************* Ai Hausa Novels **************** *************************⬆ ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ⬇ ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ⬆ ************************** 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *SHIMFIƊAR AURENA* 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *Zahra Surbajo* *Bismillahirrahmanir rahim* *Wannan littafi na kudi ne ki siya 500 ki karanta,,in kinsan fitarmin dashi zakiyi to karma ki siya kibar kuɗinki.* *daban yake da sauran se kin karanta zaki fahimci hakan* *FREE PAGE DAGA 1-15* *Zahra muhammed nasir 2084024749 UBA* *07044600044 Aturo shaidar biya ta nan* *1* "Prince ya kamata kayi wani abu akan lamarinnan,yin shurunka ne fa ke Ƙara haifar da tarin matsaloli acikin gidan nan,me martaba kanshi in yaji bazeji daɗi ba in baka ɗauki mataki ba"cewar Sadeeq Wanda aka kira da prince gyara zamanshi yayi sannan ya lumshe ido,gami da taɓe baki,alamun abun be dameshi ba. Sadeeq bin shi yayi da kallo,baki buɗe,dama yasan baze yi magana ba dan inda sabo ya saba da halayensa.cikin girmamawa yaci gaba da faɗin. "Bayyanar video na tsiraicinka ranka ya daɗe abune da masarautarnan bazata iya kare zubewar mutuncinka ba,ya kamata ka duba batunnan"sadeeq ya sake faɗi cikin damuwa. Har yanzu idonsa a lumshe suke,bashi da niyyar buɗesu,hakanne yasa sadeeq ya fahimci bazeyi magana ba yanzu,dole tasa sadeeq miƙewa yay masa sallama sannan ya fice daga falon. Ba tare da damuwar komai ba ya gyara zamansa ya ɗauko remote ya sauya tashar da yakeson kalla,be jima ba ya miƙe cikin takun isa da ƙasaita yabar falon,yana tafiya kamar wanda aka yiwa dole. Ƙofar da zata sadashi da ɓangaren mahaifiyarsa ya nufa,fadawa da bayin gida se zubewa suke ƙasa suna masa kirari,har ya shige ƙofar. Koda ya shiga bata falon ƙasan,dan haka taka stairs yayi zuwa sama inda yasan ze sameta,ilai kuwa yana shiga yaganta kishingiɗe,ana matsa mata ƙafa,yayin da jakadiya ke gefenta tana bata labarai masu daɗi. Sallama yayi ya shiga,suna ganinshi jakadiya da ɗayar matar dake matsamata ƙafar suka zube suna miƙo gaisuwa gareshi,ganin mahaifiyarshi na gurinne yasa ya amsa a daƙile sannan ya zube agaban mahaifiyar tashi yace"barka da hutawa mami"ya faɗi cikin wani daddaɗan sauti. Miƙewa zaune tayi fuskarta ɗauke da fara'a tace "Aliyu hydara na kaine da rana haka?" Shuru yayi bece komaiba,sema samun guri da yayi ya zauna,ita ta haifi abunta dan haka tasan halin kayanta.dan haka dubanta takai gun jakadiyya tace"ku ɗan bamu guri,zan gana da yarima" Ba musu suka rusuna alamar girmamawa sannan suka fice daga falon. Suna fita ya rarrafa ya isa gareta,ya kwantar da kanshi a cinyarta,yafara magana kamar ƙaramin yaro cike da shagwaɓa,"mami don Allah kisa baki Abbana ya barni in tafi Swizland ɗinnan,bada wasa nake ba na gaji da zama anan please mami"ya ƙarasa maganar cikin magiya yana jijjiga hannunta. "Wai Hydar so nawa kakeso a faɗa maka ne,Abban ka yace bazaka koma ba,so yake ka fahimci shaanin mulki da kyau sabida kaine magajinsa,meyasa bazaka masa biyayya bane Hydar?"mami tayi maganar tana shafa gashin kanshi dake kwance lub kamar na larabawa. Miƙewa zaune yayi ya tattaro dukkan natsuwarshi sannan yace"mami ke mahaifiyatace,nasan dole kinason farinciki na,kuma duk wani abu daze taɓa mutuncina bazaki so shi ba" "wannan hakane Aliyu na"mami ta bashi amsa. Ajiyar zuciya yayi sannan yaci gaba da faɗin"Mami wata ƙaddara ta faɗo min,ni ba mazinaci bane mami amma se ga wani video an turomin shi ni ɗin a tsirara tare da wata yarinya wacce ko saninta banyi ba,ana barazanar sakin videon a cikin masarautarnan"ya ƙarasa maganar cikin yanayin dake nuna ɓacin rai. A zabure mami tasa hannunta akan bakinshi ta toshe masa baki wasu siraran hawaye na biyo idonta. Rungumeta Aliyu yayi,ya saki wani kuka,wanda tunda abun ya faru be taɓa nunawa kowa ya dameshi ba,amma sosai abun ya ɗaga hankalinshi matuƙa,gaba ɗaya kanshi a kulle yake.se yanzu daya iso gaban mahaifiyarshi ne yasamu kukan yazo masa. Hannunshi taja suka bar falon suka koma ɗakinta,kan gado ta zaunar dashi sannan ta kulle ƙofar,ta zuge glasan window,ruwa ta ɗebo masa a dispenser me sanyi ta bashi yasha,ya ɗan numfasa sannan tace cikin rauni. "Tunda mahaifinka ya bayyana ka a matsayin mejiran gado Hydar nasan ƙalubalen rayuwane zasui ta tunkaroka,wanda sede ƙarfin addua ne kawai ze warware duk wata matsala,na yarda da tarbiyyar da nai maka Aliyu,ka ɗauki komai muƙaddarine daga Allah kuma ze wuce"ta faɗi tana shafa kanshi. "Mami inaso ne na binciko koma waye yay min hakan,shine yasa nakeson zuwa can ɗin dan abun zefi sirri"ya faɗi yana ƙoƙarin kauda damuwarshi,dan yasan inde yashiga damuwa mahaifiyarshi na shiga wacce tafi tashi,kasancewar shi kaɗai Allah ya bata. "kabar komai a hannun Allah zeyi magani,kabar batun tafiyar tukuna muga me ze faru"mami ta faɗi cikin ƙarfafa masa guiwa. Dole ya bar batun tafiyar,ya ɗan zauna agunta ta gama yimasa nasiha da adduoi,sannan yay mata sallama ya tafi,koda ya baro gurinta babu me cewa shine yay kuka yanzu sabida ya dawo yarima hydar ɗinsa me cikar isa da ƙasaita. Muje zuwa Surbajo for life. 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *SHIMFIƊAR AURENA* 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *Zahra Surbajo* *DUK WACCE TABIYA BAN SATA BA PLS TAIMIN MGN NA RASA NUMBERS ƊIN KUNE* *na kuɗine ki siya ki biya ki karanta,kar ki bari aɗauko abaki ki karanta kyauta,na taka muhimmiyar rawa gurin kawo muku wannan littafin,daban yake da sauran,karki bari abaki labari,akwai soyayya,abun dariya,ban haushi,tausayi,da abubuwan ban mamaki,magunguna,da tarin adduoi ma banbanta,domin kariya daga dukkan sharri,salon iya ba shimfiɗa hakkinta,duk acikin wannan littafi akan farashi 500 kacal,baki da danasani,asiyansa* *ga wanda besan marubuciyar ba,to marubuciyar littafin SURBAJO,UMMU AYMANA,KANO TO JIDDA,DA SAURANSU CE,kowa ko yaji gangami ay yasan da labari😄* *Zahra Muhammed Nasir 2084024749 UBA* *Aturo shaidar biya tanan 07044600044, bana adding agroup na faɗi anƙi ji to yanzu inayi ki turo ɗari biyar ta adding ɗin zan saki,in novel dinama kikeso tsoho ki turo dari biyar ɗin😊🤝* *FREE PAGE 1-15* *2* Da mahaukacin gudu ta faɗo gidan,da wanke wanke taci karo da ike idonta a rufe yake sam bata lura ba seda ta faɗa cikin kayan,jikake kwacham,ko tsayawa batayi ba ta sake fallawa da gudu cikin ɗakin, Kwance take kan tabarma tana sauraron shiri agidan radio taji,an taka mata ciki an wuce da gudu,a firgice ta miƙe zaune,dan tasan ko aykin waye,ilai kuwa itan ce,dan ta hangeta lokacin da take ƙoƙarin shigewa ƙarƙashin gadonta na ƙarfe. Da sauri ta miƙe jin hayaniya a tsakar gidan ta fito,yara ne maza sun kai su bakwai a tsaye suna ta haki,kowa rai aɓace. Gyara tsayuwar ɗaurin ɗankwalinta tayi sannan tace"to me kuma ya faru naganku,tsaye anan?"inna ta tambaya. Ɗaya daga cikin yaranne yabata amsa da cewa"Inna Deeyanah ce muna ball tazo ta ɗauke ta fasa mana,shine mu kuma muka biyo ta ta biyamu". Ɓata rai inna tayi dan aduniya in akwai abinda inna ta tsana to shine ace ga laifin Deeyanah."Deeyanar ce zata iya wani fasa muku ball sabida tsabar rashin tsoron Allah kunbi kun addabi yarinya bata ci muku ba bata sha muku ba to wallahi kuji tsoron Allah Deeyanah marainiyace in kuka cuceta se kun shiga wuta" ta faɗi cike da masifa. "Inna ƙarya suke min,ni ko ball ɗin ma ban gani ba,ina cikin tafiyata suka biyoni da gudu"cewar Deeyanah daga can ƙasan gadon Inna. "bari ɓata bakinki,shalele,sharri irin na mutanen garin nan wanne ne ban sani ba,kuma wallahi zasuyi su bari"Cewar inna. "wallahi inna ba sharri muke mata ba,ita ta fasa kuma fasasshiyar tana hannunta,aduba mana"cewar wani yaron kamar zeyi kuka. "dama ay kai jabiru da ganinka anga munafuki,harda in duba to ubanka zan duba,kunsan Allah in baku fice daga gidannan ba na lahira seya fiku jin daɗi."inna ta faɗi tana ƙoƙarin ɗauko ma doki ayko da gudu yaran suka fice daga gidan. Ɗakin dake kusa da nata ne aka buɗe aka fito,mace ce dattijuwa kamar innar,"kinga yaya,wallahi kibi rayuwa a hankali,wannan abun da kikeyi ba abinda ze haifar se lalacewar tarbiyyar Deeyanah,kuma in ta lalace ke kanki bazaki so ta ba"bata ƙarasa me takeson faɗi ba, Inna ta katseta cikin hargagi da masifa. "Aniyarki ta biki Uwani,wallahi bakinki yasari ɗanyen kashi,wato fatan ma da kikewa gudaliyar jikar tawa ma kenan ko,ay dama najima da sanin maƙiyan Deeyanah harda na gida,to duk zakuyi ku bari,Deeyanah ta tauraruwa ce"cewar inna kamar zata daki uwanin. Deeyanah ce ta fito hannunta ɗauke da ball da ta fasawa yaran da suka biyota. Kallonta inna tayi cike da mamaki tace"gudaliya,a ina kuma kika samo fasasshiyar ball ɗin?"ta faɗi tana jawota jikinta. Cikin taɓara da shagwaɓa tace"a ƙasan gadonki mana" Cikin borin kunya inna tace"au eh anyi haka,jiya na samota nima"tayi maganar tana satar kallon gefen da uwani take. Uwani ko salati ta shiga yi tana tafa hannaye tace"yaya kiji tsoron Allah ball ɗin da aka kawo ƙarar ta akan tace fa yanzu,amma sabida tsabar ɗaurin gindi data samu shine kikace wai ke kika samo jiya" "to na faɗi ɗin in da abinda zakiyi kiyi,muje ciki gudaliya ta"inna tafaɗi tana jan hannun Deeyanah suka shige cikin ɗakinta. Uwani ko tsananin mamakine yasa takasa cewa komai bare tai yunƙurin,barin gurin.itade tasan wannan ba gata bane ake mata. Muje zuwa. Surbajo for life. 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *SHIMFIƊAR AURENA* 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *Zahra Surbajo* *na kuɗine ki siya ki biya ki karanta,kar ki bari aɗauko abaki ki karanta kyauta,na taka muhimmiyar rawa gurin kawo muku wannan littafin,daban yake da sauran,karki bari abaki labari,akwai soyayya,abun dariya,ban haushi,tausayi,da abubuwan ban mamaki,magunguna,da tarin adduoi ma banbanta,domin kariya daga dukkan sharri,salon iya ba shimfiɗa hakkinta,duk acikin wannan littafi akan farashi 500 kacal,baki da danasani,asiyansa* *ga wanda besan marubuciyar ba,to marubuciyar littafin SURBAJO,UMMU AYMANA,KANO TO JIDDA,DA SAURANSU CE,kowa ko yaji gangami ay yasan da labari😄* *Zahra Muhammed Nasir 2084024749 UBA* *Aturo shaidar biya tanan 07044600044, bana adding agroup na faɗi anƙi ji to yanzu inayi ki turo ɗari biyar ta adding ɗin zan saki,in novel dinama kikeso tsoho ki turo dari biyar ɗin😊🤝* *FREE PAGE* *3* Yau kasuwa,dan haka tun safe inna ke tuyar wainar rogon da Deeyanah zata kai mata tallah kasuwar. Farin bokiti aka cika mata da ita,sannan tayo wanka,ta sauya kaya,taci adonta,tazo inda innar ke suyar. "Inna gaskiya yau in na siyar miki ɗari biyu zaki bani,dan inaso in biya jimmalo bashinta na kafi zabo da nasha mata"Deeyanah ta faɗi a tsanake kamar ba ita ba. "ba komai gudaliya zan baki kede kidawo da wuri kawai"cewar inna tana murza mata gammo. Tana gama naɗa mata gammon ta ɗora mata bokitin,tai mata sallama ta fice inna ta bita da adduar samun kasuwa. Deeyanah na fitowa ta fara ciniki,ana siya itama tana siyan abun da yay mata daɗi ba abinda yay mata zafi. Yaran matane sa'anninta suka tsaida ita,tsayawa tayi tana dubansu cikin alamun rashin gaskiya,"yauwa yau wa muka kama?"ɗaya daga cikin yaran tace, Shuru Deeyanah tayi dan bata da mafita yau a hannunsu, "ko ki biyani kuɗin kafi zabona ko muyi miki na jaki yanzu nan"inji jimmalo dake ƙoƙarin cakumo Deeyanah. Cinikin hannunta ta miƙa mata,ayki jimmalo ta amshe suka duddungure mata kai suka wuce,suna faɗin"shegiya da ido kamar mayya". Wani lungu Deeyanah ta shiga da bokitin tallan,tai zamanta,bokitin ta buɗe taci taci ta ƙoshi sannan ta rufe,tana saƙa abunda zata yiwa su jimmalo wanda bazasu taɓa mancewa da ita ba. A taƙaice de Deeyanah seda ta cinye wainar rogon tass sannan ta kamo hanyar gida,bayan tayi birgima acikin jar ƙasa tai futufutu,ta fasa bokitin. Kuka take kamar ranta ze fita,haka ta shigo gida tana ɗingishi ga hijabinta duk a yage. Inna ta tada sallahr laasar kenan tajiyo kukanta,ko sallamewa batayiba ta fito da gudu,haka itama uwani da hanzarinta ta fito dan ganin meke faruwa. Inna na hangota tace"Nashiga uku na ni Fatima,na lalace,gudaliyata meyasameki haka"ta ƙarasa maganar hawaye na biyo idonta,ta ƙarasa ta kamota,ayko sharab ta faɗa jikin innar tana sakin wani marayan kuka. Hankalin Inna in yayi dubu ya tashi,dan haka tun kan taji abinda ya sametan itama take kuka,dan tasan ba ƙaramin iftila'i bane kukan Deeyanah. Seda suka ci kukansu ma'ishi sannan Deeyanah tace cikin kukan"naje kasuwa na gama siyar da wainata tass har wani mutumi yace inyi sauri inzo gida in ƙaro ze siya ta ɗari uku,na taho akan hanya,shine su jimmalo da Hari ƴar gidan sabo kafinta,suka kamani a hanya suka min dukan tsiya suka kwace kuɗin suka yagamin kaya sannan suka fasa bakitin,jimmalo harda cewa nida kakata mayu ne"ta ƙarasa maganar tana me sake rushewa da kuka. Kamar guguwa haka Inna ta miƙe ta kamo hannun Deeyanahr tana faɗin"duk wanda besan balai da masifa ba arayuwarsa to Deeyanahr Inna ce be taɓo ba,yau se naga uban daya tsaya musu a garinnan,zasu san ko waye ubanki a ƙasar nan,ni zaa yiwa iya shege,taso muje in gwada musu matsayinki"tayi hanyar ƙofar gidan tana surfa zagi. Da sauri uwani ta dakatar da ita,tace"don Allah yaya kiyi haƙuri kibi komai a sannu,wallahi ta iya yiwuwa ƙaryar Deeyanah ce,se kinje kuma azo aji kunya" "munafuka me baƙar aniya,har Deeyanahr ce take ƙarya,to wallahi ko ƙarya takeyi yau se sun san matsayinta,dama ay ke ba ƙaunarta kike yiba ba abinda bazaki faɗi ba"tana kaiwa nan ta fincike tayi wucewarta riƙe da hannun gudaliyar tata. Suna fita kai tsaye shagon Isa me saida waya suka nufa.yana ganinsu ya miƙe da hanzari,yace"subuhanallahi,Inna me yasamu Deeyanah naganta a haka?ko mashin ne ya buge ta?"yayi maganar yana ƙarewa Deeyanahr kallo. "wanne mashin Isa,jimmalo ƴar gidan me gari,da yarinyarnan hari ta gurin sabo kafinta,sune suka haɗu suka mata wannan dukan suka kwace kuɗin tallan ta,sannan sukace nida ita duk mayune,Isa ka duba fa kagani,wallahi bazan yarda ba"inna ta faɗi cikin tsananin masifa kamar isan ne ya mata laifin. "to inna ande bincika ko an tabbatar da afkuwar lamarin?"isa ya tambaya a ɗan tsorace. "binciken uban me zan tsaya yi bayan abinda idona ya gani kuma kunne na yaji,kai ni banson wannan maganar dan ba ita ta kawoni ba,maza ka kiramin,Habubakar a waya yanzunnan kabani shi"ta faɗi cikin faɗa. Ba musu Isa ya danna lambar mahaifin Deeyanah,bugu ɗaya ana biyun ya ɗaga,cikin girmamawa isa yaɗan rusuna ya gaisheshi sannan yace"ranka ya daɗe,dama innace zatayi magana dakai" Inspector general of police Abubakar Adamu Kaita,shine Mahaifi ga Deeyanahr Inna. Yana tsaka da meeting da kwamishinonin sa ne wayar isa ta shigo,yasan kiran na Mahaifiyarsa ne,dole ya tsaida taron ya fito don amsa kiran,dan ita kaɗai yake waya da ita a wayar shiyasa ko yaransa be ba wayar koda yaushe tana tare dashi. Miƙawa Inna wayar isa yayi ya koma gefe. "Habubakar ina son ganinka ne yau yau ɗinnan base gobe ba"cewar inna batare data amsa gaisuwar da yake mata ba. Dafe kanshi IG yayi da yay mugun sara masa,ga shugaban ƙasa yabashi wani assigment,ga shi Inna tace yazo yau ba gobe ba,cikin biyayya yace"inna zuwan nawa nada muhimmancine a yau,kece ba lafiya ko takwarar taki?" "Ban sani ba nade ce kazo,in kuma bakazo yau ba wlh seka haɗu da fushina"tana kaiwa nan ta cillawa isa wayarshi ta ja hannunta suka koma gida. Isa be ce komaiba ya kwashe wayar a ƙasa ya koma bakin kasuwancinshi. Ɗakin taron IG ya shigo,cikin yanayin damuwa yace "kuyi haƙuri wani uzurin gaggawa ya sameni yanzu,sede ku kasance cikin shiri,ƙarfe goma na daren yau zamu sake zama,zan yi ƙoƙarin dawowa akan lokaci". Fatan alkhairi sukai masa sannan ya fice masu tsaron lafiyarsa suka mara masa baya,kai tsaye airport suka kaishi,kamin ya ƙaraso an shirya pjet ɗin daze kaishi,be jima sosai ba suka ɗaga zuwa katsina. Tafiya ce ta sauri,shiyasa yana sauka a katsina yace sukaishi kaita a helicopter kawai,ba musu akayi kamar yadda ya buƙata. Muje zuwa. Surbajo for life. 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *SHIMFIƊAR AURENA* 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *Zahra Surbajo* *na kuɗine 500 kacal kibiya kisha karatu,update biyu arana insha Allahu,ze ƙayatar daku masu karatu* *Zahra muhammed nasir 2084024749 UBA* *a turo shaidar biya ta nan 07044600044 whatsapp* *4* Filin ball na garin ya sauka,kasancewar ba nisa zuwa gidan innar daga gun a ƙafarsa ya tako,masu tsaron lafiyarsa na take masa baya. Yayin da mutane suka taru suna kallon shi,duk inda ya wuce se ya ɗaga musu hannu gamida sallama,har ya iso gidan na mahaifiyarsa,wanda har kwanan gobe yana baƙin cikin zamanta acikinsa. A tsakar gida ya samesu su duka har da Inna uwani,cikin ladabi ya tsuguna agaban inna yace "inna barka da yammaci mun sameku lafiya?" "Da baka same mu lafiya ba zaka ganmu ne"inna ta bashi amsa kamar zata dakeshi. Shuru yayi ya duƙar da kanshi ƙasa,a hankali ya furta"kiyi haƙuri inna" "ka riƙe haƙurinka,ba shi na kiraka ka ban ba,Deeyanah tace wasu yara agarinnan suka kama suka daka,taƙamarsu bata da galihu har da cewa ni da ita mayune,to yanzi base anjima ba inaso kasa ƴan sanda su wulaƙanta min su a gaban Deeyanah dan ranta yayi fari"ta faɗi tana huci kamar kububuwa. Ɗago kai yayi da sauri ya dubi mahaifiyar tashi sakamakon jin maƙasudin kiran nasa tun daga Abuja zuwa kaita. Dubansa ya kai gun Deeyanah,dake rakuɓe a gefen inna tana ware ido alamun rashin gaskiya.take ya fahimci batun akwai ƙarya acikinsa. "inna kin tsaurara bincike sosai kuwa kar azo ayi abunda zaa ji kunya,tunda de kinfa Deeyanah ba kunya ce da ita ba,kar aje ko laifin tane"IG ya faɗi cikin girmamawa. "binciken uban me zanyi habubakar,wato ƙiyayyar da kakewa uwar Deeyanah kakeson maida ta kan ɗiyarta marainiya,to wallahi kayi kaɗan kayi tsururu, kuma ay ba shawarar ka na nema ba bare kace zaka tsaramin yadda zaayi,umarni na baka ka aykatashi yanzu" Miƙewa yayi jiki asanyaye yace "Deeyanah zo muje kuje da jamian tsaro akamo yaran da kukai faɗan"ba musu ta bishi suka fice agidan. Cikin mintunan da basufi goma ba jimmalo da hari suka bayyanah agaban Deeyanah da inna, Binciken abinda ya faru yayi ,Deeyanah tayi wiƙiwiƙi. Tsananin takaicine yasa ya kasa magana,dan haka miƙewa yayi ya fice daga gidan ko sallama beyiwa Innarba. Muje zuwa *Assalama alaikum* *Ina mata ma'abota son gyara nazo muku d hadaddan maganin Gyaran breast sadidan* *Y'r uwa maza garzayo maganinmu* *ingantaccene nono ko yakai silifas kwanciya insha Allah kikai amfanid maganinmu zakiga aikinsa mace sai d gyara nono shine martabar* *mace* *Maganinmu yana ciko d breast su tashi suyi bul bul a 1week maganinmu Bashi d side effect* *Maganinmu masu yaye suna amfani dashi y'anmata kowa zai iya amfani dashi mata adaure adinga gyara ki kankaro mutuncinci* *WhatsApp 08063114606 Call08120337219* *Location: Kano* Surbajo for life. 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *SHIMFIƊAR AURENA* 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *Zahra Surbajo* *Shawara karki soma karantawa in baki biya ba gudun ya ɗauko daɗi ba ƙarashe😄ki siya abunki kai waye,akan kuɗi 500 kacal,babu danasani awannan littafi,kisiya muyi tafiyar nan dake,munayin ki over surbajo,to nide banga alama ba😄tunda kinƙi siyan littafina kina jiran na kyauta* *Zahra Muhammed Nasir 2084024749 UBA* *A turo shaidar biya tanan 07044600044* *5* Takaici da baƙin ciki ne yasa IG wucewa batare da yayiwa inna sallama ba,ace akan shirmen banza ataso shi tun daga Abuja zuwa kaita dan kawai yaji ƙarya,kai gaskiya inna bata masa adalci. A nata ɓangaren inna borin kunya ta shiga yi tana faɗin"da basu dungure mata kan ba ay da bazatace su ɗin bane," Uwani dake gefe tana kallon ikon Allah ajiyar zuciya tayi tace "kowa ya biye zuciya zeyi dana sani,Allah ya kyauta"tana kaiwa nan ta miƙƙe ta shige ɗakinta. Inna maimakon tayiwa Deeyanah faɗa,rungumota tayi jikinta,tana shafa kanta tace"barsu gudaliyata duk zasuyi su bari,ke ɗin dashen Allah ce" ******** A can Abuja ko IG daya koma ɗage zaman dayace zeyi yayi zuwa kwana uku masu zuwa,dan gaba ɗaya baya jin daɗin jikinshi. Zaune yake a falon shi yana duba jaridun da aka kawo mishi kasancewar yau saturday yana gida. Hajiya maryam ce ta shigo falon cikin wani leshi daya gaji da haɗuwa,tayi kwalliyarta data ƙara fito da kyanta. Gefen mijin nata taje ta zauna ta langaɓar da kai gefe,dake nuna tana cikin damuwa. Ɗago kai IG yayi ya dubeta,cike da kulawa ya ajiye jaridar hannunshi ya kamo hannunta dayasha jan lalle yace "ya akayi ne gimbiyata?,menene matsalarki?" Kwantar da kai tayi kan kafaɗarshi tace cikin muryar shagwaɓa"Abban Deeyanah,yanzu fisabilillahi haka zaka zuba ido kabar Deeyanah a hannun Inna ba makaranta,ba ilimin addini bare na zamani,sede tallah da yawon banza tana ɗauko magana tarbiyarta na daɗa lalacewa?" Runtse ido IG yayi dan matar tashi ta soso inda ke masa ƙaiƙayi,kullum da wannan baƙin cikin yake kwana yake tashi,cikin damuwa yace. "a har kullum maryamu ban taɓa danasanin zama dake ba,kina sona kina son duk wani abu nawa,sede mahaifiyata ita bata sonki da duk wani abu daya shafeki,tunda Aisha ta mutu gun haihuwa,inna ta alaƙanta hakan dake,ko kaɗan bata ƙaunar ta bamu Deeyanah,na rasa yazanyi in amshi yarinyar nan in inganta rayuwarta,gaba ɗaya yarinyar yanzu in kika ganta wlh irin yaran nan ne marasa kunya ga ƙarya da haɗa sharri,kuma ita inna bata ganin hakan a matsayin laifi,ita har kullum son Deeyanar ne baa yi shiyasa ake mata hakan". "Duk wannan Alhaji ni be dameniba,kawai tsorona ranar lahira Allah ze tuhumeka kan tarbiyar Deeyanah,yakamata de kayi wani abu akai" Shuru ce ta biyo baya,kowa na saƙa da warwara azuciyarshi domin neman mafita. Yinin Ranar IG yayi shi gun tunanin yadda zebi inna ta bashi ƴarshi cikin ruwan sanyi batare da sun samu matsala ba. Bayan kwana biyu ya yanke shawarar zuwa kaita ya tuntuɓi inna akan maganar. Da azahar ya isa garin,cikin rakiyar jami'an tsaro ko ina ya kaure da jiniya. Yau ta gama suyar wainar rogonta kenan ya shigo gidan,dan haka arziƙin gurin zama ma be samuba se uwani ce ta shimfiɗa masa tabarma ya zauna. "Deeyanah kiyi sauri kizo ki wuce rana tayi,kisamu ki shishshigar da ita kamin la'asar"cewar inna tana naɗa mata gammo. Da saurinta ta fito,taci adonta tana gyara mayafinta,tace "inna yau in na siyar zan siyo rinbom acikin kuɗin"cewar Deeyanah wacce ko kallo mahaifin nata be isheta ba,sabida inna tace mata shi da matarshi ne suka kashe mata mahaifiyarta,Allah ne ma ya tsare da har da ita zasu haɗa. Ɗora mata wainar tayi,tabita har soro tana mata fatan samun kasuwa,sannan ta dawo cikin gidan tayi kamar batasan dashi a gurin ba. Wasu hawayene masu zafi suka gangaro daga idon IG ganin shi da yaba Milliyan dubu baya,gashi ƴarshi ta ɗauki tallan dabe wuce na dubu ɗaya ba zataje tayi gogayya da maza.share hawayen yayi sannan ya ƙarasa kusa da innar. Tsugunawa yayi yace "inna barka da rana mun sameku lafiya?" Seda tagama shan ƙamshi sannan tace"lafiya" Shuru yayi na ɗan lokaci sannan yace"inna dama nazo ne neman alfarma agunki,kiban Deeyanah mutafi Abuja asata a makaranta,zamanta a haka beda amfani in kikayi laakari da cewa...."tass inna ta ɗaukeshi da mari,wanda yasashi yin shuru badan ya shirya yin hakan ba,lalle inna kin kai ƙwaruwa the whole IG guda. Rintse idonshi yayi,ya dafe gurin,cikin tsantsan mamakin mahaifiyar tashi,da ta maida marin fuskarshi kamar abun wasa. "a sata a makaranta ko kuma ku ida nufinku akanta nason ganin bayanta,to bazan baka ba,kai daga yau kakuma zuwamin da magana makamanciyar wannan wallahi seka gane kuranka,ɓacemin da gani,sullutu bawan mace".cewar inna bakinta har kumfa yakeyi. Bece komai ba ya miƙe ya fice dag Gidan jamian tsaronshi dake waje suna jiransa suka mara masa baya. Suna cikin tafiya,ya hangi Deeyanar gurin wasu leburori ta ajiye tallan tana ta rawa atsakiyarsu suna mata tafi,wani har jan hijab ɗinta yake. Runtse ido IG yayi yana karanto duk adduar data zo bakinshi, umarni yabada a ɗauko masa ita. Ba musu jami'i ɗaya ya fice a motar ya isa inda take bece komai ba ya sunkutota,tana ihu yasa ta a motar kusa da mahaifinta,direba yaja suka bar garin da hanzari. Muje zuwa Surbajo for life 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *SHIMFIƊAR AURENA* 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *Zahra Surbajo* *na kuɗine 500 kacal,ki biya ayi tafiyar dake,akwai tarin ilimi acikinsa,da nishaɗantarwa uwa uba soyayya me tsayawa a zuciyar me karatu,ki turo naki mu jera dake😄* *Zahra muhammed Nasir 2084024749 UBA* *07044600044 Aturo shaidar biyan tanan,whatsapp* *ta acct kawai ake biyan kuɗin littafin,in baki da acct akwai pos so in son siya kike se ki turo ta pos ɗin,nagode* *6* Tunda ta waigo taganta zaune kusa da mahaifin nata setaja bakinta ta tsuke,ta dena kukan dan tasan inde inna nada rai ba wanda ya isa yay mata tilas. Koda suka isa katsina airport aka kaisu,lokacin da jirgin ze tashi ne Deeyanah ta fara ihu tana faɗin"wayyo Allah na innata zasu kaini saman jannati,wayyo kayan cikina duk sun kwashe su,wallahi amai zanyi ku saukeni"da ike a ɗaure take da seat bell ba wanda yabi takanta. Suna isa Abuja kai tsaye gidanshi aka kaishi shi da Deeyanah. Hajiya Maryam na zaune a falo taga mijin nata yashigo ya taso ƙeyar Deeyanar agaba tana turo baki gaba. Cike da farin ciki hajiya ta miƙe ta kamo Deeyanar tana faɗin "Alhmdllh,ƴata ta dawo gareni,Allah na gode maka" Da sauri Deeyanah ta kwace hannunta ta matsa gefe tace cike da tsiwa da rashin kunya "ƴarki ko de ƴar kishiyarki da kika kashe,ay wallahi nima nice ajalinki"ta faɗi ba tare da tsoron kowa ba. A fusace IG ya ɗauketa da wani gigitaccen mari,wanda nan take ta saki futsari ta fashe da kuka. Da sauri hajiya ta shiga tsakaninsu tace"haba alhaji taya zaka daka ta tata,ay yarinyace abi komai a sannu,in kace da zafi zaka bi komai baze haifar da ɗa me ido ba"ta ƙarasa maganar cikin sigar rarrashi. Guri IG ya nema ya zauna,yana huci dan gaba ɗaya haushin Deeyanar yake ji kamar yay ta dukanta se ta dena motsi. Jan hannunta hajiya tayi,da bazata bita ba amma tuno zafin hannun IG bata san lokacin data bi tan ba tana kuka. Sashin yaran gidan takaita,dawowarsu daga makaranta kenan,suna ganin hajiyar kowa ya duƙa yana gaisheta,amsawa tayi cikin walwala,tacewa ƴar babbar wacce zasuyi saanni da Deeyanah "Munauwara ga sister ku nan ta gurin innarku ta kaita,maza ki sa tayi wanka ta kimtsa,taci abinci kamin in dawo". Bata jira amsar su ba ta saki hannunta ta koma gun mijinta dan ta kwantar mai da hankali,dan ta fahimci acikin zafin rai yake. Ruwa ta ɗebo masa me sanyi ta bashi yasha sannan tajashi zuwa ɗakinsa,ta taimaka masa ya rage kayan jikinsa,sannan taje toilet ta haɗa masa ruwan wanka ya shiga. Kamin ya fito ta fito masa da kayan dazesa marasa nauyi,sannan ta kwaso abincinsa ta kawo ɗakin,yana fitowa taimaka masa tayi ya kimtsa,sannan ta zuba masa abincin yaci yasha ruwa ta kwashe kayan,sannan ta dawo. Jikinshi taje ta kwanta,tace cikin taushin murya"Abban Deeyanah ina fatan de da yarda da amincewar inna kuka taho,dan naga tafiyar kamar ba shiri kuka yo ta?"ta ƙarasa maganar tana wasa da hannunsa. Murmushin takaici yayi,sannan yace"maryamu bada izinin inna na taho da deeyana ba,"daga haka ya kwashe duk abinda ya wakana ya shaida mata. Sosai tausayin mijin nata ya kamata wasu siraran hawaye suka shiga zubo mata cikin kuka tace "shekara da shekaru Abban deeyanah rashin jituwa kaida mahaifiyarka duk dan saboda ni,"da sauri ya rungumota jikinshi ya fara rarrashinta da kalamai masu daɗi. Dena kukan tayi sannan tace"ayi gaggawar saka deeyanah makaranta,dan akwai duhu na jahilci a tattare da ita,sabida a samu ta natsu,duk wani sakarci dena shi zatayi in Allah ya yarda," "hajiya kiyi haƙuri da halayenta,ko kaɗan deeyanah bata da kunya,don Allah ki zama me juriya watarana ze zama labari"IG ya faɗi cikin sigar rarrashi. Murmushi tayi sannan tace "uwace fa ni Alhaji,kadama wannan ya dameka insha Allahu zan jure har zuwa lokacin da zata fahimci gaskiya"cewar hajiya tana murmushi. A can kaita kuwa,da Inna taga har laasar bata ga Deeyanah ba mayafinta ta ɗauka ta tafi neman ta hankali a tashe. .Muje zuwa Surbajo for life. 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *SHIMFIƊAR AURENA* 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *Zahra Surbajo* *free pages sun kusa ƙarewa,hanzarta ki mallaki naki 500 ne kacal ba tsada,domin ki shigo cikin tafiyar ayi dake,shimfiɗar aurena yasha bam bam da saura,shi ɗin na musamman ne* *zahra muhammed nasir 2084024749 UBA* *A turo shaidar biyan tanan 07044600044 ta acct kawai banda recharge card* *9* A zabure dukansu suka miƙe suna kallonta,dan sosai suka tsorata da ganin nata. Baki na rawa hajiya maryam tace"sannu da zuwa inna" Ay kamar jira inna take ta fara da cewa"munafuka baƙar daga me fasa taro,tauraruwa me wutsiya ganin ki ba alkhairi ba,kin tarwatsamin farincikina dana ahalina," IG ne ya matso kusa da Hajiya maryam yace mata cikin sigar rarrashi "go inside,please kiyi haƙuri"hawaye ke bin idonta amma seda tayi masa murmushin ƙarfafa guiwa sannan ta juya ta bar gurin. "bariki alalen gero,wato habubakar ni ka maida ƴar iska sabida matarka,to wallahi ku da kwanciyar hankali se kun miƙomin jikata gareni,baku isa ba wallahi kunyi tsararo" Tsugunawa yayi gabanta cikin damuwa da tsantsar takaici yace"inna kullum burinki shine kiga ina miki biyayya,sabida haihuwata da kikayi,amma ni fafur ƴata kin hana taga mutuncina ma bare har ayi tunanin zata soni wata rana,kinsa ta tsaneni bata ganin girmana,inna me nai miki ne da zafi har haka dayasa bakyason kwanciyar hankalina,nine fa Abubakar ɗinki ɗanki ɗaya tak a duniya,ba ƙya gudun ciwon damuwa ya kamani nima ki rasa ni shikenan kin huta"yayi maganar hawaye na biyo idonsa. Sosai jikin Inna yayi matuƙar yin sanyi,jin kalamin na IG tabbas in ya mutu ko ta shiga uku,dan bata da sauran ɗan da zata nuna a mazaunin nata baya ga shi ɗin. Hannunta IG ya kama ganin ta ɗanyi sanyin ya kaita kan kujera ta zauna batare da musun komai ba,ruwa ya kawo mata me sanyi,sannan ya je dinning ya haɗo mata abinci da zafinsa yasha kayan lambu da naman kaza yazo ya durƙusa agabanta,yasa cokalin ya ɗebo abincin ya nufi bakinta dashi,seda ta doka masa harara sannan ta amshi abincin,to dama in banda fitinar Inna ta ɗebo yunwa,dan haka sosai taci abincin da IG ya zubo matan,ruwa tasha tayi hamdala sannan tace "ina gudaliyata?"tayi tambayar kadaran kada han. "inna deeyanah na lagos can na kaita karatu,kuma insha Allahu sun kusa samun hutu,da zaran ta dawo zaa kawo miki ita tai miki hutun acan"cewar IG cikin dabur dabur. "lagos fa kace habubakar?kai ko wacce irin tsana ce kaiwa yarinyar nan daze sa ka kaita lagos makaranta?"inna ta faɗi cikin faɗa. "kiyi haƙuri inna,ilimin can yafi nanan shiyasa na kaita ba ƙiyayya tsakani na da deeyanah har abada sabida ƴata ce kuma ina sonta,bazan taɓa yin abinda ze cutar da ita ba"cewar IG cikin biyayya. "habubakar nifa ba kai ne bana so ba,matarka ce bana so ƙiriƙiri ta kashe Aisha amma ido da addini ka kasa miƙata ga mahukunta su kasheta itama, taya kake tunanin zan iya ganin farinta har in yarda jikata ta zauna agunta,to wallahi da sake"cewar inna cikin ɓacin rai. "inna kinfi kowa sanin maryam ba ta kashe Aisha ba,hasalima taimakonta taje yi,tsautsayi da ƙarar kwana yasa Aisha ta rasu,to akan wanne dalili kikeso ki manna alhakin mutuwar Aisha akan maryam,inna kifa tuna zamu mutu muje ga Allah duk abinda muka tabbatar da bamu da yaƙini akansa abu mafi sauƙi mu watsar dashi dan wucewa lami lafiya" Be ida me yakeson faɗiba yaji ta rushe masa da kuka,tana faɗin"habubakar nice nakewa matarka ƙarya da sharri ko,ni kasa agaba kana wulaƙantawa har haka,ba komai Habubakar na barwa maryam ɗin kai duniya da lahira tunda ta fini agurinka" Cikin tsananin tashin hankali,ya zube a gabanta yana magiya kan ta janye furucinta na cewa ta barwa maryam shi,da ƙyar yashawo kanta ta haƙura ta janye. Ɗakin saukar baƙi ya kaita da kanshi ya gyara mata gado da duk abinda zata buƙata sannan ya fito yajawo mata ƙofar. Gaba ɗaya ya rasa meke masa daɗi,komai ya kulle masa yarasa ta ina ze fara. wannan wacce irin rayuwace. *********; Wata guda inna ta kwashe a Abuja zaman jiran dawowar deeyanah,ba irin wulaƙanci,ƙasƙanci da cin mutuncin dasu IG basu gani ba agun inna azaman nata a gidansu. Ta hanasu saƙat acikin gida sede ko yaushe suna ɗaki,in ba gurin aykiba.dan motsin kirki sukayi agabanta se tace zaginta sukeyi,ko tace munafuncinta sukeyi. Ana wannan bidirin ne Deeyanah ta iso daga lagos sakamakon hutun da aka musu.cike da mummunar manufa ta iso gidan na mahaifinta. Ga mamakin inna rawar ƙafar da take tunanin deeyanah zatayi in ta ganta setaga batayiba,dan har wani shan ƙamshi takewa innar. Hmmmm Muje de zuwa Surbajo for life. 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *SHIMFIƊAR AURENA* 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *Zahra Surbajo* *To jiya na kammala littafin TAYI MIN ƘANƘANTA,yanzu ga SHIMFIƊAR AURENA na kuɗine daban yake da sauran,kibiya 500 kisamu damar karantashi har ƙarshe,karki fara baki samu ƙarashen ba ki soni kiso littafina ki siya ki biya shine soyayya😄* *Zahra muhammed Nasir 2084024749 UBA* *07044600044 a turo shaidar biyan ta nan,ta acct kawai banda kati* *7* Inna yawo take lungu da saƙo na garin neman Deeyanah tun tana sa ran ganinta har ta soma fidda rai,zuwa yanzu kuka take wiwi, Ta shawo kwanar lungun gidansu ta haɗu da Audu ɗaya daga cikin leburorin da aka ɗauki deeyanah agun su.ganin tana kuka ne yasa yace"Innar Deeyanah lafiya kike kuwa?" Cikin kuka tace"Deeyanah ce tunda ta fita da tallah banganta ba,na nemeta har na gaji"ta ƙarasa maganar cikin matsanancin kuka. "Deeyanah ay tun ɗazu wasu ƴansanda suka ɗauketa takai tallah gurinmu,sun tafi da ita a motocinsu masu jiniya"cewar Audu cikin yanayi na tausayawa. Ay Inna bata jira yagama bayaninba ta juya da gudu ta nufi gun isa me waya tana faɗin"Shikenan gudaliyata Habubakar yakai min ke inda zaa kasheki kamar yadda aka kashe mahaifiyarki,wayyo ni fatima ina zansa rayuwata ba marainiyar Allah"a haka ta ƙaraso gun isan,jamaa se kallonta akeyi. Isa na ganinta ya taso da saurinsa,yana faɗin "inna lafiya kuwa?"bata bashi amsa ba se cewa da tayi"ka kiramin yaron nan mara mutunci,nace ka kiramin habubakar yanzun nan"tace cikin ƙaraji. Jikin Isa har rawa yake ya danna lambar baban Deeyanah. IG na zaune a falo yaji ƙarar wayar daya ware domin inna,dama yasan zaayi hakan,dan haka cikin dauriya ya ɗaga wayar. Isa na jin an ɗaga ya miƙa mata,ay yana bata ta fara da cewa. "yau na tabbatar da cewa habubakar kai ba jini na bane,wato na hanaka tafiya da deeyanah shine kasaceta ka kaimin ita inda zaa kashe to wlh cikin daren nan ka kawomin ƴata" "Inna kiyi haƙuri amma batu na gaskiya Deeyanah bazata dawo gunki ba sabida tsarin da kika ɗorata akai,in muka koma ga Allah ni zaa tuhuma game da amanarta da Allah ya bani,inna ina miki biyayya sede wannan karon Deeyanah ta dawo kenan kiyi haƙuri ki kwantar da hankalinki"yana kaiwa nan ya kashe wayar gaba ɗaya ya kwantar da kanshi jikin kujera yana tunanin mafita game da matsalar inna. Inna ko jin ya kashe ne yasa ta shiga surfa masa zagi tana birgima agurin ita ala lalle dole se isa ya kaita Abuja. da ƙyar isa ya rarrasheta yakaita gida,ranar kwana tayi tana kuka,inna uwani tayi rarrashin har ta gaji. IG na kashe wayar miƙewa yayi ya nufi ɓangaren yaranshi,ayko suna ganinshi kowa ya taso yazo ya rungumeshi suna masa sannu da zuwa banda Deeyanah wacce tunda ya shigo take doka masa harara,gami da taɓe bakinta. Zama yayi cikinsu yana sauraron kowa da damuwarsa,Abulkhairi ne yace "daddy waccan auntyn bata da kirki tun ɗazu take ta dukanmu"ya faɗi yana nuna deeyanah. Ɗago ido IG yayi ya dubi Deeyanar data cika tana jiran ko ta kwana,murmushi yayi sannan yace "laifi kukai mata,shiyasa ta dokekun" Taɓe baki tayi ta kauda kanta gefe. Kallonta kawai IG yake,cikin nuna kulawa yace mata "mamanah ya baƙunci?"ya faɗi lokacin daya kamo hannunta. Ƙoƙarin kwace hannun takeyi amma ta kasa,dan haka shuru tayi tana kallonshi,batare data amsa masa ba. murmushi yayi yace"cikin satin nan zaki makaranta,ki samu ilimi dan ki koma gun innarki ki kula da ita"se alokacin tayi magana jin ya ambaci inna,"ni amaidani gunta banason makarantar,ay sabida rashin makarantar ne yasa ka tsani mamana har kuka kasheta dan ita bata da ilimin boko,to nima bana son makarantar" Sosai batun ya taɓa zuciyarshi amma yasan deeyanah bata da laifi me laifin inna ce dan duk itace ta cusa mata ƙiyayyarshi a zuciyarta. Be ce komai ba ya saki hannunta yabaro ɗakin yana saƙe saƙe a zuciyarshi. Muje zuwa ************* Ai Hausa Novels **************** *************************⬆ ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ⬇ ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ⬆ ************************** Surbajo for life. 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *SHIMFIƊAR AURENA* 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *Zahra Surbajo* *na kuɗine ki biya kan ki karanta,dan samun damar karance shi gaba ɗaya 500 ne kacal* *zahra muhammed nasir 2084024749 UBA* *A turo shaidar biyan tanan 07044600044* *10* Deeyanah wanka tayi taci abinci sannan ta dawo falo ta zauna tana girgiza ƙafa,tana cika da batsewa. Inna ce ta shigo jikinta har ɓari yake taje kusa da ita ta zauna fuskarta ɗauke da murmushi,ta kamo hannun deeyanah tace"gudaliya ta kinga yadda kika ƙara yin kyau kuwa?" Yatsina fuska deeyanah tayi sannan tace"ko?" "Kwarai gudaliya shiyasa nakeso gobe muyi asubancin tafiya kaita,sabida nasan muna zuwa samari se sunyi kamar su cinyeki"inna ta faɗi tana washe baki. "ku tafi ina,?ke da wa kuma?"deeyanah tayi tambayar tana ware ido. "mu tafi kaita mana,ni da ke"inna ta faɗi tana dariya. Wata shewa deeyanah tayi sannan ta miƙe ta fara juyawa agaban inna tana faɗin"haba inna yanzu ke ko dole aka miki kan ki tafi dani kaita kya fara,?kuma samari ay nafi ƙarfin na can sede na nan"ta faɗi tana wani kakkarya jiki. Baki inna ta saki tana kallonta,da ƙyar ta iya cewa"nufinki ke bazaki koma can ba?" "yauwa tunda kin fahimta,eh ni nazo kenan bazan koma ba,"deeyanah ta faɗi batare da damuwar komai ba. Hawayene ke biyo idon inna,cikin kuka tace"yanzu ni zaki watsawa ƙasa a ido,deeyana,bafa irin rashin mutuncin da banyiwa mahaifinki ba kan tahowa dake bada izinina ba" "kinga inna ina cikin nishaɗi yanzu karki ɓatamin rai,nace bazan koma ba,kibarni mana,akwai burika da nakeso in cika anan,in natafi taya zanyi hakan,"deeyanah ta faɗi cikin sigar nuna ƙosawa. "nima ba inda zani inde ba zaki bini ba"cewar inna tana share hawayenta. "better"cewar deeyanah lokacin data miƙe tabar falon. bin bayanta inna tayi da kallo,a ranta ta ce "yaro man kaza" Deeyanah,ko tana barin gurin,kitchen ta shiga,morning fresh ta ɗauko,tazo ƙofar ɗakin mummy ta juye shi a ƙasa kan tiles. Tana gamawa ta ƙwanƙwasa ƙofar ɗakin,tana ƙwanƙwasawa ta koma gefe da gudu,ta ɓoye,Hajiya maryam zuciyarta guda ta buɗe ƙofar,ganin bataga kowa bane,yasa tayi yunƙurin leƙawa falo taga ko me ƙwanƙwasa ƙofar can ya koma. Ay tana saka ƙafarta se kan morning fresh ɗin,ayko santsi ya kwasheta,suuuuu ji kake tim ta daku da ƙasa,ay deeyanah na ganin ta faɗin ta fito daga inda ta ɓoye ta fara cashewa agabanta tana dariya tana faɗin"faɗuwar guzuma,sede kaji tim tim,"tana faɗi tana zagaye hajiya maryam wacce ta kasa motsawa bare ta tashi sabida buguwa da hannunta da ƙugunta sukayi, tana rawa da waƙa. Wasu hawayene masu zafi suka shiga ambaliya a idon hajiya maryam ɗin.ganin yadda deeyanah ke mata,akan laifin da na nata ba. Muje zuwa Surbajo for life. 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *SHIMFIƊAR AURENA* 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *Zahra Surbajo* *masu maida novels ɗina Audio kuyi hattara,wahala nake na rubuta,ku kwashe a bati,ku je kuna neman kuɗi dasu,to kusani duk wanda ya maida littafina audio ya nemi kuɗi dashi alhalin ni ba siya yayi aguna ba,wallahi bazan barshi ba,zanyi duk me yiwuwa wajen ganin na bi kadin hakkina,in so kake ka ɗora akwai numbata a book dina kadauka muyi ciniki kaje kayi neman kuɗinka,wanda akayi a baya wannan ya wuce amma wlh yanzu ba sani ba sabo* *Free page daga 1 zuwa 15 ƙoƙarta ki mallaki naki,500 ne kacal,karki bari abaki labari SHIMFIƊAR AURENA shi daban yake da sauran* *zahra muhammed nasir 2084024749 UBA* *07044600044 A turo shaidar biyan tanan.ta acct kawai banda kati* *8* Wasa farin girki,tun inna nasa ran ganin andawo da deeyana har ta fara cire rai,hakan ne yasa ta fara shirin zuwa Abujan da kanta, Deeyanah zuwa yanzu ta saduda da batun komawarta gun inna,dan taga ko maganar baa mata,duk rashin kunyar da take musu ba wanda yabi ta kanta,kowa sabgar gabanshi yake. Kamar yadda suka tsara IG da hajiya maryam kan cewa makarantar kwana zaa kai deeyanah can birnin lagos hakan ce ta faru. Duk wani abu daya kamata a tanadar mata na jin daɗi a makarantar an tanajeshi,koda akace ta fito zaa kaita makarantar bata damu ba,dan ta ɗauka jeka ka dawo ce,kuma tana da yaƙinin innarta bazata barta ba a hannun maƙiyanta. Hajiya maryam ce ta tafi kaita makarantar sabida IG nada taron gaggawa daze halarta, Koda Deeyanah taga hajiya maryam zata tafi da gudu tazo gurinta tana kuka cikin kuka tace "har yanzu ƙiyayyar da kikewa mamana bata bar zuciyarki ba,shiyasa kika kawoni cikin wainnan ƙabilun su kashe miki ni ko?"tayi mata tambayar tana zubda kwalla. Hawayene suka taru a idon hajiya maryam cikin dauriya tace "dede da rana ɗaya deeyanah ban taɓa ƙin mahaifiyarki ba,ina sonta,kuma kema ina sonki,ƙaddarace ta gibta da ƙarar kwana yasa mahaifiyarki ta rasu amna bani na kasheta ba,kuma nan dana kawoki mahaifinkine yasa ni in kawoki" "ke da mahaifin nawa dama cikinku waye masoyin nawa,ay duk kanwar ja ce,nide na barku da Allah kawai azzalumai"tana kaiwa nan ta juya gun kayanta ta zauna ta haɗa kanta da guiwa tana kuka. Jiki a sanyaye hajiya maryam ta baro deeyanah badan tana son yin hakanba. Hostel aka kai deeyanah inda take bin kowa da ido,gashi abun takaicin yarabanci kawai ketashi da turanci gashi ita ba wanda takeji aciki,har aka kaita ɗakinsu bata ga bahaushiya koda mutum ɗaya ba. Zama tayi gefen gadonta tayi tagumi,hawaye na biyo idonta,tausayin kanta duk ya kamata da tunanin innarta,ji tayi an dafa mata kafaɗa,da sauri ta ɗago kanta dan ganin wanda ya dafatan. Wata kyakkyawar yarinyace wacce bata wuce shekarunta ba,tsaye tana mata murmushi,ga mamakin Deeyanah se ji tayi ta mata magana da hausa. "haba preetty kukan ya isa haka,muma da haka muka saba,kidena kuka haka kinji"ta faɗi lokacin da take ƙoƙarin zama kusa da ita. Share hawayenta tayi ta dubi yarinyar tace"ke bahaushiyace ?"murmushi yarinyar tayi sannan tace. "Sunana Jameela Abdullahi,muna zaune a Abuja,amma mahaifina shine sarkin garinmu,Abuja kawai de zama mukeyi in mun samu hutu,mu ƴan kano ne"cewar jameela tana murmushi. Ajiyar zuciya deeyanah tayi sannan tace"ni a kaita nake,amma yanzu an dawo dani Abuja daga can kuma akayo dani nan,sunana Deeyanah Abubakar Adamu kaita" "Abubakar Adamu kaita IG ?"Jameela ta tambayeta cike da mamaki. ɗaga mata kai deeyanah tayi,cikin faraa jameela tace"naji daɗin haɗuwa dake daga yanzu mun zama ƙawaye duk abinda baki iya ba ki tambayeni zan koya miki" Tun daga wannan rana ƙawance me ƙarfi ya ƙullu tsakanin deeyanah da jameela,har takai kowa ya faɗawa kowa labarinsa. Jameela irin shaiɗanun yaran nan ne da basajin magana dan haka shawarwari tashiga ba deeyanah ta yadda zata kashe hajiya maryam da baƙin ciki kamar yadda ta kashe mata mahaifiya. Cikin ƙanƙanin lokaci deeyanah ta waye ta iya ado da magana cikin natsuwa,gashi daidai gwargwado tana gane karatun sabida tana da ƙoƙari,gashi bakinta har ya fara iya yarukan da akeyi a makarantar bisa jagorancin jameela. ****** Inna haɗo kayanta tayi ta taho Abuja,da ike tasan gidan bata sha wahalar ganewa ba,hajiya maryam da IG suna zaune suna hira gameda shaanin tsaron ƙasar se ganin inna sukayi tsulim ta shigo falon tana huci kamar wuta. Muje zuwa Surbajo for life. 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *SHIMFIƊAR AURENA* 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *Zahra Surbajo* *Saura page huɗu free page su ƙare,ki hanzarta ki biya kuɗin naki dan ayi tafiyar nan dake babu danasani a wannan littafi ki biyo alƙalamin surbajo bazan kunyataku ba,500 kacal ba tsada,maso ɗan tsuntsu shike binshi da jifa.* *Zahra muhammed nasir 2084024749 UBA* *07044600044 Aturo shaidar biyan tanan,ta acct kawai banda kati,* *11* Miƙewa Hajiya maryam tayi daƙyar ta koma ɗaki batare da ta cewa deeyanah komai ba. Deeyanah falo ta dawo ta kunna kallo cikin shirin ko ta kwana,dan ta shiryama kowa na gidan. Hajiya ko tana shiga ɗakin wanka tayi ta gasa inda ta bugun,sannan ta dawo kan gado ta kwanta dan gurin sosai yake mata azaba. IG se dare ya shigo gidan ga aladar sa ya saba ze samu hajiyar a sashin ne,tana jiran dawowarsa. Koda ya shiga yaga be gantaba kuma baa kimtsa masa komai ba ne yasa yayi gaggawar yin wanka ya nufi ɗakinta. Can kan gado ya hangota kwance,da sauri ya ƙarasa gunta ya tallafota yana faɗin"hajiya lafiya kuwa kike yau?" Murmushi tayi masa ta shafo fuskarsa tace cikin dauriya "Tsautsayi ne na gamu da shi ɗazu na faɗi a toilet to na samu buguwa sosai a ƙuguna dan ko tafiya da ƙyar nakeyi"ta faɗi tana cije baki. A razane ya ƙara kamota,yana duba gurin yace cikin tausayawa,"subuhanallahi amma shine bakimin waya ba,oh my god sannu hajiya,ya kamata muje asibiti a dubaki"ya faɗi yana ƙoƙarin ɗaukarta. "ka kwantar da hankalinka yanzu dare yayi mu bari se gobe da safe se aje"cewar hajiya cikin yanayi nason kwantar masa da hankali. Haka taita lallaɓashi ya amince zuwa safiyar dan da sam be yarda ba. Gari na wayewa ya shiryata ya ɗaukota da kanshi dan gun ya kumbura ko tafiyar ma batayi. Ta gaban deeyanah da Inna ya wuce ba tare daya gaishe da innarba sabida hankalinshi dake tashe. Bayan motar yaje ya kwantar da ita direba ya tada motar,sannan ya zagaya ɗayan gefen ze buɗe ya shiga,ya jiyo muryar inna abayanshi tana faɗin. "to bita zaizai,gidan ubanwa zaku da ya ɗauke ma hankali ka kasa lura dani mahaifiyarka kazo ka wuce baka gaisheni ba?" "inna kiyi haƙuri maryam ce ba lafiya shiyasa nake sauri muje asibiti faɗuwa tayi a banɗaki jiya"IG ya faɗi yana duban agogon hannunsa. Tsaki inna tayi sannan tacs"dan ta faɗi shine harda wani ɗaukota ko kunya babu a gaban idona kai ga me mata,wannan da kishiya gareta da kun kasheta kwananta be ƙareba da baƙin ciki" Carab deeyanah ta amshe zancen kamar anayi da saanninta tace "hmmm inna kenan kishiya kuma ta nawa,ay irin wannan cin amanar suka dinga yiwa mahaifiyata har sukai nasarar rabata da rayuwarta"jikake tau tau IG ya ɗauke deeyanah da mari kan ta gyagije yasa ƙafa ya kwasheta tai sama ta faɗo ƙasa,sannan ya fara magana yana huci kamar tsohon zaki. "na gamsu ke ƴatace amma tarbiyarki batawa bace,duk rashin mutuncin da kike zuba ido kawai nayi ina kallonki bawai dan bani da yadda zanyi dake ba,kije ki tambayi kakartaki ta baki labarin rayuwar mahaifiyar taki,in de cin amana ne mahaifiyarki itace babbar maciyiyar amanar, maryam ta mata dukkan hallacci amma sakamakon da tai mata bame kyau bane,kije kakar taki ta shaida miki labarinta mana inde da gaske takeyi cewa mun kashetan,ko dan nayi shuru,kije ki binciko wacece Aisha mahaifiyarki,ki tambayeta mana ta baki amsa,ta gina rayuwarki ne akan munkashe miki mahaifiya,sabida ki tsanemu,hakan ze bata damar ɓoye aynihin labarin mahaifiyar taki"yana kaiwa nan ya sake kwallo da ita sannan yasa kai yayi shigewarshi motar direba yaja suka bar gidan. Inna wacce tunda yafara dukan Deeyanar take kuka,da ƙyar ta rarrafa gun deeyanar ta kamota,wacce tuni bakinta ya fashe da hancinta jini na zuba. Cikin kuka Deeyanah ta faɗa jikin inna tana faɗin"inna wacece mahaifiyata?pls inna ki faɗamin,shin tana da wani aybu ne?"deeyana take faɗi bakinta na jini tana kuka,innar itama kukan takeyi ta kamota ta rungumeta ajikinta. muje zuwa Surbajo for life. 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *SHIMFIƊAR AURENA* 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *Zahra Surbajo* *kin siya ko kina jiran a sato ki karanta😊Saura page biyu free page ya ƙare,ki hanzarta siyan naki domin ayi tafiyar dake,bawai kiji wai wai ba,500 ne kacal ba tsada,ki soni kiso littafinnan shine soyayya😄godiya ta musamman ga wainda suka siya Allah ƙara muku buɗi,ya cika muku burukanku na alkhairi,nidaku akwai ƙauna😍* *Zahra muhammed nasir 2084024749 UBA* *A turo shaidar biyan ta nan 07044600044* *13* Jiri ne yaji yana ɗaukarsa,duniyar na juya masa,wani duhu na giftawa ta idanunsa,yayinda zuciyarshi take barazanar fashewa sabida ƙunar da take masa. A Sukwane yayi kansu,iro ya cakumo,ya ɗagoshi,jikinshi se ɓari yake sabida yazo yin releasing kenan Abubakar ya zaro shi. Wani mahaukacin duka,ya shiga kirɓa masa,kan wani lokaci tuni ya sauya masa kamanni. Aisha miƙewa tayi a tsorace take dan haka bata jira ɗaukar kayanta ba ta ruga da gudu zuwa ɗakin Inna tana haki. A gigice inna ta kamo ta tana tambayarta "lafiya kike kuwa Aisha? ina kayanki?me ya sameki?"duka jerin tambayoyin ba amsa se kuka take. Warin maniyin da inna taji ne na tasowa ajikin Aishan yasa ta fahimci meke faruwa da ita,sosai hakan ya gigita inna a ɗimauce take girgiza Aisha tana faɗin"waye yay miki wannan aykin ki faɗamin Aisha nace waye"ta ƙarasa tambayar cikin ƙaraji. Wani sabon kukan Aishan ta saki sannan tace "Yaya Abubakar ne"tana rufe bakinta yana shigowa ɗakin da belt ɗinsa a hannunsa yana huci. Da gudu Aisha tayi bayan inna dan kare tsiraicinta,Inna wacce ta ɗauki salati jin cewa Abubakar ne ya yiwa Aisha wannan ayka aykar,ganin shi atsaye ne agabanta yana ƙoƙarin damƙo Aishar yasa tai saurin ɗaukeshi da mari. Ta fashe da wani kuka me tsuma zuciya cikin kuka take faɗin "Ka cuceni Habubakar,ka cuci zumunci ka cuci marainiyar Allah ka wulaƙantani ka wulaƙanta kanka da zuriar mu baki ɗaya,Allah ya isa tsakani na da kai"ta ƙarasa maganar lokacin data kife agun tana kuka. Da gudu Aisha tayi ƙasan gadon inna ta ɓoye kanta,shi ko Abubakar jikinshi ne ya ɗau kakkarwa jin kalamin inna,cikin dauriya ya duƙa ya kamota yana faɗin"innata me nai miki kike irin wannan mugayen kalaman akaina?"marin data ɗaukeshi dashi ne yasa yayi shuru,ita kuma ta fara magana "ubanka kaimin Habubakar,nace ubanka kaimin,kajini ko in ƙara faɗa maka,?kayiwa Aisha ƴar uwarka fyaɗe kuma dan rashin ta ido har kazo kana tambayata me kaimin?,nace kan ubanka kaimin"inna ta ƙarasa maganar cikin tsananin masifa. Wayyo Abubakar tashin hankali baa sa maka rana,duniyar juya masa take,da ƙyar ya tattaro ƴar ragowar natsuwarshi yace"inna ni alaƙa makamanciyar wannan bata taɓa haɗa mu ba da Aisha,kuma ko yanzu da iro na kamasu suna masha'arsu na koreshi,ita kuma ta gudo gida". "ba ruwan iro inna wlh shine,?"cewar Aisha daga ƙasan gadon inna. "bar ɓata bakinki,ba se ma kin rantse ba,dani yake maganar" Abubakar tsananin mamaki da takaici da baƙin ciki ne sukasa ya kasa magana,muryar inna ce ta katsemai tunani. "kayi nasarar ɓata ta,to wallahi ka rubuta ka ajiye baka da matar aure se ita,dan wallahi seka aureta,kanka ka ɓatawa"cewar inna batare da tunanin komai ba. "taya yarinyar da akawa fyaɗe zata samu wannan ƙawarin guiwar da Aisha keda shi a yanzu,inna kinsan fyaɗe kuwa?"cewar Abubakar cikin fushi. "taya zan sanshi nida baka taɓa ayko wanj cikin watsatstsun abokanka wani yayimin ba"cewar inna cikin fushi. "innalillahiwainnailaihirrajiun"itace kawai kalmar da Abubakar ke maimaitawa azuciya da bakinsa. Juyawa yayi yabar ɗakin,nashi dake soron ya nufa,kayanshi da yazo dasu ɗazu ya haɗa,ya ɗauka yabar gidan,ya koma inda ya fito,dan gaba ɗaya ji yake kamar ana watsa masa tafasasshen ruwan zafi yayin zamansa a gida ɗaya dasu innar. Inna ko ruwan zafi ta ɗorawa Aisha ta sirka mata takai mata toilet,harda na wankan tsarki a buta. Ba kunya tazo ta shiga tayi ta fito,se sannu innar ke mata, Inna uwani wacce lungun soron ke ta bayan lakinta,kuma windon ta ta lungun yake,tun farkon faruwar lamarin,ba abinda bata ji ba,sanin da tayine ko ta faɗi a banza ƙarshe ma inna ta liƙamata tace ita tai musu sharrine yasa tai shuru da bakinta. Amma ƙazafin da aka yiwa Abubakar tasha alwashin insha Allahu seta kuɓutar dashi koda me innar zata ce. Aisha bata ɗauki zancan auranta da abubakar da muhimmanci ba,sabida ita a duniya iro kawai takeso,kuma bata jin akwai namijin daze gamsar da ita kamar shi,dan haka shaaninta kawai taci gaba da sha. Rayuwa taci gaba da garawa,Aisha likkafa taci gaba,yanzu har gida take bin iron ya biya mata buƙata ta dawo gida,sosai yake dirzarta,son ranshi,amma bata gajiya sabida iron na mata yadda takeso. Yauma kamar kullum iron yazo taɗi gun Aishar,tabarma inna ta bata tace ta shimfiɗa musu dan tsayuwar bata da daɗi. Iro na hango Aisha ya ƙaraso da sauri ya rungumeta,boobs ɗinta ya shafo yana lashe leɓe yace "wallahi Aisha jiya daƙyar nai bacci,shaawarki gaba ɗaya ta dameni,ga wainnan ƴan tagwayen naki da basa barin bakina gane ɗanɗanon abinci"ya ƙarasa maganar yana ɗan matsa su,wata ƴar ƙara ta saki sannan ta zira hannunta cikin wandonshi ta kamo bananarsa tace tana shafota,"Ta iya ayki yadda ya kamata shiyasa kullum nakeson injita a marata ta cikani fam tana zubamin ruwan daɗi"ta ƙarasa maganar tana murza samanta. Sosai shaawar junansu ta taso musu me ƙarfi,ta barmar da inna ta bata ta nufi lungun soron ta shimfiɗa,musu,suka haye, A hankali iro ya fara shafe mata mara,wani daɗine ke ziyartar kan aisha daya sata take miƙa tana ɗan ware ƙafa,sannu a hankali,ya zira hannunsa cikin haq ɗinta yafara fingering ɗinta,ayko take ta fara ambaliya sabida daɗin da takeji,tuni ta fara kukan daɗi. Uwani kamar a mafarki ta fara jiyo sautin kukan na Aisha,a zabure ta miƙe ta ɗan leƙa,ta windo ilai kuwa ta lungun kukan ke fitowa,wanda kuma ko tantama batayi tasan zinar suke aykatawa. Ɗakin inna ta nufa,da sallamarta. Da faraa inna ta amsa mata,sannan uwani tace. "Yaya yau de ina da albishir me daɗin dazan baki,kuma nasan har tukuici se kinmin"cewar uwani tana murmushi. "ke uwani ki bari don Allah,niko wanne albishir ne wannan?"inna ta faɗi cikin dariya. "taso muje ki gani da idonki ay gani ya kori ji"uwani ta faɗi lokacin data kama hannun innar suka fito zuwa soron, Kai tsaye lungun tayi da ita,hankalin inna ne ya fara tashi,jin kamar muryar Aishanta.fitilar hannun uwani ta haskesu dashi,fes komai akan idon inna,Aisha tayi goho Iro na baza mata ayki. Tirƙashi. To mude je zuwan. *hanzarta ki biya kuɗinki 500 ne kacal,karki bari a baki labari page biyu ya rage na kyauta* Surbajo for life. 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *SHIMFIƊAR AURENA* 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *Zahra Surbajo* *Saura page ɗaya na kyauta ya ƙare,hanzarta ki turo kuɗinki 500 kacal domin kiji badaƙalar dake cikinsa,karki bari abaki labari,* *Zahra muhammed nasir 2084024749 UBA* *Aturo shaidar biyan tanan 07044600044* *14* Wata ƙara inna ta saki kana daga bisani ta yanke jiki ta faɗi ƙasa sumammiya,ƙarar da tayin ce ta dawo dasu Aisha hayyacinsu da gudu iro ya maida wandonsa ya fice daga gidan.ita kuma Aisha zani ta ɗaura tayi tsuru agurin. Uwani ce ta ruga cikin gidan ta ɗebo ruwa tazo ta yayyafawa innar,Ajiyar zuciya ta saki me ƙarfi sannan ta buɗe idonta. Wani marayan kuka ta saki me tsuma zuciya,inna Uwani ce ta kamata suka koma cikin gida. Ɗakinta ta kaita ta zaunar da ita kan tabarma,sannan tace"ba fa kuka zaki zauna yi ba,na farko godiya zakiwa Allah dayasa ma kika gano gaskiyar ɗanki,Aisha da iro sun jima suna tafka masha'arsu Abubakar ba ruwanshi amma idonki ya rufe kika ci mutuncinsa" "uwani Aisha yarinyace fa,wallahi nasan Asiri iron yay mata,inba haka ba bazata yarda dashi ba,nasan halinta sarai"cewar inna tana fyace majina. "ikon Allah wato ke har yanzu baki waazantu ba ko,to wallahi abinda Aisha zata aykata ko ke bazaki aykatashi ba dakike cewa yarinya ce,oho miki de kowa rai zewa daɗi barin me shine"inna uwani tace lokacin data miƙe ta fice daga ɗakin. Sum Sum Aisha tazo ta shige ɗakin inna,tana matso hawayen munafunci,tsugunnawa tayi agaban innar tana faɗin"innata kiyi haƙuri,Allah bansan lokacin daya kwanta dani ba" Kamota inna tayi cike da tausayawa tace"sharrin samarin zamani Aisha waye be sanshi ba,Allah ya saka miki maza je kiyi wanka kizo ki kwanta shi da Allah". Ayko hakan akayi taje tayo wankanta tazo ta haye kan gadon innar ta fara tuno irin aykin da iro yau yay mata,sosai ta samu gamsuwa a yau ɗin dan ita tariga tayi releasing shi iron ne beyi ba su inna suka ɓata wasan,take tausayinshi ya kamata,tasan yanzu yana can marar shi na masa ciwo,wasu siraran hawaye ne na tausayinshi suka zubo mata. Kasa bacci tayi dan haka fakar idon inna tayi ta ɗauki buta,kamar zata bayi tana fita daga ɗakin tayi waje abunta,cikin saurinta ta ƙarasa ɗakin iron,dan ba nisa daga gidansu. Tana kwankwasa ƙofar yace"waye?" "Aisha ce buɗe" Da hanzarinsa ya buɗe mata tana shiga ya maida ƙofar ya kulle,ya juyo gareta fuskarshi ɗauke da faraa yace "shiyasa nake yinki ƴanmatana,sabida nima kina yina"ya faɗi lokacin daya zame wandonsa. Kayan jikinta ta cire sannan ta tsuguna yasa mata kulkin nasa abaki ta fara tsotsa,shi kuma yana murza kan nipples ɗinta.cikin kwarewa Aisha ke tsotse kulkin na iro kamin daga bisani suka haye kan katifarsa,ta ware ƙafarta shi kuma ya nutsa ya fara ayki. Ya kwashi kusan Awa guda akanta kan yasamu buƙatarsa ta biya,ya sauka. Bata ɓata lokaci ba ta maida kayanta ta ruga zuwa gida.shiko iro baccin gajiya ne ya ɗaukeshi cikin kwanciyar hankali. Har ta koma gida inna batasan ta fito ba dan tana fita a ɗakin bacci ya ɗauki innar. Koda gari ya waye Aisha wankan tsarki tayi sannan tai sallah,bayan ta idar ne inna tace"Aisha dama jiya danacr kiyi wanka bakiyi ba kenan?" "inna mafarki nayi shine nayi wanka yanzun"ta faɗi cikin yanayin jin kunya. Tausayinta ne ya kama inna inda azuciyarta take faɗin"ƙiri ƙiri ya maidarmin da ƴa fitinanniya,dole Abubakar ya auri Aisha dan asirina ya rufu," ********** Abubakar ko acan gun aykinsa ya haɗu da maryam,sosai ya yaba da hankalinta da tarbiyyarta,soyayyacs sukeyi me tsabta,inda har gidan su maryam ɗin suka buƙaco ya turo iyayensa. lokacin dayazo ya samu inna akan maganar auran nasa tsalle tayi ta dire tace batasan zancenba ta ƙara da cewa"wallahi kayi kaɗan habubakar Aishan ubanka ka bari ya aureta to wlh bada yawuna ba" Ran Abubakar in yayi dubu ya ɓaci dan haka gidan ƙanin mahaifinshi kawu sani yaje ya sanar da shi komai,inda yace "ka kwantar da hankalinka aure de dama mune masu zuwa nema maka kuma zamuje insha Allahu nanda jibi,ka fita harkarta kar kaji komai"cewar kawu sani. Godiya yay masa sannan ya koma gida. Ko ta kan innar be sake biba,yaci gaba da soyewarsa da maryam ta waya tana kwantar masa da hankali. Kamar yadda kawu sani yace hakance ta faru sunje kaduna nemawa Abubakar Auran maryam,duk da kasancewarta ƴar masu kuɗi amma baa raina iyayen Abubakar ɗinba.komai cikin girma da mutuntawa akayishi.aka tsaida lokacin auren. ko kaɗan inna bata da labarin auran na Abubakar ɗin,dan ita burinta Aisha ze aura. Kwanci tashi asarar me rai,yau aka ɗaura auran Abubakar da Aisha,cikin jagorancin dangin mahaifinsa,se bayan an ɗauro auranne kawu sanj da kawu muntari,suka samu inna suka shaida mata komai,ayko tayi faɗan tayi faɗan har seda muryarta ta dashe sannan ta dena. Gidajen da ake ba police akaba Abubakar ɗaya ya tare da amaryarsa. Seda komai ya lafa kimanin watanni biyu da auran ya ɗauki maryam a sabuwar motarshi daya siya satin daya wuce suka nufi kaita dan suba inna haƙuri kuma suga juna ita da maryam. Muje zuwa. *hanzarta ki turo naki kuɗin kar ayi babu ke,shi wannan littafin daban yake da saura.500 ne kacan ba tsada* Surbajo for life. 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *SHIMFIƊAR AURENA* 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *Zahra Surbajo* *saura page uku na free ya ƙare,in kina buƙatar cigaban labarin ki turo kuɗin ki 500 asaki a group dan ki karanta hankali kwance,babu danasani a siyan wannan littafi zaki tabbatar da haka ne inkin siya kin karanta* *Zahra Muhammed Nasir 2084024749 UBA* *07044600044 A turo shaidar biyan tanan* *12* Sun jima a asibitin ana dubata,kamun asallamota su dawo gida, Tun a hanya hajiya ta lura mijin nata be tattare da walwalarsa,dan haka shiru tai masa suka iso gida tukunna. Masu ayki ne suka dafa abincin ranar inna da deeyanah suna ɗaki tasa ta agaba seta bata labarin mahaifiyarta,se kuka take mata kamar ranta ze fita. "deeyanah gaba ɗayanki yanzu shekarunki sha huɗu,ba abinda zaki fahimta inma na shaida mikin ki yi haƙuri ki dena kuka,na miki alƙawarin sanar dake komai,in kika ƙara girma"cewar inna tana share kwallah. "in kuma kika mutu kamin lokacinfa?kinga inna ni ba fa yarinya bace kamar yadda kike kallona abaya,ki faɗamin dan insan zaman da zanyi da kowa,amma in baki faɗi ba wlh duniya zan shiga"cewar deeyanah ba tare da tunanin komai ba. Inna share hawayenta tayi sannan ta gyara zamanta ta fara da bata labarin kamar haka. *WAIWAYEN BAYA* Su biyu mahaifinsu ya haifa inba da ƴar uwata saudatu,tun tasowarsu akwai soyayya me ƙarfi a tsakaninsu,har zuwa auran su. Dukansu a kaita sukayi Aure,inda inna a shekarar data yi Aure Allah ya bata ciki ta haifi Habubakar,saɓanin ita Saudatu ko ɓatan wata bata taɓa yi ba. Shekararta biyu da Aure mijinta ya auro uwani,a matsayin matarsa ta biyu. ShekararAbubakar biyar A duniya Allah yayiwa mahaifinsa rasuwa,da ike ya bar musu tarin gonaki da yawa yasa basu wahala ba bayan mutuwar tashi. Seda abubakar ya shekara goma a duniya Allah yaba yaya saudatu rabo ta haifi mahaifiyar deeyanah akasa mata sunan mahaifiyar su Aisha. Kwananta goma da haihuwa,jini ya ɓalle mata kan ayi wani yunƙuri Allah yay mata rasuwa,se ruƙon Aisha ya dawo hannun Inna. Madarar shanu ake bata,har ta girma tai wayo Allah ya rayata. Abubakar yana kulawa da Aisha a matsayinta na ƴar uwarsa kuma marainiya.sede tun da Aisha ta fara wayau suka fara samun saɓani,sabida inna gaba ɗaya ta sangartata bata kuma son laifinta,komai tayi daidaine,shi kuma Abubakar yana ƙoƙarin kwaɓarta amma inna ta taka masa burki hakan yasa ya dena shiga sabgarsu. Ana haka ne yasamu addmission a jamiar Ahmadu bello dake zaria.san haka zamansa ya koma zaria gaba ɗaya,sede in ansamu hutu ya zo gida ya koma. Mahaifin Aisha ma Allah yay masa rasuwa sakamakon hatsarin mota daya rutsa dashi. Aisha tun tasowarta idonta ke buɗe,bata kunya ko kaɗan gata da yawan son muamala da maza,ansha zuwa acewa inna taja mata kunne kar rayuwarta ta lalace amma sam so ya hana inna taga hakan. Abubakar ya kammala karatunshi cikin saa inda yashiga kuma ta horar da aykin ƴan sanda sabida dama shi burinsa kenan.besha wahala sosai ba yasamu aykin sabida dagewarsa. Bayan wasu shekaru,tuni Aisha ta girma ta zama budurwa,a wannan lokacin sosai take rashin kunyarta,musamman kyanta da yake ruɗata,sam taƙi karatu inna kuma bata takura mata ba. Yau Abubakar ya shirya zuwa ganin gida,dan haka siyayyar kayan abinci yayo musu,masu ɗan dama. Sosai Inna tai murna da zuwan nasa,se albarka take ta faman sa ma sa. Shigowar magriba yayi shiyasa da bega Aisha ba yace"Inna Aisha fa,naga bangantaba tunda na shigo?" Kame kame inna ta fara dan ita ko zaa kasheta batasan inda Aishan take ba.can de tai ta maza tace"ta tafi makaranta dare,se anjima zaa taso su" Sam be gamsu ba,amma seya ce mata"to badamuwa Allah dawo da ita lafiya"ya miƙe ya baro ɗakin. Duhu yayi kuma soron gidan akwai ɗan lungu agefensa,hakan yasa Abubakar yin amfani da fitilar hannunsa me shegen haske ya haska soron dan yaji daɗin tafiya. Sede fara tafiyarsa acikin soron keda wiya,yafara jiyo wani sauti daga cikin lungun soron wanda ko tantama baya yi muryar Aisha ce ya tsinkayo tana faɗin. "wash iro kayi da ƙarfi,da daɗi,ah ah ah wash wayyo daɗi,dage de iro" Hankalin Abubakar in yayi dubu ya tashi,sam baya cikin hankalinshi,me Aisha keyi acikin lungun da daren nan waye iro kuma meye me daɗin da yake mata,da wannan tarin tambayoyin ne ya nufi lungun dan ganin meke faruwa da ita. Waiyyazubillah,Haihuwar iwa da uba ya gansu,Aisha ta ɗage ƙafafu sama,Shi kuma iron yana tsugune yana zuba mata ayki,fitilar Abubakar ta hasko masa Haq ɗin Aishar da bananar Iron akan idonsa yake zarota,ya sake maida ta cikin haq ɗin Aishar,ita ko se kukan daɗi take. Hmmmmmm Muje zuwa. Surbajo for life. 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *SHIMFIƊAR AURENA* 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *Zahra Surbajo* *laifin daɗi ƙarewa😄,to na batin ya ƙare,meson jin cigaban labarin se ya turo 500 ɗinsa,acigaba da turo masa,wainda kuka nuna min soyayya kuka sayi littafinnan nagode sosai da ƙaunarku gareni,dan mesonka shi keson cigabanka,Allah ya ƙara muku buɗi na alkhairi nagode sosai* *zahra muhammed nasir 2084024749 UBA* *A turo shaidar biyan tanan 07044600044,* *15* Sosai inna tai mamakin ganin Abubakar da maryam,haka ta bisu da ido batace komai ba. Duƙawa maryam tayi har ƙasa,tace"inna barka da yammaci mun sameku lafiya?" "Da baku samemu lafiya ba da a asibiti kukeson ganinmu,munafuka algunguma,to wlh kinyi tsararo ki malkakemin ɗa,kuma Aisha ƴar uwarsa dole se ya aureta koda zaki haɗiyi zuciya ki mutu munafuka"cewar inna kamar zata zane maryam ɗin. Shuru maryam tayi ta tsugunar da kanta ƙasa tana share kwallar data taru a idonta. "inna baa haka maryam baƙuwarkice,yau ne karo na farko da kuka taɓa haɗuwa,koma menene inaga ay ba yau ya kamata ki nuna mata ba"cewar Abubakar fuska ɗauke da damuw. "Dalla yimin shuru saɓo tumaki ɓallo jaka,kai har kana da bakin magana,to wallahi ka fita idona habubakar dan kasan karon mu da kai"cewar inna cikin faɗa. Shuru duka sukayi,ganin bata da niyyar saukarsu ne yasa ya miƙe,yaja hannun maryam yakaita ɗakin inna uwani. Ayko cikin mutunci ta karɓi maryam ,fura ta miƙa mata,ta ɗebo mata ruwa me sanyi,ta bata,ayko maryam ta ɗan sake a ɗakin, Shiko Abubakar badan dare ya musu ba da ba abinda zesa yama kwana agarin da matarsa. A daddafe sukayi sati guda,koyaushe fitinar da inna zata ɓullo da ita daban,maryam har baƙi tayi ta rame sabida balain inna. Ranar da zasu tafi a ɗaki suka sameta da safe Abubakar yace"inna mu zamu wuce a yafemu,Allah kuma ƙaddara saduwarmu" "ku tafi ina,ay wallahi ƙafarka ƙafar Aisha da ita zaku tafi,kuje ta tayaku zama acan birnin"cewar inna cikin faɗa. Agigice Abubakar da maryam suka kalli juna,sannan Abubakar yace"inna ɗakinmu nacan fa ciki da falo ne taya zamu zauna da ƙatuwar budurwa kamar aisha a irin wannan ɗakin?"Abubakar ya faɗi kamar zeyi kuka. "ay ko ɗakin ciki ɗaya ne sekun tafi tare kaji de na faɗa maka" Haka sukayi tsuru har tagama haɗawa Aisha kayanta,itama Aishar bata son tafiyar dan tafison zamanta anan sabida iron ta,amma yata iya tunda yayan nata ya nuna beson zuwan da ita se taje taga uwar da suke ci ɗim acan. Haka inna ta tilasta Abubakar tafiya da Aisha badan ransa na soba,bare kuma maryam. Har suka iso kaduna ba wanda ya yi magana acikinsu, Haka maryam ta kaima Aisha kayanta cikin ɗakim baccin nasu, Haka rayuwarsu taci gaba da tafiya maryam sede tai musu shimfiɗa ita da Aishar a falo shi kuma Abubakar ya kwana a ɗakin. Ba wani Abu da yake shiga tsakaninsi sabida Aisha data kasa ta tsare,magana ta fatar baki bata haɗa Aisha da Abubakar,sede tayi da maryam shima sama sama. Yau Abubakar tun yana office sha'awar matarshi ta taso masa,tsawon watanni biyu kenan be kusanceta ba sabida Aisha,amma yai ji yake baze iya daurewa ba. Koda ya dawo da dare a idonsa maryam ta gano damuwarsa,to itama Allah yasani haƙuri kawai take bawai dan bata soba,haka de ta lallaɓashi har zuwa lokacin bacci,tai musu shimfiɗa da Aisha suka kwanta,seda dare yayi taga Aisha tayi bacci ta zame jikinta ta gudu gun mijinta. Ayko Abubakar sosai yaji daɗin zuwan nata,kamota yayi kamar mayunwacin zaki yafara kissing ɗinta itama tana maida masa martani. Sun lula duniyar maaurata wacce suka kwana biyu basu lula ba,kowa se kukan daɗi yake,kamar a mafarki Aisha take jiyo sautinsu,firgigit ta farka ta miƙe zaune.ko baa faɗa mata ba tasan me ke faruwa. Miƙewa tayi a hankali ta ƙarasa bakin windon ɗakin,dake buɗe kuma basu rufe baga haske acikin ɗakin shima basu kashe ba.maƙalewa tayi ta inda bazasu hangeta ba,ta fara leƙensu😭 Sosai shaawar Abubakar ta kamata me ƙarfi ganin yadda yake shiga maryam yake fita cike da kwarewa,take taji ta fara jiƙewa,tana kallonsu har su ka gama,kan kujera ta dawo ta kwanta ta fara biyawa kanta buƙata da hannunta.tana nishin daɗi. Koda gari ya waye bata nuna musu tah gansu ba illa iyaka wandon Abubakar da take kallo take lashe baki. Tundaga wannan rana kullum seta musu laɓe,batare da sun sani ba. Ana haka maryam ta koma makaranta,yazamana bata da isasshen lokacin da zata zauna agida sabida likitanci take karanta. Aisha kullum adduarta Allah yabata dama akan Abubakar,dan kullum shaawarshi kamar zata kasheta. Yau da wuri ya dawo gida,Aisha kawai agidan maryam vatanan,shima zuwa yayi yayi wanka ya fita. Be kulata ba yashige cikin ɗakin,kayan jikinshi ya rage sannan ya shiga toilet ɗin dake cikin ɗakin,ya gama wanka da saurinsa ya fito ɗaure da tawul,ya nufi gaban mudubi.dan ya kimtsa. Ga mamakinsa Aisha ce tsaye a bayansa ba kaya ajikinta,tana lashe baki,tana tura hannunta ɗaya gabanta ɗayan kuma tana murza boobs ɗinta,ba ƙarya duk inda akeson mace takai Aisha takai gurin kyau da diri ba wanda bata dashi. Kasa ɗauke idonshi yayi akanta,har ta ƙaraso jikinshi,haɗuwar ƙirjinsu guri guda ne ya haifar masa da wata irin kasala,a hankali take goga masa manyan boobs ɗinta dake tsaye kƴam a ƙirjinshi,tana lashe baki gamida fari da ido,tawul ɗin daya ɗaura ta kama a hankali ta warware,take abinda take ƙauna ya bayyana agareta,duk yadda Abubakar yaso yayi yunƙurin dakatar da ita ya kasa sosai shaiɗan yasa masa Shaawar abinda take masan,kulkin ta kamo cikin salon da dole seda yace "ah ah shhhhh" Maryam ce ta turo ƙofar ta shigo dan dawowarta daga makaranta kenan tana ta sallama afalo baa amsa ba yasa ta shige cikin ɗakin. Hmmmmmmm "turo taki 500 ɗin ayi dake,kar kiji wai wai,har yanzu fa ko labarin stars ɗin baa soma ba waywayen baya muke,shin ko kin manta da labarin prince hydar da tashi badaƙalar,duka 500 ɗinkice zata baki damar sanin sauran labarin" Muje zuwa Surbajo for life ************* Ai Hausa Novels **************** *************************⬆ ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ⬇ ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ⬆ **************************