can na kaimaka" "ok" kawai yace ya gewayeta ta fice daga kitchen din itama ta rufa masa baya Ta maida yara dakinsu daga ita sai shi a falon,zuba masa ido tayi sosai tana kallonsa canji qara ta hango tattare da alin,fara'arsa ta sake qaranci sosai,tsiyayar lemon kawai yake yi yana dirkawa cikinsa,yadda bai tanka ba itama bata ce kamzil ba har sai da ya tashi da roba biyu ta ruwa da lemo,ya dago kai ya kalli antin hadi da sakin ajiyar zuciya "ni wai uncle meke damunka?tunda kazo naga kamar a hargitse kake?"wata ajiyar zuciyar ya kuma saki "fadeelah nake nema mummyn kausar" kamar gaske ta nuna alamun rashin fahimta sosai "kamar yaya?fadilan da kuke tare,yaushe dududu sumayya ta ke gayamin kun dawo daga china zaka ce ita kake nema kamar wadda ta bata" "bata tayi....bacemin tayi"ya fadi yana jingina jikinsa da kujera,yayin da fadila dake labe cikin kitchen ta zaro ido jin cewa wai nemanta yake "yayimin me? Me zayayimin ne?"ta tambayi kanta ba tare da tasan amsar tambayar ba Ya dora cikin wata iriyar murya "tayi tsammanin bana sonta ne bayan nima na dade ina sonta,tayi zatin maqiyinta ne ni alhali duk duniya babu mai sonta kamar ni...ta dauka ina zaune da ita ne bisa dole bayan kan son raina nake zaune da ita.....anty ta yimin gurguwar fahimta,ta gujeni a lokacin da na qara zurfi cikin qaunarta....ta gujeni a lokacin da dukkanmu ni da ita muka fi buqatar kasancewa da juna"ita kanta anty hauwa baki ta saki tana tsammanin ba aliyu bane,aliyyun da tunda take tare da shi zata iya cewa bata taba ji ko ganin yana kwatanta qaunar da yakewa wata diya mace ba aduniya koda uwar 'yarsa,fadila kam dake cikin kitchen duburburcewa tayi,sai jikinta ya fara rawa qafafunta suka gaza daukarta ta lallaba ta ja jikinta ta zauna kan kujerar roba bakinta rufe da tafin hannunta yayin da hawayen da sukayi kwana da kwanaki tana qumshe su yau suka samu qofa. Lallai ma yaudararta aliyu keson yi?,dama shi din shahararren mayaudari ne,shine a yanzu zai furta cewa yana sonta?wanne irin zama ne basu yi ba baice yana son nata ba sai ayanzu?sai yanzu da ya kwanta da ita?,ya tabbata kenan jikin nata yake so kamar yadda tayi zato tun farko? (Illar zato),sha'awarta yake kenan ba qauna yake mata ta cikin zuciya ba?,kuka ne sosai mara sauti ya kufce mata yayin da shi din ma ke can zaune dirshan gaban anty hauwa yana fayyace mata irin zaman da sukayi da fadilan,kunne sosai ta saka tana jinsa duk da yake tamkar tishi yake mata,duk yadda fadilan ta fada hakanne harda wasu abubuwan da fadilan ta boye ta qi fada Kafin ya kammala tuni har qwalla ta cika idanunsa duk da bata gai ga zubowa ba amma qiris take jira,soyayyar 'yan uwan taka sai Allah tuni tausayinsa ya kamata don zata iya dafa qur'ani kan aliyyu bai taba shiga makamancin wannan halin ba akan wata mace,ta karanto gaskiyarsa qarara,don dama ko ada bai iya qarya ba tun yana qaraminsa,zai gaya ma gaskiya ne ko za'a tsireshi don haushi,to saidai bata jin kuma zata shiga haqqin fadilan ta karya alqwari da ta daukar mata don aliyyu nata ne,bata jin zata sarayar mata da haqqinta tunda nata din ne,ita ke da iko da abunta,ita kadai tasha haqurinta ita kadai tasan me ta hadiya Cikin sanyin jiki da qunar rai yace"wai anty roqona take na saketa,tana tsammanin sakin nata abu ne mai sauqi har irin haka a gurina?" Ya kada kai yana cewa"bazan iya ba,bazan iya furta wadan nan kalmomi gareta ba koda duka duniya zata taru a kaina" dole ka sake ni aliyyu dole mu rabu ,bani kake so ba jikina kake sha'awa" ta fadi haka qasa qasa cikin kuka mara sauti,ya miqe "zan tafi tafi tunda kema bata gunki zan ci gaba da nemanta",tuni ya juya ya fice daga gidan,tausayin dan uwan nata ya kamata don tasan wahla kawai qanin nata zaici gaba da sha tunda fadila na tare da ita Kifa kanta tayi kan cinyarta ta sake sakin wani sabon kukan mai dan qaramin sauti,wani qunci zugi da radadi data rasa na meye take ji cikin ranta,anty hauwa ta kama hannayen fadila tana kallin qwayar idonta "fadila.....fadila,naga abubuwa da dama cikin qwayar idanun aliyu,naga soyayya naga qauna cikin cikin idonsa irin wadda ban taba gani ya yiwa wata 'ya mace ba,kinji komai da kunnuwanki no need na maimaita miki" Kada kai fadilam keyi,"anty na yarda aliyu na sona a yanzu bazan qaryata ki ba,anty amma ba ni fadilan yake so ba wani abu dake gareni yake so,tun yaushe anty....tun yaushe nake tare da shi nake kyautata masa bai taba cewa yana sona ba sai yanzu?sai yanzu da wani dalili ne ya jawo hakan?...Thank god aliyu na sona yanzu anty,saidai ......is too late anty I already displaced him from my heart,na goge cikin kundin rayuwata zan rayu da shi" kalmar ta fito daga bakinta hade da hawaye Sai dariya taso kama anty hauwa amma ta gimtse,with confidence fadila ke fadin maganar saidai qwayar idanunta kadai ta ta qaryata ta,bata sani ba ita kanta qaunar aliyyu tayi mata illar wadda take huduwa tun daga zuciyarta har zuwa idanunta da bakinta,bata da abunyi anty hauwa ta sani wani daci ne da fadilan ta dade tana guntsa taje fesarwa idan ta hanata kuma bata yi mata adalci ba,tasan cewa kokwanto ne yasa fadila fadin wadannan maganganun amma ba har cikin zuciyarta bane,ta kuma gama gasgatawa wani irin salon rikicin soyayya ne ya kunno kai kawai tsakaninta da aliyyun,sanoda haka sai kawai tave mata "shikenan fadila kici gaba da addu'o'inki ki yi ta istihara,Allah ya zaba abinda yafi alkhairi" Har anty hauwan ta kai bakin qofa fadila ta dakatar da ita ta hanyar cewa"am sorry anty idan maganganuna sun bata miki rai" murmushi ta saki "don't mind,banji komai ba araina fadila" murmuahi itama tayi mata tace "na gode" haka Allah yayi fadila bata aon bacin rai ko yashin hakai ko kadan kamar yadda bata son taa ta batawa wani rai ko ta shiga haqqinsa Kwana biyu yama cikin wannan hali,duk wasu harkokinsa na gida dana waje yaqi maida hankali kan kowanne,daga qarshe dai kasa jurewa yayi gani yake kamar su suka boye masa fadila,yana ganin da wani yashin hankalin gwara wani,da ya rasata gwara a yanke masa duk wani hukunci da za'a yanke masa idan yaso su bashi ita,ya gaza jure kewarta komai nasa ya yi missing dinta, 🔅🔅🔅🔅🔅 Tsakiyat uncle abba da momi ya zauna ya warware masu abinda ke faruwa kamar yadda halayyarsa take fadin gaskiya,momin ce ta saki salati mai nauyi yayin da uncle abba yayi shiru gami da yin tsai da ransa,sai a lokacin ne kuma hankalinsa ya soma tashi momi tayi shiru ne tana jiran jin umarni ko me mijin natazaya fada?,yayin da uncle abba ya rasa me ma zaya ce din?,sama da minti biyar kafin ya dago yace "tashi kaje aliyyu" cikin firgici ya dago kai yana kallon uncle abban,ya sake maimaita masa"ka tashi kaje nace mu zamu nemota" alhaji yaje fa kace?" Momi ta fada cikin fushi,a nutse uncle abba ya kalleta "to maimunatu mai zai zauna yayi min?,yaje kawai tunda ya gama nasa aikin ko,mu kuma ba sai muyi namu ba?" Tasan sarai halin mijin nata saboda haka ta gamsu da abinda yace "gaskiyane"shi kam aliyyu yadda bai tanka ba sabida rudani haka ya kasa tashi kansa na sunkuye jinsa yake kamar wani mutum mutumi,har sai da uncle abban ya gaji da ce masa ya tashi shi da momin suka taahi suka bar masa falon Da azahar momi ta dauki wayarta ta kira anty hauwa kamar yadda uncle abba ya ce ta ce mata yana son ganinta ko zuwa najima ne,sai kuwa aka taki sa'a suna cikin gaisawa kausar ta soma qwala kiran "anty fadilah!anty fadila!!na kasa daukowa"nama ne tace ta ciro mata cikin fridge sunce suna son dambun nama to naman ya riga yayi qanqara,tuni momin ta tsaya da amsa gaisuwar "maijidda wace fadilance a gidanki?" Cikin son boye boye tace "am ....fadila ce ta zo mu gaisa,dazun aliyun ya sauketa" "mu kuma dazu aliyyun ya bar nan yana cigiyar ta ba"momi ta katseta "aljanu ke miki wasa da hankali ko gida biyu su aliyun suka rabu?" "A'ah momi ai" "kinga dakata shi aliyun ya riga da ya sanar da babaku komai da kansa,dama maganar da na kira ki kenan akai,saboda haka idan anyi magariba ki dauko ta kuzo" Hawaye bibbiyu fadilan keyi"anty me yasa kika sanar musu anty,munyi alqwari dake anty,me yasa suka sani?" "Fadila aliyyu da kansa yakai kansa gun abba,momi kuma ta san kina gidan nan dazun da kausar ke qwala miki kira" "me yasa aliyyu zai min haka?,don me yasa zaije ga uncle abba?,me yasa baiyi sakin cikin rufin asiri ba?,so yake kowa sai ya ga laifinshi kenan?"sai lokacin tayi dana sani,tayi data sanin da ta fito tun ranar da yazo gida anty hauwan ya bata takardarta ba tare da kowa yaji ko ya gani ba,suna sake doso unguwar bugun zuciyarta na daduwa,tabbas da kafin su yi nisa naty hauwan ta gaya mata inda zasu babu shakka ba zata ba sauka zatayi,gaba daya jikinta rawa yaje ta kasa nutsuwa sai da anty hauwan ta riqeta sannan ta iya shiga falon......... *mrs muhammad ce*👑 📘📘📘📚📚✍🏻✍🏻 [10/16, 2:11 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WA YASAN GOBE?....* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 👉🏼 *PART 3* 👈🏼 9⃣&1⃣0⃣ Umminta ta gani da mominta zaune kujera daya,uncle abba da abban nata kuma na kujera daya,sai iftihal dake zaune dare dare kan cinyar abban nata,duk kansu suka amsa sallamar,sosai taji dadi cikin ranta don rabon da tasa iyayen nata a ido har ta manta,sai dai hararar da ummin nata ta watsa mata ita ta sagar mata da gwiwa,anty hauwa ce ta fara gaida su sannan itama ta gaidasun,sama sama ummin ta amsa mata don har gwara abbanta,cikin salubewar jiki ta koma gefan kujera ta rakabe Aliyyu ne ya shigo cikin sallama yana sanye da shadda dinkin tazarce kansa babu hula,da gudu iftihal tayo gurinsa,hannunta kawai ya iya riqewa bayan da ta gaidashi,gaida su yake saidai abba da umminta ne kawai suka amsa masa,yana shirin samun guri ya zauna uncle abba ya dakatar da shi ta hanyar cewa "kai....dakata ba zama na kiraka kayi ba...ungo nan" ya miqa masa farar takarda da abun rubutu "rubutawa yarinya sakinta tunda Allah yasa mun ganta" da sauri ya daga kai ya soma rarraba ido cikin filin falon yana neman inda fadilan take,can ya hangota a takure a gefan kujera kanta a qas Gaba daya idanunsa suka rufe,tuni ya manta da cewa akwai wasu wai iyayensa a falon ya durfafeta,idanunsa qir bisa kansa,wani shauqi mai cakude da matsananciyar qaunarta yake fisgarshi,sai da yaje daf da ita uncle abba ya daka masa tsawa wadda ta sashi dawowa cikin hayyacinsa "qaniyarka nace dawo nan" inji uncle abba yana masa nuni da gabansa inda zai zauna din bayan daquwar da ya watsa masa,a salube ya nufi gun yana tafiya yana waiwayen fadilan da kanta ke qasa idonta na digar hawaye,takardar ya sake miqa masa "ungo nan rubuta" sai a lokacin abban fadila yayi magana "haba alhaji bai kamata ba,ya za'ayi yaro da matarsa kuma yana son abarsa a tilasta masa saki,abinda ya faru ai ya riga ya faru,kuskurene kuma babu wanda baya yi,kuma ni idan banda shirmen quruciya irin na fadilan ma banga abun da yayi zafi haka ba,tunda kuma alhamdulillah ya gane sai muyi addu'ar Allah yaci gaba da hada kansu" "Wa?wannan?"uncle abban ya fada yana nuna aliyu da yatsa, "ai bai isa ba tunda tafiso ya saketa sai ya saketa,ai zaluncin ma alhaji yayi yawa,mun zaba mata miji ba tare da jin ta bakinta ba ko musa mana bata yi ba ta karba harda godiya tayiana biyayya,taje ta zauna da shi zuciya daya amma ya dinga azabtar da ita,babu kuma wanda ya taba sani ko sau daya sama da shekara guda har da kusan rabi,kuma yanzu don bamu da adalci tace bata da buqatar zama sai mu tilasta?don me?,mu zamu yi mata zaman auren?," sai lokacin itama ummi ta tanka "to alhaji tunda ya gane kuskurensa don Allah sai abar maganar,ke fadila wallahi tallahi na kuma jin kin furta mijinki ya sake ki ko mai ya hada ku kuwa sai....." "a'ah hajiya,ya kuke neman daure ma yaro qarqashi ne?" Inji momi" "barsu indai baso suke su nanamin su suka haifi fadila ba"inji uncle abba Cikin sauri hajiya amina(ummi) tace cikin girgiza kai "Allah ya kiyaye alhaji Allah ya sawwaqe,haba haba da kai da kaya ai duka mallakar wuya ne"ya dauke kansa ya maida kan aliyyu "saketa nace ko?"ya nuna shi da yatsa "kuma don ubanka" (aliyyu bai yaba jin yayi zagi ba ko da wasa sai ranar "a gidan nan zata ci gaba da zama ni ne dai ubanta "qasa yayi da kansa yaqi furta uffan,babban abunda yasa jikinsu yayi sayi ganin hawaye nabin fuskar aly,mutumin da komai tsanani ba zaka ga koda qwalla bane bisa fuskarsa yau shi ke kuka saboda mace?,anty hauwa kamar ta tayi haka take ji don dai kawai zancan manya ne kuma basj bata damar shiga ba,sauqinta daya ma iftihal tayi bacci kan cinyar ummi "Abba wallahi ko wuqa zaku sa ku dinga yankan naman jiki na bazan iya sakin ta ba,kuyi min afuwa abba" abban fadila ya dubi uncle abban "don Allah salim a naci albarkacin amintaka ina mai baka haquri kan ka sassauta fushinka kan yarona"falon ya dauki shiru na wasu lokuta kamin abban ya saki ajiyar zuciya "naji...naji,abu na farko da zan fara fada shine alhj abbas kai da hajiya amina ku yimin alqawarin babu wanda acikinku zai tursasawa fadila koda ta bayan fage ne kan sai ta koma gidanta ba tare da ita ta yanke hakan ba?" Ba yadda alh salim ya iya don yana tausayama aliyun yace "nayi" ummi ce tayi shiru har sai da hajiya maimuna tace "baki ce komai ba" "nima nayi"itama ta fadi cike da tausayin aliyu "Abu na biyu,anan gidan fadila zata zauna har sai taji ta amince don radin kanta zata koma,idan yaso naga mara kunyar da zai koreta don ba gidansa bane haka nan ba da qwandalarsa na hada na gina gidana ba"ya fadi yana muzurai,sarai aliyun ya sani da shi abban yake amma sai ya sunkuyar da kansa,saboda shi kam a yanzu kome zasu fadi yaji ya gani kuma ya yarda suyita fadin,ko bulala dukkansu zasu dauka suyita zabgarsa yaji ya amince zai kuma shanye tunda dak an janye batun saki cikin lamarin,uncle abba ya nuna shi da yatsa "saura kuma naga qafarka inda take bare kace zakayi yunqurin takurawa ko tursasa mata sai na saba maka fiye da tsammaninka,tashi ka bawa mutane guri mutumin banza kawai",bashi da zabi illa barin falom kamar yadda abban ya umarcesu ya miqe ya fita bayan ya duqa yace "na gode Allah ya saka da alkhairi ya qara girma,Allah kumabya huci zuciyoyinku"yana tafiya yana satar kallonta har yanzu kanta na duqe taqi ma ta dago ya kalli koda fuskarta ne Sosai uncle abba bayanin dalilin yin wannan hukuncin bayan ya sallami fadilan da anty hauwan,yana sone koda aliyun yayi nadama ya sake sanin darajarta da amfaninta a gunsa kafin ta koma masa,cikin dariya abban ke cewa"haba alhaji ai ba sai kace komai ba,amma dai don Allah a sassautawa yarona haka"dariya duk sukayi,daki aka bawa fadilan kusa da nasu sumayya,amma tace tafiso ta zauna cikin su sumayya,a daren aka kawo mata madaidaicin gado da cupboard irin nasu rabi'ah aka sa mata duka adakin kasancewar dakin qato ne sosai,su suka taya ta shirya kayan suna ta rawar jiki zasu zauna tare,batasan lokacin da su ummunta suka tafi ba sai da anty hauwa ta hauro saman take sanar mata Cikin daren babu dan qaramin haukan da baiyi ba,kuka ma kasa zuwa masa yayi sai zafi da radadi da zuciyarsa keyi,daurewa kawai yakeyi yana sakar musu jiki don kada ya shiga haqqinsu,wani lokaci idan kewar ta isheshi dakinta yake tafiya yayi bacci cikin bargonta ya kalli hotunanta sannan yake samun relief (Qalubale a agareku iyayemmu mata har ma da mazan,da kuna ji kuna gani 'ya'ya yenku zasu dinga auri saki,babu kwaba balle hantara,wani lalacewar ma idan anyi sakin wai sai ya kwaso yaran ya kawowa uwar ita ce mai riqe masa kuma tana ziga shi har kina furta gwara da ya saketa,,to ahir din mu domin kuwa kada mu manta mun haifa ko bamu haifa ba an haifa mana,za'a yiwa taki 'yar ko 'yar 'yan uwanki kiji idan da dadi? Ai ko.matar ba ta gari bace akwai matakai da Allah s.w.a yace abi kafin akai ga rabuwar bawai rana tsaka daga an dan saba masa laifin da bai kai ya kawo ba ya karkace ya danqaro saki ba,to wallahi muji tsoron Allah,shi mai sakin dake mahaifiyar me goyon bayansa ina zato a cikin 'ya'yansa ko jikokinki ba za'a rasa mace ba,ya zakuji yayin da aka koro muku ita?,saki yayi yawa musamman acikin al'ummar mu ta hausawa,don Allah mu daure mu gyara ko ma samu gyaruwar al'ummar mu wadda wata tabar barewar tarbiyya daga an saki uwa ne shikenan sai gida ya tarwatse kowane yaro yayi nasa alqibla,babu mao saita siu kan hanya wato uwa ta gari,Allah kasa ku dace mufi qarfin zuciyarmu,ameen) 🔅🔅🔅🔅🔅 Sosai ta koma bakin aikinta don uncle abba yace babu mai hanata,babu yadda aliyyu ya iya haka ya zubawa sarautar Allah ido,ina ma yaga bakin magana koda yana da ta cewar?,don ko yazo gidan iyakacinsa parlour ko kallon upstairs inda dakunan baccinsu yake momi ta shiga balla masa harara kenan,haka zatayi kicin kicin da fuska har sai ya gaji da muzurai ya qara gaba Ita kuwa uwar tafiyar tun daga lokacin da akayi hukuncin bao sake sanyata cikin idonsa ba,har addu'a yake Allah ya hadasu amma daidai da gilmawarta Allah baisa ya gani ba,tana sane ta sani,matuqar taji muryarsa to babu ita babu fitowa tana qule cikin daki ko kitchen idan a qasa take har sai ya bar cikin gidan 🔅🔅🔅🔅🔅 Da yammacine suna zaune cikin parlour ita da sumayya da rabi'ah,momi bata nan ta tafi dubiyar yayanta da baya jin dadi alh datti ita da iftihal suka wuce,gidan sai su ukun,lokaci lokaci rabi'ah naeqa kitchen ta duba abincin dare da ta daura sumayya kuma na tsefewa fadila calabar din da take kanta,saboda tsawo da santsin gashi da hannu suke tsifar,yayin da fadila ta jawo wasu fuskarta tana tayata,wani film da suke masifar ao suke kallo a m.b.c bollywood,na soyayya ne sosai,jarumin film din na musu kama da aliyyu sosai hatta da halayya,don haka wani lokacin ma ya aliyu suke kiransa duk sanda aka sako film din,suna son film din don haka idan ana kallonsa ko hira ba'ayi,saidai idan anzo wani gun daya burgesu, A hankali aliyyun ya turo qofar falon with confidence don tun a gate ya tambaya aka sanar masaomin bata nan,basu ga shigowarsa ba sai sumayya kawai don rabi'ah na kitchen duba girkinta,fadila kuwa gashin da ya rufe mata fuska da yadda film din ya yafi da hankalinta sosai yasa sam bata lura ba Sumayya ta bude baki zata yi masa sannu da zuwa ya dora yatsansa kan labbansa,gum kuwa tayi shiru,ya bata umarni na gaba da ido alamun ta tashi a hankali ta haye samansu,ba musu kuwa cikin sada ta haura saman,gurbin da sumayyan ta tashi nan ya maye,harda dan jawota ya jinginar jikin gwiwoyinsa,fadila uwar 'yan son jiki kuwa ya jingina abunta harda cewa"yauwa sumayya dama baya na ya gaji,calabar ko ashirin bata kai ba amma taqi tsefuwa ta dadin rai?"baice uffan ba ya kama jelar kitson ya soma tsefe mata kamar yadda yaga sumayyan nayi,ita kuma bata damu da rashin amsawar sumayyan ba ta bayar duk film din ne ya dauki hankalinta,rabi'ah ce ta fito da sauri daga kitchen din don kada tayi missing wani gurin,turus tayi ganin aliyyun a gun da sumayya tasan ta bari,itama yatsan ya dora mata kan lips nashi,yayi mata nuni da ido kan ta koma kitchen,nan ne ma fadilan taga giftawar komawan rabi'an kitchen din "rabi'ah za'a wuce gun da kike son kalla fa" "ina zuwa anty ban qarasa hada miyar bane" Gaba daya ya shagala,wani irin farinciki ke ratsa shi,santsi kyau da qyallin gashin ya hanashi ganin wahalar tsifar,sai gashi sun kusa gamawa saura guda daya,yana ankare da yadda take bawa film din muhimmanci,murmushi kawai take zubawa hadi da sakw gyara zama,sai da aka zo wani gu da yayi masifar qayatar da ita ta saki murmushi tana cewa "hmmmm......soyayya" ta dan waigo tana cewa"don Allah sumayya basu burgeki ba yadda....."kasaqarasa maganar tayi ganin aliyyu zaune dare dare saman kujerar yaa mata tsifa,to sumayya ce ta rikide ta zama shi ko idanunta ke mata gizo?....... *Mrs muhammad ce*👑 📘📘📚📚✍🏻✍🏻✍🏻 [10/16, 2:12 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WA YASAN GOBE?....* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 👉🏼 *PART 3* 👈🏼 1⃣1⃣&1⃣2⃣ Sai da yasa bakinsa ya hure mata idon sannan ta dawo hayyacinta,da hanzari ta miqe sannan kuma a guje tayi sama tamkar wadda taga dodo,binta shima yayi a hanzarce yana kiran ta tsaya,ganin da gaske take ba tsayawa zata yi din ba ya sanya shi cafkota a matattakalar qarshe,cak ya dagata yayi dakinsu rabi'an da take son shigewa,cikin sauri sumayya dake zaune saman dressing chair ta fito ta bar musu dakin Tsakiyar gado ya direta sai haki suke dukkansu saboda gudun da suka kwasa a step din benan bugu da qari yadda zuciyar kowannensu ke bugawa,sun zubawa junansu ido cirko cirko da su kamar zakaru,a hankali yake hawowa gadon yayin da ta soma ja da baya har ya qureta,suka sake zubawa juna ido,shi nashi na tsantsar so da qaunace da suke sake huruwa cikin zuciyarsa take kuma aika saqonni zuwa sassan jikinsa,yayin da nata kuma na jin haushi tsoro da fargaba ne don bata manta wannan dare ba,kasa jurewa yayi sai da ya miqa hannunsa ya janyota ta fado jikinsa ya matseta gam a qirjinsa Cikin fusata haushi da mamakin aliyyun ta soma tureshi,saidai ko motsi baiyi ba don qarfin ba daya bane,a hankali ya soma sinsinar wuyanta cikin kunnuwanta zuwa gashin kanta,ya dago fuskarta a hankali ya tura harshensa cikin bakinta,tsotsa yake sosai tamkar wanda ya samu sweet yayin da ita kuma take turje turje hadi da yunqurin tureshi daga jikinta saidai sam ma shi baisan tana yi ba,ganin duk iya qoqarinta ta kasa barin jikinsa sai ta fashe da kuka,hawayen da ya gangaro fuskarta ya taba nashi fuskar shi ya ankarar da shi,ya zare bakinsa daga nashi ba tare daya bari ta bar jikin nasa ba,kukanta take sosai yayin da ya zuba mata ido,gaba daya ya marairaice ya koma kalar tausayi " *fadeelahhhhh*"ya kira sunanta cikin wani irin yanayi tamkar mai rada,da sauri ta dago kanta ta kalleshi don wannan shine karo na farko da ta taba jin sunanta a abakinsa, "fadeelah" ya sake kiran nata ta sake itama kallon nasa "please fadeelah forgive me,I know I hurt you I break your heart,babu wanda ya wuce kuskure,fadeelah I love you more than words can say,I can't do without you,na kamu da soyayyarki,pls kada,pls kada kice zaki hukuntani da tarin laifuffuka na,if bazaki iya yafemin ba ma na amince kiyimin kowanne irin hukunci zan dauka,amma bazan iya jure rashin ki ba" "Haka aliyyu ya shahara da yaudara?,haka aliyu yake?,taya mutumin da ya qika ya kuma sanar maka bazai taba sonka ba yanzun yace yana sonka?,bazai taba yiwuwa ba it can't"ta fadi hakan cikin zuciyarta tana girgiza kai,tayi wani kukan kura ta shammaceshi ta fusge daga jikinsa,jikinsa ya riga da ya mutu shi yasa ta samu nasarar qwacewar,tana yunqurin sauka shi kuma yana yunqurin sake cafkota aka turo qofar dakin,tuni fadila tayi amfani da wannan damar ta shige toilet "qaniyarka,qaniyarka nace" cewar momi dake watsowa aliyyu daquwa,sunkuyar da kansa yayi qasa yana Tsakiyar gadon da tuni ya bedsheet dinsa ya yamutse,ta qaraso cikin dakin tana riqe da murfin qofar dakin da daya hannun ta nunawa aliyyu waje "zo ka fice ka bawa mutane guri mara kunya,ka keta idanun qannenka ka biyota har kan gadonta" "kai momi kamar ba mata ta ba"ya fadi hakan cikin zuciyarsa yana ficewa daga dakin Momi ta qarasa bakin qofar toilet din ta qwanqwasa tana cewa "fito" fadilan kanta a sunkuye kunya da takaici na sakadarta ta fito,momin ta dafa kafadarta tace "ko wani bak gaya min ba na sani kina son ali,muma kuma bamu taba fatan aurenku ya rabu ba har a qiyama,munyi hakanne don ya sake sanin darajarki da qimarka ta yadda ko nan gana bazai sake wasarere da lamuranki ba,ki samu yi duk mai yiwuwa ki tabbatar da soyayyarki cikin zuciyarsa kin fahimceni?" Cikin gamsuwa ta gyada kai tana yabawa momin ta yadda son kai bai rufe mata ido ba,bata duba cewa aliyyu danta bane bare ta bari tana gani a cutar da ita ba,qaunar momin da qimarta suka dadu cikin zuciyarta *_1:30 am_* Qarfe daya da rabi na talatainin dare fadila na kwance rub da ciki tsakiyar gadon ta,gaba daya ta rasa bacci cikin idanun nata,duk juyin da zatayi qamshin turaren aliyyu take ji daga bakinta har kayan jikinta,har kaya ta sauya amma a banza man kare don bata daina ji din ba,tana kallon yadda su sumayya ke baccinsu hankali kwance sai take jin dama ita dince su,basu da wata damuwa,wayarta dake gefan pillow dinta ta soma haske wanda ke nuna alamun kira ne ke shigowa,cikin mamakinta daga wayra tana duban kiran baquwar numbace,ta zubawa kiran ido har ya katse,ba'a fasa kiran nata ba har sai da ta tashi da missed call bakwai ana takwas dinne ta yanke shawarar dagawa ko wani abunne ya faru,ta danna ok ta kara a kunannta tayi shiru ba tare da tace komai ba "Bakiyi bacci ba fadeelah?" Ya tambaya cikin wata iriyan sassanyar murya wadda har sai data sanya fadila runtse idanun ta,tana jin qaunarsa na yawo cikin jinin jikinta,shiru tayi masa har ya qara cewa "me ya hanaki yun bacci a irin wannan lokacin fadeelah?" Nan ma shirun ta sake yi masa,saidai ita kadai tasan yadda take ni'imtuwa da jin muryarsa mai tsada "nasan kika jina fadeelah,kuma bana tantama abunda ya hanani bacci shi ya hanaki....,sau da qauna ne ke dawainiya damu baki daya,tunaninki shi ya hanani sakat kamar yadda na san cewa tunani na shi ya hana miki yin bacci,da zaki ganni a yanayin da nake ciki zaki tausayamin,da zan iya ciro zuciyata kiga dumbin qaunar ki da ta cikata fadeelah da nayi,na tabbata da sai kin min addu'ar Allah ya rage min,jin shirun yayi yawa yasa yace "hello,are you there?" Ya duba phone dinshi tana nan bata yi hanging up ba,ya sake maida wayar kunnensa yana cewa "please fadeelah say something ko zan samu relief,am sorry fadeelah and I said it really" tsananin mamaki ne ya mamaye fadila,shin da gaske ne ba mafarki take ba aliyyun ne kuwa?aliyyu salim maitama? Aliyyunta?,mafarkinta na kullum,burin zuciyarta,shike gaya mata wadan nan tsadaddun kalamai?....kalaman da ta dauki tsawon shekaru tana dakon jinsu?irin qaunar da ta jima tana lalubenta daga gun aliyyun,shin da gaske ne a yanzu ta samesu?,eh...yes ta samesu but he didn't deserve ya samu amsarta a arha har irin haka,now its her turned,its her field to play her game..... Muryarsa ta tsinto cikin sanyi yana cewa"fadeelah I know you gave me happiness and I gave you a reason to cray,u gave me your care and I stabbed you from behind,am sorry for having given you nothing in return for you having given me everything am sorry kiyi haquri....." kasa jure ci gaba da jin kalamansa tayi,tasani ko iya wannan ya isheta,ta samu qauna daga gun aliyyun,ta samu soyayyarshi,ya kawo mata kansa yana begging dinta ta bashi soyayyarta.....,tuni ta katse wayar wani dadi na nuqurqusarta,ta sani tabbas zai kuma gwada kiranta saboda haka ta kashe wayar gaba daya,cikin zaqi da gardin kalaman da aliyu ya kasheta da su bacci yayi awon gaba da ita tamkar dama au take jiran ji,bacci ne mai cike da mafarkan aliyyun a yanayi daban daban,shi kam tsai yayi da wayar a hannunsa cike da al'ajabin yaushi mace ke kashe wa waya?,tabbas ya sake yarda fadilan tana da wani matsayi da babu wata 'ya mace da ta kama koda gefanta ⚜⚜⚜⚜⚜⚜ Tunda ta kashe wayar bata kunnata ba sai washegari sha daya na safe tana shirin tafiya office sha daya na safe,cikin shadda take pinch sai maiqo take dinkin doguwar riga aka mata,cif cif rigar tayi mata kamar a jikinta aka dinkota,ta bude sosai daga qasa rigar,tana cikin yafa orange mayafinta sumayya na koda kyawun da tayi"wallahi anty kyawunki na daban ne Allah kuwa ba don wai nayi ziga ba,ko bakiyi kwalliya ba kyanki fitowa yake,zanso yaya yaga wannan kwalliyar" Harararta fadilan tayi"ke dai kin shiga tara,tuni rabi'ah ta dade a school ke kin zauna kanzagi kinqi fita,to bazai ga kwalliyar ba,sumayyan ta qyalqyale da dariya hadda kwanciya saman gadon"wallahi anty kiyi a hankali kada amiki qwace don har yau yayin ya aliyyu ake ba'a dena ba,kullum Allah ne da kullum wallahj dai ya fatattaki 'yammata,kada ki dauka qananu,a'a wlh anty hadaddu masu ji da kansu 'ya'yan manya kuma",fadila ta tabe baki kishi na cin ranta duk datasa haka dinne amma sai tace "dawar wani karkarar wani abincin wani kuma gubar wani"ta dauki wayarta dake gefan sumayyan zata fice sumayyan nata sheqa dariya,text ne taji ya shigo hakan ya sanyata dakatawa daga yunqurin fitar da takeyi,number din da aliyyu ya kirata ne jiya Tun shidan safe saqon ya shigo "if u can't see the tears in my eyes,I beg you feel the pain in my heart....fadeelah na rantse I will do anything and everything just to take away all d hurt that you feel,please na roqeki give me and let me set thing straight,am sorry once again fadeela and I love you I really love you...."gaba daya ya zare mata dukkan kuzarinta,jikinta ya saki,maimakon fita sai ta koma bakin gado ta zauna,sumayya daketa leqen wayar tana qumshe dariya tace "anty lafiya dai ko?" Ta saki ajiyar zuciya gami da dauke idonta daga kan screen din wayar "lafiya lau me kika gani?"sumayya ta kada kai tana cewa "gani nayi kin shirya zaki fita kin dawo kin zauna,jiya kuma fa anty naga cikin dare baki yi bacci ba ko" hararar fadila ta sake aika mata tana kada kai cikin zuciyarta tana cewa "lallai na yarda ba qaramin illa soyayyar aliyyu ta yimin ba,a fili sai kuma tace "naji to sai kuma akayi yaya?" Ta fada tana ci gaba da jifanta da hararar wasa,miqewa summayan tayi tana ci gaba da qunshe dariyarta tace "k'n,uhmmmm,a'ah anty ni bance komai ba daga wannan,amma dai anty kiyi a hankali saboda yayammu gwarzo ne kuma gwani ne,he is hero,zai iya saaaaaace zuciyarki ba tare da kin sani ba" Pillow dake kan gadon ta jawo ta jefi sumayyan da shi tana cewa "ban guri mara kunya" gocewa tayi ta fice da gudu tana dariya,sake mai da kanta fadila tayi kan saqon taa sake karantawa,ba shakka aliyyu shu'umi ne,so yake ta qarfi da yaji ya wargaza mata duk wasu makaman yaqinta,ya shirya tunkararta da duk wasu makamansa wanda tana tsammanin indai haka ne mawuyacine ta iya kubuta daga kaifinsu,duk ya kashe mata jiki kamar yadda ya saba ta qarfin tuwo ta gayyato dauriya sannan ta samu ta fita,ta tadda momi da sumayyan a falo,ta yiwa momin sallama,sumayya tace "a dawo lafiya anty.....momi dama inason baki labarin abinda na gani dazu,wata soyayya ake mai fada fada aciki"ya fada tana satar kallon fadila dake qoqarin ficewa daga falon fuskarta dauke da murmushi,a sace fadilan ta watsa mata harara mai nufin gargadi a fakaice ta qarasa ficewa,sumayyan nata qyatunta tace "na fasa anty kada ki hanani kudin ankon".......... *Mrs muhammad ce*👑 📘📘📚📚✍🏻✍🏻✍🏻  [10/16, 2:13 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WA YASAN GOBE?....* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 👉🏼 *PART 3* 👈🏼 1⃣3⃣&1⃣4⃣ Qarfe hudu dai dai ta kammala sallar la'asar dinta a masallacin mata da nan cikin gidan radiyon,ta goge kyakkyawar fuskarta da hoda,ta murza dan qaramin turarenta na (asaal brush perfume)wanda bata rabo da shi cikin jakarta saboda dadin qamshinsa gashi kuma qaramine baya da cika guri,ta saba jakarta bisa kafada sannan ta dauki wayarta ta nufi office dinsu don ci gaba da aikin takaddun programme dinta na gobe da ta baro ta taho yin salla Ta tura qofar ta shiga kasancewar babu kowa ciki fauziyya ta tafi yiwo wani aiki a a ministry of education shi yasa bata damu da yin wani sallama ba, Taja takardun gabanta bayan ta zauna ta dora daga inda ta tsaya,sosai yanayin tsarin programme din na gobe ke burgeta muhawarar da za'a tafka cikin shirin,lokaci lokaci takan saki murmushi gami da gyada kai,hakanan cikin jikinta ta dinga jin tamkar ana kallonta,cak ta tsaida rubutun,kan ta kai ga yin komai an zuro hannu an zare takaddun,tabi hannun da kallo har zuwa fuskar wanda ya gabatar da aikin,aliyyu ne tsaye qyam a agaban teburin nata,sanye yake da shadda ruwan madara(milk colour) dinkin yarbawa,rigar iyakacinta gwiwa hakanan hannun rigar shima gajere ne iya gwiwar hannu,sai manyan aljihu gefe da gefe,wandon dogo ne,kanshi babu hula sai kyakkyawar sumarshi dake cike da gayu da tsafta,idanunsa na saye da gilashin nan nasa fari qal wanda tana iya hango fararen qwayoyin idanunsa dake zube fes a kanta Kallonta yake sosai ba tare da yace komai ba,da azama ta miqe hadi da ture kujerar da take kai baya,tasa hannu zata dauki jakarta gami da qoqarin ficewa daga tsakanin table din,taku uku yayi ya tsare mata hanyar ficewar,baya tayi da sauri saboda ganin yadda yayi gab da ita kamar mai shirin fadowa jikinta,ganin ta sake yin baya ya sanya shi sake shigowa cikin shima,da haka har ya danganeta da bango,sosai take jin fitan numfashinsa wanda ke cakude da qamshin turarensa Ya dage sai ya sanya qwayar idanunsa cikin nata,saidai sam taqi yarda hakan ya faru,lumshe idanunsa yayi gami da nufar bakinta kai tsaye yana mai kwadayin tsotsar tattausan lips dinta,tuni ta gano manufarsa ta sunkuya ta qasan table din ta zille,bai san hakan ya faru ba sai da ya jishi ya dangane da bango,da sauri ya bude idanunshi,can ya hangota har ta dora hannunta kan handle,cikin zafin nama irin na cikakken da namiji ya haura ta saman table din don sai yafi masa sauri,taku hudu ya isa gareta,lokacin tuni har ta sanya qafarta waje Jawota yayi har sai da ta fado jikinsa uasa hannayensa ya rungumeta,da qarfin tuwo take son qwatar kanta saidai hakan ya gagara,batasan wani yazo gilmawa ya gansun a hakan saboda qimar da take da ita agun dukka ma'aikatan gidan ba zata so hakan ya faru ba,ta kuma kasa bude baki balle tace ya saketa sai kawai hawaye ya balle mata,Allah ya taimaketa sai ua dauketa cak ya dawo da ita cikin office din hadi da murza masa maqulli ya kullesu Kujera ya janyo ya dora ta akai yana maida numfashi,tsaye ya sake yi a kanta ya zube hannayensa cikin aljihun wandonsa yana sake qare mata kallo kai kace ranar ya soma ganinta,ita kuwa tana zaune sai qananun hawaye take,ya sake taku biyu ya matso gabanta cikin wata iriyar cool voice yace da ita "fadeelah pls stop craying,I can't take it anymore,I know shirun wanda aka ma laifi yake nufi...I know,ki hukuntani kawai fadeelah kimin hukuncin da kike jij shi zai sa temper din da kike ji game da ni zai tafi,zan iya dauka,nasan duka girman laifi na ne ya jawomin,amma fadeelah kinja bakinki kinyi shiru,kinqi cewa komai kwata kwata why?,please(ya hade tafukan hannayensa)ko zagina ne kiyi fadeelah indai zakiyi magana indai kuma hakan shi kadai ne hanyar da zai saki ki huce,ko duka na ne ma kike so kiyi indai shine zai saki ki huce am ready fadeelah" Ko daga kai ta kalleshi bata yi ba balle yasa ran zata ce wani abun,hakan take masa ko wani lokaci,ya tsani shirun nan nata,yana ci masa tuwo a qwarya,ya fuskanci babu ta yadda za'ayi su fuskanci juna babu ta yadda za'ayi ya samu abinda yake buqata matuqar ya barta taci gaba da yin shirun bayan kullum bai cikin nutsuwarshi duk ta sanadiyyarta....duk ta sanadiyyar qaunar da yake mata,bayan kk yaushe bashi da wani muradi sai nata,ta riga da ta gama kashe masa jiki da qwayoyin sonta da bai taba tsammanin akwai kalarsu a duniyarmu ba,banda time to time yana ganinta da yana tsammanin tuni ya dade da zaucewa,yana tare da ragowar matansa amma ita yake gani,zaici abinci amma sai ua bude hotonta cikin wayarsaa fakaice yana kalla ko da su salima na gun sanna zai samu ya iya ci A yau dai yaci alwashin ba zaya qyaleta ba sai yaji ta bakinta,bazai barta ba sai anyita ta qare,ya jawo daya kujerar ya zauna a gabanta gwiwarsa na manne da tata,yayi mata kane kane ya hanata ta ko motsa duk lokacin da tayi yunquri sai ya maidata ya zaunar,idanunsa sun kada jajur "I promised ko da yau zamu kwana anan indai bakice komai ba na shiryawa hakan,ni ko ke babu inda wani zaya motsa,u stole my happiness any moment in my life am feeling am lonely,ina jin na rasa komai na rayuwata,why me yasa ba zaki yafemin ba?" "Na sani I let you down,I made you frown,na sani I dont deserve forgiveness,but I want you to see the depth in my apology just listen to mu heart,it has been torn apart broken,but it still beats for you,ina sonki fadeelah ina sonki!!!..... "Baka sona! stop saying it aliyyu,already ka riga ka gayamin *baka sona baza ka soni ba ko anan gaba kada nayi tsammanin zaka soni*,ka manta aliyu?..ka manta?,duk wanda yace baya sonka da safe ya dawo da yamma yace yana sonka he does not mean what he said,yana nufin wani abu ne na daban ba son ka ba Sak yayi yana kallonta,bai taba tsammanin tana da baki har haka ba,but....at least yaji dadi...yaji dadi da yau ta bakinta ya gaya masa wani abu da ta qunshe cikin zuciyarta game da shi,don haka yana ganin dama ce ta samu gareshi,hannayenta ya kamo tana qoqarin zamewa,hakan bai dameshi ba ya riqe hannayen qam qam, "duk abinda kike tuhumata da shi na amince na aikata din,annabimmu ya umarcemu muyi soyayya saisa saisa don zata iya juyewa qiyayya,hakanan ya umarcemu da kada mu zafafa qiyayya don wata rana zata iya zama soyayya,na mance da hakan,na tozarta kyautar da iyayena suka min shi yasa yanzu Allah ke mani hukunci,na manta da cewa *babu wanda yasan gobe sai Allah*,but now fadeelah I identified my mistake,I made so many mistaken,sai dai ki zama mai afuwa yafiya rangwami da sassauci" ta sake zame hannayen nata da sauri ya kama su "I love you.....I love you" "nooooo!" Ta fadi hawaye na zirya a kumatunta, "baka sona aliyyu....bani kake so ba jikina kake soo.....don me yasa da can baka kusance ni ba sai da nayi amfani da wani abun?,don me yasa baka soni ba sai da ka kusanceni?,ina buqatar amsoshin wadan nan tambayoyin aliyu!"ta qarasa fada a dan tsawace wadda kanta bata san ta iya ta ba balle aliyyu da ya zuba mata ido hadi da sakin hannayen ta ba tare da ya sani ba Kafin yace komai akayi knocking qofar ana fadin "yau kuma me muka samu a office din namu anty fadila ta rufe mana qofa?"cewar fauziyya da yarinyarta dake tayata knocking qofar,kasa motsi fadilan tayi koda na yunqurin goge hawayen ta ne,cikin rashin kuzari ya isa ga qofar ya bude,fauziyya ta kalli fadila da aliyyun tana son tuna inda tasan fuskar,sai ta saki murmushi tana komawa baya "oh...sorry na katse ku ko?,ku gafarceni"ta juya zata wuce tana murmushi"anty fadeelah iman tace a rage kukan nan,duk da ta sani na soyayya ne"aliyu baisan sanda yace "baiwar Allah....don Allah sai ya zama laifi don mutum na tsananin aon matarsa?,don kawai......... Zumbur tayi tace"ni din ma bance laifi bane"fadilan ta katse shi da sauri,dariya fauziyya ta sake yi ta gyada kai bayan ta gama qare musu kallo"wow,salonsoyayyarku abun sha'awa ne,ya burgeni hakan,well.....koma dai mene ne naga zallar son junanku cikin qwayar idanunku,Allah ya bar soyayya"tayi gaba ta kama hannun iman da tuni tayi gabanta tana ta tsalle tsallenta,ta nufi ofishin da zata kai aikin da taje yi A sanyaye ya koma gabanta ya tsaya ya zubawa qasan office din ido wanda ke shimfide da terrazzo,a hankali ya saki hannayen nasa,ya tsugunna a gabanta tamkar mai kama ruwa ta yadda zai iya gano fuskarta sosai don kuwa kanta na duqe tana sharar qwalla,"fadeelah" shiru tayi ya sake cewa "fadeelah kin daina sona?" Nan ma shiru "fadeelah kin daina qaunata ko?!" Ya fada cikin dan fusata,a zafafe itama ta mayar masa "amsa kake so kaji?"daga girarsa yayi idanunsa na kanta"yes!" "Na daina sonka bana sonka,kai ada din ma ba sonka nake ba,ban fahimta bane sai yanzu!" Ta fada kanta tsaye ba tare da kawaici ba,lumshe idanunsa yayi yana jin radadin saukar kalaman cikin kunnuwansa kamar ana soka masa mashi,kusan wannan itace kalma mafi muni da yaji wadda ya jima baiji irinta ba,mace ta farko da zuciyarsa ta soma so don radin kanta ta kuma yi mata wani irin kyakkyawar masauki can cikinta tunda Allah ya ginata,irin masaukim da bai taba budewa wata mace koda bakin qofarsa...yau ita ke furata bata sonsa,kalmar da tunda yaje babu wata 'ya mace da ta taba furta masa ita sai ita din,wani daci na kalmar qiyayya da aka gaya masa ke ratsa zuciyarsa Sai yaga bashi da wani mataki da zai dauka saboda haka itama ta dandani makamancin wannan dacin koma wanda ya fishi,saidai yana son tabbatatwa da kansa da gaskene bata sonsa?,ya bude idanunsa ya zubesu fes a kanta har yanzu kanta na qasa tana share qwalla,"fadeelah!" Ya kirata cikin wata iriyar murya,bata amsa ba hakanan bata kalleshi ba,ta sani babu abunda bai so irin shirun nata "fadeeelahhhh!"ya fada cikim qaraji,bata sanda ta dago kai suka hada ido ba,da sauri tayk qoqarin maida kan nata amma sai ya fita hanzari,da sauri ya riqe habarta ya dago kan nata........ *note*:don Allah masu caccanza numbers na novel dina na roqeku ku daina🙏🏻,sai nayi typing sai acanza tsarin number a dinga rikitarmin da makaranta na to gaskiya bana so,idan kuma aka ci gaba to ba shakka zanyi Allah ya isa,sannan na samu wata kuma tana samin number din wayarta cikin typing dina,to itama na roqeta ta bari,idan bata ji ba zan kai qararta gurin Allah,don kuwa yana gaggawar amsa addu'ar wanda aka zalunta,ku barmin novel dina yadda na tsara,kuma kuyi naku ba wanda ya hanaku,Allah yasa mu dace🙏🏻 *Mrs muhammad ce*👑 📘📘📚📚✍🏻✍🏻✍🏻 [10/16, 2:13 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WA YASAN GOBE?....* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 👉🏼 *PART 3* 👈🏼 1⃣5⃣&1⃣6⃣ Da sauri ya riqe habarta ya dago kanta,"ki kalli qwayar idona ki gaya min baki sona,I promised zan bace daga rayuwarki kamar yadda kikamin alqawari kema!" Ta sani qwarai aliyyun kaifi daya ne,yana aikata duk abinda ya furta komai tsananinsa,tashin hankali da tsantsar rigima da take hangowa yanzun a qwayar idanun aliyyun ba kadan bane,ko bama haka din ba tana jin ko kanta za'a sanya gabas a dora mata wuqa ba zata iya kallon qwayar idanunsa tace bata sonshi ba,ita kanta ma tasan ta yima kanta qarya koda ta fadi hakan,wannan ma wasa ne Ko motsi kasawa tayi don tasan abinda yake buqata din ba qaramin girma ke da shi ba a gunta, "uhummm.....am waiting,tell me fadeelah.....tell me baki sona kamar yadda kika fada dazun"shirun dai ta kuma yi din bata da abun cewa,yasa yatsunsa ya sake dago fuskarta ta sosai still dai taqi yarda su hada idanun"fadeelah ni na sani kina sona,kina qaunata,amma me yasa ba zaki yafe min ba?me yasa ba zaki manta komai ba?,if u are nt willing to forgive someone,then you don't truly love them,fadeelah silence the mind and hear the heart,ina sonki fadeelah ina sonki har bansan adadi ba"cikin murya dake nuna alamun karaya ta dago kan nata ba tare da ta dubeshi ba ta dawo da tambayarta ta dazu "na gaya ma baka sona aliyu jikina kake so!" Cikin rudu ya sake kamo hannayen nata da ta sabule ya riqe gam "wa ya gaya miki hakane fadeelah?,who told you?" "Ni na gani da idona,baka soni ba aliyyu sai da kwanta da ni?" Bai son wanna kalmar da taje furtawa bai san sanda ya zauna dirshan ba qasan office din,"wallahi Allah fadeelah idan ba tare muka fara son juja ba to da kadan kika rigani,wani kurman so nake miki fadeelah ki yarda da ni ba tare da ni kaina na sani ba,zuciyata na sonki ba tare da nasan hakan ba,na sani......kuma na zaci haka dama zaki zaci cewa jikinki nake so,saboda ban tashi sanar dake ina sonki ba sai a wannan gabar,bani da kalmar da zan kare kaina da ita,amm abu daya ne zai tabbatar miki da gaskiya ta,abun kuwa shine....ki amince ki dawo gidana fadeelah wannan shi zaisa ki tantance wanne irin so nake miki,zaki gane za kuma ki fahimci ba wani abu daya nake kwadayi tare da ke ba....a'a....kedin gaba dayanki nake qauna nake so fadeelah,na miki alqawarin baza sake taba koda yatsanki ba har sai kin nutsu kin amince da soyayyar da nake miki "Fadeelah na sani ni da bakina nace miki bana sonki amma wallahi Allah shine shaida ba haqiqanin abinda ke zuciyata ba kenan,ban taba jin qinki a zuciyata ba dai dai da qwayar zarra,wallahi fadeelah da bana sonki bazan aurenki har na iya zama da ke ba,bana iya zama da abunda zuciyata ke qinsa,mata nawa ke sona?mata nawa aka kawo min a take na qisu?,amma fadeelah na amince na aureki na zauna qarqashin inuwa guda dake.....nake ci daga abincin da hannayenki suka sarrafa shi....nake buri da muradin sha daga abunda hannunki ya hada,nake kuma kwanciya bigire daya dake qarqashin rufin kwanon daki guda" "Fadeelah.....kalli qwayar idanuna na tabbata sun isa amsa a gareki,ban iya qarya ba fadeelah,amma karo na farko da na fara yinta a rayuwata,na bugi qirji nace bana sonki bayan nasan ba haka bane,nace bazan soki ba koda wata rana ne bayan *bansan gobe ba,ba wanda yasan gobe sai Allah*,gashi yau wata ranar tazo ta riskeni ta qaryatani......kuma nima na qaryata kaina da kaina"yayi shiru idanunsa na kanta yana maida numfashi Gaba daya ya gama da ita,ya lalata mata dukkanin tunaninta,ya tarwatsa duk wani mummunan tunani zato da tsammani da a da take da shi a kansa,maimakon haka ma sai wata sabuwar qauna da soyayya tasa dake ratsata har jinin jikinta,ahankali take fasa qashi tana malala har zuwa bargonta,jinta take kamar ba'a duniyarmu take ba,abinda ta jima ta jima tana bege da yaqin samu gashi yau a gabanta,yau ga aliyyu zaune dirshan a gabanta,yauga aliyyu zaune ya zamo kalar tausayin a qasan qafafunta,bayan babu abinda ya rasa a rayuwarsa soyayyarta kawai yake nema,aliyyun nan dake bata tsoro,aliyun nan dake da girman kai aji da kuma kwarjini yaushi yake roqon soyayyarta?,to itakam idan bata sallama ba tayi haqurin ai ta yiwa Allah butulci,me take nema dama idan ba wannan din ba?,tasan wasu daga halayensa sarai kamar yadda kowa ya shaideshi bai iya qarya ba....shi din kaifi daya ne da ko gaskiyarsa ba zata faranta maka ba hakan bai dameshi ba Cikin cool voice da wani irin kunya da nauyi kanta a qas tace "na yafe maka,komai ya wuce "lumshe idanunsa yayi wani sanyi na kwara cikin ransa,ji yake kamar an masa gafara da bushara da aljanna,me yafi so dadi?,me yafi qauna faranta rai?,amma duk da haka yana neman qarin bayani,ya bude idanunsa ya sake matsowa jikin gwiwoyinta,"fadeelah kalmomin da zan miki godiya da su na tabbata sunyi kadan,bani da su saidai na kwatanta yin hakan don bani da abunda zan iya saka miki da shi,na gode na gode Allah ya miki sakamako da aljanna,but I need more fadeelah I need more,please tell me kina sona kina qaunata kuma zaki koma gida na"kafin tace komai aka sake knocking,da sauri ta daga kai ta kalleshi "please ka tashi daga qasa ka koma kan kujera,za'a iya shigowa a ganka a haka fa" ya noqe kafada ko matsawa baiyi ba yana ci gaba da kallonta "no,I don't care ko waye ma zai ganni a haka,a gaban fadeelah ta nake kuma ta cancanci komai har ma fiye da hakan,idan tana sone ma na kwanta ta dinga taka gadon baya na tana tafiya am ready if I can make her happy"dariya ce ta subuce mata tasa tafin hannunta tana qunshe bakin,ya kalli qwayar idanunta da suka sake yin kyau da 'yar ragowar qwalla aciki wadda tasa shi ya koma kamar oily eyes ya dage girarsa "oh,kina tantama ne?,let me show you"tuni ya soma qoqarin ruf da ciki a qasan,batasan lokacin da ta kama hannunshu ba tana qoqarin hanashi ba"no haidar,I trusted you"yabi hannayen nasu da kallo yadda ta riqe masa hannu da tattausan hannunta,ganin yana kallon yadda ta riqe shin sai kunya ta kamata tayj saurin janye hannun hadi da yin qasa da kanta tana murmushi,shima murmushin yake sannan ya nufi bakin qofar ya bude,fauziyya ce har ya dawo tace cikin fara'a "ina fatan kun kammala ban sake katse ku ba karo na biyu duk da takaddu kawai na shigo diba zan wuce gida"yasa hannu ya dauki baby iman dake ta miqa masa hannu taba masa dariya tamkar dama can ta sanshi ya soma mata wasa,baice mata komai ba sai hanya da ya bata yace"bismillah" Yana ji tana tsokanar fadila haddi da yi mata sallama "yau dai ban sani ba ko anan office din zaku kwana ke da ogan" cikin murmushi ta mayar mata "a haba fauziyya,gida za muyi yanzu muma"ya sauke mata iman hadi da zurawa yarinyar five thousand cikin awarwarayenta dake hannunta,yaro ba wayo sai kallon kudin take gami da qoqarin zarosu tana ganinsu kamar abun wasa ne,yana ta murmushi son yara na dada kamashi,fauziyya ta masa godiya,shi ba ma'abocin son ayi masa godiya bane don yayi kyauta don haka baice komai ba ya dauke kansa ya maida kan fadeelah dake qoqarin miqewa don hada kan komatsanta da niyyar tafiya gida,wani jiri ya debeta duhu ya gilma idanunta tayi baya luuuu zata fadi,cikin zafin nama ya qaraso gareta ya mata kyakkyawan masauki cikin faffadan qirjinsa yace "subhanallah",fauziyya dake yunqurin jan qofar ta dakata gami da juyowa "sannu fadila jirin ne dai?" Da mamaki a fuskarsa ya kalli fauziyyan "dama jiri take yi?" "Wallahi tunda ta dawo aiki take fama da shi,kullum haka take yi,matuqar tayi dogon zama ko zirga zirga,nayi zaton ma ta gaya maka,don nayi nayi da ita taje taga likita sam taqi,don ko jiya sai da na dan riqeta na wasu mintina sannan ta zama normal" "Thank you" yace ya maida idanunsa kan fadilan wadda ta sake cusa kanta cikin qirjinsa tana shaqar daddadan qamshin da jikinsa keyi,dadi qamshin ke mata sosau kamar su dawwama ahaka haka take ji,maidata yayi ya zaunar saman kujerar ya hada mata dukkan takardun da take buqata din cikin hand bag dinta ya dauka sannan ya zo ya miqar da ita ya rungumeta ta kafadarsa yadda zasu iya tafiya a hakan *ku yimin afuwa makarata rashin chargy*👏🏻👏🏻 *Mrs muhammad ce*👑 📘📘📚📚✍🏻✍🏻✍🏻 [10/16, 2:14 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WA YASAN GOBE?....* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 👉🏼 *PART 3*👈🏼 1⃣7⃣&1⃣8⃣ Ganin ya nufi qofa alamun ficewa za suyi ya sanya fadila zaro ido "a haka zamu fita?" Ya dubeta "yes ko yayi miki kadan na daukeki ne?" Ta kuma zaro ido cikin marairaicewa tace "no,please ka cika ni ka ban jakar,ai na daina jin jirin zan iya tafiya da qafata" Girgiza kai shima yayi"no,bazan iya barinki ba,bazan bari kisha wahala ba indai ina tare da ke,ko ki bari mu tafi a haka ko na daukeki gana daya na kaiki har cikin motar" Ta san halin aliyun kadan ne daga aikinsa,zai iya aikatawa ba tare da yaji ko dar ba,tilas tayi shiru suka fita tana sunne kai Motarsa taga ya nufa da ita,ta dago da kanta tana ce masa "amma da ka bari tunda a motata na zo sai na koma aciki ko?kada momi ko uncle abba su gammu tare" Ya tabe baki sannan ya saki dan qaramin murmushi dake qayata fuskarsa "kada su gammu tare?,so what?,ai ni dama haka nake so,kinga daga nan sai su tarkata min mata ta mu koma inda muka fi wayo"murmushi ta saki ta maida kanta don dariya aliyun ya bata,ya bude mata gidan gaba kusa da shi sai da ta shiga ya dan kwantar mata da kujerar ya sumbaci goshinta duk tana kallonshi "ki zauna a haka don bani so a ganemin ke a hanya"murmushi kawai tayi cikin jin kunya,cikin zuciyarta tana cewa"idan banda abun sa wa zaya ganni mota duk baqin glass"ya zagaya nasa bangaren ya bude yana shirin shiga Wasu 'yammata su uku suka fito daga reception,daya daga cikinsu ta finciko hannun dayar tana nuna mata aliyyu,damar da ta jima tana neman kena taga aliyun don haka ta jawo hannunta ta rakota har bakin qofar motar,yana shirin sanya qafarsa yaji ance "ranka ya dade ya kai kyakkyawa" kusan ha saba jin irin wadannan babatun abakin 'yammata saboda haka bai juyo ba sai da ya shiga motar ya rufe qofar sannan yayi qasa da glass din,fuskarsa a yamutse kamar ya ga kashi yake kallonta,yayin da ita kuma ta harde hannaye ta zuba masa ido tamkar mayya tana zabga murmushin neman shiga "kina da matsala da ni ne?",cikin murmushin tace "yes,babba ma kuwa"aliyu ya fasa kunna motar da yake qoqarin yi da dayan hannun nasa ya dogara hannun jikin murfin motar yana shafa sumarshi hadi da tsareta da ido,ya sani sarai qarya take don yaci karo da mata irinta sunfi dari Sai yayi mata kwarjini domin shi din ba kalar wasa bane,ba tare da ya sake tambayar tata ba ita da kata cikin diriricewa tace "zuciyata ka sace min ne,kuma na jima ina jiran rana irim wannan da zan sanar da kai"fadila dake kashingide cikin motar kalaman suka shiga kunnuwanta,amma sai taga meye nata tunda ba'asa da ita ba,bari taga ya drama din zata kaya,sake kallonta aliyu yqyi cikin raini "ke! Ki shiga hankalinki,ni ba sa'an wasanki bane,bana son shashancin banza" yaja tsaki yana shirin tada motar ya kunnata ya fara dan janta yana duna inda zaiyi ribas,"ko baka sona ni ina sonka wallahi kuma suna na mansurah"ya leqa kansa ta window "sai ki bada himma ko,stupid" "Iove you idan baka soni ba bazaka hanani in soka ba aliyyu salim kuma sai na aureka na shigo gidanka"zuciyar 'yan maza ta motsa ya tsani mata masu naci irinta haka,niyyarsa ya fice yayi maganinta ta kama hannunsa dariya na shirin subuce mata "haba sonka fa tace tana yi ba qinka ba,masoyi ai yafi maqiyi meye laifinta?" Tana gama fada dariyar ta kubce mata Qyal qyala dariyarta take sosai,cak ya tsaya yana kallonta,kyawunta ne ya fito sosai,tuni ya mance da wasu ya shagala da kallonta,ita kam bata ma lura ba dariyarta take har da toshe baki,a hankali ya kai yatsansa lobawar nan ta tsakiyar habarta da ta dauki hankalinsa sannan ta farga ita yake kallo,ta yi qoqarin gintse dariyar ta janye fuskarta a kunyace,ajiyar zuciya ya saki kana ya tada motar,tuni ya manta da wata halitta wai ita mansura,fadila ce ma idanunta suka kai gun tayi sakato a tsaye tq zuba musu ido ita mansuran sai lokacin ta kula bashi kadai bane cikin motar,tamkar ta fashe da kuka takaici ya cikata,'yar rakiyar tata kam dariya take ta qyalqyala mata"ai na gaya miki mansura,banda abunki ki duba fa kanki ki dube shi ki dubi kuma wadda suke cikin motar tare,wanda yake da kamar wannan ai baki isheshi kallo ba,ke babu lallaima ko a 'yar aiki ya daukeki indai zaki hada kanki da wada suke tare din nan" ashar ta lailayo ta dirka wa qawar,ita kuwa tayi gaba ta fice abunta Tuqi yake amma gaba daya kaf hankalinsa na kanta,duk second biyar zuwa goma sai ya juyo ya kalleta,sai daga baya ta lura da hakan "please ka maida kanka gun driving,kaga muna kan titi ne"ta fada idonta na kallon kan titi,gani tayi yayi gefan titi a hankali ya gangara gefan kwalta yayi parking din motar sannan ya kashe ta,ta juyo ta dan dubeshi don bin ba'asin abunda suka tsaya yi din,amma sai ta kasa furta komai saboda wani mayen kallo da yaje binta da shi wanda ya haddasa mata jin wata matsananciyar kunya mai kashe jiki,ya sake raunata mata zuciya da gangar jikinta da wani kurman saqon soyayya mai zafi,bata san sanda ta maidq bayanta jikin kujerar ba ta lafe hadi da langabar da kanta gefen kafadarta hagunta A hankali yasa hannunsa ya juyo da fuskarta zuwa gareshi, "no,kada kimin rowar fuskarki baby na,barni in more abuna" bata ce komai ba sai dan qaramin murmushi da ta saki wanda ya sake shagaltar da aliyyu,sannu a ahankali ta dora qwayar idanunta cikin nasa tana morewa kallon aliyyun,rana ta farko da hakan ta soma kasancewa tsakaninsu,dukkaninsu kallon so qauna aminci da yarda suke wa junansu A hankali ya soma motsa labbansa da yakejin suna mishi nauyi still idanun nasa na cikin nata yace "please,tell me kina sina baby nah"ta dan lumshe idanun nata tana jin wani shauqi cikin zuciya da gangar jikinta sannan ta sake budesu ta watsa su cikin idon aliyun "bau wasu kalmomi da zasu iya bayyana abinda nake ji cikin zuciyata, I love you more than I did yesterday,and I will love you more tomorrow than I do today,kai na fara so kuma kai zanci gaba da so har qarshen rayuwata,inaji a jikina an halicceni ne kawai saboda kai" jinsa yake tamkar yana yawo a sararin samaniya,yana jin tamakar su dawwama a gun tana ci gaba da bayyana masa irin qaunar da take masa da sweet voice dinta Karo na farko da fadeelah taga dariya mai cakude da murmushi cike da nishadi kwance bisa fuskar aliyyun,har yanzu idanun nasu na manne dana juna "is what I see in your eyes true or the mirror?"gyada kai tayi tana mai bashi tabbaci "its true,da gaskene miji na" "really?" Ya sake tambayarta "yes its real"ta amsa masa tana sake bashi tabbaci,hannayenta ya kamo ya matse cikin nasa tafin hannun,"please ina neman alfarma guda daya" gyada kai tayi alamun tana saurarensa,ya sake matsowa kusa da itan har suna shaqar numfashin juna yana murza tattausan tafin hannunta "ina roqonki fadeelah if u reprimand me hug me and give me bliss and let it to be a loving touch,please na roqeki kada ki sake yin nisa da ni,kada ki kuma barina,kada ki kuma raba ruhina da naki,kimin alqawari fadeelah na,are you promised to do it?"ta gyada kai tana murmushi "yes I promise you" "good and I promise you too....I will never do it again,all I want is to see you smile forever not just for a while...." ya rungumeta tsam yana fadin"am sorry I will never hurt you again" "ya wuce wallahi ya wuce,Allah ma muna masa laifi ya yafe mana" Tsawon mintina yana rungume da ita yaqi sakinta,ita din ma dadin hakan take ji sosai,don ba zata yaudari kanta ba sosai tayi missing soft skin nashi,tayi missing scent nashi masu dadi,kai komai nashi ma tayi missing dinsa,sai gashi lokaci guda Allah ya maido mata da shi da kuma abunda bata taba tsammanin ba ma,duk da ta sani addu'a bata faduwa qasa banza dama,kuma lallai wani jinkirin alkhairi ne,sai da taga lokaci na qoqarin qwace musu gashi bai da niyyar sakinta bare ya tada motar su tafi "lokaci na tafiya fa,kada momy taga ban dawo on time ba"ya dagota yana kallonta"sai kice mata kin sha'afa ne kina tare da lovely husband dinki"ta rufe fuskarta da tafin hannunta "momin zan cema haka?"ya dage girarsa "yes kinga sai tace tattara kayanki kibi mijinki,kinga fine komai yayi kyau ko?",sai ta maida jikinta kan kujerarta tana murmushi qasa qasa,qamshin turarensa da ya manne a mayafinta yana sake yi mata dadi tamkar yau ta sanshi Kusan sai da suka tsaya sau kusan uku kafin sukai gida,kallonta yake ne yaqi maida kanshi yayi tuqin,idan tayi masa qorafin hakan sai ya yace "gaskiya gaskiya bazai iya tuqi baya kallonta ba,saidai a haqura da tuqin idan ya gama kallon nata sa tafi,lokacin da suka isa gida tuni anata tada iqama,tana qoqarin ficewa daga motar ya kamo hannayenta,ta dan fiddo da idanunta tana kallonsa,ta shagwabe fuska kamar zata yi masa kuka " please ka sakemin hannu muna cikim gida ne fa yanzun,it can be possible wani ya fito ya gan mu a....." kanta qarasa tuni ya janyota jikinsa daidai lokacin uncle abba ya fito daga cikin gidan hannunsa dauke da carbi da alamu masallaci zashi Sarai ya gansu amma sai ya dauke kai tamkar bai kula da su agun ba,farinciki yaji sosai cikin zuciyarsa "alhamdulillah"kawai yaje fadi cikin ransa,bisa dukkan alamu sun sasanta kansu kenan,yanzu yake ji a zuciyarsa zai iya maida fadilan gidan aliyyu,don duka alamu sun nuna na qauna da soyayyar da suke ma juna,fadila ce ta soma ganin abban lokacin har ya basu baya,ta zare jikinta da sauri tana gyara yafen mayafinta zuciyarta na bugawa tace "innalillahi" aliyu ya kalleta"lafiya baby?" Uncle abba ta nuna masa da yatsa tuni idanunta suka cicciko da qwalla "ya ganmu wallahi,sai da nace ka bari ka bari fa" Dariya ya saki cikin nishadi "to mene ne?,kinga addu'ata ta karbu kenan,kuma ma baby naga da mijinki ya ganki fa mene na rudewa har irin haka?" Ya jawo hannunta yana goge mata qwallar da ta soma gangaro mata "calm down my unique,don't cry again,kin gama kuka a duniya ai matuqar ina tare da ke,I will never let your tears to fall down again.....muje ma raka ki ciki"sai taga tunda abba ma ya riga ya gansu a dazun don rakata ma cikin gida ba komai bane,abun kunyar dai an riga an gama tafka shi,tayi tayi da shi ya bata jakarta ta riqe yaqi yace sai ya kaita har ciki,sai da yace idan ma ta fiya matsawa zai goyata ne ya kaita har cikin gidan,tasan kadan ne daga aikinsa,tilas ta bar masa tayi gaba yana take mata baya...... *Mrs muhammad ce*👑 📚📚📘📘✍🏻✍🏻 [10/16, 2:15 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WA YASAN GOBE?....* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 👉🏼 *PART 3* 👈🏼 1⃣9⃣&2⃣0⃣ Ai kuwa sukayi kyakkyawan gani cikin parlour,momi ce da iftihal dukkansu suna zaune kan kujera sanye da hijabi da alama sallah suka idar,karatun qur'ani iftihal keyi da ka momi na gyara mata kura kurenta,kallo momin ta bisu da shi daga bisani sai kuma ta dauke kanta tamkar bata gansu ba,ya miqawa fadila jakarta da take ta Allah Allah ta bar falon kunya gaba daya ta rufeta,gogan harda hadawa da hannunta lokacin da zai miqa matan,ta zame hannun nata da sauri ta haye sama inda dakinsu yake,ya wani bita da kallo ko kunya baiji ba,sai da ta qare hawa sannan ya janye idonsa ya juya da niyyar gaida momi Ashe idanunta na kansa take suka hada ido,sai yaji wata kunya ta kamashi,yasa tsinin key din motarsa yana sosa tsakiyar kansa irin najin kunya,yakoma gefe ya tsugunna yana gaidata yayin da tuni iftihal tayo qaura gurinsa,maimakon momin ta amsa sai tace "rasa kunya beran tanka,tashi ka bani guri,kada na kuma ganin kana takura mata daga yau,na gaya maka ka qyaleta tayi hukunci da qashin kanta,idan ba haka ba tamu ce ni da kai"ya miqe yana murmushi lokacin da yake maida iftihal kan kujerar kusa da momin,abinka da wanda bai iya qarya ba sai yace "momi ba takura mata nake ba,ai tama gama yanke hukuncin,mun gama magana da ita momi"baki sake ta bishi da kallo lokacin da ga fara tattaki zai bar falon "iye?,me kace?"  "A'ah momi bari inje nayi sallah"shima ya fada yana waiwayo wa gami da sakin dariya wa momin har ta fice "Ja'iri ka maida ni kakar ka ko?" "Momi ai dama kakarsa ce ke"inji iftihal dake faman wasa da bezar hijabinta,duk sai suka bata dariya 'yar da uban,cikin zuciyarta tqna addu'ar Allah ya daidaita ya sake tsakaninsu Kowa ya hallara a dining har aliyyu da yaqi tafiya amma qememe fadila taqi saukowa,ita kam ba zata iya ba,bala'in kunyarsu abban take ji don aliyyu ya gama kunya tata,kuma ta sani ko da ta sauko din tunda aliyun na gun ta tabbata sai ya sake kunyatata kafin a tashi,haka abban yace a qyaleta don yasan me take yiwa kunyar,sam sai yaji abincin bai masa dadi don mafi rinjayen zaman cin abincin nasa saboda ita ne,suna tsaka da cin abincin ya soma tari kamar ya qware,sai yaqi daukan ruwan dake kan table din yayi hanyar kitchen su abba na masu sannu,ganin idon kowa bai kanshi sai kawai ya haye matattakalar sadaf sadaf yayi sama,momin ce ta soma ganoshi ta dan tabo uncle abba yadda su sumayya ba zasu gani ba ta nuna masa aliyyun,dariya uncle abban ya saki shida momin duka, Tana zaune dirshan tsakiyar gadon,gabanta system ce a bude tana faman aiki cikinta,doguwar rigar yellow din material mai santsi ce a jikinta,mai tankakken hannu ne dinkin ,babu abinda ta shafa illa man lebe da ya qarawa lips dinta taushi,sai jikinta dake tashin qamshin turaren asaal,kyakkaywan gashinta baqi sidik mai tsawo da qyalli yasha gayara ta tajeshi ta daure shi da qaramin ribbon yellow ya sauka gadon bayanta yana reto,hundred percent hankalinta na kan system din,alewar mints ce a bakinta tana tsotsa a hankali,sai da ya gama qare mata kallo iya son ranshi "unique lady"ya fada cikin ransa,komai nata mai aji ne,yanayin zaman nata bisa gadon sai ya zamewa aliyyu abun sha'awa,lallabawa yayi ya haye gadon ta bayanta,sai jinta kawai tayi rungume jikin mutum,a dan firgice ta waiwayo ya manna mata kiss a goshinta tare da sakin murmushi"me yasa kika qi saukowa kici abinci bayan kin sani bazan iya tafiya ba tare da na kalli wannan kyakkyawar fuskar taki ba"ya qarashe maganar yana shafa gashinta da ya qayatar da shi Zumburo baki tayi kamar na shagwababbun yara tana dan kici kicin qwace kanta "haba mana dear dakinsu sumayya ne fa,suna iya shigowa su ganmu"daga hannunwansa yayi yana murmushi🤗"is ok,indai so kike na qyaleki sai idan kin yarda zaki bani hot kisses a matsayin sallamarmu ta yau"sak tayi ta kuma yo kicin kicin da fuska,murmushinsa ya dadu yace "uhm,am waiting dear"nan ma shiru,ya dora kansa saman kafadarta yana leqen fuskarta,saura kadan ya fashe da dariya yadda yaga tana zare idanu,ta gintse dariyar yaba cewa "don't mind dear,if you are not ready kinga sai muyi zaman mu a haka ko?"da sauri ta noqe kafada "no am ready,but.....Please ja rufe idanunka" "ok....ok" ya fadi yana cikata gamida rufe idanun Shiru yaji hadi da qarar qofa,da sauri ya bude Idanun nasa,ta qarasa sa key din qofar toilet tana qyakqyala masa dariya,sai ya harde hannayensa ya zubawa qofar ido fuskar sa qunshe da murmushi"no baby,kin karya agreement,kisses sun qara nukuwa,sun zama double yanzu,ko ki fito ki bani ko in kunce gidan key din yanzun nan in shigo toilet din"dariyarnan tata mai saurin shagaltar da shi taci gaba da yi Sai da taji sukur sukur dinshi jikin qofar sannan ya sata nude qofar da sauri,wayo dama ya mata ba wani gidan muqulli da zai kwance,ya cafkota ta fado jikinsa suna dariya,dariyar tasu ta tsaya lokacin da wayarsa ta soma ruri,ya cirota daga aljihunsa yana dubawa,salima ke kira don itace da girki dama yau zata fita,ya kara a kunnensa,da qorafi ta fara masa kafin sallama, "ok gani nan"kawai yace mata ya maida wayar aljihun,fadila tayi lamo jikinsa kishi na sukarta,ya dago fuskarta yana kallo sai yaga alamun ta dan canza,yasan dalilin hakan saboda haka dadi ne ya kamashi don yasan abunda ake so ake kishi, "oya babe,give me"ya fadi yana sake dago fuskarta gareshi,wani hot kisses ta soma bashi wanda ita kanta bata san ta iyasu ba sai yau,sosai ta rudashi har suka gagara tsaiwa suka zube saman carpet,shigowar rabi'ah da komawarta da baya da sauri shi yasa fadila saurin zare jikinta,a kasalance ya maida idanunsa kanta,kanta a qasa tana tattare gashinta da ya yamutse tana maida shi cikin ribbon,ya sake maida idonsa bakin qofa inda rabi'ah ke tsaye a bayan labulan ta yadda yanzun bata iya hangosu "yaya,momi ce ke kiranka" "bace min a gun stupid kawai,baki iya sallama ba zaki shigowa mutane daki kai tsaye?" Sum sum ta juya tana tabe baki cikin ranta tana cewa "sallamar miliyan nawa kakeso nayi muku ,ka shiga wannan yanayin koda ganga nake sallama taya za'ayi kaji,su yaya aliyyu ashe haka aka iya soyayya?" Sai ta qyalqyale da dariya ita kadai,yasa yatsunsa ya dago da fuskarta yana son kallon qwayar idonta amma taqi yarda "I need more please..."ya fadi muryarshi qasa qasa tamkar mai rada,tuni ta shagwabe fuska tana cewa "please.....Please,na yima fa,kuma momi ke jiranka fa ma"ya yunqura ya miqe yana gyara botiran rigarshi da suka balle yana cewa "ok"sai da ya gama ya miqa mata hannunsa har lokacin tana zaune kanta a qasa "oya get up"a hankali ta dora hannunta saman nashi ya dagata,sai jirin nata ya kwasheta tuni ya riqeta don kada ta sha qasa "fadeela I think you are not well"  "am well" "A'ah,ki shirya gobe zan daukeki ta office in kaiki kiga likita"  "Amma....ai zan...."ya tsansa ya dora kan lips dinsa "shshshsh...kada kice komai"shirun tayi ya leqa fuskarta "zaki rakani gun momi muyi sallama?"girgiza kanta tayi "um um"yayi murmushi "shikenan to kwanta abinki"ya zaunar da ita gefan gadon,system din ya fara kashe mata ya maida mata ita saman madubi,ya dawo inda take yana kallonta ya kama hannunta ya sumbaci sama yana cewa "good night my dear baby na,sweet dreams,I love you"a hankali ya bude bakinta tace "I love you too my dear *haidar*"farinciki ya cikashi kamar ya taka rawa,tuni saboda kunya ta cusa kanta qasan pillow tana murmushi har ya fice Momin kawai ya tadda a parlour din yanzun ma ita da iftihal dake shimfide kan cinyarta tana baccinta abunta,a yatsine momin ta kalleshi "sannunka kaji?" Murmushi kawai yayi idanunsa na kan 'yar diyarshi,ya shafa kan iftihal din "ayi haquri momi zan tafi sai da safe" "kada naga qafarka da safe a gidan nan" da sauri ya dawo da baya ya taugunna gaban momin "yauwa momi na,Allah indai kika bani fadeelah ta ba zaki kuma gani na da sassafe a gidan nan ba,saima kin aika a nemo miki ni" dariya taso qwace mata amma sai ta kaba habarta yana cewa "o'o'o,sannu mara kunya,to anqi din har sai ta yarda da kanta" ya kama qafar momin yace "wallahi momi fadeelah ta haqura" ta dake dariyar dake cinta "kaga,mu bata gaya mana ba yallabai sai ka jira har sai ta gaya mana da kanta"ya marairaice "momi kunya fa kinsan take ji,ba zata iya gaya muku ba"momin ta tabe baki "ok,sai kai wato rasa kunga shine kazo kayi rashe rashe a gabana kake gaya min ko,don Allah tashi ka tafi gidanka ni na gaji da ganinka anan" Kai yake gyadawa kamar qadangare "shikenan momi,shikenan sai da safe"ya miqe ya fice cikin zuciyarsa yana fadin "zan shuka tsiya kawai,komai ta fanjama fanjan,su momi basu yanda nake ji bane"uncle abba dake can tsaye yana kallonsu yqna shan dariyarsa ba tare da sun sani ba ya qaraso "haba maimunatu,ayi haquri haka nan a bashi matarsa,tunda sun sasanta kansu,ni kam na fara tausaya masa,kinsan ciwon da namiji ma na da namiji ne"ya qarashe fada cikin zolaya,dariya uncle abban ya bata sosai"shikenan tunda abun wariyar launin fata ce nima ai ciwon 'ya mace na 'ya mace ne,sai na gyara diyata nima,idan yana so jibi ko gata sai a bashi ba don halinsa ba" Ya sunkuya yana qoqarin dauke mata iftihal daga kan cinyarta "mudai tunda za'a bamun ai shikenan godiya muke,bari in dauke miki amaryar taki,kije ki huta kema"ta saki murmushi tana cewa "godiya nake abba"ta miqe tabi bayansa tana barwa sumayya da rabi'ah dake kitchen auna wanke kwanukan da aka bata don basa barin wanke wanke ya kwana sallahun idan sun gama su kashe duk qwaya qwayai da kayan electronic na parlour da kitchen din Tunda ya zaunar da ita a gun ta bingire ta kwanta saboda kasala,juyi kawai take tana tariyar abinda ya farun a wunin gau gana daya tsakaninsu,babuabunda take saki sai murmushi,shi din ma koda ya fito daga wanka kasa hasala komai yayi,sai da ya zauna gefan gado ya dauki wayarsa ya kirata,tana tsaka da juyin nata ne kiran ya shigo mata,ta gyara kwanciyarta hadi da rungume pillow sannan ta amsa,sallama ta masa da muryarta mai sanyi wadda ke saka susuta shi "fadeelah bazan iya bacci ba sai naji muryarki" "But...."sai kuma tayi shiru "But what?,pls gaya min abu daya wanda zai sani samun nutsuwa idan nazo baccina" numfashi ta ja sosai sannan tace"i love you for all that you are,all that you have been,and all you're to be my haidar"kalaman sun tsaru sosai cikin kunne da zuciyarsa,ta kashe masa jiki da zaqin kalamansa,idanunsa na a lumshe yace "are you sure babe?" "Yes am sure,duk abinda na fada I mean it"dogon sumba ta bashi a wayar sanna ta kashe tana murmushi qasa qasa,shi kuwa mutuwar zaune yayi gaba daya tsigar jikinsa ta zuba.......... *Mrs muhammad ce*👑 📚📚📘📘✍🏻✍🏻✍🏻 [10/16, 2:16 PM] 💍🍬🛍Salma🛍🍬💍: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WA YASAN GOBE?....* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 *WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 👉🏼 *PART 3* 👈🏼 2⃣1⃣&2⃣1⃣ Shi kuwa mutuwar zaune yayi gaba daya tsigar jikinsa ta zuba ⚜⚜⚜⚜⚜ Zaune take a nutse cikin office din,sanye take da shadda dinkin riga da zani rapper marun,sosai shigar ta yi mata kyau matuqa ta kuma dace da fatarta,hakanan take kullum ba dai tayi kwalliya a kushe ba,ta iya dressing sosai,hannunta dan madaidaicin cup ne cike da coffee tana dan kurba kadan kadan don babu abinda ta iya ci tunda gari ya waye,gaba daya hankalinta na gun aliyu tunaninsa take,amma idan ka kalleta a zahiri qata news paper dake gefan hannunta ta zubawa ido tamkar mai nazarin wani abu a cikinta Yafi minti goma a atsaye bakin qofa,sam baya gajiya da kallonta,baiqi su dawwama a haka ba,tsarin shigar tata yayi masifar tafiya da shi tayi wani das tamkar fure,sai kuma aka taki sa'a shi din ma marun din shaddar ce a jikinsa Har ya iso bata ankara ba,a hankali yasa hannu ya zare cup din coffeen dake tsakiyar tafukan hannayenta "irin wannan zurfi a tunani bai dace da kyakkyawa ba" ya fadi yana maida cup din gefe,yaja kujerar dake opposite dinta ya zauna yana cewa "nasan dai ji kike tunani ko....to gani na iso ai sai abar hasashe a koma zahiri"murmushi ta saki a kunyace tayi qasa da kanta,ya sake binta da mayun idanun nan nasa,gani yake tamkar kullum wayewar garin Allah kyau ake dada mata,ya jawo tattusan hannunta dake zube saman table din yana matsawa,ji tayi kamar wani sinadari yake zubamata cikin jikinta,ta soma qoqarin zame hannunta tun kafin yayi mata illa cikin kunya "no baby,your hand fits in mine like its made just for me,kada ki cire" Ta dan zame dag kan kujerar ta gaidashi,noqe kafada yayi "naqi,ni ban irin wannn gaisuwar nake so ba,let me show you irin wadda nake so"kafin tace komai ya zagayoda ita zuwa inda yake zaune yayi mata mazauni kan cinyarsa,qam ya matseta,sai da ya yamutsata son ransa sannan yace "irin wannn gaisuwar nake so ko a ina muke right?"gyada ka tayi cikin jin nauyinsa,ta bishi ne da haka amma itakam rashin kunyar aliyyun tafi qarfinta "a'ah dear,ki daina min rowar sweet voice dinki,ki dinga bude baki kina magana sannan ki dinga bude idanunki sosai kina kallona,zuciyarmu ta riga ta zama daya....dubi"ya fadi yana juna mata dressing din da suka yi "baki san me zansa ba nima bansan me zaki sa ba amma saboda zuciyarmu na manne da juna mukayi shiga iri guda" Murmushi ta saki tana kwantar da kanta a kafadarsa,"ok,I hope kin shirya,don daga nan sai asibiti,gwara muje kiga doctor sa'adah"ya fadi yana sunkutarta kamar wata bebin roba,wutsil wutsil ta soma yi da qafafunta "please my haidar,zan iya tafiya kada ka fita da ni a haka"dariya taga ya saka,ta dan saci kallonsa don bata taba ganin dariyar tasa haka ba,ya maimaita abinda tace cikin kwaikwayar muryarta sannan ya direta "matsoraciya,dama tsokanarki nake"duk da haka bai qyaleta ba sai da ya kamo hannuwanta,a haka suka isa bakin motar,ya bude mata ta shiga sannan shima ya shiga Ko a office sai da doctor sa'adah tayi masa wayo koreshi waje da qyar don ya hana fadila sakat ,kunyar doctor din fadilan keji shikam ko a jikinshi,da zarar fadilan ta bude baki zatayi magana sai yayi sauri ya rigata cewa "doctor rabu da ita,awo na kawo miki ita,na jefa qwallo a raga" mamaki da kunya suka kama fadila haka aliyyun yake?,tamkar ba wannan aliyyun nata ba,ita kanta doctor sa'adah din tayi mamakin yadda ya sake yana ta raha har irin haka kamar ba aliyu salim maitama ba,mintina talatin doctor sa'adah ta gama duk wani bincike da gwaje gwajenta,madaukakiyar fara'a da farinciki da ta gani kan fuskar doctor din shi ya bata mamaki "congratulations fadila,naji dadi da ya zamo nice ta farko da zan taya ki murna,Allah ya albarkaceki da samun juna biyu"ta fadi tana sanya tafin hannunta cikin na fadilan Sak fadilan tayi tanajin kunnuwanta kamar basu ji mata dai dai ba,ciki gareta da gaske?,cikin aliyyu a jikinta?,aliyyu masoyinta?, *alhamdulilahil lazi bini'imatihi tatimus salihaat*,wannan baiwa da ni'ima ta Allah da me tayi kama?,Allah kenan mai kyauta da qari,buwayi gagara misali,mai azurta bawa a duk sanda ya so,mai amsa addu'ar bayinsa,yau ga aliyyun Allah ya bata kuma ya bata dan aliyyun cikin cikinta,ya zabeta cikin matansa yace ita zata haifa,batasan lokacin da hawayen farinciki suka balle mata ba,a hankali bakinta ya soma salati ga fiyayyen halitta,sannan ta dora da godiya ga ubangiji, "na godewa Allah gwanin iyawa,doctor pls bana son ki sanar da aliyu batun cikin nan yanzu,nasan bazai iya shiru ba sai kowa ma ya ji,kuma....." Dai dai nan aliyyu ya turo qofa ya shigo,da sauri ya qaraso a rude ganin hawaye kan fuskar fadilan,dagota yayi ya rungume yana goge mat fuskan"me ya faru ?,doctor me kika yiwa mata ta?"ya fadi cikin hade rai,dariya sa'adah tayi "farinciki ne yayiwa matarka yawa,don ance lafiyarta qalau shine don shagwaba take kuka"ta miqa masa takardar magunguna "wadan nan zata dinga sha,but gaba buqatar hutu da kulawa sosai,idan an gama lallashin ku rufe min qofar office din sir,zani inyi round na marasa lafiya,ta sanya lab coat ta fice tana musu dariya" Ko cikin motar kanta na langabe ne jikin sit,gaba daya jikinta yayi sanyi,sai ta ruda aliyyun gaba daya ya kasa driving din dole yayi parking din motar yana tambayarta,murmushi ta saki"am fine my haidar" duk da haka sai da ya sanyata cikin jikinsa sannan ya samu ya iya ci gaba da tuqin,ga zatonta zai maidata ne gurin aiki amma sai taga yayi nassarawa da ita,cikin rashin fahimta take dubansa "nayi zaton zaka maida ni ne office ko tunda ban tashi ba"ya girgiza kai "no fadeelah,yau gidammu zamu koma" da sauri ta dubeshi "gida haidar?,bada izinin su uncle abba ba?" "Shshshshsh!" Yace "nafi kowa iko da ke fadeelah,na gaji da rashinki,na qosa kiyi haquri kawai idan naje gidan ni zan sanar musu,zan fahimtar da su ba laifinki bane,bare ma ba zasu ce komai ba I know" Ta zumburo zata sake magana "tuni ya sanya bakinsa cikin nata ya hanata cewa komai,saura kadan sitiyarin ya kubce masa Allah ya taqaita ya kamo shi Da kanshi ya bude mata part din nata don babu key din a a lokacin a hannunta,sai zumbure zumbure take ita a dole fushi takeyi da shi,shi kam dariyarsa ma yake lokaci lokaci,bai damu ba tunda burinsa ya cika,fridge ya nufa ya ciro ruwa duk da babu sanyi kasancewar wutar bangaren a kashe take,ya jawo gabanta ya durqusa,ya jawo ledar magungunan ya ballo mata,ya bude gorar ruwan sannan ya kalleta "haa" yace da ita,shiru ta masa sai da ya sake cewa "bude bakinki"nan ma tayi shiru,sai ya dire ruwa da maganin kan center ya miqe yana shirin core rigarsa yana cewa "tunda kin zama kurma inada muqullin bude bakinki" a razane ta dubeshi,bata san lokacin da tace "me zaka yimin?"yadda ta razanar da kuma yanayin yadda tayi maganar shi ya bashi dariya,ya tuntsure da dariyarsa yana maida rigarsa da ya soma cirewa har fara qal din vest dinsa ta soma bayyana,ya koma gabanta ya tsugunna yana cewa "ashe dai matsoraciya ce,baki shirya fadan ba amma kika takaloshi,oya bude bakin"bata ko sake musawa ba ta bude ya sanya mata magun gunan sannan yasa maya ruwan a baki har sai da ta hadiye Ya miqe ya cire mata mayafin da dankwalinta,ya zare mat sarqa da dan kunneta duk tana kallonsa,ya debe qafafunta ya maida saman kujera ya dora mata pillow sanann ya harde hannayensa a qirjinsa yana duba agogon dake manne a bango "oya,maza kwanta kiyi bacci ko na one hour ne don maganin yafi saurin bin jikinki,after one hour sai ki tashi kiyi sallah ok?" Cikin shagwaba wadd ta ruda aliyun tace"amma dai kasan ban kyauta ba ace daga zuwa gun aiki ace na dawo gida na ko?"sauje hannun nasa yayi ya dawo gaban kujer ya tsugunna har yana jingina gwiwoyinsa jikin kujerar,ya koma serious sosai,yasanya tafin hannunta cikin nasa,sosai ya sa qwayar idonsa atata "fadeelah" kallon cikin idonsa tayi,yadda taga ya zama serious hakan yasa ta bawa maganar tasa muhimmanci "duk duniya babu mai haqqi a kanki daya kaini,bana so ki dinga sawa ranki damuwa kan binda yake mai sauqi ne,su momi sun ajjiyeki ne don ku sasanta kanmu da kanmu ba tare da kowa ya shiga ciki ba,sannan ni na sake gane kuskure na,to yadda suke so din duk ya faru,me kuma ya rage?uumm?,sai mu dawo gidan mu fadeelah mu shimfida sabuwar rayuwar auratayya wadda zata kuma farantawa iyayemmu rai,ina kuma fatan zan samu goyon baya daga gareki?" Sosai take gyada kai "insha Allah mijina,na yi maka wannan alqawarin" ta dam zamo daga saman kujerar ta durqusa itama a gabansa "ka yimin afuwa ranka ya baci,ya saki qayataccen murmushi "ba komai baby na,bakya taba yin laifi a guna"ya sumbaceta sanna ya maidata ya kwantar saman kujerar,"kiyi bacci sosai,banda cewa zaki tashi kiyi aiki,gidanki babu dattin komai,don kullum sai na share miki shi"tana daga kwancen ta qwalalo ido "shara?kuma da kanka?"murmushi ya kuma saki"kina mamaki ne?,kinfi gaban haka,mene ke baki bani ba a rayuwarki fadeelah?"itama murmushin tayi "haqqina ne ai In maka har fiye da hakan" "jiniina kai yayi cikin zuciyarsa yana godewa Allah,babu shakka yayi gamo da katar da mace ta gari,wanda samuntabke matuqar wuya a wagga zamani "ina sonki my baby fadeelah har bansan adadi ba,ina alfahari dake,ina alfahari da kasancewarki cikin rayuwata"ta rufe fuskarta da tafin hannunta "ina sonka haidar dear,nima kuma ina alfahari da kasancewar ka miji a gareni har abada"wani dadi yaji ya kama shi,ya sake sumbatar bayan hannun nata yave "na gidewa Allah fadeelah,sai na dawo,zansa nasiru ya kawo miki motarki ,sannan zan daukar miki excuse gurin aiki su baki hutu na sati"bata ce komai ba don bata son ta kasance mai yawan musu da shi,bare itama zata so hakan,don tana buqatqr lokaci da zatayi wasu 'yan gyare gyare,sabida haka kai kawai ta gyada masa tana satar kallonsa ta tsakanin yatsunta har ya fice,wani annushuwa da farinciki da kwanciyar hankali mara misali taji yana ratsata Ta janyo wayarta ta nemo number din farida,bugu daya ta dauka tamkar dama tana jiranta ne,cikin ihu take cewa "yeyyyyyy sister yaushe kuka dawo haka babu labari?"cikin murmushi fadeelah ke cewa "wayyo Allah zaki kashemin dodon kunne mana,cikin satin nan ne,kiraki nayi dama nace miki ki turo min mai gyaran jikin nan don Allah"wani ihu faridan ta sake saki cikin dariya "kai mutuniyata,wallahi da labari,tafiya tayi kyau mune winners ko?" "Kai....faridaaaa....sai yaushe zaki girma ne don Allah?" Tayi qasa da murya "kai sister,rowar story zaki mun kenan don Allah?"dariya ta bawa fadilan don tasan farida akwai son jin tsurku "hab abokin kuka ai ba'a boye masa mutuwa,zaki sha labari har sai kin gaji kin toshe kunnuwanki" "a'ah nasan halinki fa sister,zaki dai bani wanda kika ga dama,yanzu zan mata waya na gaya mata"tayi dariya "yauwa ko da yamma ne sai tazo,sau nake ta fara yimin yau don gaskiya nag ta iya" "kai sister sosai ma,ko sau daya fa ta miki sai kinga kin canza gaba daya,akinta da kyau sai tsada,bayan gyaran jiki har kitso da qunshi ma ta iya sosai"  "to yayi,ina humairata,Allah sarki aishana,nayi missing dinta a lot"  "Yanzu babanta ya fita da ita sitting room yayi baqi"hamma ta kubcewa fadilan har sai da faridan taji "idan sun shigo kice ina gaidasu ita da abban nata,ni zan kwanta" Dariya farida ta saka "tabdi lallai sister,kai saidai na zo kawai"  Katse wayar fadila tayi taba murmushi don tasan halin farida bata qi su kwana suna abu guda ba......... *Mrs muhammad ce*👑 📘📘📚📚✍🏻✍🏻✍🏻 ********************** ⬇ ************************** ************* Ai Hausa Novels **************** *************************⬆ ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ⬇ ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ⬆ **************************