Compilied By Abubakar Saleh AlQuyraemey Whatsapp Number 08138873799 Visit www.rumbunlabarai.com For More Complete Documents 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na~ 🍃 *Rukayya Ibrahim* 🍃 ✨✨Godiya ta tabbata ga Allah da ya nuna mini wannan Rana da Zan fara rubuta lbr na na farko cikin hukuncin ubangiji Allah ka bani ikon gamawa lfy 🤲✨ ✨Tsokaci wannan shine novel Ina na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error amini afuwa 👌 Free page Page 1️⃣ Kuka nake baji ba gani bakin ciki ke dankare a cikin zuciya ta Wanda in har banyi kuka ba bazanji saukin suba Wai ni ce amarya amaryan ma na makaho mara ido na daga lulubena kasanciwar dakin akwai wutan nepa glop ya haska Koh ido shiya bani Daman ganin daki dakin da Koh a mafarki van taba tunanin akwai ranan da Zan iyya rayuwa a irin Shiba Wai yau shi ake Kira da dakina na aure ni sumayya bansan lokacin da wani irin kuka ya sarkeni ba cikin takaici Mai tarin yawa ya Allah me naiwa Yan uwan mahaifina da suka sakamin da wannan rayuwa Mai na tsare musu da suke mini irin wannan muguwar tsana da hassada ya Allah duk wannan magana cikin kuka nake yinsu Tsaye yake yafi minutes 30 Amma ya kasa karasawa cikin kofar wani irin fargaba ne dankare a cikin ransa Wai yau shine da mata sukutum Koh a mafarki Bai taba tunanin aure ba kasan shiwarsa makaho maraya kuma Mara galihu sai abinda ya nemawa kansa Amma yau har Mata aka basa wance Bai taba tunanin samun taba amasayinsa na miskini Anya zata karbesa a matsayin miji zata yarda ta rayu dashi cikin akwai Koh babu wannan sune abinda suka tsaya masa a Rai yayi ta maza ya daga kafarsa hade da Bismillah Yana tafiya da sandar sa Yana ma kansa jagora zuwa filin kewayayeyyen kofar su Dan madaidaici ya juya ya tura kofar ya rufe harda lalubar sakata ya saka a sannu a hankali yake takawa har yaji ya taba Dan tudu kadan hakan ya nuna Masa ya iso dakalin kufar daki haurawa yayi sama Yana lalube tar yaji ya laluba ginin daki Yana bin ginin a hankali har yaji ya shafa window yanabi a hankali har yaji ya Kama labule mai masifan laushi da kamshi Wanda tunda yake a rayuwarsa Bai taba tunanin zai taba irinsaba kasan shewarsa mutunne shi Dan babu ruwana ba ya maula Koh bara baya neman taimakon kowa in dai na abin duniya ne sai dai na lalurarsa Wanda ya zamto Masa dole Da sallama a bakinsa ya daga labulen tare da jingina sandar sa a kofar dakin ta waji ciki ciki na amsa sallamar itama Dan ta zama dole na daga kaina ina kallon wanda Koh ba'a fadaba nasan shi ake nufi da ango makaho cikin wani irin takaici nake kallonsa don matashine Wanda bazai Gaza shikara 28 zuwa 30 ba laifi makanta da wahalan rayuwa su kadai za'a kira cikas a tare dashi don kyekkyewa ne na karshe dogo fari tas wanda wahala ta kodar da fatarsa Amma duk da haka fatar daga Gani zatayi matsifar laushi gemu mayalwaci sosai ga idanu masu girma da haske amma mara amfani a ganina bakinsa madaidaici Mai shegen kyau ga hanci har baka Mai yalwan gera don daga gani yanada yalwan gashi sosai sai gashin kansa Mai yawa amma rashin samun wadasheshen gera sai ya Yi wani iri Amma daga Gani gashine na Fulani asali duk da babu datti don fes Kan take kiransa na zaratan mazane masu Kiran karfin sosai na kurawa kayan jikinsa ido wani kudadden yadine na shadda wando da riga Mai guntun hannu Wanda suka Sha ruwa sosai wai su ya saka kenan ranan aurensa daga Gani sune na gindin akwatin sa Koh Bai fada ba ni Kam na raya a Raina kauda fuska nayi kamar bansan mutun ya shigo ba shi kuma cikin sanyin jiki da lalube yaji ya taka wani cafet Mai shigin laushi a cikin dakin duk da baya gani yasan tabbas Mai tsadane Koh me na dakin Nan don Bai mantaba dazun khadija take Masa gulma wai dakin Aunty'amarya Mai kyau da Kaya irin na gidan murtala Hon na unguwan su harma nata yafi nasu kyau tun daga lokacin jikinsa ya kara sanyi don ya tabbatar ba yar kananun mutane bane aka aura Masa a matsayinsa na makaho da lalube ya iso tsakiyar dakin Wanda yaji abubuwa Kamar filo a xuzxube a kasar cafet in dakin a hankali ya zauna tare da aje ledan dake hannun sa baka cikin zazzakar muryarsa Mai cike da Kamala ya gai Dani Koh juyuwa vanyiba don bana son ganin sama bare na sake Jin ya sake furta Ina wuni nayi wani dogon tsaki Jin haka yasa shi Jin wani mummunan faduwar gaba Amma baice kome ba yayi shuru munkai minti goma babu Mai shiwa kome sai Karan fanka Kiran OX babba wance Taki bawa dakin wani irin iska Mai sanyi sosai cikin rawar murya yace ga kaza nan kici sai muyi nafina mu gode wa Allah cikin zafin nama da takaici na hayyaya Koh Masa cikin fada Wanda duk Wanda ya sanni yasan ba halina bane Kuma Koh kyau Bata mini ba nace baza'a ci matseyacin kazar kaba kuma sallah kayi tayi har alfijir ya ketoh Bai shemin kome ba Amma kallo daya namar nasan maganar ta dake sa sosai a hankali ya laluba yafita waji yayi iyya nemar buta Koh Randa baiji inda aka aje ba saboda duk kayan kofar an sauya Mata zama kasanciwar sabbi aka kakkawo hakan yasa ya koma dakin a hankali da sallama Ina dai zaune Ina kalonsa yazo ya fara lalube a hankali ya daga labulen ya tura kofar ya rufe harda sakata cikin nutsuwa Naga ya fara lalube ban ankaraba naji ya lalubu ni cikin wani irin shock daga ni harshi muka Masa baya shikam harda buge kafar sa da katakun gado cikin i'ina nace meye haka cikin Dan sanyi jiki yace kiye hakuri ina neman gadone Zan kwanta cikin gadara nace wallahih bazan kwanta dakai gado daya ba gadai kujira a Chan jika kwanta a hankali ya fara lalube Ina dai zaune Ina kallonsa haka ya ringa zagaya dakin daker ya gane kujiran a hankali ya zauna ya cire rigansa ya kwanta a hankali cikin lumsheshen kujira na alfarma 3sita Nima kayan na cire tunda dai ba idone dashiba na ragi daga ni sai brz da siket nayi adu'a na kwanta a hankali nake sauke ajiyar zuciya har bacci ya dauke ni shikam ya kasa bacci sai tunane tunane yake yanason yin lafilfilu Amma ba Hali tunda baisa inda zai samu ruwa ba a kofar tasu Kuma baison zuwa rijiya a Darin nan gudun wani a cikin mutanen gidan su gansa su Masa abinda suka Saba rashin mutunci a sannu a sannu wani bacci Mai Dadi ya daukesa don a tsawon rayuwarsa Bai taba bacci ana zafi da fanka ba sai yau lol asuba da gari amarya da ango Free page ban yarda da a sayarmin da littafi ba😠pls Jinjina ga Yan Free books💃🏼💃🏼💃🏼 Mom Abba 🙄 Mrs jabeer😘 Sarah 😒 Zee black🤐 Nafisa voice note 😜 K🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃Rukayya Ibrahim🍃 ✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwa 👌 ✨ Bismillalahih rahamani Rahim✨ Free page *More comments* *More post* Page 2️⃣ Kiran farko akan kunnensa ya farka a hankali tare da addu'an tashi daga bacci kafarsa yazura ya sauke a kasan cafet da Bismillah ya mike saye ya fara laluben rigarsa daya cire jiya da dare da zai kwanta cikin hukuncin Allah ya samu rigan ya saka a hankali ya nufi kofa cikin lalube ya gane kofar ya bude ya fita ya tuna baisan inda buta take ba don baiga tsohon tasaba sake dawowa yayi a hankali yake lalube harya lalubo gado ba tare daya hauba yasa hannu yana laluben ta cikin sanyi Amma baijitaba a cikin ransa ya kitsima lallai wannan gadon babbane sosai Hawa yayi a hankali Yana lalube har yaji hannunsa ya taba wani abu Mai masifan laushi sosai Kamar fatar jinjira da sauri ya zari hannun cikin murya kasa kasa yake. Tattaba filon da yaji kanta akai inda Allah ya Sosa ma Mai nauyin vaccine ita da Allah Bata San ya taba Mata jiki ba cikin bacci take Jin ana bubuga Mata filo ido ta bude a hankali don baccin Bai ishitaba ta sauke idon ta a kansa Yana zaune kusa da ita cikin sauri ta Mike da masifa tace Kai lfy meya kahoka Kan gadona eye ,, cikin sanyi Wanda na Lura halittansane yace Daman buta nake so ki nuna mini na ibo Mana ruwa asuba tayi wani haushine ya kamani wannan miji ne Koh rainon sa zanyi Amma saboda albarkacin sallah yasa nace toh muje na dauki rigana nasa na fita a dakin nayi wajinda aka kewayemin da fallange Dan madaidaici Wai kitchen na shiga kayan kitchen ne na alfarma kome yaji yar an rasa wajin sawa an koma da saura Kamar yanda aka maida kujiruna da wasu Abubuwan kayan dakina masu yawan gaske na shiga na kunce butan a cikin kwalinsa na karfine cikin kayan da aka saimin da na roba na hada biyu na fitoh na samesa a saye yana jirana Mika Masa nayi cikin kaushin murya nace randuna na babu ruwa cikin lalube ya karbi butan hade da furta bara na ibo a rijiya kala bance Masa ba ya fita sai gasa ya dawo da ruwa a buta daya ya shigo ya ajimin ya koma ya dauko dayan ni kuma tuni na idar da alwala harna shiga daki na bude akwatina na dauki hijab da sallaya na shinfida na tada sallah Alwala yayi ya tafi masallaci da sandar jagoransa Ina idar da sallah nayi lazimi har lokacin Bai dawo ba na daga idanu na na kalli agogon bango Wanda aka likawa bangon dakin karfi Shida saura naja dogon tsaki Dan a lokacin aka dauke nepa ni kuma bana iyya bacci ba AC Koh fanka Sam nasan Koh na kwanta bazan iyya bacci ba Ina zaune har karfi Shida lokacin gari ya waye dakin yayi haske a hankali nake bin dakin da kallo dakine madaidaici sai gadona Wanda yaci Rabin dakin da kujira dogo guda daya don sauran babu wajin zama Mai dasu akayi plasma TV ta gefin gadon aka makala don ba fili da waddrop ta daya gefen sai kafet da su kushin da aka saka a tsakiyar dakin da karamin freezer ata bakin kofa kayan sawana makil a akwati set dake gefen Kan gado sai fankan kasa sune suka samu wajin zama a dakin a hankali nakai hannu na dauki jakana na bude na dau waya ta Ina dannawa tunda babu nepa bare na kunna TV an hadamin kayan kallo harda Star Time Ina da sallama naji ya shigo dakin na amsa ya laluba kujira ya zauna cikin sanyi yace ina kwana kamar bazan amsa ba na amsa da lfy klau cikin sanyi yace me zakici na sai Miki cikin mamaki da al'ajabi Wai sayo abinci Ina amarya akawoni cikin gidansu Amma arasa Mai bani abinci sai ya siyo duk da ban karewa gidan kallo ba nasan babbane tun jiya da dare maganar sa ce ta dawo Tani daga duniyar tunani Dan wake Koh alele Koh kosai za'a karba miki cikin mamaki nake kallonsa sai Kuma naji ya bani tausayi tun jiya yake kokari yaga ya kyautata mini yasa cikin sanyi nace Masa Gaisuwa ga members😜 🪀My WhatsApp number 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 * ~ Na ~ 🍃 *Rukayya Ibrahim* 🍃 ✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwa 👌 Free book 🤧 Page 3️⃣ "Basai ka saya abinci ba, akwai kayan abinci, ruwa nake so, asaya da bread sai kayan meya" cike da kuzari ganin na masa magana, a taushashe sabanin jiya, ya Mike ya fita, Yana fita, ya laluba aljuhunsa Aiko Allah yasa,Yana da gudan dari biyu da dari, na cinikin mangoron sa na jiya, da safe da Yan change ya hada ya fita tsakar gidan, sai ji yayi an saka ihu da shewa, daga mata har matasan samarin, ana ga ango ga ango, wanda Koh tantama babu,duk wanda yaji yasan na raini wayo ne, da shikiyanci kasanciwar ya Saba da irin wannan tozarci na Yan gidansu, sai abin Bai damunsa Sam, wuce warsa waji yayi, ya fita kofar gida, dayake bakin titi ne gidan nasu, yasa shi sayuwa a bakin kofar gidan, Bai jima ba dayake safiya ne, yaji Mai ruwa na bugawa kiransa yayi duka ya saya, ya hadasa da yaron makwantansu, ya nuna Masa kofar amarya, shi kuma ya shiga shagon haladu, sayan bread na dari Mai kyau ya hada da Lipton na goma, da sugan hamsin, ya karasa table in gwanja yasai kayan meya ya hada ya kamo hanyan gida , Mai ruwa ya shigo da yaro "na tashi na fitar da randana, na roba Mai girma sosai irin Mai cin jarka Sha biyar innan, Mai ruwa na Gama juyewa, Yana shigowa ya biya kudin ruwan, ya ajimin laidan cefenen "dauka nayi nawuce kitchen", shi kuma ya fita, "kitchen na shiga kome an jiramin kuma ba laifi kitchen din ya dauki Rabin kayan da akai mini, gas na kunna na dauko dankalin turawa na fere na daura a tukunya, kwai na fasa na zuba kayan hadi na aji a gefe, kettle na ruwan zafi, naso daurawa Amma ba nepa dole na daura bojuwa, ( tukunya) a dayan Kan gas in na zuba kayan kamshi da Lipton na rufe, naji" buruntun bude kofa lekawa nayi nagansa rike da Ghana must go na kaya madaidaici na kayansa ya shigo da lalube' ya fada cikin dakin yaje ya aje sai gasa ya fitoh yana lalube cikin Dan tausayin sa, wanda bansan Ina dashi ba, "nace maikake nema ne" ? cikin sanyin halinsa yace bokati, "na mike na dauko masa" sabon boket, da kwandon soso, na kayana da soso sabo da sabulu, na wanka Mai sada na akwatina," hada a kwandon na Mika Masa" ya karba cikin lalube ya lalubi kwandon yace La!! ai Ina da soso harda sabulu barshi kawai "cikin Jin haushi nace na sani ai na baka kayi dasu" Bai Musa ba ya karba yaje ya zuba ruwa a bokatin ya cika, da lalube ya shiga ban daki, ya ajiye ya dawo ya lalubi inda ya aji butar da yayi alwalan, asuba ya dauka ya cika ruwa ya wuce bayin, "Cikin kankanin lokaci na hada breakfast, Mai kyau na soyayyen dankali da kwai tie ga bread a gefe naji daki na dauko kazar dana Gama zagi jiya nazo na juye a kwando na makala gudun karya rube, da rana nayi meya dashi' na fada dakin na kakkabe gado na jira filon Kan kujira, na share dakin na fesa turarukan daki, na fitoh na share baranda na hada da kasar kofar duk da ban taba share kasa ba, sai dai tayis Koh seminti haka na lallaba na share, Ina gamawa" Yana fituwa a wanka daure da zani, tsoho a kwankwaso hannunsa dauke da kayan sa daya cire, a boket Yana lalube ya dibe ruwa ya zuba a boket in, ya jika kayan ya mayar bayan gida ya aje, ya fito Ya shiga dakin, "na ibi ruwa Nima na shiga Wanka da soso da towel na Ina fituwa na fada dakin, ban Damu ba, tunda ba kallo yakeye ba" "Ina shiga na gansa zaune a kasa ya chanja Kaya zuwa jallabiya fari duk da yasha ruwa jallabiyan, Amma a wanke tas, "na shiga na bude akwatina na dauki Kaya, rigane dogo na material Mai kyau da tsantse, NASA na hada da hula fari na fita waji na shanya towel in a igiya da kayan da na cire samun kar suye tsami, na shiga kitchen na dauko abincin na fada daki da plet na zuzzuba karyawan na Mika Masa" "na ibi nawa nayi Bismillah Muka fara ci" babu Mai magana a tsakanin mu tunda yasa, abincin nan a bakinsa yake godiya wa Allah a zuciyan sa, daya mallaka Masa sumayya amasayin Mata, tunda zata iyya dafa Abu ta basa yaci Wanda rabon da adafa abasa tun kafun ummarsa tabar duniya shiyake sayawa kansa, abinci she yake nemawa kansa, "muna tsaka dacin abinci naji an banko kofar shashin mu an shigo, ba sallama aka daga Mana labule dukkan mu dagowa mukayi don ganin wani ishanshen ne, haka sabanin shida Banga mamaki a fuskar Saba sai dai alamu sun nuna baiji Dadin hakan ba, ya kurawa kofar ido Kamar Mai kallo yanda nayi sakake Ina kallon kofa cike da mamaki....... 💃🏼💃🏼Yan free books💃🏼💃🏼Naga comments naku naji dadin karfafa mini gwuwa Mom Abba Umme Nafisa voice note Dr humaira Da sauran su 🪀My WhatsApp number 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 * ~ Na ~ 🍃 *Rukayya Ibrahim* 🍃 ✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwa 👌 Free book🤧 Page 4️⃣ Budurwa ce zata Kai kusan sa'ata cikin gadara da taunan cingum. tace amarsu ta ango karyawa ake ne? gashi nazo kallon dakin Amarya ***kala bance Mata ba shema duk da baiji Dadin hakan ba Amma shuru yayi ba abinda yace ,haushi sosai naji Amma naja bakina nayi shuru don banda lokacin wannan Mai zubin karuwai, abinci muka cigaba da ciii ba Wanda ya kulata cikin mu biyun, cikin bacin Rai tayi tsaki ta juya tafita. Koh ido ba mudu bane yasan kema ni ba sa'ar yinta bane kallo daya tamin ta gane ni ba kallan raini wayo bane Kamar yanda suka Saba Raina Masa, **mamaki ne ya kamani, lallai sai nayi da gaske Zan iyya zama da Yan gidan nan. don dagani Basu da mutunci wallahi😒 Muna Gama karyawa ya mike ya dauki kwanukan da mukaci abinci harda nawa ha Hada ya fita dasu a kitchen ya Ajjye, Dawowa cikin dakin Yayi cikin sanyin halinsa ya bude baki a Hankali ya furta Zan fita wajin sana'a Koh akwai abinda Zaki bukata,? Kamar bazan tanka ba Amma na daure nace "babu"Koh zaka dawo kaci abincin Rana"? cikin natsuwa yace min ah..ah Zan saya naci sai yamma Zan dawo, "har Ina ne wajen sana'ar taka" ? Cikin D'anjin Dadi jin Ina kulasa yace bakin titin kofar gida ta gefen shagonan, su haladu ** Ni Kuma Ina nasan wani Haladu bare shagonsa😏a Raina nake fada Amma a zahiri cewa nayi "toh Inna Gama ka tura yaro yazo ya karba maka abincin" da zumudi yace toh ......toh Zan turo bayan azahar. Ya sa Kai ya fita ***Daki na koma na bubbude akwatunan Kayana na bubbude kayan Ina jirawa a whtdp wasu a dressed mirror kayane na alfarma atamfufe dinkaku da Wanda ba dinkaku ba takalma da jakunKuna gyeleluka abaya material duka na shirya Kayana a nitse make-up kit na aje sa a drowarn mirror mayuka da turaruka na jirasu saman mirror. sauran kayan da suka rage na mai dasu cikin akwaiti ba wajen jirawa duk ya cika ba fili na rufe na Mai dasu saman whdrp ", yarane suka fara shigowa ba sallama ba gaisuwa suka shigo mini daki harda Yan matan gidan suka cika dakin Wai sunzo kallon daki ga makwanta nata shigowa da sunan ganin daki Koh gulma ne oho, ana haka aka kawo NEPA Daya Daga cikin Yan matan ta Mike ta kunna TV haka aka sake cika Wai ana kallo har baranda nidai abin daya isheni kawai na dauki wayata na fita waje, " kitchen na wuce kazar jiya nake son hada miya dashi Amma kayan miyar jiya tayi kadan dole na shiga daki jakana na hannu mai kyau na dauka na fito waje budewa nayi na dau gudan dubu daya na aiki yaro a cikin Yan kallo kayan Miya Mai Dan yawa na Kara Masa da dubu biyu ya sayo harda kaza, don so nake na Kara na jiya bazai isaba ga yara a kofar. Yaron na dawo mini da kayan Miya na fara aiki ba wance ta taimake ni Koh da jijjigen kayan Miya ne shinkafa da miya na dafa Ina Gamawa na zuba a sabon kula Mai kyau na saka a basket da shukali da plt, na Koma dakin na bude freezer na dauki ruwan gora, na hada Masa a basket in na Ajiye, d'aid'ai yaron da Zai aika ya shigo na basa. sauran abincin na zuba a babban faranti na hadawa yaran daban na sawa manyan daban daya ke nayi abincin da yawa sosai, Mika musu nayi ba kunya suka amsa gabaki daya Koh kwanukan Basu daga ba suka barsa a Inda suka ci sun batamin daki da datti sosai, na ibi nawa na zauna a baranda kan darduma nayi Bismillah na fara ci ban tashi agunba saiga wani yaro ya shigo da sallama amsa Masa nayi, "waalaikumu salam"ya gaidani, "amsa wa nayi don naji dadin gaidani da yayi kaf yaran gidan da suka shigo ba Wanda ya gaidani Koh sallama babu, Wai inji inji MAKAHO Mai mangoro aban abinci, Wani Takaici ne ya kamani Wai sunan sama da MAKAHO ake kira "shap wallahih bazaiyu ba watoh nima haka za'a na kwatantani da MATAR MAKAHO Ina bazaiyu ba" duk Araina nake zancen nan. Mikewa nayi na dauko masa basket in, basa nayi ya wuce azahar yayi Amma kaf yaran gidan ba Wanda yayi Haraman Sallah Nima bance musu kome ba, na mike na dauro Alwala na koma dakin Hijab na dauka na fitoh waje nayi sallah na kwanta a sallayan Ina Danna waya, Mutane Basu bar mini kofa ba har na Gama Tuwon dare na kwashe sukaci tukun suka fara watsewa daya bayan daya. Har suka watse suna fita na share dakina na goge, dakin Yayi kaca kaca sosai chanja zanin gado nayi yara sun kakama mini na jikin gadon da hannu yayi daud'a na fesa Turarukan daki na wanke dakalin kafun naji kofar yamin dama daman shekan iska Mai Dadi, wanka na shiga a gurguje nayi alwala na fada dakin na shirya nazo daukan turare Naga an min satan Mai Harda turare, Raina ya kara baci don na tsani mutun ya dauki abuna ban basa ba, na kudurta Araina bazan sake Basu wannan fuskan ba tunda basuda mutunci gobe ba shegen da zai shigarmin kofa😂( tab kofarki Koh na makaho) Kaya nasa na jona wayata a cherge da laptop duka, **na koma gefen gado na zauna tunani na shiga yi lallai rayuwa ba tabbas yau Koh mutun daya daga cikin dangina Koh kawaye, babu Wanda yazo. watoh tunda talaka na aura kenan,? alhalin duk wance tayi aure zuwa ake washe gari kallon gida da masu sallaman Amarya, a ranan. Amma ni ba Wanda yazo kallon daki ma bare sallama uhmm, Karfe biyar da rabi MAKAHO ya dawo gida da kwandon abinci a hannu sai sandar jagoransa da lalube yakai kulan kitchen ya aje, wanka yayi ya fada dakin Yana shiga na fita na basa waje ya shirya, Tana fita ya lalube Ghana must go insa ya dauki Kaya yasa ya fitoh waji lalube yayi ya dauki buta ya Kama alwala. ya wuce masallaci,don har an Tada sallah, **lokacin Nima sallah na Tayar ,Bai dawo ba sai da ya hada da isha'i Tukun ya dawo, *** abinci na zuba Masa ***na Koma Kan gado na zauna TV na kunna na kamo Tashar Arewa 24 Ana cikin Shirin kaddaran rayuwa. bayan ya Gama cin abincin, kwanukan ya dauka yakai kitchen hade da wanke hannu ya Sha ruwan Randa, ya shigo dakin, cikin lalube ya lalubo kujira ya zauna a hankali cikin magana Mai sanyi yace nagode da abinci yayi Dadi sosai Allah ya biya." Amin" nace hankalina nakan TV, jawo laidar da ya shigo da ita baka yayi ya fitar da sabulu da omo. sai wata laidar mangoron yako, ya Miko mini ta inda yake tsammanin saitin nake, Cikin sanyin jiki da zullumin zata Amsa kuwa? Yace ga mangoro ba yawa ***ban gwatselesa ba na karba na mike naje na bude firij na aje. fita waje yayi, ya hada kayansa daya jika a ban daki da safe da Wanda ya cire dazun ya wanke ya shanya ya sake dawowa dakin yayi cikin magana d'ari..d'ari yace Koh Zaki kawo kayanki Mai datti na wanke miki, ***cikin mamaki nake kallonsa Wai ya wanke mini Kaya, lallai da wani idon Zan basa Kayana na fada a Raina, Amma a zahiri nace "ah ah na gode Zan bada wanki inya taru" baice kome ba ya lalube kujira ya zauna kawai yayi shuru ya kurawa TV da yake aiki ido kamar Mai kallo, ***abin har yaso bani dariya Amma na maze. muna zaune har goma, bacci na faraji, mikewa nayi na chanja kaya zuwa na bacci, kashe TV da glop nayi na Kara gudun fanka zuwa 3 Addu'a bacci nayi na shafa na kwanta, a hankali ya Tashi yaje ya rufe kofar duk Ina jinsa dawowa yayi kwanta, kwanta a kujira addu'an bacci yayi shima ya shafa. **Nima gyara kwanciya nayi, Tun daga jiya zuwa yau, a Takure nake Sam ban Saba kwana da namiji a daki ba, Amma ya zanye, dole na kwanta tunda daki D'aya ne bare na koresa falo. Misalin karfe biyu na dare ya farka......... My WhatsApp number 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 * ~ Na ~ 🍃 *Rukayya Ibrahim* 🍃 ✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwa 👌 Free book🤧 Page 5️⃣ Dan a irin lokacin da yake tashi sallolin dare, mikewa yayi ya riga ya gane ma'ajiyin Randa da buta fita yayi a dakin alwala ya daura ya dawo dakin,ya tada sallah sai uku ya koma ya kwanta, Kiran farko na asuba ya farkar dashi, Addu'a tashi daga bacci yaye. A hankali ya sauka a kujira cikin sanyi ya lalube gadon ya tsaya a bakin don bazai iyya Hawa ba kar a maimaita irin na jiya a hankali yake kiranta **sumayya!! sumayya!! * **A hankali na bude idanuna cikin bacci nace "naji habba" baice mini kome ba ya daga kafarsa a hankali da lalube ya bude dakin ya fita **Niko waya na laluba a gefen filo don dakin ba haske na kunna hasken ya haska dakin sauka nayi Nima nayi waje don d'auro Alwala, **fitana yayi daidai da kammala tasa alwalan mikewa yayi Yana laluben sandanrsa,Harna kammala alwala Bai gane sandar ba. *Ina kammala alwala na shiga daki daukar wayata nayi na fitoh na haska kofar aiko Naga sandar Ashe faduwa yayi a kasa, dauka nayi na zungure sa da sandar a hannu * da sauri ya mika hannunsa ya amsa cikin sanyi sanyin sa yace nagode, * batare da nayi magana ba don takaice waini sumy nice yau da miji MAKAHO shap wannan ai abin kunya ne ma Wanda ya sanni ya gansa a matsayin mijina, Tabbas nayi Wasa da Damata a rayuwa, shiyasa Allah ya jarabce ni a lokacin da ban taba tsammani Koh tunanin hakan ba, **Da sauri nayi istigifari na kauda tunanin a Raina * Koh amsa Masa banyi ba nayi shege daki na tada sallah, Ina idarwa Qur'an na dauka cikin jakansa Mai kyau na bude, *nayi azkar in safiya, dana sabayi kullun na mike nabi lfyn gado bacci ya dauke ni, sai shidda da rabi ya shigo dakin da sallama hannunsa rike da bakar laida na kayan shaye da kayan miya Jin ba'a amsa ba ya lalube kujira ya zauna, numfashi Daya ji kasa kasa hakan ya tabbatar Masa ta koma bacci a hankali ya mike,waje ya fita da lalube ya Isa kitchen aje laidan yayi , shanyar kayansa ya dauko a igiya ya nade ya shigo dakin ya lalube Ghana must go in sa Daya aje a lungun kujira da firij yasaka kayan,ya dawo Kan kujiran ya kwanta a hankali wani irin bacci Mai Dadi ya sauke sa, **Ban tashi ba, sai Takwas na safe shima ihu da ashariya na dandazon mutanen gidan Wanda Koh tantama banayi tambe ake, shiya farkar Dani,mikewa nayi sanye da kayan baccina Wanda na saka jiya da dare riga da wando Mai taushi sosai sai hulan bacci d'uka farare ne tas. * da sauri na dirko daga Kan gado nafitoh dakin naje na rufe kofar shashen mu don nasha Alwashe yau bamai shigarmin kofa kallo Koh ganin daki bare naji yau da tambe aka tashi* 😂 (Anya ba tsoro ba kuwa?) *Kitchen na wuce, ganin laidan kayan Miya a kasa, * dauka nayi na bude kayan miyane su tarugu albasa da tattasai sai dayan kayan shaye ne yau harda Madara, na laida da bouviter, bread, sugar, da Lipton, ruwa na zuba a kettle nasa Lipton, don yau muntashi da NEPA na jona a socket bude caton indomie, na kayan garana laida biyu na dauka manya shap shap na daura na dau kwai na soya cikin 40 minutes na Gama hada breakfast na Kama shara, ✨ (tabbas aiki a wajen mace ribace babba duk kudin gidan ku duk mulki Koh gata ilimi da kyau in har mace Bata iyya girki ba gtoh Bata cika macen da za'a kira Tauraruwa ba Yan Mata a Kara bada himma karki xamantu baki da aiki sai adafa a baki kici ki kwanta kina Danna waya.koh makaranta kike zuwa at lest ki ware wasu lokutan a Rana kina Taya ma'aifiyarki, aikin da kika tsana kina ga ana matsamiki ana bautar dake wallahih ribarta na zuwa don bakisan inda Allah zai kaiki ba)✨ *shawarace* **Tun sa'ilin da aka fara Yar Hali watoh dambe, a tsakar gidansu ya farka Amma Bai Mike ba har **fitanta da rufe kofar duk akan kunnensa duk yanaji Yana kwance , a hankali ya mike ya fitoh cikin sanyin halinsa da nutsuwa ya bude baki yake gai Dani, **shuru na Masa naki amsawa * baiyi fushi ba ya kara tambaya ta, Koh Zan Kama Miki wani aiki ? Abin nasa harda rainin wayyo kenan, Wai ya kamamin aiki? da wani idon Amma saina maze nace "wanke-wanke nakeso kamin" ba musu ya lalube sandarsa da takalminsa shinyayye ya saka Da lalube harya lalube boket, ya dauka ruwa ya Iba a Randa ya aje a gefe da laluba har yakai cikin kitchen nidai Ina binsa da ido kawai, ganin garajen sa, cikin tsawa nace "kaiiii aje kulanan abincine a ciki" " tsaya na nuna maka kwanukan da zaka wanke" " Wai baka ganewa ne? Hala banda rashin gani ma? harda rashin basira? zaka dauki kula kaje da nauye basiranka bazai baka abincine a ciki ba zaka zungumu?? Kala baice mini ba ya ajiye kawai ya jingina a gefen kitchen ya tsaya, Zuwa nayi na dauki kwanukan nakai masa gefe na hada ruwan kunfa na aje kwando da kujira na tsaya agefe cikin masifa masifa nace gashinan Bismillah sai kazo ka wanke jiki a sanyaye yazo da lalube harya zauna Niko Ina saye a gefe ina ganin ikon Allah wanke kwanuka yake Kamar Mai ido tas suke fita Yana kifewa Kai Koh Mai ido albarka, mamakine y kamani Amma ban nuna Masa ba, **Shara na kammala na gera daki na na jona kask'wan lantarki na zuba Turarukan wuta a dakin fita nayi Naga har yanzun Yana Kan wanke wanke Kwanukan akwai Dan yawa na abincin jiya da yara sukaci ban samu na wanke ba Harda na dare, *Wanka na shiga Ina fitowa na tarar ya kammala Yana zaune a kujiran tsugunne, " Koh Mai ban shafa ba na zura kaya atamfa super Mai kyau siket da riga Mai k'wala da hannun roba* dinkin zamani *abinci na zuba ina ci daidai lokacin shima wankan ya shiga yana fitowa wanka ya shigo dakin, Alhamdulillah Koh ba kome na Lura Yana da tsafta duk da bana rayawa a Raina Koh da Wasa zanyi rayuwar aure dashi Mai tsayi dole ya sake ni yaje ya nemi miskiniya irinsa Amma kafun lokacin bazan cutu da wari ba tunda Yana wanka ( lol😅uhmm muje zuwa zakiyi bayani ) *Fita nayi na basa waje* Kaya ya saka wani jimemmen t-shirt da wando jeas duk da tsofene Amma sunyi Masa kyau sosai ya laluben kujira yayi ya zauna, Ina waje ban kulasa ba naci gaba da cin abinci na kammala zamana nayi A wajen naki basa abinci shi kuma Bai tambaye ni ba Danna waya nayitaye sai kusan goma na safe na iba Masa a plt da shaye a Kofi na shiga dakin na aje Masa na koma Kan gado na kwanta, ya jawo plt in yayi Bismillah ya fara ci Yana tsaka dacin abinci muka ji bugun kofar shashen mu mikewa yayi zaiji ya bude na dirko daka kan gado cikin fada fada nace "bazafa ka bude kofar nan ba don yau bamai shiga kofar nan ehen kaji na gaya maka don Naga alama Yan gidanku basuje islamiyya ba" Baice mini kome ba ya koma ya zauna Jin Mai bugun yaki barin kunne na ya huta, hijab na dauka na zura na fita ,don gani wani isheshshine, Bude kofar naye idona y sauka akan wata yarinya kyakkyawa sosai farace Mai Kama da MAKAHO sak banbancin ita mace Mai karancin shikaru 18 zuwa 19 she Kuma namiji ne sanye take cikin riga na kodadd'in shadda sai hijab wuyan duk ya sabule gashinta har ya leko ta gaban goshi, *Tunda aka kawoni wanna kaddararerren gida ban ganta cikin yaran gidan da suka zo kofana ba, Aunty Ina kwana tace hanya na Bata cikin dakewa nace "lafiya shigo" Shigowa tayi daidai lokacin shi kuma ya fitoh cikin dakin murmushe dauke a fuskarsa itama murmushin take da sauri tazo ta amshi kwanukan hannunsa hade da gaishe sa ya amsa,Yana tambayar ta ya su Goggo Aminar, Ta basa amsa Tace in nazo nace tana gaida Amarya,ta fada tana kallona Amsa Mata nayi ba yabo ba fallasa "Ina amsawa" Fita zaiyi hade da tambaya ta Koh akwai abinda za'a saya Kai tsaye nace "babu "sa Kai yaye ya fita hade da cewa Khadija in Zaki tafi ki biya ta guna, da toh ta amsa Masa Nidai daki na wuce naje na kwanta sai da Naji fitarsa tukum na kwala Mata Kira " Khadija shigo daki Mana kina tsaye a waje" don haka kawai naji yarinyan ta kwantamin sosai a Rai duk da bansan Alakarsu ba amma nasan akwai alakar jini a tsakanin su, Da sallama ta shigo dakin na amsa Mata tana kukarin zama a kasa nayi saurin cewa tahau kujira Amma Taki da kerta zauna, firij na bude na dauko mangoron jiya da yayanta ya kawo na hada Mata da drinks harda ruwa na aje mata hira take mini Kamar na saba da ganin akwai ta da surutu sosai tun Ina amsa Mata har bacci ya dauke ni, Ban farka ba sai 1:30 na Rana shima kiraye kirayen sallane ya tashe ni sai a lokacin na tuna Ashe fa Ina da bakuwa, A hankali na sauke idona akan kujiran da na barta akai da mamaki sai Naga wayam ba kome, Sauka nayi a gadon na fita a dakin cike da mamaki nake bin kofar da kallo har idona ya sauka akanta cikin sabon mamaki ganin ta a cikin.................... Good morning fan's 🌥️ An gaishiku Yan free books💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼 🍀MATAR MAKAHO FAN'S GROUP 🍀 Naga comments naku naji Dadi Kuma Ya karfafa mini gwwa 🪀My WhatsApp number 08084453785080844537850808445378508084453785awata ta kaina Salma Adam Allah ya bar 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 * ~ Na ~ 🍃 *Rukayya Ibrahim* 🍃 ✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwa 👌 Free book🤧 😒 *More comments* 😏 *More post* Page6️⃣ shanyan Kayana da sukaye datti harda zanin gado Ashanye a igiya an wanke harda kayan yayan Khadija (MAKAHO) Khadija na gani cikin kitchen, tana aiki, * a Hankali na daga kafata na Isa kitchen in, "Khadija kece akitchen?" da murmushi a fuskarta ta amsa mini da Aunty, Naga har Rana baki tashiba shine na daura Miki Abinci shinkafa da wake miyane ban Gama ba ya kusa, "Kayan nan fa waya wanke ?" Nice Aunty ta bani Amsa, *wallahih in banji Dadi ba nayi karya sosai naji yarinyar ta shiga Raina sosai da fara'a nace Mata" gaskiya Khadija nagode wallahih Amma aikin ya Miki yawa da baki wanke Kaya ba, La Aunty babu yawa fa kayan, ta bani Amsa "Khadija tashi muyi Sallah tukum tunda miyar kin daura a wuta" ..Toh Aunty Sallah mukayi, na sauke abinci na raba na zuba Masa na hada Kamar jiya, na Bata ta Kai Masa " in kin Kaifa ki dawo Khadija" da toh ta amsa mini, Tana dawowa na iba Mana nida ita a plt daya, Muka zauna a waje munaci muna Hira cikin hiran nema nakejin ainahin sunan sa a bakin Khadija Ashe *Al'ameen* ne sunan sa saboda larurar da Allah ya daura Masa shine aka batar da sunan zuwa MAKAHO Kai duniya, "Tambayar ta nayi a gidan nan take"? Ah ah Aunty ni agidan Goggon mu nake , "Har wani unguwa ne haka"? Ta bayan layin nan ne tsakanin mu ba nisa sosai Aunty, Sosai muke Hira Kamar mun Dade da sabawa, "Aikin dare na hanatayi nace ta Huta ni nashiga kitchen nakama girki* kin zama tayi dutsen guga ta dauka ta fara gogan kayan da ta shanya duk yanda na hanata sai da ta gogi, 4:10 na yamma tace min zata tafi hanata, nayi sai da na Gama girkin abinci na sata tayi wanka Kayana na Bata cikin dogayen rigunana nakanti na Bata daya Dayake tana da tsawo sosai ya zauna Mata na hada Mata da gyele medium size kalar fulawar rigan, Sosai kayan ya karbe ta na hada Mata da Mai turare harda powder,man baki, da Jan baki biyu, maskaras da sauran kayayakina da basa cikin set na make-up kit Ina na babata daker ta karba sai godiya take min, *nayi nayi taci abinci dare Amma Taki,zuba Mata nayi a kula Taki karba sai da nace Goggo zata kaiwa kafun ta Amsa ta wace, Fitar Khadija sai da ta biya wajin yayanta sosai take basa lbrn abin arziki Dana Bata da irin sakar Mata fuska da nayi, Har cikin ransa yaji dadin daraja.masa kanwa danayi sosai, Hatta damuwar da ya fita da ita na safiya ganin yanda yau na tashi da zafi zafina abin ya tsaya Masa a Rai, Wannan abinda nama Yar uwarsa tilo da yafi so sai yaji zuciyansa wasai. Mangoro ya bata hade da naira dare ta rike a hannunta ya kara Mata nasiya sosai da hakuri A duk inda Allah ya ajita kafun ta wuce, *Khadija na fita wanka nayi nasa siket in kanti da t-shirt Mai kyau na daura gyele karami a kaina laptop na..... Sai kusan shidda ya dawo gida yauma da kwandon sa a hannu, da sallama a bakin sa *amsa Masa nayi, kaina nakan laptop, * Wanka yayi ya tafi masallaci yauma Bai dawo ba sai Isha waje na fita ganin yau ba NEPA, na fitar Mana da babban darduma na shimfida, *abinci na iba masa, nasa nawa na aje Mana tare da Masa Bismillah zama yayi shima Muka fara ci * Khadija ta tsanar Dani abin arzikin da kika Bata na gode, naji muryansa cikin sanyi sanyin sanan, Ba kome wallahih abinda ba yawa, Jin yanda na Masa magana a mutunce abin sai ya Masa Dadi sosai, mun Gama cin abincin har lokacin NEPA shuru na kasa shiga dakin saboda tsananin zafi da ake yau ga sauro, Tashi yayi ya fita yaje ya sai Mana maganin sauro, Yana dawowa na karba na kunna, kitchen na shiga na yaga caton in indomie, zanyi fifita dashe, * Wanka na sake shiga tsaban zafin da nake ji Kaya nasa vest sai wando Yale yale dogo har kasa, Kushin na dauko a daki na zuba akan cafet in na kwanta Ina fifita,Yana zaune a gefe shima ya jingina da jikin gini, Shuru mukaye dukan mu ba Mai magana,shikam tunani yake azaman da yaye da Sumayya ya fahimci Abubuwa cikin halayan ta, in Abu ya Bata Mata Rai, toh kowa ta shafa, in aka faranta Mata kowa zaiga fara'ar ta akwai ta da tsafta akwai iyya girki ga nutsuwa sam.bata da rawan Kai, *Har Sha biyu bamu shiga ba, ganin dare yayi ban tashiba ya mike a hankali yaji ya rufe kofar shashen mu, ya dawo ya shiga dakin ya cire kayan jikinsa yadau wando iyya gwuiwa sai riga Mara nauye , ya dauko filon kujira ya rufe kofar dakin harda k'wado key in yasa a cikin filon sa, Dawowa yayi ya tsaya a gefe cikin sanyin jiki yace "uhmm Daman Naga Kamar baki shiga daki ba kwanan waje zamuyi kenan? "Eh wallahih Amma tunda akwai maganin sauro"? Sake tambaya yaye in akwai wani abin kwanciyan a bani,Gefen dardumar na nuna Masa ya kwanta hade da furta" ita dayace" kwanciya yayi tare da Addu'an bacci, a hankali bacci ya dauke sa *Sai kusan karfe daya kafun bacci ya dauke ni da ker' Saboda rashin samun bacci da wure da bayi ba shiyasa yau Bai tashi yin sallar dare ba *Nikam ban sake sanin kaina ba sai asuba........ Ayi manage ba yawa😩 Masu complain in page na kadan 🪀My WhatsApp number 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya Ibrahim* 🍃 ✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwa 👌 🌿Jumma'at Mubarak to All my fan's Free book🤧 Page7️⃣ *A hankali nakejin sanyin asuba na ratsani har cikin kashi kowa yasan yanda sanyin asuba yake alokacin zafi, *Juyi nayi a hankali Amma sai me jina nayi Kamar Abu ya tukare ni, bude ido nayi sosai, me Zan gani ni Sumayya a kwance rabe-rabe a jikin MAKAHO, ai bansan sa'ilinda da na wantsala gefe ba, kwalbar maganin sauro na buge harya fadi a simintin dakali, ya fashe Jin Karan fashewan Abu shiya farkar dashi cikin sauri ya mike Yana tambaya ta lfy? **Nikam na kasa basa amsa toh me zance? cewa zanyi ka tabani Koh Kuna nace ajikinka na farka na ganni * Cikin Dan daburcewa nake magana" am am Babu fa Daman na tashine ban sani ba na buge kwalba ya fashe" Bai dai ji Miki ciwo ba ya fada cikin hanzarin karasuwa wajen da yake jiyo muryata, "Ah ah banji ciwo ba" Ok Allah ya kiyaye gaba, *Da Amin na amsa * Daga ni harshi Alwala muka hanzarta farawa Jin har anyi raka'a daya a masallaci, Muna kammala Alwala daki ya bude ya cire kayan jikinsa yadau jallabiya ya saka ya, *Nikam hijab kawai na dauka har kasa, sai sallaya biyu nazo na shinfida Mana Jin an sallame sallah a masallaci, *Na hau Kan sallaya Daya nayi gyran murya * Jin hakan yasa a hankali ya Suma takawa Yana nufo inda yaji nake tsaye ganin ni yake nufuwa yasa" nace ga sallah na shimfida maka tunda Naga baka samu jam'i ba" Ba musu ya ringa lalube harya Ji kafarsa ya taka wani abu Mai laushi sosai Wanda laushin ya banbanta da cafet in dakin,hakan yasa she gane sallaya ne " Hawa yayi ya saita gabar ya Tada sallah Ina binsa, Muna idarwa Naga ya Kama karatun Alkur'ani cikin suratul Qafe cikin zazzakar muryarsa Mai dauke da nutsuwa irin na mamilallun maza,da Kai (hadda) Nima.mikewa nayi na dauko Qur'an na bude Ina duba ayoyin da yake karantawa,harya Kai karshe ba gargada Koh wani harafi an basa hakkinsa, sosai nayi mamaki Amma Dana tuna ido kawai Allah ya jarabcisa ba zuciya Koh k'wakwalwa bane, ba abin mamaki bane, sai da yakai karshen surah. *Mukaye azkar sai kusan bakwai na tashi nade sallaya nayi nayi waje, Duk da akwai NEPA hakan Bai saka na kwanta ba fita waje nayi na tattara Mana shimfidar na mayar daki, Tsintsiya na dauka na share baranda na fara sharan qasa, Jin Bata dawo ta kwanta ba Kuma yaji tana shara yasa ya mike yayi waje shima, Gaidani yaye na amsa ba yabo ba fallasa, takalmin sa ya saka cikin lalube yayi kitchen wajen da yasan Ina Tara kwanuka da bojuwaye yafara tattarawa Yana kawowa mawanki harya Gama kwashewa, Boket ya dauka. Randa ya wuce a hankali ya dau Moda dake Kan randan da hannu daya ya bude randan da daya hannun sa, moda ya zura a randa zai ibi ruwa yaji wayam,sai da ya rank'wafa kafun yaji ruwa, hakan ya nuna masa ruwan Randa saura kadan fasa iban yaye ya dauki boket in ya Kama hanyan fita" Ganin ya Kama hanyan fitane,yasani tambayr sa" Ina zaka da boket kuma"? Cikin sanyin sa na halitta yace, ruwan Randa saura kadan Inna iba bazaki samu na aiki ba shiyasa Zan Iba a rijiya" "Rijiya"? Na sake tambayar sa, Eh yaban amsa, Kamar Zan hanasa,sai kuma nayi shuru na Kama kwashe shara, Jin bance kome ba yasa shi cigaba da tsayuwa, *Ganin yaki tafiya yasani cewa "yakuma ka saya" Fita yayi, ni Kuma na shiga kitchen na Kama hada breakfast, Yana fita rijiya ya nufa da lalube harya Isa Dayake rijiyar ba bakwansa bane Yana gane hanya, ya lalube guga a gyfen rijiya, ya zura hade da Bismillah, sai da ya Bari na Yan second kad'an kafun ya sake dagawa Jin ta cika yasa yaja, sai da ya cika boket dam kafun ya sunkuce boket da hannu d'aya d'ayar hannun yana lalubar hanya har ya samu ya shigo kofar ya zuba a Randa, Ganin wahalan da yasha kafa d'aya ma kafun ya kawo duk rabi ya zube Masa a jiki gashe yafi minti 10 daga rijiya zuwa kofar mu Yana lalube kafun ya gane, Haka kawai na tsinci kaina da" dakatar dashi ganin Yana kokarin juyawa ya karo Ka bar iban ruwan nan an.... Ban karasa ba saboda ganin d'aya Daga cikin yaran gidan budurwa ta shigo ba Koh sallama, tana cewa Wai inji inno ka Bata d'ari biyu zata sai goro, Cikin sanyi yace yau ban kwana da kudi ba sai naira d'ari d'aya kacal Kuma ita nake son saya Mana kayan miya zamu karya, tayi hakuri zuwa anjima inna fita na samu ciniki Zan bada a kawo mata, Cikin bala'i take cewa eh lallai watoh matar ka tafi inno kenan, dadin abin munsan auren liki aka maka ba Wai don ka Kai abaka ba, shidai kala baice Mata ba. Ke Kuma duk kudin da kike dashi Koh nace gidanku suke dashi sai kin jira D'arin karyawa mtwss,tana fada tana nunani, *Ai bansan lokacin da nayi super ba na saya a gaban ta " keee karki kuskura ki sake sakani a cikin haukarki na jahilci karki yarda in karta Miki layin rashin mutunci a gidan nan iskancin ku ya tsaya ku wak'u karku kuskura ku sani, idan takamarku bariki da rashin kunya wallahih ni Zan gyara Miki zama," "bace min daga gani" cikin tsawa na karasa maganar,Ina nuna Mata kofa, Tabbas ta tsorata Dani sosai don Bata dauka Ina da baki haka ba,da saurinta harda tuntube ta fita, Juyawa nayi na kalle sa Yana tsaye Kamar ruwa yacisa, Wani abu Mai kamada tausayi-tausayi takaici-takaici ya kamani, ganin kwata kwata na rasa me yasa Yan gidan nan suka Raina Masa wayone oho, *Daki na shiga na d'au jakana gudan dubu na dauko * fitowa ta yayi daidai da shigowar wata dattijuwar Mata cikin bala'i ta,toh Ina kike karamar Mara kunya, harkin Isa ki shigo gida jiya jiya ki nuna Mana iskanci, Daman tunda Naga yau kwananki uku a gidan nan Koh gaishemu baki zo kinye ba nasan ba banza Kika rasa miji ba Rana tsaka aka lika Masa ke, * ba tare da na kalle taba nace, "Yayan khadija pls ka Bata kudin da ya kwana a aljuhunkan, ba musu ya lalube jallabiyarsa ya d'auka ya Mika mata, fizga tayi tana ta tsababi zadai kaji da munafurcinka, *daga ni harshe bamu tanka mataba harta fita, *Albarkacin girmanta yasa naja bakina bance kome ba, Jin ta fita yasa na Mika Masa dubu d'ayar "gashi ka sai kayan Miya Mai D'an yawa Dana shaye ka hada da Kiran Mai ruwa" cikin sanyi yake cewa, kiye hakuri Sumayya Nike da alhakin daukar nauyinki akaina bazan iyya karban kudin kiba, sannan Ina Mai baki hakuri da abinda Yan gidan mu sukayi Miki, Bari naje na karbo kayan miyan da na shaye, "Da wani kudi Koh ba yanzun naji kace D'arin ne da Kai ba"? Eh hakane Amma Zan karbi kayan a shago Inna fita sana'a Allah ya bada kasuwa tunda mak'wancina ne saina Mika Masa Amma ni bazan iyya karban kudinki ba. "Au ni in cema akaye kyauta na baka ai bashine Inka tashi ka biyani" nace Masa ganin da gaske bashin xai fita ya karba, D'an Jim yayi sai Kuma ya karba ya fita, kitchen na koma na sauke macaroni ganin ya nuna na juye a kwando, Wanke wanken da ya Tara na Kama wanke wa da yake babu yawa plt ne biyu sai cup biyu shukali sai bojuwa biyu, kafun ya dawo harna kammala Yana dawowa nayi miyan stew da kefe busheshe manya-manya, guda biyu Wanda aka mini caton guda na gara Wanka yayi ya chanja kaya ya kwanta a kujiran daki, Ina Gama girkin na zuba Masa na Kai Masa daki hade da gyran murya na fita Wanka nayi na shiga daki da towel Mai Dan girma na daura yaukam zama nayi na shafa Mai da powder NASA kwalli sai man baki, Yana Gama ci ya ibi Kwanukan yakai waje, *Yana fita na ibi Kayana na saka rigane Abaya Mai kyau sosai ya karbi jikina gyelen na daura a kaina, Na kurawa kaina ido a madubi bansan lokacin da hawaye ya taru a idanuna ba, *Sun Rabani da aikina sun saka mahaifina ya datse mini Account Wanda da gumina na Tara Rabin kudin da ke ciki,sanan Kaf jalingo su rasa mijin da zasu aura min sai MAKAHON miji Wanda Koh kwalliya nayi baisan nayi ba, ni Karan kaina ma, sunar Ina matar sa Bai San ya nake ba, in badai muryata yaji ba bazaisan Ina wajen ba, me nai musu a rayuwa mina tsare musu basa kaunan cigaba na komin kankantarsa, a matsayin su na Yan uwa ga mahaifina. Duk a Raina nake zancen nan hawaye nabin kumatuna, Kinyi kyau, *abazata na juya cikin mamaki jin muryansa a dakin wanda bansan yaushe ya shigo ba Yana tsaye idonsa a....... 🪀My WhatsApp number 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya Ibrahim* 🍃 ✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwa 👌 Free book🤧 Page8️⃣ Idon sa a saitin gado, Yana kyetkyet tasu, Anasa tunanin ta saitin inda nake kenan, **Bansan lokacin da dariya ya kamanii ba hawaye nabin fuska ta duk a tare nace"da wani idon kaga nayi kyau wama yace maka kwalliya nayi nii Koh Kaya bansa ba" na fada ina dubansa, har lokacin bakina d'auke da murmushi Wanda har hakora na masu haske, d'auke da hakoran Gwal na makka har guda biyu a gyfe da gyfe na hakoran gaba, suka bayana, na kasa rike murmushin abin ya, bani dariya especially lokacin da ya furta Kuma idonsa na kallon wani wajen. Sam ransa Bai baci ba da abinda nace asalima wani sanyi yaji a ransa Jin sautin dariyar ta na farko a Kan kunnensa, Zuciya tane ya sanar dani kinye kyau "Aiku zuciyar taka Bata fada maka daidai ba, don ni banyi kwalliya ba atoh" Zaki iyya rantsewa? "na rantse nayi kwalliya Amma tsakaninka da Allah ya akayi ka gane"? Uhmm bayan kin shiga dakin nan kin zauna akan dressed mirror Ina ji ki aje Abu kamar gwangwanin Mai kinfi minutes 17 kina ajewa da dauka,hakan ya tabbatar min kwalliya kike, in Khadija tana kwalliya haka nakejin buruntun irin yanda naji d'azun,danake cin abincin "Lallai fa,"kawai nace nayi shuru Zan fita me da me za'a bukata, yace mini "No ba kome tunda kayan miyar safiya zai Mana kwana biyar Koh hudu" kaga daidai ya kare ka biyani kudina, Ok sai na dawo"toh" nace Masa yasa kafa ya fita *Komawa nayi na zauna Ina maijin haushin kaina Dana sake baki Ina tanka masa, kunna TV nayi ga fanka na kadawa k'wanciya nayi Ina kallo,Tashar zee cinema ana kallon wani film Mai suna bang bang sosai film in yamin dadi, 10:00pm naji sallaman Khadija mikewa nayi Ina amsawa na fito waje itace tsaye hannunta d'auke da kulan jiya, Ina kwana Aunty, "Lafiya Alhamdulillah ya Goggo"? Lafiya tace a gaidaki, "Aiko Ina amsawa" "Ki shigo mana" ah ah Aunty tafiya zanyi yanzun " Aiko baki isaba shige muje ciki yau ini zamuyi" Ba musu ta shigo dakin Muka zauna muna kallo sai 11:00 na mike na shiga kitchen Zan fara aiki, sai ganin Khadija nayi itama ta shigo, "Ah ah fa Khadija yau Kam zama zakiyi ki huta" Yanzun Zan kammala " Ah ah Aunty wallahih bazan iyya zama kina aiki ba Zan dai tayaki, Ba yanda na iyya haka Muka Kama aiki sai 1:30 Muka kammala tuwo da miyar kuka, nayi Tuwon da yawa harda na dare kawai, na huta d'aura sabo, zubawa yayan khadija,akula na zuba na dare a wani kulan na rufe, mukayi sallah ta Kai masa nasa, tana dawowa na zuba Mana munaci muna Hira, "Nikam Khadija wani school kike zuwane"? Aunty bana zuwa makaranta ai "Ban gane ba Khadija" Eh na kammala junior set. "Shine zakice kin Gama karatu"? Eh Aunty na Gama jss 3 Amma ban daura senior set ba "Me yasa"? Shuru tamin Naga alama batason bani Amsa ,Nima ban takurata ba, Na chanja zancen da, wani, "Khadija nikam akwai Wanda kika sani ne? ta iyya kitso, budurwa haka tazo tamin a gida Koh guda shida so nake na wanke kaina" Aunty Baga kanki a tsefe ba bazaki wanke ba sai an kitsa? "Aii Khadija bana iyya wanke Kai a tsefe sani ciwon Kai yake" Lallai Kam aunty bara mu kammala ci na kama Maki Kan in mun gama, "Au kin iyya kitson kenan"? Zandai Kama Miki, "Koh Zaki chanchara mini ba" Hh toh na yarda. Muna Gama cin abinci Khadija ta Kama mini kaina guda shida, na tashi naje nayi wanka na hada da Kai, *Sai dana rike Khadija har yamma kafun na barta,ta tafi, Sai yamma ya dawo Kamar yanda ya Saba haka yauma yayi wanka da sallah sai Isha mukaci abinci yau akwai NEPA tun na safe har yanzun Basu dauke ba dukan mu muna zaune a daki Ina kallo shima dai idonsa biyu, sai 10:25 na sa kayan bacci muka kwanta, Misalin karfe daya na dare na farka da wani irin azababben ciwon ciki Wanda tunda nake da wayo bantaba yin irinsa ba, Mai tsanani gaskiya tun Ina daurewa har dai na fara kuka Ina nishi duk iskan fankar da yake kadawa a dakin gumi nake, Cikin bacci yakejin kuka-kuka, Nishi daga ji na azaba ne, cikin D'an hanzari ya mike ya sauka a kujiran cikin azama yake magana muryarsa na rawa,Jin da gaske Sumayya ce Mai kuka da Nishi Sumayya!! Sumayya!! Lafiya kuwa ya fada Yana laluben inda nake, nikam saban azaba nama tsullubo kasan cafet daga Kan gado Ina durkushe reke da ciki,Koh amsa na kasa basa, Da lalube ya lalubo ni kafada ta ya dafa yana cewa, muryar sa na rawa,Sumayya lfy meke faruwa ne kimin magana mana, "cikina " nace Ina Kara fashewa da kuka, Hankalin sa in yayi dubu ya tashi, hannu yasa ya dauke ni cak kamar ya dauki Yar baby da lalube ya daurani akan gado. Nikam tashin hankali Bai barni nama San ya dauke ni ba, tsaban azaba, jikina har bari yake ,, sosai hankalinsa ya Tashi ,mikewa yayi zai fita cikin rawan jiki na kama Masa hannu na damke cikin nawa dake rawa sosai, ciki muryan ciwo yaci karfina nake cemai"D'an Allah karka tafi ka barni Zan mutu ka mikamin waya ta na Kira babana karna mutu" Sosai zuciyarsa ta tsinke Jin tana am batar mutuwa,Amma ya daure cikin sanyi murya yake cemin Kinga yanzun dare ne Bai kamata ki kirasa a daga Masa hankali ba, bara naje Koh Allah zaisa na samu iro ya kaimu asibiti da keke napep NASA kinji, sannu, **Gaskiya ya fada hakan yasa na sakar Masa hannu ya fita, Waje ya fita Yana lalube ya dauki sandar sa a dakali da lalube ya fita a kofar shashen Yana lalube harya Isa hanyan kofar gida wanda ke dauke da d'akunan samarin kusan bakwai, a kofar dakin iro ya tsaya ya fara buga Masa kofa Yana Kiran sunan sa, Cikin bala'i ya bude kofar ya fitoh kai don Allah lafiya Ina cikin bacci karfe daya zakazo ka bugamin kofa Dan wulakanci kome,? Don Allah iro ka taimake matatace ba lfy sosai shine nace Koh zaka taimaka mini ka kaimu asibiti, Buran uba a Daren nan ba shegen da ya isa yasani in fitoh wallahih Koh inno ne ba lfy ba inda zani bare wata banxa Wai matarka don Allah ware ka ban waje nikam, Yana Gama masifar ya koma daki ya banko kofar, Haka ya juya don yasan tunda har iro yace bazai taimake Saba ba Wanda ya Isa yasa sa daukan su , waje ya fita Amma titi shuru. Ba motsin kome,yakai minutes 30 baiji motsi ba dole ya hakura haka ya juya da sanyin jiki ya koma cikin gidan,kofar ya shigo cikin hanzari ya Isa dakin har yanzun dai kukan take,gadon ya hau a hankali ya Isa gareta cikin sanyi yake ce mata, don Allah Sumayya kiye hakuri wallahih ban samu abin hawa ba, cikin muryar kuka nace "ka dubamin wayata tana Kan dressed mirror,ka bani na Kira Abie" Ba yanda ya iyya dole ya Bata wayar ganin irin azabar da take Sha gashi ya kasa Nemo Mata mafita ga ciwo na cinta, Sauka yayi a gadon Yana lulube harya gane dressed mirror in, har Allah yasa ya samu wayar mikamata yayi, Karba nayi cikin Nishi nake lalubo number Abie na na Kira yakai sau biyar baya dagawa Daman tun Randa aka kawoni gidan nan Koh na Kira sa baya dagawa sai ana biyar in nayi sa'a ya daga cikin muryar kuka nake cewa abie Zan mutu cikina ciwo kazo ka kaini asibiti,, abinda naji abina ya fada shiya Kara hargitsamin k'wak'walwa, yau nice yau abie ke cewa Inna mutu baida asara Kuma karna sake kiransa tsakiyar dare Yana bacci, **Anya abie nane kuwa? Mai Sona da tausayina Mai son ganin farin ciki na yake furta wannan magana gareni,shikinan shima abie yanzun baya Sona 😭 wayar na sake daurawa a kunne na Amma abie ya kashe call in ban daddara ba na sake kiransa wannan Karo Kam line busy ya Danna mini. **Me nai Masa lfy lfy Muka rabu cikin kewan juna da Addu'a tare da fatan alkhari hade da nasiha, bansan lokacin da wani sabon kukan ya barke,min ba Sosai hankalin Al'ameen ya Tashi baisan lokacin da ya iso garita ba ya Kamata ya runguma cikin wani irin yanayi na tashin hankali yake lallashin ta, **Kara rungumar sa nayi na yenyene Masa ajikinsa Ina kuka maitaba zuciya wannan kukan bana ciwo bane kadai harda na bakin ciki Abiena shima ya juyamin baya adaidai lokacin da nafi bukatar sa, Haka nayi ta fama da ciwo daga ni harshe bamu rintsa ba sai addu'i yake tufa mini har hudu na asuba, Yaji taja numfashi da karfe sai Kuma yaji kome nata ya sake Daman har lokacin tana jikinsa, cikin wani irin rikice wa jinta ta Bata motse yasashi mikewa ya sabeta cak a kafada Yana lalube ya fita a dakin Koh kofar Bai rufe ba tsabar tashin hankali,fita yayi a shashen yayi hanyar kofar gida.............. *masu Tambaya na complete in MATAR MAKAHO* , *A Ranan 30/8/2021 na fara Post na novel innan bani da complete* 🪀My WhatsApp number 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya Ibrahim* 🍃 ✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwa 👌 Free book🤧 *More comments* 😁 *More post* 🤕 Page9️⃣ Haka ya ringa lalube don Koh sanda Bai rike ba ya fita waje, da ita,yaje titin shuru haka ya ringa takawa a Gefen titi ba tare da yasan inda zai nufa ba, cikin ikon Allah sai ga wani Mai mota yazo wucewa ganinsu cikin wani Hali yasa shi tsayawa a saitin, Al'ameen Yana tambayar sa lfy kuwa ya gansa da mace a bakke a kafada Bata motse gashi Koh takalmi babu a kafarsa da asuban nan? Da sauri ya juyo wajen da yakejin muryar Mai motan don Allah ranka shi Dade ka taimaka mini matatace ba lfy wallahih tun jiya yanzun haka Suma tayi Ina son kaita asibiti Amma ban samu abin hawa ba, Allah sarki shiga muje Nima kwanace ta kamani a hanya sai yanzun na shigo gari, Allah ya saka nagode,ya fada Yana laluben murfin mota tsabar tashin hankali Yama kasa budewa ,abin ya bawa Mai mota mamaki, yadai malam lafiya Naga kana lalube baka shiga ba,? Bana ganine,ka taimaka ka bude mini, Ba karamin mamakine ya Kama Mai mota ba ace mutun Kamar Wannan baya gani lallai Koh wani bawa da kaddaransa, Fita yayi yazo ya bude Masa A hankali ya shimfida Sumayya asset in baya shima ya shiga Mai mota ya rufe ya zagaya shima ya shiga mazauninsa yaja motar , Wani asibiti Zan kaiku? Duk asibitin da yafi kusa damu ka kaimu Ok ya kara gudun motar lokaci kankani suka iso FMC don yafi kusa da SINTALI ( sunan unguwansu Al'ameen) Suna Isa emergency Mai motar ya kaisu fita yayi ya shiga Hall in ya Kira nurses za'a d'auki Mara lafiya suka fitoh da sauri aka aza Sumayya bisa keken marasa lfy aka wuce da ita dakin taimakon gaggawa, Likituti suka,rufu a kanta don Bata taimakon. Gaggawa shi kuma nurse tace Masa yaje ya sai Mata card a bude mata file, Wajen sai da card in ma da taimakon Mai motar ya gane, kudin card naira 300 matar da ke windown tace, ba karamin tsinkewa yayi ba sai yanzun tunaninsa ya dawo jikinsa, don Koh sisi baida shi sai naira dari da hamsin na cinikin jiya, ya Allah ka taimake ni abinda ya ke fada kenan a ransa, Malam.koh bakaji bane nace 300 ne kudinka shuru yayi Yama ya kasa magana, Mai motar ne ya fahimci Koh sisi baida shi kenan fitar da dari uku ya Biya kudin card Menene sunan majinyacin? tambayar sa akaye me sunan Mara lafiya, Sumayya ,sunan surname?? Shuru yayi yana tunani a hankali yace Abdulsalam shugaba,ya fada Dan in Bai manta ba haka yaji agun daurin aure aka fada,sai da ta daga kai ta sake kallonsa Jin sunan da ya fada amasayin sunan mahaifin maralafiyar da suka kawo, lokaci kankani aka bude Mata file in , Yama rasa bakin godiya sai gode ma mai motar yake, nagode nagode bawan Allah ba abinda zance maka sai Allah ya saka maka, Ba kome ai ka gode Allah, sunana Ammar Ina zaune da iyayena a unguwan millionaire's sweet,ya fada Yana Kama hannun Al'ameen Yana Masa jahora zuwa masallacin asibitin sukayi sallah suka dawa Kan kujirun da ka jera a Hall in,suka zauna, Nurse ce ta fitoh tana tambayar suwaye suka kawo Sumayya Abdulsalam shugaba? Mekewa sukayi Ammar na rike da hannun Al'ameen suka Isa wajen da take Gamu nan Mika musu takardan magani,doctor yace ku saya maza-maza don ana bukatar sa emergency, Hannun Al'ameen na rawa ya amshi takardan hade da tambayar ta don Allah ta farfado ne ya jikin nata,?? Eh ta farfado Amma ana bukatan kuje ku sai Abubuwan da aka rubuta muku,.. Kama Masa hannu Ammar yayi suka wuce pharmacy suka je Mika takardan maganin sukayi karba sukayi suka duduba ruwane da allurai sai maganguna, Kudin ku naira dubu bakwai da dari biyar, Shikam Abu ya hade Masa goma da ishirin Ina zai samu kudi Mai dunbin yawa har dubu bakwai da dari biyar, Koh Kama sayar baidashi bare ya Kama ya sayar ya Saya mata magani Innalilahih wainnailaihir rajuun yake furtawa hade da karban takardan balance ya fita tsabar rudewa shikamma ya manta da wani Ammar suke tare, Ammar ne ya biyosa ganin yana faman lalube zai fita a pharmacy in da sauri ya rike Masa hannu, Habba Dan uwa karka dagawa kanka hankali Mana Yana fada ya karbi takardar ya rike hannun Al'ameen suka shiga waje biyan kudi Ammar ya biya kudin suka karbi magangunan da su ruwa da allurai suka Kai emergency, suka mikawa nurse in ta shiga dakin, sai a lokacin hankalin Al'ameen ya kwanta sosai yayita ma Ammar godiya shikam ma har kunya ya kamasa Kamar Wanda ya bawa million biyar,. Sai 8:30 aka barsu suka shiga suka ganta ta farfado Ansa Mata ruwa da alluran bacci don ta samu hutu sosai ciwon ya lafa Toh abokina Zan wuce Naga gari ya fara wayewa gashi sai kirana ake daga gida kasan Dana shigo *Jala* na Kira gida nace musu na shigo, Ba kome wallahih nagode sosai Ammar Allah ya saka da alkhari Habba wanna godiya ya Isa haka,baka fadamin sunan kaba fa har yanzun? Suna na Al'ameen,ya basa amsa A unguwan da na dauke ku kake ? ......Eh Ok toh insha Allah Zan dawo na duba Mai jiki Nagode nagode Ammar Sai anje ma, ya fada Yana kokarin fita a Hall in sai Kuma ya dawo, Koh xan kaika gida ka dauko Mata Kaya da Abubuwan bukata Kamar Kayan da zata chanja su maclen da brush da abubuwan bukata kaima ka samu ka kimtsa jikinka Naga Kamar a birkice ka fitoh Koh takalmi babu nasan har yanzun baka San kafarka ba takalmi ba hh ya fada cikin wasa Yana dariya,?? Shima Al'ameen in dariya yayi kawai, Yana cewa toh muje don wallahih rudewa Kam na rude, Hannunsa Ammar ya rike masa suka fitoh ya bude Masa mota ya shiga ya ja suka wuce, suna tafiya suna Hira Amma dai ku sabbin aure ne Koh? Eh yau kwanan mu hudu, Kai kace ango ne da kansa Koh dai Mai kashane, amarya har asibiti Dariya kawai Al'ameen yayi baice kome ba don bazai iyya fadawa Al'ameen sirrin Saba duk da yaji bawan Allah ya kwanta Masa arai Yana da kirki sosai koma zasuyi sa'o'in juna Amma hakan bazaisa ya tsake jiki dashi ba don mutumin duniya ba abin yarda bane lokaci guda, Sun Isa har inda ya dauki Al'ameen tukunna ya tambaye sa sun iso wajen da ya dauke sa da asuba ata Ina gidan naku yake? Ah ah Ammar sauke ni ma anan na gode ah ah kaidai kamin kwatance Ah ah wallahih hakan ma nagode,ganin ya nace yasa Ammar sauke sa Sukaye sallama A hankali Al'ameen ke tafiya Yana Dan yaryarfa hannunsa don Ya tabbatar inda yake sa kafarsa ba mutum Koh wani abu inda Allah ya Sosa ma tsallaken titine aka sauke sa ta barin gidansu a hankali yake tafiya Bai Ankara ba yaji an bangajesa haryaso faduwa saura kadan da yakai kasa, wani zafi yaji a yasansa don ya buge dutse sosai yatsan ke Masa zafi a hankali ya mike, Jin Wanda ya turesan Yana bala'i, ku wasu irin mutane ne in ka San baka gani wani rawan Kaine zaisa ka fitoh babu D'an jagora babu sanda, irin hakane ai sai ku hau titi mota yabi ta kanku kujawa mutum jaraban jinya inkun mutu Kuma kusa mutun azumin kaffara mtwss,, Ya fada Yana tafiya A hankali Al'ameen ya d'uka ya taba yatsar Jin damshi yasashi gane jini ke zuba, Bai damu ba ya cikaba da tafiya har Allah yasa ya iso kofar gidansu ya shiga, Yana shiga cikin gidan ya samu Yan gidan a filin tsakar gida kowa na sha'aninsa daga masu wanke wanke sai masu wanki sai masu kitso masu Jan ruwa wasu Kuma group aka hada ana ta gulma ana xagin juna,,, Ganinsa ba takalmi sanan ga jini a kafa Yana zuba, yasa Rabi'u fara magana Kai MAKAHO daga Ina haka a bujaje yau tun safe ma bamuga fitarka ba? , kafun ma yayi magana iro dake goge takalminsa zai fita yace Wai fa D'an rainin wayon nan jiya Ina bacci yazo karfe kusan daya Wai nakai matar sa asibiti Bata da lfy kaji Dan rainin wayyo wama ya sani Koh turmushe Yar mutane yayi xaizo tsakan dare yana tashina,,gabaki dayan su suka saka dariya, Shidai kala baice musu ba hanyan shashen su yayi da lalube harya shiga sai a lokacin ya tuna Ashe fa kofa a. Bude ya barta cikin D'an fargaba ya shiga dakin don shi tsoronsa ma kar Yan gidan su shigo su Ma Sumayya sata don shikam baida abinda za'a sata, wayarta daya Mika Mata jiya da dare shiya fara lalubawa akan kadon aiku yajisa, Hakan ya tabbatar Masa ba Wanda ya shigo tunda ga waya a fili Amma da an shigo wayar nan dake zaune a fili haka da an sabe sa hamdala yayi ya gode Allah Basu San ya fita ba, iban ruwa yayi yashiga bandaki yayi wanka yasa wasu Kayan ya rufe kofar ya fita don bazai iyya gane inda kayanta suke ba, Sandar sa ya dauka ya fita a gidan hanyar gidan Goggo Amina ya nufa, Yana Isa kofar gidan ya tsaya a waje yayi sallama, Shan cikin gidan kuwa Khadija nawa Goggo Amina kitso taji sallama Kamar ta yayanta Aiko ita ince amsawa tayi tare da daukan hijab inta ta fitoh waje Yana tsaya yaji isowar Khadija bakin ta na amsa sallaman sa Ina kwana Yaya ya aunty? lafiya Alhamdulillah Khadija Ka shigo mana Yaya Goggo ne kawai a gidan yau ? Toh ya amsa Mata Ta Kama hannunsa suka shiga cikin gidan kujira ta aje Masa ya zauna Yana gaida Goggon tasu, Ina kwana Goggo? Ta amsa da kulawa Lafiya Alhamdulillah Muhammad y'ay'a iyalin taka? Lafiya Alhamdulillah sai dai bataji Dadi ba jiya da ciwon ciki ta kwana yanzun ma daga asibitin nake nazo na dauki Khadija tazo muje zata dauka Mata kayayyakinta Koh kadanne Zan Kai Mata asibitin, Subhanallah Allah ya Bata lfy wani asibiti ne? Ameen a FMC ne ya amsa Mata Khadija tashi maza kuje, toh Goggo ta amsa Mata tana mikewa Shima Al'ameen mikewa yayi,hannunsa Khadija ta Kama suna tafiya a haka, Yaya jikin nata da sauki Koh? Da sauki Khadija Yaya zan bika muje asibitin? Ah ah Khadija ki tsaya a gidan namu ke dafa mana abinci tunda Kinga asibitin FMC ne babu nisa saiki Kai Mana can, A wani block ne yaya? emergency ne har suka Isa gidan nasu suna Hira dakin ta shiga ta dau jakan Sumayya mabi da ket ta Ajjye tana iban Kaya a whtdrp tana zubawa hijab D'aya, sai dogayan rikuna biyu, zani fille fille guda biyu,sabbine kal ta hada da t-shirt biyu, da hula biyu, sai maclen da brush ta hada Mata da kananan Kaya su pants brz da vest ta rufe akwaitin, Yaya na Gama Amma dai tunda kace tun asuba kuke asibiti baka samu kaci karyawa ba koh? Kai Khadija kin cika surutu wallahih inkin gama kika kawo Mana ai zanci, Amma yaya yanzun fa ana neman 09:30 na safe baka karya ba in kaje asibitin Yaya ka samu abinda zaka saya muku kuci Kaida Aunty kafun na Gama, Toh Addata Khadija Hhh ye Hakuri yayana .. Baice Mata kome ba illah daukar jakar da yayi Yana lalube zai fita a dakin idon Khadija ya sauka a Kan kafarsa a matsanancin damuwa ganin yatsan sa a kumbure gashi ya karce sosai, Yaya meya same ka a kafa haka,? Tuntube nayi kawai yace Mata Yana fita,, fita yayi bakin titi Yana tare keke da hannunsa har Allah yasa wani ya tsaya, Malam Ina zuwa? ...FMC yace Masa Shiga muje, da lalube ya shiga keken suka wuce cikin kankanin lokaci suka Isa hospital ya sauke sa abakin get don in ba majinyaci bane a Keke ba'a Bari ta shiga asibitin, ya bawa Mai keken kudin sa naira 50, Ya Kama hanya da lalube ya Isa cikin asibitin security n get yake tambaya don Allah wani shashine zaibi zuwa emergency don lokacin da suka zo da Ammar a motane bazai gane hanya ba gashi asibitin fadine dashi ga shashe daban daban, Kabi nan ka Mike har emergency zai kaika haka kuwa yayi har ya Isa emergency Yana shiga ya gane dakinda aka kwantar da ita yazo shigane ya hadu da nurse in d'azon tana ganinsa ta rufe sa da masifa Kai wani irin mutum ne zaka kawo Mara lfy kasa kafa ka fice ka barmu da ita, tun dazun nemanka ake likita nason ganinka, Kiye hakuri gida naje na dauko Mata kayane Me yasa she dayan bazai je ya dauka mata ba Kai ka zauna?, Taimakona yayi Kuma ya tafi, Jeka aje kayan kazo likita nason ganinka Da toh ya amsa Mata da lalube ya Isa inda gadon ta yake har lokacin Bata farka ba, Juyawa yayi ya fita a dakin sai da ya fita kafun, ya tuna baisan office in likitan bama tambayar wata nurse yayi da taimakon nurse innan ya gane office in doctor shiga yayi da sallama doctor ya amsa masa matashine kamarasa, Kaine ka kawo Sumayya Abdulsalam shugaba? Eh nine doctor ya basa amsa ..ok Sumayya na fama da apendes ya kunbura sosai don haka dole za'a Mata tiyata ga wannan sai kaje ka biya kudin, Atake zufa ta fara karyo Masa Innalilahih wainnailaihir rajuun,likita kudin zai Kai nawa,yafada Yana tambayan sa?, Bani bane Mai karban kudi in kaje wajen biya za'a fada maka................. 🪀My WhatsApp number 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya Ibrahim* 🍃 ✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwa 👌 Free book🤧 Page 🔟 Cikin tashin hankali ya mike ya fita Dayake shi mutum ne Mai saurin fahimta yasa dakansa ya wuce wajen biyan kudi, Kudin 50k yaji ance Masa, Innalilahih wainnailaihir rajuun take yaji Kamar kansa xai rabe biyu haka ya karbi takardan ya wuce zuciyansa sai rawa take, shi Ina yasan zai samu kudi gabaki daya jarinsa ma baifi dubu daya da dari biyar ba Ina zai samu dubu hamsin, Koh bashi zai karba wazai tinkara in ma an basa Ina zai samu kudin biya? Har cikin ransa baya kaunan wani abin bukata ya Tashi ta bangarin Sumayya ya kasa Mata har sai Yan gidansu sun Mata duk da baisan dalilin da yasa duk cikin Jala Arasa mijinda zasu aura Mata sai shi suka zaba Mata Wanda har yau ya kasa samun Amsa dalilinsu,, Kuma bayason Koh da Wasa ta Saida abinda tazo dashi daga gidansu,saboda gazawarsa wajen Bata kulawa Bai santa ba Bai ta ba ganinta ba Bai taba Jin lbrn taba Bai San ya take ba muryarta kawai ya sani Amma a D'an zaman da sukayi Yana jinta har cikin ransa,, Ya Allah ka bani ikon kulawa da wannan Amanar da aka bani, A hankali yake tafiya harya fita a get in hospital in da taimakon wani Almajiri ya tsallake titi 100 da ke hannunsa ya Saya Mata Ayaban 100 guda biyar aka basa ya baiwa Almajirin ayaba daya ya sake tsallakar dashi, cikin hospital in ya shiga yanabi a hankali da sardarsa harya Isa kofar dakin da aka kwantar da ita da sallama ya shiga dakin, "Waalaikumu salam" na amsa Masa cikin dishashesshen muryata dagaji kasan na Mara lfyne maijin jiki Sannu Sumayya ya jikin ??. "Da sauki Alhamdulillah" Sannu ya sake cewa **Kai kawai na iyya daga masa Lalube ya fara Yana neman wajen zama, "Kujiran na Gefen ka na dama"nace Masa Laluben damansa yayi yaji kujiran plastic na roba ya matso dashi Kusa da gadon inda yaji muryarta ya laluba ya aje kujiran kusa da gadon saitin kanta a hankali ya zauna, Sannu Sumayya ga ayaba na sai miki yafada yana bude laidan hade da fitar da Ayaban masu k'yau guda biyar zai bare mini, "Ah ah ka ajiye,so nake sai nayi sallan asuba nayi brush da wanka Koh zanji dadin jikina kafun NASA Abu a bakina" Toh bara na taimaka Miki ki shiga bandakin sai kiye wanka da brush in duk na kawo Miki harda Kaya "Toh taimaka min na tashi " A hankali a mike Yana lalube na harya lalubo hannuna ya Kama na mike a hankali na sauka a gadon Ina "takalmina"? Na manta ban hada Miki ba komawa nayi na zauna a bakin gado "gaskiya ni bazan iyya taka tiles na asibiti ba takalmi gaskiya" toh ga nawa kisa Yana fada Yana cire mini ciny'ayyen silifas insa "ah ah innasa naka kaikuma fa"? ba damuwa Zan tafi haka "Bazanfa saka ba sai dai ka saimin sabon silifas abakin get" Wallahih ban fita da kudi ba sai dai in Khadija tazo taji da dauko Miki"toh" na basa amsa Ina k'wanciya a Kan gadon, Khadija bayan fitar yayanta dakin ta fara kimtsawa ta share ta cire zanin godon ta shimfida wani ta share baranda da kasa ta hada wanke wanke tayi kafun ta shiga kitchen,da yake akwai NEPA ruwa ta daura a hot-plate ta zuba ruwa ta rufe, ta dauko wani bojuwan daban ta daura shima ruwan ta saka ta rufe Daya ke hot-plate in Mai uku ne, Tattasai ta dauka da dogo dogo sai albasa ta hada ta juye a blander Dayake taga yanda Sumayya tayi ranan da suka shiga kitchen kunnawa tayi ta markada she Kara Kara baiyi laushi ba dai dai irin na miyan taliya, Sannu ishesheya munafukar yarinya uwar me kike a kofar har yanzun Naga fitar *makaho* tun dazun ya fita? Taji muryan inna asabe take fada tana shigowa kofar Inna Aunty Sumayya ce ba lfy shine Yaya yace na musu girki, Oh lallai ai sai ke in zai Kira don duk gidan nan ba bawan sa Kala Khadija batace Mata ba Dan ubanki bara na kawo kwanona ki zubamin inkin gama saura kisamin kadan, Kala Khadija batace ba tana cigaba da gyaran waken da ta iba cikin Kofi Daya da rabi Keee ishassheya bakiji me nace bane Naji innah ,ta Bata amsa Fita Inna asabe tayi sai gata ta dawo da katon kula ta ajema Khadija a gaba ta fita abinta Ruwa na tafasa ta sauke taliya daya ta juye a tukunyan ta barbada gishiri ta rufe, dayan bujuwan wake ta wanke ta zuba ta rufe shima ta saka Masa gishiri, Wani sabon bujuwa ta daura ta zuba Mai da albasa Yana soyuwa ta juye kayan miyarta ta soya ya soyu tukum ta saka ruwa ta bare Maggi tasa da onga classic Wanda ta gani duk a cikin kitchen in caton in kefe ta bude ta dau uku masu kyau ta aje a roba,ruwan zafi ta zuba a kettle Yana tafasa ta juye akan kefen ta barsa yadan d'auki seconds kafun ta tsame tasa a ruwan sanyi ta gyara ta juye a miyar ta rufe Daidai lokacin taliya ya nuna saukewa tayi ta juye a k'wando ta tsame, Fita tayi a kitchen in ta dau omo da sabulu ta hada wankin yayanta Dana Sumayya harda zanin godo ta fitar waje ta aje ta fara iban ruwa a rijiya tana wanke kayan dashi lokaci kankani ta Gama wanke wa ta shanya a igiyar kofar shashen, Kitchen ta shiga ta duba miyar ta nuna saukewa tayi,ta dauki wani kula a caton insa Mai azabar kyau har Yana daukar ido Mai guda hudune uku ta dauka ta wanke dayan ta zuba taliya daya Kuma Miya sauke waken tayi shima ta juye a dayan Kular, K'wando babba na kaba Mai kyau ta jera kulan a ciki sai lokacin ta Tuna kulan Inna asabe zuba mata, tayi, Ta shiga daki firij ta bude ta dauki drinks guda biyu sai ruwan gora biyu ta hada a k'wandon da plate biyu shukali biyu,.. Wanka ta shiga tana fita ta maida kayan da tazo dashi, Jin ana Kiran azahar tayi Alwala tayi sallah, Ta dauki sallaya ta ninke tana kokarin rufe kofar dakin sai ga Inna asabe tana zuwa kitchen ta nufa ta bude kulanta ganin abinci a ciki Kuma Mai yawa yasata dauka tayi gaba abinta, Rufe kofar tayi ta dauki k'wandon ta fita a shashen shima ta rufe kofar ta rike key in ta fita dashi lokacin karfe 1 na Rana hanyar FMC ta Kama da kafa, ***********Har lokacin muna zaune nida shi anzo an sake daura mini ruwa,Yana zaune cikin wani yanayi duk da na Saba ganinsa sanyi sanyi Amma nayau yafi na kullum Wanda bansan daliliba, Jin an fara kiraye kirayen sallah yasashi tashi Yana lulube yake cemin bara yaje sallah ya dawo,da "toh" na amsa masa, Fita yayi yaje masallaci yayi sallah ya zauna agun sai kusan 2 ya mike ya nufu Hall in emergency har yayi nisa yaji muryan Khadija daga nesa tana k'wala Masa Kira, Juyawa yayi saitin inda yake jiyo muryar Tata ya tsaya harta karaso Khadija kin isone? Eh Yaya na karaso tun dazun Amma ban gane dakin da kuke ba, Muje toh Khadija ya fada Yana tafiya,itama binsa tayi a baya,. Yaya ya cikin nata? ....Da sauki Khadija Yaya Yana ganka cikin damuwa haka meke faruwa ne Koh kudin magani ne baka dashi? Khadija Ina Zan samu kudin magani in badon Allah ya rufamin asiri ba ya hadani da wani bawan Allah ba ya biya mini kome na magani, A Ina ka Sansa Yaya? Bansan Saba yadaice sunansa Ammar Toh meke damunka? Wallahih khadija appendix ke damun Aunty ki Kuma kudin operation naira dubu hamsin shine yake dagamin hankali banda sisi Koh abinda Zan sayar na biya Amma yaya baka ganin gara a fadawa Aunty tunda bazata rasa kudi a hannunta ba, tabiya ?? Ah ah Khadija karki fada Mata yanzun Ina son in munje ki zauna agunta ni Zan fita Koh Allah zaisa na samu bashi, Habba Yaya wazai baka bashi tsakani da Allah fa Kaida Koh sisi baka dashi in ba mangoron da ya rage jiya ba wazai baka bashi' Khadija kedai ki tayani da Addu'a na Allah basa karewa Hakane kam Yaya Allah yasa ka samu Yauwa ameen Khadija ta Daidai lokacin suka iso dakin, shiga sukayi Ina kwance,sauke k'wandon Khadija tayi tana gaidani Aunty Ina kwana? "Lafiya Khadija" Ya jikin ki Aunty? "Da sauki Alhamdulillah" "Khadija kiramin nurse tazo ta cire mini ruwan nan na samu nayi Sallah" Toh Aunty tace, tana fita,sai gata da nurse sun dawo cire mini sukayi, "Khadija hau godon ki zauna ki ban takalmin ki bara na shiga toilet" toh Aunty, *Ta kalmin nata NASA shi Kuma ya bawa Khadija tasa ta saka ya lalube bakin gadon ya zauna **Da taimakon Khadija na shiga bandaki ta koma ta dauko mini brush da maclen,da kayan da Zan saka, ***Wanka nayi da brush nayi Alwala na fitoh a hankali nake takawa Ina bin bango harna bude kofar na fitoh Da sauri Khadija ta tashi tazo ta taimaka mini ta shimfida mini Sallayan da tazo dashi ta shimfida mini ta Mika min hijab na saka na Tada sallah harda na asuba na biya,ina idar wa na cire hijab in, Khadija ta mikamin hula nasa, na tashi na koma Kan gadon dukansu sukaimin sannu har suna hada baki, Khadija takalminta ta saka Wanda na cire ta bawa Al'ameen nasa, Abinci ta iba min a plate ta Miko mini, "Khadija bawa yayanki abincin nan bazan iyya ci ba bakina ba Dadi Sam" Ah ah Sumayya ki karbi abinci kici ai ba'a jinya sai da abinci" Al'ameen yace Gaskiya ne Aunty rabonki da abinci tun jiya fa,ta fada tana aje mini, "Wallahih Khadija bazan iyya ci ba kidai Mika mini ayabar nan naci" Toh Aunty, Ayaban ta bani na samu naci uku ta Mika mini fresh milk in da tazo dashi daga gida nasha rabi Plate na abincin da ta bani ta Mika Masa karba yayi Bismillah ya fara ci, "Khadija ya Naga kin zauna ki ibi abinci kici Mana" na Bata umurni Iba tayi ta faraci, Yana Gama cin abinci ruwan gora daya Khadija ta bashi yasha, Khadija ki zauna da Aunty ki bara na fita sai na dawo,ya fada Yana tashi yayi hanyar waje, Toh yaya Allah ya bada sa'a ...... Ameen Khadija Nidai da ido na bisa harya fita na juya Ina kallon Khadija" Khadija waya biya kudin magangunan nan Naga harda ruwa duka"? Nima ban sani ba Aunty yanzun nazo sai dai ki tambayi Yaya, **Shuru kawai nayi na koma na kwanta Al'ameen Bai Dade da fita ba, sai ga wani matashin saurayi baki k'yakk'yawa Mai matsakaicin tsayi da jiki ya shigo dakin mu da sallama a bakinsa Amsawa Khadija tayi nikam hannu nasa na dauki hijabina da na cire a jikin karfen gado nasa, Shigowa yayi ,barka kudai ya jiki Sumayya? Mamakine ya kamani Ina kuma wannan bawan Allah ya sanni, "Da sauki Alhamdulillah" Allah ya kara sauwa kewa "Ameen" nace Al'ameen ya fitane? Eh wallahih yanzun ya fita baku hadu ba? Khadija ta basa amsa Ah ah bamu hadu ba, Koh Kaine Ammar? Nine Hala lbrna ya baki haka kikayi saurin gane ni? Eh yadai fadamin abin alkhari da ka Mana Allah ya kara bude, ...Ameen Nidai shuru nayi na barsa da Khadija suna Hira Kamar Wanda suka San juna, Khadija nikam Inaga Zan gudu fa har yanzun Al'ameen Bai dawo ba gashi Ina son muyi sallama tafiya ne ta kamani wallahih gobe Zan wuce shiyasa naso mu hadu kafun na wuce, Yace Yana zaro kudi a Aljuhunsa Yana mikawa Khadija ga wannan ba yawa a saiwa mara lfy lemo in yayan naki ya dawo kice Ina gaishe she , Mungode Allah ya saka Kuma zaiji sakon ka, Allah yasa yace Yana kokarin nufar kofa "Nagode" nace masa ba tare da na dago ba ganin irin kallona da yake tayi kamar ya samu TV tun dazun da suke hira da Khadija idonsa na kaina, Ba kome yace yasa Kai ya fita......... 🪀My WhatsApp number 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya Ibrahim* 🍃 ✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwa 👌 Free book🤧 Page 1️⃣1️⃣ Bayan fitar Ammar Khadija ta kirga kudin dubu goma ne,Mika min tayi, Aunty ga kudin "Ajjye Khadija in yayanki yazo ki basa tunda shike fama da zirga zirgan asibiti" toh Aunty ta bani Amsa tana aje kudin a cikin ak'watin Kayana, Al'ameen na fita daga asibiti da kafa ya koma har gida Dayake akwai sanda in Kuma yazo titi sai ya Kama yara su tsallakar dashi Yana Isa unguwan su(sintali) wajen shagunan bakin titi ta inda yake sai da mangoro a bakin su, Shagon malam shu'aibu ya fara zuwa don shine yafi masu shagunan abin arziki sosai alayin da sallama a bakinsa ya shiga shagon, Assalamu alaikum malam shu'aibu Waalaikumu salam Mai mangoro ne? Eh nine malam shu'aibu barka da jama'a Barka dai lafiya Kam Naga yau tun safe danazo bude shago Naga hulbairon ka a rufe dazun na aiki yaron gidana ya karbo mini yako yake fadamin baka nan? Eh wallahih malam shu'aibu iyalina ne ba lfy jiya na kaita asibiti, Allah sarki ya jikin nata? Da sauki Daman nace bara nazo ka taimaka mini da kudi dubu hamsin za'a Mata aikine appendix ya kumbura a cikin ta don Allah ka taima kamin, Kutt lallai ma a karnin nan da kowa ke takai takai Ina Zan iyya daukan kudi har 50k na baka da sunan bashi, bayan anyi operation in Ina zaka samu kudina ka biyani, gaskiya bazan boye maka ba ni nan Koh biyar bazan iyya baka ba banaji ance Yar masu kudi aka aura maka ba me yasa danginta bazasu Mata jinya ba tunda sunsan baka dashi Daman suka baka ita Shikinan malam shu'aibu na gode, ya fada Yana fita ba tare da ya basa amsar tambayar Saba, D'ayan shagon Al'ameen ya shiga shagon gwanja bayan sun gaisa shima ya rokesa Koh zai samu bashin kudi Amma Kai dai wallahih D'an rainin wayo ne ya Ina Saida kayan Miya zakace na baka dubu hamsin duk kayan shagon nan aka sayar Ina zaiyi dubu hamsin, Haka yayita bin shagunan makwantansa Amma ba Wanda ya basa Koh sisi wasu kamma da bakar magana suke binsa dashi, A haka ya iso shagon Haladu shima yace baidashi,. Wajen bairon mangoron sa yaje ya bude ya tataba mangoron rabi duk sun lalace saboda yini da sukayi a rana Kuma a rufe, zabe masu kyau yayi Yana, D'auka yana sawa a k'wando ya shiga shagon Haladu dashi, Yana cewa, don Allah Haladu Koh zaka sayar mini da mangoro na zanje na zauna a asibiti na kwana biyu daidai Matata taji sauki Gaskiya bazan iyya sayar maka ba sai dai na saya kawai na sayar Nima na samu D'an riba, Ba damuwa Al'ameen yace Masa .....Nawane mangoron? D'ari takwas da hansim .....Zan baka dari biyar don Naga wasu sunyi laushi? Ba damuwa Allah ya saka musu albarka ......Ameen Kudin Haladu ya basa ya karba gida ya shiga ya bude kofar, da yake ya karbi key a hannun Khadija wanka yayi ya saka kayansa Jin ana Kiran la'asar yayi Alwala ya lalube takalmin Sumayya ya fita dashi a hannunsa, masallaci ya tafi yayi sallah ya wuce asibiti duk zuciyansa ba Dadi ya rasa wajen wa zai tinkara da zancen kudi,, yasan Koh mutuwa zaiyi Yan gidansu bazasu taimaka Masa ba bare Sumayya matar sa, ***Muna nan da Khadija har la'asar sallah mukayi dukan mu nurse tazo ta mayar mini da laidar ruwan a hannu na, Na kwanta baccine ya dauken nabar Khadija na zaune, Ya iso asibitin da sallama ya shigo dakin Khadija ta amsa masa. Sannu yaya ka dawo? Eh Khadija Toh yaya ka samu kudin? Wallahih Khadija sai addu'a naira 500 ne kadai na samu Amma yaya ya kamata ka sanar da Aunty gaskiya don wallahih Yaya Ina Jin tsoro kaga ance appendix in ya kumbura fa tunda Allah Bai baka ikon samu ba, ka fada Mata ita sai ta biya? Toh Khadija wallahih inajin kunya a matsayina na mijinta na kasa biya Mata kudin operation don samun lfyr ta, Habba Yaya karfa ka manta Allah yaga zuciyar ka baka dashine Kuma ba abin kunya bane tunda itama tasan baka dashi, Suna cikin Hira na farka a gigice Jin wani irin mahaukacin ciwon ciki ya tasarmin " Innalilahih wainnailaihir rajuun wayyo Allah na cikina" Subhanallah Sumayya cikin ne Al'ameen Daya Mike cikin tsananin tashin hankali yake lalubarta , Khadija ma da saurin ta ta iso ni,sannu Aunty take fada idon ta ya jika da hawaye *****Nikam.na kasa Bata amsa kuka kawai nake hankali tashe Khadija tashi kije ki Kira doctor eiiii sauri Toh yaya tace tana mikewa da saurin ta Al'ameen Kam hannun Sumayya ya Kama sai sannu yake Mata a hakan likita yazo ya sameta a halinnan Da sauri shida nurse suka rufu a kanta tare da K'ura Khadija da Al'ameen waje,allurai sukai Mata harda na bacci lokaci daya bacci ya dauke ta, Khadija da Al'ameen na tsaye a bakin kofa likita ya fitoh ya kira su zuwa office, Malam Al'ameen majinyaciyar ka tana cikin condition Mai muni ya kamata ka samo kudin aiki nan da awa uku ba wallahih kome zai iyya faruwa, Innalilahih wainnailaihir rajuun kawai suke fada, Suka mike zuka fita a office in Khadija Kam kuka ta fara abin Yama Al'ameen yawa ta Ina zai fara anya zai yafewa kansa kuwa in yar mutane ta mutu ata dalilin rashin kudin aikin da Bai samo ba, Yaya ya kamata Aunty tasan abinda ke faruwa muje ka fada mata ta Kama hannunsa sukayi dakin Suna shiga suka samu Sumayya na bacci .......... Yaya Ammar innan yazo baka nan ya bawa Aunty kudi Amma Taki karba tace na baka Allah sarki Ammar yazo ne? Eh yaya kana fita Yana shiga, yace ma Wai Daman Yaso kuyi sallama tafiya ne ya kamasa, na gaggawa, Allah sarki, Allah ya saka Masa da alkhari Yan kiyaye sa aduk inda yake, Ameen yaya Khadija Miko min kudin na hada da dari biyar in hannu na naje na Basu Koh zasu mata daidai a Nemo sauran su bimu bashi, Uhmm lallai yaya kadai San asibiti bata ma matum aiki ba tare da kudi bak'oh? Khadija bara dai naje na gwada Koh Allah zaisa a dace tunda kinga hour uku aka bamu kuma yanzun bacci take, bara naje na dawo ya fada Yana karban kudin da khadijar ke mika Masa, Yana fita yaje wajen biyan kudi, don Allah Dan uwa kayi hakuri ga dubu goma da dari bayar a fara mata aikin in yaso za'a cikita muku daga baya Dan Allah ku taimaka min matatace ba lfy kuma hour 3 aka bani ake son mata operation? Amma Kai *makahon* nan Ina ga baka zuwa asibiti ne taima? Ina zuwa ranka shi Dade sai dai ban taba kawo majinyaci irin wannan ba Toh gaskiya ka gannin nan Koh biyar naci a cikin kudin da nake karba wallahih Sai an daure ni Kuma anan in baka biya kudiba wallahih baza'a Mata aiki ba Koh mutuwa zatayi gwara kaje ka Nemo duk in da kudi ya shiga ya fita shawara nake baka,Amma zance a taimaka maka toh hadai asibiti ba Shikam tsabar damuwa har jiri yakeji yana ibansa ,a rayuwar yanzun in baka dashi kana ji kana gani harka mutu indai baka da kudin jinya ba Mai taimakon ka, zama yayi a bakin barandan pharmacy in yayi shuru cikin tashin hankali da alhini, Bayan fitar Al'ameen khadija na zaune har lokaci hawaye baibar zuba ba sai ta gogi wani ya zuba, har hour 1 yayanta Bai dawo ba, *** A hankali nabude idona na sauke akan Khadija dake ta hawaye ido harya kumbura abinka da farin fata fuska tayi ja" khadija lafiya kuwa meya faru Naga kina kuka"?? Babu Aunty Daman na tsorata ne danaga cikin ki ya Tashi Ashe haka kike fama da Jin jiki sannu, Murmushi nayi "haba Khadija Menene na kuka baki ga naji dauki ba" Toh Aunty, "Yauwa khadija nikam likita ya fadi abinda ke damuna ne, Koh yake sani ciwon cikin nan"? Kafun ta bude baki ma sai ga doctor ya shigo,Wai har yanzun baku samo kudin aikin ba Koh bakuji condition inda nace muku tana ciki ba Wai ina MAKAHON yake ne? "Doctor ban gane mikake nufi ba" nace ina kallon sa? Au baku fada mata bane? Yana kallon khadija alamar tambaya Eh doctor bata sani ba khadija ta bashi Amsa,, "Wai meke faruwa ne kun sani a duhu" waza'a ma aiki?? Kece appendix ya kumbura sosai tun jiya na sanar dasu Amma haryau shuru Basu biya kudiba yanzun haka hour 3 na Basu su kawo kudin Dan kina bukatan aiki gaggawa Amma an share hour 1 shuru, Banga alaman zasu biya ba Da mamaki nake kallon khadija"yanzun khadija Ina fama da wannan babbar matsala irin wannan Amma kuke mini Wasa da rayuwa Ina da kudin da Zan iyya biya ba bandashi ba" Kiye hakuri Aunty Daman Yaya ne yace shi yake son biya " Koh ance lallai sai yayanki ne ya wajaba ya biya ai ni Karan kaina nasan Bai dashi don Bai biya ba ai bazai zama wani abu na daban ba" menene riban ya fita yana neman bashi alhalin Ina da kudi"?? Kiye hakuri Aunty,ta fada jikinta a sanye ganin Raina ya baci "Nawane akace kudin aikin"? ......50k ne "Khadija tashi ki dauki key kije gida ki dauko mini jakana wani yellow a cikin whtdp nawa ki dauko mini jakan akwai kudi a ciki" Toh Aunty ta fada tana mikewa daukan key in tayi a jakan kayana ki hadamin da wayata ki dauko darduma babba da filo, ga kayan da nacire ma kikai mini gida kisa a basket in bayan kofa" "Kihau nepep ya kaiki kofar gida ki shiga in kin dauko kudin saiki shiga ya dawo dake ki basa 1k ya d'auki kudinsa karfa kice Zaki tafi da kafa"?? Toh Aunty ta d'auki kayan nawa ta fita a dakin, doctor Kam Dan kallo ya zama Daman tun da ya ganni yake ganin alamun Jin Dadi a tare Dani Amma abinda ya daure masa Kai mutanen da suka kawo ni asibitin abin yana bashi,mamaki harda Nurses Amma basuga fuskar tambaya ba **komawa nayi na kwanta shima doctor fita yayi Tsabar rudewa Khadija Koh yayanta Bata Lura dashi ba akan baranda ta wuce, Shikam ganin lokaci na wucewa yasa ya Tashi ya shigo dakin,da sallama a bakin sa, **Amsa Masa nayi Ina kallon sa yazo ya zauna a kujiran gefena, Sumayya,yakira sunana "Na'am" na amsa Masa Kiye hakuri Sumayya na kasa kula dake wallahih nayi iyya kokari na Amma ban samu kudin ba Daman appendix ne ke damunki Kuma ya kumbura, shine ake son Miki aiki kuma........ **Da nayi niyar rufesa da matsifa Amma sai jikina yayi sanyi Jin bayanin da yake mini" ban bare ya karasa ba na katse sa"ba kome, me amfanin Ina dashi kaje kana,.. baran attaimaka maka kazo ka biya mini kudin aiki"? Karka sake mini irin wannan banaso duk abin da zai taso a waje na Koh Khadija Koh Kai, in baka dashi karka sake zuwa gun wani da sunan ya taimaka maka indai abin baifi karfina ba pls" Kiye hakuri insha Allah bazan sake ba, **Shuru na Masa Jin Bata amsa ba ya sashi yin shuru Khadija na Isa gida ta samu jama'a na cike a kofar gidan dam alamu dai wani abinne ya furu don harda motar police ga jama'an unguwan makil............... 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin,Koh kinsan mace sai da kamshi da gyara* 😉 🍀🍀🍀🍀 *Turare suna d'ayace Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin sa* 🍀🍀🍀🍀 *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da* *gyara* 🍀🍀🍀 *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace* 🍀🍀🍀 *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE* 🍀 *Na tsunguno(habil)* 🍀 *Na jiki (kwalaccam)* ( *khumra, black & white* ) 🍀 *Turaren turara jiki after birth* , 🍀 *Na d'aki(halud Al'oud)* *UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* 💃🏼💃🏼 🍀🍀🍀 *Suna bada d'aya Koh sare akan farashi Mai Rahusa* 🍀🍀🍀 *Suna bada order kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria* Contact them vie 🪀08028827241 or 09033791049 IG @umsadincense 🪀my WhatsApp number 08084453785 08084453785 08084453785 0808445378508084453785 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya Ibrahim* 🍃 ✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwa 👌 Free book 🤧 Page 1️⃣2️⃣ Cikin tashin hankali Khadija ta nufi kofar gidan tana isa taga an fitoh da inno Akan kadon asibiti da ake daukan gawa Koh Mara lfy tana kwance Koh motse batayi aka shigar da ita Ambulance sai su Inna asabe da baba lami suke ta rusan kuka Kamar ana yankasu, Khadija Kam iyya rudewa ta rude ganin Yan matan gidan duka kuka suke harda wasu mazan ma Bappa Dayyabu da bappa sulaiman harda kawu tafawa suka shiga motar Yan sanda da gani dai abin Case ne babba Ta rasa wama zata tambaya ga Goggo Amina sai kuka take , Ganin lokaci na tafiya tasan yanzun bazata samu amsar tambayar taba yasa ta wuce kofar yayan ta shanyar kayan dazun da safe takai d'akin jakar ta dauka da Abubuwan da ta lissafa Mata duka,ta rufe kofar tayi kofar gida Da sauri ta fita daga gidan ganin har yanzun jama'a na tare Tam, Hospital ta wuce direct tana isa dakin ta baiwa Sumayya jakar, Budewa nayi na zaro kudi 50k na mikawa yayan khadija "ga kudin ka dau takardan khadija ta rakaka kuje ku biya" ...Toh Al'ameen yace Yana laluben kudin ya karba hade da zaro dubu goma da dari biyar in safiya da Khadija ta basa ya hada da dari biyar in mangoron sa,ki cire dubu goma da dari biyar a cikin kudin sai na hada Dana wajena na ciki ta na biya, "Ka bar na wajen Kan ai ba'a sallame niba zasu bukace mu Sai wasu abubuwan irin su hand gloves Koh ruwa da allurai duka ai bamu Gama kashe kudi ba ba iyya aikin bane kawai ka rike kudin a gunka," Toh khadija Tashi mu tafi Toh yaya, ta basa amsa **Fita sukayi nikam zuciyata tsinkewa ya ringayi da fargaba gani nake kamar bazan rayu ba, Waya ta da khadija ta kawo mini na dauka number abie na Kira Amma Bai dauka ba, Sake Kira nayi harna fidda tsammani naji ya dauka cikin sanyin jiki na Masa sallama"assalamu alaikum abie" Waalaikumu salam ke lafiya? Lafiya Alhamdulillah abie Daman na kiraka ne nace maka za'a mini operation yau don Allah Abie in nayi maka ba daidai ba kayi hakuri abie ka yafe mini bansan Inna shiga operation room xan fita da Rai Koh a mace ah ah shiyasa na kiraka naji muryarka abie ka samin albarka Koh xanga nasara a rayuwa ta Dan Allah" Keeeeeee!!!! ce Miki akayi in za'a ma mutum tiyata mutuwa yake ne kin wani kirani kina fadamin Zaki mutu ki mutum Mana keee!!!! bara ma na fada Miki daga yau karki sake kirana!!!! wallahih, tunda na aurar dake ki barni na huta mana, ***Hawaye ne keben fuskata Wai meke faruwa da rayuwa nane haka,, Yanzun mahaifina in ma ya juyamin baya, ganin shigowar Al'ameen da Khadija yasani share hawayen, "Khadija kin biya"? Eh Aunty.... Sunce 7:00 na dare za'a shiga operation room in, "Toh bara nayi sallah mangariba Koh kafun Azo a dauke ni" na fada zuciya takaraya sosai wallahih, Shima masallaci ya tafi nida Khadija mukayi Sallah muna idarwa na sakasu suci abincin da ya rage tun safe Basu sake saka kome a cikin su tun karyawan safe na taliya da wake,, Daker suka iyyaci Amma kadan nikam na kasaci tsabar fargaba, Karfe bakwai akazo za'a dauke ni, *** Da kafata na fitoh nurse suka sakani a gaba har nayi nisa Al'ameen ya k'wala mini Kira tsayawa nayi ya iso inda nake lalubar hannuna yayi ya rike cikin damuwa sosai nasan daurewa yake, Sumayya insha Allah Zaki fitoh cikin nasara kinji ki cire tsoro a ranki kinji Allah ne ya jarabceki Kuma insha Allah shizai baki lfy kinji, "Kukane ya k'wace mini yau wa'innan bayin Allah sune gatana a yau bani da kowa a kusa Dani sai su dame Zan biya su babu, Allah ne kawai xai biyasu" rungumar sa nayi cikin kuka nake cemai "insha Allah insha Allah" Lokaci fa na wuce wa ki shige mu tafi Naji muryan Nurse ***Sakensa nayi na rungumi khadija wance tun tuni kuka take, ***Na juya Ina tafiya a hankali Kamar wance k'wai ya fashewa a ciki sudai suna bin mu a baya har Muka Isa kofar operation room aka dakatar dasu tare da nuna musu su koma Kan kujirun d'ayan block in su zauna...... Bayan da Al'ameen baiyi ba Khadija ta koma gida taje ta kwanta Amma Taki tace anan zata kwana sai da ya nuna Mata Jan ido kafun ta yarda zata tafi 500 ya Bata ta hau nepep sauran change ta rike a hannun ta ,,, . godiya ta Mar sosai ,ta dauki kula ta fita,..... Zama Al'ameen yayi agun har akayi Kiran isha'i yaje yayi sallah yanata Addu'a Allah ya yasa aiyi aiki a sa'a ya Bata lfy(muma mukace Ameen) Bayan wasu hours Sumayya aka fitar akan gado tare da kayan tiyata da hulan duka Koh motse batayi aka kaita dakin da ake aje,wa'inda akama tiyata Basu farfado ba shima binsu yayi har dakin ya shiga sun dauke ta sun daura akan gadon dakin, kujira ya samu a Gefen gadon ya zauna ganin an shanja musu daki ba dakin emergency bane tashi yayi yaje ya tattara kayansu na dakin emergency ya dawo dashi dakin da take yanzun, zama yayi a Kan kujira, Har dare yayi sosai Bata farka ba, sai karfe 2 na dare ta farka tana fizge fizge bakin ta dauke da salati tana ambatan sunan abie yayi hakuri karya gujita itama,, Abirkice ya mike Yana kakamata ganin irin girgiza da take ya tsorata da sauri ya k'wala ma nurse inda ke dakin a zazzaune Kira ganin inyace zai tashi Sumayya zata iyya raunana kanta, Da gudu suka yi kanta suka kakamata surutai tayita Yi Akan Abie da salati sai Shan anjima kadan Sumayya ta koma bacci, Likita lafiya kam meke faruwa ne da Matata?ya fada hankalin sa a mugun tashe, Ka kwantar da hankalinka ana samun haka Daman in dai mutun zai farfado sai yayi ta sambatu,.. Toh doctor yace Yana komawa Kan kujiran ya zauna hannunta ya laluba ya rike yanajin wani irin tsoro a ransa, Har asuba Yana zaune sai da yaji ana Kiran sallah kafun. Ya Mike ya fita yaje yayi ya dawo ya cigaba da zama... Khadija Taki fadawa yayanta abinda ta gani a gidansu gudun kada hankalin sa ya tashi ta Sansa da saurin birkice wa gashi Yana fama da Sumayya tazo ta Kara Masa da wani Kuma, Keke napep tahau ta wuce a kofar gidan su Goggo Amina ta sauka ta biyasa kudinsa ta shiga gida da sallama. ...... Goggo Amina ta samu zaune sai rusan kuka take Kamar wance ake yanka namar jikinta, Da sauri ta karaso gareta cikin tashin hankali tana cewa Goggo Amina lfy menene ya farune wallahih tunda na tafi hankali na yaki k'wanciya? Wallahih Khadija kedai ki bare kawai mutanen gidan mu sun dawo kashe junansu, Kamarya Goggo ban gane ba? Toh dazun bayan la'asar iro ya dawo daga aiki yazo zaici abincin ranan sa ashe suwaiba( yar baba lami) ta dauka taci shine da yazo dauka yaga babu yake tambayan inno ya abincin sa babu a kula shine fati tace masa suwaiba ne taci, Tashin sa ba wani tunani ya zaro wayan wuta ainahin na bol ya zuba mata ita kuma da taji zafi tana ihu ta zari tabarya zata muka Masa, Inno Kuma ganin za'a bugawa iron ta tabarya tazo zata k'wace kawai tabarya ya sauka a kanta,shine fa Kika ga ta mike Koh motse batayi, Ni tsorona ma yanda naga Kan Bai fitar da jini ba kinsan akwai babban hatsari ka bugu irin wannan ace jini Bai fitoh ba, Shine iro ganin inno a yashe a kasa yaje ya ibo Yan sanda akazo aka tafi da suwaiba, gabaki daya gida ya hargitse su bappa nayinku duk sun bisu station wasu suna asibiti har hanzun ba'a San takamammen halinda inno ke ciki ba mutuwa Koh rayuwa😭😭😭 wayyo ni Aminatu, ta fada tana sake rushewa da kuka ita dai Khadija Allah ya kiyaye na gaba tace ta Mike taje ta ajiye kulan Sumayya a kitchen sai gobe zataje kofarta da safe,wanka tayi, tayi isha'i ta kwanta don batajin yunwa taci a asibiti,haka tayita juyawa Amma bacci yaki daukan ta tashi tayi ta Kama lafilfilu tana nemawa Aunty Sumayyan ta lfy da nasaran aiki sai 1 ta kwanta Bangaren Al'ameen bayan sallan asuba har lokacin yana zaune Dayake dakin da suke yanzun babban falo ne Mai dauke da majinyata masu yawa wa'inda aka ma operation shiyasa Basu kadai bane a dakin, sosai Yan dakin ke mamakin MAKAHON nan shin baida Yan uwane da zasu kula da wannan Mara lfy sai MAKAHO chap lallai Kam kowa gulma na cinsa( Niko nace gulma zai karku bazakuji kome ba) Tun asuba Khadija ta farka Bata koma. Bacci ba wanke wanken Goggo Amina ta fara ta hada harda kulan aunty ta duka ta wanke tayi shara tana Gamawa ta daura dumame ganin yau Goggo Kamar Mara lfy haka da tashi ,tana Gamawa ta dauki key sai gidan yayan ta, Yauma sai da tayi shara ta daura ruwan zafi Yana tafasa ta juye a flasks ta dafa indomie da kwai lokacin karfe 7:30 wanka tayi tasa kayan ta data dauko a gidan Goggon ta tadau abincin tayi hanyar FMC ****Da misalin karfe bakwai na safe na bude idona Wanda nakejin Kamar an zuba mini barkono a ciki a hankali na sauke k'wayan idanuna a kansa a zaune yake ya tasani a gaba Kamar wani Mai kallo yayi tagumi kallo daya zaka Masa kasan a cikin zullumi yake sosai....... 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin Koh kinsan mace sai da kamshi da* 😉 🍀🍀🍀🍀 *Turaren Suna d'ayane Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin* 🍀🍀🍀🍀 *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da gyara* 🍀🍀🍀 *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace* 🍀🍀🍀 *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE* 🍀 *Na tsunguno (habil)* 🍀 *Na jiki (kwalaccam) (khumraBlack & while*) 🍀 *Turaren turara jiki after birth* 🍀 *Na d'aki (halud Al'oud)* *UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* 💃🏼 💃🏼 🍀 *Suna bada kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria* *Contact them vie* 08028827241 or 09033791049 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya* *Ibrahim* 🍃 ✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwa👌 free book 🤧 Page1️⃣4️⃣&1️⃣5️⃣ Aunty' inno ta rasu tace tana Kara karfin kukanta, "Innalilahih wainnailaihir rajuun" Allah ya jikanta da rahama yasa ta huta" nace Ameen Aunty tace tana mikewa tadau hijab inta ta nufi cikin gida, **Banyi niyar zuwaba saboda jikina Amma ganin mutuwa ne Kuma Abu da gida babba hakan zai iyya zama abin magana, yasa na mike na fita zuwa cikin gidan, Ai ban tashi sanin Yan gidan ba sai da Naga manya da yara Suna kuka harda na tashin hankali kuka suke ba manya ba yara Mai makon a ma mamaci Addu'a sai ihu da kuka nidai Ina zaune a Gefen matan makwanta da suke shishigowa Ina kallon ikon Allah Al'ameen da wannan sanyin jikin ya iso kofar gida ya tarar da jama'a makil, inno ta rasu mutuwar ta dake sa sosai don alokacin sai da mutuwar mahaifiyar sa ta dawo Masa sabo,ganin yanda iro ke kuka Wanda yasan halin iro ba kome ke tsorata Sa bama Amma yau kuka yake, tabbas mutuwar iyaye akwai ciwo,(Allah kajikan iyayen mu) Ankai inno gidan ta na gaskiya yau har anyi sadakar bakwai gida ya koma kamar yanda yake kowa na sha'aninsa sai yaranta da sukayi sanyi kadan na rashin uwa, A tsawon satin nan na fahimci yayan Khadija baida aiki haka zaije yayi ta yawo Koh sisi bazai samuba ya dawo Yana kame kame taliya Koh Maggi Koh indomie nake iba na bawa Khadija takaima masu shago su Saya da araha kafun mu samu na shifenen Miya,.. Duk da Al'ameen baisan Ina Saida garana ba, karshe dai ajesa nayi nace ya fadamin me ke faruwa, dashine yanzun,duk lokacin da ya zauna baida aiki sai tunani, Tukum yamin bayanin bashi da jari yaje tashan kayan marmari sun hanasa bashi duk inda yaje su taimaka Masa sunki, ,"Amma menace maka in Abu ya taso ta wajenka bance ka ringa fada mini ba"? Hakane Sumayya Amma ni sai Inga Kamar ni ya dace in bukatar ki ya Tashi ki tambayi ni ba Zan ringa daura Miki nauyi ba, "Au aini ma nufina bashi Zan baka Amma Ina ni Ina baka kyautar kudi sai dai bashi " Duk da haka dai Sumayya.... Ban Bari ya karasa maganar Saba na tare sa "na baka bashin ne ka rufawa kanka asiri Koh na rike kudina ka cigaba da yawo ba aiki ga azumi saura wata biyu" "Kuma bara na gaya maka in azumi yazo kayan Dadi zakana sai min Kuma kamin kayan sallah harda Khadija kaji dai na fada maka" Toh shikenan abani yace Yana gyara zama alamun dai baida mafita, "Ka Bari sai gobe Zan baka" Washe gari Khadija na tura yaro yace tazo, ba'a jima ba sai gata aikanta nayi *say* *box* ta Kira mini Daya daga cikin yaran masu shagunan sai da wayoyi da laptop's suzo tare tace Masa amarya ce ni Kuma ban fara fita ba, Don nasan in na Bata laptop innan za'a Mata cinikin wulakanci ne kawai Koh ma wani ya Mata wayo ya gudu da laptop in don nasan say box ba irin mutanen da babu a ciki, Munyi ciniki da Mai sayan system in ganin yanda Yama laptop in cinikin wulakanci yasa nace na fasa sayar wa, Buhun flower na dauko a kitchen Daman ban taba bude Saba nace wa Khadija taje gun Haladu tace Masa xai Saya buhun flower Zan Masa sauki, Bata jima ba ta dawo tace min yace ta kawo flowern ya gani, Bata buhun nayi taje shagon Haladu ta sayar mini shima naira dubu bakwai ya Saya ba yanda na iyya haka na sayar Masa Amma ni Karan kaina nasan ba haka kudin yake ba, Yayan khadija na baiwa dubu uku yayi jari na rike dubu hudu na D'an Yi sayayyan abin bukata nayi irin su pad omo sabulu na baiwa Khadija dubu D'aya, tunda har yanzun Basu gyara Mana NEPAn kofar muba don sun biya ganin mu bamu biya ba sai suka yanke wayar kofar mu Khadija na baiwa dubu daya ta mikawa bappa sulaiman kudin wutan NEPAn mu aranan sukasa aka hada mana wayar aka gyara, na baiwa Khadija dari biyar itama 😉 Haka rayuwa tayi ta tafiya Rana ya wuce sati ya shude yau Dadi gobe Akatsen sa har Muka cika wata Daya da sati biyu da aure, ba abinda ya taba shiga tsakanin mu Koh da kuwa hada gado ne, in munkwana waje D'aya toh ana zafi munyi kwanan waje ba nepa, A y'an kwanakin nan na fara fuskantan matsen rayuwa Wanda ban Saba ba, Dole sai abinda ya samu zamuci wani sa'in ma in Bai samo kome ba haka zamuci indomie d'anye wani a dafe da ruwa, in ya samu D'an ciniki Kuma muci shinkafa da Mai da yaji,Inda Allah ya sumuma garana Bai kare ba akwai taliya Mai Maggi kefe shinkafa, Amma duk da haka na D'an fada na chanjin yanayi, saboda yanzun ya hanani Saida Kayana don har Yan unguwa sun fara gulman ya kasa rikeni Kayana nake sai dawa,maganan har kunnen da yashiga shiyasa ya nuna mini baya so , yau na shirya da niyar zuwa gidan Goggo Amina, da gidan mu tunda safe na kammala aikina yau mun Sami kudin kayan shaye mukasha da safe' bayan ya fita na kammala aikina dake na sanar dashi Zan fita gidan Goggo Amina ( marikiyar Khadija ) Zan bi gidan mu d'uka Bai Musa ba saboda mun Riga munyi maganar dashi, dari da hamsin ya bani kudin Keke, Khadija zata rakani kasancewar yaune Zan fara fita, unguwa tunda nayi aure bayan asibiti ba inda naje, Sai goma Khadija tazo lokacin na fitoh wanka, Muka gaisa ta shiga Wanka Dayake tun jiya ta zo ta guge kayanda zatasa d'aya Daga cikin Wanda nake Bata, Shiryawa nayi cikin lufaya Mai tsada fari Mai Flowers brown NASA riga long sleeve brown NASA takalmi fari na dau jakama fari fuskata ba kome sai powder da man baki, Khadija dake gefe na tsaye baki bude tana kallona, "Rufe bakin ga guda zai wuce ciki"nace Mata cikin murmushi Mai karawa fuskata kyau, Hmm Aunty na gaskiya ke Mai kyauce Allah ne kadai yasan dalilin da yasa ya bawa yayana wannan k'yakk'yawar hallintar nan Ina ma Yana kallo yaga yaran da za'a Haifa Masa 😅 Murmushi kawai nayi bance kome ba don na lura ita ta yara ma take, " Khadija kiye sauri kisa kaya don Allah na masu na ganni a gidan mufa Naga abie na" Toh Aunty tace tana saka dogon riganda na taba Bata,tayi shafe shafen ta tana Gama shiryawa, Muka fita" Yaune rana na farko Dana taba karewa unguwan sintali kallo unguwa ne da ya hada ruwa biyu masu kudi da talaka wa Yan kasuwa da ma'aikata da masu zaman banxa unguwan nada kyau sosai da fasali,.. Gidan Goggo Amina mukaje da kafa , Mun samu tarba Mai kyau ba laifi matar nada kirki sai dai na Lura ita mace ce da Bata shiga abinda Bai shafe taba Sam babu ruwanta,mun D'an jima a gidan kafun Muka Mata sallama na aje Mata laidan Turare Wanda na d'auka a kayan aure na, ta rakomu har waje Muka tare keke napep , Hajiya Ina kukayi? Ya tambaye ni "Specialist" zaka kaimu, Ku hau muje yace, Dukan mu Hawa mukai yaja machine insa muka nufe unguwan specialist, Muna shiga unguwan mu na Masa kwatancen inda zai sauke mu, "Yana sauke mu na tambayi sa "nawane kudin ka" Naira dari da hamsin kudin ku kubiyu, Sai a lokacin na tuna dari da hamsin inne a jikina kacal Wanda yayan Khadija ya bani Allah dai yasa abie na gida nasan zamu samu na dawowa don karyan mu taka da kafa daga specialist zuwa sintali, biyansa nayi muka nufi kofar gidan mu Khadija mutuwar tsaye tayi ganin wani irin gida Mai bala'in kyau Wanda Koh a mafarki Bata taba ganin irin Saba Daman ita ba yawo take ba iyya kacinta kasuwa sai unguwowin kusa da sintali irin mafindi unguwa gadi da sauran unguwowin kusa da unguwan su, Amma Bata taba zuwa unguwa Mai nisan nan ba sai dai tanaji a bakin Asma'u sunje unguwan specialist Koh millionaire's sweet in suna Bata lbrn gidajin unguwan sai taga Kamar tatsuniya suke Bata bata taba zaton haka gine ginen unguwan yake ba Wai duka wannan a cikin Jala yake? ***Harna nufe get Amma sai naji Kamar ba Khadija a gefena juyawa nayi me Zan gani Khadija an sake hanci baki ido ana kalle kalle zuwa kawai nayi na jaho hannunta, sai a lokacin ta farga da kauyancin da ta nuna Cikin Jin kunya tace Aunty wallahih unguwan nan yayi kiga gidan da zamu shigan nan Kamar aljannan duniya, Kai Khadija kin cika shirme wallahih mu tafi nikam, **Get Muka nufa Mai girman gaskiya kamar get In gidan prison haka ma ginin gidan dogayene sosai anyi penti fari get in ma farine k'wank'wasa,makeken kofar get in,nayi Wani farin buzune ya leko ganina yasa ya washe bakinsa cikin hausar sa da baya fita yake cewa laaa Amarya Kaine hajiya Sumayya wallah nayi kewanka shannu da zuwa lale lalema barkama lale ya fada Yana bude mini get muka shiga, Shiga cikin gidan mu ya sake ruda Khadija ganin filin gidan mu filine babban bana Wasa ba Wanda yakai girman wani karamin unguwa,ga shuke shuke na Flowers ya kewaye gidan Wanda ya kara haska gidan sosai ga parking space babba Mai dauke da mototi na alfarma wanda akalla zasu Kai talatin duk ciki bamai araha, Nidai Ina rike da hannun Khadija Muka nufi wani babban part Wanda duk fadin gidan part inne kawai ba wasu Amma daga ganin part in kasan ba karamin duniya bace a ciki ganin shima ginine na gidan sama Mai Hawa uku,babban kofar falon NASA hannun na na bude da sallama a bakine duk da banida tabbacin za'a ji,saboda girman falon, Khadija Kam mutuwar tsaye ta sake tayi ganin cikin falon gidan mu, Kusa Kai mukayi cikin falon falone Mai girman gaskiya Wanda ke dauke da kujiru set biyar ga babban plasma na alfarma Kai fadar tsaruwar falon gidan mu Bata lokaci ne na barwa readers su keyasta, Babban falon gidan mu Yana dauke da d'akuna kusan Sha biyar haka upstairs shima dakuna goma Sha biyar ne Hawa na uku ma haka,Amma duk yawan d'akunan gidan munan falon mu dayane shine falon kasa, Wanda Koh a Hawa na uku kake kana hango falon, d'akunan kasa na samarine sai kakarmu dake zaune dasu a kasan Wai tana saka musu ido injita, dakunan Hawa na biyu na iyaye ne Hawa na uku shine na Yan Mata da d'akunan yaran gidan da sukayi aure maza,suna zaune da iyalansu ,.. duk yanda Zan fasalta muku gidan mu saifa na rage wani abin, Kaf gidan mu da colour D'aya aka kawatashi da white colour sai surkin baki Kama daga kujiru labule Abubuwan da aka kawata gidan kome farine daga sama har kasa abin sai Wanda ya gani, Jama'ar gidan mu duk Muka samu a falo da yake yau weekend ne ba aiki ba makaranta kowa na zaune wasu na kallo wasu na Danna waya wasu na Danna laptop yara na wasa wasu abinci suke ci ganin mu yasa dukansu barin abinda suke suka zuba Mana ido Kamar yau suka fara ganina,tunda Khadija ce Basu sani ba, Idanuna ne ya sauka a Kan kakata dake zaune tanacin kefe sai uncle's nawa dake zazaune wasu na cin abinci wasu na Hira wasu na duba takardu, wani abune ya tsayamin a makoshi Mai kamada Takaici sun aurar Dani Basu damu da rayuwar da nake ashan ba gasuna suna zaunen su Kamar Basu San wata Sumayya da aka bawa MAKAHO ba Basu neme sanin ya rayuwa ta kare ba waima me dalilin auran Dani ne tunda gasu Aunty miemie sun girme ni nesa ba kusa ba Amma saini kadai aka aurar auren ma da MAKAHO ba lafiyaye ba,Koh don anga mahaifiyata Bata gidan ne Kai Koh mahaifiyata Bata gidan ai ubana nanan Koh da kowa zai nuna Mini kiyayya dada zata sassauta tunda ita ta haifi babana amma Ina abin ba sauki, "Ina kwana dada,"nace Ina zama a cikin Daya daga cikin kujirun falon, Toh matan miskinai ne agidan namu yau Koh idonane,? Ah ah Kaka ba idon ki bane kinsan azumi ya karatoh anzo amsan zakkah ne, Hhhhhh Kai miemie baki da dama Amarya ce fa tazo ganin gida mutun da gidansu kece yazo karban zakkah,kubra ke fada tana dad'a tunsirewa da dariya Waiku yaran nan wasu irin Yan iska ne me yasa baku da mutunci shegu kawai ai gwara ita tayi aure Koh? Keee koh miskini kin samu yazo wajen kine da sunan aure, a cikin ku waye ta samu miskinin na zuwa wajenta,Yaya Abdu ya fada ransa a bace, Ai itama ba zuwa yayi ba lika Masa akayi,miemie ta basa amsa,.. Rufe mini baki karna ci ubanki Yar iska Abdul yace Yana mikewa, Ai duk laifin dadane Sam bansan me yasaba, Dada (kakar mu) itace babba Amma ita ke sasafo Mana bala'i yaya kabiru yace Yana maijin takicin ahlin gidansu, Abubakar kanajin abinda shegen yaron Kan nan kabiru yake shimin mutunci kayi shuru kana kallonsa,,, Kiye hakuri Dada Kai kabiru zanci kaniyarka fa inka sake shiga abinda ba ruwanka uwarka aka zaga Koh me da zaka saka bakinka a ciki, Mikewa Kabir da Abdul sukayi sukabar falon, Ganin yanda aka Mai Dani Kamar kashi ba Wanda yabi ta kaina kowa na Harkan gabansa Ganin Banga Abie na a cikin falon ba yasa na mike nayi hanyar upstairs na nufi d'akin sa nabar Khadija a falo wance ke rakube Kamar ace kitttt ta ruga, Bude kofar d'akin nayi nasa kaina na shiga Abie nane zaune a kasan tiles Yana duke da Kai sai momy (yadikko na) zaune a bakin gado daga Gani dai magana suke.................. 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin,Koh kinsan mace sai da kamshi da gyara* 😉 🍀🍀🍀🍀 *Turare suna d'ayace Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin sa* 🍀🍀🍀🍀 *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da* *gyara* 🍀🍀🍀 *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace* 🍀🍀🍀 *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE* 🍀 *Na tsunguno(habil)* 🍀 *Na jiki (kwalaccam)* ( *khumra, black & white* ) 🍀 *Turaren turara jiki after birth* , 🍀 *Na d'aki(halud Al'oud)* *UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* 💃🏼💃🏼 🍀🍀🍀 *Suna bada d'aya Koh sare akan farashi Mai Rahusa* 🍀🍀🍀 *Suna bada order kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria* Contact them vie 🪀08028827241 or 09033791049 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya Ibrahim* 🍃 ✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwa 👌 Free book🤧 Page 1️⃣3️⃣ Bayan fitar Ammar Khadija ta kirga kudin dubu goma ne,Mika min tayi, Aunty ga kudin "Ajjye Khadija in yayanki yazo ki basa tunda shike fama da zirga zirgan asibiti" toh Aunty ta bani Amsa tana aje kudin a cikin ak'watin Kayana, Al'ameen na fita daga asibiti da kafa ya koma har gida Dayake akwai sanda in Kuma yazo titi sai ya Kama yara su tsallakar dashi Yana Isa unguwan su(sintali) wajen shagunan bakin titi ta inda yake sai da mangoro a bakin su, Shagon malam shu'aibu ya fara zuwa don shine yafi masu shagunan abin arziki sosai alayin da sallama a bakinsa ya shiga shagon, Assalamu alaikum malam shu'aibu Waalaikumu salam Mai mangoro ne? Eh nine malam shu'aibu barka da jama'a Barka dai lafiya Kam Naga yau tun safe danazo bude shago Naga hulbairon ka a rufe dazun na aiki yaron gidana ya karbo mini yako yake fadamin baka nan? Eh wallahih malam shu'aibu iyalina ne ba lfy jiya na kaita asibiti, Allah sarki ya jikin nata? Da sauki Daman nace bara nazo ka taimaka mini da kudi dubu hamsin za'a Mata aikine appendix ya kumbura a cikin ta don Allah ka taima kamin, Kutt lallai ma a karnin nan da kowa ke takai takai Ina Zan iyya daukan kudi har 50k na baka da sunan bashi, bayan anyi operation in Ina zaka samu kudina ka biyani, gaskiya bazan boye maka ba ni nan Koh biyar bazan iyya baka ba banaji ance Yar masu kudi aka aura maka ba me yasa danginta bazasu Mata jinya ba tunda sunsan baka dashi Daman suka baka ita Shikinan malam shu'aibu na gode, ya fada Yana fita ba tare da ya basa amsar tambayar Saba, D'ayan shagon Al'ameen ya shiga shagon gwanja bayan sun gaisa shima ya rokesa Koh zai samu bashin kudi Amma Kai dai wallahih D'an rainin wayo ne ya Ina Saida kayan Miya zakace na baka dubu hamsin duk kayan shagon nan aka sayar Ina zaiyi dubu hamsin, Haka yayita bin shagunan makwantansa Amma ba Wanda ya basa Koh sisi wasu kamma da bakar magana suke binsa dashi, A haka ya iso shagon Haladu shima yace baidashi,. Wajen bairon mangoron sa yaje ya bude ya tataba mangoron rabi duk sun lalace saboda yini da sukayi a rana Kuma a rufe, zabe masu kyau yayi Yana, D'auka yana sawa a k'wando ya shiga shagon Haladu dashi, Yana cewa, don Allah Haladu Koh zaka sayar mini da mangoro na zanje na zauna a asibiti na kwana biyu daidai Matata taji sauki Gaskiya bazan iyya sayar maka ba sai dai na saya kawai na sayar Nima na samu D'an riba, Ba damuwa Al'ameen yace Masa .....Nawane mangoron? D'ari takwas da hansim .....Zan baka dari biyar don Naga wasu sunyi laushi? Ba damuwa Allah ya saka musu albarka ......Ameen Kudin Haladu ya basa ya karba gida ya shiga ya bude kofar, da yake ya karbi key a hannun Khadija wanka yayi ya saka kayansa Jin ana Kiran la'asar yayi Alwala ya lalube takalmin Sumayya ya fita dashi a hannunsa, masallaci ya tafi yayi sallah ya wuce asibiti duk zuciyansa ba Dadi ya rasa wajen wa zai tinkara da zancen kudi,, yasan Koh mutuwa zaiyi Yan gidansu bazasu taimaka Masa ba bare Sumayya matar sa, ***Muna nan da Khadija har la'asar sallah mukayi dukan mu nurse tazo ta mayar mini da laidar ruwan a hannu na, Na kwanta baccine ya dauken nabar Khadija na zaune, Ya iso asibitin da sallama ya shigo dakin Khadija ta amsa masa. Sannu yaya ka dawo? Eh Khadija Toh yaya ka samu kudin? Wallahih Khadija sai addu'a naira 500 ne kadai na samu Amma yaya ya kamata ka sanar da Aunty gaskiya don wallahih Yaya Ina Jin tsoro kaga ance appendix in ya kumbura fa tunda Allah Bai baka ikon samu ba, ka fada Mata ita sai ta biya? Toh Khadija wallahih inajin kunya a matsayina na mijinta na kasa biya Mata kudin operation don samun lfyr ta, Habba Yaya karfa ka manta Allah yaga zuciyar ka baka dashine Kuma ba abin kunya bane tunda itama tasan baka dashi, Suna cikin Hira na farka a gigice Jin wani irin mahaukacin ciwon ciki ya tasarmin " Innalilahih wainnailaihir rajuun wayyo Allah na cikina" Subhanallah Sumayya cikin ne Al'ameen Daya Mike cikin tsananin tashin hankali yake lalubarta , Khadija ma da saurin ta ta iso ni,sannu Aunty take fada idon ta ya jika da hawaye *****Nikam.na kasa Bata amsa kuka kawai nake hankali tashe Khadija tashi kije ki Kira doctor eiiii sauri Toh yaya tace tana mikewa da saurin ta Al'ameen Kam hannun Sumayya ya Kama sai sannu yake Mata a hakan likita yazo ya sameta a halinnan Da sauri shida nurse suka rufu a kanta tare da K'ura Khadija da Al'ameen waje,allurai sukai Mata harda na bacci lokaci daya bacci ya dauke ta, Khadija da Al'ameen na tsaye a bakin kofa likita ya fitoh ya kira su zuwa office, Malam Al'ameen majinyaciyar ka tana cikin condition Mai muni ya kamata ka samo kudin aiki nan da awa uku ba wallahih kome zai iyya faruwa, Innalilahih wainnailaihir rajuun kawai suke fada, Suka mike zuka fita a office in Khadija Kam kuka ta fara abin Yama Al'ameen yawa ta Ina zai fara anya zai yafewa kansa kuwa in yar mutane ta mutu ata dalilin rashin kudin aikin da Bai samo ba, Yaya ya kamata Aunty tasan abinda ke faruwa muje ka fada mata ta Kama hannunsa sukayi dakin Suna shiga suka samu Sumayya na bacci .......... Yaya Ammar innan yazo baka nan ya bawa Aunty kudi Amma Taki karba tace na baka Allah sarki Ammar yazo ne? Eh yaya kana fita Yana shiga, yace ma Wai Daman Yaso kuyi sallama tafiya ne ya kamasa, na gaggawa, Allah sarki, Allah ya saka Masa da alkhari Yan kiyaye sa aduk inda yake, Ameen yaya Khadija Miko min kudin na hada da dari biyar in hannu na naje na Basu Koh zasu mata daidai a Nemo sauran su bimu bashi, Uhmm lallai yaya kadai San asibiti bata ma matum aiki ba tare da kudi bak'oh? Khadija bara dai naje na gwada Koh Allah zaisa a dace tunda kinga hour uku aka bamu kuma yanzun bacci take, bara naje na dawo ya fada Yana karban kudin da khadijar ke mika Masa, Yana fita yaje wajen biyan kudi, don Allah Dan uwa kayi hakuri ga dubu goma da dari bayar a fara mata aikin in yaso za'a cikita muku daga baya Dan Allah ku taimaka min matatace ba lfy kuma hour 3 aka bani ake son mata operation? Amma Kai *makahon* nan Ina ga baka zuwa asibiti ne taima? Ina zuwa ranka shi Dade sai dai ban taba kawo majinyaci irin wannan ba Toh gaskiya ka gannin nan Koh biyar naci a cikin kudin da nake karba wallahih Sai an daure ni Kuma anan in baka biya kudiba wallahih baza'a Mata aiki ba Koh mutuwa zatayi gwara kaje ka Nemo duk in da kudi ya shiga ya fita shawara nake baka,Amma zance a taimaka maka toh hadai asibiti ba Shikam tsabar damuwa har jiri yakeji yana ibansa ,a rayuwar yanzun in baka dashi kana ji kana gani harka mutu indai baka da kudin jinya ba Mai taimakon ka, zama yayi a bakin barandan pharmacy in yayi shuru cikin tashin hankali da alhini, Bayan fitar Al'ameen khadija na zaune har lokaci hawaye baibar zuba ba sai ta gogi wani ya zuba, har hour 1 yayanta Bai dawo ba, *** A hankali nabude idona na sauke akan Khadija dake ta hawaye ido harya kumbura abinka da farin fata fuska tayi ja" khadija lafiya kuwa meya faru Naga kina kuka"?? Babu Aunty Daman na tsorata ne danaga cikin ki ya Tashi Ashe haka kike fama da Jin jiki sannu, Murmushi nayi "haba Khadija Menene na kuka baki ga naji dauki ba" Toh Aunty, "Yauwa khadija nikam likita ya fadi abinda ke damuna ne, Koh yake sani ciwon cikin nan"? Kafun ta bude baki ma sai ga doctor ya shigo,Wai har yanzun baku samo kudin aikin ba Koh bakuji condition inda nace muku tana ciki ba Wai ina MAKAHON yake ne? "Doctor ban gane mikake nufi ba" nace ina kallon sa? Au baku fada mata bane? Yana kallon khadija alamar tambaya Eh doctor bata sani ba khadija ta bashi Amsa,, "Wai meke faruwa ne kun sani a duhu" waza'a ma aiki?? Kece appendix ya kumbura sosai tun jiya na sanar dasu Amma haryau shuru Basu biya kudiba yanzun haka hour 3 na Basu su kawo kudin Dan kina bukatan aiki gaggawa Amma an share hour 1 shuru, Banga alaman zasu biya ba Da mamaki nake kallon khadija"yanzun khadija Ina fama da wannan babbar matsala irin wannan Amma kuke mini Wasa da rayuwa Ina da kudin da Zan iyya biya ba bandashi ba" Kiye hakuri Aunty Daman Yaya ne yace shi yake son biya " Koh ance lallai sai yayanki ne ya wajaba ya biya ai ni Karan kaina nasan Bai dashi don Bai biya ba ai bazai zama wani abu na daban ba" menene riban ya fita yana neman bashi alhalin Ina da kudi"?? Kiye hakuri Aunty,ta fada jikinta a sanye ganin Raina ya baci "Nawane akace kudin aikin"? ......50k ne "Khadija tashi ki dauki key kije gida ki dauko mini jakana wani yellow a cikin whtdp nawa ki dauko mini jakan akwai kudi a ciki" Toh Aunty ta fada tana mikewa daukan key in tayi a jakan kayana ki hadamin da wayata ki dauko darduma babba da filo, ga kayan da nacire ma kikai mini gida kisa a basket in bayan kofa" "Kihau nepep ya kaiki kofar gida ki shiga in kin dauko kudin saiki shiga ya dawo dake ki basa 1k ya d'auki kudinsa karfa kice Zaki tafi da kafa"?? Toh Aunty ta d'auki kayan nawa ta fita a dakin, doctor Kam Dan kallo ya zama Daman tun da ya ganni yake ganin alamun Jin Dadi a tare Dani Amma abinda ya daure masa Kai mutanen da suka kawo ni asibitin abin yana bashi,mamaki harda Nurses Amma basuga fuskar tambaya ba **komawa nayi na kwanta shima doctor fita yayi Compilied By Abubakar Saleh AlQuyraemey Whatsapp Number 08138873799 Visit www.rumbunlabarai.com For More Complete Documents Tsabar rudewa Khadija Koh yayanta Bata Lura dashi ba akan baranda ta wuce, Shikam ganin lokaci na wucewa yasa ya Tashi ya shigo dakin,da sallama a bakin sa, **Amsa Masa nayi Ina kallon sa yazo ya zauna a kujiran gefena, Sumayya,yakira sunana "Na'am" na amsa Masa Kiye hakuri Sumayya na kasa kula dake wallahih nayi iyya kokari na Amma ban samu kudin ba Daman appendix ne ke damunki Kuma ya kumbura, shine ake son Miki aiki kuma........ **Da nayi niyar rufesa da matsifa Amma sai jikina yayi sanyi Jin bayanin da yake mini" ban bare ya karasa ba na katse sa"ba kome, me amfanin Ina dashi kaje kana,.. baran attaimaka maka kazo ka biya mini kudin aiki"? Karka sake mini irin wannan banaso duk abin da zai taso a waje na Koh Khadija Koh Kai, in baka dashi karka sake zuwa gun wani da sunan ya taimaka maka indai abin baifi karfina ba pls" Kiye hakuri insha Allah bazan sake ba, **Shuru na Masa Jin Bata amsa ba ya sashi yin shuru Khadija na Isa gida ta samu jama'a na cike a kofar gidan dam alamu dai wani abinne ya furu don harda motar police ga jama'an unguwan makil............... 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin,Koh kinsan mace sai da kamshi da gyara* 😉 🍀🍀🍀🍀 *Turare suna d'ayace Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin sa* 🍀🍀🍀🍀 *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da* *gyara* 🍀🍀🍀 *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace* 🍀🍀🍀 *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE* 🍀 *Na tsunguno(habil)* 🍀 *Na jiki (kwalaccam)* ( *khumra, black & white* ) 🍀 *Turaren turara jiki after birth* , 🍀 *Na d'aki(halud Al'oud)* *UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* 💃🏼💃🏼 🍀🍀🍀 *Suna bada d'aya Koh sare akan farashi Mai Rahusa* 🍀🍀🍀 *Suna bada order kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria* Contact them vie 🪀08028827241 or 09033791049 IG @umsadincense 🪀my WhatsApp number 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya* *Ibrahim* 🍃 ✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwa👌 free book 🤧 Page1️⃣6️⃣&1️⃣7️⃣ Shigowa d'akin nayi cikin hanzari na karasa kusa da abie na banyi wata wata ba na rungume sa na fashe da kuka maicin Rai,,,, Ji kawai nayi momy ta dakawa abie tsawa, Kai Abdulsalam mainace maka akan yarinyar nan?, Ai da sauri Naga Abie ya hankad'ani a jikinsa ya mike tsaye cikin wani irin hada fuska Wanda. Bansan abiena dashi ba Naga ya mike cikin hargage yake magana Sumayya fita a dakin nan banason ganin ki banace Miki bake bani ba Koh bance ki zauna a dakin kiba, "Abie Kai nazo gani don Allah Abie Koh kowa zai juyamin baya Kai karka Bari a rabamu don Allah Abie," nace Ina fashewa da kuka, Waye uban naki?? keh daga yau niba ubanki bane bansan wata y'a Sumayya ba kaf zuriyan shugaba babu yarinya Mai suna Sumayya ki fita a gidan nan da zuriyan mu bake bani Koh mutuwa nayi banason ganinki akan gawata,yace idanunsa na taruwa da hawaye daga Gani dai maganar fatar bakine bana zuciya ba, "Amma abie menene nai maka da har zaka yanke dukkan alakar ka Dani har haka atunani na Koh kashe mutum nayi bazaka yanke alaka Dani ba abie ka rabani da mahaifiyata tun bansan kaina ba yanzun Kuma ka sallamawa duniya ni" wa nake dashi in ba kaiba kaf duniya nan abie why Abie why"😭😭?? Nafada Ina kallonsa gani nayi hawaye nabin fuskar sa,ya daga ido Yana kallon momy, Toh munafuki kallon me kake mini,Ke Kuma wuce ka sata a gaba tabar Mana cikin gida yanzun, Nikam mutuwar tsaye nayi nashiga uku yaushe abie ya zama haka zaushe ya koma yaron momy,abie da na sani ne kuwa kafun na bar gidan nan Koh maganar banxa momy Bata Isa tamin a gabansa ba bare yau har tana basa umurni ya koreni, Ban farga ba naji an janii kiiiiiii!!! Anyi hanyar steps Dani, Cikin mamaki nake kallon abie yau ni yake ja Kamar wata saniya zai koreni a gidan sa lallai fa, Jana yake tayi har Muka sauko falo abin gwanin tausayi,nikam kuka nake Kamar Raina zai fita gabaki d'aya naji duniya tamin zafi, Ganin abie ya nufi kofar fita falo Dani yasa Khadija tasowa ta biyomu a baya Yan falonka da ido suka bimu wasu na dariya ganin yanda uba ke fincikar yarsa Fincike hannuna nayi na dawo cikin falon na tsaya a gaban babuji (kanin babana) " babuji abani ducument Ina, Ina bukatar su," Don ubanki lokacin da uwarki ta haife ki da results ta haifiki ne,,,,, Don haka baza'a bayar ba koma bara ma kiji daga yau Koh a kasuwa ne karki sake hada sunanki da family shugaba, "K'warai kayi gaskiya babuji ba'a haifini da results ba Amma da kudin ubana na same su in Kuma hassadace yasa kuka k'wace karfa ku manta arziki nufin Allah ne in Allah ya tsaga da rabonka sai kayi arziki ruwa da iska Koh guguwa bazai Hanaka samuba", "Ba karatu bane kadai abinda ke sa bawa arziki rabonsa baya wuce kansa" "Baiwa ta jarina"sannan wannan tsinannen gidan naku wallahih ku rubuta ku aje sai yafi muku prison ganin.................. Tassss naji saukar wani azabebben Mari a kumatu na Wanda yasani sumar wucen gadi,ba kowa bane yamin Marin nan sai sahabi yaron babuji, Ke karamar Yar iska watoh kema harkin zama Yar bariki irin mutanen gidan da kike Koh zakizo nan ki gwada Mana kin falle toh baki Isa ba ki tsaya kina gayama ubana magana in barki ya fada Yana fincikata juyawa nayi Ina kallon abie Wanda ke tsaye kansa a duke, Bai tsaya aku Ina Dani ba har Saida ya dangana da get turani yayi waje Yana ma Mai gadi warning daga yau in ya sake barin Mai Kama Dani ya shigo gidan nan a bakin aikin sa,Yana fadan haka ya juya abinsa yayi cikin gida, ya dauko jakana da takalmi ya watso mini a jiki, Baba buzune ya fitoh yazo inda nake zaune tunda ya jefoni ban matsa ba mamaki tsoro da kuma wani irin tsana naji ya tsargan mini na family mu duka ban cire kowa ba, aciki nayi alkawari daga yau na yanke duk wata alaka da shugaba family house, Kayi hakuri yaro haka rayuwa take kaji, kayi zaman auren ka ka rike mijinka Allah zai baka mafita kaji hajiya Sumayya,kayita addu'a kaima Allah ya tsareka gidan nan yanzun sai abinda matar babanka yace, ya fada cikin tausayi,nidai Ina duke dakai sai kuka nake inda Allah ya Soni ma unguwan mu ba irin sintali bane nan kowa na cikin gidan sa Babu mutane a waje, Jin ana kamani anason mikar Dani yasa na daga kaina Khadija ce wance bansan yaushi ta fitoh ba ,Ashe tun Marin da aka kwada mini ta ruga tayi waje tazo ta Saya,... *******"""" Banyi musu ba na nike tsaye Kayana ta hau karkade mini nidai sai kuka nake Kamar zararriya gashi bamuda Koh sisi da zamu tare abin Hawa ya kaimu gida gashi Koh a gidan ma bani da kudin da Zan biyasa Kuma banda tabbacin yayan Khadija na dashi, yasa na Kama tafiya da kafa Ina kuka, Dukawa Khadija tayi ta dauki jakana Dana Bari,sai hakuri take bani Amma nai Mata banza a haka muka fara fasa hanya, Mota na gani Tasha gaban mu tayi packing Abdul ne ya fitoh a ciki ya nufe mu, don Allah Sumayya kiye hakuri da abinda kikaje Kika tarar a gida wallahih yanzun gidan mu sai addu'a abin sai gaba gaba yake, Kuma na rasa me yasa duk gidan mu ke suka tsana, *****Kala bance Masa ba don shima wani tsanar sa nakeji a Raina Sam yanzun naji banason ahalina kwata kwata na yanke duk wata alaka dasu daga yau Kamar yanda Suma suka yanke Dani, ***Kaucewa nayi na fara tafiya bance Masa kala ba, Biyo ni ya sake Yi Yana mini magiya, Sumayya don Allah badon ni ba kizo ki hau na kaiki gidanki Kinga yamma yayi bazaki samu Keke napep ba anjima anan, Wallahih Abdul Ina Ganin kimarka Inka kuskura ka kaini bango Zan maka abinda bazaka manta Dani ba Kai asuwa zakazo ka tsaya kana bani umurni wallahih daga yau Babu ni Babu Kai Koh a hanya ban sanka ba na tsaneku mugaye kawai azzalumai wallahih ku jira karshin ku, Habba Sumayya menene laifina in sun Bata Miki ni meyasa Zaki had'a Dani,.. "Ai Wanda suka Bata mini su waye ne a gunka"?na tambaye sa Ina kallon sa ido cikin ido, Iyayen mune da Yan uwan mu,ya bani Amsa, "Iyayen kadai da Yan uwanka daga yau bana D'aya daga cikin family shugaba in baka sani ba ka sani yanzun ka fita harka ta " Sumayya kada bacin Rai yasa ki ringa furta maganganu da Basu dace ba, "Na furta Abdul Koh kaima dukana zakayi" na fada Ina wuce sa Shikam mamaki ne yake son kashesa Anya Sumayya da ya sani ce wannan shuru shurun ashe haka take ganin bazata yarda tahau motarba yasa ya zare kudi a Aljuhunsa ya mikawa Khadija gashi Yan Mata kuhau Keke Koh ya fada Yana duban Khadija,.. "Wallahih Khadija Kika karbi kudin nan sai na nuna Miki true colour na" Khadija Kam ta tsorata da sauri tayi gaba kamar yanda taga nayi, Muka barsa a tsaye kamar gunki, Tafiya muke har lokacin hawaye baibar zuba a. Idanuna ba wani irin zafi nakeji a Raina a haka muka ringa fasa unguwa unguwa muna wucewa tafiyarda tunda nake. Bantaba yin irinsa ba yau shi nake kafafuna duk sun kumbura na rashin sabo, Amma yanda zuciya ke cina Bai bare naji wahalar ba, Khadija kam Koh a jikinta, Har mangariba yayi bamu ma kusa Isa sintali ba Aunty Koh zamu tare kekene in munje gida Yaya ya biya Kinga fa mangariba yayi ga hadari sosai? Khadija tace Kala bance Mata ba tafiya kawai na cigaba dayi don nasan Koh na hau munje bazamu samu kudi ba tunda cinikin nasa duka ya hada ya bani Ina zai samu wasu dari da hamsin, Tafiya mukaci gaba dayi ga yunwa don rabona da abinci tun ruwan shayen safe Amma bacin Rai baisa naji ba har aka Kira Isha adaidai lokacin aka fara yayafi sai ruwa ya sauko Kamar da bakin k'warya ganin mun iso bakin kasuwa yasa ban tsaya wani labewa ruwa ya dauke ba tunda dare ne Babu Wanda zai gane mu gashi NEPA sun dauke a haka ruwa na dukan mu muka shiga sintali hanyar gidana muka nufa tun daga nesa Muka hangesa Al'ameen ne a tsaye a kofar gida ruwa na dukansa daga ka gansa kaga Wanda hankalin sa yake tashe, Muna Isa Khadija ce ta fara Masa magana nikam cikin gidan na nufa don bana bukatar Jin kome, Yaya ya Naga kana tsaye a cikin ruwa haka gashi duk ka jika lafiya Kam? Ina Naga lfy Khadija baku dawo ba Ina Aunty take Allah dai yasa Yan gidan su basuce bazata dawo ba wallahih naji tsoro Khadija karsuce zasu rabamu? Hhhh habba Yaya bafa wani abu da zai rabaka da matarka insha Allah sai mutuwa Kama daina mugun tunani irin wannan, maganan dadewa Kuma abin hawane bamu Bamu ba da wure, shiyasa naso ma mu kwana Amma Aunty tace mu dawo kar hankalin ka ya Tashi(Tamar karya don ya kwantar da hankalin sa) Shap in kuka kwana ai nashiga uku kenan , Amma me yasa baku Kama hanya da wure ba kuka bare sai yamma kuka fitoh,gashi ruwa ya muku duka, ..Kai Yaya abinci fa muka tsaya muka ci, Yauwa Yaya kasan me yau ran aunty a bace yake don Allah ka bita. A hankali inda Hali ma karka Mata magana yanzun ka Bare sai da safe ka Mata magana in ma kaga change a tare da ita ka Mata uzuri, Meya faru Khadija? Ba kome Yaya kawai dai sun D'an samu matsala da yaran gidansu ne sai Randa ya baci, Bai yarda ba don yasan halin Khadija akwai surutu akwai boye abinda ba'a sata fada ba,shiyasa kawai ya shanja zancen, Toh khadija muje ciki in ruwan ya tsakai ta sai na raka ki gida Ah ah Yaya dare yayi fa yanzun ana neman 8:00 na dare nikam Zan koma Goggo zatayi fada, Muje na rakaki gida sai nama Goggo bayanin dalilin jimawar ki karta Miki fada, toh yaya,ta fada tana Kama hannunsa suka nufi layin su Goggo Amina, Nikam Ina shiga cikin gidan da yake ana ruwa ba kowa a tsakar gida shashen mu na nufa,aje jakana da takalmi nayi a baranda na kwabe lufayar jikina da yajika jakaf da ruwa na makala a igiya, dakin na shiga nadau towel na daura na zame dogon wando da NASA da under wear na makala a igiyar kofa , Kitchen na shiga na kunna gas na daura bojuwa (tukunya) na zuba ruwa a ciki,boket na dauko na ibi ruwa a Randa na tsaya a cikin kitchen in ruwan na tafasa na juye a boket in daidai yanda zanyi wanka na dauki boket in nayi bandaki,wanka nayi na fitoh,har lokacin ruwa ake Alwala nayi,jakana na dauka a baranda na shiga dakin, Jin dis dis Kamar panfo yazo daukewa yasa na lalube wayata a jaka na haska dakin idona ya sauka akan kujiran da yayan khadija ke k'wanciya ya jika jakaf da ruwa saitin wajen na yoyo fita waje nayi da sauri na d'auko baf nazo na tare ruwan,kaya na dauka na bacci na saka da hula harda socks don wani irin sanyi nakeji har cikin k'ashina sallaya na shinfida na Tada sallah mangariba da Isha nayi shafa'i da wutire , blanket na dauko nahau gadon na lullubu abina na kwanta da wani irin ciwon Kai da zazzabi nakeji gashi kafafuna sai zuge suke mini nama rasa meke mini Dadi Al'ameen suna tafiya da Khadija Chan dai Khadija ta kasa hakuri tace ,Yaya nikam na tambaye ka Mana? Allah yasa na sani dija, Kai Yaya ni banason dijan nan ai sunan tsofine, Toh hadixa Ina jinki, Habba yaya ta fada tana hada fuska, Sorry toh kanwata Ina jinki Yauwa Yaya nikam Aina ka hadu da Aunty Sumayyan ne harkace kana Sonta? ....Dam dam haka gabansa ke bugawa , Khadija meyasa Kika mini wannan tambayar,? Ba kome Yaya kawai na tambaye Kane , Ah ah Khadija fad'amin gaskiya nasan baki tambayar Abu banza, Am Yaya Naga baka taba bani lbrn kana da budurwa ba kawai sai naji Wai kayi aure za'a kawo Amarya, Toh Khadija ke abokina ne da saina fada Miki Ina da budurwa, auren Kuma yazone a bazata ban dauka iyayen ta zasu bani ita lokaci d'aya ba, Amma yaya kaga gidansu aunty kuwa Mai azaban kyau ga Yan gayu k'yawawa a gidan Kuma Aunty ma kyakkyawa fa Yaya toh ma Ina kake zuwa daga Tashar kayan marmari sai wajen sana'ar ka Ina kaga aunty har kuka fara soyayya? Ikon Allah Khadija Wai tambayar nan Kam na lfy kin sani a gaba da tambaya sai kace wani sa'anki , Kayi hakuri Yaya dai dai lokacin suna iso kofar gidan Goggo Amina, Muje Khadija na rakaki cikin gidan nama Goggo bayanin dalilin yin darenki , Toh Yaya , shiga sukayi cikin gidan tare, Goggo Amina ce ta amsa sallaman tasu tana fama da icce a runfar girkin ta Isa sukayi ya gaishe da ta Yamata bayanin dalilin yin Daren Khadija,.. Wallahih Muhammad Nima sai da na tura yaro yajimin lfy Khadija har dare Bata dawo ba ga aikin dare da tace zata dawo ta Kama mini, ya dawo yace min ba kowa a shashen ku, Kiyi hakuri Goggo, Basu dawo ba sai yanzun Al'ameen yace Yana mike wa, Ba kome muhammad shine ka tasata a gaba a ruwan nan Maimakon ku bare Sai ya tsakaita, Goggo Nima haka nace Mata Amma tace Zaki Mata Holo itakam sai gidan Goggo shine na rakota Gggo ruwan da yawansa bansan karfe nawa zai dauke ba shiyasa nace gwara na dawo Hakane Kam da gaskiyar ki Khadija Toh sai da safe, Goggo Allah bamu alkhari Ameen suka amsa ita da Khadija shikam fita yayi ya Kama hanyar gida, Ina kwance Amma ba bacci nake ba tunani kawai na fada nayi zugum gabaki daya gari yamin zafi, daidai lokacin ya shigo kofar duk ya jike Daman jallabiya ne a jikinsa ,, hauro wa dakalin Yayi ya zare jallabiyar sa ya aje a cikin boket in wanka dakin ya shigo daga shi Sai gajirin wando, da sallama a bakinsa Ina kwance cikin duhu don na kashe hasken wayana naji buruntu ana kokarin shigowa dakin don ni Sam banji sallamar ba, hasken wayata na kunna me Zan gani yayan Khadija ba Kaya, murd'adden damtsen hannunsa naci Karo a waje ga fafad'an kirjinsa mai cike da yalwan gashi,baki sitik kwance akan farar fatarsa kafarsa farare tas sai gashi ke kwance a lallausar fatar kafar tasa ai bansan lokacin da na k'wala ihu ba na dirko a saman gadon,na Kama hanyar waje don ni sai ma gani nake kamar ba wando a jikinsa don ajike wandon yake tsabar birkita hanyar kofa na nufa zanfita na bar Masa dakin, Jin ihunta sai ya birkitasa ya dauka Koh wani abune ya sameta Jin ihun take akai akai hakan yasa ya gigice shima ya fara neman hanyar kofa cikin lalube,da D'an saurin sa Jin itama kofar ta nufo tana ihu har lokacin, Ji kake gauuuu! sun garu da juna a kofa daga shi har ita ihu suka saka a tare, sai kawai suka kuma zubuwa ji kake timmmmmmm............ *Gobe Monday Ina da jarabawa bazakuga update ba fan's* 🏃‍♀️ 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin,Koh kinsan mace sai da kamshi da gyara* 😉 🍀🍀🍀🍀 *Turare suna d'ayace Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin sa* 🍀🍀🍀🍀 *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da* *gyara* 🍀🍀🍀 *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace* 🍀🍀🍀 *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE* 🍀 *Na tsunguno(habil)* 🍀 *Na jiki (kwalaccam)* ( *khumra, black & white* ) 🍀 *Turaren turara jiki after birth* , 🍀 *Na d'aki(halud Al'oud)* *UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* 💃🏼💃🏼 🍀🍀🍀 *Suna bada d'aya Koh sare akan farashi Mai Rahusa* 🍀🍀🍀 *Suna bada order kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria* Contact them vie 🪀08028827241 or 09033791049 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya* *Ibrahim* 🍃 ✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwa👌 free book 🤧 Page1️⃣8️⃣&1️⃣9️⃣ Washhhh yace jinsa a k'asan cafet ya zube,Bai farga ba Yana kokarin mikewa, yaji ta Fad'i a kansa daga shi har ita Kara suka saka sai Kuma sukayi shuru tare, ido na ware jina a jikinsa cikin rawan jiki duk na rikice na fara chuku chukun mikewa naji yasa hannu ya zagaye hips ina, sosai ya kara matsota kusa dashi, "Kai me haka" ? Ka sakeni Mana, Mena rike min........sai Kuma tayi shuru ta kasa karasawa, Cikin sanyin halinsa ga jikinsa na wani irin rawa Jin mace a jikinsa a karon farko a tarihin rayuwar sa kenan, yaji mace a kwance a jikinsa, Mena rike Miki? Ya tambaye ta Yana yawo da fuskarsa a kafadar ta Yana neman fuskarta, so yake ya Hada fuskar ta da tasa, "Wai ma Ina ruwanka ne don Allah nikam sakeni haii" nace cikin ihu Jin muryarta hakan ya tabbatar Masa da inda saitin fuskarta yake hada fuskar yayi da tasa har suna Jin numfashin juna, "Wai menene haka bazaka sak".........bai bare na karasaba naji saukan lips nashi masu uban dume akan nawa lips in wani abu naji ya tsargar Mini daga tsakar kaina har farcen kafana cikin wani irin birkita na yunkura zanbar jikinsa zan mike ji kawai tayi ya fisgoni gabaki d'ayana na zube Akansa , cikin wani irin zafin nama da kuzari ya cafke lallausan bakinta cikin nasa da wani irin zafi zafi yake tsotsarta Jin sai k'okarin mikewa take a jikinsa yasa kafa ya harde kafarta da nasa kafar,daga ita harshe rawa jikinsu yake, Tashin hankali da nake ciki ba'a saka Masa Rana kuka nake so nayi Amma ba Hali hawayene kawai kebin kumatuna, Jin saukar hawayenta akan face nasa ya saka sa sassauta Mata riko a hankali ya zame bakinsa cikin nata, Ai da wani irin azabebben sauri na mike tsalle D'aya nayi na fita a d'akin na tsaya a baranda duk sanyi da ake da ruwanda ake zugawa na g'wammaci na kwana a waje Data kwana a d'akin nan inaaaaa, Sumayya!!! Sumayya!!! yake kiranta cikin tsarkewar murya shima ya mike Yana lalube ya fitoh wajen, ganinsa ya sakani zabura Amma tunawa da nayi baya gani yasa na tsaya naki Koh motse kirki Ina jinsa sai kirana yake Yana lulube na a baranda in yazo lalubar Gefen da nake saina matsa a hankali na koma inda ya laluba,jikina nata rawa, Jin baijita ba don karfin ruwanda ake Bai bare yaji Koh D'an motsen taba don ruwa ake harda tsawa,sauka yayi a baranda yanakan lalube, ruwa na dukansa Yana zaga kofar Amma Bai jita ba har kofar shashen ya taba Jin kofar a rufe yasa ya gane Bata fita a kofar ba, Don Allah Sumayya ki kulani Koh zanji hankali na ya kwanta don nasan kina jina kina ganina, Wani irin tausayin sa naji ya kamani ,cikin sanyin jiki da fargaba nace "ganinan anan," Ai da hanzarinsa ya nufi barandan jikinsa ya jike jakaf da ruwa haryana diga ga gashin kansa da gemunsa duk ya jike ya k'wanta g'wanin sha'awa , Da hanzari ya iso wajen ta cikin rawan murya ya fara magana, Sumayya pls mu koma d'aki kinji, "Nidai yau bazan k'wana da kaiba a d'aki D'aya ba "nace Ina kuka Kamar karaman yarinya, Kiye hakuri kinji Sumayya muje mu k'wanta Allah bazan miki kome ba kinji Koh, "Wallahih nidai bazan shigaba" Ina fada Ina kuka, ganin Yana matsowa kusa Dani yasa na k'wala Kara Zan ruga cikin ruwa naji anyi sama Dani, D'aukarta yayi duk yanda take kuke kukenta kin kulata yayi sai ihu take tana ya sauke ta, sosai ya riketa Gam a kirjinsa Yana lalube har suka shiga dakin ya tura kofar da hannunsa d'aya d'ayan na rike da ita , A hankali yake lalube harya Iso bakin gado a hankali ya haura saman gadon kwantar da ita yayi a hankali ya lalube blanket inta ya rufa Mata ,ya sauka Akan gadon cikin lalube ya shiga neman Ghana must go in kayansa wani jallabiyan ya dauka a wanke tas ya zura ya zame jikekken gajeren wandon sa, lalube yayi ya fita waje a aje a cikin kayansa jikakko daya aje a boket, Nikam tunda ya saukeni a Kan gadon jikina yake ta rawa sosai naji wani irin tsoron Daren nan, zazzabinane ya Tashi sosai nakejin kaina na Sara mini yau tension Yama kaina yawa, Dawowa yayi Kan kujira zai k'wanta Amma yaji baho a saitin wajen, lalubawa yayi yaji kujiran a jike hakan ya tabbatar Masa lalai yo-yo wajin ya ke filon kujiran da yake k'wanciya dashi ya dauka ya lalube cafet ya aje ya k'wanta a kasan dakin wani irin sanyi ne ke shigar sa don a lokacin baiki ya samu abin rufuwa ba Amma Bai dashi Kuma baida karfin gwuwar tambayar Sumayya tunda ba ita tayi niyar basa ba, Jin motsen yayan Khadija yaki natsuwa sai jujuyawa yake ga atishawa akai akai alamudai murace ta kamasa, Wayarda na wancakalar dashi na dauka na haska inda nakejin motsen sa ganinsa nayi a kwance sai jujuyawa yake alamudai sanyi yakeji, D'an tausayi ya bani sai Kuma na tuna lokacin da bani da lfy dashi da Yar uwarsa su sukayita d'awainiya Dani Amma yau shine na Bare a kwance a kasa ga sanyi, ni Ina kwance a gado da bargo, Kamar bazanyi magana ba a hankali nace ",kazo ka kwanta a gadon kasan nan akwai sanyi Kuma naji Kamar mura nason kamaka" A hankali ya mike ya Soma lalube harya Iso bakin gadon cikin nutsuwa ya haura dai dai ta bakin ya kwanta, Nikam Ina karshen gado ta wajen jikin gini ganin Bai taba blanket in ba bare ya rufa, yasa na mike na dauko wani a whdrp na aje Masa a kansa na wuce filina na kwanta addu'ar bacci nayi na shafa na juya masa baya , Jin ta aje Masa blanket yasa she d'auka ya lulluba shima addu'ar bacci yayi ya lumshe idonsa Sam yaji bacci ya kaurace Masa wani irin yanayi yau ya tsinci kansa a ciki,Mai ban Al'ajabi Daga shi harni Babu Wanda ya rintsa har 1:00 na dare kafun bacci ya dauke ni shikam bansan lokacin da yayi bacci ba, ********* Yaukam dagani harshe sai kusan 6 mukayi sallan asuba a dadafe dukan mu biyu da ciwo Muka kwana ga yunwa don tun karyawan safe dagani harshe bamu sake saka kome a bakin mu ba, muna idarwa gado Muka koma muka sake k'wanciya don baccine ya cika Mana ido na rashin Yi da wure jiya, Jin Yana matsowa kusa Dani yasani matsawa da sauri ji kawai nayi ya mike zaune ya zura hannunsa ta saitin da nake ya jawoni duka jikinsa a hankali ya koma ya kwanta Dani a jikinsa , Yanzun Kam ban neme k'wace jikina ba saboda zazzabinda nake fama dashi ma ya isheni, A hankali nace Masa"Wai meke damunka ne tun jiya kake ta tabani"? Nima ban sani ba haka kawai nakejin inason kusanci dake,ya fada da muryarsa da ta dishe don mura kamasa Tay sosai ga fuska jazur kamar ka taba jini ya zuba, Kala bance Masa ba don ni jikina ne ya dameni,shuru mukaye gabaki d'ayan mu har bacci ya dauke mu a haka, sallama nake ji kamar muryar Khadija sama sama cikin bacci sai Kuma naji yayan Khadija na zame jikinsa a nawa, Bude ido nayi Wanda nakejin nauyinsa sosai ga xaxxabi, Khadija Kam ganin takalmin Aunty da na yayanta a bakin dakali yasa ta juya zata fita Amma dai tana mamakin har 10:10 na safe yayan ta Bai fita ba, Mikewa Al'ameen yayi ya fita a d'akin Jin alamun Mai sallamar na kokarin fita a shashen Kuma ya shaide muryar Khadija ne, Waalaikumu salam Khadija ya kina komawa kuma? La Yaya Daman nace bara nazo na duba Aunty jiya kafarta tun a hanya ya kumbura Amma dai ba kome anjima Zan dawo, Saboda me? Naga baku tashi ba Yaya, Ah ah ai gwarama da kikazo Nima Yanzun nakeson fita na nemi yaro ya kiramin ke, Lafiya Kam Koh? Naga fuskarka ta kumbura tayi ja ga murya a dishe Daman Saida na tuna haka wallahih ruwan jiyan nan ya kare a kanka, Ai bani kadai bane Khadija Aunty kima ba lfy , Subhanallah meke damunta Hala kafar ke ciwo,? Ah ah Khadija zazzabine, Meya faru da kafartan ne da kike ta cewa Yana ciwo,? Ba kome kasan jiya bamu samu Keke da wure ba Koh?da kafa Muka ringa takawa, Uhmm lallai fa,yace Yana dafe kansa dake Sara Masa, Sannu yaya kanne? Wallahih Khadija, Toh kaje ka kwanta Mana bara na gyara kofar, Khadija Aunty ki tun karyawan jiya bataci kome ba zoki karbi D'arin nan ki sai Madara 50 da bornvite 50 akwai sugar n jiya da safiya da Lipton ki hada Mata tie Koh zata iyya Sha? Toh Yaya Kaifa, Khadija hada Mata kawai taima kayan shayen bazai Isa ba? Zai Isa Yaya, Toh shikinan ki hada hardani Toh D'akin ya shiga yadau kudin ya mikowa Khadija ya dawo ya kwanta, tare da matsowa kusa dani Nidai Ina jinsu shuru kawai nayi, 10:30 Khadija ta dafa Mana shaye harda k'wai ta soya dayake jiya yasai kayan Miya na dare yazo ya samu bamu dawo ba, Tana Gama shirya kayan Karin ta nufi dakin, A bakin kofa ta tsaya tana sallama Bata shigo ba , Mikewa yayi ya zauna a bakin gadon ya sauke fararen kafarsa a kasan cafet,amsa Mata yayi hade da Bata izzinin ta shigo, Khadija ki shigo mana,yace Jin Taki shiga, Da sallama a bakinta ta shigo d'akin aje kayan hannunta tayi akan cafet,zata juya, Khadija d'auki baf in Kan kujiran nan kikai waje kizo ki jona fanka naji Kamar an kawo NEPA ki juyashi saitin kujiran samun ya bushe, Toh Yaya tace tana daukan baf in tayi waje dashi zubar da ruwan tayi , Ta dauki tsintsiya ta shigo dakin tire in kayan karyawan ta dauka ta daura akan kujiran ta share dakin, fanka ta kunna ta matso dashi Kusa da kujiran,Kamar yanda yace Turarukan UMSAD INCENSE da ta Gani a jere akan mirror ta d'auka na d'aki jona kaskun lantarki tayi Aiko take dakin ya dauki kamshi Mai Dadi (kowa yasan yanda Turaren wuta yake da kamshi a d'aki especially a damuna), Khadija na fita ya matsoni a hankali hannu yasa Yana laluba ta nikam sai matsawa nake duk inda naga hannunsa zai taba saina matsa agun,. Don Allah Sumayya ki tsaya Mana kaina ciwo yake wallahih Koh motsasa bana sonyi kina ta bani wahala yace Yana dafe Kan, Toh ni sai ka min magana da hannune bazaka mini da baki ba saikayita tabani, Sorry tashi kije ki wanke bakinki ga breakfast Khadija ta hada Mana yace Yana kwanciya, Toh Kaifa bazaka wanke bakin bane kake k'wanciya sai yayi ware? nace Masa Babu alamar Wasa, Murmushi yayi har fararen hakoransa masu tsananin kyau suka bayyana,ai kinfi kowa sanin bakina nada ware Koh babu tunda kin d'and'ana jiya , ya fada muryarsa a shake Ohon maka dai nace cikin Jin haushi mikewa nayi a hankali na nufi kofa shima mikewar yayi yabi bayana , Kofata nabi da kallo tasss Khadija ta share samunta ma nayi tana wanke wanke ga kayan na data cicire a igiya ta zuba a boket, Khadija kibar d'aurayan nan don Allah daga kin wanke Kwanukan nan ya Isa haka ke baki gajiya da aikine, Toh aunty tace mini, Wanke baki mukayi muka koma daki abincin na jawo Mana ganin hadamu tayi plate d'aya tie ne kawai kowa da cup nashi, ,k'wala Mata Kira nayi"Khadija Khadija" Na'am Aunty ganinan zuwa,, tace Tana shigowa dakin "Jiki d'auko wani cup da plate"toh tace ta fita sai gata ta dawo dasu Ajjyemin tayi zata fita, "Tsaya Khadija" nace zuba Mata tie nayi na ibi k'wai data soya Mana NASA Mata a plate itama" d'auka kije kici nasan dafawa kikayi baki ibi naki ba Khadija kullum Ina gayamiki in kin girka Abu ki ringa zuba rabonki kinji Koh kin manta nan ma gidanku ne"? Toh Aunty tace tana karban plate da cup in tayi waje, Bismillah na Masa ya matso yasa hannu kad'an naci,naji ya isheni don bakina ba Dadi sam tie kawai nashanye duka, Koh aje cup banyi ba wani irin amai ya tasar mini da gudu na fita waje na ringa shika Amain sosai, Mikewa yayi yabi bayana daga shi har Khadija sai sannu sake mini Mika min ruwa tayi na wanke bakina na koma d'aki duk k'wanciya Muka sake don shima bazai iyya fita wajen sana'a ba, Misalin karfe d'aya na Rana ana kiraye kirayen sallah azahar ya mike ya fita, wanka yayi a dadafe ya nufi waje zaije chemist in jambusko Koh zai basa bashin magani Koh iyya Sumayya kawai ma in zai samu a Bata ya gode Allah duk da yasan halin inyamurin daker ya ya basa bashi, Yana fita Nima mikewa nayi Ina Jin jiri jiri na fitoh waje Jin ana kiraye kirayen sallah Khadija na samu ta wanke Mana kayan mu daya jike jiya,tana kitchen wani aikin Kuma take, "Khadija Wai me yasa bakiji ne nace Miki kibar aikin haka " "Ke kullum kikazo guna baki abinyi sai aiki" Toh Aunty in ban Miki ba wazan ma ba lfy bane dake ga kofa kasha kasha Koh abincin da zakuci bazaki iyya girkawa ba toh Aunty in ban muku ba wazai muku A gaskiya bansan dame Zan sakawa Khadija ba Allah ne kawai xai biyata Nagode Khadija Allah ya barmu tare ya nuna mini auren ki in ban mutuba,hhhhhh nace Ina dariya Kai Aunty tace tana rufe fuska Wai kunya, Yana fita gida massalaci ya shiga ana idar da Sallah yanufi chemist in jambusko, Yana Isa sanin ba musulmi bane yasa ya ce Masa , excuse,? Yes wanene? Nine jambusko,ya basa amsa Dayake inyamurin ya Dad'e a Jala yanajin hausa sosai , Wai MAKAHO Kaine anan yau kuma? Eh wallahih madam ce ba lfy zazzabi ke damunta........ Bai bare ya karasa bama ya ce kaima ai harda Kai bakaga muryarka ba ga fuska yayi ja ido ya kumbura,kana mura, Eh harda ciwon kaima shiyasa nazo wajen ka ka taimaka kaban bashi inna d'an ji sauki zuwa anjima zanfito in Allah yasa na samu kasuwa saina biyaka, ya fada cikin zullumi don shi kansa Allah ya gani kwata kwata bayason roko Koh bashi Amma ya zaiyi bazai iyya zuba ido Yar mutane ba lfy ya barta haka na shi Karan kansa Saida lfyr zai nema musu abinci Heeeee chinekeeeee gaskiya MAKAHO nii........... *Gaisuwa na musamman gareki ummee zariya Naga special comments naki Kuma Nima na yaba Miki sosai naji dadi* 🍀🍀🍀🍀🍀 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin,Koh kinsan mace sai da kamshi da gyara* 😉 🍀🍀🍀🍀 *Turare suna d'ayace Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin sa* 🍀🍀🍀🍀 *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da* *gyara* 🍀🍀🍀 *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace* 🍀🍀🍀 *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE* 🍀 *Na tsunguno(habil)* 🍀 *Na jiki (kwalaccam)* ( *khumra, black & white* ) 🍀 *Turaren turara jiki after birth* , 🍀 *Na d'aki(halud Al'oud)* *UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* 💃🏼💃🏼 🍀🍀🍀 *Suna bada d'aya Koh sare akan farashi Mai Rahusa* 🍀🍀🍀 *Suna bada order kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria* Contact them vie 🪀08028827241 or 09033791049 IG @umsadincenseIG @umsadincense 08084453785IG @umsadincenseIG 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya* *Ibrahim* 🍃 ✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwa👌 free book 🤧 Page2️⃣2️⃣&2️⃣3️⃣ Yau da Matata Zan kwana gaskiya Da mamaki nake kallonsa"waye matarka"? Ga tanan ya fada Yana kwanciya Da ita a jikinsa "Wai menene haka ka matseni fa" nace Ina kukarin tashi a jikinsa Fuska ta ya hada da tasa fuskar har hancin su na gogan na juna, Karan in TV nan Kam kyakkyawa ne shiyasa yake burgeki? Ikon Allah yanzun Kam na gane inda mutumin nan ya dosa, maganan Karan innan ya damesa"mummuna ne kamar Kai"na basa amsa,har lokacin Ina kwance a jikinsa don karfe ya saka mini sosai Murmushi yayi a hankali yake goga Mata gashin gemunsa a Gefen fuskarta Wani Abu nakeji sosai a tare dani"Kai me haka"? "Kana goga mini gonan ciyawa a fuskata Koh so kake ya garceni ni" Kinji Dadi kenan? Kuma ni ba mummuna bane sai dai kece mummuna Hhhh shap ai in fada maka "Kai mummuna ne sosai gaka bak'i,gajere, Mai guntun hanci, ga tumbi" Wannan Karo Kam dariya ya kamayi don sosai yake cikin nishadi, ganin ya samu abokiyar Hira Farine ni, Kuma hancina dogone Ina da ido bakina irin na khadijata fuskata dogone Mai dauke da gashin gemu Mai yawa haka na kaima, akwai tabon sallah a goshina,ya Bata Amsa yana Kai hannunsa kanta ya zame hularda ta saka a hankali ya Kama gashinta da khadija ta kitsa Mata har gadon baya, Da Ina Tara gashi sai yafi naki yawa "Kutt wallahih bazaifi ba duk ma Wanda ya farfada maka haka kamannin ka yake kawai zaginka yayi Amma ba wani yanda na fadan nan dai haka kake" Dariya kawai yayi sai Kuma yace, Da ace ban taba ganin kaina a madubi ba dayau kinyi Dani don d'auka zanyi da gaske hakan nake "Au Daman ka taba kallone kafun ka makance"? Shikarata 18 na zama MAKAHO Kinga ai zuwa yanzun kamannin Bai sauyaba "Ya sauya kam gashi harda tumbi kayi"na fada Ina murmushi haka kawai na tsinci kaina cikin farin ciki yau na samu abokin Hira Wanda rabon da nayi harna manta sai in khadija tazo Cikin hanzari ya birkitota zuwa kasa shi kuma ya koma Saman ta, Zaro ido nayi cikin Al'ajabi da tsoro bakina har rawa yake"yayan khadija me haka wayyo kirjina nauyi ka d'agani" Ina da tumbi Koh Babu kinsan ba gani nake ba shiyasa na saka Miki tumbin don kiji akwai Koh Babu "Wayyo Allah cikina kirjina nauyi ka sauka a kaina wallahih baka da tumbi washhhh numfashina xai d'auke" Jin yanda duk tabi ta gigice yasa a hankali ya d'aga nauyinsa akanta Amma Bai sauka ba, "Ashhhhh toh ka sauka a kaina Mana" Shuru yayi yaki magana yanajin ta sai masifa take, ya sauka a kanta ya Mata banza don yanzun Sam baicika Jin shakkarta ba Kamar da "Ina Jin fitsari" Yayi shuru don yasan ba fitsarin zatayi ba muddin ya saketa guduwa zatayi "Koh bakaji bane, ya matseni fa" Kiyi anan kawai, ya Bata Amsa Ganin ya manna mini hauka yasa nayi shuru ganin da gaske fa ba sauka zaiyi a kaina ba bare akan gadon,ganin baida niyar yimin kome yasa hankali na ya kwanta har kusan 1 na dare idanun mu biyu daga karshe dai bacci barawo yayi gaba Dani, Jin saukar numfashin ta ya tabbata tayi bacci a hankali shima ya ringajin bacci na d'aukarsa zamewa yayi ya kwanta a gefe ya dagota ya d'aurata a kansa ya lumshe idanunsa har yaji babushi, Kiran farko na Assalatu shiya sauka akan kunne na a hankali na bude idanuna na,masu cike da bacci jina ajikin mutum yasani tunawa Ashe fa jiya tare muka kwanta zame jikina nayi a hankali Zan mike Jin tana zame jikinta a nashe ya sakasa bude ido sai alokacin yaji Kiran sallah ake Daga ni harshe waje mukayi na ibi ruwa a buta na aje Masa"ga ruwan Alwala kar a shiga sallah baka Kama Alwala ba ka rasa jam'i"Na fad'a Wai karya tuna wani abu, don yau na iba Masa ruwan Alwala Butan ya d'auka Alwala yayi ya tafi massalaci sai tunanin abinda zasu karya yake baida Koh sisi Kuma inya bude Mangoro da safe ma ba ciniki yake ba kwana biyu nan, amfiya D'an Saya da rana Koh yamma Alwala nayi na shiga d'aki, Ina iddar da sallah na kwanta a Kan sallayan don harga Allah bacci nakeji jiya ban kwanta da wure ba Gida ya shigo don ya rasa mafita Sam baisan me zayi ba,a Ina zai samo musu na karyawa tsoro yake kar hakurin Ta ya Kare wata Rana ta guje sa, da sallama ya shigo d'akin Jin Bata amsa ba yasa ya fara laluben ta akan gado Amma Bai jita ba ya sauka Yanata tattaba kujira a tunaninsa Koh tana jinsa kin amsawa tayi, Sumayya!! Sumayya!! ya kirata baki biyu Amma shuru,hankalin sa a tashe ya shiga tattaba kome na d'akin Yana nemanta hardai yajita a kwance akasan cafet,sosai hankalinsa ya kwanta shi Karan kansa ya rasa meke damunsa akan Sumayya Sam baida jarumta akan lamarin ta, Koh don ta kasance mutum na farko dake da kusanci dashi a duniyarsa ta yanzun ne oho,hannu yasa a hankali ya cicibeta Yana lalube harya Isa bakin gado kwantar da ita yayi,ya fita waje,boket ya d'auko ruwa ya ringa ja a rijiya harya cika Randa ya wanke kwanuka harda shara yayi Amma dai sharan Koh na yara albarka saboda kwata kwata batayi kyau ba (sharan Mara ido) Yana Gamawa d'akin ya shigo da lalube ya isa Kan gadon Hawa yayi,hannu yasa ya fara tataba ta Yana neman fuskarta har hannunsa ya sauka akan kirjinta Waro ido nayi Ina kallonsa Jin yaki cire hannunsa a kirjina yasa na buge hannun"me haka don Allah"? Da nayi me?ya sake tambayar ta "Ai kafini sani waima menene kake ta faman laluba ta Ina bacci" Nidai bansan kome ba tunda ba gani nake ba nadai San na taba Abu mai laushi Amma bansan kome Nene ba,ya Bata Amsa Lallai mutumin nan ya Raina mini wayo ai Koh Bai taba kallo ba a rayuwar sa yasan meya taba bare harya Kai 18 Yana kallo,jin rainin wayone ma ban sake magana ba Kin tashi lfy? "Lafiya Alhamdulillah" Uhmm Sumayya Zan fita, Koh zan samu na karyawa anjima Zan dawa insha Allah ban kwana da kudi ba "Sai ka dawo" nace Masa Ina sauka a Kan gadon don wallahih yunwa nakeji ba kadan ba Allah ya yasa,Yace Yana fita a d'akin harya bude kofar shashen zai fita yaji Sumayya na kiransa tsayawa yayi "Am Daman nace in ka fita pls ka tura yaro ya kiramin khadija"Ina magana Ina bin kofar da kallo da mamaki Toh,yace mini zai juya "Wai waye yayi aikin nan duka haka"?na fada Ina murmushi ganin sharan Kamar wata yarinya Yar 3 ce tayi Nine na Miki aiki yau dai ki huta "Aiko naji Dadi na" nace Masa don na gane so yake ya burgeni 😌 Da gaske?ya tambaye ta "Sosai ma,ka tafi Mana samun mu samu na karyawan ka tsaya surutu yanzun ana neman 8:10 na safe" Ok.toh sai na dawo "Yauwa" Yana fita a kofar gida ya aiki yaro gidan Goggo Amina ya Kira Khadija Nikam tsintsiya na d'auka na sake share kofar na gyara d'aki sosai kwana biyu nan. Nake jina a sake sosai Khadija ce ta shigo bakinta dauke da sallama, Assalamu alaikum "Waalaikumu salam"khadin Goggo Kai Aunty ni banso sunan fa nasan a bakin Yaya kikaji duk shike Bata mini suna "Toh khadin Yaya" Aunty ai khadin ne banaso "Toh khadija shikenan"? Eh Aunty Ina kwana ? "Lafiya khadija ya goggo" Lafiya Alhamdulillah,tace tana zama a bakin dakali "Wai ni khadija ya Fulani Dance in dai su kawayen Amarya jiya an rabashe kenan"? Shuru tayi sai Kuma Naga hawaye ya cika idanunta.. Da mamaki nake kallonta "Khadija me ya faru kuma daga tambaya sai kuka wani abin na Miki"? Aunty don Allah nida yayana muna da wani abin kyemane a jikin mu, da mutane ke wulakanta mu Koh saboda mun kasance Marayu ne, Koh Kuma don Yaya baya kallo ne, ta fada tana fashewa da kuka "Subhanallah khadija meyasa Kika Fadin irin wannan kalaman haka" Dole na fada Aunty kaf unguwan nan yayana baida aboki Sam ba Wanda keson rabarsa gani ake Kamar Inka jashi a jiki zai zama maka kaya, Amma wallahih Aunty yayana baida zuciyan kwad'ayi kullun so yake yaga ya neme na kansa Amma duk da haka in Kinga yayana na Hira toh ta miskinai ne irinsa Amma bayansu ba Mai son Koh Hira da yaya, shiyasa har kullum nake mamakin auren ki, Ni Karan kaina mujiyace a cikin kawaye, me laifin mu aunty mu muka d'aurawa Kan mu Talauci ne Koh akwai Wanda yafi karfin maraici ne? "Gaskiya Babu khadija Amma meya faru ne haka"? Na tambaye ta idanuna na cika da hawaye tabbas khadija Allah ne ya tsare ta a irin zamanin da muke cikin nan yanda Yan Mata suka baci da son kyelekyele Amma ita ta kauda fuska ta cire buri a ranta ta zauna a matsayin da Allah ya d'aurata,samun irin khadija kalilan ne a yanzun yarinya Mai hakuri Aunty Kinga wulakancin da kawayen Amarya suka mini jiya a wajen bikin nan? ta fada tana kuka "Ah ah khadija me suka Miki" Aunty' Wai daga zuwana naje na tsaya agun da kawaye ke tsaye kawai Ina zuwa suka mimmike suka koma wani wajen Wai kunya suke kar abokan ango suganni a cikin kawaye za'a Raina class nasu,kinsan ma Aunty me yafi Bata mini Rai? "Ah ah khadija" Wai Aunty danaga duk sun watse saina koma cikin mutane na tsaya kawai kowa na tsaya kusa dashe sai ya Kama matsawa Wai kar ace tare Dani yazo, don ban saka kayan Fulani ba koma banyi ado ba Sosai naji wani irin haushi kamar zai kashe ni Aunty bazan sake zuwa bikin kowa ba daga yau "Yau me za'a yi"? Kamu,ta bani Amsa "Zaki je bikin nan khadija har a Gama dake za'a Gama insha Allah" Aunty ni bazan sake zuwa ba a wulakanta ni,don Yaya yace Koh mutun baida kudi in dai ya rike mutuncin sa bazai wulakanta ba "Ki kwantar da hankalinki insha Allah bazasu sake wulakanta kiba" na fada Ina Mai Jin tausayin baiwar Allah nan D'aki na shiga na barta tana kuka akwatina na bude Kaya na d'auka Atamfa da les masu azaban kyau a dinke sai Turare na d'auka guda D'aya na fitoh a d'akin dasu a hannuna "Khadija rike kayan nan Naga kamar akwai tailoli a tsallaken titi ki Kai musu wa'innan kayan su rage Miki yayi daidan ki yanzun in Kika fita, wannan Turare Kuma kasuwa nakeso ki Kai shagunan masu Turare Koh zasu Saya kudin sa 20k ne Amma Koh 10k Kika samu Koh kasa dashe ki karba kawai" Aunty ba Yaya yace ki daina Saida kayanki ba? "Khadija Zan zauna da yunwa ne Ina da abinda Zan tsayar naci a cikina sai na zauna" Gaskiya ne Aunty Amma fa Yan kasuwa bazasu Saya ba don yanzun Suma tsoron sayan kayan hannu suke karsu Saya na sata,sai dai akwai wata Mata dillaliya ta bayan kasuwa sai na Kai Mata don ance itakam Koh kayan satane Saya take don Yar rikici ce sosai "Yauwa khadija Allah yasa ta Saya wannan kayan in kin fita ki fara kaisu shagunan dinki" Aunty wazaki bawa kayan Kuma ai Naga daidan kine naji kince a maidashe daidai na? "Ina ruwan Ki,nidai tashi kije mini aika na, sannan in ta Saya Turaren ki shiga kasuwa ki sai Gam bak'i Mai kyau ki hada da Turaren lalle,sajan,tsamiyan kanti, ki sai bakin lalle guda biyu shima" Aunty lalle zakije ne? "Kai Khadija banson tambaya ki sai mini kayan Miya duka,in kin dawo ki biya tailan kudinsa ki karbi kayan Saiki saimin doya soyayye a bakin titi na karya" Toh Aunty tace ta karbi kayan tasa a laida ta fita D'aki na shiga Ina ta tunanin halin rayuwa da khadija ke ciki Sai karfe 10 khadija ta dawo kayan na bubbude na Bata ta gwada Aiko yayi Mata daidai jikinta sosai kayan ya karbe ta,doyan na bude Mana mukaci tare Kam in na manna a tire na kwaba Jan lalle, "khadija zoki zauna na Miki lalle"nace Mata Ina zama akan dakali Aunty Daman ni Zaki ma lallen ne har Kika Saida Turaren ki Mai tsada a naira 5k? "Khadija bazan d'auki wulakanci ba Sam insha Allah yau saikin fi Amaryar kyau bama kawayen ba" Daman kin iyya lalle ne Aunty?ta fada tana zama "Sosai ma khadija ai lokacin da nake primary school innaje makaranta sai nayita zana flower lalle a takanda na Inna dawo gida sai ummie na tace zata buge ni sai abie ya k'waceni yace bazata bugeni ba ai batasan Koh baiwar da Allah ya mini ba kenan, sai ya sai mini takkadar lalle daban duk lokacin da zanyi Zane saina dawo makaranta sai ya bani takardar na zana, lokacin da na Gama primary sai ya sai k'wallon dayes ya baiwa Mai aikin mu ta dafa mini da lalle,sai nayi mole na zuba a ciki,abie ke saimin hydrogen Ina ma yaran gidan mu lalle harda yaran makwanta, harna girma Ina lalle duk yaran gidan mu da aka aurar Mata Ninake musu lallen aure da make-up haka kawaye na da Yan unguwan mu sosai nake Alfahari da lalle khadija"nace Ina manna Mata Gam a gafa Kenan Aunty kina sana'an lalle da kwalliya? "Ban taba yin lalle kudi ba Koh make-up khadija don ba abinda na nema na rasa a rayuwa a lokacin" Allah sarki, tace Lalle na tsarawa khadija sosai bak'i da ja sai bayan azahar Muka Gama, tunda nake da khadija ban taba ganin farin cikin Dana gani a lokacin da na Gama Mata lalle ba bini bini saita duba lallen tayi murmushi "Wai nikam khadija baki taba lalle bane" Aunty Kenan Koh a sallah bana lallle in Kinga nayi lalle toh gaggo ne ta mini yabe "Toh yaukam kinyi design na flower"nace Ina mikewa sallah Mukayi kafun Muka girka abincin Rana har lokacin yayan Khadija Bai dawo ba, Sai biyu da rabi na Gama abinci zuba Mana nayi mukaci har lokacin fuskar khadija na d'auke da murmushi ***Nima sai naji Ina cikin farin ciki ganinta tana walwala "Khadija ga abincin yayanki kikai Masa" Toh Aunty ta d'auki kulan tana kukarin fita,"yauwa khadija in kinje ki dawo da wure samun mu fara make-up in da wure" Toh Aunty nagode,tace tana fita,cikin farin ciki duk Wanda ya ganta yau yasan Bata da wata damuwa Tun daga nesa ta hango yayanta a zaune g'wanin tausayi sai zufa yake................ 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin,Koh kinsan mace sai da kamshi da gyara* 😉 🍀🍀🍀🍀 *Turare suna d'ayace Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin sa* 🍀🍀🍀🍀 *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da* *gyara* 🍀🍀🍀 *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace* 🍀🍀🍀 *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE* 🍀 *Na tsunguno(habil)* 🍀 *Na jiki (kwalaccam)* ( *khumra, black & white* ) 🍀 *Turaren turara jiki after birth* , 🍀 *Na d'aki(halud Al'oud)* *UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* 💃🏼💃🏼 🍀🍀🍀 *Suna bada d'aya Koh sare akan farashi Mai Rahusa* 🍀🍀🍀 *Suna bada order kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria* Contact them vie 🪀08028827241 or 09033791049 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya* *Ibrahim* 🍃 ✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwa👌 free book 🤧 Page2️⃣4️⃣&2️⃣5️⃣ Karasawa tayi kusa dashi, Assalamu alaikum Waalaikumu salam khadija Na'am yaya, lfy Kam na ganka haka a zaune, a Rana gashi sai zufa kake Lafiya khadija wallahih Ina cikin damuwa ne, tun safe na fita nabar Aunty ki Koh karyawa batayi ba gashi har ana neman la'asar banyi cinikin Koh biyar ba Yaya gaskiya ya kamata ka shanja sana'a yanzun mangoro yayi a raha ba lallai bane kana cini ki sosai Gaskiya ne khadija Nima Yanzun so nake na sare lemo in gwada na gani Amma bani da jarin, Toh Yaya Allah dai ya Bud'a maka kaji kabar saka kanka a tunani kaje ka jawa kanka ciwo a banza Allah yasa khadija Yauwa gashe Aunty ta bani abinci na kawo maka Abinci kuma?ai na ta samu kudi har taye cefene? Ina Zan sani Yaya nidai data kirani saita aike ni kasuwa(ta Masa karya karyace Sumayya batajin maganar sa) Koh dai kayanta ta sayar ne khadija? Kai.yaya bana tunanin haka fa,ga abincin kaci pls kaji yayana sannan ka tashi a ranan nan ka koma Gefen shagon Haladu ka zauna Toh khadija,yace Yana karbar kulan da take hannunta, khadija Turaren wa Kika saka ne naji kina kamshi? Hh wayyo yayana lalle ne Aunty ta mini, yanzun ma kwalliya zata mini Inna koma Lalle Kuma khadija kuma yake kamshi? Eh Yaya Turare aka saka sai aka kwaba dashi Inta Miki kwalliyar Ina zakije? Kamun Asma'u Mana Yaya ka manta Ban manta ba sha'afa nayi khadija, Amma ya za'a yi bani da kudin machine in da Zan baki fa Yaya za'a d'auke mu a mota gidansu Amarya,kasan yaufa zansha kyau,ta fada cikin farin ciki, zanje sai mu tafi tare... Sai kin dawo Allah ya tsare mini ke kanwata,yace yanajin wani Annashuwa, kanwarsa na farin ciki Kuma Sumayya ce sanadi, gaskiya Sumayya Rahama ce Allah ya masa,daya basa ita Ameen Yaya,tace tana tafiya Bayan fitar khadija wanka nayi na chanja Kaya wando nasa da riga t-shirt na kwanta akan kujira Ina jiranta, Assalamu alaikum Aunty na dawo Aunty "Waalaikumu salam khadija kiyi Alwala sai kizo mu fara make-up in Kinga Koh an Kira Sallah sai kiye kawai" Toh Aunty, tace tana iban ruwa Alwala tayi ta shigo d'akin Make-up kit nawa dana aje a cikin drawer na d'auko budesa nayi babbane ba abinda babu na make-up a ciki,zama nayi na tsarawa khadija makeover, Kai Masha Allah duk Wanda yaga khadija mundin ba mugun sani ya Mata ba bazai taba zato Koh tsammanin ita bace heavy make-up na Mata irin na Amare, amaren ma sai agun dinner,"khadija muyi sallah sai kisa Kaya Koh" Toh Aunty, tace sai murmushi take Bayan mun iddar da sallah Less in na Bata ta saka black ne Mai ratsin pink, gel na samata a gashi na d'aura Mata dankwali Mai ubansu, sarka da d'ankunne warwaro, zube, na Bata dukansu golden colour,takalmi pink, gyale da purse black,Kai duk Wanda yaga khadija a yau Koh shakka bazaiyi ba zaice Amarya ce, Ina Gama shiryata Tsayawa tayi tana kallon kanta a mirror, kamar taga abin tsoro, Innalilahih Aunty nice na koma haka? Aunty Kinga yanda na koma kamar ba ni ba,ta fada hawaye na cika Mata ido "Kece khadija ki share hawayen nan karya Bata Miki kwalliya kinji maza share" Toh Aunty,tace tana goge hawayen ta Wayata Kiran iPhone na d'auko"tsaya Khadija na Miki hoto"nace Ina gyara Mata gyelenta Tsayawa tayi,Aunty ta ta Mata hotona harda video sosai tayi kyau "A Ina za'ayi kamun ne"? A Taraba hotel ne,Wai ta hanyar government house "Hhh ba Taraba hotel ba, Taraba motel ake cewa sannan Bata government house bane,hanyar ne Amma ta Amazon yake " Au nikam Ina Zan sani Aunty ba zuwa nake ba, kawai nima naji jiya ana fad'ane "Ga 200 ki hau machine kije kinji ki dawo da wure fa khadija karki Kai mangariba"na fada Ina Mika Mata kudin Ki bare Aunty mota za'a kawo a gidansu amarya zai d'auke kawaye "Aikam yau a motar zaki,maza ki hanzarta Amma ki.karbi kudin Incase Toh aunty sai na dawo,tace tana fita a d'akin "Toh khadija Allah ya dawo dake lfy" Ameen, khadija na fita a kofar shashen yayanta, duk Yan gidan suna zaune a tsakar gida daga maza har Mata,ido suka bita dashe kureeeee suna mamakin bakuwar nan Sam tun safe suke zaune Amma basuga wucewar taba,baki a tsake suka bi khadija da ido harta fita, Khadija Kam duk tabi ta tsargu don Sam tunda take da wayonta Bata taba kwalliya irin na yau ba har kofar gida ta fita duk masu shaguna suka bita da ido suna mamakin Wannan kyakkyawar meya shigo da ita gidan Adara, Amma wasu basa mamaki in sun tuna MATAR MAKAHO fa Yar manya ce Kamar yanda aka saigunta musu, Kuma sun rasa dalilin auren nan Basu mamaki yake,mutum talaka miskini,a d'auki lafiyayye ya abasa Kuma Yar masu kudi,masu kudin ma zuriyan shugaba,abin nan na mugun Basu mamaki,Amma Basu da halin sani Khadija Kam ganin ido caaaa akanta yasa ta ruga gida da gudu ta koma kofar Sumayya "Kee khadija lfy meya faru Naga kin shigo kofa Koh sallama Babu Kamar an koroki" Aunty duk inda na wuce bina fa ake da ido,ni gaskiya tsoro nake ji "Kai khadija akwai wauta,don ana kallonki saiki kame jikinki ki nuna musu kauyanci,ai dakewa zakiye kici bom" "Koh gun kamu kikaje neman kujira zakiyi ki zauna abinki karki kuskura kicewa kowa kome Wanda ya gaidake ki amsa Wanda Bai Miki magana ba karki Masa kinji" Toh Aunty,tace tana fita Sai yanzun Yan gidan suka gane ta cikin mamaki Iro yace,buran uba muna d irin wannan kayan a gida Amma ace har yanzun banyi aure ba aradun Allah Naga Mata Kutumar ubanka iro D'an iska watoh kaga kasa ya rufe idon uwarka shine bare ka karya alkawarin da mukayi akan auren ka da salame,watoh munafurcine kullum akace ka fitoh a muku aure,sai kace baka da kudi, ah ah sai kayi gini ashe iskancine,baba lami tace Kinga baba lami wallahih kibini a hankali Daman ni har yanzun haushin ku nakeji, Aini ba shege bane dazan aure kanwar Wanda tayi sanadin mutuwar inno na ba, Koh inno ne ta dawo nasan bazata yafe mini ba Inna aure yarki, iro yace Kai karamin D'an Tasha wallahih karka kuskura, kace zaka zagarmin uwa inba haka ba naci ubanka a gidan nan, manu ya fada,babban yaron Inna asabe Inka fasa shege kake,iro yace Yana huci Ai Bai Gama rufe baki ba manu ya shakumosa suka hau dambe Duk yanda matasan ke ta kokarin rabasu abin ya faskara abinka da tamben maza, Mazan ma masu zuciya Hatta iyayensu maza an Kira Amma duk sunki rabuwa sai an rabasu an Kama D'aya sai D'aya ya fizge ya shakumo D'aya Inka shiga tsakani duka ya sauka akan ka Abin da yafi karfin Yan unguwan police aka Kira,suka zo suka kwashe su,inda sabo an Saba da ganin fiye da hakama agidan Adara ******************* Bayan fitar khadija kwanciya nayi don yau dai naji na gaji da cin cimar mu tunda inada sauran 2k Kuma akwai kayan Miya da yawa,don haka yaudai zanci wani abin special Duk abinda ke faruwa Ina kwance Ina jinsu sai dai.bansan ainahin abinda ya had'asu ba"garin kallon fad'a a kasheni a banxa " nace Ina gyara kwanciya na sai kusan 5:30 Al'ameen ya koma gida kwata kwata naira 30 yayi ciniki Sam yau Kam sai a hankali,ya shigo gidan jiki a sanyaye hannunsa d'auke da kwandon kwanuka,bakinsa dauke da sallama "Waalaikumu salam,sai yanzun"nace masa Eh Sumayya yau inne ba kasuwa shiyasa ban dawo Koh da Rana ba "Toh Allah ya bada kasuwa gobe" Ameen yace Yana aje Kwanukan a mawanki,Mika Mata talatin in yayi "Ka rike kawai agunka" Ok yace,boket ya d'auka ya ibi ruwa, band'aki ya shiga yayi wanka Yana fitowa yayi Alwala,daidai lokacin aka Kira mangari ba, masallaci ya wuce "Sallan mangariba,nayi wanka Nima zani na d'auka fille D'aya na had'a da t-shirt sai hulan bacci, Jin ana kukarin shiga sallan isha'i, Ina da Alwala hijab kawai nasa na Tada sallah, 7:40 Al'ameen ya shigo d'akin bakinsa d'auke da sallama Amsa Masa nayi"yauwa jiranka nake ka dawo daman"nace Ina mikewa Toh Allah dai yasa lfy?yace "Kasan inda ake Saida tsire"? Tsire Kuma Sumayya? Eh "tsire de" Hmm eh na sani a tsallaken titi akwai Mai nama, kusa damai shayi Yauwa karbi kudin nan 2k ne ka sai Mana tsiren 1500 sai Kuma ka sama Mana drinks Mai Dadi guda biyu yau Dadi zamuci gaskiya" sai ka sai Madara bornviter da sugar in change ya rage kasai bread Nokia Ina da ruwan zafi a flasks,sai mu karya dashe gobe da safe" A Ina Kika samu kudin nan? haka Sumayya don khadija tace mini ba kayanki Kika sayarba Sosai naji Ina Kara kaunar Khadija yarinya Mai hankali hartasan ta rufa mini asiri agun D'an uwanta, Amma ni bazan Masa karya ba"uhmm uhmm nidai gaskiya bazan maka karya ba Turarena na sayar" Amma Sumayya banace ki daina Saida kayanki ba ,ni ban Kara Miki ba, Bai kamata in rage Miki ba "Habba ya Ina da abinda Zan sayar na saka abakin salati saina zauna da yunwa tsakani da Allah fa, yau baka samu kome ba da haka Zan zauna tun safiya har warhaka banci kome ba kenan"na fada Ina Bata Rai Ganin Kamar taji haushi sai ya sassauta murya,toh Yi hakuri kawo kudin naje na saya Miki Mika Masa nayi bance kome Ba Lalubar kudin yayi harya rike,ya fita Baifi hour 1 ba ya dawo lokacin Ina kallo a d'aki Shigowa yayi da sallama Amsa Masa nayi,Ina karban laidodi Daya ke mika mini, karba nayi, na mike waje na fita na d'auko plates da cups harda flasks na shigo d'akin, bude laidan tsiren na zuzzuba a plate,Goran pineapple juice in Mai sanyi na juye Mana a cup,d'aukan NASA nayi na Mika masa,"gashi naka" karba yayi hade da Mata godiya,a hankali yasa hannunsa a cikin plate in ya dauki Naman da Bismillah yasaka a bakinsa ,lumshe ido yayi,rabonsa da yaci tsire tun lokacin da mahaifinsa kenan,bazai manta ba shike sayo musu duk dare, lokacin ma ba'a haifi Khadija ba Nima cin namana nake Ina korawa da drinks ba karamin Dadi naji ba kai.talauci ba kyau talaka sai yafi wata baici nama ba, Ashe haka talakawa keji,tabbas badon jarabawar da Allah ya jarabceta ba bazata taba sanin rayuwan Talauci haka yake ba Alhamdulillah Alah kulli halim Daga ni harshi duk nacin mu bamu iyya cinye namarnan ba, sai da muka rage wani,nikam har zafi hakorina naji yake mini kafun na aje Naman don yau cin yunwa na masa,sabanin da, da nake ma nama cin kwad'ayi kawai Jin ta aje plate nata yasashe magana,sumy Wai harkin cinye ne ga nawa ki Kara wallahih na kasa cinye wa, "Kutt bazanci sauran abinda kaci ba,Kuma nima ga nawa ban ciny......... Bai bare ta Gama magana ba taji ya fizgota sosai suka zube akan gado kanta yahau cikin gaggawa ya hada bakin su waje D'aya y'awonsa ya juye Mata a baki Ware ido nayi Jin y'awonsa cike a bakina so nake na zubar Amma ba Hali har lokacin bakin mu a hade,ji nayi kamar numfashina xai d'auke ai da sauri na had'iye Ina rumtsa idanuna Jin ta had'iye yasa a hankali ya kamo harshen ta sosai yake tsotsarta cikin zafi zafi.. Fizge bakina nayi,"don Allah ka Bari banason abinda kake minin nan"na fada Ina ta kukarin turesa a kaina Ni Kuma inaso,ya Bata Amsa,Yana Kai hannunsa, akan t-shirt nata Yana kokarin cirewa Ai bansan lokacin da na Kama kokarin fizgo kaina ba ganin da gaske fa mutumin nan riga zai cire mini Jin ta isheshe da fizge fizge shima ya biye Mata inya d'aga riga sai yaji ta jawo rigan kasa,inya cire hannu D'aya sai tasa d'ayan Tambe muka fara sosai abin dariya abin haushi,daga ni harshi mun jikkata sosai Amma ba Wanda yayi niyar barwa Dan uwansa dama ni naki yarda ya cire mini riga shi Kuma yaki yarda ya hakura, Hannu yasa da karfi ya fizge zanin jikinta, Gwalalo ido nayi jina ba zani,wani yunkuruwa nayi da karfin gaske Zan mike zaune Cikin zafi nama ya maidata kwance Yana Kara Hawa kanta, daidai lokacin mukaji sallama na muryoyin Yan Mata a kofar mu....,..... 🌾 *Juma'at Mubarak* 🌾 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin,Koh kinsan mace sai da kamshi da gyara* 😉 🍀🍀🍀🍀 *Turare suna d'ayace Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin sa* 🍀🍀🍀🍀 *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da* *gyara* 🍀🍀🍀 *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace* 🍀🍀🍀 *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE* 🍀 *Na tsunguno(habil)* 🍀 *Na jiki (kwalaccam)* ( *khumra, black & white* ) 🍀 *Turaren turara jiki after birth* 🍀 *Na d'aki(halud Al'oud)* *UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* 💃🏼💃🏼 🍀🍀🍀 *Suna bada d'aya Koh sare akan farashi Mai Rahusa* 🍀🍀🍀 *Suna bada order kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria* Contact them vie 🪀08028827241 or 09033791049 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya* *Ibrahim* 🍃 ✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwa👌 free book 🤧 Page 2️⃣6️⃣&2️⃣7️⃣ Ba karamin Dadi naji ba,da saurina Amsa musu sallamar muryata na rawa"waalaikumu salam"nace Ina kallonsa ganin baiyi niyar sakeni ba,"toh ka tashi Mana naje naji suwa ke sallama" Wayace kiyi magana? "Au amsa sallaman ne,laifi" Toh ai badon Allah kika.amsa ba ya fada Yana sauka a hankali ya kwanta a Gefen ta Jin ya sauka akaina ai da sauri na mike zanina da ya yasar a kasa na tsunguna na d'auka,fita nayi a d'akin duk jikina sai rawa yake, na barsa a kwance akan Gadon. Yan matane zasu Kai su biyar gabaki D'aya bazasu wuce sa'o'in Khadija ba,"sunnunku da zuwa" Sukam mamakine ya cikasu,wannan ne MATAR MAKAHO Mata Kamar balarabiya Aiko Mai kudi lafiyayye ba kowa bani yake sa'ar samun mace Mai kyaun Sumayya, yauwa,Ina wuni Aunty sumy? Suna had'a baki "Lafiya Alhamdulillah bara na d'auko muku abin zama" La ki barshi kawai Aunty,sauri muke ma dare yayi. "Gaskiya Kam Kuna Mata yanzun ana neman 10 na dare fa,kuna waje" Eh wallahih Aunty nasan bazaki ganemu ba,Daman mu kawayen Khadija ne,wata acikinsu tace "Kawayen Khadija Kuma aini Khadija batace mini tanada kawaye ba bayan Asma'u"nace musu haka don na gane kawayen Amaryar ne,ganinsu da Anko Eh Aunty dukan mu kawayen Khadijan ne harda Asma'u, "Toh Allah dai yasa lfy ba wani abin bane ya faru"nace Ina zullumi kar wani abinne ya samu khadija Eh Aunty yanzun ma gidan su khadija Muka fitoh akan ta rakamu wajen ki,shine tace Wai yayanta ya hanata fitan dare "Gaskiya ne Bata fita bayan mangariba, Allah dai yasa lfy kuke son ganina"? Eh lfy Daman mun tambaye tane akan inda tayi lalle da make-up jiya, Shine tace Mana Wai agun matar yayanta,. Shine mukazo mu tambaya Koh zamu samu lalle gobe,da kwalliya in Allah ya kaimu? "Bazaku samuba" nace Ina zuyawa na shiga d'aki Koh bin ta kansu banyi ba, saboda sanin da na musu sune suka ma khadija rashin mutunci jiya agun Fulani Dance. Ina shiga d'aki akan kujira na zauna, gaskiya Ina son yin lalle Koh don na samu na biyan bukata Amma bazan ma Yan iskan nan ba. Sumayya meyasa bazaki musu lallen ba? Al'ameen ya tambaye ta "Ina ruwanka watoh ka fara sa ido Koh" Ina Naga idon bare na saka ni duhu nake gani,ya Bata Amsa "Watoh kaima ka iyya bakar magana Koh" Ai agunki na koya "Badai aguna ba malam ehen" Amma Sumayya dakin musu lallen ai. "Bafa Zan musu ba Yan iskan yara bakasan me suka mini bane," Yaushe sukazo gidan nan har suka Miki Abu? "Kai jama'a yaushe ka koma D'an jaridane ban sani ba" Baimin magana ba mikewa Naga yayi Yana kokarin sauka a gadon ai ihu na saka na mike zanyi waje. Wallahih Kika fita a d'akin nan saina Miki abinda bakiso "Me kenan"? Kin fini sani,yace Yana nufar kofa, waje ya fita yaje ya rufe shashen mu ya dawo ya rufe kofan d'aki Ina dai zaune sai raba ido nake,ganin ya nufu kujiran,da nake yasa na mike a hankali na lallaba na chanja waje, zuwa gaban mirror na tsaya, Jin motsen takunta yasa ya gane lallai tabar Kan kujiran.. Fara lalube yayi nidai sai chanja waje nake in ya nufi inda nake saina chanja waje,duk magiyar da yake min, kin tsayawa nayi. Muna cikin zagaya d'akin kawai aka d'auke NEPA gashe ban San takamemmen inda na aje wayata ba. Jin tsayawar fanka,yasa ya gane an d'auke NEPA ne, shiyasa ya fara tafiya a hankali Yana laluben ta sanin da yayi yanzun itama ba ganinsa zatanayi ba. Raraba ido nake ta faman Yi banajin motsensa Sam sannan Banga wayata ba.matsawa nayi sosai jikin kujira na sunguna Zan duba wayata,ji kawai nayi ya rungumeni ta baya "Wayyo Allah nikam ka sakeni wallahih banaso" yanzun dai kema baki ganin kome kamarni. "Allah ba kamar Kai bakam" Koma yayane dai baki gani "Nikam sakeni hai" Naki yace Yana dagata "Wayyo nashiga uku,ka saukeni"nace Ina ta faman mutsu mutsu Kiye shuru Mana mu k'wanta "Niki shurun nikam ka sakeni" Kin saketa yayi duk yanda tayi ya saketa ki yayi Ina ji Ina gani ya kwanta akan kujira d'aurani yayi akansa,tun Ina masifa harnayi shuru Jin ana iska da yayafi ,sanan aka kece da ruwan sama, Baccine ya d'auke mu dukan mu biyu akan kujiran muka kwana Da safe,shayi mukasha da bread,wanke wanke na fitar Ina wanke wa Sanin da yayi Koh ya fita ba lallai bane yayi ciniki sai wani ikon Allah da safen nan, gashe mangoron duk sunyi labo labo. Kayansa ya fitar Wanda Bai wuce kala hudu ba a igiyar bayan gida inda take Tara kayansa masu datti,d'aukar basket in kayan Sumayya yayi ya fitar dashe waje ya zuye a dakali,ibo ruwa yayi ya fara wanke musu kayan. Ina wanke wanke,Yana wanki,dukan mu shuru Babu Mai magana Assalamu alaikum, khadija ce tayi sallama hannunta d'auke da laida "Waalaikumu salam khadija" Ina kwana Yaya? Lafiya khadin Goggo Ina kwana Aunty,tace tana murmushi "Lafiya khadija ya Goggo" Tana gaisheki,tace tana zama a Gefen yayanta dake zaune abakin dakali da boket in ruwan kumfa "Aiko Ina amsa wa" Aunty kinsan me? Kai jiya Naga abin mamaki,tace d'auraye kayanda yayanta ke wankewa "Me Kika gani haka"? Na tambaye ta Aunty kinsan Allah Ina fita a gidan nan,na wuce gidansu Asma'u duk inda na wuce sai ayita kallona , Ina Isa na samu an kawo mototi sunkai ashirin,kinsan Aunty mijin Asma'u shima Mai kudine? "Ina Zan sani khadija ai sai kin fad'amin"? Ina isowa wajen mototi sun cika har ana kokarin tafiya,kawai saina nemi gefe na tsaya, kawai wani abokin Ango yazo kusa Dani,Wai hajiya baki samu mota bane? Nace eh ban samu ba ku tafi kawai Zan hau machine, Wai harda cewa Wai babban Dani ba girma na bane Hawa machine bara a sama mini wajen zama, Kawai yaje ya fidda kawar amarya ya sani a motar "Hhhhhh Kai habba dai khadija"nace Ina dariya Yanzun abin dariyane agunki Sumayya an fidda wani Ansa wata,Koh ke zakiji d'adi a Miki haka, Al'ameen ya fada Yana Bata Rai Khadija Kam tsoro ne ya kamata Sam ta manta da yayanta agun ta sake baki tana zuba "Kasan me suka matane"? Koma me suka Mata hakan Bai kamata ba cin fuska ne, Fad'a Masa kome nayi akan abinda suka ma khadija Koma me suka Mata banji Dadi ba "Khadija tashi mu shiga ciki muye sirri"nace Mata Ina Kama hannunta Muka shiga d'aki "Khadija karasa mini sai akayi yaya"na tambaye ta Ai Aunty in gaya Miki kawai na Shiga abina kawayen fa Basu gagane niba sai da Muka Isa Taraba motel in da Muka fifita a motar,duk Saida suka Raina wankan su Aunty kaf insu harda Amarya Babu Wanda kwalliyar ta yayi kyau irin nawa, Sai da nama Amarya magana kafun suka gane nice, wallahih Aunty baki ga yanda aka maida ni abin kallo ba masu vedion aure sai d'aukana suke harda hotuna,Kinga agun kawaye uku nayi yaran masu kudi,samari Kuma sai turawa suke Wai suna son magana Dani a waje. Kin zuwa nayi kawayen ma naki kulasu,ai Aunty badon Allah ba kenan suke Sona, tunda Basu Soni a khadija ta ba Saida suka ga nayi kyau,ta karasa maganar tana washe baki "Gaskiya ne khadija bare ma insha Allah karatu zakiye insha Allah"nace Ina murmushi don tabbas khadija akwai kaifin tunani Aunty jiya fa goshin mangariba na fitoh a Hall in Zan dawo gida Kinga yanda abokan Ango ke ribibin zasu kawoni gida,. Amma naki, "Gwara da Kika ki khadija yanzun mutum ake kiwo. Ba dabba kad'ai ba" Wallahih kuwa Aunty kawai da dare saiga wani yazo gidan mu bansan ma waya nuna Masa ba Wai ana sallama dani, "Lallai kanwata tayi goshi" Allah Aunty kin fita nayi Goggo tayita fad'a "Don me khadija wulakanci ba kyau fa dakin fitan ai" Gaskiya ni Aunty banason Abu da masu kudi, don mudi yace mini da babban mota yazo,Kinga masu kudin nan in Kika aure su wallahih Kina Yar talaka,basa ganin daraja. Yan uwanki Ah ah khadija ba duka aka zama D'aya ba indai da kyakkyawan Niya akayi aure badon kyau Koh kwad'ayi ba,insha Allah ba abinda zai faru Hakane Kam aunty,au Ashe fa na had'a da Aunty a magana ta am sorry (don tace auren masu kudi basa ganin darajan Yan uwan matan su,in talaka wa ne) "Uhmm khadija kenan,ai Nima na zama talaka yanzun" Amma ai gidan ku akwai kudi? "Gidan mijina babu" Aunty jiya wasu sunzo wajenki karfe kusan 10? "Eh Khadija" Nima jiya suka zo gidan mu Wai na fad'a musu Wanda tamin lalle,da Wanda tamin make-up "Kawayen Amarya Koh"? Eh Aunty sune,suka mini wulakanci agun Fulani Dance "Aiko shiyasa nayi maganin su nace bazan musu lalle ba" Meyasa Aunty "Saboda kee kad'ai Zan ma kwalliya har Agama programs na auren Asma'u" Kiye hakuri ki musu Aunty Zaki samu kudi sosai fa yau HENNA DAY, Kuma da yamma za'ayi Algaita "Gaskiya khadija bazan musu ba " Shikinan Aunty ga kayanki nan na dawo Miki dasu "Habba khadija ki rike na bar miki"Daman kyauta na baki ba aro ba" Aunty' ai yayi yawa "Ki rike duka" Allah ya.......... Bata karasaba mukaji sallama na muryar mace babba Al'ameen dake zaune a waje ne, ya amsa Sannu Ina kwana hajiya,yace Yana tsame hannunsa a wankin Lafiya Alhamdulillah don Allah nan ne kofar MATAR MAKAHO?don ita Bata zata Al'ameen baya kallo ba Kafun Al'ameen ya Bata Amsa Muka fitoh a d'akin dagani har khadija kallon matar muke hajiyace Kuma hamshakiya daga ganinta naira ya zauna "Hajiya lfy" nace Ina kallon ta dajin haushin sunan da ta kirani Wai MATAR MAKAHO mtwss yauwa wajenki nazo "Ok Bismillah khadija d'auko Mata darduma" nace saboda d'akin mu D'ayane bazan iyya saka baki a ciki ba "Bismillah hajiya ga wajen zama" Zama tayi Muka gaisa Ni sunana hajiya sa'a findon Asma'u kawar Khadija kanwar mijinki nasan khadija Kam ta ganeni Koh? tace tana kallon khadija Eh Aunty sa'a, khadija tace Yauwa Daman nazone akan in ba damuwa,Koh Asma'u zata samu lalle inda halima harda mu,don jiya na turo kawayen ta sunce Wai bazakiyi ba shiyasa nazo da kaina, "Gaskiya hajiya ni Ina da aure bazan iyya zuwa in ma amarya lalle ba,tunda Henna day ne yau" Habba wallahih ba kome zamu zo har gida ki Mana itama Amaryar zatazo saiki mata,tunda ba'a d'aura aure ba kuma gida baki da hanci "Shikinan hajiya" Yauwa nace zata iyya zuwa yanzun don anjima akwai Algaita da yamma,saiki Mata kwalliya ma duka "Toh hajiya gaskiya bazaku samu lalle yauba don indai lallen Amarya ne Dole za'a jima ga kwalliya duka" Saiki Mana gobe da safe,tunda Walima ne kwalliya kawai zaki Mana da yamma saiki Mana lalle da safe, "Ku nawa ne"? Mu bakwai Zaki ma lalle da Amarya 8 Amma bansan kawayen ta mutun nawa ba "Ok za'a ma Amarya lalle da kwalliya yau"In yaso ku sai amuku gobe hannu bibiyu sai kwalliyar walima,saboda time"Amma banda kawayen don bazasu samu ba Ba damuwa Daman booking mukayi har Agama bikin zakina Mana kwalliya in ba damuwa "Ok shikinan" Nawane kudin ki? "Hajiya kwalliyar Amarya kashi biyu ne ana heavy make-up a dinner, bud'an Kai, kamu sai light make-up anayi a Walima, Algaita, Arab night Kinga kenan light make-up Zan mata yau" "Kudin kwalliyar yau 5k ne, lalle 10k na Amarya" "Kwalliyar ku 3k ne Koh wani mutum D'aya" Ok na gobe fa ? "Lallen ku na gobe hannu bibiyu ne Kuma ja da baki za'a muku a hannun dubu D'aya da d'ari biyar ne, in da lalle na Kuma 2k Koh wani mutum D'aya" Ok tace ta hada lissafi ta bani kudin a hannun,gashe kudin kwalliyar Amarya da lallen ta nayau da kwalliyar mu sai na lallen mu na gobe,in mukazo kwalliyar walima sai muyi lissafi harda na dinner,tace tana mamakin wayewar Sumayya, da akace mata MATAR MAKAHO ne ta d'auka Koh zatazo taga bagidajiya sai taga hatta MAKAHO ma bazaka zata baya gani ba Ok hajiya" nace Ina karban kudin kirgawa nayi Naga ya cika,hajiya watoh harda kudin lalle Kika bayar kenan"? Eh zuwa kawai zamuyi goben,Amma Amarya na zuwa da lallen ta,kinsan ana kawo kayan rufi da lallen Amarya ? "Gaskiya ne shikenan saina ganku anjiman" Allah yasa tace tana Mike wa ta tafi Khadija Kam da Al'ameen mutuwar tsaye sukayi,Wai kwalliyar da ake gogiwa shine za'a biya dubu biyar ayi ai gwara ma lalle zaiyi sati.. Aunty yanzun duk wannan kudin na lalle ne kawai da kitso? khadija ta tambaye Sumayya "Kai Khadija ba abin yayi bane,Kuma kayan kwalliyar ma tsadane dashi" Ikon Allah,tace "Kinga khadija tashi maza kije kasuwa ki mini sayayyan lalle sai ki sai Mana semolina yau tuwo zanyi na gaji da shinkafan nan na fada Ina Mika Mata 10k ki sai Mana harda kaji biyu a gyara Miki a kasuwan,ki hada mana da kayan Miya harda su vegetable" Toh Aunty tace tana karban kudin Al'ameen Kam baice kome ba ,Yana shanya kayanda yawanke Khadija na fita Koh minutes uku batayi ba mukaji Karan faduwa timmm sai muryar Khadija data k'wala Kara,irin na azabar nan,dagani harshi da gudu Muka nufi kofar fita a shashen mu, ganin tsabar rudewa Bai gane hanyar kofa ba yasa na Kama Masa hannu na Masa jagora Muka fitoh, me Zan gani khadija ce a.......... 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin,Koh kinsan mace sai da kamshi da gyara* 😉 🍀🍀🍀🍀 *Turare suna d'ayace Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin sa* 🍀🍀🍀🍀 *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da* *gyara* 🍀🍀🍀 *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace* 🍀🍀🍀 *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE* 🍀 *Na tsunguno(habil)* 🍀 *Na jiki (kwalaccam)* ( *khumra, black & white* ) 🍀 *Turaren turara jiki after birth* , 🍀 *Na d'aki(halud Al'oud)* *UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* 💃🏼💃🏼 🍀🍀🍀 *Suna bada d'aya Koh sare akan farashi Mai Rahusa* 🍀🍀🍀 *Suna bada order kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria* Contact them vie 🪀08028827241 or 09033791049 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya* *Ibrahim* 🍃 ✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwa👌 free book 🤧 Page 2️⃣8️⃣&2️⃣9️⃣ Khadija ce a zube a kasa cikin ruwan cab'alin rijiya,salame na ruwan cikin ta,ta hakikance sai jibganta take Sake hannun yayan khadija nayi Da wani irin gudu nayi Kan salame,don na fahimci Yan gidan nan in har baka koma irinsu ba zasu kasheka,yarinya sa'ar khadija Amma khadija ta sake jiki tana dukanta Koh martani Bata mayarwa sai k'okarin Kare kanta,kafun na Isa ba zatoh ba tsammani sai kawai Naga Iro ya kwashe salame da kafa daga Kan khadija yayi ball da ita sai da ta zube a Gefen rijiya bakin ta ya sare simintin rijiya,kafun kace me tuni ya rufe salame da duka sai a lokacin Yan gidan suka firfito,Abu kamar Wasa fad'a ya zama babba,don fadan yanzun Kam mutane sunkai biyar suke dambe,kama khadija nayi wance tunda Iro yayi ball da salame take gefe tana kuka duk jikinta sai rawa yake, "khadija tashi mu shiga kofata sannu" Mikewa tayi a hankali,suka nufi kofar shashensu Al'ameen Kam Yana tsaya Kamar andasa sa don baya gane kome tsabar yanda surutai da koke koke ke tashi a tsakar gidan,sai raba ido yake kawai Muna zuwa saitin inda yake hannu kawai nasa na Kama NASA Muka shiga cikin kofar tare, Sake hannunsa nayi, Ruwa na iba na Kai Mata band'aki na Kama hannunta muka shiga, kanta na wanke Mata kafun na fita na barta tayi wanka Kaya na makala Mata a jikin kofar band'akin, Tana fitowa. D'aki Muka shiga zaunar da ita nayi da sauri na d'auko D'an kwalina na d'aura Mata akanta dake ta zubar da jini"khadija meya hadaku meya faru? Wallahih Aunty Ina fitowa kofarki kawai nazo wuce gindin rijiya,Daman salame na iban ruwa kawai ta kwashi kafafuna na zube shine tahau kaina tana dukana,kallifa Aunty ta fasamin Kai,ta fad'a tana Kara karfin kukanta "Kiye Shuru khadija,share hawayen ki yanzun za'a bi Miki hakkinki wallahih in sunsan wata Basu San wata ba" nace Ina duba inda na aje wayata In Raina dubune yau ya baci na gaji da bala'in Yan gidan nan da Talaucin da muke ciki zamuji Koh da tashin hankali'wayana na d'auka tunawa da nayi,da wani school mate nawa lokacin da na shiga jami'a shi Kuma Yana final year insa,yanzun police ne yana da babban mukami a hukuma, muna mutunci sosai kamar yan uwa danayi aure ne dai bamu sake magana dashi ba. Me zakiye Sumayya? Al'ameen dake zaune a kujira yayi tagumi ya tambaye ta "Mataki Zan d'auka" Wani irin mataki? Akwai Wanda Zan Kira wallahih Koh tantama banayi daga gidan nan direct sai prison Koh station bazata shiga ba Kuma sai naso za'a bada belin ta". Wa Zaki Kira? "Wani friend Ina ne" Toh wallahih ba'a gidan nan ba "Ban gane ba'a gidan nan ba kenan kana nufin abarsu suci bulus kenan kaga yanda suka fasawa yarinya Kai kace a barsu" Ina dai kanwata aka fasawa Kuma nace bana bukatar ki d'auki mataki "Ok nuna mini kake khadija ba kanwata ba koh"fine shikenan gaka ga Yan gidan naku,Daman nice bare"nace Ina aje wayata na fita waje sosai maganar Al'ameen tamin zafi Wai kanwarsa Kuma yace baya bukatar mataki,watoh ba ruwana kenan a maganar Al'ameen Kam harga Allah Bai Fad'a,don wani abuba kawai ya fad'ane don ta janye maganar rufe salame,baisan maganar zai Mata zafi harta fassarasa wani iri ba Khadija Kam sosai taji Bata kyauta ba a sanadin ta ma'aurata sun samu sabani,mikewa tayi ta fita waje, wajen da Sumayya ke zaune ta karasa Aunty bara naje kasuwar "Khadija Wai kina nufin kudin nan na hannunki"? Ni na d'auka ma Koh kin yasar dashine tuntuni" Ah ah Aunty Daman a bakin zanina na soke Kuma Allah ya taimakeni Bai fad' ba "Ok kibar zuwa cefenen"nace Ina karban kudin hannunta Ah ah Aunty maganar Yan lallen fa,don Allah Aunty karki fasa lallen nan,Akan abinda ya faru. "Ah ah khadija rike 1k innan kije chemist a Miki dressed in wajen Naga har yanzun jini Bai tsaya ba" Toh Aunty na gode tace tana mikewa zata fita Khadija tsaya muje na rakaki, Sumayya ki kawo cefenen Inna rakata chemist sai na wuce kasuwar, Al'ameen yace Kala bance Masa ba don haushin sa nakeji sosai,hakurin sa yayi yawa shiyasa ake cutar sa kullum Aunty Yaya na magana Wai zaije kasuwan, "Ka barshi kawai gobe Zan aiki Yan lallen suje kasuwa su sai mini abin hadin" Toh Aunty ki basa kudin cefenen sai ya sayo muku,ya iyya zuwa kasuwa, khadija tace cikin rashin Jin Dadi ganin yanda na Had'awa yayanta fuska "Ungo"na Mika Masa 6k Matsowa yayi Yana lalube ya karbi kudin a hannuna Me da me Zan Saya? "Ka tamabaye khadija na Mata lissafi " Ok yace cikin sanyin jiki don wallahih Bai d'auka maganar zatayi zafi haka ba Suna kokarin fita Asma'u na shigowa da kawayen ta,suka gaisa da Al'ameen kafun suka shigo,khadija kuma suka fita Shimfid'a musu darduma nayi,suka zazzauna Tashi nayi naje na chanja kaya,na manna Gam a faranti,na kwaba lalle,Muka fara Khadija ta dawo lokacin kusan karfe 10 "khadija ki shige d'aki kije ki kwanta Naga an kawo NEPA ki huta kinji"nace Mata Ina kallon kanta da aka mannawa plaster Toh Aunty tace tana shigewa d'akin, kwanciya tayi a kujira,banci ya d'auke ta Al'ameen Kam kasuwa ya wuce yaje yayi sayayan kayan abinci,Amma Sam yau Baya cikin walwala tunda suka D'an samu sabani da Sumayya,don shi Sam bayason yayi abinda zai bawa wani haushi harya kullace sa abin damunsa yake Yan matan sunata Hira,inama Amarya lalle,saiga Al'ameen ya dawo da laidodi a hannunsa na sayayyan kasuwa,mikewa nayi na karbi laidan gudun kar na tozartashi a gaban su,kitchen na shiga da laidodin shima bayana yabi Yan Mata Kam sai ido suke bin MAKAHO da MATARSA suna mamaki Muna shiga kitchen in,na aje laidodin Sumayya Naga Yan sana'ar sunzo Koh Zaki kawo na girka Mana abincin? in yaso "Kai bazaka fita bane"? Zan fita Amma sai bayan azahar "Toh ka iyya girkine? koh da wani idon zaka girka Mana abinci muci"? Eh na iyya girki,sai ki jera mini Abubuwan da Zan girka Zan iyya "Bana bukata"nace Ina Shirin fita Jin Amsar da ta Bashi ya tabbatar har yanzun haushi takeji,hannu yasa a hankali ya rikota Jin zata fita a kitchen in "Ka sakeni"nace ba Wasa a muryata Sumayya kiye hakuri in abinda na fada Bai Miki Dadi ba "Ka sakeni nace maka" Am sorry "Ka sakeni" Baki hakura ba? "Ka sakeni" Toh innaki fa,ba Matata na rike ba "Matar ka ai da Ina da wannan matsayin da gaske da bazaka nuna mini banda matsayi agun khadija ba" Amma ba nace kiye hakuri ba,yace Yana jawota jikinsa "Nima ai bance maka naji haushi ba" Amma gashe sai fushi kike Haka dai Kai kake gani,nikam sakeni Rana yayi bamu karasa lalle ba Bana gani sai dai ji "Oho maka dai" Mana dai,ba ni kadai ba "Toh sakeni Mana",nace Ina banbare jikina a nasa Sumayya abinda yasa Kika ga naki ki d'auki mataki,da hukuma toh a gidan nan Babu Mai tsoron station Koh prison don ba bako bane agunsu, bare ya saka musu tsoro don kinsa an rufe salame,wata fitinar kika kunna,zaman gidan nan sai ya gagare mu "Kai kake tsoron fitina bani ba' akan gaskiya na Koh Ina zanje" In Miki girkin?yace Yana kauda maganar "Ka bare Zan girka" Toh shikinan,yace Yana saketa, Tsayawa nayi ya rigani fita a kitchen in, Ya Kama hanyar kofar fita a shashen mu Nima fita nayi,"am please bara na d'aura Abinci, Rana yayi sai nazo mu karasa" Aunty bara na d'aura miki,wata Yan Mata a cikinsu tace "Ah ah ki bare kawai"nace Ina tunanin karfa Bata iyya girki ba ta Bata mini kaji a banza Kai Aunty Koh dai kina tunanin ban iyya girki bane? Ba haka bane,Daman Ina tunanin karna takura Miki ne,Amma tunda kina sonyi shikenan,ki tuka semo laida babban duka, Kitchen ta shiga ni Kuma d'aki na shiga naje na leka khadija har lokacin bacci take Sai azahar na kammala lallen Amarya,na tashe khadija mukayi sallah abincin da farida kawai Amarya ta girka na zubawa yayan Khadija nasa, na zuba na Daren mu, sauran na zuba ma kawayen, na ibawa Amarya na zuba Mana da khadija,sosai Tuwon yayi Dadi,bamu Gama ciba aka turo yara da kulolin Abinci daga gidansu Amarya shinkafa muka dad'a, yaran na baiwa na yayan Khadija su Kai masa Ganin da sauran lokaci yasa nama farida lalle (wance tamin girki) Sai la'asar Asma'u tayi wanka sosai na zuba Mata light make-up tayi kyau Kamar me,ganin kawayen nata d'aukar ta hoto yasa Nima na fitar da wayata,na d'ad'auki hotonan lallen ta da kwalliyar da na Mata duk da hoto nason gida Mai kyau Amma wanka na gyara hoto ma ba gida kawai ba ************ Bayan tafiyar Amarya da kawayen ta, wanke wanke nayi na share kofar don yayi kaca kace,kowa yasan gidan Mai lalle in ta Tara customers,yanda yake baci Wanka nayi,donna gaji sosai yau innan,vest nasa na d'aura zani don ba kowa a kofar nawa khadija ma ta tafi gida,don yau ba zuwa program Kai ya fashe Bayan sallar mangariba ya dawo Kamar kullum wanka yayi mukaci Tuwon da farida ta dafa Mana da rana Bayan sallan isha'i yau Koh jiran ya dawo masallaci banyi ba na kwanta don gabaki d'aya bacci nakeji ba kad'an ba ga gajiya sosai. Yana dawowa ya tarar tayi bacci shima gadon ya hau don tabbas yau yasan ta gaji,tabata yayi yaji alamun bacci take,a hankali ya cire mata vest in jikinta daga ita sai wandon bacci,shima kayansa ya cire dagashi sai guntun wando a hankali ya rumgumeta,kome a hankali yake gudun karya ta tashi,sosai yaji wani irin yanayi Mai matukar shauki a tare dashe,amam haka yake dannewa,har bacci ya dauke sa Misalin karfe 3 na asuba kamar a mafarki naji ana tattaba min kirji da sauri na bude ido,tashi nayi na zauna jina ba riga,sake taba jikina nayi don na tabbatar Aiko da gasken bani da riga, "Wai meyasa kwana biyun nan ka chanja ne kanamin abinda ranka yake so"? Mutum da halaliyarsa, ya Bata Amsa Kamar Wanda tama Dole "Ka tashi mini a wajen kwanciya" Ina kenan? "Gado" Naki, gaskiya yanzun bazanna kwana ni kadai ba alhalin Ina da mata. "Don Allah nikam ka tashi, kaga yanzun ma Banga rigata ba ga d'akin duhu" Saiki kwana haka "Akan wani dalili Zan kwana ba riga,Kuma karka sake ciremin riga in Ina bacci banaso" Inna cire fa? "Au tamabaya ma kake sai me? Eh tambaya nayi "ka Dameni sai surutu kake sani tsakar dare" Wani dare ai na yau ya wuce sai dai na gobe "Ka tashi nace" Naki "sauka zanyi na bar maka d'akin ma in baka sauka ba" Toh na hanaki ne Mikewa nayi na sauka akan gadon nayi hanyar kofa Koh riga ban dashi, Ba riga Zaki fita waje? "Ai baka fini ido ba"nace Ina kokarin bude d'aki, kawai ji nayi y........... *Aye manage in page bani da charge* 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin,Koh kinsan mace sai da kamshi da gyara* 😉 🍀🍀🍀🍀 *Turare suna d'ayace Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin sa* 🍀🍀🍀🍀 *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da* *gyara* 🍀🍀🍀 *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace* 🍀🍀🍀 *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE* 🍀 *Na tsunguno(habil)* 🍀 *Na jiki (kwalaccam)* ( *khumra, black & white* ) 🍀 *Turaren turara jiki after birth* , 🍀 *Na d'aki(halud Al'oud)* *UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* 💃🏼💃🏼 🍀🍀🍀 *Suna bada d'aya Koh sare akan farashi Mai Rahusa* 🍀🍀🍀 *Suna bada order kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria* Contact them vie 🪀08028827241 or 09033791049 IG @umsadincenseIG @umsadincenseIG @umsadincenseIG 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya* *Ibrahim* 🍃 ✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwa👌 free book 🤧 Page3️⃣0️⃣&3️⃣1️⃣ Ji kawai nayi ya rumgume ni ta baya, zare ido nayi jinsa shima ba riga,mannani yayi da jikin kofar shi koma ya rumgume ni sosai ya d'aura kansa a kafad'ata "Wai menene haka don Allah" ? Dadi ne,ya Bata Amsa "Dad'au matau" Jin Amsar da ta Bashi yasa ya juyo da ita da karbi ya rungume ta Ware ido nayi jina sukutum a kirjinsa dukan mu ba riga "Wayyo Allah meye haka" Mele,shima ya Rama "Nikam.ka sakeni" Bakinsu ya hada,a hankali yake kissing in lips nata na sama Bansan garin Yaya ba Koh yaushe ba na tsinci kaina da Kama lips nashi na kasa Nima na shiga tsotsa Jin ta Kama Masa lips yasa a hankali ya zame bakinsa cikin nata,ai da sauri yaji ta kamo kansa ta sake maisa bakinsa cikin nata Sosai suka shiga farantawa junan su Rai , ba zatoh Koh tsammani muka zube a kasan cafet,nice a sama shi koma a kasa, da sauri ya birkitota kasa Yana lalube da D'an kokarinsa zai zame Mata wandon baccin da ke jikinta Da sauri na Kama hannunsa Jin aika aikan da yake so yayi Don Allah ki bari musamu nutsuwa "Nidai wallahih ah ah" Please kinji Kokarin mikewa na fara a jikinsa, Da sauri ya kamota,Ina Zaki "Anafa Kiran sallah" Sakinta yayi Jin da gaske Kiran Assalatu ake Mikewa nayi a hankali daga jikinsa Jin ya sake ni,"d'akin ba haske fa" Ki kunna glop Mana "Bana gani" Ok bara na lalubo glop in "Toh,Ina rigana"? Bara na kunna wutan sai ki duba,yace Yana mikewa daga kasan cafet Mikewa yayi Yana lalube ya Isa wajen makunnen NEPA ya kunna D'akin ya gauraye da haske,da sauri na rufe kirjina da hannu sai koma nayi tsaki tunawa da nayi bama gani yake ba Menene kike tsaki kuma? "Banga rigana ba" Riga Koh vest? "Oho" Wai kikam wace irin matane Mai tsewa "Green in Mata ka aura" Toh Green Sumayya,mu fita kar ashiga sallah? "Kai ka fita Mana Koh na d'aureka ne" Toh Green sumy Lalle mutumin nan ya Raina mini wayo,ji kawai nayi ya kamo mini hannu Yana kokarin fita Dani a d'akin cikin lalube "Ban saka rigaba ka sakeni Mana pls" Sakin ta yayi Jin Wai Bata da rigan da gaske Bayan fitar shi rigana na d'auka na fitoh Jin harya kammala Alwala ya wuce masallaci Bayan idar da sallah dukan mu bacci muka koma Misalin karfe 7:00 na safe aka doka Mana sallama a kofar d'aki,bude ido nayi a hankali ganin Yana kokarin sauka a gadon yasa na gyara kwanciya Amsa musu yayi ya zura jallabiyar sa ya fitoh, Ina kwana yayan Khadija? Lafiya Alhamdulillah Gun Aunty Sumayya mukazo,Yan matan sukace Ok,bara na kirata yace Yana komawa d'akin Hawa gadon yayi,ya yaye blanket inda ta rufu "Menene"? Baki kikaye,Kamar Yan lallen ne fa "Gaskiya bazan tashi ba suje su dawo anjima" Ah ah Sumayya wulakanci ba kyau ki lallaba dai ki tashi kinji Green sumy "Wallahih Inka sake fad'amin sunan nan Mai rabani da Kai sai Allah" Me Zaki mini ai Babu abinda Zaki mini sai abinda Allah yaso "Hmm" kawai nace na mike,fitowa nayi na shimfid'a musu darduma muka gaisa Yan matane guda biyu Amma ba kawaye bane, "ban fa Saya lalle jiya ba bansamu D'an aika ba gashi 8:00 ake bude kasuwa Koh zaku karba kuje ku sayo"? Eh Daman mu biyu mukace bara muzo kafun a Gama Mana kafun sauran su karaso,ba damuwa a bamu kudin bara muje mu sayo in "Ok bara na kawo muku kudin"dakin na shiga na d'auko musu kudin,suna fita wanka nayi na kimtsa kofata yayan Khadija ya ibo Mana ruwa, Shinkafa da wake dafa duka na dafa Mana direct harda na Rana Bayan mun karya fita yayi, ni Kuma muka fara lalle, Sai kusan 3 na karasawa matan lallen su dukansu su bakwai kowa hannu hannu na Masa ja da baki,sai kwalliyar walima Gaskiya yauma ba laifi na damka kudi Mai tsoka sosai.. Naso.muyi cefene Amma yau khadija batazo ba ni koma ba fita nake ba bare na aiki yaro Yayan Khadija Kam Yana fita yaje ya bude mangoron sa duk sun rube haka ya zubar dasu don Koh ya bude ba Saya za'a yi ba haka yayita zama har yamma don yasan tabbas Sumayya zata sama musu na abinci Amma yanajin kunya ace kullum ita ke ciyar dashi Haka yayita zama sai mangari ba ya mike bayan yaje masallaci ya kamo hanyar gida jiki a sabule Bayan sallar mangari ba ruwa na Ina na shiga wanka Yana shiga gidan da sallama ya shigo kofar Jin shuru Bata Amsa ba ya zata Koh tana d'aki ne,ruwa ya Iba ya shiga ban d'akin Goga soso nake a zaune kawai naji mutum ya shigo bayan gidan A matukar tsorace na kwana Kara,"wayyooo" Shikam zuciya D'aya ya shiga bandakin Bai d'auka tana ciki ba shiyasa ihun yazo Masa unexpected,yasa ya gigice, Sam Bai d'auka dalilin shigarsa bane yasata ihun,d'auka yayi Koh wani mummunan abune ya same ta Subhanallah Sumayya lafiya? yade? yace Yana matsowa inda yaji ihun nata "Wallahih Inka zo inda nake saina kwara maka ruwan nan",nace cikin tsawa Ina d'aukar bokatin ruwan wanka na in,damuwa na kawai na ja towel inda na makala a saman kofar band'akin,na d'aura Sai yanzun ya gane dalilin ihun nata,manna Mata hauka kawai yayi ya Kama cire riga "Wallahi ka fita a toilet innan na ratse Zan kwara maka ruwan nan",duk tabi ta rikice Ikon Allah waini idone Dani bare na kalli abinda kike boye wan Kuturu,kawai nace,Ina daga boket in ruwan ganin Yana matsowa inda nake Jii kawai yayi shaaaaaaaa Sumayya ta kwarara Masa ruwa,Bai d'auka da gaske take zata kwara Masa ruwan ba, Nikam ganin Yana ta faman sharte ruwan fuskar sa yasa,na ruga zanyi waje da gudu Koh Kaya bansa ba , Ai.jin gudunta yasa ya bita shima da gudun Ina kokarin fita a band'akin kawai naji ya jawoni ciki, Allah yasa Ina kusa ta towel jawosa nayi a hannusa Wallahih Sumayya baki Isa ba ki kwaramin ruwa Kuma ki.gudu Ganin fa na shiga hannu,inda Allah yasoni ma na d'aura towel in"don Allah kayi hakuri yayan Khadija kuskure ne" Kuskure ai baki isaba kinji na rantse Kuka na fara ganinsa in yaci serious,Babu Wasa a fuskarsa da gaske yake b barina zaiyi naci bulus ba "To Kayi hakuri" Naki,ke Inna Miki Abu ai baki hakura "Wallahih inayi kaji yayan khadija" Bazanfa hakura ba malama To me koma Zan maka Koh dukana zakayi ne? Ah ah wanka Zaki mini "Wanka"😳? Eh Kinga Daman ba gani nake ba kullum.bayana baya fita "Nima ai bana ganin bayana kuma ni ban iyya ma manya wanka ba" Ah ah kina kallo Mana,Kuma Zaki koya "Wallahih ni banason irin abinnan, nace maka ka sakeni kanaji fa ana Kiran isha'i Kuma sai magana kake sani a bayan gida kasan ba kyau fa" Tsakanin nida ke waya fara magana a ban d'akin nan tunda ba idone Dani ba, ba kallo Miki abin zanyi ba me na ihu harda kwara mini ruwa🤥 "Toh kayi hakuri kaji yayan Khadija wallahih mantawa nayi baka kallo" Da gaske kina mantawa bana gani? "Eh sosai ma,ai ba kowa.ke.ganinka yasan baka kallo ba"nace don ya barni Ok wayo Zaki mini kenan harda wani yabona toh naki wayon in Kinga na barki kin fita toh kin zabi Daya a cikin ukun nan, Koh ki wanke mini baya Koh ki wanke mini Kai Koh ki haske mini gemu Lallai mutumin nan yaga wajen baccina nice ma Zan wanke Masa baya Kai Koh aski, Toh Zan maka aski Amma sai gobe kasan yanzun dare ne bazaiyi kyau ba gashi ba NEPA Kai Kuma bakada shaver" Kinyi Alkawari Zaki aske mini gobe? "Eh" Toh wanke mini "Toh,ka sake mini hannu Mana saika zauna na wanke maka" Na sakeki ki gudu "Allah bazan gudu ba" Ban yarda ba Yace Yana Jan hannuta,ya zauna akan kujiran hannunsa na rike da nata "Toh a hakan Zan wanke maka Kai kana rike da hannuna" Ai Inna sakeki nasan guduwa zakiye "Allah bazan guduba" Toh tunda kikace Allah na sakeki,yace Yana sake Mata hannu "Ina abin wanke Kai in"? Gashe yace Yasa hannu a k'wandon soson nasa ya d'auko guntun soda,gashi nan "Kana nufin da soda Zan wanke maka Kai"? Eh man ba Yana kunfa da cire datti ba "Uhmm Ina zuwa",nace Ina kokarin nufar kofar band'akin Kinye alkawari fa Zaki wanke mini,shine kike son gudu "Abu Zan d'auko na dawo" Toh yace Yana kokarin cire jikekken rigansa Ina fita a band'akin na shiga d'aki bude akwatina nayi na d'auko Abubuwan wanke gashi, na Mata masu kyau da shaver,na dawo ban d'akin wayata na kunna na jinginasa da jikin gini matsowa nayi inda yake zaune daga shi Sai wando dogo na jeans Rangwafawa nayi na fara wanke Masa gashinsa sosai na zuzzuba Masa Abubuwan wanke Kai gashinsa mai yawa irin na Fulani,sosai ya fita nasa Masa Abubuwan laushin gashi cikin Yan minutes gashinsa yayi masifar kyau, shaver da na d'auko na saka Masa a fuska zan aske Masa gemu Ke sumayya ragewa fa zakiye ba askewa ba "Na sani ai"nace Ina gyara Masa gashin gemun Ina Gamawa nace NASA"ka duba Koh yayi" Ina Naga idon dubawa sai dai na taba,ya Bata Amsa Yana tana fuskar sa, gaskiya kin iyya gyaran fuska "Uhmm kasan me"? ah ah saikin fada "Ai.......ban karasa ba Jin ana kokarin shiga masallaci sallan isha'i yasa ban karasa maganar da nakeson Yi ba, "kaYi sauri ka kwara ruwa ana shiga sallah"Ina maganar na fita a band'akin Jin fitarta yayi wanka shap shap ya tafi masallaci Yana fita ruwan wanka na Kuma ibo wa na Shiga band'aki,Ina wanka inata tunanin shin yau meke damuna ne Abubuwan da suka faru sai bani mamaki suke Ina fita na shiga d'aki bayan nayi Alwala sallan nayi na kwanta akan kujira don yau ba karamin gajiya nayi ba don Koh girkin dare bansamu nayi ba gashi inason zuwa gidan Goggo Amina na duba Kan khadija yau kwata kwata ban ganta ba Sai kusan 8 ya shigo d'akin, Sumayya kin kwanta ne? "Eh Amma idanuna biyu" Jin muryar ta saitin kujira,yasa ya nufo inda take Ina kallonsa harya ido wajen kujiran Yana kokarin zama mini akan kafafu da sauri na mike zaune na nade kafafun nawa"yanzun zama mini zakaye akan kafafu daban d'aga ba ka karyamin kasusuwa Koh me"? Au kafarki nagun ne?ya tamaya "Kaji nace maka Ina kwance sannan kazo zaka zauna akujiran" Sanann yanzun kana tambaya ta Ina kwance ne" Sorry yace Yana zama a inda ta d'aga kafartata, Sumayya!! Na'am Sumayya Ina Mai baki hakuri nasan tabbas band'auke Miki nauyin da ya rataya akaina a matsayina na mijinki b Ina Mai neman afuwanki wallahih Sumayya bani dashine shiyasa yau kwana biyu ban baki kome ba "Ba kome ai nasan baka dashin ne sannan ni don na samu na sai Mana abinda zamuci ai ba kome wata Rana Allah zai baka kaima sauka sai mana"nace Ina kallonsa Nagode Sumayya Allah ya saka mini da alkhari "Ameeeeeen Daman jiranka nake kazo muje mu duba jikin khadija kasan yau ban samu zama ba tun safe" Amma bakin gaji ba ki bari gobe Mana sai muje "ah ah muje dai, gobe ma akwai masu zuwa kwalliyar bud'an Kai dana dinner har dare Ina busy" Ok toh yace Yana mikewa Hijjab nawa har kasa na d'auka nasa da karamin purse D'aukar sandar sa yayi ya tsaya Yana jiranta a kofar d'akin "Yau fa bazaka tafi da sandar nan ba atoh" Akan me? "Akan zaka fita Dani" Ke asuwa? "Asu masu ido" nace Ina kamo hannunsa ba musu ya aje sandar Tsaya na rufe kofar, yace Sake Masa hannun nayi ya rufe mana kofar,Yana rufewa sake kama Masa hannun nayi Muka fita a shashen mu Tsakar gidan kaman ba dare ba duk jama'ar gidan na zazaune wasu a taburma wasu a kujira,nidai ganinsu baisa na sake hannunsa ba Ke fasuma Wai me kika ganine a tare da miskini kike zaune dashi kamar auren tsafi,d'aya daga cikin Yan gidan Tama Sumayya gogar zana Ai toh auren tsafinne Mana inba haka ba mutun da arziki ya zabi Talauci,fasuma ta bata amsa.. Nikam ban tanka musu ba Donna fahimci Yan gidan nan sai shiriyar Allah don mutum Kam sai wani ikon Allah,tunda mutuwar inno Bai saka sun tsakaita da dambe da cacar baki ba ai hukuma ma bazata iyya dasu ba, kamar yanda Al'ameen yace Waje muka fita,Ina rike da hannunsa muna tafiya,duk.inda muka wuce sai an bimu da kallo bare ga mazan unguwan da Basu sanni ba suna Daijin kwatance a bakin matansu,duk.madalisan da Muka wuce bin mu ake da kallo ga hasken sola ya haska Koh Ina, a hakan har muka shigo layin su Goggo Amina, na saima Khadija kankana da lemo, da sallama a bakina na shiga gidan,don shi yace bazai shiga ba sai ammasa iso "Assalamu alaikum" Waalaikumu salam barka dai Sumayya sannu da zuwa Goggo Amina ta fad'a tana shimfid'a mini taburma "Yauwa Goggo Ina wunin ku" "Lafiya Alhamdulillah Sumayya kece da Daren nan" Eh Goggo tare muka taho na fad'a Ina sunkuyar da Kai,(Wai kunya🤥) Shine ya tsaya a waje ai aikin muhammad kenan kamar gidan bakonsa ne,kice ya shigo "Toh Goggo" nace na koma kofar gida "Ka shigo"nace Ina juyawa Toh kin hanani rike sanda sanna kin tafi kin barni "Yanzun bazaka iyya shiga da kanka ba"? Eh bazan iyya ba Uhmm kawai nace na Kama hannunsa da yake dare ne koma ba NEPA sai da muka kusa isa kusa da Goggo na sake Masa hnnu, Zama nayi a taburman shi Kuma ya zauna a kujira, Goggon Ina wuni? Lafiya Muhammad hala kunzo duba khadija ne? "Eh wallahih Goggo shuru yau najita bata zoba shine muka taho mu duba Koh kan nata ne har yanzun"? Wallahih Sumayya ta fad'amin abinda ya faru,zaman gidan mu sai hakuri kuma.ku Kara hakuri kinji kome zai wuce "Ba kome gaggo" Aiko khadija kam.na kwance a d'aki yau Koh fita batayi ba Kai na ciwo ga zazzabi duka,Daman khadija akwai raki ku shiga ku duba ta,inji Goggo Mikewa mukayi, muka shiga d'akin Khadija ce a kwance tana bacci, Fita mukaye don bamu tashe taba "Toh Goggo zamu tafi ga wannan ba yawa Allah ya Bata lfy wannan Kuma 5k ne yayanta ya bani Wai na baki koh gobe saita je asibiti"nace Ina aje laidan da na shigo dashi,hade da mikawa Goggo kudin Wai Al'ameen d'awainiyane har haka daka bare Koh chemist taje goben sun Kara Mata wasu magani Koh na 200 ma Al'ameen Kam mamakine ya kamasa yaushi ya samu kudi har 5k da zai bawa khadija,Amma Sumayya tace in jisa, "Goggo taje asibitin dai zaifi tunda jiya chemist in ta fara zuwa ba'a dace ba"na fada Ina taka kafar yayan Khadija Jin yayi shuru baice kome ba Am am gaskiya ne Goggo ki karbi kudin inyaso taje asibitin Amma kudin yayi yawa ai muhammad Ba wani yawa Goggo In change ya rage ku rike zai D'an rage muku wasu Abubuwan Kai Amma mungode muhammad, Sumayya Allah ya saka "Ameeeeeen" har muna hada baki dashi Fita mukaye daga gidan Goggo Amina kafun na rike Masa hannu Jin tayi hanyar titi ba hanyar gida ba yasa yace Mata Sumayya Ina zamuje koma bafa nan bane hanyar? Sai da Kai zanyi nace Ina tare keke napep............ 🏵️🏵️ *Gaisuwa na musamman da fatan Alkhari ga special FAN'S na MATAR MAKAHO Naga sakonku, Allah yabar kauna,Ina godiya* 🏵️🏵️ 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin,Koh kinsan mace sai da kamshi da gyara* 😉 🍀🍀🍀🍀 *Turare suna d'ayace Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin sa* 🍀🍀🍀🍀 *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da* *gyara* 🍀🍀🍀 *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace* 🍀🍀🍀 *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE* 🍀 *Na tsunguno(habil)* 🍀 *Na jiki (kwalaccam)* ( *khumra, black & white* ) 🍀 *Turaren turara jiki after birth* , 🍀 *Na d'aki(halud Al'oud)* *UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* 💃🏼💃🏼 🍀🍀🍀 *Suna bada d'aya Koh sare akan farashi Mai Rahusa* 🍀🍀🍀 *Suna bada order kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria* *Contact them vie* 🪀08028827241 or 09033791049 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya* *Ibrahim* 🍃 ✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwa👌 free book 🤧 Page3️⃣2️⃣&3️⃣3️⃣ Keke napep na sayar ban kulasa ba Hajiya Ina Zaki?Mai napep in ya tambaye Sumayya. "MEGA restaurant" na basa Amsa Ok hau muje Sumayya restaurant Kuma?Koh dai banji daidai bane? Al'ameen ya tambaye ta "Daidai kaji,yau agun zamuci abincin dare,banyi girki ba" Sumayya ai akwai wajen Saida abinci Koh round about ana sai dawa basai munje restaurant ba. "Nidai gun zamu Kuma sai kaje" Wai hajiya bazaku hau bane? Koh nayi tafiya tane? ,kun tsaidani Kuna Bata mini lokaci ga dare nayi "Yi Hakuri. yayan Khadija muje" nace Ina Kama hannunsa muka shiga keken A MEGA restaurant, Mai keke ya saukesu Biyansa nayi kudinsa bayan mun sauka,Kama hannunsa nayi muka shiga ciki, Al'ameen Kam binta kawai yake baida baki ,sai dai yaji sun shiga wani waje Mai mugun sanyi sai Kuma D'an motsen jama'a d'aid'ai ku Har lokacin Ina rike da hannunsa,D'aya daga cikin kujerun dinning table dake wajen,na nufa ja Masa kujera nayi"ka zauna"nace Ina zama a nawa kujeran Ok , yanzun cikin inda muke nan shine restaurant in? ya tambaye ta Yana zama "Eh Mana Hala baka taba zuwa ba"? Nasan restaurant Amma bana shiga. "Toh yau ka shiga" Waiter ne yazo, sannunku da zuwa mega restaurant,ga list nan ka duba abinda za'a kawo muku,yafada Yana mikawa Al'ameen Takardan hannunsa "Yauwa bani Anan"nace Ina karban list in. "Me za'a kawo maka"? Duk abinda kike so, Al'ameen ya Bata Amsa "Tamabyar ka fa nayi" Amsa na b'aki "Ok toh a kawo maka tuwo Koh shinkafa Koh doya"? Aban doya Ok,mikawa waiter in nayi hade da basa amsa"ka kawo plate biyu D'aya na doya da miyar kaza,D'aya Kuma fried rice with chicken yaji vegetable sosai,in Kuna da exotic a had'a mana da ruwa" Ok ma, an gama,ya karbi takardan in ya wuce Sosai mutanen restaurant in suka bisu da ido tun shigarsu kowa yake gulman su da ido wasu Kam har kasa hakuri sukaye sunayi da baki,abin mamaki ya Basu ganin matsiyacin MAKAHO Koh suturar arziki Babu a jikinsa,mace Kamar Sumayya tana rike da hannunsa Koh tantama Babu daga ka gansu kasan ma'aurata ne,Amma kallo D'aya zakama Sumayya kasan ba karamar classic bane Bayan an kawo Mana abincin,tura Masa nayi nasa a gabansa shukali na Mika Masa"ungo shukalinka abinci na gaban ka" Abinci muka faraci a nitse idon mutane na Kan mu sosai har abin ya takurani Sumayya!! "Na'am" Nikam wajen nan akwai mutane sosai ne? "Eh akwai Amma ba sosai ba kasan yanzun dare ne" Amma dai kallon mu suke koh? Mamakine ya kamani Amma na maze, "ah ah ba Wanda ke kallon mu kowa harkar gabansa yake,Amma meyasa ka tambaya" Jikina ya bani ana kallo nane tunda muka shigon nan "Aiko ba Wanda ke kallon mu",na basa amsa Taima ke kike kallona. "Akan me Zan kalleka Kuma"😒? Waya sani Koh kyau na Miki,Kinga dogon hanci "Ina abin yake bare a yabasa" Abinci muke ci muna Hira har muka Gama Amma dukan mu bamu cinye duka ba, list aka akawo mana,na duba kudin mu dubu 3,800 ne, bude Purse nayi nabiya kudin, ordern ice cream nayi aka Mana takeaway a laida Mamakine ya Kama Al'ameen yanzun abincin da sukacin nan shine 3800 ,ai cefenen dubu uku da dari takwas zai musu wata ma suna dafawa. Suna fitowa a restaurant in ganin titi ba napep yasa Sumayya duba wayar ta Karfe 10:3 na dare ne,"asaifa mun jima a wajen nan 8 fa Muka bar gida" Gaskiya Kam Kuma bana majin dirin machine sai mototi "Ba machine Kam sai dai mu taka da kafa"na basa amsa Ina Kama hannunsa muna tafiya inda Allah ya somu ma tsakanin sintali da mega ba nisa sosai "Nikam azumi saura wata nawane"? Saura sati nawa dai?ya Bata Amsa "Satitika kenan baikai wata ba?Ashe shiyasa aketa aure aure" Gaskiya Kam saura sati uku da kwana hudu Lalle kam,"kasan yanzun haka gobe, za'a yi bud'an kan Amarya da yamma,sai ayi fitan Angonci duka,da dare Kuma dinner,Kuma nice duka Zan musu kwalliya, shiyasa nake son in Allah ya kaimu gobe sai ka nemo mini yaro yaje Mana kasuwa Ina son Gama girki da wure" Yaro Kuma wani yaro.kike ga Zan iyya aika a unguwan mun nan har kasuwa ,sai dai naje kawai tunda khadija ba lfy. "Toh Allah ya kaimu,ni chemist ma nakeson mu shiga nasai maganin gajiya,Amma dare yayi" Ah ah Sumayya da kankantan shikarunki karki Bata shi dashan maganguna, don kina aikin gajiya,in Kika riga Kika saba,toh zai biki Koh yaushe kikaye aiki sai kinsha "Gaskiya ne Amma wallahih bayana ya tokare ni sosai,gashi yanzun ma sai tafiya muke da kafa" Da kafa suka taka har sintali suna tafiya suna Hira,Dayake gidan Adara ba'a rufesa Koh karfe d'ayan dare ne yasa suka samu kofa a bude, Shigan su, suka shige shashen su bakin su d'auke da sallama Al'ameen ne ya bude d'akin Muna isa ruwa na iba duk yanda nake tsoron toilet in dare yayi Amma zafin da nakeji Bai barni naji tsoron ba, band'akin na shiga na kwara ruwan na fito, d'akin na shiga. Al'ameen na zaune a Kan kujera Yana jiran Sumayya ta fito shima ya shiga Wanka don yaukam ba NEPA an d'auke "Assalamu alaikum"nace Ina shigowa d'akin Waalaikumu salam, gaskiya yau Kam Alhamdulillah akwai.zafi Kam "Gaskiya ni a waje ma zanyi shimfid'a yanzun" Ok.bara nayi wanka daidai kinyi shimfid'ar?yace Yana fita a d'akin ban d'aki ya shiga bayan ya ibi ruwan shima Yayan khadija na fita na saka.kayana saboda zafin da ake have vest na saka ,da wandon bacci fankalele shara shara har kasa,kayan shinfid'a na fitar na shinfid'a mana darduma a baranda na shinfid'a zanin gado da filoluka, kwanciya nayi a gefe tsabar gajiya Koh hula ban saka ba,bayana sai damuna yake koh bacci na kasa. Yana fitowa d'akin ya shiga 3quiter yasa Koh riga baisa ba ya rufe kofar, ya nufi inda yake kyautata zaton agun ta musu shimfid'a Ina kwance Ina kallonsa harya matso inda nake kwance hannu yasa ya tattaba shimfid'ar sai Kuma ya fara laluben Kan shinfid'ar bayan ya xauna. Jin ya tabata yasashe Hawa Kan shinfidar kwanciya yayi a Gefen pillow n da ta d'aura kanta akai "Bakaji pillow da na aje maka bane" Naji Mana Amma a naki nakeson kwanciya "Kaga ka rabu Dani jikina ciwo yake mini" Hannu kawai naji yasa a bayana Yana mammatsa mini baya,naso hanasa amma Jin yanda message in ke kauda tsamin da bayana yake mini yasa nayi Shuru Yana ta mamatse Mata baya da kafa duka har yaji tayi bacci, gyara Mata kwanciya yayi,daga kefuwarda tayi shima ya kwanta a Gefen ta bacci ya d'aukesa. Misalin karfe biyu na dare ya farka Jin iska na kad'awa ga kamshin kasa na tashi bude ido yayi sosai, ya mike zaune hannu yasa ya taba Sumayya Aiko tana kwance Koh juyawa Bata sake ba tun gyarata da yayi, Sumayya!! Sumayya!! "Ummmm menene"nace cikin magagin bacci don harga Allah yau dai baccin gajiya nake Ana iska ga hadari,ki tashi mu shiga d'aki "Da wani idon kaga hadarin ni wallahih ka barni nayi bacci",na fada Ina gyara kwanciya Sumayya ruwane fa da gaske Shuru na Masa abina na koma bacci Jin Taki tashi yasa ya mike key ya d'auka ya bude d'akin, d'aukarta yayi a hannu a hankali yake tafiya Yana lalube harya shiga da ita d'akin,Kan gado ya haura ya kwantar da ita,Jin an Soma yayafi da sauri ya fitoh a d'akin shimfid'ar su ya tattara ya Kai d'aki randar robansu ya zubar da ruwan ya hada da bokataye ya jejjera a bakin baranda,daidai lokacin aka fara ruwa sosai Kamar me . Alwala yayi ya shiga d'akin sallaya ya d'auka ya shimfid'a wa yayi ya Tada kabbara,lafilfilu yake har kusan karfe uku na dare kafun ya kwanta shima a gefenta *Washe gari* Kamar kullum yaukam da safe kudi na basa yasai Mana manya manyan gongomin Madara da bornviter na sai suga Rabin kwano Lipton kwali d'aya na had'a da cornflakes,dashi muka karya ya fita Al'ameen kam yasan baida abinda zaiyi haka ya fita yaje ya zauna a bakin titi ya rasa mafita Allah ya gani Yana iyya bakin kokarinsa wajen niman abinda zai rufawa kansa asiri,Amma abin yaki yasan kome na Allah ne Kuma Bai manta dashi ba a hakan ma yana kara godewa Allah tunda Sumayya nada rufin asiri da ace Bata sana'a a war yanzun da kayan abincin ta ya fara karewa baisan yanda zaiyi ba. *********** Khadija ce ta shigo bayan sallan azahar lokacin Ina kanwa matan da suka zo make-up, Assalamu alaikum "Waalaikumu salam" dukan mu muka amsa Mata "Ah ah khadin Goggo idonki kenan"?nace Ina kallonta sanye take da atamfar dana Bata riga da zani sai gyle da takalmi harda jaka sai laida Mai tambarin asibiti a hannunta sosai tayi kyau fuskarta tayi fayau alamu dai batajin dadi,abinka da farin fata Wallahih Aunty na fitoh asibitine nace bara dai nashigo yau Goggo takece mini kun shigo da dare Ina bacci. "Eh wallahih mun shigo da yayanki nace abarki kawai kar a tasheki" Allah sarki,tace tana gaida matan dake zazaune suna jiran na Gama wa Wanda nakema make-up "Khadija ki shiga d'aki Mana akwai NEPA ki jona kittle akwai kayan shayi asaman freezer" Aunty bazan iyya shaba bakina ba dadi Sam shiyasa koh abincin dare ban iyya ciba Haka karyawa ma. Ah ah khadija dadai kin daure kinsha shayin Daya fi Amma ace bakinki ba Dadi saiki kicin abinci,ai ko magani in ba abinci baya aiki,D'aya daga cikin customers nawa ta fad'a "Gaskiya ne khadija,ki shiga in kinsha saiki kwanta ki huta" Toh Aunty tace tana shiga d'akin, kittle in ta d'auko ta zuba ruwa ta jona,shayi ta hada kad'an ta iyya Sha ta balle maganin Tasha kwanciya taye lokaci D'aya bacci ya d'auke ta Sai kusan 4:30 na Kamala wa sauran kwalliyansu Daman Amarya tun 3 na yamma na Gama Mata saboda bud'an Kai, Gaskiya yau na damki rabona mutane kusan goma nama makeup heavy make-up Simple make-up Light make-up Duk yau ba Wanda banyi ba sosai na samu kudi 50k yau na damka nan ma banyi na dinner ba kenan. Misalin karfe biyar khadija ta mike zata wuce gida Aunty nikam Zan wuce sai gobe "Toh khadija Allah ya Kara lafiya ga wannan ki D'an samu abinda kike bukata ki Saya dashi" nace Ina Mika Mata 10k Aunty ki barshi kawai d'awainiyar tayi yawa jiyama fa Goggo tace mini kun kawo Mana 5k naje asibiti danaje in ma,Ina saurayin da nace Miki yazo guna? "Eh na tuna har kikace bazaki fita ba"na Bata Amsa Ashe Dr ne Ina zuwa na gansa shine ya sayo mini magani kyauta, "Allah sarki, Allah ya saka Masa da alkhari" Ameen Aunty "Wancan yayan kine ya baki wannan Kuma nawane,ki karba khadija kid'an Saya Abubuwan da baki dasu" Gaskiya Aunty nagode Allah ya saka da alkhari,tasa hannu ta karbi kudin "Ameen khadija" Yauwa aunty nace Koh Zaki aje mini tunda Naga azumi ya kusa Inna tashi zuwa kasuwa saina karba naje na sai kaya,samun na samu dinki da wure? "Ah ah khadija insha Allah, Allah zai Bud'a Mana har yayanki ya sai Miki kayan Sallah, wannan dai ki sai Abubuwan bukata irinsu kananan Kaya da mayuka Turare pad omo sabulu ke dai irin Abubuwan bukatar Yan Mata haka" Toh shikinan Aunty Daman bani da kananan Kaya sai na saya pant biyu Brz sai vest shima biyu Amma na gwanjo Zan Saya aunty sauran chanjen, Ina materials da ake yayi yanzun ana yankawa a dinka dogayen riguna dasu? "Eh khadija"na gane su Yauwa yadi d'aya dari uku su Zan Saya kala biyar na dinka "Gaskiya khadija kinye tunani Mai kyau kema saiki samu na chanjawa kwana biyu" Toh Aunty Zan tafi nagode Allah ya Karo customers "Ameen khadija yanzun ma wasu na zuwa da dare maganar dinner aike alkhari ce tunda sanadin ki nake samun kudin" Ah ah Aunty Allah ne ya tsaga da rabonki , shiyasa kike ci "Hakane Kam khadija" nace Ina shiga kitchen da sauri nake na d'aura Mana abincin da zamuci Bayan fitar khadija girki na Gama na juye Mana a kula,sai goshin mangari ba yayan Khadija ya dawo Sumayya sannu da gida? "Yauwa sannu yayan Khadija sai yanzun" Eh wallahih ya aiki? "Lafiya klau" nace Ina kallon sa ganin Kamar a cikin damuwa yake D'azun Bashir wani makwancin mu ke tambaya ta Wai MATAR sace taji labarin Wai kina lalle ke kikama Asma'u na aure shine Wai yake tambaya ta zata samu lalle gobe,make-up jibi da Rana? nace ya bari saina tambaye ki inyaso in mun hadu a masallaci anjima na fad'a Masa amsar ki. "Lallen me za'a ma MATAR tasa"? Suna ne haihuwa tayi jibi suna "Gaskiya nifa bazanje home service ba,in mutum nason lalle Koh kwalliya yazo ya same ni a gidana" Amfa Sumayya haihuwa ne ya za'a yi mace maijego tazo lalle gidanki? "Wallahih yayan Khadija ni raini ne banaso a rayuwa na kar mutun yaga kaje Masa lalle ya Raina ka" Kai Sumayya ba wani raini ai sana'a ce ta kaiki ba maula ba,ki daure kije ki Mata kinji? "Shikenan Allah ya kaimu goben Amma bansan gidansu ba da yamma ta tura yaro yazo ya kaini" Sumayya har yamma?ya tambaye ta "Eh man saina Gama aikina,Koh so kake na tafi da safene,jibine fa sunan" Toh shikenan Allah ya kaimu yace Yana mikewa ,ruwa ya ibo a boket ya shiga bandaki Muna idar da sallan mangariba Koh abinci bamu ciba Yan make-up na dinner suka zo su biyar ne dukansu harda Amarya heavy make-up suke so,Dole tasa na hakura dacin nawa zuba Masa nayi na d'auko Masa ruwa a freezer na jira Masa,a d'aki na fitoh waje,don ni bana saka baki a dakina Sam kowa ya zauna a waje kawai Sai da yaye isha'i kafun ya shigo gidan, gaisawa sukaye da customers nawa,don na fahimci yanzun mutane na ganin kirmansa tunda kofarsa suka shigo "Abincin ka na d'aki yayan Khadija"nace Masa ganin ya nufi d'akin kar yaje ya zubar da abincin tunda a kasa na jira. Toh yace Mata Yana shiga d'akin Make-up na Amarya na fara, Gamawa ta biyani akazo aka d'auketa saura hudun ma duk na Gama musu kafun 9:00,kudin da suka bani 25k Inna hada Dana d'azun kusan dubu saba'in na samu kenan Alhamdulillah yau kawai na tashi da kudi dubu sittin da biyar in aka cire 10k Dana bawa khadija Wani tunanine ya fado mini akan kudin, murmushi kawai nayi na nufi d'akin Ina bude labulin idona ya sauka Akan plate inda nasama yayan Khadija abinci nakai dubana garesa da mamaki ganinsa a.............. *My Real and special Fan'S* *Princess* 🏵️ *Maryam najibu* 🏵️ *Mummy*🏵️ *Shamsiyya Gombe* 🏵️ *Ummu na'eem*🏵️ *Faeexetion* 🏵️ *Zainab*🏵️ *Bebi* 🏵️ *Maman khairat*🏵️ *Oum Abdullahi*🏵️ *UMSAD INCENSE* 🏵️ *Ummul husnah*🏵️ *Duk Naga comments naku Allah ya bar kauna Nima Ina yinku* 🏵️🏵️ 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin,Koh kinsan mace sai da kamshi da gyara* 😉 🍀🍀🍀🍀 *Turare suna d'ayace Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin sa* 🍀🍀🍀🍀 *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da* *gyara* 🍀🍀🍀 *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace* 🍀🍀🍀 *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE* 🍀 *Na tsunguno(habil)* 🍀 *Na jiki (kwalaccam)* ( *khumra, black & white* ) 🍀 *Turaren turara jiki after birth* , 🍀 *Na d'aki(halud Al'oud)* *UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* 💃🏼💃🏼 🍀🍀🍀 *Suna bada d'aya Koh sare akan farashi Mai Rahusa* 🍀🍀🍀 *Suna bada order kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria* Contact them vie 🪀08028827241 or 09033791049 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya* *Ibrahim* 🍃 ✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwa👌 free book 🤧 🍀 *Wannan shafin sadaukarwa ne gareki haj j Aisha Ahmad Allah yabar kauna* 🍀 Page3️⃣4️⃣&3️⃣5️⃣ Al'ameen ne, Sumayya ta gani zaune ya zuba tagumi Koh abincin Bai d'and'ana ba. Cikin mamaki ta karaso cikin dakin"yayan Khadija lafiya kuwa"? tace tana matsowa kusa dashi Firgigit ya dawo hayyacinsa, Sumayya har kun Gama kwalliyar? "Eh mun gama,Naga bakaci abincin kaba Allah dai yasa lfy Koh" ta Kara tambayar sa. Lafiya Sumayya jiranki nake in kuka Gama saimuci"ya Bata Amsa Da mamaki sumayya ke kallonsa"banace kaci ba"? Sumayya na kasaci ne, kece Kika nema Kika dafa Taya zanyi na rigaki ci bayan ke kina ta faman aiki. "Karka Kara fad'amin irin wannan magana daga yau" Don me?ya tambaye ta "Saboda duk abinda na baka ni gani nake kamar kaika bani mukeci banason Kara Jin irin maganar nan,Ina zaune itdakai ne badon kome ba sai don Allah,rufin asirin ka nawa ne nawa nakane"ta fada tana kallonsa Shikenan Sumayya nagode, "Bana bukatar godiyan ka ka gode Allah"tace tana matsowa kusa da abincin budewa tayi tasa shukali"Bismillah muci"tace tana iba Toh yace Yana laluben nasa shukalin Abinci sukaci Amma cikinsu Babu Mai magana kowa Yana cin abinci ne,bare Hajiya sumy Suna Gama cin abincin Al'ameen ne ya tattara Kwanukan yafita dasu waje Sumayya Kam wanka ta shiga,tana fita tayi Alwala,kayan bacci tasa ta kwanta Al'ameen Jin ta kwanta yasa shima fita wajen ruwa ya Iba yayi wanka.kamar yanda yazamo musu Al'ada wankan dare kafun su kwanta,Yana fitowa ban d'akin kofar shashen su ya rufe,ya shigo d'akin,rufewa yayi a hankali yake takawa Yana laluben gadon harya iso, Hawa gadon yayi ya kwanta a hankali, Sumayya Kam mamakine ya kamata ganin sa a hakan Sannan yahau gadon ma Bai Saba Mata yanda yake Mata ba, watoh son mannuwa kusa da ita. A hankali ta mirgina kusa dashi hannu tasa ta Kama NASA hannun"yayan Khadija" Cikin sanyin halinsan nan ya amsa mata, na'am. "Menene yake damunka ne Wai" ? Ba kome Sumayya me Kika gani?ya tambaye ta Yana Mai dagota ya d'aurata a jikinsa gabaki d'aya "Ba kome, yauwa nace kanada National ID card ne"? Sai dai voters card bani da National ID card "Ok shima zaiyi Daman inason na bude account a bank ne kasan banzo da details nawa ba" Toh shikenan Allah ya kaimu goben saina baki "Zaka rakani bank in? Koh naje da kaina"ta fada tana gyara kwanciyar ta akansa Duk yanda Kika gani goben ne Zaki bank in Koh yaushe? "Sai na Gama lallen da akayi booking innan" Toh shikenan Allah ya kaimu saina rakaki,in khadija taji sauki Kuma sai kuje tare kinsan me?ya tambaye Sumayya "Ah ah" Khadija na son zuwa bank Kamar me haka lokacin kudin covid 19 ta dameni Wai sai naje mun bude account muma,mun cika Koh zamu samu kudi,Amma da mukaje bank hanani Shiga sukayi security Wai ba'a bara a banki,Kuma su tsaya su saurare mu sunki Haka suka kuramu waje. Sosai naji maganar ta tabamin rai"aiko Insha Allah da ita zani taga bank,Amma kaima fa Dole zamuje tare tunda account Kai za'a budewa ba niba. Toh Allah ya nuna Mana yace Yana zura hannunsa a cikin rigan bacci dake jikinta Jin hannunsa a riganta unexpected yasa ta zabura sai Kuma ta koma ta kwanta a hankali ta lumshe ido Jin abinda yake Mata da hannunsa a cikin riga"kasan me"? Ah ah ya Bata Amsa "Nikam Ina ga Zan Saida laptop Ina da waya" Akan me Zaki saidasu toh? "Saboda Banga amfanin suba inba kallo ba me nake dasu shiyasa Zan sayar"tace. Tana taimaka Masa ganin Yana kokarin zare rigar Tata Umm umm Sumayya waike bazaki ringa d'aukar kwalliya kina sawa a media ba Koh Allah zaisa asamu location naki Kinga ai sai afi saninki sosai a Jala "Kasan ba kowa keson asa hotonsa a social media ba shiyasa ban fara posted ba,Nima nayi wannan tunanin" Eh ai tambayan su zakinayi Zaki d'aura hotonsu kiyi Tallah Amma fa Yan Mata banda matan aure, insun Amince shikinan,tunda wasu da yawa in sunyi kwalliyar ma post suke. "Gaskiya ne Amma waya fad'a maka ana d'aura kwalliya a online? Kuma ya akayi kasan ana Post"?Sumayya ta tambaye sa tana kakkama Masa gashin kai Jin wani magic dake bin jikinta a sanadin abinda yake Mata Uhmmm ai inaji ana Hira koma ni lokacin da na makance ma waya tayi araha a hannun kowa ba,Kamar yanzun Washhhh toh,uhmm tace tana zillewa daga kansa ta sauka a gefe. Jin ta zame yasa ya bita shima, tana kwanciya ya kwanta akanta rumfa ya Mata da kirjinsa,ya had'a fuskarsa da Tata fuskar yayi Yana tsintsinar bakinta,dake kamshi "Wayyo ka sauka nauye"tace tana mutsu mutsu tana damke damtsen hannunsa Shagwaba Koh bafa nauyina na d'aura miki ba "Nidai ka sauka,kawai tsoro nakeji" Tsoron me?ko ni dodone?ya tambaye ta Yana Mai Kara matsota garesa "Ka sauka" Naki,yace Yana Kara Danna kansa akanta "Nifa bacci nakeji kaji muye bacci" Nikam banajin bacci "Nikam ai inaji Koh"? Sai kiye ai na hanaki ne? "Amma ai ka tokareni" Shuru ya Mata yaki kulata sai bidirinsa yake a kanta jifa jifa tana taimaka Masa Jin abin NASA ya fara yawa yasa ta fashe Masa da kuka A tsorace ya mike a kanta sauka yayi gefe cikin tsoro,yake tambayar ta,ke Sumayya menene,Yana tattabata yaji Koh lfy Saura kad'an dariya ya kubucewa Sumayya Jin yanda duk ya tsorata dagajin kukanta kawai,ta rasa ma wani irin namiji ne Mai shegen tsoro haka "Toh ba Kaine ba nace maka inajin bacci sai matseni kake"ta fada da muryar kuka tana kallonsa tana Masa gwalo ganin yanda sai zazzare ido yake kamar kace kittt ya ruga Shine abinda ya saki kuka? "Eh Mana" Toh Yi hakuri kwanta toh. Dariyace ta subuce mata Jin abinda yace Yana kwanciya a gefenta baima mannu kusa da itaba Cikin mamaki ya Tashi zaune Jin tana dariya, Sumayya Anya lfy kuwa daga kuka saiki koma dariya? Shuru tayi gudun karya harbo jirginta"babu kawai ji nayi kamar jakulkule ake mini a ciki" Shuru yayi baice kome ba illah rufe ido da yayi Yana nazarin Rayuwa yau Wai shine da Mata,Ashe haka zama da mace yakeda Dadi duk halinda kake ciki muddin ka samu mace na gari ka Gama samun Jin dadi,duk halinda namiji zai shiga mundin dare yayi zata ga tayi kokarin kauda damuwar tasa Koh Bata cireba,zatayi iyya bakin kokarin ta taga ta d'auke Masa hankali Jin yanda Sumayya keta motse yasa shi kiranta, Sumayya!! "Na'am"ta amsa tana gyara kwanciya Bakiyi bacci ba? "Umm banyi ba" Saboda me? "Haka kawai" Jin Amsar da ta basa yasa a hankali ya matso gareta,lumshe ido tayi Jin yanda tsikar jikinta ke tashi,Jin gashin kirjinsa na goguwa da bayan ta Hannu yasa a hankali ya Kama waist inta d'an zabura tayi kad'an,yasa hannu ya maidata,watoh kukan shugwaba Koh? "Bawani shugwaba,Kuma ni ba shagwabebbiya bace atoh" Shugwabebbiyace Mana ai duk lukutaye akwai shagwaba "Waye lukutar"?ta tambaye sa tana juyowa suka fuskanci juna Daga Sumayya har Al'ameen wani yanayi sukaji a tare da junan su sosai kusancin su yayi yawa akwance da suken nan Kece Mana, lukuta kiga nan naki fa Kato,yace Yana Kama Mata bombs, Hannu tasa ta buge Masa hannu"ai naka yafi nawa girma" Zare ido yayi Kamar tana ganinsa,ai Dana shiga uku ai,sai wando Mai shape za'ana dinka min. Hhhhh Sumayya ta Kama dariya "Wai wando Mai shape waya ganka kana tafiya kana murgud'asu a cikin jallabiya"ta karasa maganar da kamo hannunsa dake Kan kirjinta don wallahih kirjin zafi yake Mata Shi Karan kansa Al'ameen abin sai da ya basa dariya,Amma yakiye, murmushi kawai yayi,Jin ta Kama Masa hannu kafarsa ya daura Mata akan kafa. Kokarin mikewa ta fara har lokacin hannunsa na rike a nata Wai don karya taba Mata inda bataso Jin tana kokarin tashi yasa sa tambayar ta,Ina Zaki Kuma dare fa yayi. "Rigata nake nema" Kiye me dashi? "Me ake da riga" Sawa, ya Bata Amsa "Nima sawan zanyi" Nikam gaskiya banso kawai mu k'wanta haka. "Jikinka Koh nawa?wato mu k'wanta haka ka karasani ba" Sorry zafi yake mikine? "Eh Mana duk ka mammasa mini jiki" Amma ai kinji Dadi "Banjiba"ta basa amsa tana mikewa zaune Ai da sauri yasa hannu ya rike Tata hannun,yana kwance Bai tashi ba,kiyi hakuri mu k'wanta haka ba abinda Zan sake Miki. "Ai kasan bakyau kwana ba Kaya" Menene a jikinki Koh tsirara kike yanzun? "Rigan fa" Ai nace bazan miki kome ba yace Yana jawota jikinsa matseta yayi a hankali ya jawo blanket inda ke Kan kadon ya rufe jikinsu. *********** Washe gari Kamar kullum bayan Al'ameen ya dawo sallan asuba, sunnah TV Sumayya ta kunna musu daga ita harshi in suna kwance suna sauraron wa'azi. Sai wajen 7:3pm Sumayya ta mike shara tayi yayan Khadija ya Mata wanke wanke, ruwan zafi ta jona abuta,Yana tafasa ta juye a boker tasawa yayan Khadija nasa, ta shiga ban dakin tana fita yayan Khadija ma wanka ya Shiga. Vayan sun Gama shiryawa kudi ta mika masa 1k"ka sai Mana egg's guda biyar sai bread na 500 Mai kyau ka hada Mana da butter " Karban kudin yayi,ya fita. Bayan ya sayo k'wai da bread, soya k'wai in Sumayya tayi ta hada musu cornflakes ga tie,jira musu tayi a kasan cafet,kamo hannunsa tayi suka zauna a kasa, bubude abincin tayi"karbi shukalinka" Toh yace Ya karba shukalin ,tattaba plates in yayi Jin plate biyu ne ga bowl d'aya ga cups biyu,wannene abincin nawa Naga Kwanukan da yawa? Duka zakaci d'ayan soyayyen k'wai ne d'ayan bread ne da butter a jikinsa sai Kuma bowl na cornflakes,sai cups na tie"nace Ina tura Masa plate in k'wai a gabansa"kaci kwai sai kana Had'awa da tie ga bread" Shikam Al'ameen ya kasa magana Wai karyawane da abinci Kala uku shi Al'ameen,ganin Al'ameen bai fara ci ba ita har tayi Rabin cup na tie inta yasa ta aje kofin,hannu tasa a cikin k'wai in ta yagi babba ta tura Masa a baki Shikam Jin abinci a bakinsa da Kuma yatsarta sai faman tura Masa take yasa sa cizon yasan kad'an, Ai Kara ta sake hade da yarfa hannun nata"wayyo yatsana jini jini yake na bunu tace tana duba hannun". Da mamaki Al'ameen yace jinii ma Sumayya? "Eh gashi shikinan ya gusuramin yatsa" Mu gani "Bazaka gani ba sai kace idone da kai" Toh muji. Bazakaji ba din,tace tana daukar kofin shayen ta Jin tayi Shuru yasa sa gutsurar bread Mai butter,Wai zai Bata itama d'ayar hannun nasa yasa ya lalubo fuskarta,Jin fuskar Tata yasa ya fara lalubar bakinta da hannunsa "Kasan Allah Inka samin hannun hagunka a bakina ba"tace ganin Yana ta tattaba Mata baki da hannun nasa Kayya abinci Zan baki,yafada Yana Mika Mata gutsuren bread inda ke hannun damansa a baki, Rufe bakin tayi Taki budewa. Shikam sai goga Mata bread in yake a lebe gashi duk butter ya Bata Mata fuska "Kanata Bata mini fuska da butter"tace bayan ta rike hannunsa Toh ba kinki bude bakin ba sai kokari nake, Kaga kaci abincin kan, ka barni naci nawa,tace Masa tana goge fuskar ta Toh ki bare na baki wanann kawai kinji Ganin yanda ya nace Mata yasa ta bude bakin Yana saka Mata bread in da sauri ta datse hakorin ta,Wai don ta cije yatsarsa shima abin mamaki da sauri taga ya cire hannunsa kafun ma hakorinta ya Sauka akan yatsar,Yana dariya Ai Daman nasan saikince Zaki Rama shiyasa Nima nayi taka tsamtsam da yatsana. Shuru ta Masa Bata tanka masa ba. Haushi ya shigane bakutuwa? Kara ta sake tayi kansa "nice bakutuwa" Jin ta hafto, yasashi Kare kansa, hannu yasa ya tare fuskarsa. Ganin haka sai abin yayi mugun Bata dariya waishi harga Allah tunani yake wani abin zata Masa haryana tare fuska. Jin shuru baiji tayi Masa kome ba yasashi fara laluben ta Aiko ya jita a kusa dashi,da sauri ya rikota, sorry kinji "Ni......shuru tayi Bata karasa ba Jin sallama a kofarsu amsawa tayi ta mike kaci abincin kafun na dawo" Toh yace Yana saka hannunsa ya d'auki cup inda ta aje masa... Sumayya tana fita taga wata budurwa irin classic innan zata Kai kusan sa'ar ta kyakkyawace Amma baka Tasha kwalliya tana rataye da school back "sannuki da zuwa"tace Mata tana shimfid'a musu darduma"Bismillah ki zauna" Yauwa Ina kwana?bakuwar tace tana zama akan sallayar "Lafiya ykk ya gida"? Lafiya Alhamdulillah,ya aiki? Lafiya klau,Ina zuwa Sumayya tace tana mikewa d'akin ta shiga ta hada cornflakes da ruwa Daya a fijrij ta hada a tire ta kawowa bakuwarBismillalahih ka abin Kari ba nauye Kam"tace tana ajemata a gaba La d'awainiyane haka Allah dakin barsa yanzun na fitoh gida zanje school ne ma nace bara na biyu dai ta gidanki "Allah sarki Amma dai ki saka Koh albarkane yafi dai kikici bazanji Dadi ba" Shikenan bara dai NASA albarkan tunda kin Masa tace tana iban cornflakes in da shukali uku tayi tace Alhamdulillah "Badai harkin koshi ba"? Alhamdulillah wallahih ya isheni,suna na kamila Ina zaune a unguwan gadi,Daman nazone wajen ki in Babu damuwa inason zan fara Training in make-up,Naga wanda kika ma kanwata a auren Asma'u shine nace tamin kwatancen gidanki inyaso sai nazo inji. "Toh gaskiya ni bana koyarda make-up saboda bani da shago sai gidana Kinga Kuma Ina da ayyuka yau da gobe"tace Mata tana tunanin ta yarda ne Koh karna yarda Ba damuwa sister Nima Ina zuwa school Kinga saiki bani time inda zanna zuwa Koh ki ban number ki duk lokacin da kike free sai ki kirani Koh Kika samu Yan make-up. "Shikenan yanzun dai ki bare Inna ma mijina magaa in ya Amince xakiji daga gareni" Ok ba damuwa saiki bani contact naki Koh in ba damuwa sannan nawane kudin da Zan biyaki Kinga Inna koma Koh yaushe Kika kirani saina tawo dasu Toh, make-up dai kashi kashine sanann yanayin kwakwalwar mutum wata a wata D'aya zata koye make-up wata biyu wata fiye da uku ma Bata iyya ba so ni bansan ya yanayin d'aukar kwalliyarki ba Amma dai inso samune wata uku kina koya" Ok yanzun wata ukun nawa ne kudina "50k Koh wani wata kudinki na wata uku 150k kenan" Wai habba sister kudin nan yayi yawa Mana dubu dari da hamsin, Gaskiya kenan Kinga a cikin kudin Zan Saya make-up kit sabo duka,saboda bazaiyu Ina baki na aikina kina koya dashi ba, sanan infa kika iyya a kwana uku Zaki iyya samun sama da kudinda Kika biya na koyo" Hakane Kam Amma dai ki duba ki rage mini kinsan baban mu yace in zaiyu nida kanwata zai biyawa. "Shikenan Zan rage dubu goma" ok shikenan an gode saina jiki Shikenan bara na baki number,daidai lokacin Al'ameen ya fito d'akin hannunsa rike da cup inda yasha shaye What?? wa nake ganin nan Kamar Muhammad Al'ameen Yusuf bakuwar tace tana zare ido A matukar razane har bakin sa na rawa yace kamilaaaaa........... 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin,Koh kinsan mace sai da kamshi da gyara* 😉 🍀🍀🍀🍀 *Turare suna d'ayace Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin sa* 🍀🍀🍀🍀 *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da* *gyara* 🍀🍀🍀 *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace* 🍀🍀🍀 *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE* 🍀 *Na tsunguno(habil)* 🍀 *Na jiki (kwalaccam)* ( *khumra, black & white* ) 🍀 *Turaren turara jiki after birth* , 🍀 *Na d'aki(halud Al'oud)* *UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* 💃🏼💃🏼 🍀🍀🍀 *Suna bada d'aya Koh sare akan farashi Mai Rahusa* 🍀🍀🍀 *Suna bada order kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria* Contact them vie 🪀08028827241 or 09033791049 IG @umsadincenseIG @umsadincense *IG 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya* *Ibrahim* 🍃 ✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwa 👌 free book 🤧 Page 3️⃣6️⃣&3️⃣7️⃣ Kamila kice Koh dai Mai irin muryar tane, Al'ameen yace cikin d'unbin mamaki Ikon Allah Ashe da rabon za'a sake ganin juna Muhammad,kamila tace tana me Kara kallon Al'ameen Wallahih fa kamila yace Yana isowa kusa dasu sumayyar Oh duniya Muhammad Daman a unguwan nan kake? Anan nake kamila,ya bayan rabuwa ya maigidan ki da yara? Jiki a sanyaye kamila tace,hmm muhammad mijikam aure ya kare, yara Kuma Allah Bai kawo ba tukum. Allah ya kawo masu albarka Ameen Muhammad,Amma nayi mamaki wallahih wannan ce matar ka,ta fad'a jikinta na Kara sanyi tunawa da abinda ya faru a shikarun baya da suka wuce Eh kamila matatace sunanta Sumayya Masha Allah gaskiya matakam tabar kalla Masha Allah wallahih gata kyakkyawa son kowa kin Wanda ya rasa,tace tana kallon Sumayya har lokacin Haka Allah yake abinsa sai ya baka abinda baka taba tunani Koh tsammani ba, shiyasa duk abinda bawa ya samu a rayuwa rabonsa ne ba Mai hanasa muddin Allah ya basa Gaskiya ne muhammad,Aiko shikenan Daman kwalliya nazo tambaya Allah dai yasa madam in zaka barta ta koya mini,tace tana Mai Al'ajabin Rayuwa su kamila kenan yaushe Kika dawo Jala ne? Shap aini na jima a Jala, Amma Dad nawa transfer mun dawo nan Allah sarki toh ya gidan naku da aiki? Gida Alhamdulillah aiki Kam Babu sai karatu. Karatu Kuma,kamila? Eh Mana ai kasan bayan rabuwar mu aure nayi sai karatun ya tsaya sai yanzun na samu na Shiga TSU Gaskiya ne Allah ya bada sa'a.. Ameen, muhammad Kai ya lbrn karatun? Kai kamila wani karatu Kuma makaho talaka zaiyi ba kudi ba ido ya fad'a Mata maganar cikin murmushi Sosai taji wani abu ya Tukare Mata makoshi Jin kalaman da ya fad'a ya tuna Mata da kuskuren da ta tafka a rayuwar ta tabbas Al'ameen Mai hakuri ne da wanine haduwarsu yanzun bazai ma saurare taba Cikin sanyin jiki tace,toh nikam Zan tafi Sumayya saina jiki Koh,ta fad'a tana kallon Sumayya dake zaune a Kan darduma Sumayya Kam ba karamin haushi taji ba Kamar ta tashi ta Basu waje, Amma saita maze gudun karta bada kanta agun kamila,"yauwa"kawai tace tana kallon kamila dake Shirin fita a kofar Sumayya! Al'ameen ya Kira sunan ta Kin amsawa tayi Tamar kunnen uwar shegu Sumayya Koh kin tashi a wajen ne? Nan ma Sumayya kin amsa Masa tayi. D'aki ya shiga a zatonsa ta koma d'akin ne Amma ya Gama laluben ta bai jita ba Sumayya Kam na zaune duk haushi ya Gama kasheta Jin yanda Al'ameen ke wani sake baki Yana Hira da Yar banzar bazawaran (Kai Sumayya harda zagi) Ji kawai tayi Al'ameen ya rungume ta a zaune da take "Menene"tace tana zame jikinta a nasa "Me yasa kika ki amsa mini bayan kinji Ina kiranki,yace Yana Kara lafewa a bayanta "Oho Kuma ka sakeni" Meye Kuma nayi Miki haka hajiya "Bansani ba nika sakeni nace maka" Habba bakutuwa "Ka sakeni fa" Green sum...... Sumayya Bata bari ya karasa ba kawai ta dasa Masa hakoranta a hannunsa D'aya zagayo dashi Kan kirjinta Washhhh Allah na yatsata,yace Yana yarfa yatsar don harga Allah da gaske Sumayya ta cijesa,ni Kika ciza? "Eh din kuma,ka sakeni nikam" Wai menene Kam? "Bansani ba" Karki sani Kuma kamila zata fara zuwa make-up gobe nace Mata na, Amince kamar yanda Kika Bata umurni,yace ya na son gane dalilin fushin nata Koh saboda kamilane, don shidai lfy suka rabu kafun ta fitoh waje "Bazan Yi ba ai ba'a dole karta kuskura tazo mini gida don kurinta zanyi" Kishi kike da ita? "Akan me zanyi kishi da ita kuma" samayya tace tana Jin bugun zuciyarta na karuwa Akan mijinki,Mana "Ina mijin yake" Au bakisan inda yake ba? "Eh ban sani ba saika sanar dani" Jin abinda Sumayya tace yasa Al'ameen zabura da karfi ya fizgota jikinsa ya juyarda ita suna fuskantar juna,kikace in sanar dake Ina mijin yake? Sumayya ni kike fadawa wannan magana saboda Ina miskini Kuma kina ciyar dani,ya fada ransa a matukar bace Sosai Sumayya ta razana harga Allah batasan maganar ta fita ba Sam ita Karan kanta bazatace ga abinda ya harzukata ba yanzun yanzun nan Tambayar ki nake Sumayya saboda kina ciyardani? Koh saboda bana gani shine kike wulakantamin aure? Sosai ta Shiga rud'ani Bata d'auka Al'ameen da ta sani yanada irin wannan fuskar ba"Kayi hakuri"tace tana zame damtsen ta a hannunsa D'aya damke Kala baice ba mikewa kawai yayi ya d'auke sandarsa da ciny'ayyen takalmin sa yafita Bayan fitar Al'ameen sosai Sumayya ta Shiga Dana sani,tabbas magana zarar budu inta fitoh Bata komawa,da tasan haka zai Bata Masa Rai da Bata fara ba Mikewa tayi ta Shiga d'aki ta kwanta sosai zuciyarta ke Mata zafi Bangaren Al'ameen Kam bayan fitarsa gida Tashan kayan marmari ya nufa, duk yanda yaso ya samu bashin Kaya abin ya gagara haka yayita yawo Amma shuru Bai samu kome ba ,tabbas irin wannan yake gudu Sam bayason mace ace ita ke ciyar da miji,Sam maganar Sumayya Ada Baya Masa ciwo Amma yanzun yaji wani irin ciwo akan maganar sosai,sanann ya Mata hakan ne don ta kiyaye gaba in zata Masa magana ta ringa taunawa,ya fahimci kishine kawai ke d'awainiya da ita Jin ana Kiran azahar yasa Sumayya mikewa sallah tayi ta d'aura shinkafa da wake,zubawa tayi a flasks don itakam Sam bazata iyyacin kome ba yanda take Jin tsananin damuwan nan,gashi batasan Ina Al'ameen ya Shiga ba,har yanzun Bai dawo ba Har yamma Al'ameen shuru Bai dawo ba duk inda hankali Sumayya yake ya Tashi sosai ta Shiga damuwa matar Bashir data ma alkawarin lalle day uku tana Aiko yaro karshe ma Sumayya tace yaron yace Mata bazata samu zuwa ba "ya Allah ka dawo mini dashi lfy"tace tana zabga tagumi Sai bayan Isha'i Daya idar da Sallah Aljuhunsa ba kome yanda ya fita haka ya dawo Koh abinci Bai Karaci ba bayan na karyawa,da sallama ya shigo d'aki Sumayya dake cikin dogon tunani tana zaune akan sallaya Koh hijab Bata cireba , da sauri ta amsa"waalaikumu salam yayan khadija lfy kuwa baka dawo ba sai yanzun"tace tana isowa garesa Uhmm sai yanzun, kawai yace Mata Yana k'wabe rigansa,jallabiya ya d'auko a cikin kayansa ya fitoh waje Bai Kara Mata magana ba Baki a sake Sumayya ta Bisa da kallon mamaki harya fita,ta koma ta zube a jikin kujera hawaye na cika Mata ido,ta Shiga uku sauran hope natan Daya saura shine shima yake kokarin juya Mata baya Wai meke faruwa da itane me yasa duk Wanda zai sota daga baya sai ya kaurace Mata,kuka kawai ta sake "nikam na Shiga uku"tace tana cigaba da kukanta, Al'ameen Bai taba fushi da itaba sai yau menene Bata Masa ba Abaya Bai taba fushi ba sai yau daya ga kamila. Al'ameen Kam wanka ya Shiga Yana fita yaji muryar Sumayya kasa kasa tana kuka da sauri ya aje kayanda ya cire,Wanda yaso wankewa Amma baida omo. D'akin ya shiga Amma saiya maze ya kwanta akan kujera Bai kulata ba Sumayya Kam Jin yanda Koh damuwa baiyi da kukan da yaji take ba yasa a hankali cikin muryar kuka tace"yayan khadija ga abincin ka"ta fada tana mikewa ta dauko a saman freezer Na gode Amma bazanci ba yace, ba tare da ya Koh motsa a inda yake ba Kuka kawai Sumayya ta sake kamar ana yankata"nikam na shiga uku tunfa safe banci kome ba bayan karyawa saboda Ina jiranka ka dawo Amma shine ka dawo kace bazaka ci ba" Na hanaki cine ai ban hanaki ba kici Mana ni indai nace bazanci ba "Wayyo Allah na ni Sumayya Yaya zanyi da Raina ne" Da na Miki me? "Kaci abincin toh kaji" Ah ah naci ai "Waya baka kudi ka saya" Ai Ina da sana'a Koh? "Nidai don Allah Kayi hakuri kaci kaji" A matsayina nawa Kika damu da sai naci abincin ki?ya tambaye ta "A matsayinka na"...... Sai Kuma tayi shuru tana kallonsa Uhmm ,kawai yace Yana lumshe idanunsa so yake ya kitsema wannan baiwar Allah Koh Amafarkine Yana son kallonta, tunda ya makance Bai tanajin yanason kallo ba irin haduwarsa da Sumayya sosai yakeson ganinta da idanunsa "Wa.....i mi...jin..a.."tace cikin eeii eiiina Waine ma kenan? "Mi..ji...na" Sumayya!ya Kira sunanta "Na'am" Meya Bata Miki Rai d'azun? "Babu" Akwai Kam? "Babu"tace hawaye nabin kumatunta Nine Koh kamila?ya Kara tambayarta "Koh D'aya" Ki fadamin gaskiya wannan shine kad'ai zaisa na hakuri. "Kaine" Me nayi Miki har zakina fad'amin magana irin Wannan "Toh ba Kaine ba" Nine me? Kaketa Mata dariya harda wani.....sai kuma tayi shuru Jin subutar baki da tayi Shikam murmushi ne ya subuce Masa hade da wani irin farin ciki tunda Sumayya na kishinsa,Kuma duk inda akwai kishi akwai alamun so, sai Kuma akace ki gaggaya min magana? "Kaye hakuri don Allah"tace tana mikewa a hankali ta matso garesa fadawa tayi kansa da karfi ta sake kuka Rumtsa idanunsa yayi Jin saukan hawayen ta a kirjinsa tamkar ruwan guduma haka yajisu, Sumayya!ya Kira sunan ta Yana Mai Kara matseta a jikinsa "Na'am"ta amsa Masa hade da cusa kanta a kirjinsa ji take Kamar numfashin ta zai d'auke Sumayya na hakura Amma karki sake mini Wasa da aure kinji banaso. "Wallahih bazan sake ba" Allah yasa,yace Yana shafa rigan jikinta Sumayya wannan ba kayanda kikasa da safe ba? "Shine" Ta basa Amsa Miya hanaki wanka? sai tsami kike ma,ya fada hade da shafa Mata baya "Damuwa ne ya hanani,Kuma ni bana tsami" Bagashi ba sai tsami kike, yace Yan sunsunar wuyanta,dake tsananin kamshin Turaren ta "Zakaci abincin na baka"?ta tambaye sa cikin damuwa A koshe nake ki bare sai da safe sai naci. "Nidai ban yarda ba wallahih Koh kaci saikaci nawa" Toh zanci,kije kiye wanka ki wanke tsami kisa Kaya "Bayan na Gama sai muyi me"? Saina karbi hakkina,ya Bata Amsa shima "Niii..... niii.. Babu ruwana,abinci nake nufi" Ai kema abinci ne,ya Bata Amsa "Wacece kamila"? Uhmmm abinda ya hanaki sukuni kenan? "Nidai ka fad'amin kawai malam" Toh malama bakutuwa kije kiyi wanka sai kizo kici abinci sai mu k'wanta da safe saina fad'a miki,. "Har gobe kuma"tace tana hada fuska Eh na gaji bacci nakeji yanzun yace Yana cire Mata riga "Bacci Kuma kake kwabeni"? wanka zakiy i,ya Bata Amsa hade da karasa cire Mata rigan Wanka Sumayya ta Shiga tana fitowa lokacin karfe 8:00 dai dai, shiga d'akin tayi Kaya tasa,tana Gamawa ta jawo abincin "yayan khadija muci abinci" Sumayya kici nikam na koshi saiki dumamin da safe. "Ni wallahih ban yarda ba,toh bakace ka hakura ba Koh baka hakuran bane" tace tana hawaye Tabbas ko yaki Koh yaso Sumayya ce rufin asirin sa inba itaba bashida wajen da zaici abinci tunda ba kudi Koh sana'a bane dashi,sauka yayi ya matso Yana lalube ya zauna shukali Sumayya ta Mika masa,ya karba suka faracin abincin Koh minutes uku basuyi ba sukaji sallaman yaro a kofarsu, "Kai wallahih nifa na gaji habba matan nan bazata samu lallen nan ba" Wace Mata Sumayya kardai kice min matar Bashir baki je kin Mata lallen ba?da mamaki yake tambayar ta "Nikam banje ba" Saboda me? "Saboda baka dawo ba,Kuma ni yanzun dare yayi" Amma sumy gobe nefa sunan Kuma baki je kin Mata ba,sannan yanzun Kuma kice kin fasa,baxataji d'adi ba in Kama mutum Alkawari Yana da kyau ka cika Kinga na riga nace wa Bashir zakizo kima matar sa lalle bazaiji Dadi ba in Kika ke zuwa Kuma gobe suna. Hakane kam, Sumayya tace tana fitowa waje Ina wuni Aunty?yaron ke gaida Sumayya "Lafiya ya mamarka"? Lafiya aunty Wai inji mamana inzo in fada Miki Wai don Allah kiye hakuri kizo ki Mata lalle ta nemi me lalle Bata samu ba Toh shikenan bara na d'auko hijabina, Sumayya tace tana shiga d'akin "Yayan khadija zanje lallen saina dawo ga abincin ka karasa ci"tace tana d'aukar hijab nata da jakan lalle purse ta bude 50k ta d'auka,zata fita a d'akin Toh baki karasa cin abincin ba? "Ah Ah Alhamdulillah kaci kaikam nikam sai nadawo" Sumayya muje na rakaki kinji?yace Yana mikewa "Ah ah ga yaro zamu tafi tare,sai dai kazo ka d'auke ni anjima" Kamar karfe nawa? "Kana da agogone"? Oho,nikam ki fad'amin. "Yanzun 8:12 zuwa 10:00 sai kazo ka d'auke ni" Toh shikenan yace Yana zama,d'aukar abincin yayi ya cigaba da ci Sumayya Kam fita tayi da yaron,sai da sukazo kusa da titin first bank taga shagunan a bude kamar Rana ga wuta ako ina,"tsaya Kai mu Shiga shagon nan" tace ma yaron tana Kama hannunsa suka tsallaka titi,shagon ta shiga"excuse me"tace ganin Mai shagon inyamurine Yes ma barka da zuwa shigo ciki customer ki duba Kaya Da mamaki sumayya ke kallonsa Ashe ya iyya hausa,yauwa "sannunka,Kaya nake so" Ok wani iri? "Jallabiyoyi" Ok ki shigo gasunan kizo ki zaba Wanda ya miki,yace Yana zazzaro Mata jallabiyoyi sunfi kala goma Guda uku sumayyaa ta zaba masu masifan kyau fari da baki Mai maiko sosai da hula sai Kuma Mai aiki ruwan sararen samaniya,takalmi ta sai Masa Mai kyau na tambarin Adidas silifas ne,sai t-shirt da 3quiter sai Jean's,sosai Sumayya Tama Al'ameen sayayya harda Turare na maza ta sai Masa da abin haske Kai da gemu,sai kusan 9:26 suka je gidan Matan da zatama lalle Lalle Sumayya ta Mata baki da ja, Al'ameen tun 10 yazo Amma Basu Gama ba,ya zauna Yana jiranta a kofar gidan Suna Gama lallen Sumayya ta karbi kudinta laidan da ta aje a kulle a gefe na kayan da ta saima Al'ameen ta saba,waje ta nufa Tana fita taga yayan khadija a zaune "Yayan khadija mu tafi Koh"tace Masa Kun gama? "Eh mun Gama" Ok yace Yana mikewa tafiya suke shuru,can dai Al'ameen ya kasa hakuri Jin yanda yakejin motsen laida a hannun Sumayya Sumayya nikam laidan menene a hannunki Kato haka don nasan dai laida kananu basa Kara haka? "Abu na saya"ta basa amsa Kala baice ba suka cigaba da tafiya har suka Isa gida,Dayake sunyi wanka dazun yasa Kaya kawai suka chanja Yauma kwanciya sukayi tare bayan Al'ameen ya Gama kwsan rabonsa Washe gari da safe bayan Al'ameen ya tafi masallaci, Ghana must go nasa ta bude Daman jiya ta kirga kayan jallabiya ukune sai wando da riga D'aya sai 3quiter D'aya sai armless D'aya sai gajeren wando biyu vest D'aya, kwasosu tayi ta juye a basket na dattin kayanta,sabbin kayanda ta suyo jiya ta mayar cikin bakkon ta shirye Kamar yanda kayan suke a kirge sauran Kuma ta aje sai Randa ya wanke kayansa biyu masu dattin saita musanya Masa, Vaseline insa da ya kusa karewa ta juye a laida daukar manda ta siyo Masa tayi ta diga a cikin gongomin kamar yanda baseline insa yake, Haka ma tamasa da sabulu Sai 6:30 Al'ameen ya shigo gidan Sumayya Kam ganin ya shigo d'akin da sauri ta d'auki takalmin sa ciny'ayyen ta saka Masa sabo,ta dawo d'akin,kudi ta basa 2k yasai musu dankalin turawa boket D'aya sai k'wai guda biyar, Fita yayi a d'akin bayan ya karbi kudin yazo ya zura takalminsa,sai Kuma ya cire da sauri,ya ringa laluben bakin dakalin Amma wayam baiji takalminsa ba Sumayya!!ya k'wala Mata Kira "Na'am"Sumayya ta amsa tana fita a d'akin itama Sumayya Banga takalmina ba pls ki duba mini Mana? "Ba gashinan a gefenka ba" tace tana kallonsa Wannan ba nawa bane "Nawa kenan?kadaisan banda takalmi irin wannan soson"? Amma ni sai inaji Kamar ba nawa bane,nawa fa da laushi sosai ya kode "Toh wannan in fa",ta tambaye sa tana mamakin fahimta irin nasa Kamar sabo sabo, "Hhhh lalle zaka tafi da kafa kenan tunda dai ga takalminka kace Wai ba naka ba" Sumayya bafa Wasa nake ba Wannan ba takalmina bane "Nidai naka na gani atoh"tace tana komawa d'akin Al'ameen Kam ba yanda ya iya Haka ya saka takalmin Amma har ransa yanaji ba nasa bane. Bayan fitar Al'ameen Sumayya aikace aikacen ta na gida ta Gama ta d'aura ruwan zafi a kittle. Al'ameen Kam bakin kasuwa yaje ya musu sayaya ya kamo hanyar gida Bayan Al'ameen ya dawo Sumayya ta soya dankali da k'wai sai ta hada musu tie, rufewa tayi ganin Al'ameen ya Shiga wanka Al'ameen aban d'aki mamakine ya kamasa Jin sabulunsa na kamshi ,Amma baiyi magana ba bayan ya fitoh, d'aki ya Shiga a hankali ya bude bakkon sa jallabiya D'aya ya zare a ciki ya zaro gajeren wando da vest. Sumayya na zaune akan kujeran tana kallonsa saka wando yayi da vest sai Kuma taga ya tsaya Yana tattaba vest in,Amma baiyi magana ba ya d'auki jallabiyar yasa,sai Kuma ya juye kayan bakkon duka a cafet Yana tattabasu. Sumayya!ya kirata "Na'am"tace tana kallonsa Sumayya wa'innan ba Kayana bane? "Akan me zakace haka" Sumayya wa'innan Sabine kijifa kayan kamshin sabbin Kaya suke bama Turare ba kiji da karfi fa kayan ba masu laushi irin nawa bane? "Nidai naka na gani" Sumayya me Kika sayo jiya da naji laida na kayo kayo a hannunki? "Ina ruwanka"ta basa Amsa Indai baki fad'amin gaskiya ba toh bazan fad'a Miki wacece kamila, menene hadin mu da ita ba Tabe fuska Sumayya tayi "Gaskiya n................ 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin,Koh kinsan mace sai da kamshi da gyara* 😉 🍀🍀🍀🍀 *Turare suna d'ayace Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin sa* 🍀🍀🍀🍀 *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da* *gyara* 🍀🍀🍀 *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace* 🍀🍀🍀 *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE* 🍀 *Na tsunguno(habil)* 🍀 *Na jiki (kwalaccam)* ( *khumra, black & white* ) 🍀 *Turaren turara jiki after birth* , 🍀 *Na d'aki(halud Al'oud)* *UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* 💃🏼💃🏼 🍀🍀🍀 *Suna bada d'aya Koh sare akan farashi Mai Rahusa* 🍀🍀🍀 *Suna bada order kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria* Contact them vie 🪀08028827241 or 09033791049 IG @umsadincense@umsadincense*@umsadincense@umsadincense08084453785kyauna 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya* *Ibrahim* 🍃 ✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwa👌 free book 🤧 Page 3️⃣8️⃣&3️⃣9️⃣ "Ni Kaya na saya" ta basa amsa Wani irin Kaya kenan? sannan Ina Kayana? "Nina yarda kayayyakin ka duka sabo na sai maka Naga nakan sun kode,Amma kayi hakuri bazan sake ba" tace tana Kama hannunsa dake kokarin zare jallabiyan jikinsa Sumayya akan me Zaki sayamin Kaya bazaki fad'a mini ba saboda bani da ido saiki zo ki musanya mini,kamar wani yaro. "Kayi hakuri kaga yanda jallabiyar nan ta karbe ka kuwa yayan khadija" tace ta ja maza zip in gaban jallabiyar,hade da d'aukar Turare ta fisa Masa,vayan ya shafa Mai Nagode Allah ya miki albarka ya hanani Miki butulci a rayuwa Sumayya "Ameen" tace tana jera abincin karyawan, Bismillah ta Masa suka fara ci cikin kwanciyar hankali Bayan sun Gama cin abinci tattara Kwanukan yayi yakai waje,bayan ya ajeye, d'akin yadawo "Toh yayan khadija wacece kamila"Sumayya ta tambaye sa Nifa nayi Miki Alkawari ,ai basai kin Kara tambaya taba nida kaina Zan fad'a Miki kome Daya shafe kamila. "Uhmm ba Dole na tambaya ba tunda sai jamin Rai kake yaufa da wure na Gama aiki Amma sai wani sham kamshi kake" Nasha kamshin, kema saiki Rama. "Wallahih ka Gama iyya jarabanka bazan biye maka ba sai naji lbrn nan ehen" Toh zoki zauna a kusa Dani samun lbrn yafi Dadi,yace Yana zama akan kujera Saboda tsabar sonjin lbr yasa Sumayya mikewa da sauri tazo Kan kujeran ta xauna kusa dashi Hannu yasa ya matsota jikinsa a hankali ya rungume ta a jikinsa cikin sanyin hallintarsa murya a sanyaye yace Sumayya! "Na'am yayan khadija" Yau Zan baki labarin kamila Amma saikin ji labarina Nima kafun ki gane lbrn kamila dakyau. "Yauwa Aiko Ina sonjin lbrn ka da dangan takarka da gidan ADARA duk da Ina tunanin dangin mahaifinkane Amma halayenku sun banbanta,hakan matsayinka da khadija a gidan nan na fahimci a kaskance kuke ba Kamar sauran Yan gidan ba" Duk xakiji insha Allah Koh Nima Zan samu amsar dalilin auren mu Wanda har yau bansan dalili ba. "Wai kana nufin ba Kaine kace kana Sona ba,aka aura maka ni "?ta tambaye sa cikin zare ido. Nima ban sani ba Sumayya bansan dalilin auren muba Amma koma menene inaji a jikina insha Allah haduwar mu dake alkhari ce "Insha Allah insha Allah yayan khadija" tace tana share hawaye Daya gangaro mata Gyara zama Al'ameen Yayi a hankali ya fara magana................ *Shikaru Talatin da biyar da suka wuce baya* 🕢 Malam Yusuf sumul, shine cikekken sunansa da aka Sansa dashi matashine Dan shikara 35,Yusuf mutum ne Mai Hakuri addini ga kawaici baid'auki duniya da zafi ba,Yana da tsananin zurfin ciki duk yanda zaka zauna dashi bazaka taba fahimtar wani abu a tattare dashi ba shiyasa ba Wanda yasan shid'an inane Koh daga Ina yake, duk da kowa ya gansa Kuma yaji yanayin hausar sa da maganar sa Dole yasan cewa ba D'an kasa bane . Alhaji Rabi'u ubangari. Wanda akafi sani da ubangari,maikacin gonnati ne Kuma Mai rufin asiri sosai,Yana da Mata biyu. shine Mai gidan Yusuf, saboda tsananin hankali da nitsuwar yusuf yasa ya d'aukesa Kamar D'an gida ya basa d'aki a cikin gidansa,Yusuf na Masa aikace aikace kamar zuwa kasuwa wanki da gugan kayan yaransa da NASA na kansa Yana Kai kananun yaransa makaranta ya dawo dasu, Yaran ubangari guda biyar ne sai yaran Yan uwansa maza biyu Mata hudu,kenan yara goma Sha D'aya ne a gidan ubangari Zainab Fatima Auwalu lukman Nasir,sune yaran ubangari na cikinsa Haidar Umar khairat munira safara'u murja sune yaran Yan uwansa Dayake rikewa Yusuf da ubangari akwai kyakkyawar fahimta a tsakaninsu duk da baisan Yusuf ba Amma da zuciya d'aya yake zaune dashi ganin tsawon shikaru Bai taba nuna wani mugun halinsa Wanda mutane zasuye Allah wadai dashi ba. Yaran gidan na basa girmansa kasancewar duk yaran gidan ya fisu a shikaru,yanajin dadin zaman gidan sosai don tun kafun Alhaji yayi aure suke tare har Allah yasa yayi aure Yaran suna ganin girman Yusuf saboda yanda mahaifin su ke tare tashi hakan yasa suke kiransa da bappa yusufa Zaman Yusuf a gidan ya fara gunduran sane bayan girman Yar Alhaji Rabi'u ubangari zainab,wance Allah ya diga Mata son yusuf Mai tsanani duk da a lokacin tana da shikaru 14 yayin da Yusuf keda shikara 35 Tun tana boyewa har abin ya gagara ta tinkare Yusuf da maganar. Sosai Yusuf ya ja Mata kunne akan zancen kuma ya tabbatar Mata shi bazai aureta ba donshi a matsayin diyarsa,ya d'auketa duk yanda tayi kokarin ganin tashawo Kan Yusuf abin ya gagara,taso fad'awa mahaifyarta zancen tanason Yusuf Amma khairat Yar bappanta ta hanata saboda tasan mundin maman zainab tasan zancen daker zainab ta aure Yusuf. ADARA FAMILY HOUSE haifafun jalingo ne tun iyaye da kakanni anan gidan Adara suka tashi don duk fad'in sintali ba gida Mai dumbin tarihi da shikarun mazauna ciki irin family ADARA tun husul sai chanje chanjen gini da ake in zamani ya shude, Tun husul ma haka suke mutane ne masu masifan tsiya ga fad'a kamar ahlin dambe shiyasa aka musu lakabi da ADARA Aishan ADARA d'aya ce daga cikin yaran gidan adara ,macece Mai matsifa na bugawa a jarida duk yanda kaga mala'in yaran gidan ADARA Aisha ta damasu ta shanye saboda tsananin masifarta yasa Koh saurayi Bata dashi don a lokacin abin kunyane mace takai shikara 20 batayi aure ba Amma Aisha shikarunta 20 Koh saurayi Bata dashi saboda tsananin tsoronta da maza keye Gidan ADARA tun asali haka yake har wa yanzun. Aishan ADARA na Saida Dan wake a bakin kasuwan main market na jalingo Sun hadu da Yusuf ne lokacin da yaje kasuwa sayayyan kayan Miyan gidan ubangidansa,ya saye danwaken ta by mistake robanta ya fashe a hannunsa, Ba karamin bala'i Aishan ADARA ta sauke Masa ma kwando kwando da Kuma uzzurawa saiya biyata robanta Yusuf Kam ba karamin mamaki yasha ba ganin irin bala'in da Mai danwake ke Masa akan robanda Bai wuce sule biyar ba sai bala'i take Masa Kamar ya Mata Satan jari Sosai Yusuf yaji haushi kala baice Mata ba ya Kama hanya Yana tafiya itakam sai binsa take sayya Biya robanta Yusuf kam yasha Alwashin bazai biya ba ganin jarabanda take Masa haka tayita binsa harya Gama cefenen ya Kama hanyar gida bayan ya tare machine. Duk jaraban Aishan ADARA yau taga iyyakarta don ba zagi ba duka da Mannin hauka Yusuf ya rabu da ita Bayan dawowar Yusuf gida Sam ya rasa sukuni,tunanin Mai danwake Kam ya hanasa sukuni Sam Ta bangaren Aishan ADARA ma hakane Sam bayan tafiyar kyakkyawar mutumin da Bata Sansa ba gabaki daya ya hanata sakat a tsawon shikarun ta Bata taba bi takan soyayya ba Amma wannan Karo tayi tuntuben so a bakin titi Wanda Bata San inda zata sake ganinsa ba Bayan sati biyu Sam Yusuf ya kasa sukuni ya kasa hakuri sosai Y'an kwanakin nan ya gane meke d'awainiya dashi,sai a lokacin yaji tausayin zainab Ashe haka takeji yake wulakanta ta, Farga bansa d'ayane kar yaje gareta da soyayya ta tsigalesa don Tabbas daga ganinta Yar bala'i ce sosai Abu na biyu Kuma asalinsa kar rashin sanin danginsa yasa a hanasa auren ta. A hankali Yusuf ya fara zuwa gun Aishan ADARA cin danwake Wasa Wasa harya kasance ba ranan da baya zuwa ci haka ba ranan da basa fad'a a tsakaninsu kafun su rabu ,har shakuwa yazo ya shiga tsakaninsu Mai tsanani Wanda a zahiri kowa son junane ke d'awainiya dashi,Amma ya kasa sanar da D'an uwansa A hankali Yusuf ya fahimci masifar Aisha a tarbiyan gidansu yake a Hankali ya Soma nutsar da ita sosai yake nuna Mata abin Bai dace ma Abu kamar Wasa Aishan ADARA ta nutsu sosai sai dai fa har lokacin in ka tabota zaka Sha bala'i sai dai in abinda ba ruwantane Bata Shiga haka zalika ta daina dambe da kowa,abin harya fara bawa jama'a mamaki sauyawan ta Lokaci da Yusuf ya bayyana ma Aisha soyayyarsa gareta Babu wani jinkiri ta amsa sosai suke zuba love Yusuf ya samu Alhaji akan maganar Aisha ba karamin murna alhajin yayi ba dayaji Yusuf ya samu wance yake so don burinsa kenan,ya tambaye Yusuf danginsa don maganar aure Dole ana bukatan dangi na jini Hankalin Yusuf ya Tashi matuka don har kwanciya yayi a gadon asibiti Akan zancen danginsa da Alhaji ya matsa Masa akai Karshe dai fa ubangari yaga abin fa nayine yasa sa hakura da tambayar Yusuf shi yashiga maganar auren Yusuf Da yake ubangari ya jima tare da Yusuf kowa gani yake kamar Yan uwane hakan yasa ba dogon zance aka basa auren Aisha don Suma sun Matsu tayi aure ganin ta girma a gida Ta bangaren zainab Yar ubangari Kam in hankalin ta yayi dubu ya Tashi tayi kuka tayi kuka Kamar zatayi hauka Amma khairat ta taka Mata birki tare da Mata alkawarin sai Yusuf ya aureta amma tabare ayi auren taga matakin da zata d'aukar Mata Bayan auren Yusuf sumul da Aishan ADARA, Alhaji yaki yarda Yusuf ya Kama gidan haya a gidansa sukaci gaba da zama, soyayya suke shimfid'a wa Mai tsafta sosai Aisha ta nutsu suna zaune da yaran ubangari da matansa lfy Sam bata nuna musu Yar Hali sai daifa basa shiri da zainab ganin kallon banza da take mata Sai Bayan shikara uku da auren Aishan ADARA da Yusuf kafun Allah ya baiwa Aisha ciki sosai sukayi farinciki da wannan cikin da Allah ya azurtasu,sukaci gaba da rainon cikin cikin farin ciki Bayan Aisha ta haihuwa sun samu d'a namiji Mai matukar Kama da mahaifinsa Kamar an tsaga Kara, mahaifinsa yasa Masa suna muhammad. Mahaifiyarsa na kiransa Al'ameen. Da sauri Sumayya ta d'aga ido tana kallon Al'ameen dake Bata lbr"kana nufin kace mini gidan n........" Bai bare ta karasa ba ya girgiza Mata Kai Yana Kara kwantar ta ita a jikinsa,ki aje tambayoyin ki Inna Gama saiki tambaya Kai kawai ta gyad'a Masa Ya cigaba.....har lokacin zainab Bata saduda da soyayyar Yusuf ba don a lokacin ta kammala secondary school nata,Amma Taki aure Dole yasa babanta nema Mata wani makarantan gaba da secondary taci gaba Bayan haihuwa Al'ameen da shikara uku Aisha ta Kara haihuwar wani da namiji yaci sunan Salim, tun daga lokacin Aisha Bata sake samun ciki ba,sukaci gaba da kula da yaransu don a lokacin Alhaji ya budewa Yusuf shago yabar aikace aikacen gida basuda wata matsala sai na d'ansu Salim Wanda ke fama da mummunan ciwon zuciya,duk bayan wata D'aya sai sunga likita Kuma sai anci kudi. A hakan rayuwa tayita tafiya yau Dadi gobe akasinsa Al'ameen da Salim suna matukar samun kula daga iyayen su suna Isa shiga makaranta aka sakasu yarane da suka shagu da junansu matika Kamar wasu tagwaye Dayake Salim nada gaban girma tuni ya tsara da yayansa har lokacin Aisha Bata San cewa Yusuf ba Dan uwan Alhaji bane duk da tana yawan tambayan sa labarin Yan uwansa Amma Yusuf daga tayi tambar saiya hau hada Mata fuska Bayan wasu shikaru lokacin Al'ameen nada shikara 11 Salim nada shikara 8 a duniya. Aisha na d'auke da karamin ciki. wata ranan juma'a da zuriyan yusuf bazasu taba mantawa da ranan b a tsawon rayuwansu ba har Abada ciwon bazaibar zukatan su ba Da misalin karfe bakwai na dare yusuf ya dawo gida,Yana kokarin shiga shashen su sai ga khairat taresa tayi cikin kuka Wai zainab ba lfy tana dakinta Alhaji yace yaje su kaita asibiti Da gudu yusuf ya bi bayan kairan zuwa shashen Yan matan gidan,shiya fara Shiga d'akin Yana shiga khairat taja kofar ta rufe kofar ta waje da makulli. Yusuf na shiga d'akin ya ware ido ganin zainab ba Kaya daga ita sai d'aurin kirji a zaune akan gado Tambayar ta yusuf ya farayi, zainab menene haka Kuma ki nemi riga ki saka yace Yana Mai kokarin bude kofar Dariya zainab ta sake hade da furta wallahih kaji na rantse maka Yusuf tunda ka hofantar da soyayya ta kasa kafa ka shureta Nima saina jazamaka bala'i inda zaisa ka aureni Dole wannan itace kad'ai abinda zanyi na mallakeka,ka 'dauka Koh shurun da nayi na hakurane? Ah ah wallahih ban hakura ba tanadi nake maka. Subhanallah shine abinda yusuf ya furta cikin gigita, zainab Ashe bakida hankali wani irin shirmene haka Hauka zakace ba shirme ba tabasa amsa tana matsowa garesa hade da fizgo kwalar rigansa ta yaga sosai tana ihu Sosai yusuf ya razana ya Shiga kokarin k'wace kansa Khairat Kam tana rufe d'akin ta tsaya kamar minutes biyu kafun ta fara rafka salati a tsakar gidan wayyo jama'a wani zaima zainab fyade a d'akinta yanzun nazo shiga kawai naji kofa a rufe zainab nata kuka ku kawo d'auki Da gudu Yan gidan harda Aisha da makwanta Dayake darene ga madalisa a kofar gidan suka ruga da gudu zuwa d'akin zainab da suke Jin kukanta na tashi har lokacin Jin kofar a rufe yasa matasan samarin unguwan suka dauko katon itace suka bugawa kofar take kofar ta balle,cikin mamaki tsoro Al'ajabi suka zubawa d'akin ido ganin abinda ke faruwa kamar a mafarki y................ 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin,Koh kinsan mace sai da kamshi da gyara* 😉 🍀🍀🍀🍀 *Turare suna d'ayace Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin sa* 🍀🍀🍀🍀 *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da* *gyara* 🍀🍀🍀 *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace* 🍀🍀🍀 *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE* 🍀 *Na tsunguno(habil)* 🍀 *Na jiki (kwalaccam)* ( *khumra, black & white* ) 🍀 *Turaren turara jiki after birth* , 🍀 *Na d'aki(halud Al'oud)* *UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* 💃🏼💃🏼 🍀🍀🍀 *Suna bada d'aya Koh sare akan farashi Mai Rahusa* 🍀🍀🍀 *Suna bada order kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria* Contact them vie 🪀08028827241 or 09033791049 IG @umsadincense 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya* *Ibrahim* 🍃 ✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwa👌 free book 🤧 🏵️Wannan shafin nakune🏵️ Ummu Muhammad 🍀 Zainab mansur🍀 Surayya🍀 Page4️⃣0️⃣&4️⃣1️⃣ Yusuf ne kwance akan zainab suna dambe Salati dumbin Alumman dake wajen suka sake,zainab Kam da sauri ta sake Yusuf ta matsa gefe tana kuka da rawan jiki Yusuf Kam ya kasa magana sunkuyar da Kai kawai yayi don bazai iyya hada ido da ubangari ba Yusuf Ashe Kai Maci Amana ne Yusuf Ashe Kai mugune Yusuf shiyasa tsawon shikarun nan kake zaune Dani da fuska biyu azzalumi maha'inci kawai wallahih nayi Dana sanin zama dakai, Allah ya isan mini tunda ka rasa Wanda zakabi sai Yar cikinka,yace hawaye na taruwan Masa a ido,matasan samarin nan basuye wata wata ba suka rufe Yusuf da duka duk yanda yaso musu bayani Basu basa dama ba Aisha Kam ba karamin shock ta Shiga ba Daman Yusuf ba D'an uwan ubangari bane? shiyasa inta tambaye sa Ahlinsa sai yahau fushi Ashe baida gaskiya ne kwata kwata, Aisha Kam kuka take tana dana sanin Yusuf, ya zubar Mata da mutunci ya ha'ince ta Matar ubangari waya ta d'auka ta Kira police lokacin Amma Yusuf jina jina Koh tsayuwa baya iyyayi,ga matan sa da yaransa duk suna kuka, A lokacin yaran basusan me uban yayi ba Amma tabbas sunsan ba lfy Police na zuwa daker suka k'wace Yusuf ganin ana kokarin kisan kai, lokacin da police suka Kama Yusuf za'a fita dashi cikin tsananin azaba yake rokonsu su barshi yaga MATARSA zai Mata magana. Ba musu domin tabbas su kansu police a lokacin sunji tausayin sa sosai da sosai,wani ne a cikinsu ya taimaka Masa suka nufi wajen da Aisha ke duke tana kuka Yusuf na Isa dukawa yayi yasa gwuwarshi a kasa cikin galabaita ya fara magana, Aisha Koh kowa zai yarda akan abinda yafaru don Allah Aisha ke kad'ai ki yarda Dani, yardan ki kawai nafiso akaf fad'in duniyan nan bayan yardan Allah,don kece abokiyar rayuwa ta in kowa zai juyamin baya ke Kika rungumeni bani da kaito Aisha Ina neman Wannan alfarman. ya karasa maganar hawaye nabin fuskar sa Aishan ADARA Kam yau Hali ya motsa jikinta har bare yake cikin kakkauran murya ta mike ,Yusuf Yusuf wallahih nayi Dana sanin haihuwa da Kai Yusuf, nayi Dana sanin auren ka Yusuf ka cuce kanka ka cuceni Yusuf bana bukatar ka a rayuwa ta ni daga yau mijina ya mutu. Sosai Yusuf ya fashe da kuka maicin Rai Wai waye zai fahimce sane kowa bazai yarda dashi ba kawai don an gansa a d'akin yarinya Babu bincike sai kawai ad'au mataki, me yasa tunani bazaizo musu ba duba da cewa ya rasa inda zai nemi zainab sai a cikin gidansu? Yunkurin magana yafara ais......,da saure Aisha ta d'aga Masa hannu Yusuf Koh Babu Kai zamu rayu da yarana Koh bakai Zan iyya rayuwa Koh ba Kai rayuwar zata Mana Dadi,Amma zaman ka acikin mu shine kuncinta ka tafi bana bukatarka a yanzun,tace tana Mai kokarin baren wajen. Da sauri yusuf ya Kama hannun Aisha,bataye wata wata ba ta tsinka Masa Mari. Da sauri Yusuf ya sake Mata hannu Da sauri Al'ameen Yayi wajen babansa cikin kuka ya rungume sa,abbajo menene Kaye musu suke dukanka abbajo ga fuskarka duk jini,abbajo muje asibiti a maka treatment kaji abbajon mu ka bawa police hakuri karsu tafi dakai,kuka Yusuf ya sake hade da rungumar d'ansa Dayake Jinsa Kamar bugun numfashin sa, cikin su biyun yafi kaunar Muhammad sosai. Karka damu muhammad Zan dawo kaji laifin da ba nawa bane aka d'aura mini Wanda duniya kaf ni ake gani da laifin ,Yusuf yace ma d'ansa Yana Mai d'aukar sarkan dake wuyansa fari Mai azabebben kyau da walkiya ya d'aurawa Al'ameen a wuya, Muhammad ka kula da mamanku da kaninka kaji in mamanku ta haifi mace kace asa Mata khadija Inna mijine asa masa Shitu,Yana fad'a Masa hakan police sukazo suka Tisa keyarsa zuwa cikin mota Bayan an tafi da Yusuf, Alhaji ubangari da danginsa Koran Kare sukama Aisha da yaranta,sosai Aisha tayita kuka tana tattara kayanta zubawa tayi a ak'watin karfe ta d'aurawa Al'ameen da salim,suka Kama hanyar sintali. Gari gabaki d'aya ya d'auka zancen Yusuf yayi kokarin mawa Yar ubangidansa fyade,bayan isar Aisha gidan ADARA zuwa lokacin labari yazo kunnensu Dayake unguwan da suke da sintali ba nisa Bayan isar Aisha gida ta sake haduwa da wani tashin hankali shine mahaifinta yace sai ta mayarda yaran Yusuf gun danginsa kafun ta zauna musu a gida Dayake mahaifiyar ta tarasu tun kafun auren ta,yasa ba Wanda yayi yunkurin baiwa baban ta hakuri Aishan ADARA ta shiga tashin hankali ba kad'an ba na rashin sanin asalin Yusuf abin yayi mugun daga Mata hankali,ta rasa Ina zatasa kanta taji Dadi,don da ta koma gidan ubangari tunda shine waliyin Yusuf ya fad'a Mata inda dangin Yusuf suke Amma rashin mutunci da aka Mata a gidan Koh kyaun gani Babu,karshe dai wani abokin Yusuf ne Wanda sukaye mutunci sosai ya taimaki Aisha bayan Jin labarin abinda ya faru tabbas shima ya shiga tashin hankali Amma Sam Bai yarda Yusuf ne zai aikata wannan abinba, d'auko Aisha yayi ya Basu d'aki a gidansa duk da MATARSA ta tsani zaman su Aisha Amma ba yanda zata iyya Aisha ta koma gidan abokin Yusuf da zama. Wannan zaman gidan abokin Yusuf shine mafarin haduwar Al'ameen da kamila An Kai Yusuf kotu,Amma bashi da hujjan Kare kansa haka yanaji Yana gani,laifinda ba nasaba aka yanke Masa hukunci. Bayan Shari'a abubuwa sun ma Aisha yawa na rashin mijinta don abinda zataci ma gagaransu yake Dole karatun su Al'ameen a private ya gagara ta ciresu ta maidasu Government school, sukaci gaba da zuwa,itakam wankau take Koh daka take sama musu abinda zasuci sosai Aisha take fama da rayuwa ga bakin cikin_ abinda Yusuf ya aikata,ba karamin bakin jini ya shafawa yaransa ba Hankalin Aisha Bai Kara tashi ba Saida lokacin komawar Salim asibiti Amma Bata da Koh sisi haka ta d'aukesa sukaje asibitin Amma abin mamaki duk yanda suka Saba da zuwa ganin likita Amma yau kawai da basu da kudin magani haka suka dawo gida kayan sakawarta Aisha ta tattara da kayan dakinta take sayarwa a hakan ta ringa ma Salim jinya da kayyakinta don abokin Yusuf d'aki kawai ya Basu Amma abinci Kam sai dai ta nema musu, Ta bangaren zainab Kam tayi Dana sani Dana saninda har abada bazata daina yinsu ba sai yanzun take ganin wautarta na biyewa khairat harta aikata wannan mumunan kazafi wa Yusuf gashi abin Bai tsaya iyya Yusuf ba ta raba ma'aurata ta raba uba da yaransa ganin Yusuf da take taji Dadi yanzun Babu shi gashi Koh samarinta ma yanzun duk sun gujeta a dalilin labarin da suka samu Zainab rayuwa ta Mata zafi Koh baccin kirki Bata iyya wa taso sanar da iyayenta gaskiya Amma kairat ta kwabeta don hakan zai iyya zubar Mata da mutunci fiye Dana yanzun da take ciki. Al'ameen da kamila yaran makwanta ne gidansu kamila.na kusa da gidan bala abokin Yusuf, Kamila dalibar makaranta i private school ne Wanda ke kusa da goverments day da Yusuf ke ciki Farkon haduwar kamila da Yusuf a hanyar makaranta zai tafi itama zata fita. Tunda kamila.taga Al'ameen take yawan shige Masa har gidansu take zuwa tun Al'ameen baya kulata hardai ya fara kulata Aisha Karan kanta da farko bataso mu'amalar Al'ameen da kamila ba ganin Al'ameen lokacin shikara biyar ya bawa kamila Amma haka ta barsu ganin karatu Yusuf ke koya Mata kullum insun hadu Bayan wata uku lokacin cikin Aisha ya Shiga wata bakwai,zuwa lokacin Aisha Bata da kome a dakinta sai taburma sai sarkan wuyan muhammad sai tsummo karansu saboda duk kudin sun Kare akan kudin maganin Salim ga rayuwa dai anata gargarawa Yau ranan juma'a Al'ameen da Salim sun dawo makaranta bayan sun kara kamila gida don yanzun shakuwane Mai tsanani a tsakanin su wanda in kamila bataga Al'ameen ba zatazo gidansu haka shima, suna zaune dumamen safe da ya rage shine Aisha ta Basu itakam haka ta hakura saboda yau sun tashi bako sisi,zainab ce ta shigo gidan da sallama a bakinta Aisha ta amsa Mata Dan Sam bata Jin haushin family ubangari don Koh itane abinda Yusuf ya aikata saita Masa fiye da haka Kallon zainab take Wanda duk tabi ta rame kallo d'aya zaka Mata kasan Bata cikin hayyacinta,bayan sun gaisa zainab ta d'aga ido tana kallon Aisha Bata San ta Ina zata fara ba yau tayi Alkawarin zata Fad'i gaskiya Koh zata samu sassauci a rayuwan ta Hawaye ne ya cika idanun zainab ta bude baki a Hankali tace,maman Muhammad akwai wani magana da zanfada Miki bansan ya Zaki d'auki maganar ba Amma na g'wammaci na karbi Koh wani hukunci akan Wanda nake ciki Cikin mamaki Aisha kam ke kallon zainab a iyya zamansu da zainab Bata taba ganin ta Mata magana a mutunce ba Kamar yau,toh zainab Allah yasa naji alkhari Gaskiyan abinda ya faru maman Al'ameen babu ruwan Yusuf aciki,tace tana kallon Aisha Kamar ya bangane ba zainab? Eh tabbas Kamar yanda nace , Yusuf Babu ruwansa a ciki nice da khairat Muka had'a kome a tunanin mu Koh in aka Kama Yusuf xai mini fyade babana zai tilastashi ya aure ni Amma ban taba tunanin abinda na aikata ba daidai bane Saida Naga yanda na wargaza muku farin cikin na dasa muku bakin ciki, wallahih maman Al'ameen nayi nadama,Dana biyewa khairat ban tashi nadama ba Saida naji jiya tana Hira da kawarta a waya suna mini dariya, na tsokancin danayi harna yarda da abinda ta gayamin Ashe itama son Yusuf take,ta karasa maganar hawaye ya zuba akan fuskarta Aishan ADARA Kam daskarewa tayi a zaune itakam wace irin mace ce Mai mantuwa me yasa ta kasa yarda da Yusuf, namijin daya yarda zai rayu da ita Bai damu da tarbiyan gidansu ba Koh halinta ba ya aureta Koda Yusuf Zina yayi hukuncin da ta yanke Masa yayi tsauri,wani irin murdawa mararta yayi na tashin hankali atake jini ya balle Mata durkusawa Aisha tayi tana Kiran sunan Allah. Da gudu matar Bala dake tsaye tun d'azun tanajin bayanin da zainab keye tazo da gudu,tana kwalawa mijinta Kira da gudu ya fitoh su uku suka ciccibi Aisha zuwa asibiti Al'ameen Kam Kama hannun Salim yayi suka Kama hanyar gidan ADARA,suna Isa kakansu suka samu a kofar gida suka fad'a Masa mamarsu ba lfy an kaita asibiti, hankali baban Aisha ya Tashi matuka don shi Karan kamshi korinda Yama Aisha na haushin yaran Yusuf ne, Amma Yana son yarsa tura su Salim yayi gidan Amina (Goggo) shi Kuma ya wuce gidan Bala agun ya samu wa'inda ke zaune aka fita da Aisha, aka Masa kwatancen asibitin da aka Kai Aisha Bayan zuwansa ne yaji labarin abinda ya haddasa ma Aisha nakudar Dole abakin Matar Bala,shima sosai ransa ya baci duk da Bai gamu da zainab a asibitin ba Amma ransa ya matukar baci gida ya koma ya sanar da yaransa da yaran Yan uwansa akan suje su fara d'aukar mataki akan zainab kafun hukuma ta shiga Ayarin gidan ADARA daga Yan Mata har zaurawa da samari sukaye Ayari guda suka fasa unguwa da kafa suka taka har gidan ubangari. Zainab Kam gabaki d'aya ta rasa nutsuwarta Koh zama takasa waje Daya, tunda ta gudo daga hospital karshe dai Saida mamarta ta tambaye ta Koh meke damunta haka? tunda abinnan ya faru ta fahimci walwalar zainab ya d'auke, zainab Kam kin fad'a Mata gaskiya tayi Suna zaune dukansu a gida dayake yau Friday ne ubangari ya dawo aiki da wure haka Yan makaranta,ji kawai sukaye an bankado get in gidan an shigo ciki kafun ma su gama tantance suwaye ne har kanwar Aisha ta nufi d'akin zainab jawota sukaye har kofar gidan da gudu su ubangari suka Mara musu baya. Rufeta da duka ADARA sukaye, saiga khairat tafitob gida makwantan su, Aiko kamota sukayi suka Had'asu suna jibga duk yanda Yan unguwa da ubangari suke kokarin k'wace zainab da khairat abin ya gagara ganin zasuye kisan kai don zainab ta Suma Amma haka Ayarin gidan Adara Basu daina jibgarta ba Saida ta farfado da duka Police aka Kira lokacin unguwan ya cika makil day'an kallo, abinka da Friday kowa na gida, bayan zuwan police kafun aka samu aka k'wace su zainab anso Kama Yan ADARA Amma Ina abin ya gagara don fad'ane ya kusa zama na police da Yan gidan Adara,ganin jaraba irin na Yan gidan yasa polisawan tambayar musabbabin fad'an don dai sunyi sunyi su bisu station aye kome agun Amma sunki, D'aya daga cikin samarin gidan ne ya nuna zainab,ke don uwarki fada musu meya faru tsakaninki da yusuf mijin Aisha? Hakika zainab tayi mugun tsorata hakan yasa Bata boye kome ba ta fad'a duk abinda ya faru,atake Alumman suka fara Allah wadai da zainab da khairat ubangari Kam yanke jiki yayi ya Fadi hawan jininsa ya tashi, police ma tafiyarsu sukaye Basu d'auki kowa ba. Ta bangaren Aisha Kam ganin tana kokarin rasa Ranta yasa likitoti Mata operation aka cire baby girl bakwaini aka saka a kwalba,Aisha na farfadowa sunan mijinta ta fara Ambata tana sambatu,tunda ta farfado batada magana sai a kaita wajen Yusuf ta nemi gafaransa Amma ba'a barta ta fita a asibitin ba saboda yanayin jikinta Dana baby. Ta bangaren ubangari ma hakan take jinya ya kwanta har kusan sati baisan inda kansa yake ba abubuwa sun taru sun Masa yawa,Yana Jin sauki kad'an ya Tashi da kafarsa ya koma wajen Alkalin da yayi musu Shari'a, An nemi ganin Yusuf don a wankesa a kotu Amma abin tashin hankali shine, Yusuf a Randa aka kaisa prison Bai kwanaba ya fita tare da sa hannun kotsosin kasa Wannan magana ita tafi ko wace magana tashin hankali agun Aisha don anye iyya bincike an had'a hannu da masu kudin da Yusuf yayi mu'amalan kasuwanci dasu don binciko inda Yusuf yake Koh suwa suka fiddasa Duk Wanda aka tuhuma Mai hannun a cire Yusuf magana D'aya yake fad'a baisan Yusuf ba kawai umurni aka basa daga sama Wannan magana tayi mugun dagawa Aisha hankali atake ta sake kwantawa ciwo Wanda an rasa kansa kullum gaba gaba yake duk abinda babanta ke dashi ya kare a jinyar Aisha da Salim don shima zuwa lokacin zuciyarsa ta fara tashi. Tsawon wata biyar ana binciken case in Yusuf Amma shuru ba wani cigaba,yau dai jikin Aisha da sauki,bayan Salim da Yusuf sunzo duba mamar tasu ,don yanzun suna zaune a gidan Adara ne A hankali ta Kama hannun Al'ameen ta rike cikin nata ta fara magana hawaye nabin Gefen idanunta,Al'ameen ga kaninka nan da Yar uwarka khadija Muhammad ka kula dasu ka zama uba a garesu Koda kowa zai gaji dasu Kai ka zaman musu gata, jagora,Garkuwa,inaji a jikina wata Rana zaka Hadu da mahaifinka,kace Masa ni Aisha Ina neman afuwarsa ya yafe mini Koh Zan samu salama,ka zamo Mai hakuri kamar mahaifinka duk abinda zakaye a rayuwa ka ringa bincike karka yanke hukunci a cikin fushi don karshin sa Dana sanine. Al'ameen duk da yarone Amma hankalinsa in yayi dubu toh ya tashe in Bai manta ba haka abbajonsa yayi Masa, shikenan ya gudu ya barsu don shi har yanzun baisan takammamen abinda yake faruwa ba, Mami kema gudu zakiye kamar abbajo ki barmu?yace Yana kuka shida Salim dake kusa dashi Ah ah Yusuf ba gudu zanye na barku ba inda zanje kowa ma zaije in lokacin sa yayi sanan abbajonka Bai gudu ba wata Rana zai dawo kaji,ga kaninka na kuka ka rarrashesa karka barsa ya zubda hawaye kasan ciwonsa bayason damuwa Koh?ta tambaye sa muryanta na shakewa Kai muhammad ya gyad'a Mata hade da Kama hannun Salim Yana rarrashensa, Ji kawai yayi mamin su na wani irin shakuwa hade da Kiran sunan Allah,da sauri ya fita a d'akin yaje Kiran Doctor Suna shigowa dakin da sauri Muhammad ya matso gareta cikin matukar razana ganin maminsu Bata m................... 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin,Koh kinsan mace sai da kamshi da gyara* 😉 🍀🍀🍀🍀 *Turare suna d'ayace Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin sa* 🍀🍀🍀🍀 *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da* *gyara* 🍀🍀🍀 *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace* 🍀🍀🍀 *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE* 🍀 *Na tsunguno(habil)* 🍀 *Na jiki (kwalaccam)* ( *khumra, black & white* ) 🍀 *Turaren turara jiki after birth* , 🍀 *Na d'aki(halud Al'oud)* *UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* 💃🏼💃🏼 🍀🍀🍀 *Suna bada d'aya Koh sare akan farashi Mai Rahusa* 🍀🍀🍀 *Suna bada order kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria* Contact them vie 🪀08028827241 or 09033791049 IG @umsadincense 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya* *Ibrahim* 🍃 ✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwa👌 free book 🤧 Page 4️⃣2️⃣&4️⃣3️⃣ Aishan ADARA ne kwance Bata motse, cikin sauri Al'ameen ya Isa gareta yana kuka,don zuwa yanzun sun fara sanin ciwon kansu daga shi har Salim in,rungumar mahaifiyar sa yayi Yana kuka,don Allah Mami karki tafi ki barmu mami karki tafi ki barmu wayyo mamin mu yace Yana fashewa da kuka Salim Kam tsabar tashin hankali ciwon sa ne ya tashi,da sauri likitoti suka Kira baban Aisha dake waje a zaune yazo ya fitar da Al'ameen shi Kuma Salim Nurse suka d'aukesa zuwa wani gadon. Sumayya dake kwance a kirjin Al'ameen kukane ya k'wace Mata hannu tasa ta Kara rungumar sa tana kuka,shikam gabaki d'aya jijiyoyin kansa sun mike sosai, kallo D'aya mutum zai Masa yasan ran maza ya tsogalu. Kafun ya Kara bude baki, ji kawai sukaye kuka na tashi a bakin kofar d'akin su da sauri Sumayya ta mike hade da kamo hannun Al'ameen suka fitoh wajen tare Khadija ce duke tana kuka fuskarta harta kumbura Alamu dai ta Dade tanayinsa kasa kasa sune dai basuji ba. Yaya Daman gidan ADARA ba dangin mahaifin mu bane? Shiyasa suka nuna Mana launin fata,khadija ke tambayar yayan ta Ah ah khadija ba saboda haka bane suke wulakanta mu dama can haka kaddarar Rayuwar mu take, kishare hawayen ki maza ki tafi gida Ni wallahih Yaya inason Jin karashin labarin mu don Allah Yaya kaga ba Wanda ya taba ban Tarihin iyayen mu kullum na tambaye ka Koh Goggo sai kuce mu Marayu ne. Al'ameen nada niyar magana Sumayya ta regasa"gaskiya ne khadija tayi girman da zata San abubuwanda suka shafeta especially irin wa'innan Tarihin" Shikenan naji ana Kiran azahar bara nayi sallah Kuma kuyi Inna dawo saimu d'aura daga inda na tsaya,yace Yana Mai laluben buta Da sauri Sumayya ta nufi butar dake zaune a Gefen baranda ta Mika Masa. Alwala sukayi Sumayya kudi ta baiwa Al'ameen 1k in zai shigo gida yasai musu doya soyayye a bakin titi na 500 Ba musu ya karba ya fita Bayan an idar da sallah Al'ameen doya yasai musu suka ci su ukun, duka a plate d'aya bayan Sumayya ta matsa musu don har lokacin khadija kuka take Kamar yau Abubuwan da suka shige ya faru. Khadija inkin San kuka zakiyi toh Zaki bar gidan nan Banga amfanin kina kuka Kuma kice na cigaba da baki labarin ba kije ki samu wani damuwanne Koh me? Al'ameen ya fad'a ransa a bace,don shima dauriyane kawai "Don Allah yayan khadija kayi Hakuri mutuwar iyaye Koh shikara d'arine zafine da shi" Kayi hakuri Yaya,khadija tace tana share hawayen ta Dukansu Basuci wani abin kirki ba Al'ameen Kam doya yanka biyu kawai yace khadija Kam ma tanaci Amai tayi saboda yanda take ajiyar zuciya Bayan sun wanke hannunsu Al'ameen ya cigaba........ Bayan mutuwar Aisha Alhaji ubangari yaso d'aukar su Al'ameen ya rike, Amma baban Aisha ya murza ido yace ba dashi ba Koh kudi ubangari ya baiwa su Al'ameen sai an mayar Masa da kayansa sosai abubuwa suka ma ubangari yawa don yanzun Koh fita zainab Bata iyyawa,tana fita ana nunata . Khadija Kam, kanwar Aisha aka bawa wance ta h Bata jima da haihuwa ba ta shayar da khadija, Amma khadija Taki karban nono Sam sai madara,ganin Amina Bata taba haihuwa ba yasa baba karban khadija ya Baiwa Amina Amana. Al'ameen sunyi matukar kewar iyayensu Wanda Salim yafi saka abin a ransa shiyasa kullum cikin ciwo yake don yanzun dai Al'ameen wani abokin babane ya ajesa a shagonsa Yana sayar Masa da kayan marmari duk Rana Yana biyansa,da wannan yake Tarawa su had'a da baba akai Salim asibiti Duk da wannan d'awainiyar Salim Bai hanasu karatu ba a hakan Alameda yake zuwa makarantan gwannati Dayake lokacin duniya sanyi kalau ba kamar yanzun ba da ake kashiwa makarantan gwannati kudi. Relationship insu da kamila ba abinda ya ragu kullum saiya rakata gida kafun ya nufi unguwan su sosai Abu kamar Wasa shakuwarsu ta Kara karfin sosai saidai kamila Bata taba zuwa unguwan dasu Al'ameen suka koma ba shine dai Mai zuwa gunta, Ubangari Kam zaman jalingo ya gagaresa don lafiyarsa Dana zainab sai a hankali don yanzun saita kwana ta wuni Bata cewa kome makarantar ma yanzun Bata zuwa sosai rayuwa ta musu kunci,ganin Halinda suke ciki, yasa matar ubangari Kiran Yan uwansa ta sanar dasu abinda ke faruwa, Aiko a yanda suka tarar da ubangari da zainab don har an dakatar dashi agun aiki ganin Halinda yake ciki yasa Yan uwansa Saida gidan da suke ciki suka tatttarasu dashi da yaran NASA suka koma garinsu,Daman aikine ya kawo ubangari jalingo, Wannan kenan. Khadija taci gaba da samun kulawa Awajen Amina Alhamdulillah yarinya ta fara girma ga wayo sai daifa Sam Bata da jiki Yar firet da ita kyakkyawa sosai don Kamar ta da Yusuf ne sak shiyasa ita da Al'ameen Koh baka sansuba ka gansu kaga jini d'aya Daman Salim ne baki a cikin su don da Aisha yake Kama. Zaman su a gidan Adara Bai sauya musu hali ba, da yake abin a jininsu yake sanyi Hali da hakuri Amma fa Salim akwai zuciya mundin aka Bata Masa Rai in fa baisamu ya Rama ba saiya kwanta ciwo. Bayan wasu shekaru mahaifin Aisha dai ya kwanta ciwon kafa Wanda Koh kofar gida baya iyya fita Sai an Taimaka masa, don haka Abubuwa sun ma Al'ameen yawa ga kudin maganin Salim ga D'an abinda yake D'an kaima Yar kanwarsa khadija ga zaman shago ga zuwa makaranta ga soyayyar kamila wanda yake jinta har ransa. Haka baban Aisha yayita fama da ciwo har Allah ya d'auke ransa Wanda kafun ya mutu Saida ya jaddada wa yaransa Koh bayan ransa Bai yarda Yusuf da Salim Subar gidan nan Adalilinsu ba d'akinsa da yake ya bar musu halak malak, baya cikin gado, Wannan shine kalmarsa ta karshe Kuma itace sukecin Albarkacinta har yanzun suna cikin gidan ADARA. Bayan mutuwar baban Aisha rayuwa fa ta zamo ma su Al'ameen wani iri Sam a gidan Adara Babu Mai taimaka musu Koda ta abinda zasuci ne,Dole tasa Salim shima ya fad'a Tashar marmari Yana ma wasu jiran Kaya suna biyansa,saisu had'a da kudin Al'ameen su fidda na asibiti su fidda na abinci su fidda Wanda zasu baiwa Amina ta rage d'awainiyar khadija,hakan yasa Al'ameen aje karatunsa don ko yaje makarantan baya fahimtar kome tsabar damuwa, Ganin ya aje karatunsa Salim ma yaki zuwa makaranta ba yanda baiyi dashi ba Amma yake ganin Al'ameen ya matsa Masa yasa sa cewa Al'ameen,Yaya moha Koh naje makaranta asaran kudi zakayi tayi Kaine yafi cancanta Kayi karatu Koh don kanwarmu ta samu rayuwa Mai inganci Jin Amsar da Salim ya basa Saida Hankali Al'ameen ya tashe cikin damuwa yace Masa,salim ban gane ba kana nufin Kai Babu Amfanin karatun nakane, ka sani Koh Kaine Mai rabon Tallafawa Khadijan? Ah ah Yaya Kaine ya dace Kaye karatu don Allah badon niba Yaya ka koma makaranta nikam bazanje ba karatun ya isheni haka ya karasa maganar da kuka Rungumar sa Al'ameen yaye shima sai yaji hawaye nabin fuskarsa don yanzun sosai sukayi wayo girma ya fara zuwa musu Kuma labarin abinda ya faru ya riskesu,sosai suka kullace zainab a ransu Kuma har abada bazasu manta da fuskarta ba. Haka ba yanda Al'ameen ya iyya ya koma makaranta don lokacin ma ya Shiga SSS class yayinda khadija ta Kai shiga primary school da Taimakon Goggo Amina aka sakata Soyayya Kam tsakanin kamila da Al'ameen tayi girma don har abin yakai ga iyayensu sunsan kome,don kamila Kam Amfara zama Yan Mata kowa yazo da sunan soyayya haka zata koresa itakam fa sai Al'ameen,sosai mahaifyarta ta tsani wannan mu'amalar Al'ameen da kamila ganin ba'a San Asalin ubansa ba haka zuriyan maman sa Yan Ta'adane,gashi baida wani kakkauran sana'a Koh inda zaisaka kamila,Amma haka kamila ta nace sai shi, duk yanda zata zugata Koh fad'a Mata abinda ya dace kamila bataji Bata gani itafa sai Al'ameen. Hakan yasa baban kamila Kiran Al'ameen don ya yaba da Tarbiyan sa ga nutsuwa, yace Masa zai basa kamila Amma ya dage yayi karatu in waec nashi yayi kyau,ya d'auki d'awainiyar karasunsa harya kammala shi Kuma ya Masa Alkawarin xai basa kamila. Jin hakan sosai muhammad ya Kara dagewa da neman na kansa da Kuma karatunsa don sosai yanzun yake son kamila Shekaru sunja lokaci ya tafi rayuwa nata juyawa yau Dadi gobe Akatsen sa,hakan take a wajen su Al'ameen Ranar 3/8/2009 ranar da Al'ameen bazai taba mantawa dashi ba,yau ne suka kammala waec nasu gabaki d'aya makaranta kowa ka gani farin ciki ne d'auke a fuskarsa wasu Kam har kukan rabuwa da juna suke, don irin Wannan ranane Inka rabu da wani har abada bazaka Kara ganinsa ba Haka take a wajen Al'ameen ranar farin cikinsa ne ya kammala karatunsa na secondary sai Kuma jiran result,farin cikinsa harda hawaye ganin yau ya Gama jarabawa Amma bayada Wanda zai zauna ya nuna Masa farin ciki Kamar yanda sauran daliban iyayensu ke Basu kyaututuka da walima na murnar Ranar A hankali yake tafiya jikinsa sanye da uniform na makaranta Yana tafiya Yana tunane tunane rayuwa don a lokacin sun girma shi yanada shekara 18 Salim 15 Khadija 6 Ji kawai yayi wata mota Tasha gabansa kafun ya Ankara ma har sun Wasa Masa wani abu Bai Kara tuna Koh sanin inda yake ba sai bayan sati D'aya D'aya bude ido ya jisa a asibiti Amma baya ganin kome sai duhu,Wanda yake zaune dashi shine Wanda ya tsintosa a bayan gari wajen kauyensu ya fitoh gona kenan yaga wasu sunzo sun yarda Al'ameen a cikin ciyaye,shine ya daukosa ya kawosa hospital da vajin jikin uniform NASA aka gane makarantarsu har labari yaje gidan Adara Amma Amina ne kawai da Salim suka zo asibitin Kuma suke kokarin jinyansa da taimakon mutumin da ya tsintosa, Al'ameen sosai ya Shiga damuwa Daya waye gari baya gani gashi Doctor's sunyi iyya binciken su Amma basuga ciwo ba shi Karan kansa Al'ameen bayajin kome a cikin idon nasa Haka tun Yana kuka harya sadakar ya karbe kaddararsa,bayan makantarsa abin mamaki Koh da kamila ta samu labari batazo Koh duba Al'ameen ba sai abokansa na makaranta dana unguwan sune sukazozzo don ganewa idanunsu shin da gaske ne labarin da sukaji Al'ameen ya makance shine da kansa Yakama Salim ya Masa jagora zuwa gidansu kamila Amma Koh ganinta basu samuyi ba duk abokansa yanzun basa son Koh zama waje d'aya tare dashi kowa gudunsa yake Bayan waec ya fitoh Salim ne ya karbo Masa result,ya samu 9credit sosai Al'ameen ya rungume result nasa a kirji Yana hawaye,yaci buri akan result nan yayi karatu har bacci bayayi,Ashe ba rabon zaiga abinda ya samu ma da idanunsa sai an duba an fad'a Masa. Rayuwa fa Tama su Al'ameen zafi don abinda zasuci ma ya zamo musu aiki sai salim ya fita ya nema kafun su samu gashi yanzun an sallame Al'ameen a shagon da yake zama don ganin baida ido duk yanda yaso su taimake sa zai iyya ciniki koda ba idone abin ya gagara Bayan wata D'aya da makantar Al'ameen yaje gidansu kamila yafi kafa goma Amma kullum sai ace Masa Batanan,Wasa Wasa jikin Salim ya Tashi don ba'a je ganin likita ba har wata ya wuce,ganin ciwo yaci karfin Salim ga bamai taimakonsu, yasa Al'ameen neman taimakon yaran unguwa suka kaisa asibiti Likita yace Masa wannan karon aiki za'a ma Salim gashe kudi masu yawane,sosai hankalinsa ya Tashi ga rashin ido gashi basuda abinda zasu Kama su sayar sai sarkanda mahaifinsa ya bar Masa Wanda shi kad'aine abinda yake gani a matsayen Abu Mai girma da muhimmaci a Rayuwansa Wanda zai buga kirji yace Awajen iyayensa ya gada,Amma baikai Dan uwansa ba muhimmaci ba. Haka ya d'auki sarkan yakai kasuwa don a Saya Amma masu sarka sukace bazasu Saya ba gudun karsu sayi abin sata bare sarka Mai shaki Kamar Wannan Basu taba ganin sarka Mai zubinsa ba Duk inda Al'ameen yasan zai samu a taimaka Masa yaje Amma babu Wanda yayi yunkurin taimakon sa har gidansu kamila yaje Amma Koh sauraron sa mahaifinta baiyi ba Karshe dai Koran su akayi a asibiti ganin Basu da Koh sisi kullum Kuma kudin gado karuwa yake,dawowar Salim gida ciwo ya Kara Tashi gadan gadan,haka Al'ameen yanaji Yana gani jikin Salim na tsanani Amma Babu yanda zaiyi haka yake fama ga rashin ido Yauma Kamar kullum suna kwance a d'akinsu Wanda kakansu ya mutu ya barmusu tun 1:00 na dare jikin Salim ya tashi ko rimtsawa Basu samu sunyi ba dukansu biyu Al'ameen na zaune Salim ya kwantar da kansa akan cinyar D'an uwansa sosai yake Aman jini Al'ameen Kam sai kuka yake Yana Kara tallafar Kan D'an uwansa Jin Aman da Salim keyi Yana karnin jini yasaka yatsansa ya lakuto Aman tsuntsunawa yayi tabbas jinine ba Wai ba, ai da gudu ya fita tsakar gidan Yana kuka Yana bubuga musu kofa Amma ba Wanda ya taimaka Masa Asalima zaginsa suke,insun bude kofar,da gudu yayi waje. gidan makwancinsu ya shiga Yana kuka ya ringa buga masu kofa,mutumin na budewa yaga Al'ameen ne,hakika yau yaji tausayin yaran da gudu ya Kama Al'ameen sukaye cikin gidan Jin Al'ameen nace Masa Salim na Aman jini Suna isowa zuwa lokacin salim kam jiki yayi tsamare sosai haka mutumin ya cicibesa Al'ameen na binsa a baya sai tuntube yake Yana buga kafarsa saboda rashin sandar jagora Koh D'an jagora A haka suka fitoh kofar gidan, aje Salim mutumin yayi yace bara ya d'auko machine su kaisa hospital Mutumin na shiga gidansa Salim ya ringa Kiran sunan Al'ameen Yana tari jini nabin Gefen bakinsa,Yaya Muhammad !!Yaya muhammad zuciya na, zuciya na na ciwo Yaya kamin fifita zafi nakeji a jikina Yaya bana ganinka Yaya zansha ruwa kishi nakeji gabaki d'aya Al'ameen ya rude iyya rudewa da gudu ya ruga yayi randar masallaci saboda rashin jagora, ya hadu da pol ji kake Gauu ya buga goshinsa jini ya balle Masa duk irin azabar da yaji hakan baisa ya kasa tashi ba haka ya mike a daddafe yayi randar masallaci dumbulo ruwa yayi Yana kuka Yana sauri ya karaso kusa da Salim tsungunawa yayi ya d'ago kansa jikinsa na rawa Jin Salim ya daina kakarin Amai gashi kansa yayi nauyi daker ya d'agasa ya d'aura akan cinyarsa lalubar bakin salim yayi ya kafa Masa mod'an Amma Ina ruwa baya tafiya sai bin Gefen bakin yake Yana zuba,dagajin haka Al'ameen ya k'wala Kara Yayi daidai da lokacin mutumin ya fitoh da machine da sauri ya karaso gunsu Jin ihun Al'ameen Yana zuwa cikin hanzari ya haska su idonsa ya sauka akan Salim kwance ido ya kafe a sama jiki a sake Wanda Koh ba'a fad'a ba yasan lokacin Salim ne yayi Innalilahih wainnailaihir rajuun kalmarda ta fitoh a bakinsa kenan Aiko Wannan kalmar ita ta Kara tabbatar wa Al'ameen lallai ya rasa kaninsa, a karo na uku Yana rasa mutanen da sukafi soyowa a ransa, farin cikinsa,duka a gabansa suka Amsa Kiran mahalincin su(Allah Kasa mu cika da imani,muyi kyakkyawan karshe) Ji kawai mutumin yayi Al'ameen ya Fad'i timmmmmm............. 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin,Koh kinsan mace sai da kamshi da gyara* 😉 🍀🍀🍀🍀 *Turare suna d'ayace Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin sa* 🍀🍀🍀🍀 *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da* *gyara* 🍀🍀🍀 *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace* 🍀🍀🍀 *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE* 🍀 *Na tsunguno(habil)* 🍀 *Na jiki (kwalaccam)* ( *khumra, black & white* ) 🍀 *Turaren turara jiki after birth* , 🍀 *Na d'aki(halud Al'oud)* *UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* 💃🏼💃🏼 🍀🍀🍀 *Suna bada d'aya Koh sare akan farashi Mai Rahusa* 🍀🍀🍀 *Suna bada order kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria* Contact them vie 🪀08028827241 or 09033791049 IG @umsadincense 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya* *Ibrahim* 🍃 ✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwa👌 free book 🤧 Page 4️⃣4️⃣&4️⃣5️⃣ Al'ameen ne ya yanke jiki ya Fad'i,sosai mutumin ya rikice yahau salati cikin kidema Hayaniyar sa shiya matashe samarin dake kwana a d'akunan kofar gida,Suma dai sosai mutuwar Salim ta shigesu ruwa aka watsawa Al'ameen Amma Ina Koh farfadowa baiyi ba Dole tasa wasu daga cikin matasan d'aukar sa zuwa asibiti Usman makwancinsu shiya d'auki gawar Salim zuwa gidansa Washe gari agidan malam Usman aka shirya salim. Al'ameen dake asibiti kam Yana farfadowa da asuba ya tashi hankalin kowa sai ya dawo ankai Salim tare dashi Haka aka kamasa g'wanin tausayi zuwa gidan malam usman,Yana shiga gida aka Kaisa Kan gawar D'an uwansa a hankali ya zauna Kan cafet in hannu yasa Yana lalube ya bude gawan jikinsa na bare yasa hannu ya shafa fuskar Dan uwansa murya na rawa hawaye nabin kuncinsa yake ma D'an uwansa Addu'a Salim sosai ya samu jama'a kamar me don duk wanda yasansa, kuma yaji mutuwarsa yazo,tare da Al'ameen aka kai D'an uwansa kabari. Bayan mutuwar Salim sosai kewa da kad'aici ke damun Al'ameen Koh bacci baya iyya wa saboda kewan D'an uwansa shikenan yanzun baida abokin Hira baida Wanda zai fad'awa damuwar sa baida Wanda zai kwana tare dashi sai Yar kanwarsa khadija ita Kuma mace ce Mai gidan Salim shiya bawa Al'ameen kudi Ya sari mangoro Koh a bakin kofar gidane ya fara saidawa don Bai dace Yana tsallake titi kullum zuwa kasuwa zaman shago ba Ba musu Al'ameen ya karbi kudin yad'an fara business dashi,Kuma Allah yasama abin Albarka Yana samun na abinci da biyawa Khadija D'an hidindimun makaranta Zancen kamila Kam baiyi fushi ba duk da Bata Masa ta'aziyar D'an uwansa ba haka ya sake Kama Khadija don lokacin ta d'anye wayo sukaje gidansu kamila. Kamila ce tsaye da kawayen ta a waje tare da wasu samari uku A bakin mota Al'ameen suna Isa kofar gidansu kamila,yaji hayaniyar maganar mutane Kamar harda ta kamila hakan yasa cikin murna yau dai zasu gana, tunda ya jima Yana zuwa baya samun ganin ta Da saurinsa yace wa Khadija suye wajen da Yake jin muryan mutane Ba musu Khadija na rike da sandar sa suka nufi wajen, Assalamu alaikum Waalaikumu salam D'aya daga cikin samarin ya Amsa Masa Ina wunin ku, Al'ameen ya gaidasu Lafiya samarin suka amsa d'ayan ya zare kudi a Aljuhunsa Yana mikawa Khadija,ungo Yan mata Khadija Kam kin karba tayi don bata Saba bara ba koma yayanta ya hanata roko Koh karban abin hannun Wanda Bata sani ba Karba Mana yarinya D'aya daga cikin kawayen kamila ta fad'a don Bata San Al'ameen ba Yayana ya hanani karban kudin Wanda ban sani ba, Khadija ta fad'a musu tana noke kafad'a Da mamaki samarin ke kallon su Al'ameen mutum ya fitoh bara abasa yace bazai karba ba,toh lfy meya kawo ku gun mu inba bara ba Am don Allah Ina da tambaya ne? Al'ameen yace Allah yasa mun sani Yauwa Kamar muryan kamila nakeji d'azun a cikin ku? Eh ganinan lfy?kamila ta basa Amsa Lafiya kamila in ba damuwa inason magana dake ne Ina jinka,tace tana Masa kallon banza Don Allah mu koma gefe Kai MAKAHO akan me zaku kebe da matar da Zan aura Kai asuwa d'aya daga cikin samarin yace Wani abune ya cake zuciyar Al'ameen shikenan kamilar ma ya rasata shikam yaushe zai samu farin ciki ne duk mai kokarin faranta Masa wata Rana gudu yake ya barsa Kamila aure zakiyi?yace Yana kokarin faduwa tsaban shock Eh aure zanyi Koh kana da matsala da hakan ne Kamila Ina Alkawarin mu? Alkawari kana nufin na aure ka kana MAKAHO Kuma talaka da wanne zanji da ciyar dakai Koh da ciyar da yaranka Koh da maka jakora Koh d'awainiya?Zan dai iyya auren ka a Talaka Amma banda kana MAKAHO kam. Sosai zuciyar Al'ameen ta tsinke Dariya matasan da Y'an Matan suka sake na shekeyanci,Kai kamila bakida mutunci wallahi 😒 soyayya ce fa saikuje kusha love da lalube D'aya daga cin Yan matan ta fad'a tana dariya Budurwar da ke gefe sanye da hijab itace kad'ai Bata ma Al'ameen tozarci ba Kama hannun Khadija taye hade tacewa Al'ameen su tafe A hankali Al'ameen ke tafiya Kamar k'wai ya fashe Masa a ciki Bai d'auka Koh nakasa zaisa kamila gudunsa ba Koda kowa zai gujesa Suna sharan kwanan nayin, kawar kamila ta dube Al'ameen,kaga bawan Allah don Allah Ina Mai rokon alfarma a gareka shine ka rabu da kamila Koda itace autar Mata ka barta duniyace ai Koda zata rabu dakai bada tuzarci Koh kushen halitta ba Amma ita Bata dube hakan ba y Ta wulakanta ka kaima ka barta bari na har Abada,Kaye hakuri Allah Yana tare da musu hakure. Insha Allah baiwar Allah na rabu da kamila Nima na hakura da ita Allah ya had'a kowa da rabonsa, Ameen ta basa amsa tana Mai komawa layinsu tabarsa tsaye da Khadija Wannan shine Ranar da Al'ameen ya fita a Rayuwan kamila. Bayan wasu shekaru karatu ya fara zama sai da kudi, a hakan yake ta faman ganin Khadija tayi karatu Koh ba kome zata tallah fawa kanta, Amma Ina kudi ya gagara don yanzun mangoron ma sai a hankali Bai wuce a Rana yayi cinikin 200 Koh kasa da hakan. Gashi a ciki Kuma yake ciwa cikinsa hakan yasa karatun Khadija tsayawa iyya Junior. *An dawo labari* ........... Khadija Kam kuka take kaman me,haka ma Sumayya Allah sarki Ashe haka rayuwar wa'innan bayin Allah yake, tasu kaddarar kenan,a cikin Yan watanni nan da mahaifinta ya juya mata baya taji kamar tafi kowa matsala,ashe itakam ma in an had'a kaddarar ta dana Muhammad nata ba kome bane tunda har tayi karatu ta tashi cikin kudi da lfyr ta Amma shifa ga maraici ga kuncin rayuwa da Talauci. D'aga ido tayi tana kallon Al'ameen dake zaune a kujera fuska tayi ja"yayan khadija baka bani lbrn auren mu ba"?ta tambaye sa Khadija tashi ki tafi kinji kukan ya isa haka, Al'ameen yace batare da ya amsawa Sumayya tambayar taba Mikewa Khadija tayi zata fita a d'akin cikin kuka abin g'wanin tausaye"Khadija"Sumayya ta Kira sunan ta Na'am Aunty "Khadija kiyi hakuri kome na rayuwan duniya Mai karewane Sannan Yana da iyyaka kinji"? Toh Aunty tace tana share hawayenta "Ki d'auki doyan nan ki tafi dashi gobe da safe sauki kawo mini ducuments naki kinji Khadija" Toh Aunty kawai tace tana d'auki laidan doyan ta fita "Yayan khadija na tambaye ka shine kaci no face" Sumayya nagaji wallahih ki barni nad'an huta Mana waima me zakiye da ducuments in Khadija ne? "Oho ba'a sani ba Ina maka magana kana tambaya ta Nima naki fad'an" Shuru ya Mata tare da lumshe idanunsa Itakam ganin ya Mata shuru tasan dai akwai abinda bayason fad'a matane,tashi taye a hankali ta Isa garesa faduwa tayi a kansa da gangan Washhhh yace yana gyara Mata kwanciya "Don Allah ka fad'amin Mana" Kinga Sumayya nifa banason na fad'a Miki abinda zaizo Yana d'aga Miki hankali. "Allah bazan d'aga hankalina ba kawai ka fad'a mini" Ok toh shikenan Amma sai da dare Zan fad'a Miki "Gaskiya Nina gaji da abinda kake minin nan wani irin sai dare Kuma Wannan ai Jan Raine" Banace Zan fad'a ba ki barni Mana zuwa Daren in ban fad'a Miki ba saiki Tuhume ni "Uhmm toh yanzun me zakayi"? Bacci,ya Amsa mata "Bacci a hakan"? Eh..... Tashi Sumayya tayi taje ta d'aura abincin dare ta barsa a d'akin Bayan fitarta sosai yake tunani akan ya fad'a matane Koh karya fad'a Mata karshe dai ya yanke shawaran ya fad'a matan kawai Bayan isha'i Sumayya ce da Al'ameen kwance akan gado Sumayya taye matashe da cinyar Al'ameen sunfi minutes 20 a haka,tunda sukaci abincin dare sukayi sallah, suke a haka Amma Al'ameen baice mata kome akan labarin ba abin sosai ya dame ta Amma ta danne tunda yace zai fad'a zata barsa ya fad'an da kansa. Sumayya!!ya Kira sunanta Yana Mai shafa gashin kanta mai tsawo da kamshi "Na'am"ta amsa Masa Sumayya banso fad'a Miki dalilin auren mu ga ganin cewa kece kikafi kowa sanin hakikanin gaskiya don bana tunanin har yanzun ana cikin zamanin da za'a ma mace aure batare da tasan miji Koh miji ya santa ba. "Me kake nufi"? Sumayya ta tambaye sa fuskar ta a hade Jin abinda yake fad'a Mata Yanzun masifa Zaki mini Koh Jin lbr zakiyi? "Aiba labarin kake bani ba sukata kake"Sumayya tace,tana kokarin sauka a gadon Sorry toh, yace Yana kamota "Nikam ka sake ni " Kin saketan yayi yana rungume da abarsa, naki sakin kin in kajimin mata fa "Allah ni ka sakeni nace maka"tace tana kokarin xame kanta a jikinsa Fushi kikayi ne Gimbiya? " waye Gimbiyar"? Sumayya mana. "Gimbiyar wa"? Al'ameen... Uhmmm kawai tace bata kara magana ba Kinga na miki Alkawari, zan fad'a miki gaskiyan abinda na sani akan auren mu? "Nima nafasa ji yau sai gobe"ta fad'a tana mai sa hannu ta d'auko wayarta dake gefen filo, airp inda ke makale a jikin wayar ta manna a kanne Sai magana yake baiji ta amsa masa ba hannu yasa yana tattaba ta, Gimbiya ina magana kin mini shuru Duk da sumayya taji Al'ameen ya taba ta Amma taki koh sauraransa Shikam gane fushi take yasa sa dagota sama daga jikinsa ya jefata gefen gadon Ihu sumayya ta sake bawai zafi taji ba don laushin katifar dana blanket bazai bari taji zafi ba tsorata kawai tayi don bata tsammaci hakan ba" wayyo wuyana ya karye" Nashiga uku sumayya inga wuyan da gaske kinji zafi dan Allah kiyi hakuri ban dauka zakiji zafi ba, yace yana matsowa kusa da ita Sumayya kam langobewa tayi wai wuya ya bugu"wayyo wuyata shikenan ya kasheni jama'i Don Allah kiyi shuru muga wuyan wallahi bada niya nayi ba Sumayya kam kara lafewa tayi jin ya cicibeta ya daura a cinya kamar wata baby Sannu sumayya koh muje asibiti ne? "Nidai goyona nakeso kayi"ta karasa maganar da make murya Jikinsa na rawa yace, toh... toh... hau, yana dukawa a kan gadon "Nika d'agani bazan iyya tashi zaune ba" Cicibar sumayya yayi ya goya haka ya ringa lalube yana zaga d'aki zuwa baranda da ita sai kusan 10:00 sumayya taji gyangyadi kafun tace masa, " ka kwantar da ni bacci nake ji" Ai da sauri bawan Allah yayi d'aki da ita da lalube ya shimfid'ata a gadon duk ya gama gajiya ba kad'an ba shiyasa daya samu taye bacci ba karamin dadi yaji ba gudun fitina ma koh tabata bayyi ba a gefe ya kwanta yanata tunanin wuyan sumayya don harga Allah ya d'auka da gaske ne Da asuba ma hakan take sashi tayi ya d'auketa har waje tayi alwala ya dawo da ita d'aki kafun ya tafi masallaci. Misalin karfe 9:12 na safe Al'ameen ne ke bacci a d'aki bayan dawowar sa sallan asuba Sumayya data gama aikinta a nitse tayi girki duka don bata tashesa ba saida ta gama harda wanka tayi kafun a Hankali tashigo d'akin wayanta ta d'auka ta danna play in waka ta kara volume, ta saka Eirps kunnen Al'ameen ta mannawa Ai kam yana cikin baccinsa yaji abu tibbbtibb ga waka kamar a kwakwalwarsa, da sauri ya mike zaune hade da furta, innalilahi sumayya wuyank........sai kuma yayi shuru jin dariyan sumayy a kusa dashi Hannu yasa sosai ya damkota kwantar da ita yayi a gefensa yahau kanta sosai yayi lamo yana daidaita bugun zuciyarsa har lokacin abin na kunnensa "Wayyo menene haka"? Shikam koh jinta bayayi, sai dad'a lumshe idonsa yake jin wakar da ke tashi a kunnensa sosai yatafi dashi Da sauri sumayya ta zare eirps in jin sai magana take baya kulata Da sauri ya bude ido, tare da kamo hannunta data cire masa abin kunnensa, mena cirewa? wakarfa bai kareba "Inata magana kamin banxa badole na cire ba" Toh mekike son na miki kenan guda daya? tunda jiya ma ai magana nake miki kika saka abinnan a kunnenki kika manna mini nima, duk wai akan maganar jiyanne kiketa fushi koh? Shuru sumayya tayi Dalilin auren mu....... nidai bazance Miki nasan kome akan auren mu ba illah dai bazan manta ba wata Rana wani mutum yazo ya sameni agun sana'a ta yasai Mangoro ya tafi bayan kwana biyu Kuma sai gashi ya dawo Amma baifita a motarsa ba aika yaro yayi ya kirani nakai masa mangoro bayan naje ne yace na Shiga motarsa, Yana da magana Dani,ni kuma naji tsoro gudun kar Amaimaita na baya(Randa aka makantar dashi) shiyasa naki Shiga motar duk yanda yayi Dani ki nayi,karshe dai agun mukayi magana,Kamar haka Ni sunana mamman Ina da yarinya Naga hankalinka da nutsuwarka shine nayi maka kwad'ayin Koh zaka Amince in baka auren ta? Sosai naji mamaki nida bana gani ad'auki yar Mai mota sukutum a bani gani Talaka haka kawai sainaji Raina Bai Kama zancen ba, shiyasa nace Masa bana bukata batare da Kuma sauraransa ba nayi tafiya ta Bayan sati D'aya kawai bappa sulaiman yakirani Wai za'a mini aure,sosai abin yaban mamaki za'a mini aure kuma kamar mace,bappa aure Kuma Kamar Yaya?na tambaye sa Kamar yanda kaji bappa sulaiman ya bani Amsa Duk Azana Yar gidan nan za'a bani Amma bappa yace Wai Yar shugaba family ne tunda naji haka kawai nasan lallai wannan aure mai dalili ne ba auren Angani anaso ba,da farko naso nunawa bappa illan auren nan Amma ya murza ido yace sai anyi daga karshe ma cemin Yaya Wai yarinyar tanada Wanda zata aura matsala aka samu bayan anyi test shine aka samu tana d'auke da c................ Compilied By Abubakar Saleh AlQuyraemey Whatsapp Number 08138873799 Visit www.rumbunlabarai.com For More Complete Documents 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin,Koh kinsan mace sai da kamshi da gyara* 😉 🍀🍀🍀🍀 *Turare suna d'ayace Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin sa* 🍀🍀🍀🍀 *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da* *gyara* 🍀🍀🍀 *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace* 🍀🍀🍀 *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE* 🍀 *Na tsunguno(habil)* 🍀 *Na jiki (kwalaccam)* ( *khumra, black & white* ) 🍀 *Turaren turara jiki after birth* , 🍀 *Na d'aki(halud Al'oud)* *UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* 💃🏼💃🏼 🍀🍀🍀 *Suna bada d'aya Koh sare akan farashi Mai Rahusa* 🍀🍀🍀 *Suna bada order kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria* Contact them vie 🪀08028827241 or 09033791049 IG @umsadincense 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya* *Ibrahim* 🍃 ✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwa👌 free book 🤧 Page 4⃣6⃣&4⃣7⃣ Wai yarinyar tana d'auke da ciki shiyasa sukeso na rufa musu asiri na aure ta Sosai nayi mamaki kuma zuciya ta takasa Aminta akan zancen cikine kawai ba, tunda yaran masu kudi da yawa suna cikin shege Amma ba'a bawa talakawa saini MAKAHO sam nakasa yarda. Dana matsawa bappa da tambaya ma cemin yayi koh naki koh naso sati mai zuwa d'aurin aure Harga Allah banso auren ba sam, don inaji a jikina ba batun ciki bane, imma cikin ne taya za'ayi a d'aura aure da ciki a jikin budurwan kenan, koh an zubar?karshe fa akafi karfine kafun sati d'aya ba wanda baisan zancen auren mu ba saidai sam ba wanda yasan dalili kuma duk wanda yaji batun auren saiya digawa auren ayar tambaya Amma ke sumayya menene dalilinki na aure na? "Auren ka, ina ma na sanka kajimin mutumi fa" ?ta fad'a cikin kuka sosai abin ya mata zafi watoh bayan auren kaskanci da akaso mata har b'atata akayi a wajen mijin don aga abinda yafi wanda suka sata😭muni Sumayya nifa tambaya kawai nayi kuma abinda nayita gujema kenan, kika ga nake gudun fad'a miki gaskiyar abinda na sani, ya karasa maganar da kara rungumarta jikinsa "Shikenan yanzun koh inada cikin sai ka yarda ka zauna dani" ? Indai har cikin babu a jikinki koda kin tabayene zan zauna dake a hakan ma naji dadi ai, na samu mata Kuka sumayya ta sake sakewa watoh duk zaman da suke da Al'ameen na kokonto ne tayi ciki koh batayi ba kai wai meta tsarewa dangin mahaifintane, na mahaifiyarta kamma bata sansu ba bare Kiyi shuru sumayya mundin bakece kika gaji da zama dani ba ni bazan taba juya miki baya ba a duniya, bayan khadija da ke sai goggo bayan ku banida mutanen da suke sona tsakani da Allah, ke kuma kin nuna mini tsantsar hallaci a rayuwa, don wata koh da gaske tayi ciki aka aura matani bazatayi hakurin zama dani ba bare ta taso cikin kudi yanzun kuma tana fama da rashi harsai ta nemi na kanta Da sauri sumayya ta rufe masa baki cikin kuka tace"karka kara fad'ar haka banaso nima a yanzun kaine kad'ai Garkuwa ta kaine bangon da zan jingina ya rikeni, insha Allah kome zai wuce kamar ba'ayi ba. Allah yasa toh yanzun ya maganar kamilar? "Bazan koya mata ba gaskiya kartazo tana shigewa mijina don yanzun kai ba tsaranta bane" Yanzun shikenan saboda ni saiki rasa makudan kudi haka? "Wani makudan kudi kuma bayan jiya ma na samu mutum uku da zasu fara zuwa, shiyasa yau zamu fita dakai muje bank zan bude Account maganar kudin koyar, shiyasa zan bude Account transfer zasu mini ta bank kuma yaran manya ne sosai fa, inaga anya ma bazan bude shago ba"? toh Allah ya bada sa'a, Amma banda maganar shago kam banyarda ba matar aure da shago kamar wata inyamura. "Ayya koh a shagunan kofar gida saina kama d'aya tunda bakin titi ne" Sumayya ban Amince ba, yace yana tashi akanta hade da karban eirps in hannunta ya mayar kunnensa kawai ya kwanta Ganin ya kwanta yasata tashi ta d'auko musu karyawa jejjerawa tayi, ganin bai sauko ba yasa a hankali tahau kan gadon agadon bayansa ta kwanta luf ta lumshe idanunta "breakfast is ready" Shuru taji bai amsa ba Amma dai yasa hannu ya tabata,hannun ta buge hade da cire masa abinda yasa a kunnen san ta makala a kunnenta wakar umar m shareef ke tashi a ciki Jin ta cire masa yasa sa mikewa da sauri ya Amshi abin a kunnenta, wakar dadi tamin don Allah ki maida mini, ya fad'a mata yana mai mika mata wayar hannun nasa jin wakar ta chanja Hhh"waikai kam anya ka taba saka eirps a kunnenka kuwa"?ta karasa maganar da sauka akan gadon Da sauri shima ya sauko had'e da cewa wallahi kamar kin sani inadai jin ana zancen sa Amma ni bantaba sawa ba ashe da dadi "Hhh toh zauna kaci abinci sai na baka bluetooth harda wa'azi da karatun qur'ani zakaji a ciki ba waka kawai ba" Menene bluetooth kuma, banda na waya? "Baka san ana posted a waya ba? toh ai yakamata kasan bluetooth da mp" Nasan mp mana, bluetooth ne bansani ba saina tura abu a waya inaji anacewa kai bude bluetooth naka na tura maka waka koh vedio. "Kayi kokari wannan kuma na yayi ne a kunne zaka makala ba tare da igiya kamar eirps ba ka gane" Eh na gane..yace yana zama Abincin sumayya ta zuba musu mika masa tayi bayan ta damka masa shukali a hannu, wai nikam me kika maidani ne? an gaya miki bazan iyya d'aukar shukalin bane? "Waya sani koh abincin ma saina fara baka" Kwafa yayi kawai ya fara ci Suna tsaka da karyawa sukaji sallamar khadija amsa mata sumayya tayi hade da bata izinin shigowa Khadija bataso shigaba ganin yayanta na d'akin, Amma ba yanda ta iyya haka ta shigo, ina kwana Aunty? "Lafiya khadija ya goggo"? Tana lafiya ina kwana yaya, tana maganar tana kokarin zama Lafiya khadija...ya Amsa mata " khadija matso muci" sumayya tace wa khadija Ah ah Aunty nagode, daman takarduna ne na kawo miki duka kamar yanda kika bukata. "Lallai ma khadija bansan yaushe zanna baki abu kisa hannu ki karba ba tare da kin mini filako ba"tace tana mikawa khadija plate na abincin data zuba mata sabo Ba musu khadija ta karba "Yayan khadija" Na'am sumayya.. Inaso zamu fita da khadija, zanje na sama mata makaranta tunda yanzun muna first time bazamu sha wahalar samun aji ba, Amma yakace ka Amince koh yaya" Sumayya bazance miki kume ba sai dai nace Allah ya biyaki, tabbas yau zaki cikamin d'aya daga cikin buru kana dana so cikawa amma kana naka Allah na nasa. Aunty makaranta zaki sani😳??khadija ta tambaya cikin zare ido fuska a washe "Insha Allah kanwata zaki shiga makaranta yau yau ma amma wani school kikeson shiga"? Koh wanne ma aunty nagode kin gama min kome arayuwa tunda zaki sani a makaranta bani da wani zabi koh wanne ki sani. Matsalata dake kenan khadija in mutum yace kaza sai kice kaza, yanzun ni in baki fad'amin makarantar da kike soba ina zansan makarantan da ya dace ki shiga" Nidai aunty na baki zabi "Shikenan bari yayanki ya zaba miki" Da sauri Al'ameen yace, nikam ba ruwana tsakanin ku nida ba idone dani ba ina nasan makarantu inba na gw'annati tada ba "Shikenan yanzun Art kikeso koh science"? Aunty science nakeso. "Shikenan sai muje GSSSJ ina ga makarantar tafi inganci a harkan science" Kai Aunty tsadane fa da school in kuma ga kudin registration mai yawa gashi wai sai anye Attitude test kafun abawa mutum gurbin karatu. Khadija kenan indai kin yarda da kanki Attitude test bazai baki tsoro ba maganan tsadan registration, kuma ai kyaunsa yasa kudin yayi yawa, duk da makarantar goverment ne"? Gaskiya ne sumayya kinsan koh lokacin mu ba makarantar da ta kaita inganci kyau da doka kuma sai wane da wane ne a ciki a kaf Taraba daga goverment har private Amma yanzun xamani ya chanja saidai a sata a lissafin goverment school mafi inganci "Yauwa bara na tashi in shirya kaima sai muje dakai yayan khadija zan bude account a bank da voter's card naka" Nikam gaskiya ba inda zani tunda khadija tazo da National ID card nata sai a bude miki babban Account kawai. "Kace kawai bazaka ba shikenan"sumayya tace tana mikewa,kaya ta fitar zata saka ganin haka yasa khadija fita a d'akin ta bata waje Nifa kawai zuwanne banji shiyasa nace kije da khadija "Toh zamuje daga nan saina wuce bank in, nama manta ban fad'a maka ba nayi posted na vedio n make-up da lalle harda photos yanzun haka next week za'ayi bikin yar kanwar Deputy Govnor an bani kwangilan musu lalle da make-up kawaye kawai da Amarya" Duk sunzo gidan nan?Al'ameen ya tambaya da mamaki "Ah ah a online fa muka gama kome har balance na fad'a musu yanzun ma jiran Amaryar take na tura mata account numbar na" Wow Allah abin godiya Amma dai sunan ki da suka ganine yasaka su baki aikin hala? "Wani irin suna kuma?toh ni ban ma saka sunana ba wani sunan na saka" Wani suna kenan? "Basai kaji ba" tace tana yafa gyalenda ta d'auko sai jaka da takalmi data rike a hannu zata fita a d'akin sai kuma ta sake juyowa ta kallesa jin tambayar da ya mata Sumayya baki bani bluetooth in ba? "Ikon Allah"tace hade da nufar cikin kayanta, Allah yasa ma tayi charge insa, makala masa tayi a kunne ta saita da wayanta," waka zan saka maka koh wa'azi"? Waka.... Wakar ta kunna masa"ga wajen da zaka taba ta gefe in zaka danna next koh back koh stop koh play"tana fad'a tana kama hannunsa tana nuna masa gun Eh na fahimta, saikin dawo "Allah yasa zanbi kasuwa duka me zan saya maka"? Kasuwa kuma sumayya? "Eh mana koh bakason naje? na saima khadija uniform ne da kuma d'an cefene nakeso na mana na sati uku kafun a fara azumi" Saikun dawo Allah ya kiyaye hanya "Ameen baka fad'a mini abinda zan sai maka ba" Am waken Gembu(Red beans)nakeso inkin iyya dafawa yanda suke innan asa tarugun Gembu(yellow pepper) da ice fish, irin dafin. "Hhhh eyeee kaima har kasan hadin dadi haka bansani ba" Allah inason abincin sosai... "Shikenan zan saya maka sai mun dawo" Allah yasa... Ameen, sumayya tace tana fita a d'aki, suka nufi kofar gidan da khadija Sunje makarantan kuma Alhamdulilah khadija ta samu gurbin karatu a makarantar science bayan interview da aka mata don an riga anyi Attitude test tun bayan sati uku, sun bawa khadija class, sumayya ta biya kudin kome atake aka mata registration aka bata su textbook, notebook , da tarkacen kayan makaranta su rigan sanyi rigan house socks vaji da sauran abubuwa Bayan sun bar makarantar yau kam duk wanda yaga khadija koh ba'a fad'a masa ba yasan tana cikin farin ciki sosai bank sukaje sumayya tasa aka budewa khadija Account . Kasuwa suka wuce tasai ma khadija uniform jaka da takalmi don sune kawai ba'a basu ba, a kasuwar ta baiwa tailor ya d'inka musu kala ukune jibi khadija zatazo ta karba Turare ta saima khadija da mayuka masu kyau sai Dutsen guga karami na wuta. Cefene tayi mai yawa sosai ta sai harda su drinks, doya, dankalin hausa, harda na turawa, vegetables, kai abubuwa sosai sumayya ta saiya saida kudin hannunta ya kare na machine kawai ya rage musu da d'an abinda baza'a rasa ba Bayan sun dawo gida da sallama, suka shiga gabaki d'aya dan dazon yan gidan suka bisu da ido ga kaya niki niki kamar masu kaura suka wuce suka shiga kofar ga yara na rirrike da laidodi Wa'alaikumus sallam, sannun ku da hanya Al'ameen yace yana cire hannunsa daga cikin kwanukan da yake wankewa "Yauwa yayan khadija" sumayya tace tana bin kofar da kallo ganin kayansu daya wanke ga randa a cike da ruwa Alamu dai jido yayi Yaran na sauke kayan sumayya 10 10 ta basu da murna suka karba kowa na jin dadi suka fita Sallah khadija da sumayya sukayi kafun suka baje cefenen suna dubawa, khadija kam ganin yanda sumayya ta loda mata kayan sayayyanta a gabanta kuka kawai ta sake tana rungumar sumayya,yanzun aunty duka wannan nawane? yaya kaga kayan kuwa wai duka nawa😅, tana fad'a tana kamo hannun yayanta ta d'aura akan damin kayayyakin abin ma abin dariya da tausayi Shima karan kansa Al'ameen yayi mamakin kayan, sumayya abubuwan nan basuyi yawa ba kinje kin kashe kudi da yawa haka sumayya kina ga ba aiki nake fita ba bazaki tattala kudinki ba sai kina fashaka haka. "Allah zai kawo kuma maganar baka aiki bazai hana nayi walwala ba kaima insha Allah kafun d'aya ga azumi zaka daina zaman gidan nan" Allah yasa Amma dai sumayya kayan yayi yawa Babu wani yawa yar fa makaranta ce sai da guga da wanki da gyara, kema khadija duk safiya kina zuwa kafun ki tafi makaranta kizo ki karya,ki karbi kudin tara dana keke kinsan sunce sai 2 ake tashi kuma ana dukan letti Toh Aunty amma zanna karyawa a gida saina zo na karbi na kudin. "Shikenan monday zaki fara zuwa jibi, kije ki karbi uniform in ki gobe ki goge, gata sai school"😃 Hhh hakane Aunty in tafi da kayan naje na nunawa goggo kona barshi Anan? "Ai yanzun kayanki ne ki tafi dashi" Toh aunty tace tana rungumar kayanta ta fita Khadija na tsananin farin ciki yau wanda rabon dana gansa har na manta, Al'ameen ya fad'a yana lalubar hannun sumayya ya kama "Insha Allah zaka yita ganin sa yanzun harka gaji" Allah yasa, kema Allah ya biyaki "Ameen, na sai maka waken Amma na gaji gaskiya bazan iyya dafawa yanzun ba kasan sa da wahalar nuna" Shikenan sumayya Allah ya kaimu goben "Ameen", tace tana d'aukar wayanta dake neman agaji"Assalamu Alaikum" Shuru tad'anyi sai kuma yaji tace "toh bara na tura miki ta WhatsApp" "Ok shikenan", tace tana aje wayan "Kasan waya kira"? Ah ah ... "Yar kanwar deputy ne waina tura account number" Toh Allah ya bada sa'a Ameen, bara na tura musu Tashi Al'ameen kam yayi yaje ya cigaba da wanke wanken sa sumayya kam Account numbar ta tura musu koh minutes 10 ba'ayi ba taji Alert kudine ya shigo account in khadija dayake da layinta aka bude account in..... Khadija kam na fita a gidan yayanta da kaya niki niki sai sauri take kamar zata fad'i damuwarta kawai taga ta isa gida ta nunawa goggo abin Alkhari data samu, bata hankalta ba tazo tsallaka titi koh ganin gabanta batayi, ji kawai tayi jama'a na illalilahi keeee kalli gabanki Ai jiii kawai kake kiiiiiiiiiiiii kauuuuuuuuu............. 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin,Koh kinsan mace sai da kamshi da gyara* 😉 🍀🍀🍀🍀 *Turare suna d'ayace Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin sa* 🍀🍀🍀🍀 *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da* *gyara* 🍀🍀🍀 *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace* 🍀🍀🍀 *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE* 🍀 *Na tsunguno(habil)* 🍀 *Na jiki (kwalaccam)* ( *khumra, black & white* ) 🍀 *Turaren turara jiki after birth* , 🍀 *Na d'aki(halud Al'oud)* *UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* 💃🏼💃🏼 🍀🍀🍀 *Suna bada d'aya Koh sare akan farashi Mai Rahusa* 🍀🍀🍀 *Suna bada order kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria* Contact them vie 🪀08028827241 or 09033791049 IG @umsadincense 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya* *Ibrahim* 🍃 ✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwa👌 free book 🤧 Page 4⃣8⃣&4⃣9⃣ Da karfi khadija ta watsar da kayan hannunta tsungunawa tayi jikinta na bari ta kama kai, gabaki d'aya ta gama sadakar wa yaukam sai Ta Allah Cikin zafin nama da haushi mai motar ya fitoh da fad'a fad'a,kee wace irin wawuyace wai kina tafiya koh ganin gabanki bakyayi da yanzun na kadeki fa baki jawo mini matsala ba gashi yanzun kinsa na buge keke napep innan da sai dai me zan buge? nosense kawai stupid Khadija kam har yanzun bata dawo daidai ba ga kuma tsawar da ake buga mata, d'aga kanta tayi tana kallon mutumin don Allah kayi hakuri wallahi bangan ka bane Da mamaki mutumin ke kallon ta sai kuma yayi murmushi, ke bakece kanwar Al'ameen ba? Eh.....eh..nice Murmushi kawai yayi hade da dukawa a tsakar titin yana tattara mata kayanta,saiki taso ai inba so kike wani motar tabi ta kanki ba Khadija kam cikin had'a fuska don sai yanzun takejin haushin zagin da ya mata, mikewa kawai tayi ta koma gefen titin Kizo ki shiga mota na kaiki gida? Bazan hauba, kuma ka bani kayana nikam. Kinji haushine khadija? Da mamaki take kallonsa toh a ina ya santa gashi itama tun d'azun sai tunanin inda tasan wannan fuskar take Ke yar Kauye bar kallona Naki dainawa kuma miko mini kayana, ta karasa maganar da kai hannu zata karbi laidodinta Da sauri ya kauce hade da cewa, ke khadija nifa yau gidan yayanki zaki kaini yau kusan wata biyu ina sintiri a sintali kowa na tambaya Al'ameen mijin sumayya sai ace ba'a gane saba yau ma Allah ne yasa zamu hadu shiyasa na biyo ta bakin kasuwa. Aikuwa bazan nuna maka ba, ba zagina kake ba Yi hakuri haushi naji Shiyasa yanzun muje ki nuna mini gidan yayan naki Gaskiya ni yanzun gida zan koma ba gidan yaya ba sauri nake iyeee nace ki nunamin gidan da nafi wata biyu ina nema shine zaki wanice kina sauri Kaga malam ni yanzun ma haka gidan na fitoh gaskiya bazan koma ba saidai nama kwatance Toh shikenan yi mini, kuma ga kayanki karki shiga motar inkin ga dama Oho maka dai, inka tsallaka titin nan sai ka mike kaga lungun shan kana shiga zakaga babban titi da yayi barade ka tambaye masu shagunan wajen, gidan Adara za'a nuna maka saika aike yaro kofar MAKAHO Ok toh shikenan naji, yace yana komawa wajen mai keken biyansa yayi asaran da ya masa, ya shiga motarsa yaja Khadija kam da ido ta bisa ta kasa tuna inda tasan bawan Allah nan Amma tabbas akwai inda ta sansa. ************** "Yayan khadija gaskiya nifa yau bazanyi girki ba wallahi na gaji wanka zanyi na kwanta " Kidaiyi wanka amma banda kwanciya kinsan bakyau bacci bayan la'asar koh? "Gaskiya ne amma dai zan d'an taba kafun goshin mangariba saika tashe ni" In ance abu ba kyau sumayya ki gujesa don Allah kidai kwantan koh waya koh TV ki kallah Amma banda bacci kam. "Toh shikenan akwai kudi a purse nawa anjima ka sayo mana abinci" Ah ah zan dafa... "Zaka dafa kuma yayan khadija, kaji mini kaudi"🤕 Nine mai kaudi?😳 "Eh man in ba kaudi ba ina kai ina girki, salon kaje ka kone koh ka yanke ba" Amma dai wallahi sumayya kin gama raina mini wayo me kika maidani ne wai? "Sorry toh me zaka iyya girkawa" Oho..... "Yi hakuri mana wasa fa nake maka" Ba wani, ya karasa maganar yana zama a bakin dakalin "Banace kayi hakuri ba, habba danejo Am heedee Am buddi Am yafannam lee"ta karasa wakar da kamo hannunsa ta nufi kitchen in dashi Kinga sakeni nafa fasa girkin bara kiji karma ki kama mini wani waka wai ma tsaya ke bafulatana ne daman? "Bororoje ce ba bafulatana ba, kuma girki sai kayi ehen" Ke wai ana girkin dole ne? "Yau sai kayi ai duk wanda yayi niyar aikin lada sayya karasa" Toh nace na fasa koh "Nikuma nace sai kayi" ta karasa maganar da dokarasa akan kujeran kitchen in Kin zama yayi inta dosana sa saiya cije"wai kai kam menene haka kasan Allah yau saikayi girkin nan" Zama yayi ba yanda ya iyya "Me ka iyya girkawa"? Me kikeso na girka miki? "Iyeee lallai ma watoh am bani zabi kenan irin ga k'wareren nan" Eh fad'a mini me zan girka miki? "Waken gembun jiyan nan zaka girka" Ah ah gaskiya banda shi don nidai ban iyya ba, don ni ba d'an gembu bane. "Hhhhh bakar magana koh"? Kema Aishi kika fad'amin "Shikenan yanzun me ka iyya dafawa maganar gaskiya nafa gaji da tsayuwa kwanciya nake son nayi fa" Doya na iyya soyawa da indomie, kwai, harda taliya dafa duka sai Tie "Doya Da k'wai ka iyya soyawa ko daban daban"? Soyayyen doya,kwai ma soyawa na iyya, da dafawa "Ok sai ka soya mana doyan da salt daban saika soya kwai shima daban akwai yaji a roba ka hada mana da ruwan bunu" Sannu hajiya,😒 yace yana kokarin lalubar bojuwa(tukunya) "Waye hajiyan kadaiji dashi"bojuwan sumayya ta wanke ta d'aura akan hot plate tasa masa mai Amma bata kunna ba Albasa ta yanka a ciki, doya ta d'auko da kwai tarugu Albasa lawashi maggi gishiri ta aje masa a kusa dashi koh wanne a roba koh tire koh gwangwa ninsa ruwa ta iba a boket tasa kofi ta aje masa duka don ya huta da tashi koma ransa innan" ga kome a zaune Allah yasa yayi dadi"tace tana fita a kitchen in Baiyi magana ba kawai wuka ya d'auka yafara feran doyan Ruwa sumayya ta iba tayi wanka kaya tasa ta kwanta duk da Al'ameen ya hanata amma baccin tuni ya sace ta Al'ameen na tsaka da feran doya yaji salaman yaro, amsa masa yayi Wai ana sallama da MAKAHO Inji wa? Nima ban sansa ba yace dai in masa sallama dakai Ok kaje kace masa ina zuwa Toh, yace yana fita a kofar Tashi Al'ameen yayi ya wanke hannun sa ya shiga d'akin, sumayya!ya kira sunanta jin shuru bata amsa ba sai numfashin ta dake sauka akai akai, girgiza kai kawai yayi ya d'auki sabon riga da wando da sumayya ta sai masa ya saka ya cire 3quiter dake jikinsa, waje ya fita yana mamakin waye yazo gunsa yau haka Waje ya fita yana tattaba jikin ginin kofar gidan don jin ina mai sallama dashin ya tsaya jin baiji motsen saba ya sakasa, kara maimaita sallamar Wa'alaikumu salam Al'ameen Laiiiiii wana kejin muryarsa kamar Ammar? Baka mantani ba Al'ameen ka rike sunana baka manta ba. Habba Ammar wanda ya maka hallaci irin wanda kamin ai ba mutumin da zaka manta dashi bane Hakane Ya mai jikin? Da sauki sosai Ammar, ya aiki ya gida? Lafiya kasan yau kusan wata biyu da dawowa na ina zuwa unguwan nan ban gane kaba wallahi har Hospital in na koma sukace ai an mata tiyata ma har an sallame ku tuntuni Eh kam satin mu d'aya aka sallame muma tuni. Allah sarki yamai jikin toh? Da sauki fa sosai kamar ma ba'a taba yanka taba, na barka a tsaye muje bakin dakali Ok toh in ba damuwa naga dakalin da rana kazo mu shiga cikin mota mana? Tsakake Al'ameen yayi yana nazari kutt anya zai yarda ya shiga motar mutun da bai sansa ba(lokacin da ya taimake ka ka sansa ne) Am daman ina d'an aikine a gida nama manta na d'aura tukunya Murmushi Ammar yayi watoh har yanzun Al'ameen bai yarda dashi ba kenan, toh ba kome nima bara na wuce naga yamma tayi sai na sake zuwa Toh shikenan nagode da ziyara Ammar Toh aje a cigaba da aiki mijin hajiya hhhhh Hhh Ammar kenan, ya fad'a yana mikama Ammar hannu sukayi musabaha a karo na biyu Bayan tafiyar Ammar cikin gida Al'ameen ya wuce yana tunane tunane sai kuma yaji bai kyauta ba da Ammar nason cutar dashi da randa ya d'auke sa da sumayya ya cuce su, ta wani bangaren kuma sai yaji gwara masa hakan babu ruwansa da mutanen duniya sai mutunci yanzun bai yarda da kowa ba haka zalika tsoron shiga mota ne dashi tunda masu mota suka makantar dashi, kauda tunanin yayi ya cigaba da aikinsa, daya ya gama fere doyan ya zuba a roba wankewa yayi ya tsame a kwando ya zuba gishiri kunna hot plate in yayi ya kama Aiki. Bayan kammala girkin Al'ameen juyewa yayi a kula ruwan shayi koma a flask wanka yayi yashiga d'akin, har lokacin sumayya bacci take, hawa yayi kan gadon a hankali ya kamota d'agata yayi cak yayi waje da ita ajeta yayi a kan dakali Ido sumayya ta ware jinta a sama kafun ma ta gama nazartar inda take taji an ajeta a dakali"menene haka"? Mangariba ake kira baccin ya isa haka, watoh bakiji bakisan baccin mangariba akwai matsala bako "Baccin kwasheni yayi ai" Sai kiyi Alwala nikam na tafi masallaci, bai saurare abinda zatace ba ya fita abinsa Itama samayya Alwala tayi ta shiga d'aki... Bayan sallan isha Al'ameen ne ya shigo kofar su, kitchen ya wuce ya d'auko kulan da 🍽 ya shige d'aki Sumayya dake kwance fuskarta sanye da glass ta d'aura system inta akan cikinta tana daddan nawa,d'ago kanta dake kan fillo tayi tana bin Al'ameen da kallo ganinsa d'auke da kula sosai tayi mamaki matuka, don ita harma ta manta da zancen zaiyi girki" ikon Allah wai da gaske kake kayi girki"? Idanunki zai nuna miki, yana magana yana fita a d'akin bayan ya aje kulan hannun sa da plate da shukula, sai kuma gashi ya dawo dauke da flask da cups, ajewa yayi a hankali akan cafet ya zuzzuba doyan da kwai sai yaji a gefen plate ya tsiyaye tie a kofuna Itakam sumayya sai ido kalala take kallonsa dashi"wai duk wannan kaika soya"? Eh man bakin raina ni ba an gaya miki in mutum baida ido shikenan sai akace bazai iyya abinda masu ido keyi ba, ai harma yafi namasu ido muna iyyawa "Ah ah kwadai kwatanta Amma badai yafi ba malam" Au karya zan miki kenan? "Bance ba,ina nawa doyan naga ka zuba plate d'aya"? Eh namu ne yau tare zamuci a plate d'aya Sumayya batayi magana ba sauka kawai tayi akan kujeran hannu kawai tasa ta fara cin doyan " kai maggi yayi yawa" Kiji tsorin Allah fa sumayya "Toh da tsoron ka zanji" Amma dai k'wan nan babu maggin da yaji inba sharri ba "Nikam naji, k'wan maggi ga Albasa doyan kuma bai soyu ba, tie in kuma sugar baiji ba"😕 Hannu yasa ya d'auke plate in gabanta da cup in tie in ya rike a hannunsa "Yaya haka kuma"? Ki miko mini kudi inje in sai miki abinci amma badai wannan zakici ba kowa ma ya hakura Almajiri zan kira na bawa, karasa maganar yayi yana shirin fita a d'akin Da sauri sumayya ta biyosa hade da kamo rigansa"dan Allah yayan khadija ka aje abincin mana waikai bakasan wasa bane?wasa fa nake maka" Wasa koh?toh ni da gaske nake kuma sakar min riga karki yaga "Habba don Allah yaga riga sai kace wata mai farashunan mayu" Toh waya sani "Yasan me"? Sakarmin riga hajiya "Ayya ka bani abincin mana wallahi wasa nake doya yayi d'adi haka tie ma k'wai innan inda kasan dafin Turai" Mika mata plate in yayi shima ya koma ya zauna abinci suka cigaba daci Bayan sun kammala ci yaukam ita ta d'auki kwanuka, bayan ta kaisu waje brush tayi shikam Aswakin sa ya d'auka ya goge bakinsa d'akin suka koma kayan bacci sumayya ta saka rigane da wando cotton mai laushi da socks na sanyi a kafarta, jin an fara yayyafi yasa Al'ameen fita waje ya tattare musu ruwa shima kayan baccin sa da sumayya ta sai masa ya yasa Sumayya gado tahau iyafis ta d'auka ta jona da wayan ta ta manna a kunne tana kallon film a ciki Shima bayan ya gama shiryawa d'akin ya rufe ya hau kan gadon, tattaba kan gadon yake har yaji ya tabota kwanciya yayi kusa da ita yasa hannu ya zame hular kanta Hannu tasa ta cire kunne d'ayan ta makala masa a kunne Kwanciya yayi akan filon da take gabaki d'aya ya nutsu yana sauraron abinda ke kunnensa, sai kuma yasa hannu ya taba sumayya hade da kiranta, sumayya! "Na'am" Uhmm Amma wannan indi'an film ne koh? "Eh..ya akayi ka gane"? Muryansu mana duk da Turanci suke magana amma dai sai kiji suna maganar sari koh bauta "Gaskiya ne kasan sunan film in"? Ah ah "this is fate, watoh kaddarar Rayuwa na Arewa 24" Oh film in karam koh? "Eh shine ma ke magana yanzun" Ai da sauri ya zare abin kunnesa tare da sa hannu ya zare na sumayya, kinsan Allah bazaki kalli film innan ba "Ikon Allah akam me bazan kalla ba"? Nidai kawai bazaki kalla bane. "Toh me kakeso na gani"? Wani film banda wannan "Uhmm nikam gaskiya shi nakeson kallo" tace hade da karban abinta ta mayar kunne Da sauri ya fizgo abin gabaki d'aya ya had'a da system in yana kokarin sauka akan gadon Da sauri sumayya ta cakumosa baya hade da kokarin karban system in Duk yanda taso kwatar abinta abin yaci tura duk inda tayi saiya zillar da hannunsa karshe ma hakura tayi takoma gefe tana maida numfashi Tashi yayi jin ta kwanta, zuwa yayi ya aje system in akan kujera, ya dawo ya kwanta abinsa Ganin ya aje yasa ta saurin mikewa zaune cikin azarbabi take kokarin sauka ta gefen kadon a hankali, tana sauka saboda matsen d'akin yasa dole saita biyo ta bangarensa kafun taje kan kujera, a hankali take tafiya Shikam tun tashinta zaune da saukarta duk a kunnensa shuru kawai yayi yana son ganin gudun ruwanta Tazo daidai dashi har zata gifta a bazata kawai taji ya fisgota baya ta fad'a kansa Kokarin tashi take, ya sake maidata, wai sumayya meyasa ne bakijin bari sam "Me nayi kuma"? Yanzun ina zaki? "Waje zan fita" Me zakiyi a wajen? "Fitsari mana koh an hana fitane in aka kulle kofa" Jin amsar da ta basa ya saka hannu ya mannata da jikinsa sosai kamar zai maidata ciki Karan shagwaba ta sake da karfi"wayyo" Ke menene haka saikin tara mini jama'ane "Toh ba kaine ka matseni ba" Toh ai ke ince bakiji koh kad'an kannan naki taurine dashi fa Eh naji kaina taurine dashi kuma ni ka sakeni fit......... Bai bari ta karasa ba kawai ya manna bakinsa da nata sosai yake kissing inta yana dad'a matsota garesa kamar zai maidata ciki A hankali tasa hannu ta kama kansa da karfi ta danke gashin kansa masu yawa sosai, hade da ajiyar zuciya Washhh ashhh kawai Al'ameen yace bayan ya zame bakinsa a nata, hannu yasa ya kamo hannunta data rike masa gashi ya d'aura a kirjinsa, da sauri ya maida bakinsa cikin nata Sosai yau sumayya da Al'ameen suka farantawa junansu duk da tafiya tayi nisa sumayya ta copsa Shi kuma Al'ameen tsoro. *RANAN MONDAY* Yaune fa hajiya khadin Goggo zata makaranta jiya koh baccin kirki bata iyya ba, da sassafe ta tashi tayi wanke wanke shara kafun 6:00 har tayi wanka dumamen da goggo ta duma shi taci, uniform nata tasa fari kal wando da hijab harda riga duka farare ne socks ta saka fari ta d'aura bakin d'an kwali(kallabi)ta zura hijab, sandal inta da Aunty ta tasai mata kala biyu d'aya 👟 ne d'aya sandal, 👟in ta d'auka bakine shima don a dokar makarantar baki da fari suke so, tasa a kafarta sai agogo shima baki turare ta fisa fuskar nan washe kamar gonan Auduga takema goggo sallama hade da d'aukar school back nata shima baki mai kyau, ta fita a gidan Sumayya da Al'ameen ne a kitchen suna girkin karyawa kamar kullum yauma hakan take watoh ana aiki ana fad'a Assalamu Alaikum "Wa'alaikumus sallam, yan makaranta" Kai Aunty ina kwana? "Lafiya khadija harkin shirya gaskiya ne Allah yasa hakan ya d'aure banda littin" Ameen Aunty, ina kwana yaya? Lafiya khadija harkin shirya? Eh yaya na shirya D'aki sumayya ta shiga naira 200 ta d'auko sai drinks d'aya da goran faro d'aya ta fitoh "ungo khadija wannan kudi yayanki ne ya bada na baki koda zaki zo ya fita ashe da rabon zaku hadu ma kihau keke sauran d'arin saiki rike a hannunki ga wannan kuma kisa a school back naki kinji, banda kawayen banza banda abota da maza kinga makaranta ne da Christian sukafi yawa sosai kuma benchi d'aya ake had'a maza da mata don haka babu ruwan ki da yaran Christian abinda ya kaiki shi zakiyi kinji ki maida hankalin ki akan abinda ya kaiki Allah ya tsare mana ke" Hannu khadija tasa ta karbi kudin da drinks in hade dama sumayya godiya, yaya na tafi Al'ameen kam ya rasa ma me zaice da sumayya sumayya Alkhari ce garesa matar rufin asiri, toh khadija saikin dawo kindaiji abinda Auntin ki tace miki koh? Eh yaya.. Adawo lfy Bayan fitar khadija sumayya kam kitchen ta koma taci gaba da aikin ta Al'ameen na tayata Assalamu Alaikum "Wa'alaikumu salam" sumayya ta amsa tana fita a cikin kitchen in da sauri jin muryar wance ke sallamar Aiko itace da mamaki sumayya ta bita da kallo, Al'ameen ma da sauri ya fitoh a kitchen in jin muryar me sallamar "Lafiya" sumayya ta tambaye ta Eh lafiya daman n................ 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin,Koh kinsan mace sayanzunshi da gyara* 😉 🍀🍀🍀🍀 *Turare suna d'ayace Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin sa* 🍀🍀🍀🍀 *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da* *gyara* 🍀🍀🍀 *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace* 🍀🍀🍀 *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE* 🍀 *Na tsunguno(habil)* 🍀 *Na jiki (kwalaccam)* ( *khumra, black & white* ) 🍀 *Turaren turara jiki after birth* , 🍀 *Na d'aki(halud Al'oud)* *UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* 💃🏼💃🏼 🍀🍀🍀 *Suna bada d'aya Koh sare akan farashi Mai Rahusa* 🍀🍀🍀 *Suna bada order kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria* Contact them vie 🪀08028827241 or 09033791049 IG @umsadincense 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya* *Ibrahim* 🍃 ✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwa👌 free book 🤧 *HAPPY INDEPENDENT DAY* 🇳🇬 Page5⃣0⃣&5⃣1⃣ Lafiya daman nazo akan maganar make-up inne, naji shuru baki kirani ba inna kira ba'a picking call in. "Ok toh ai na zaci koh kina da fahimta ne, ki gane me nake nufi" Kamar ya sumayya ban gane ba? "Ok toh kamila bara na miki gwari gwari, bazan koyar ba" Akan me? bayan kince sai mijinki ya yarda kuma a gabanki yace ya Amince. "Eh ya amince nima haka yace mini sai dai ni ban Amince dake ba har kizo gidana kina kare mini tanadi" Kamar ya bangane ba me kike nufi?zanzo gidan ki in kare miki tanadi?ina ma gidan yake bare "Hhhhh hayyeeee nanayeeee ashe gidan ba yanda yake akazo cin moriyan masu shi" Ke sumayya nafiki rashin mutunci don naga baki dashi ya daga abin Arziki sai tsiya ya biyo baya matsalanka da matsiyaci kenan bai gaji arziki ba "Ehhhhhh yariya tsiyama waje ya samu ki kalleni da kyau daga ni har mijina kinga Alamun yunwa a tare damu, kuma ki kallen sama da kasa koh uwar ubanki bataci arzikin da naci ba harta mutu ke uwarki data aure ubanki har yanzun bataci arzikin danake ciba. A'uzu sumayya wani rin , zagine haka kar in sake jin kin tanka mata shige ki wuce d'aki, don Allah kamila kiyi hakuri Kutt ni kike xagi? ai kamila super tayi da jakarta tayo kan sumayya da mugun sauri "Sumayya da gudu tayi kitchen tabarya ta rarumo ta rike"don uwarki kizo yau saina rusa miki kai shegeya harni zakima bariki kizo mini da yaudara da sunan koyan kwalliya" Ai da sauri kamila taja birki, in ba tsoro ba ki aje abinda ke hannunki yau saina nuna miki true colour na. "Shegeya akan me zan aje nasan dame kikazo kizo kima mijina asara a banza " Shammatar sumayya kamila tayi tana magana, da sauri tayi kanta gadan gadan da kwalba a hannu Ai ji kawai tayi Al'ameeen ya hankad'ata gefe, don duk abinda suke hankalinsa na kansu, keee kamila kin isa kizo har gida kice zaki bugarmin mata kimin asara akan me? Ke kin kini na samu mai zama dani shine zaki bugeta Wayyyo nashiga uku na lalace wayyo hannu na innalilahih kun kasheni, kamila ke ihun nan tana rike da hannunta wanda Acid ya zube mata akai "Subahanallah daman abinda kike da niyar watsa mini kenan Algunguma shegeya, aikokin watsa min bashine yake nufin karewar auren mu ba tunda ba idone dashi ba bare yaga yanda na koma" Sumayya meke faruwa ne haka meya sami hannun nata naji kina cewa zata zuba miki Kamila kam ihu take kamar ranta zai fita Ihun kamila shiya jawo da hankalin jama'ar gidan kofar su Al'ameen, da sauri daga maza har mata yara da manya suka nufi kofar donjin ba'asi "Ruwan Acid tayi niyar watsa mini Allah yasa ka shureta shine ya zube a hannunta hannun sai d'ayewa yake" Subahanallah Al'ameen yace yana nufar inda kamila take, kee kamila tashi muje asibiti tashi tashi yau an bonu Kaiii karka kuskura ka taba ta kaji na fad'a maka, keee Kinsan su waye a gidan nan har kika iyya d'aukar Acid zaki zo ki zubawa mutum a cikin gidan Adara? kutumar uba iro yace yana nufar kamila Salame ce ta Lailayo Ashar ta maka, Ci ubanta dan uwarta(wa'iyyazu billah) koh dabban gidan Adara bama bari aci zalinsa bare mutum Ai kafun Al'ameen yace wani abu tuni iro ya fara wanke fuskar kamila da ruwan maruka ji kawai kake kauuu kauuuu kauuuu Ihun kamila ke tashi yanda kasan ranta zai fita bugunta suke tana kokarin gudu wasu su kamo ta, Al'ameen karan kansa hankalin sa ya tashi da kukan ta kamila keyi duk yanda yaso kwatarta abin yaci tura karshe ma salman turesa yayi saura kad'an ya fad'i sumayya ta taro sa Jama'ar kofar gida su suka shigo gidan jin kukar mace kamar me, shigowa sukayi ganin abinda ke faruwa yasa su rugawa a guje suka kwace kamila Ai kamila na ganin ta tsira da wani irin matsifeffen gudu ta falla waje kamar walkiya ga hannu duk ya d'aye fatar Bayan gudun kamila suwaiba ce ta d'auki jakar kamilar, Kai Allah ya mini ga jaka mai azaban kyau maybe ma harda cash a ciki, takara sa maganar da fita a kofar Bayan fitar jama'a a kofar Al'ameen rai a bace ya fara magana sumayya yanzun kin kyauta fisabilillahi daga abin arziki saiki kama zagin yarinya "Ok watoh laifina kake gani kenan na zagi budurwan ka koh"? Waike sumayya meye haka duk wacece ummulkaba'isin wannan matsifar tun farko me yasa zaki zageta akan wani dalili yanzun mutuncin kine ashar koh zamanki a gidan nan ne kika koya, ni fad'a nake miki a matsayina na mijinki ba saurayin kamila ba, yana karasa maganar yayi d'aki ya barta tsayi kamar an dasa ta Sai yanzun sumayya tayi data sanin biyewa kamila koh yaushe kamila tazo gidan saita had'ata fad'a da mijin ta ina bazai yuba, kitchen in ta shiga taci gaba da ayyukan ta, don batason basa hakuri yanzun ganin ransa ya baci sosai Da misalin karfe 11:20 saiga yan koyan make-up inta sunzo a waje suka zauna ta shinfid'a musu taburma suka fara training don yau kwanan su biyu da fara koyo Jin d'uriyar jiniyar motar yan sanda sukaji ya tsaya a kofar gida, ba'a wani jima ba saiga matan yan sanda sun shigo gidan har kofar su sumayya Sallama dai... "Yauwa sannunku da zuwa lfy"? Lafiya ba lau ba don duk wanda yagan mu baiga lfy ba, wacece sumayya? "Ikon Allah nice wani abinne ya faru"? In munje station zakiji dalili, shige muje d'ayar yar sandan tace tana kokarin kama hannun sumayya Da sauri sumayya ta fizge hannunta tare dama police in kallon banza, babu inda zani wallahi akan me banyi kome ba Awani ce za'a tafi dani Babu wanda zai tafimin da mata ba tare da sanin laifinta ba, Al'ameen da yafitoh d'aki da sauri yake fad'a musu haka Kai ka iyye bakinka fa kasan a gabansu wa kake babu ruwan mu da makantar ka wallahi koya maka hankali zamuyi. Sannu uwar sa koya masa hankali na rantse kika tabamin miji ubanki za'a taba, station ne dai baza...... Bata karasa ba taji saukar mare tasss a fuska police in ta tsinketa dashi ai kafun ta sauke hannunta Al'ameen ya watsa mata rabonta itama duk da ba'a fuska ya saita ba amma ta maru kam Kutturu hukuma ka mara yau daga kai har matar taka sai munga gatan ku a jala yau innan, waya tayi wasu mazan yan sanda biyu suka shigo aka rufuwa Al'ameen da sumayya da karfin cin tuwo za'ayi waje dasu Al'ameen kam anfa kasa tafiya dashi sai kokuwa suke, yau sunga ikon Allah kama MAKAHO ya gagare su sumayya kam an fita da ita waje bayan ta sanya hijab Ammar ne yayi packing mota da sauri ganin yanda jama'a suka cika kofar gidan ga sumayya an tisata a gaba cikin sassarfa ya karaso wajen yana tambayar ba'asi ganinsa da daula yasa police in saura ransa suka masa bayanin sunzo kama sumayya ne Al'ameen ya mari police Cikin gidan Ammar ya shiga da mamaki yake kallon Al'ameen dake ta fama da police da sauri ya karaso wajen hannun Al'ameen ya kama ya rike hade da kiran sunan sa Tsayawa da kokuwar yayi, Ammar kaine? Eh wai meke faruwa ne, meka musu? Wallahi ba musan me muka musu ba daga zuwa wai zasu tafi da sumayya na tambayi dalili wai sai munje office insu kajifa. Gaskiya ne Al'ameen ba'a fad'awa mutum laifinsa sai a station kazo muje ba abinda zai faru mundin kaine da gaskiya Binsa Al'ameeen yayi police kam sai hararan Al'ameen suke da kitsima irin dukan da zaisha a hannunsu in ya shiga cell Alfarma Ammar ya nema a barsu sumayya su shiga motar sa inyaso sai police shigo ciki Bayan an isa station kenan officer ya had'asu da iyayen kamila a office insa sannan ya kalli sumayya, an kawo mana karanki kinyi kokarin zubawa wata Acid a fuska Allah ya kiyaye ta, ya zube a hannu bayan haka baki barta ba kika mata duka yanzun haka tana kwance a police clinic don haka zamu rikeki anan don iyyayenta zasu kai kara kotu Amma dai yallaboi kafun a kamata ai sai an tambaye ita sumayyar ba'asi itama aji tata jawabin sannan kamila ta kawo shaida ku kuma saiku kamata ku rufe, Amma daga fad'a muku magana kuma sai ku rufe mutun ba bincike haka ake Hukunci?Ammar ne ke maganar yana nuna officer in Toh kai kuma malam asuwa har zaka nuna mini abinda ya dace nayi koh kafini sanin doka ne? Ban fika sani ba haka zalika bazan barka ka rufe baiwar Allah ba dalili ba akan me? Kai malam dakata kasan a gaban wa kake kuwa? d'aya daga cikin police in yake Tambaya Ammar Koma waye ne shi, nadai gama magana sumayya fad'a musu menene Ainahin abinda ya faru Sumayya ba tsoro ta bayyana gaskiyar hakika nin abinda ya wanzu tsakaninsu da kamila Kuna daiji koh asalima kamilar ce bata da gaskiya koh a hukunce wanda yazo ya sameka har cikin gidan ka kuma yajaka da fad'a kome akai masa shiya kai kansa, sannan a maganar nan ba ruwan sumayya haka zalika Al'ameen bada niya ya zubar da acid in a jikinta ba haka zalika itace take kokarin cutar masa da mata kunga kenan duka wannan abinda ya faru ba ruwan sumayya da Al'ameen duka, kuma jama'ar gidan ne suka mata basu ba ya karasa jawabin yana bin officer in da kallo Kaima ai yanzun gashi ka yanke hukunci ba tare da bincike ba menene hujjar ka? nace wa kamila ce taje da acid in, baban kamila ya tambayi Ammar Ku tura d'aya daga cikin yaran ku officer aje a d'auko goran acid in Allah dai yasa sumayya baki taba bako? "Eh yana nan ata gefen kitchen a kasa" Ok aje a d'auko saiku saka a gwada yatsun hannun wanda aka gani a kai wannnan ma ai hujjane koh? Wai kai a matsayinka nawaye har zakana bamu order kai waye? Hannu Ammar yasa a Aljuhu ya zaro ID card nasa ya nuna Ai da sauri duka police inda ke wajen suka kame tare da sara masa A gaskiya station nan yana bukatar gyara tunda bakusan aikin kuba A matsayin ku na hukuma masu kare hakkin wa'inda aka zalunta shine zaku zamo masu tauye masu rauni ku aje hujja akan masu kudi, Ammar ya karasa maganar da tsantsan bacin rai Don Allah sir kayi Hakuri wallahi kuskure aka samu Shiyasa kuma duba da irin rauni dake jikin ita yarinyar da aka ma dukan shiyasa muka d'auki matakin gaggawa officern ke magana cikin magiya Mtwss Ammar yaja tsaki hade da rufesu da fad'a sosai, muje koh muhammad, yace yana kamo hannun Al'ameen "Ina da magana yallaboi" Wace magana kuma sumayya bayan an kashe case, Al'ameen ya karasa maganar da kamo hannun sumayya su tafi Ah ah Al'ameen ka barta muji meke tafe da ita. Ah ah Ammar mu tafi kawai yafi Sumayya yi maganar ki, Ammar yace bai saurare Al'ameen ba "Yauwa so nake Amana iyyaka da kamila Amata iyyaka da mijina Arubuta a ajiye don ban yarda da ita ba wanda yayi niyar zubama acid wata rana zai dabama wuka" Keee ki iyye bakin ki yar tamu yar daba'ce? da zata daba miki wuka wallahi karki kuskura ki kara jefin yarmu da mummunan kazafi, Kallon d'an sandar Ammar yayi Da sauri yace an gama sir, ku kuma daga yau ku jama yarku kunne karta kuskura muji koh mu gani tsakanin ta da sumayya koh muhammad Suna Fita a station in motar sa suka hau sumayya a baya Muhammad a gaba da Ammar Don Allah kuyi hakuri da abinda ya faru sannan ke sumayya gaskiya banji dadin abinda ya faru ba yara irinsu kamila da basusan kwaba babu Alkhari rigima dasu . "Gaskiya ne Ammar ni karan kaina danasan wannan fad'ar zata kai ga haka daban fara ma tanka kamila ba" Allah ya kiyaye na gaba "Ameen" Al'ameen kam kala baice ba shuru ya musu fuskar nan a hade don yau sumayya ta kular dashi tunda yake police basu taba kamasa ba yau ta janyo har station ya shiga😆 kad'an ya rage bai shiga cell ba Suna isa kofar gidan Ammar yayi packing sumayya ce ta sauka tayi cikin gida abinta Ammar kam maida kallonsa yayi akan Al'ameen dake kokarin sauka a motar, abokina kayi hakuri don Allah kasan halin mata kuma duk da bansan ainahin abinda yake tsakanin ku da kamila ba na fahimci kishine kawai ke damun sumayya, kuma koh wace mace iyya abinda zata kwatanta kenan Ba kome Ammar amma wallahi naji haushi sosai yau innan gashi sumayya harda Ashar Hakuri zakayi sai kuma ka mata fad'a a siyasa karkace zaka d'aga jijiyoyin wuya, mata sha'aninsu sai su Ba kome Ammar nagode da taimakon ka gareni ashe kai police ne? Eh muhammad Amma babba koh naga suna baka girma Eh, wani aiki kake ne muhammad? kullum nazo a gida nake samun ka badai bara kake bako irin yanda wasu keyi? Ah ah ammar ina sana'a bana bara Sana'ar me? Mongoro, abakin titi Amma meyasa kullum bana ganin ka a wajen sana'ar, inna zo? Shuru Al'ameen yayi yanajin kamar ya fad'i gaskiya kamar karya fad'a, a hankali yace jarin nawane ya karye don mangoro yayi Araha yanzun ba ciniki shiyasa bana fita Toh dame kake ciyar da iyalin kuma? Had'a fuska Al'ameen yayi jin Ammar na masa tambaya kamar ya masa sata Kayi hakuri muhammad ina ta tambayar ka Abinda bai maka dadi ba Ah ah ba kome, daman ita ke kwalliya da lalle tana mana cefene da sauran abin bukata. Gaskiya hakan bai dace ba Al'ameen ace kana namiji mace ke d'awainiya dakai ya kamata ka samu ka dogara da kanka, zan baka jari kamar na 300k sai ka kama shagon haya tunda azumi yazo kaga zama afi ciniki kayan narmari cikin azumi ga kankana ga lemo ga sweet milo harda dabino saika had'a, kana saidawa kaga saika kula da matar ka, ita kuma kudin da take samu saita kashewa kanta da kanwar taka hakan zaifi maka mutunci a wajen mace koh bata maka gori ba, koh bata nuna wani abinba Amma dai inka kasance kaike ciyar da ita kimarka daban yake a idon ta Ammar ni...... Da sauri Ammar ya tare numfashin sa kaje kayi shawara da matar taka yanzun dai bana son jin kome bayan kwana biyu xan dawo inji Amsar ka eh koh Ah ah kawai nake bukata. Shikenan nagode, Al'ameen yace yana fita a motar Ta bangaren kamila kam da bacin rai iyayen ta suka shigo cikin clinic in tana kwance akan gado inda kasan wance tayi Accident haka ta koma gwanin tausayi sai kawarta dake gefe a zaune Amma dai ke kamila bakijin bari ba saida namiki tsakani da yaron nan ba shine tsabar rashin zuciya kika ibi kafa kika tafi gidansa harda zuwa watsama matar sa acid kamila? Nifa mama wallahi bani bace itace ta d'auko zata watsa mini Uban me ya kaiki gidan ta? Koyan kwalliya naje Kwalliyar ubanki?dabani na haifeki ba sai ki gayamin wannan zance na d'auka yarinyar da bata jiran kanta. Habba Rabi da wanne zataji ne da ciwon da ke cinta koh da fad'anki? babanta ya fad'a Fita mamar kamila tayi, Kamila tambayar baban ta tayi ya aka kare a station Bai boye mata kome ba ya fad'a mata, tare da fita a d'akin Kamila tun farko saida na fad'a miki karki fara abinda bazaki iyya ba matar Al'ameen ba wawuya bace kamar yanda kike zatoh mace mai shikara 26 koh 25 kema kinsan bazaki nuna mata tawaye ba shiyasa nace kibi abin ta bayan gida. Wani banzan kallo kamila tama kawar ta, kinsan Allah sadika sai sumayya tayi dana sanin sanin muhammad saina dasa mata bakin cikin da yafi wanda nake ciki, muhammad kuma nawa ne tunda nayi aure nasan dadin abin kinga yanzun na gane ba kyau koh ido ne jin dadin aure ba keda kanki kinsan Al'ameen zaije duk inda ake so, Don haka yanzun ma jira nake naji sauki mai gabaki d'aya zan musu. Me kike nufi? Uhmm ba sun mini iyyaka da su ba toh Malamai zan shi............. 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 08146017245 *hohoho wani Kaya Sai amale shin kunsan kayatattun magungunan Mata na maman haidar* *Kayan maman haidar basuda matsala domin traditional medicine ne Kuma anahadasu da ingantattun itatuwa masu karfi da Basu da illah* 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 *1 Gumbar kankana da ayu* 🍀🍀 2 *Gumbar ayu zallah* 🍀🍀 3 *Gumbar Madara da kwakwa*🍀🍀 4 *Kaza mekwai* 🍀🍀 5 *Zabo me zuma*🍀🍀 6 *Kaza me allurai🍀🍀 sahihiyar mallaka ba boka ba malam*🍀🍀 7 *Kwallin idonka inadona*🍀🍀🍀 8 *Tauwadar mata*🍀🍀🍀 9 *ketar larabawa magani me kankarowa mace kima da daraja* 10 *Maganin sanyi me fatattakarsa duk kuwa nacinsa Koda bakya haihuwa indai matsalar sanyice gwada wnnn* 11 *Maganin nono. Sahihi* 12 *Maganin hips and bobbs* 13 *hodar. Ni I'ma koramar mata* 14 *nakasan Mara babban sirri* 15 *kafi jijjibi* 16 *daga Sha Sai wanka kasaitacce magani* 17 *Dan kwankwalati namata da mazajensu Kevin Mata* 18 *matsin kinfi budurwa dubu ko haihuwa nawa kikai Babu magana* 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 *Maman haidar Bata tsaya anan ba* *takawomuku hadaddan sabulun gyaran jiki da hadin dilka Mesa sheki da laushin fata gaman kitso Wanda laraba ke amfani dashi inkin gwada saikin dawo kudai kunemeta awannan number* 08146017245 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya* *Ibrahim* 🍃 ✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwa👌 free book 🤧 Page5⃣2⃣&5⃣3⃣ Malamai zan shiga, ke koh yawo tsirara zanyi don naga bayan sumayya sai nayi Amma dai kamila baki da imani habba don Allah kin wulakanta bawan Allah ya fita a Rayuwan ki sannan yanzun kice zaki wargaxa masa farin ciki ai wannan baso bane Wace farin cikin bayan nice farin cikin sa har gobe ina da gurbi a zuciyar sa Hhh hayya lallai kamila kina da gurbi a zuciyarsa ya hankad'aki akan matar sa koh an gaya miki so na dauwa mane a zuciya? duk mai sonka muddin baka kyautata masa toh fa kamar fure ka shuka baka ban ruwa tum tana bushewa aje aje wata rana zata mutu Kee sadika na fahimci daman ke yar hassada ce shiyasa kwata kwata tafiyyar mu bata kyau dake Nidai gaskiya nake fad'a miki kamila kuma gaskiya d'aya ce da wannan haukar ai gwara kije garesa da soyayya koh xai dawo ku daidai ta kinga sai ayi na biyu dake Ina ma yake fita kullun yana gida, naje inda akace min yana bude sana'a ma naje Amma shuru bantaba ganin sa ba, kuma ni nafi karfin kishi da sumayya sai dai ta fita tabar min shi iii in kamila karkije kikai kanki a mahallaka wallahi wani rabon kashe ki zaiyi Ya kashe ni mana indai akan Al'ameen ne kowa ma ya mutu Wallahi badai kowa ba, nidai mai sonki ce zan fad'a miki gaskiya koh kinki koh kinso rabuwa da bayin Allah nan shiyafi miki mutunci Akasinsa kuma bismillah zaki ga. Bakin ki ya sari d'anyen kashi ba abinda zan gani sai Alkhari Ai baki neme Alkharin ba mutumin da keson kashe Auren wasu shine zaiga Alkhari?tace tana Mikewa tayi ba tare da tajira Amsar kamila ba tayi mata sallama ta fita a asibitin Sumayya na shiga cikin gidan kofar su ta wuce da mamaki take kallon kadija dake zaune tana rusa kuka"ke khadija lfy"? Da gudu ta tashi zuwa wajen sumayya rungume ta tayi tana kuka'Aunty ina yaya? ina dawowa daga makaramta ake ce mini wai an tafi dake da yaya,. "Babu inda akaje damu khadija yayan ki na waje shine kika kama kuka koh uniform baki cire ba kika zauna haka" Toh ni Aunty fisabililah yazanyi na cire uniform yayana da Aunty na na station "Toh gani na dawo ki ibi ruwa kiyi wanka na baki kaya kisa dai dai yayan naki ya shigo" Toh kawai tace tana d'aukar boket, wanka tayi sumayya ta bata kayanta ta saka abincin da suka girka na karyawa daba su ciba shi ta ibawa khadija Khadija na cikin cin abinci sai gashi ya shigo da sallama Amsa wa khadija tayi hade da gaidashi, yaya sannu da zuwa Yauwa khadija ya makarantar Lafiya yau subject 6 aka mana a rana d'aya Assignment biyu Masha Allah ki gama ci sai muyi assignment in Hhh yaya ka iyya ne? Toh khadija ba nayi secondary ba koh azatan ki duk abinda na koya ya gudu ne? Yi hakuri yayana D'akin ya shiga sumayya kam daman tana kitchen Bayan khadija taci abinci wanke uniform nata tayi ta shanya,school back nata ta d'auko ta bude Assingment ne aka busu na physics sai English, yaya na gama inzo muyi Assingment in? Bara na fitoh khadija, Toh yaya Fitowa yayi suka zauna a dakali sumayya na kallon sa yana ma khadija bayanin assingment in yanda zata fahimta sannan yana fad'a mata Amsa tana rubutawa Bayan sun kammala gida khadija ta tafi tabar uniform nata a shanye, mikewa yayi ya ibi ruwan wanka ya shiga yana fita yayi Alwala ya wuce masjid Bayan fitarsa da ido sumayya ta bisa haka kawai yau taji tana jin shakkarsa sosai abinci ta juye a kula takai d'aki tayi sallah sanin baya dawowa sai bayan isha yasa tayin wanka d'akin ta shiga zani fille da T-shirt ta saka sai hulan bacci. TV ta kunna tana kallo gabaki d'aya yau ta rasa nutsuwar ta gabaki d'aya zuciyarta cike yake da tsoro Bayan ya dawo sallah abinci ta gabatar masa baiyi magana ba kawai ya zauna ya fara ci Itakam taji ba dadi koh fad'ane ya mata akan wannnan shariyan ba karamin damunta yake ba Bayan sun kammala cin abincin wanke baki sukayi, Al'ameen kwanciya yayi a gadon yayi shuru baice mata kome ba Sumayya dake kwance a gefensa hawaye ne ya cika a idanunta itakam ta shigesu da mutumin nan Sunfi, minutes 30 a haka baice kome ba itama batayi magana ba Amma kowa yasan d'an uwansa baiyi bacci ba A hankali sumayya ta matso garesa kwanciya tayi a gabansa sosai ta shige jikinsa Al'ameen yana jinta kala baice mata na shuru kawai yayi don so yake ya mata horo ta ruwan sanyi yanda gobe baza tayi Abinda bayaso ba. Hannu tasa a hankali ta na cire botur in shirt insa nan ma baiyi magana ba "Ni da wannan fushin ai gwara duka da wannan shariyan" Kala baice mata ba sai kama hannunta dayayi wanda ke yawo a jikinsa "Dan Allah ka kulani" Kinsan Allah sumayya in baki rabu dani ba sai na sauka a gadon na koma kan kujera habba Ana dole ne? "Kayi hakuri bazan kara bafa" Sauka yayi niyar yi da sauri ta riko sa hade dasa ihu"wallahi nidai ban yarda ba kayi hakuri toh na tuba" Fasa saukar yayi ya koma ya kwanta itama kwanciyar tayi a gabansa sosai ta mannu a jikinsa Haka suka kwana tsakanin su babu shiri sumayya dai na makale da muhammad duk yanda yaso cireta a jikinsa taki Washe gari haka suka tashi salam Al'ameen yasha mata mur sosai duk yanda tad'au abin da sauki abu fa ya wuce nan don da gaske muhammad yake Bayan sun karya ta d'aga ido tana kallon sa"yayan khadija" Na'am "Daman maganar make-up inda zan ma yar kanwar Deputy ne saboda tsaro bazasu iyya zuwa ba shine wai naje na musu a gida har kwana biyar ana biki" Saikin dawo kawai yace yana fita a d'akin Sosai shariyan Al'ameen ya damu sumayya, haka dai ta lallaba ta shirya tad'au hijab nata ta saka rufe kofar tayi ta fita. Bakin titi ta tsaya idonta ya sauka a kan Al'ameen ne zaune a bakin masallaci kusa da masu bara suna hira dasu, kara sowa tayi inda suke bakin ta d'auke da sallama, "Assalamu Alaikum" Mutanen bakin masallacin gabaki d'aya suka zubawa sumayya ido suna mamakin ina zata, wa'alaikumu salam su Al'ameen suka had'a baki wajen Amsawa shikam cike da mamaki meya kawo sumayya gunsa bayam tace gidan deputy zata, tashi yayi ya matsa gefe Binsa sumayya tayi inda ya tsayan ba mutane, itama tsayawar tayi batace kome ba Lafiya? "Lafiyar kenan koh laifine in nazo wajen ka"? Babu laifi... "so nake ka rakani" Rakaki ina?da mamaki a fuskar sa "Gidan da zanin mana" Hala baki gani ne? "Ah ah ina gani so nake ka rakani" Bazani ba, yace yana tafiya Ai da sauri sumayya ta riko rigansa Keee menene haka? koh baki ganin a gaban mutane muke ne "Toh sai me in a gaban mutane muke koh ba mijina na rike ba kuma wallahi in baka shige mun tafi ba saina rungume ka a gabansu" Uhmm Allah ya kyauta shige mu tafi Mutumin da ke saida ruwa kusa dasu Al'ameen ne ya dubi abokin sa, Kai Amma yariyar nan bata da kunya har masallaci zatabi miji bata maji kunyar idon mu ba muna zaune? wama yasan dalilin da yasa aka aura masa yarinya kamar wannan? Gaskiya ne haruna daga gani idon yarinyar a tsatsaye yake.. Haka sumayya tasa muhammand a gaba har gidan kanwar deputy har falon baki aka kai Al'ameen aka had'asa da abin motsa baki sumayya kuma ta shiga falon matan gidan Har yamma suna gidan sallah kawai ke d'aga Al'ameen yaje yayi ya dawo Sai kusan 5:43 na yamma suka fitoh gida gaskiya sumayya ta yaba da karamcin y'an gidan don Take Away na abubuwan da aka shirya na biki aka iba mata" yanzun ina zamu"? Sama jannati zamu, Al'ameen ya bata Amsa "Ni kake fad'awa bakar magana"? Eh an fad'a in ai nafi mai Ashar kuma bakar ma agunki na koya "Badai aguna ba kuma in kayi tsiya saina gudu na barka ka bata" Kanki kika ma Asara bani ba. "Akan me xan ma kaina asara kuma"? Aikan mijin da kike dambe mana "Dambe ni banyi dambe akanka ba" Au habba daman tabaryar ta burgane? "Ai na razana tane, karka wani zata fad'a nake akanka" Na nawa kuma. "Allah ba wani" Ke kika sabi dai mutum sai taurin kai "Kamar kai" Shuru ya mata don ya fahimci sumayya inya biye mata fuskar da ya d'aure bazai san lokacin da zai sake ba. Keke suka hau suna isa gida ana kiran mangari ba masalaci ya shiga ita kuma ta wuce cikin gida Bayan ya dawo sallah take Away in ta bude musu donut da kaza rabi sai drinks d'ayan take away in kuma fried rice ne da lafiyayyen naman shanu suna kammala ci, muhammad kam kwanciyan sa yayi Sumayya TV ta kunna ta koma ta kwanta tana kallo a kwance"yayan khadija"ta kirasa tana kallonsa ganin ya natsu waje d'aya yana tunani, jin bai Amsa ba yasa ta dafa kafad'an sa Da sauri yace Am Ammar kudin nan basuyi yawa ba, sai kuma da sauri ya fara kame kame don sam subutar baki ne abinda ke zuci shiya fitoh fili "Wani kudi kuma Waye Ammar"? Am ba kome. Akan me zakace ba kome duk kabi kasa kanka a damuwa in ma bashi ake binka bazaka fad'amin na biya ba duk kudin da nake tarawa Wallahi tatali nake maka naga kudin yayi yawa sosai kafun na baka ka kama sana'a mai d'an kauri mu samu murufawa kan mu asiri, amma ina dalili ina dana rufin asiri kabar kanka a rikici" Ba haka bane sumayya ba'a rikici zansa kaina ba wannan magana ne daban. "Wace magana kenan?koh bankai naji damuwar kaba"? Daman Ammar ne ya mini magana jiya zai bani jari dubu d'ari uku na kama shago kafun azumi tunda saura sati biyu ne ga kayan marmari a azumi akwai kasuwa. "Bazai yuba wani ma Ammar inne d'aya? akan me zaice zai baka kudi tun da baisan zai Taimake kaba sai yanzun" Sumayya bamu fa dade dashi ba kuma insha Allah ba abinda zai faru "Gaskiya ban Amince ba ka bari inna gama had'a kudin saina baka kabar masa nasa" Gaskiya sumayya gwara na karbi nasan kawai na gwada kasuwar tunda ba kyauta yace ba koh bashi saina tambaye sa in kyauta ne ni karan kaina bazan Amince ba Amma in bashine saina karba ke kuma saiki tara kudin ki wata rana zai mini Amfani. "Yanzun ka zabi karban nasa akan nawa kenan"? Ni bance ba Amma dai gwara nasan akan bashin tsakanin mata da mijin nan bana sha'awarsa sai in ya zama dole "toh ce maka akai bashi nace ne"? Koma dai yayane kiyi hakuri bazan iyya karba ba Sumayya juyawa kawai tayi ta kwanta bata kara magana ba a hankali yasa hannu ya d'agota kwantar da ita yayi a jikinsa cikin sanyi yake mata magana, don Allah badon niba sumayya ki daina Ashar koh don yaranda zamu haife su tashi da kalami mai kyau a baki banji dadin abinda ya faru ba koh kad'an yau ace anzo an d'auki matata a motar yan sanda wannan ba mutuncin matar aure bane sai in ya zamo mata dole " insha Allah bazan sake ba"ta karasa maganar da kara kwanciya a jikinsa Allah yasa... "Ameen" shuru sukayi dukansu biyu ba wanda ya kara magana a hankali Al'ameen yasa hannu ya yaye hijab da sumayya tasa don yau sanyi ake sosai "Sanyi fa nake ji" Nima ai sanyin nakeji kinga nasa abune? "Ai kai daban ni daban" Nida ban, inji wa? "Sumayya" Uhmm muyi bacci "Banaji" Saboda? "Sanyi " Uhmm toh bara na rufeki sai kibar jin sanyin, yana maganar yana hawa kanta Saboda sabo da hakam yasa bai dame sumayya ba baccin ta kawai ta kamayi bata san ma yaushe yayi nasa ba Washe gari Ammar yazo Akan maganar su Al'ameen ya Amince, Tare da tambayar Ammar kyautane koh bashi kai tsaye Ammar yace bashine don ya fahimci muhammand kalansa daban ne mutum ne wanda baison banza damuwar sa kawai ya nemi na kansa Cikin sati d'aya Ammar ya sama ma muhammad shago mai kyau ta tsallaken first bank kaya ya cika masa makil a shago kama daga mazar kwaila dabino kayan marmari ba wanda babu su dangin Apply duk ba'a barsu a baya ba,yaune Aka kammala had'a shagon kai masha Allah shago kam saidai makiya suji haushi Muhammad Anya zaka iyya kasuwancin nan babu yaro a kusa dakai kaga yanzun shagon nan babba ne idanun barayi zai sauka akai bare an ganka baka da ido za'a iyya baka d'ari ace dubune, Amma in kana da yaron daka Aminta dashi mai hankali a Unguwan naku sai yazo ku zauna tare kana d'an basa nasa ladan sai inga kamar zaifi? Gaskiya ne Ammar daman Akwai wani yaro shagari d'an wani makwancin mune daya rasu toh yaron ba boko ba Arabic tunda iyayen sa suka mutu dai abin sai a hankali ba kula dashi ake ba saina d'auko sa yazo mu zauna tare Amma muhammad yaro irin wannan da ba boko ba arabic bazai cutar dakai ba kasan fa halin yaran yanzun? Ba kome insha Allah bokon ma iyya secondary ya tsaya arabic in tunda iyayen sa suka rasu ya daina zuwa saboda rashin mafad'i Amma najashi a jiki kaga inda rabo sai kaga Allah ya dad'a nitsar dashi Haka ne kam sai kaje wajen bappan nasa kuyi magana saika d'auki yaron Insha Allah Ammar nagode Allah ya tsaka maka da Alkhari ya bani ikon biyan abinda ka bani Ameen, ni bara na wuce Allah ya kawo kasuwa Ameen, Al'ameen yace yana rufe shagon gida ya nnfa fuskar nan a washe Bayan ya shigo gidan da sallama lokacin sumayya nama wasu lalle Amsa masa tayi tana kallon sa ganin sai murmushi yake"yayan khadija lfy"? Lafiya kun gama lallen ne ? "Saura hannu d'aya meya faru"? Babu kome ki gama dai sai muje ki gani Toh sumayya tace da sauri sauri ta kammala musu don ta kagu taji menene" na gama muje" Kiye wanka dai kisa kaya da hijab amma daga gama lalle sai fita "Nidai gaskiya Ah Ah muje inna dawo zanyi" Hannunta kawai ya kama har ban d'aki ya fitoh ruwa ya iba ya kai mata, kiyi wanka malama Ba yanda sumayya ta iyya haka tayi wanka ta shirya ya saka ta agaba har shagon sa sosai sumayya tayi mamakin girman shagon da abubuwan da aka zuba masa gwanin sha'awa kai gaskiya "masha Allah waje yayi waje" Gaskiya ne nima ina ji wajen ba karamin kyau zaiyi ba "Ya mayi Amma dai ya kamata kane mi abokin zama saboda tsaro" Eh munyi magana da Ammar, gidan su shagari zani koh xa'a amince ya tayani zaman shago "Gaskiya ne hakan yayi kyau sosai wallahi Allah ya kawo kasuwa" Ameen, muje ki rakani gidan su shagari "Toh"sumayya tace tare suka tafi gidan su shagari kuma Alhamdulilah sun Amince Cikin sati d'aya ba karamin mamaki yan sintali sukayi ba ganin muhammad da babban shago gashi bai fad'awa kowa kome ba inka tambaye sama sai yace Allah ne ya rufa masa Asiri yayi shuru , sosai yake cefene yanzun kome na gidan sa ya d'aukewa sumayya duk yanda taso hanata yake gashi Allah yasawa abin Albarka Arana d'aya yana cinikin dubu goma gashi Shagari ya kaisa wajen wani mai kayan marmari ya had'asu da dilan yan gembu yanzun masa ordern kaya ake daga gona sai dai kawai ya tura shagari tasha in kaya ya sauka a d'auko masa. yanzun kam Alhamdulilah sumayya kudi na shigo mata wallahi kowa ya ganta zai zaci daki Ac falo Ac mota AC office Ac ne tsabar yanda ta dawo tayi kyau tayi fresh sosai har wani yellow yellow tayi yanzun koh tunanin gidan su batayi ita karan kanta tana mamakin yanda take mantawa akwai abie A duniya, wata rana har mamakin kanta take saitaji kamar ta kirasa sai kuma ta fasa hatta shi muhammad yanzun in ka gansa zaka san kwanciyar hankali ya samu matsunguni. ga suturu masu kyau yanzun shima da kudin sa yake sayan kaya ya saka duk ya watsar da tarkacen kayansa hatta khadija yanzun daban ta koma kamar ba khadija ba gata ba yaya ba, ba Aunty ba Yaune aka ga watan Ramadan gobe za'a tashi da azumi sumayya yau da khadija kasuwa suka shiga sosai sumayya ta musu sayayyan azumi kome buhu buhu katon katon ga kaji ka kifi, vegetables daman bata da matsalan fruit bayan sun dawo kasuwa kowa ka gani fuskar sa a washe Adalilin gobe azumi Bayan isha muhammad ne da sumayya suke cin abinci a waje, zazaune suke akan taburma don yanzun sumayya ta saya Assalamu Alaikum "Wa'alaikumu salam"muhammad da sumayya suka Amsa " sannun ki da zuwa sumayya tace tana tashi, ta d'aukowa bakuwar kujera don a tunanin ta koh customer ne Ah ah ba zama nazo ba magana zanyi dake Ni kuma?sumayya ta maimaita Eh ke dai, ina dai kice sumayya Abdulsalam shugaba? Eh nice Nazone na shaida miki koh na gargade ki Akan i................ 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 08146017245 *hohoho wani Kaya Sai amale shin kunsan kayatattun magungunan Mata na maman haidar* *Kayan maman haidar basuda matsala domin traditional medicine ne Kuma anahadasu da ingantattun itatuwa masu karfi da Basu da illah* 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 *1 Gumbar kankana da ayu* 🍀🍀 2 *Gumbar ayu zallah* 🍀🍀 3 *Gumbar Madara da kwakwa*🍀🍀 4 *Kaza mekwai* 🍀🍀 5 *Zabo me zuma*🍀🍀 6 *Kaza me allurai🍀🍀 sahihiyar mallaka ba boka ba malam*🍀🍀 7 *Kwallin idonka inadona*🍀🍀🍀 8 *Tauwadar mata*🍀🍀🍀 9 *ketar larabawa magani me kankarowa mace kima da daraja* 10 *Maganin sanyi me fatattakarsa duk kuwa nacinsa Koda bakya haihuwa indai matsalar sanyice gwada wnnn* 11 *Maganin nono. Sahihi* 12 *Maganin hips and bobbs* 13 *hodar. Ni I'ma koramar mata* 14 *nakasan Mara babban sirri* 15 *kafi jijjibi* 16 *daga Sha Sai wanka kasaitacce magani* 17 *Dan kwankwalati namata da mazajensu Kevin Mata* 18 *matsin kinfi budurwa dubu ko haihuwa nawa kikai Babu magana* 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 *Maman haidar Bata tsaya anan ba* *takawomuku hadaddan sabulun gyaran jiki da hadin dilka Mesa sheki da laushin fata gaman kitso Wanda laraba ke amfani dashi inkin gwada saikin dawo kudai kunemeta awannan number* 08146017245 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya* *Ibrahim* 🍃 ✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwa👌 free book 🤧 Page5⃣4⃣&5⃣5⃣ Akan ibada don naga d'an changen rayuwa da kuka samu haryasa kuna sanyi da ibadan koh, toh bari kuji irin wannan daman makiyan ku suke jira sumu ku mai gabaki d'aya in kukayi sake da ibadah toh tabbas zasuga bayan ku sarkin yawa yafi sarkin karfi, watan da muka shiga wata ne mai Albarka ni'ima da falala ku dukufa wajen neman tsari da kariya a wajen mahaliccin mu. Sake baki sumayya tayi tana kallon matar da bata santa bama gashi dare ne ba nepa bare ta mata kallon sap"malama wani irin magana ne haka sannan suwaye makiyan mu"? Baki bukatar ji nidai na fad'a miki tace tana fita a kofar Sumayya kam kamar doluwa haka ta kuma sai bin hanyar da matar ta fita kawai take tana Al'ajabi"yayan khadija kaji wani magana kuwa"? Uhmm sumayya maganar matan nan koh bamu gaskata ba, Amma tunda ibadah tace toh mu dage koh ba makiyi Addu'a makamin mumini ne "Gaskiya ne" sumayya tace duk jikinta yayi sanyi sosai abincin ma kasa cigaba daci tayi Al'ameen dake cin abinci tsayawa yayi jin sumayya shuru hannu yasa ya tabata sumayya yadai? "Uhmm babu kome kawai dai ina mamaki ne" Mamakin me kuma? inna matan nan ne ai ba abin mamaki bane don duniya da fad'i kika san menene Alakarta da su kedai mu rike ibadah hannu bibiyu insha Allah ba Abinda zamu gani sai Alkhari kici Abinci pls? Toh tace tana cigaba dacin abincin"yayan khadija me zan dafa mana na sahur"? Me kike so? "Uhmm aikai na tambaya koh"? Nima saina tambaye ki "Toh ai mata ke tambayar miji abinda za'a dafa" Au yanzun kam an yarda ni mijine kenan? "Oho dai nikam ka fad'a mini abinda zan dafa so nake mu kwanta da wuri samun mu tashi da wuri" Ki mana tuwon shinkafa miyan shuwaka "Nama koh kifi"? Duk wanda ya dace ki saka "Ok" kawai tace tana tashi kitchen ta shiga ta barshi zaune akan taburma Girki sumayya tayi sai kusan 10:30 ta kammala aikin girki juyewa tayi a kula takai d'aki tayi tatan kamu da khadija ta karbo mata a inji tana gamawa tattara taburman tayi, ta rufe kofar su zuwa lokacin Al'ameen yayi bacci tuntuni itama kwanciyar tayi bata tashesa ba don bacci takeji itama Misalin karfe 1:30am Al'ameen ya farka jin sumayya ajikinsa yasa sa tata bata, sumayya!! sumayya!! "Menene"? Ki tashi mana "asuba yayi ne"? Baiyi ba sallah zamuyi tashi maza kinji "Uhum"tace tana mikewa sauka tayi akan gadon ta kamo hannunsa suka fitoh waje bayan ta kunna hasken wayan ta Alwala sukayi suka tada sallah Sai karfe uku suka sallame sosai suka dukufa suna Addu'an neman tsari wajen mahallincin mu da neman gafaran sa 3:41 sumayya ta d'auko musu tuwon ta bude da zafin sa kamar yanzun akayi zuba musu tayi sukayi sahur basu koma bacci ba sai data cika ruwan randa a laida fari ta d'add'aure ta cika firij nata bayan asuba suka koma bacci Dayake Cikin Ramadan ba'acika sayan kaya da safe ba sai yamma yasa Al'ameen yabiye wa sumayya suka cigaba da bacci basu suka tashi ba sai kusan 9 Al'ameen ya tafi masallaci tafsiri sumayya ma islamiyar unguwan taje wata babbar malama ke tafsir wa matan aure a ciki sai bayan Azahar Al'ameen ya fita shago, sumayya kam sallah tayi ta shiga kitchen abinci ta dafa dankali ne da kwai ta soya sai ruwan tie ta musu macaroni da miya duk ta zuzzuba a kula ta zuba wasu goggo ma a manyan kula guda biyu, kiran yaro tayi ya kira mata khadija bayan ta dama kunu cikin bokatin penti fari babba, wanka ta shiga kafun ta fitoh saiga khadija ta shigo bayan sun gaisa ta bata boket in da cups na roba wanda ta saya jiya ta had'a mata takai masallaci sadaka sai ruwan da tasa da asuba a firij sunyi guda shima boket ta cika ta d'aurawa Almajiri yabi khadija Rarra bawa khadija tayi a masallaci sosai jama'a ke sawa abin Albarka don koh masu kudin unguwan basa kawo kome a azumi sai talakawa ke kokarin ciyar da masu azumi (Allah ya kyauta) Bayan khadija ta dawo da bokata yen, kulan abinci sumayya ta bata ta kaima goggo suyi bud'a baki Al'ameen ne ya had'a kankana da dabino sai sweet milo, yasa a laida biyu ya rike a hannunsa barin shagari yayi a shago hade da basa kudi yasai abin bud'a baki shima Gidan goggo ya wuce ya bata laida d'aya ya kamo hanyar gida Tun akan hanya ake ta masa godiyan kunu da kankara sosai yayi mamaki wani kunu kuma amma baiyi magana ba amsa musu yayi ya shiga gida daidai lokacin aka kira sallan mangari ba Assalamu Alaikum "Wa'alaikumu salam" Jin bakin sumayya cike da abinci ta amsa sallamar yasa sa da mamaki yace toh yau koh jira babu hajiya har an kai loma? "Ai a azumin nan ba jira kaji in gaya maka ana kiran sallah sai ci yaushe zan jiraka kuma" Uhmm yayi kyau yace yana zama akan dakalin da take, mika mata laidan yayi ganin yau koh karba batayi ba sai jin karan shukali kawai yake Amsa tayi ta bude dabino ne guda biyar ta damka masa a hannu sai ruwan shayi a kofi Karba yayi ya bude baki da addu'a bayan yaci dabinon ruwa ya kurba kawai yayi Alwala ya tafi masallaci Sumayya kam sai da ciki ya d'auka kafun ta zakud'a itama sallar tayi bayan ya dawo masallaci shima yaci nasa Abincin sauran kayan marmari da ya rage ta saka a firij Da misalin karfe 11 bayan ta gama aikace aikacen girkin asuba yake tambayar ta akan kankara da kunu "Yanzun don zanyi aikin lada saina fad'a maka yayan khadija watan azumi ne fa" Allah ya karbi ibadun mu "Ameen, FATAN MU(next novel)kenan insha Allah" Ta bangaren kamila Alhamdulilah jiki yayi sauki sosai harma an sallame ta sai dai fa fatar hannu kam ba kamar nada ba Yau dai gidan kawarta ta nufa Assalamu Alaikum Wa'alaikumu salam wanake gani anan koh dai idanuna ne kemin gezo lallai kamila duniya ashe ana iyya tunawa damu Ke matsalar ki kenan Harira daga mutum yazo gunki koh wajen zama baki bani ba kin kama mini korafi Ai dole na miki kamila tun auren ki na sake saki a idanu na? koh wayarki na daina samu sai dai inji a gari kinzo kin koma yar buru uba har zaki ce ban baki mazauni ba Yanzun dai kiyi hakuri ki zauna wata magana ce ta kawo ni Aikam sai ta kawo ki badai kika kawo kanki ba Kee habba don Allah jarabar ta isa haka Naji meke tafe dake kamila Yauwa zancen dai na muhammad ne Wani muhammad in? Ki jiki da wani banzan tambaya muhammad nawa nake dashine wai Nidai nasan tsohon mijinki dai ba muhammad bane MAKAHO... Kwal uba yanzun kuma tsohon zuma aka koma Ai daman tafi magani, ke Harira kinsan meya kashe min aure? Ah ah Toh rashin biyamin bukata ne bayayi, don bana gamsuwa shiyasa na kashe aure na don ni yanzun duniya kaf in dai zan samu namiji gwarzo ba ruwa na da talauci koh kyau kin gannin nan don nabisu banga da kyau ba Amma ke dai kamila akwai shirme kece miki akai shi Al'ameen in jarabebbe ne kamar ki? Hhh habba Harira ido fa ba mudu bane amma yasan kema Hhhh shegiya ta faso gari, ta karasa maganar da bawa kamila hannu suka tafa, toh yanzun me kike so ayi ne Yauwa MAKAHO fa aure yayi kuma wata yar iska ya aura family shugaba 😳shugaba fa kikace? Eh nima nayi mamaki auren nan yar iska in kika ganta sai gaban ki ya fad'i tsabar kyau Kema dai kamila aikin san zuriyan gidan daman kyawawane sai dai na wani yafi na wani Gaskiya ne in gaya miki wai dana gama bibiyar muhammad na tataro kome nasa na samu cikeken bayani akansu shinefa naje da sunan koyan kwalliya wajen ta yar iska kinga duka da suka mini karshe ma acid inda zani makaranta dashi zamu shiga lab zuciya ya ebeni na d'auko zan watsa ma yar banza kawai in gaya miki abin mamaki muhammad ya zabi matar sa akaina da kansa ya hankad'a ni har acid ya zube a hannuna, ta karasa maganar da nunawa Harira hannun Cap wani mataki Dad ya d'auka akansa? Ai ban fad'a masa gaskiya ba cewa nayi ita ta zuba mini Aiko kinyi wauta Ai ma abin ba inda yaje don bata kamu ba Kema ai kinsan bazata kamun ba, yanzun dai me kike so ayi Yauwa Harira wajen malaman nan naki nake so ki kaini akan maganar nan Hhhh yar iska ba kullum fad'a kike mini akan malamai ba angaya miki ana zama hakane ai kikace zaki zauna haka toh bone ya sameki Gaskiya kam don akansa babu abinda bazan aikata ba ke so nake inga koh kaunar ganin sumayya baya so yaji kaf duniya ba wanda yaki jini irin ta, ba wanda yake so irina Shegiya ba kome tashima kiga bara na d'auko mayafi muyi gaba kinsan har kauyen mutum biyu ne in bamu tafi yanzun ba sai kuma gobe saboda hanya ba kyau ga dare Amma harira haka zaki tafi naga mai gidan baya nan gashi yara daga su sai yar aiki Kee waya gaya miki sai na jira sa ai wallahi sai abinda nace Uhmm kai nima fa za'ayi tafiyar nan naku dani Amma dai kin taho da kudi kam koh ? Karkiji kome akwai kudi akwai mota sai ki tukamu tunda ke kika san hanya Ok muje haka kamila da Harira suka d'auki hanyar mutum biyu wajen boka a watan azumi koh tsoron Allah babu Sai la'asar suka isa cikin mutum biyu dole tasa suka faka motar su a bakin titi suka hau machine mai kafa biyu zuwa ciki cikin kauyen bayan sun iso ma sai da suka tsallake ruwa Wani dutse ne baki kiren hayaki na fita akai tunda suka nufo wajen wani irin wari ne yake bugan hancin su da sauri kamila ta tushe hancin ta Cikin gaggawa Harira ta buge hannun, kamila ke kamila ki rufa mana asiri kar muje ciki a haka kin tushe hanci wani irin iskanci ne wannan? Amma Harira baki jin wari da doyi na tashi ne? Ina ji amma rufe hancin ki daidai yake da rasa aikin ki Kamar ya? Kamar haka tace tana kama hannun ta su koma baya Ke Harira menene haka? Bakin ce baki gane ba shine zan ganar dake Yi hakuri muje Haka suka nufi cikin kokon kamila kamar zata mutu tsabar wari ai bata gama ganin tashin hankali ba sai data shiga kokon taga tashin hankali mutum ne a zaune kamar an sassaka sa jikinsa duk kuraje sunyi ruwa sun cika sai doyi yake dagashe sai fata kawai ya d'aura a Gabansa ga gashin kansa sa tsitsige kamar shaid'an gashi jikin kokon kadangaru ne sunfi dubu a mamman ne koh ta ina bazama kaga jikin kokon ba tsabar yawansu gasu a shure waje d'aya Kai ku dakata ku dakata nace, yafad'a da muryarsa mai amoi gata muryar yar irin jarirai cikin tsawa yayi maganar Sosai kamila ta razana da gudu tayi hanyar fita Karki kuskura ki fita a nan ba tare da an gama da bukatun ki ba Tabbas zaki sami Muhammad MAKAHO....... Aijin ya ambace zata samu muhammad yasa ta dawo da sauri jiki na rawa ta tsunguna kamar yanda Harira tayi Kallon ta bokan yayi sannan ya rufe idonsa yana wani irin magan ganun tsibbo na d'an wani lokaci kafun ya bude idanunsa kallon cikin kwaryar yayi nad'an wani lokaci kafun ya d'aga ido yana kallon kamila Tabbas zaki samu muhammad amma fa rabasu da sumayya babban Had'ari ne saboda kaddarar su a manne take dana juna akwai makiya sama dake idanunsu kullum na kansu sannan asirin dake yawo akansu yafi wanda kike so a saka musu Amma akwai mafita d'aya Jiki na rawa kamila tace kamar ya kenan Allah gafarta malam Wani irin tsawa ya daka mata, keee ba'a kira mana Allah Anan kinsan akwai sane kika zo neman biyan bukata wajen mu(Wa iyyazubillah) Tuba take na kan dutse sabuwa ce Amata afuwa Ammata Harira amma ta kiyaye nan bama son shirme Zan...z..nkiyaye..takara sa maganar cikin tsoro harga Allah mutumin razana ta yake Yanzun ana tsaka da ibadan watan Azumi kuma sun tsaya dakyau wajen ibadah basu bada wani kofa da Za'a kawo musu farmaki ba sai dai akwai dama, nan da sati biyu zata Fara jini mundin tayi sake da ibadah zamu farmata Kamar ya malam?kamila ta tambaye sa Ranan juma'a 17 ga azumi da misalin karfe 1 na rana zata fara jini a lokacin zuwa kwana biyar kina da daman da maganin zai cita mundin tayi sakaci da ibadan da suke yanzun Ok toh malam ni yanzun wani mataki koh ince wani aiki d'aya za'a mini Akaf asirin da za'a musu don ganin yakita, bazaici ba don an musu bakin asiri na zama tare da juna abu d'aya zan miki shine Ama sumayya kurciya tabar kasan gabaki d'aya ta manta da NIGERIA a rayuwar ta kwata kwata da rayuwar da tayi a ciki, Wannan damar xaki samu na auren muhammad, duk da hakan zai batawa wasu shirin su da suka dade sunayi Na Amince wallahi na yarda ayi mata koma menene Shikenan zaki kawo bakar tinkiya da jan tatabara sai rakuma biyar masu ciki Malam ina zan samu wa'innan abubuwan sai dai in b Da hali na bada kudin sai a nema asaya Ba damuwa ki kawo Nawa ne? Bama yanke kudi biya kawai ake Kudi kamila ta basa kusan 500k Kije ki dawo gobe in mun had'a aiki sai kizo ki karba Toh mungode Fita sukayi da Harira sosai taji dadin jin za'a mata maganin yar iska ************** Sosai sumayya da Al'ameen suka dage da ibada sallan dare ga sadaka duk yamma sai sumayya tayi kunu da kankara shi kuma muhammad yayi sadakar lemo ma Almajirai koh dabino Khadija kam haryau basu kara haduwa da Ammar ba bata kuma san shiya bude ma yayanta shago ba taci gana da zuwa makaranta har azumi yakai 17 sumayya batayi sakaci da ibada ba kwanciya da Alwala in Muhammad ya tashi da dadare yana tada ta itama ta zauna tana lazimi sosai suke ibada Awatan koh bacci yanzun basu da lokacin sa sai bayan asuba Ta bagaren kamila sun koma wajen boka washe gari a idanunsu ya kamo wata katuwar mujiya ya fade mata ciki layoyin da ya rubuta sunan sumayya ya saka ma mujiyar a cikin da Allura da zare yasaka ya dinke cikinta ya baiwa kamila tayi ta kula da ita a keji ta mata jinya nan da kwana 16 ranan da sumayya zata fara Al'ada kenan kuma ana son karta sake azumi daga ranan sai randa sumayya ta fara Jini saita saketa da tsakar dare tana mai Ambaton sunan sumayyar kafun gobe da safe zataji kyakkyawar lbr Duk da kamila na tsoron mujiya Amma dayake shaid'an ya buga mata ganga haka ta cici a kwando tayi jalingo Yau aka kai azumi 20 a daren ranan sumayya ta samu tsarki bayan isha'i tayi wanka Al'ameen kam bayan ya dawo daga Ashan kwanciyan sa yayi don yau Tahajjud zasu shiyasa yake son kwantawa da wuri Sumayya kam abincin asuba tayi sai kusan 9:39 ta kwanta Da misalin karfe 12:10 Al'ameen ya farka Tada sumayya yayi sukayi Alwala kaya suka chanja daga na bacci zuwa jallabiya ita kuma tasa dogon riga sai hijab sallaya ya d'auka suka rufe kofar suka fita Gidan goggo suka wuce don khadija tayi ta rokon su zata bisu itama bayan sun isa sumayya ce ta shiga gidan da sallama jin shuru yasa ta buga kofar d'akin khadija tashe tayi Itama Alwalan tayi suka fita a gidan Haka su uku suka kama hanya koh ina ka wuce group group ne na Al'umma musulmai suna tafiya manyan masallatai kamar rana ne ba dare ba Sumayya da khadija da Al'ameen da kafa suka taka har macilin babban masallacin juma'a na Dr Ibrahim jalo jalingo Sai 3 aka tashi Ana fifita a masallacin, ture ture tsabar yawan jama'a cunkoson ne yaraba sumayya da khadija Bayan khadija ta fitoh daker tsaya tayi tana dube duben sumayya Amma bata ganta ba A haka ta fitoh bakin SINTALI GIOBAL ta tsaya saiga yayan ta don daman sunyi agun zasu hadu in An tashi Bayan isarsa da mamaki jin muryar khadija kad'ai banda sumayya ya tambaye ta, ke khadija ina Aunty taki? Wallahi yaya banganta ba tunda muka.............. 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 08146017245 *hohoho wani Kaya Sai amale shin kunsan kayatattun magungunan Mata na maman haidar* *Kayan maman haidar basuda matsala domin traditional medicine ne Kuma anahadasu da ingantattun itatuwa masu karfi da Basu da illah* 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 *1 Gumbar kankana da ayu* 🍀🍀 2 *Gumbar ayu zallah* 🍀🍀 3 *Gumbar Madara da kwakwa*🍀🍀 4 *Kaza mekwai* 🍀🍀 5 *Zabo me zuma*🍀🍀 6 *Kaza me allurai🍀🍀 sahihiyar mallaka ba boka ba malam*🍀🍀 7 *Kwallin idonka inadona*🍀🍀🍀 8 *Tauwadar mata*🍀🍀🍀 9 *ketar larabawa magani me kankarowa mace kima da daraja* 10 *Maganin sanyi me fatattakarsa duk kuwa nacinsa Koda bakya haihuwa indai matsalar sanyice gwada wnnn* 11 *Maganin nono. Sahihi* 12 *Maganin hips and bobbs* 13 *hodar. Ni I'ma koramar mata* 14 *nakasan Mara babban sirri* 15 *kafi jijjibi* 16 *daga Sha Sai wanka kasaitacce magani* 17 *Dan kwankwalati namata da mazajensu Kevin Mata* 18 *matsin kinfi budurwa dubu ko haihuwa nawa kikai Babu magana* 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 *Maman haidar Bata tsaya anan ba* *takawomuku hadaddan sabulun gyaran jiki da hadin dilka Mesa sheki da laushin fata gaman kitso Wanda laraba ke amfani dashi inkin gwada saikin dawo kudai kunemeta awannan number* 08146017245 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya* *Ibrahim* 🍃 ✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwa👌 free book 🤧 Page5⃣6⃣&5⃣7⃣ Tunda muka fitoh Banganta ba. Wani irin baki gantaba kuma hauka kike ne khadija koh me? Wallahi yaya da gaske nake banga Aunty ba. Nashiga uku ni muhammad, yace yana kamo hannun khadija suka tsallaka titi zuwa cikin masallaci sosai suka dudu ba Amma basu ga koh mai kamada sumayya ba sosai abin ya gigitashi, ke khadija a daidai ina kuka rabune wai? A kofar fitane fa yaya cunkoso yasa muka rabu. Jingina kawai yayi da jikin ginin masallacin shikam dai ya shiga ukun sa ina sumayyar ta shiga ne wai? Yaya koh dai aunty gida ta koma ne? Wani irin gida kuma khadija bayan saida nace ku jirani a global xaki wanice ta koma gida nadai san sumayya bazata koma gida ba Daga khadija har muhammad hankalin su ya tashi har hankalin yan agaji ya dawo kansu d'aya daga cikin su ya tambaye sa malam lafiya naga kana ta zaga masallaci kaje ka dawo, tun dazun yanzun fa ana neman 4:00 bazaka tafi gida ba ga kanwarka ma naga kuna ta yawo tun d'azun lfy kam? Ina fa lfy wallahi ranka ya dade da matata mukazo masallaci amma ban ganta ba gabaki d'aya na gama iyya dubata amma bangan taba Wace irin magana ce wannan ita matar taka yar yayece koh jaririya da za'a nema a rasa koh hanyar gidane bata sani ba? Ranka shi dad'e ni nasan bazata koma gida ba tunda nace ta jirani toh tabbas zata jiranin Kaga malam karkazo ka d'aga mana hankali a wani unguwa kuke ne? Sintali ne.. Sintali😳A koh B? Sintali A ne ranka ya dade Amma dai kai d'an rainin wayo ne ina sintali A ina macilin da bazata iyya komawa da kanta ba kazo kana kokarin daga mana hankali? Kayi hakuri ranka ya dade Na hakura amma ka fita kakama kanwarka kubar masallaci nan ya zakazo da maganar da hankali bazai d'auka ba matar ka ta bata, ina macilin ina sintali?da bazata koma ba Kayi hakuri.. Kama gabanka malam? Haka Al'ameen ya fita kaman k'wai ya fashe masa a ciki Da sauri khadija tazo ta kama masa hannu haka suka fito a masallacin gwanin tausayi Tsallake titi sukayi suna tafiya Gabaki d'ayansu inka gansu kaga wa'inda basu da nutsuwa gabaki d'aya zuciyar Al'ameen bugawa take kamar ance masa sumayya zata barsa Sunzo daidai titin doruwa kamar daga sama khadija ta hango mace da hijabi tana tsallako titi Allah yasa akwai wutan sola shiya bata daman ganin wance ta tsallakon da karfi ta kwala ma sumayya kira Aunty!!! Ai da wani irin mugun sauri Al'amesn ke magana, kee kin ganta ne ina sumayyar take tana ina? Kafun khadija ta basa amsa da gudu sumayya ta karaso karesu"lafiya har yanzun baku koma gida ba"? Kee sumayya kina da hankali kuwa banace miki kafun mu shiga masallaci, kujirani a gidan man sintali ba koh ba haka nace ba, shine zakisa kafa ki koma gida don tsabar kin raina min wayo gani d'an iska koh? "Don girman Allah kayi hakuri, wallahi sace mini takalmi akayi shine na tsaya nema na jira mutane suka fifita duk ban gane ba dana fitoh wajen global, nan ma ban ganku ba shine nayi tunanin kun koma gida saina koma nima danaje kuma naga baku dawo ba, shine nabiyo ku" Don Allah yaya kayi hakuri tsabani aka samu! Na hakura khadija Amma sumayya karki sake mini haka Am warning you? "Insha Allah" tace tana kama hannunsa dake cikin na khadija don baizo da sanda ba suka tsallaka titi Bayan sun isa gida ganin sun kusa makara yasa sumayya hana khadija zuwa gida abincin sahur ta iba mata tuwo ne miyan kifi d'anye suka zauna a waje suna ci Al'ameen kam tuwo kawai yakeci da miya baya cin kifin Da mamaki sumayya tace "yayan khadija ya bakacin kifin gashi mun kusa makara fa"? Sumayya bazan iyya cin kifi d'anye ba kar kashi ya makale min a wuya " tarwad'a ne fa" Nikam ah ah Hannu sumayya tasa a kwanon miyan ta yago kifi tasa mai a baki"toh bude bakin nasa maka" Da sauri khadija ta kauda kai kamar bata gansu ba don wallahi sun bata kunya Al'ameen kam bude baki yayi sumayya sai da ta ciyar dashi kifi har yace ya isheshi kafun ta ci nata Bayan sunyi sallan asuba khadija ta koma gida Al'ameen kam bacci suka koma suna ramakon na jiya Yau koh tafsir basu samu zuwa ba saboda baccin dake idanun su har 12:00 suna bacci a d'aki Assalamu Alaikum!! wasu yan matane guda hudu ke sallama sunfi minutes 8 suna buga sallama shuru Al'ameen kamar a mafarki yake jin sallama akai akai mikewa yai hade da amsa musu Ina kwana? Lafiya, ya amsa Am wajen sumayya mukazo Ok lafiya kam? Eh munzo tambayar lallen sallah ne Ok bara na tada ta Ah ah ka barta in bata tashi ba inyaso gobe sai mu dawo Ok toh Allah ya kaimu Ameen, in ba damuwa inta tashi kace yaran gidan Malam yunusa ne sukazo tambayar Lalle kar wasu suzo su riga mu? Toh yace yana d'aukar boket bayan sun fita wanka yayi ya shiga dakin dayake yanzun yasan soket in kunna TV jin an kawo nepa ga fanka na hura d'akin danna soket in yayi daman jiya sunnah suke kallo aka d'auke, zama yayi yana sauraron wa'azi hannun sa d'auke da calbi yana ja Sumayya bata tashi ba sai azahar nan ma shiya tashe ta kafun ya tafi masallaci ******************* Haka rayuwa yayi ta tafiya axumi nata karewa a hankali hankali customers na sumayya suke zuwa tambayar lalle tun sallah saura kwana goma ita karan kanta batasan adadin wa'inda suka tambaye lalle ba ita dai ta amsa zatayi amma suzo da wuri, sannan tana musu tallan wanda zaiyi kitson sallah kanwar mijinta nayi ai kuwa khadija ma tatara customers sosai, kayan sallah ma bana muhammad ne ya d'auke sumayya da khadija har kasuwa sukayi sayayyan sallah duk da sumayya taki yarda ganin tana da wasu zanunuwan a akwatin ta amma ina yace na akwati daban na sallah daban, ba laifi yasai musu kaya itama ta dad'a wasu da kudin ta haka ma khadija ta kara mata har kala biyu bayan wanda ya musu she karan kansa gezena biyu yasaya sumayya ta kara masa biyu duk sunka kai dinki. Akwana A tashi yau dai saura kwana d'aya sallah kofar sumayya makil da jama'a daga masu kitso harda masu lalle, harda su suwaiban adara yau ana bin layi a kofar, sumayya na hango sanye da riga da wando baki tana ta fama da lalle sai khadija dake ma wata yarinya kitson brazil kulu da bit Har yamma mutane ne makil ba ita ta rabu da mutane ba sai kusan goma na dare nan ba hakuri ta basu akan gobe su dawo da asuba Al'ameen dake d'aki kwance yana lazimi shiya raka khadija gida Yau sumayya koh girkin asuba bata samu tayi ba na bud'a bakin ma watace ta mata girki tana ma yarta lalle Yauma bayan sunje tahajjud suna dawowa ne suka samu tuwo a bakin titi na asuba suka saya, dashi sukayi sahur Sumayya suna komawa gida suna sallah ta kwanta ai koh gama d'aukarta bacci baiyi ba tafara jin sallaman mutane ga idonta duk bacci kin tashi tayi Al'ameen ne ya fita ya basu hakuri akan sumayya na bacci Amma haka bayin Allah nan sukaki tafiya taburma suka shimfid'a suka zazzauna🤣suna jiran sumy(masu lalle gaskiya kuna ganin abu a sallah har kwana ana muku a d'aki) Surutun su shiya hana sumayya komawa bacci haka tanaji tana gani ta kasa bacci dole yasa ta fitoh jin jama'a sai dad'uwa suke Ai tana fita saiga khadija da tawagar masu kitso sun tasata a gaba😎 Haka suka dukufa suna neman halal nasu, Al'ameen fita yayi a d'akin sumayya! yakira sunan ta "Na'am"ta amsa tana mai mikewa ta bisa d'akin ganin ya koma Sumayya zan fita na karbo mana dinki, maganar zuwa kasuwan fa muna sa ran gobe sallah fa naga bamu shirya kome ba? "eh kam gaskiya nima naso naje kasuwan nan da kaina amma yanzun ba iyya fita zanyi ba sai dai ku tafi da khadija in yaso sai na rubuta mata list"? Ok nace na saya mana watanda ne?(naman shanu da ake yankawa a ranan jajeberi ana saidawa a unguwa) "Ah ah ka saya mana kaji gaskiya tunda sallah ne" Shinkafa koh tuwo zakiyi? "Habba tuwo ranan sallah, shinkafa zanyi da miya sai coslow da kaji sanan zanyi masa da miya" Ok daman so nake ranan sallan nan mu kaiwa gidan su Ammar abinci kuma muje mu gaida iyayen sa sai kuma nayi tunanin kar suce don kudin su yasa muke son rabansu fa? "Ah ah yayan khadija in zakayi abin Alkhari kayi kawai karma ka bari shaid'an ya saka maka wani tunani daban a ranka kaji"? Shikenan sumayya Allah ya kaimu goben kinyi lalle kuwa?yana maganar yana kama hannun ta "Ina naga lalle daga ni har khadija ba lalle ba kitso" Kai gaskiya nifa an takurani tun sallah saura kwana hudu ban sake cin abincin kiba ki taimaka ki mana girkin sallah da kanki "Insha Allah la'asar nayi zan sallami kowa wanda ya samu da wanda bai samu ba duk sai suyi hakuri nima na samu nayi aikin sallah" Ok kiramin khadijan inkin gama rubuta list in mu tafi Haka koh akayi sumayya list ta rubuta ta baiwa khadija duk yanda jama'a masu kitso suka ringa roko sai da sumayya ta d'aga khadija suka tafi kasuwa dinki suka fara karbowa sai cefenen da sukayi sosai sukayi cefene sai da ya cika bairo. Bayan khadija ta dawo sumayya tashi tayi ta gyara kajin duk da wasu sunso karba mata Amma taki yarda soya kajin tayi daman guda biyar ya saya ta rabawa mutane d'aya sosai tayi ta ayyukanta wasu kamma ganin aiki take kuma ba karewa zaiyi ba, zuciya kawai sukayi suka tafi abinsu wasu kam kama mata aikin sukayi duk da ta nuna su bari amma kin bari sukayi wasu sun gyara mata tattasai wasu sunkai nika cikin kankanin lokaci ta kammala had'a abubuwan sallan ta miya ma ta soya amma bata sa ruwa ba saboda ba'a tabbatar anga wata ba vegetables ma bata yanka ba tadai sasu a firij ne Bayan Ansha ruwa sumayya sallamar mutane tayi wa'inda bata musu ba ta basu hakuri wasu kuma sukace gobe koh jibi zasuzo Amusu Yau kam saida muhammad ya saya mata matsala 8 tasha tsabar yanda bayanta ke ciwo amma fa gaskiya ta samu kudi bana wasa ba a sallan nan khadija karan kanta kudi ta samu sosai Har dare ba'a sanar anga wata ba haka su sumayya suka kwanta da niyar inba'a gani ba zasu tashi da azumi Aiko hakance ta faru don da asuba ji sukai ana atashi ayi sahur jama'a gobe ba sallah bane😌 Ai yau kam sanin da sumayya tayi ba karamin mutane ne zasu zo ba yasa tana sallan asuba ta tattara boron lallen ta tayi gidan goggo Al'ameen ta bari a d'aki yana bacci tace masa zata saloon gyaran gashi sai tayi lalle tama khadija Gidan goggo taje tayiwa khadija lalle ja da baki itama tayiwa kanta sai dai bata ma hannun dama ba manna masa gam tayi khadija tasa mata lalle akai Lallen su na kamawa ita da khadija saloon suka wuce aka gyara ma khadija gashi don ita kam bata wanke kanta a sefe, kitso khadija ta watsa mata a saloon sai kusan la'asar sumayya suka dawo, kai taga ikon Allah jama'a ne tirem a kofar ta Al'ameen ya rufe kofar d'aki ya fita sukam suna zazzaune a baranda haka ba yanda ta iyya ta hau musu lalle Dayake ana da tabbacin gobe sallah ne yasa khadija had'a musu miyan sallah ta d'aura zobo tana gama had'awa ta juye a robobi tasa a firij muhammad ma ya turo kayan marmari da sumayya tace zata markad'a a blander tayi juice dashi Sai dare sosai mutane suka watse ita da khadija suka kai nikan shinkafa bayan sun dawo suka kwaba, yaukam khadija a gidan ta kwana da sumayya a waje yayanta na d'aki *RANAN SALLAH* yau take sallah ranar farin ciki ga dukan wani musulmi kowa ka gani fuskar sa d'auke da farin ciki hakan take a wajen su sumayya tun asuba khadija ta fara tuyan masa sumayya ma wuta ta hura ta d'aura shinkafa don yau dai ba'a gas koh hot plate za'ayi girki ba Vegetables inta ta kama yayan kawa su green beans green pepper yellow pepper piece cabbage carrot harda k'wai ta d'aura a wuta ga babban kwalban BAMA a zaune agefe karfe 7:30 sumayya sun gama girkin sallah, manyan kulolin ta masu shegen kyau, bata taba bude suba sai a ranan mai guda biyar ne ta zuba shinkafa masa coslow miyan ganye da miyan stew sai manyan manyan kofunan zamani ta juye zobo a ciki d'aya kuma mango juice duk sunyi sanyi har suna raba ta sake maidasu firij, wannan na gidansu Ammar kenan, sauran juyewa tayi a babban kula haka ma miyar duk d'aki ta shigar dasu sanin halin mutanen gidan Wanka tayi ita da khadija suka saka kayansu mai kyau da hijab Al'ameen ma gezena insa sabo ya saka koh sanda sumayya ta hanasa rikewa ita ta kama hannunsa khadija ta rike musu sallaya rufe kofa sukayi lokacin karfe 8:30 sauri suke karsu rasa sallah Suna fita a gidan sun tsaya a bakin titi amma ba keke koh wani keke suka tare a ciki haka suka fara takawa, kamar hadin baki saiga Ammar ya shawo kwana da motar sa packing yayi a gabasu hade da budewa ya fitoh sanye yake da wani d'anyen yadin shaddane mai kyau sai hula da takalmi agogonsa sai d'aukar ido yake. Ashe gwara danayi sauri tun d'azun ina ta tunanin bazan same kuba taima ? Laii Ammar kaine sannu ina kwana? Lafiya muahmmad barka da sallah. Ai ba'ayi sallar ba tukum, muhammad ya basa amsa "Ina kwana"?sumayya tace tana had'a fuska ganin yauma kamar kullum idonsa akanta Lafiya sumayya muntashi lafiya? "Lafiya mungode Allah" Khadija kam kuri tayi tana kallon sa toh a ina tasan bawan allah nan ne kam ta kasa tunawa, a hankali ta ma sumayya magana, aunty nikam a ina kukasan wannan ne? "Habba khadija kin manta mutumin da yazo asibiti lokacin da za'a mini tiyata ya baki kudi ki ban" Oh na tuna na tuna Aunty , ina kwana?tana gaida Ammar kin amsawa yayi hannun muhammad ya kama muje koh ku shiga mota muyi sauri karmu rasa sallah Ba musu dukansu motar suka shiga yaja suka kama hanyan masallaci Allahu Akbar anyi sallah lafiya jama'a kamar kasa suna ta fitoh wa a edi kowa ka gani fuskar sa a washe sai gaisawa ake da juna abin gwanin sha'awa kowa na sanye da sabin kaya sai dai na wani yafi na wani tsada Bayan su Ammar sun fitoh a cikin cunkoson jama'ar dake masallacin, yaso kaisu muhammad gidan su amma sukace ya maidasu gida zasu d'auko abincin da zasu kai gidan nasu Ba musu ya mai dasu gida abincin muhammad ya d'auko musu a kula ya fitoh waje dasu juice taburma ya shinfid'a musu ba kyama Ammar ya zauna sukaci abincin da muhammad sai santi hake don gaskiya abinci ne na kece raini Ta bangaren sumayya abinci ta sassaka a kwanuka ta baiwa khadija ta rabawa mutanen gidan ADARA kowa da plate nasa ta zubawa goggo ma ta kai mata tana dawowa sukaci abinci tukum kafun suka sake wanka lokacin azahar yayi sallah sukayi sumayya ta watsawa khadija make-up sosai khadija tayi kyau tana sanye da dogon riga na zani holland mai shegen kyau sai gyele da jaka tare da takalmi hada agogo da su sarka masu azaban tsada sosai sumayya ta kashewa khadija kudi a sallan nan Ita kam les tasaka sai mayafin ta babba powder kawai ta shafa sai kwalli da man baki don A matsayin ta na matar aure hakan baidace ba tayi kwalliya ta fita tana d'aukar hankalin maza Al'ameen ne ya shigo duba su sumayya sun gama shiryawa ne Ammar ya dawo yana jiransu "Don Allah yayan khadija ka sake wanka mana ka chanja kayan jikin kan nan"? Meya samu na jikin nawa? "Ba kome amma dai ya kamata ka chanja tunda gidan masu kudi zamu gwara mu kece raini" Kai sumayya kin cika shirme amma dai bara na watsa ruwan shap shap yayi wanka ya fitoh sabon gezena da sumayya ta d'inka masa shiya saka mai tsadane sosai sai takalmi da agogo yau harda glass sumayya ta d'auko tasa masa lias na hannu riga duk ta makala masa, hannunsa ta kama suka fitoh bayan khadija ta rufe kofar Kulolin suka d'auko guda biyar sai jup na juice da zobo duk suka jera a boot na motan Ammar Tunda sumayya ta fitoh idon Ammar ya sauka akanta gabaki d'aya ya tatara hankalin sa Gareta sai kallon ta yake kamar idanunsa zasu zazzago Sumayya kam tun fitowar ta ta lura da kallon da Ammar ke mata kamar maye duk d'aga ido da zatayi sai sun had'a ido ganin yanda duk yabi ya zuba mata na mujiya yasata juyawa da sauri cikin haushi tayi cikin gida Khadija dake kokarin shiga motar ganin sumayya tayi cikin gida yasa ta kwala mata kira, aunty sumayya kin manta wani abune? Sumayya koh juyowa batayi ba tayi shegewar ta ciki da sauri Al'ameen ya fita a motar jin khadija tace masa sumayya ta koma cikin gida yabi bayanta.......... 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 08146017245 *hohoho wani Kaya Sai amale shin kunsan kayatattun magungunan Mata na maman haidar* *Kayan maman haidar basuda matsala domin traditional medicine ne Kuma anahadasu da ingantattun itatuwa masu karfi da Basu da illah* 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 *1 Gumbar kankana da ayu* 🍀🍀 2 *Gumbar ayu zallah* 🍀🍀 3 *Gumbar Madara da kwakwa*🍀🍀 4 *Kaza mekwai* 🍀🍀 5 *Zabo me zuma*🍀🍀 6 *Kaza me allurai🍀🍀 sahihiyar mallaka ba boka ba malam*🍀🍀 7 *Kwallin idonka inadona*🍀🍀🍀 8 *Tauwadar mata*🍀🍀🍀 9 *ketar larabawa magani me kankarowa mace kima da daraja* 10 *Maganin sanyi me fatattakarsa duk kuwa nacinsa Koda bakya haihuwa indai matsalar sanyice gwada wnnn* 11 *Maganin nono. Sahihi* 12 *Maganin hips and bobbs* 13 *hodar. Ni I'ma koramar mata* 14 *nakasan Mara babban sirri* 15 *kafi jijjibi* 16 *daga Sha Sai wanka kasaitacce magani* 17 *Dan kwankwalati namata da mazajensu Kevin Mata* 18 *matsin kinfi budurwa dubu ko haihuwa nawa kikai Babu magana* 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 *Maman haidar Bata tsaya anan ba* *takawomuku hadaddan sabulun gyaran jiki da hadin dilka Mesa sheki da laushin fata gaman kitso Wanda laraba ke amfani dashi inkin gwada saikin dawo kudai kunemeta awannan number* 08146017245 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya* *Ibrahim* 🍃 ✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwa👌 free book 🤧 *Wannan page nakune Queen fauzee da ogan ki naga comment naki jiya*😂 Page5⃣8⃣&5⃣9⃣ Cikin gida yabi sumayya, yana kiranta amma koh juyawa batayi ba, har suka shiga kofar su Ke sumayya bake jinane, koh me? sai magana nake kin mini banza. "Na fasa zuwa kaban key na bude d'aki"? Akan me kika fasa zuwa, koh ince me akai miki, nadai san lafiya muka fitoh? Ba kome kawai dai na fasa ne, tace tana tunanin ta fad'a masa abinda Ammar ke mata, wani zuciyar kuma ya gargade ta, kartayi ta jawo wata rigimar kuma abanza. Ke sumayya koh ba magana nake miki bane, nace menene dalilinki na fasa zuwa ? "Nikam nafasa nace maka kuje kawai"? Akan wani dalilin? "Kaina ciwo yaka kuje kawai" Ai shikenan nima na fasa zuwa, bara nakira, khadijan ta dawo,yakarasa maganar da kokarin juyawa "Da sauri ta rike masa hannu"nifa ba ina nufin ku fasa zuwa bane,bafa" Ni kuma in bakije ba bazanje ba "Shikenan muje" Haka sumayya tanaji tana gani tabi muhammad suka fitoh waje, ido ta d'aga ta kalli Ammar Sunkuyar dakai Ammar yayi, tunda yaga fitowar su bai sake d'aga ido ya kalleta ba Shiga motar sumayya tayi, muhammad ma gaba ta bude masa ya shiga, ita da khadija a baya. Ammar motan yaja suka cillah titi,sai millionaire sweet khadija kam sai bin gidajen unguwan take da ido, kamar wata wawuya, tana d'aga ido, suka had'a da Ammar ta mirrow hararanta yayi ya kauda fuska A kofar wani makeken gida sukayi packing Ammar ya danna hon, da gudu maigadi yazo ya bude musu get, kusa hancin motarsa yayi zuwa ciki. Suna packing Ammar ne ya fara budewa ya fita da,sauri ya zagaya ya bude ma muhammad bangaren sa hannunsa ya kama, yatai maka masa ya sauko Sumayya ma budewa tayi ta fitoh ta tsaya, tana kallon khadija dake ta kalekale koh fita takasa "khadija menene haka bazaki fitoh bane"? Da sauri ta fitoh tare da d'an sosa kumatun ta najin kunya. Cikin gidan suka shiga, sumayya kam, koh d'aga ido batayi ta kalli waje sau biyu ba , gaban ta kawai take kallo, don ita wannan gida baikai ta masa kallon hauka ba Suna isa kofar falon Ammar yasa hannu ya bude,shiga sukayi bakin su d'auke da sallama Wa'alaikumu salam oyoyo laleemon bee warugo, wata bakar mata hajiya kyakkyawar gaske, kallo d'aya zaka mata kasan ita ta haifi Ammar,sai wasu yan mata guda biyu, da saurayi zaiyi sa'an khadija, duk suka mike ganin su sumayya sun shigo cikin falon. Murmushi d'auke a fuskar muhammad ganin yanda mutanen gidan suka taresu da mutunci,yauwa hajiya jam bandu, noi shumre yan julijam? Jam sai jam,muhammad?tace tana kallon sumayya dake tsaye, bismillah sumayya on jod'a mana? Ba musu sumayya tazauna akan d'aya daga cikin kujerun falon Ammar ma waje yanunawa muhammad ya zauna sai khadija da tuni ta dade da zama abinta. Gaisawa sukayi da hajiya, kannen Ammar suka gaidasu,Kayan ciye ciye aka jera musu a gabansu, dangin nama da kayan ci. Ammar ne ya aike kannen sa suka d'auko abincin da suka kawo a motar,sosai mamarsa taji d'adin ziyaran nan, abincin ma atake suka zuzzuba suna ci, sosai hakan yama sumayya dadi ganin basuda wulakanci koh jijidakai sam. Har yamma suna gidan sosai khadija ta sake sai hira take da yan matan, muhammad ma hira yake da Ammar da Abbas sabanin sumayya da hajiya keta janta da hira, itakam daga eh sai ah ah . Kai Aunty sumayya tsaya maimuna ta d'auke mu hoton sallah, khadija tace tana matsowa kusa da sumayya don tun d'azun hotona suke d'auka, ba musu sumayya ta mika wayarta iPhone wa maimuna ta dauketa da wayan. Da mamaki maimuna kanwar Ammar ke kallon wayan, da sumayya ta mika mata, koh su basu rike waya mai tsadan wannan ba, sai wannan da yayansu yace rayuwansu abin tausayi, Amma ita bata ga tausayi anan ba mata kamar balarabiya, ga aji, dajiji dakai, ga sutura mai tsada irin wanda mom in su ke sawa, Karba tayi khadija da sumayya suka gyara ta fara d'aukarsu hoto Ganin maman Ammar tabar falon, yasa sumayya tashi ta kamo hannun Al'ameen ta jashe zuwa d'aya kujeran suka zauna, dafa kafad'arsa tayi "maimuna d'auke mu pls hoton yayi kyau Ai da gudu khadija ta dawo bayan kujeran ta tsaya, daman 1siter ne Al'ameen azaune akai, sumayya a hannun kujera, ita kuma ta tsaya a bayan kujeran, d'aukarsu hoto maimuna take duk da muhammad ba kallo yake ba, Amma dai hoton yayi kyau, saidai ba camera yake kallo ba TikTok maimuna ta shiga ta kunna waka, tana musu vedio sosai yayi kyau, fa'i ma shiga tayi da Abbas kannen Ammar, duk sun shiga vedio abu da iphone ga background, ba karamin kyau sukayi ba, Ammar ne kawai bai shiga ba. Sai dare maman Ammar ta barsu suka tafi bayan sunci abincin dare, da suka tashi tafiya turare da zani ta baiwa khadija, sumayya kam sarka mai kyau ta bata fari, sosai sukayi godiya. Tunda suka kama hanyan dawowa, sumayya ta lura akwai abinda ke damun mijinta, ganin yanayin sa ya sauya sosai. Bayan sun dawo gida, har gida Suka raka khadija,ruwa ta iba takai band'aki ganin yanayin Muhammad, kamar ba lafiya, gabaki d'aya yayi laushi kamar bashi ba"yayan khadija nakai maka ruwa, koh zakayi wanka"? Toh,kawai yace yana mikewa,wankan ya shiga koh towel bai d'auka ba, saida sumayya ta kai masa Bayan ya fitoh wanka d'aure yake da towel, daga kagan sa, kasan ba lafiya,a hankali yake tafiya yana dafe da kirjin sa, yashigo d'akin. da sauri sumayya ta bisa da kallo,dayake yanzun basa shakkan juna, sosai bakaman daba,yasaka ta tube kaya a dakin, towel nata ta d'aura ta fita, ban d'aki ta shiga tayi wanka, fitowa tayi ta shiga dakin da mamaki take kallon Al'ameen, ganinsa har lokacin zaune koh kaya baisa ba yayi tagumi. Al'ameen dake zaune ji kawai yayi sumayya ta kamo hannunsa,A hankali tayi magana "yayan khadija lafiya"? Janyota kawai yayi gabaki d'ayanta ta fado kansa, a hankali ya sa hannu ya dad'a mannata a jikinsa. " yayan khadija bansa kaya ba"? Na sani sumayya ai naji jikin ki d'aure da towel. "Meke damunka"? Zuciya ta ke dokawa da karfi, sumayya inaji a jikina akwai wani babban Al'amari dake tinkaro ni. " kamar ya"? Sumayya zuciyar kowa na bugawa, sannan wani sa'in mutun najin zuciyar sa na luguje, Kamar yaji tsoro,koh baida gaskiya,koh yayi laifi. "Hakane" Amma ni wannan bugun zuciyar bana tsoro koh fargaba bane. "Name kenan, bangane ba"? Lumshe ido yayi yana kara manna sumayya a jikinsa,irin wannan lugujen na ringaji lokacin da mami na zata bar duniya, Aranan haka na wuni da lugujen zuciya. Haka ranan da zan makance, ma irin bugun nan na ringa ji, haka ranan da salim zai bar duniya,sumayya inaji a jikina akwai abinda zai faru dani duk da bansan gaibu ba. "Subahanallah insha Allah ba abinda zai tinkare ka sai Alkhari" Insha Allah....Sumayya! "Na'am yayan khadija" Don Allah sumayya, yau ki bani hakkina, sosai nakejin wani irin matsanacin bukata, tun da yamma............. Ta bangaren hajiya kami, kamar yanda boka yace, haka ta d'auke mujiya har cikin gidansu, bayan ta saka kejin a buhu, a d'akin ta ta ajesa a karkashin gado, kamar d'a haka take masa jinya, A washe garin ranan da sumayya zata fara period, a daren ranan, Alarm kamila tasaka a wayan ta, da misalin karfe 2 na dare ya tashe ta, mikewa tayi a hankali ta bude kejin zata d'auki mujiya. Da wani irin mugun sauri taja baya tare da zaro ido.....mujiya ne tayi mushe, bakinta har rawa yake ta d'auki waya, lalubo number Harira tayi, ta kara wayan a kunne Ta bangaren Harira kam,tana tsaka da baccin ta,don a silent ta saka wayar sam bata san ma, wata kamila na kiranta ba Jifa kamila tayi da wayan,jin Harira bata d'auka ba Washe gari da sassafe koh karyawa,kamila batayi ba ta ciccibi mushen mujiyan nan, tayi gidan Harira,don wallahi ta kudurta A ranta bazai yuba, bazata kashe kudi abanza ba, sai an biyata kudin ta, haka kawai ita ba muhammad ba, ita kudin ta ya tafi Koh sallama babu ta shigo falon Harira, tana kwala mata kira. Da sauri mijin harira ya d'ago, yana kallon kamila, lafiya baiwar Allah? Lafiyar kenan, ina Harira? Kafun ma yayi magana, harira ta fitoh daga d'aki cikin mamaki jin muryan kamila da sassafen nan, kamila lafiya? Lafiyar kenan, kika gannin nan,wallahi kinji na rantse bazanyi asaran kudina ba, kin sanni bani da mutunci tam. Da sauri Harira ta kamo hannun kamila, sukayi wani d'aki dake cikin falon, ganin mijinta a zaune a falo, kamila ke kokarin tona mata tsilili Ke kamila bana son iskanci kinji koh, zaki zo mini gida da sassafe,agaban mijina kina kokarin zubar mini da mutunci. Au mijin da kikace kin shanye ne, har zakiji tsoron yasan wani abu a game dake? Ji hauka toh don ka asirce, mutum sai akace ka fad'a masa ka masa asiri ?ji mahaukaciya Ke duk ni ba wannan ba,mujiya ta mutu, tana boot na mota na,ki wuce mu koma inda muka karbo she, yaban kudina in yasan bai iyya aiki ba, mena karbamin kudi(daman wannan halin kamila ne indai akan kudin tane bata da mutunci) Ke da sassafe, koh karyawa banyi bane, zan kama hanyar mutum biyu,toh baki isa ba, don uwarki ni, xaki tsaya kina bawa umurni. Ganin Harira tad'au zafi, daman ita bata iyya fushi ba sam, yi hakuri Harira raina ne ya baci, don Allah ki taimaka,mu koma wajen mutumin nan. Ki jirani nayi wanka, na karya saimu tafi? Ok kawai tace tana zama,abakin gadon d'akin ta zabga tagumi. Sai kusan 9 suka d'auki hanya, gabaki d'aya kamila sai masifa take, akan malamin bai iyya aiki ba Bayan sun isa,aje masa kejin mujiyan, kamila tayi a gabansa D'aukar mujiyan yayi ya kakkala, yanka cikinta yayi ya fitar da layan,warwarewa yayi atake, yaga rubutun sunan sumayya ya kone murus, kamar wanda aka saka kalanzir da petur aka banga masa, d'aga ido yayi ya kalli kamila. A gaskiya raba Wa'innan ma'aurata baban matsalane, don asirin da aka musu mundin aka rabasu, xa'a iyya samun matsala aikin wasu warware wa zaiyi,gashi sun rike ibada sosai,koh wajen kofa da Aljan zai kusance su sun tushe sa,makiyansu na tare dasu, tabbas suka gane akwai mai kokarin bata musu shiri,zasu iyya ganin bayanki don su mutuwa koh Rayuwa,agunsu don cika buri ba kome bane. Ina mai baki shawara,kamila ki hakura da kokarin rabasu,kidai nemi wani hanya da zaki malleke sa, Amma banda asiri tunda kika ga nayi iyya kokari na ba'a dace ba toh ki hakura. Wani irin na hakura,sai dai kace baka iyya aiki ba, kuma maganar kudina, Amaida min tunda aiki baici ba. Keeeeeeee!!!! dakata, bamason rashin kunya a wajen nan,inba haka ba wallahi zamuyi maganin ki, nan ba wajen shirme bane, kuma kudi inya shigo baya fita Ganin tana kokarin magana,yasa Harira matse mata baki Buge hannun Harira kamila tayi,don gabaki d'aya ranta ya gama baci,sosai zuciya ya ibeta,kai bokan banxa, bokan wufe mai karyan aiki,yana cin kudin mutane,wallahi baka isa kace zaka dakeni ka hanani kuka ba, kudina ne sai ka bani,tunda aiki na baka, kuma aiki baiyi kyau ba,kai harka isa kace zaka min abinda Allah bai mini ba? O' kinsan da hakan ne,kikazo guna yau saina nuna miki aikin, nakan dutse gaskiya ne, wani irin maganganu yayi take kadangaru dake manne a jikin kokon,guda goma suka ruga da gudu zuwa jikin kamila, ai kam da sauri suka manne mata a jiki, daman dogon riga da d'an karamin gyele ta yafa, biyar sukayi kasan dogon rigan suka mamakale mata a cinya wasu sukayi cikinta wasu kan breast inta, suka makale wasu kam gashin kanta suka shiga suka kwanta. Ai wani irin ihuuuu Harira ta sake, da gudu tayi waje, kamila kam wani rin tsalle tayi ta bugu da kasa hade da kurma ihu, tana bawa nakan dutse hakuri,amma ina koh kallon ta baiyi ba,jin kadangarun manne a jikinta, kamar sun samu jikin gatanga, yasata yarda d'an kwali da takalmi da gyele,da gudu ta ruga tayi waje tana ihu, jinsu sai yagushinta suke, b'anb'arawa tayi da gudu harta wuce, Harira data dade da fita,cikin gari ta fitoh tana ihu tana kokarin kwabe riganta Allah yasa akwai brz da dogon wando Ai jama'a salati suka d'auka, ganin kadangaru mammanne,a jikin kamila gashi duk inda ta wuce sai wasu kadangaru dake wajen,sun bita da gudu,ai itama saita kwasa a guje suma suka bita gayya guda a baya Duk mai imani inya kalli kamila saiya tausaya mata, wasu kam sai Allah kara suke mata jin tana sambatun, mugun abinda taso aikatawa hakan ya faru da ita Harira batabi dakan kamila ba,duk tabi ta tsorata motar taja sai jala. Tana isa gidan su kamila ta wuce direct, tana kuka ta sanar, da iyayen kamila abinda ya faru, sosai hankalinsu ya tashi, hade da tsinewa Harira,su sunsan yarsu batasan wajen boka ba Harira ne ta kaita A take suka tasa keyar Hariya zuwa mutum biyu, suna isa ake sanar dasu ai kamila tayi daji,don gudu take kadangaru na binta, da gudu iyayenta suka nausa hanyar da aka nuna musu kamila tabi. Kamar wasu zararu haka suka fasa daji, suna neman kamila,Acan gindin wani bishiyan kuka,suka ganta zaune sai ihu take tana kama kadangarun dake jikinta tana hurgarwa, da gudu zasu dawo su like mata, gabaki d'aya katangaru ne a mammanne a jikinta, wasu suna manne da jikin bishiyan da take kai, saboda basu samu fili ba abin gwanin tausayi gabaki d'aya ta zareeee. Maman ta kam kwala kara tayi, tayan ke jiki ta fadi, da gudu baban ta yayi wajen da niyar kamo yarsa, duk da kadangarun sun matukar bashi tsoro, amma haka yayi ta maza Ai kadangarun nan,na kallon baban kamila na tahowa da gudu suka zabura, sukayi kansa Ganin kadangaru sun juya garesa,yasa sa b'anb'arawa da gudu yakoma baya,suma koma sukayi inda suke kamar da Ganin Halin da maman kamila take ciki, yasa Harira da baban kamila,d'aukarta yayi suka fitoh cikin gari da ita,asibitin mutum biyu suka kaita, bayan an bata gado,waya baban kamila yayi ya kira maman sa, da yan uwansa ya sanar dasu abinda ke faruwa, Harira taso fecewa,Amma baban kamila yace ina, kafarsa kafar Harira in Harira taga tabar mutum biyu toh da kamila za'abar garin............. 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 08146017245 *hohoho wani Kaya Sai amale shin kunsan kayatattun magungunan Mata na maman haidar* *Kayan maman haidar basuda matsala domin traditional medicine ne Kuma anahadasu da ingantattun itatuwa masu karfi da Basu da illah* 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 *1 Gumbar kankana da ayu* 🍀🍀 2 *Gumbar ayu zallah* 🍀🍀 3 *Gumbar Madara da kwakwa*🍀🍀 4 *Kaza mekwai* 🍀🍀 5 *Zabo me zuma*🍀🍀 6 *Kaza me allurai🍀🍀 sahihiyar mallaka ba boka ba malam*🍀🍀 7 *Kwallin idonka inadona*🍀🍀🍀 8 *Tauwadar mata*🍀🍀🍀 9 *ketar larabawa magani me kankarowa mace kima da daraja* 10 *Maganin sanyi me fatattakarsa duk kuwa nacinsa Koda bakya haihuwa indai matsalar sanyice gwada wnnn* 11 *Maganin nono. Sahihi* 12 *Maganin hips and bobbs* 13 *hodar. Ni I'ma koramar mata* 14 *nakasan Mara babban sirri* 15 *kafi jijjibi* 16 *daga Sha Sai wanka kasaitacce magani* 17 *Dan kwankwalati namata da mazajensu Kevin Mata* 18 *matsin kinfi budurwa dubu ko haihuwa nawa kikai Babu magana* 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 *Maman haidar Bata tsaya anan ba* *takawomuku hadaddan sabulun gyaran jiki da hadin dilka Mesa sheki da laushin fata gaman kitso Wanda laraba ke amfani dashi inkin gwada saikin dawo kudai kunemeta awannan number* 08146017245 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya* *Ibrahim* 🍃 ✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwa👌 free book 🤧 Page6⃣0⃣&6⃣1⃣ Da sauri ta d'ago kanta jin yanda yayi maganar a matukar sanyaye, kamar wanda zai nemi Alfarma itafa halaliyar sace,amma ga yanda yake had'ata da Allah, yayi matukar kokari, yanzun ana neman kusan wata uku da auren su, koh ma fiye da haka, ba tare da ya taba tilasta ta akan hakkinsa, kullum ya bukace hakan, zata saka masa kuka, koma hakan koh baya so yake kyaleta. Jin batace kome ba yasa sa lalubar fuskar ta,In baki Ra'ayi kiyi hakuri sumayya,na hakura. Da sauri ta kamo nasa fuskar hawaye na cika mata ido, "yayan khadija hakkin kane fa?kaima da kanka ka fad'a, kaga kenan ni bani da damar hana ka, tunda naka ne, duk abinda zaka bukata a gareni mallakin kane, na amince kayi duk abinda kake so dani, ta karasa maganar da fashewa da kuka. Jin ta fara kuka yasa muhammad, da sauri yace, sumayya kiyi hakuri nama hakura, shikenan tashi kisa kayanki mu kwanta. "Ba kuka nake ba" Hannu yasa ya shafo kumatun ta, toh me kike, kuma menene a fuskar taki? "Kayi hakuri" Fuskar sa ya had'a da tata fuskar, baki min kome ba sumayya. "Toh insa kaya koh haka xamu kwanta" ? Shikam ba karamin dariya sumayya ta basa ba harya kasa hakuri, saida ya dara, hhh menene haka kuma sumayya? "Toh ba tambaya nayi ba, koh tambaya laifine"? Ah ah ba laifi bane, yace yana d'aura fuskarsa a kafadar ta, yana goga mata gemunsa. A hankali sumayya ta manne masa gam a jiki, hannu tasa ta kama gashin kansa, jin kamar zai zautar da ita, jin bakinsa akan wuyan ta. Ahhhh, yace yana kamota, d'agota yayi gabaki d'ayan ta, yana lalube harya hau gadon, kwantar da ita yayi ya hau kanta, bakinsa ya jona cikin nata, sosai yake tsotsar bakin ta, jikinsa sai rawa yake. Sosai sumayya ke tare da farga ba, don yanayin muhammad kawai yau zai tabbatar maka, da gaske yake son Angon cewa. Washhh Ashhhhh sumayya tace, lokacin da taji muhammad ya yaye mata towel in jikinta, shima tuni ya watsar da nasa daga ita harshe babu sutura a jikinsu....... Zafafan Romance Al'ameen yake wa sumayya, da zafi zafi don A lokacin bazaka taba tunanin koh baya gani ba, aikin dake gabansa kawai yake. Sumayya dake kwance rumtsa ido tayi, jin Al'ameen na ware mata kafa, bakinsa d'auke da Addu'an saduwa da iyali Kara ta kwala da karfi, tare da ware ido, jin wani Al'amari mai girma daya ratso rayuwarta, a karon farko hannunta dake free, ta d'aga a zabure ta cakumo gashin kansa. Da karfi ya fizgo Hannunta, daga gashinsa ware hannun yayi ya danne da jikin katifa, sosai ya kara bada himma akan abinda yake, bai taba d'aukar zaiji wani d'adi ba tunda Abbajon sa ya barsu, wahalar rayuwa bai barsa ya tuna akwai wani dadin da zai iyya d'and'ana wa, maka mancin wannan dadin ba, sai gashi yau sumayya ke shayar dashi. Sumayya kam gumi ta had'a sosai, duk da an fara yayyafi, Amma daga ita har muhammad zufane ya jikasu, sosai sumayya ke kuka tana goga kanta da jikin pillow, ba zafin da Al'ameen ke d'and'ana mata bane yafi ratsata, wani irin sarawa taji kanta nayi kamar wance ake fisgar gashin kanta da karfi, haka takeji a kanta kuka tasa, don abin ya hade mata biyu, ga azaban da Al'ameen ke gana mata sosai, kanta ke bugawa ji take kamar kwakwalwarta zai fita, sai salati take tana murza kan da filo. Ta bangaren Al'ameen kam, yau ba'aji ba'a gani am amsa sunan MAKAHO yau, don koh kukan sumayya baji yake ba, hankali..sa na gefe, damuwar sa kawai yaji abinda yake gabansa. Sumayya jin wasu irin bugawa da kanta keyi akai akai jijiyoyin kanta takeji kamar zasu tsinke, koh gani bata iyyawa yanzun sosai, duk da a duhu suke Amma duhun da take kallo yanzun yafi karfin duhun d'akin. Sosai bakin ta ya bushe, sai shakuwa take, tana kiran ruwa da muryarta da baya fita sosai. Amma ina muhammad baisan tanayi ba abinda yasa agaba yake fama. Jan numfashi sumayya tayi da karfi jin wani irin wahalallen shakuwa, ya gudu da numfashin ta duka, sakewa tayi jagab ta koma jikin filo, Muhammad bai farga da halinda sumayya take ciki ba sai da ya gama samun nutsuwa, A hankali ya zare jikinsa a nata, aiji yayi kamar an watsa masa Allurai a idanun sa, soki yakeji a cikin kwayan idonsa, sunfi d'ari rumtsa idon yayi da karfi, yana kiran sunan Allah jin wani irin barkono da soki na cakansa, tunda yake bai tabajin azaba irin wannan ba, kansa ya had'a da jikin gado da karfi ya buga ji kake gauuuuu ...........ya sulale kan katifar baya motse. Har Asuba muhammad da sumayya suna sume, basu farfado ba, babu wanda yasan halinda suke ciki, sai mahallincin mu, A Hankali sumayya ta fara motse, a hankali take kokarin bude idanunta, sai kuma ta maida su ta rufe da sauri, jin wani irin nauyi daya mata, sai da tafi minutes 10 kafun ta sake bude idon, a hankali harta budesu duka, ware idon tayi tana kallo dishi dishi har idanunta suka sauka akan muhammad, dake yashe a gefe ga goshin sa a fashe. Cikin matukar razana ganin sa kamar wani matan ce, haftowa tayi da kuzari zata mike, kara ta sake tana Ambatan sunan Allah, ta koma ta kwanta jin wani irin rad'ad'i dake ratsata, ta kasa A hankali ta mike zaune, tana cije lebenta, ta fara rarrafawa zuwa garesa, matsowa tayi sosai ta tattabasa jin baya motse, yasata sake kara"innalillahi wa'inna'illahi raji'um nashiga uku, don Allah muhammad karka tafi ka barni wayyo nashiga uku, wayyo mijina na bonu,ganin kamar suma yayi, sai kuma ta rarrafa da sauri taja blanket in ta rufe masa jiki, da rarrafe ta sauka akan gadon, towel inta dake yashe a kasa ta d'auka ta d'aura. Firij ta wuce ta d'auki ruwa, haka ta rarrafa ta iso bakin gadon ta saitin da yake, hannu tasa ta bude bakin goran, ta tsiyaye ta wasa masa a fuska, Amma ina shuru muhammad bai tashi ba, kuka ta sake tana bulbula masa ruwan sanyin a fuska, Amma koh motse baiyi ba,"wayyo muhammad wayyo mijina, na shiga uku Allah ka taimake ni" A matukar gigice ta saka kunnen ta a kan kirjinsa, jin zuciyarsa na bugawa, yasa hankalin ta kwanciya don ta gane suma yayi. Tunawa tayi da number maimuna kanwar Ammar, a wayan ta koh ta kirata ne? ta had'ata da Ammar koh Zai taimaka mata mijinta ya tashi tunda itama, tana bukatn taimako, gashi bata san wazata kira ya tallafa musu ba. Da rarrafe ta isa kusa da wayan d'auka tayi jikinta sai bari yake, ta kira maimuna tanajin ta d'aga tace"Assalamu Alaikum" Wa'alaikumu salam Aunty sumayya ina kwana? "Lafiya maimuna don Allah Ammar na gida"? Lafiya kam aunty sumayya, naji muryan ki a dishe? " nace miki Ammar na gida"? Ah ah wallahi yau yabar gari da asuba lfy? Kashe wayar in sumayya tayi, don bata da lokacin maimuna. Da sauri wani tunanin yazo kanta, ta rarrafa ta isa wajen kayan sa, budewa tayi tana ciro masa kaya, in yaso sai ta saka masa, ta fita ta kira keke su tafi asibiti, duk da ba lafiya bane da ita, koh da rarrafe zata fita ta taimake rayuwar mijinta. Kayan sa ta bude ta, dauko jallabiya tayi ta aje, tasa hannu zata d'auki gajeren wandon sa, taji hannunta ya taba wani abu mai karfi kamar gidan agogo, hannu tasa ta zaro abin, haka kawai taji hankalin ta bai kwanta da wannan karamin akwatin ba, hannu tasa ta bude. Da sauri ta rufe Idanun ta ganin wani irin haske daya kashe mata ido,A hankali ta sake bude ido ta kurawa sarkan ido, yayi haske yasa ke mutuwa farine sosai, mai kyau sai zanen zaki dake tsakiyar gaban sarka, sosai sarkan ke sheki yana komawa normal. Jiki na bari ta rike sarkan, indai bata manta ma Al'ameen yace baban shi ya basa sarka, koh dai wannan ne sarkan? menene dalilinsa na cirewa? a wuyansa, rarrafe tayi ta isa garesa, sarkan ta d'auka ta d'aura masa a wuya. Ai sarkan nan na shiga wuyan Al'ameen, ya wani irin haske sosai sai kuma ya koma normal bai sake hasken ba. Da rarrafe sumayya ta fita a kofar dikin"subhanallah"tace ganin har rana ya fitoh don lokacin ana neman, kusan karfe 8:00 na safe koh sallan asuba basuyi ba,da rarrafe ta shiga kitchen kittle ta jona a soket, tana zaune a wajen ya tafasa juyewa tayi a boket, ta sake saka wani saida ta juye kittle uku,sannan ta fara kokarin mikewa,don d'aukar boket in ta juye a band'aki, Amma ta kasa, kuka kawai ta sake, ta koma ta zauna. Muhammad kam tunda sumayya ta fita a d'akin ya farka, sosai idanunsa ke masa zoge kamar an kwakule masa su,tun d'azun yana kwance don duk jikinsa a sake yake. Da sauri ya mike zaune jin kukan sumayya ta window, sai yanzun tunanin abinda ya faru ya fado masa,take yaji tsikar jikinsa ya miki, hasbinallahu wani'imal wakin, yace yana mikewa zaune, dafa kansa yayi da karfi jin wani irin rad'adi a inda ya buge, a haka dai ya lallaba ya mike zaune, jin baida sutura a jiki yasa sa fara laluben gadon, ji kawai yayi hannun sa ya taba wani abu damshe damshe, ga karnin jini. Da sauri ya mike, sauka yayi ya d'auki wando a cikin kayansa ya saka, yana dafe da kansa har lokacin idanunsa a rufe suke. Sumayya!!!sumayya!! Menene?yace yana karaso wa kusa da ita. Ai barin kukan sumayya tayi, ta zare ido ganin Al'ameen akan kafafunsa, hannu tasa ta kamo nasa hannun"na kasa tashine, ga rana yayi bamuyi wanka ba, gashi ina son kai ruwa band'aki na kasa, gashi ka suma hankali na ya tashi"tana maganar tana kuka. Rungumar ta muhammad yai da karfin gaske, A hankali ya bude baki daker, kamar yanajin tsoron magana, sumayya ina sonki, sumayya ina tsananin kaunar ki, bazan taba mantawa da daren jiya a rayuwa ta ba, har abada kece cikon farin cikina, ina fatan har in koma ga Allah, karna miki butulci matata. Kara rungumar sa tayi sosai, taji wani sanyi a ranta da tausayin mijinta"nima babu abinda zance maka sai dai na mana fatan gamawa da duniya lafiya, mijina har abada bazan taba barin kaba harsai ranan da na daina numfashi in Allah ya yarda. Toh bakice kina sona ba? "143" Meyake nufi? "Kayi tunani mai zurfi, wanka nakeso nayi nayi sallah, rana yayi ka kaimin ruwa bayan gida" Toh yace yana saken ta, boket na ruwan zafin ya d'auka, yana tafiya har lokacin idanunsa zafi suke masa, kuma bai bude suba. Bayan ya aje ruwan, dawowa yayi ya ibi na sanyi a wani boket in daba. Sumayya dake zaune har lokacin a dakali"ga baf a kitchen ka kaimin ban d'akin"tace masa Haihuwa kikayi ne wai gimbiya? "Mutuwa nayi" Insha Allah ba yanzun ba, yace yana d'aukar boket in, kaiwa yayi band'aki yana fitowa, sumayya dake kan dakali ya ciciba yayi bayan gida da ita, ajeta yayi. "Toh ka fita mana, waima menene naga ka rufe ido yaukam kaki budewa"? Idanun ciwo suke mini, yau kamar borkono a ciki. Uhmm kawai sumayya tace tana had'a ruwan wanka, duk yanda taso muhammad ya rabu da ita ki yayi shiya taimaka mata tayi wanka, ya d'auko mata wani towel in, ta d'aura ruwa ya cika a buta ya bata tayi Alwala. Shima wankan yayi ya fita a d'akin har lokacin idanunsa a tamke, yayi Alwala yashiga d'aki, zuwa lokacin sumayya tayi sallah tana zaune tana lazimi. Bayan ya idar da sallan, a hankali yasa hannu ya shafo sarkan wuyansa da mamaki ya kalli sumayya, gimbiya yanaga sarka a wuyana kuma, ke kika d'auko koh? Da mamaki sumayya ke kallonsa, yau kuma gimbiya ta zama kenan"eh nina saka maka, kace babanka ne ya baka sannan baka sakawa, akan me"? Sumayya naki saka sarkan nan ne, dom sau biyu ana kokarin fizgesa a wuyana,shiyasa na daina sawa. "Kamar ya ban gane ba"? Wallahi barayi mana, kaje kasuwa xaka saida abu anki saya, Amma barayi na kokarin sata. "Allah ya kyauta , wai bazaka bude idon bane" Ba musu yad'an fara kokarin, bude idon a hankali a hankali harya budesu duka. "Ya illahih"sumayya tace lokacin da idanunta ya sauka akan kwayar idon muhammad, yayi jajazur kamar jini zai digo, inka ga idon zaka d'auka koh buga masa shi akai jini ya taru. Sumayya menene naji kina salalami? "Ba kome, yayan khadija kaga idanunka kuwa"? Taya zan gani, bayan ba gani nake ba, me idon yayi? Wallahi kamar jini zai digo jajazur" Kuma Nima rad'adin da nakeji sosai fa. Allah ya kyauta, bara naji sauki sai muje asibiti, Amma dai yanzun, kaje chemist ka siyo mini magani rage rad'adi, kaima saika sayawa kanka naga, har wajen ya kumbura"? Gaskiya ne, kannawa ciwo yake wallahi, gashi ma yunwa nake ji, kema nasan kinaji bara na had'a duka nasai mana. Nikam bazanci kome ba, ka biya shago kawai ka d'auko mini lemo, bakina d'aci, ka tura a kira khadja tazo tad'an gyara mini kofar, nikuma bara nayi sauri na fitar da zanin gadon ya baci sosai" Toh ki zauna kawai tunda tafiyar taki batayi kyau ba, bara na jika zanin gadon inna dawo zan wanke? yace yana fita a d'akin bayan ya d'auki zanin gadon, waje muhammad ya fita bayan yakai zanin gadon band'aki, tsallake titi yayi, yaro ya samu ya aika gidan goggo, a kira masa khadija, shikam ya wuce chemist in jambusko. Yana isa chemist yasamu layi dole ya zauna har akazo kansa, maganguna ya saya harda wanda zai diga a ido, yabi shagon sa lokacin har shagari ya bude, d'aukowa sumayya lemon yayi, yasai abinci duka yana rike da laidodin a hannunsa har lokacin idanunsa rad'adi suke masa. Yazo tsallaka titi kamar daga sama yaji mota yayo kansa gadan gadan da gudu ya fara kokarin kauce wa, Amma ina saida suka cin masa, kamar zasu kadesa, amma suna zuwa kusa dashi suka ja birkiii Sosai ya tsorata sai kiran sunan Allah yake, wasu kattai hannun su d'auke da bindigogi, suka fitoh a motar duk sun rufe fuskokin su da mask........🍀 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya* *Ibrahim* 🍃 ✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwa👌 free book 🤧 Page6⃣2⃣&6⃣3⃣ Kamo muhammad sukayi, suka d'aga sa sama suka tura a mota sai ihu yake yana ataimake sa, amma ina mutane kowa gudu yake kar a had'a dashi, muhammad naji aka turasa a mota suka ja.... Khadija data tsallake titi, ganin yayan ta yasata tsayawa tana jiransa ya tsallako su karasa gidan tare,kamar a mafarki take ganin abinda ya faru da d'an uwanta, ihu tasa ta ruga a guje ta tsallaka titin kafun ma ta isa garesu tuni sunja motar sunyi gaba, kuka ta sake sosai tana a taimake yayan ta sai a lokacin jama'a suka fara dawowa. Sosai surutu ya tashi a unguwan anata bawa khadija hakuri wance ke kuka kamar ana tsikaran ranta da tsinke, wasu kam maida zancen yanda ya faru suke, khadija dake duke tana kuka taji an dafa ta, d'agowa tayi da sauri tana kallon sa. Lafiya khadija mai ya faru naga mutane na tare a bakin titi, gaki kina kuka kuma? Wayyo shagari yayana barayi suka sace, duk sun rufe fuskar su da mask, tana maganar tana kuka. Innalilahi wa'inna ilaihi raji'um yanzun fa yabar shago, ya d'auki lemo, yake sanar dani yau bazai fitoh ba na zauna a shagon, saida ya fita naga ashe ya manta bai d'au maganin daya shigo dashi a hannun sa ba, shine na biyo na kawo masa, yana maganar hawaye na zuba, Khadija mikewa tayi, har tana ganin jiri jiri shagari yana rike da ita da taimakon sa suka koma gidan goggo, don bazata iyya zuwa gun sumayya ba a halin yanzun da take cikin nan . Assalamu Alaikum,shagari yayi sallama a kofar gaggo. Wa'alaikumu salam, lafiya me zan gani meya samu khadijan? Zaunar da ita shagari yayi a hankali, shima ya zauna akasan koh kujera bai nema ba tsabar tashin hankali, khadija na kuka shi kuma yana hawaye duk da yana namiji Amma b'atan muhammad ya shiga jikin sa. Kun zauna kuna kuka bazaku fad'amin abinda ya faru ba, gabaki d'aya kunsa raina sai tsinkewa yake?goggo ta fad'a jikin ta na rawa har zani na kuncewa. Goggo wallahi oga Al'ameen ne, wasu sukazo suka d'auke sa? Kamar ya suka d'auke sa bangane ba? Eh ina ga kidnap ne fa. Kidnappers kuma wani irin yan garkuwa da mutane, kuma muhammad ina yaga kudin da yan garkuwa zasu sansa, sai kuma ta fashe da kuka, na shigesu ni Amina, ya Allah ka taimake wannan bawa naka ka tsaresa a duk inda yake, Albarkacin Annabi da Alkur'ani. Ameeen goggo, shagari yace yana dafe kansa koh mutuwar mahaifin sa baiji tashin hankali irin nayau ba koh don baban nasa ya rasu baiyi wayo sosai bane sai Allah. Goggo Aunty bata sani ba, ina tsoron kar wani yakai mata labari tazo ta d'aga hankalin ta, gwara dai ke, ki sanar da ita goggo. Hakane khadija ki daina kukan ya isa haka, addu'a yake bukata ba kuka. Dole nayi kuka goggo, shikad'ai nake dashi, nake gani hankali na ya kwanta, yau an waye gari bansan halinda zai shiga ba. Kiyi hakuri khadija, bara naje gidan yayan naki, na samu sumayya. Toh goggo, kawai tace tana cigaba da kukan ta, shagari ma mikewa yayi kamar ruwa ya cisa yayi waje. Ta bangaren sumayya kam bayan fitan muhammad, kwanciya tayi haka kawai takejin faduwar gaba, for no reason, har bacci ya d'auke ta. Goggo tunda ta fitoh gidan ta, sai zulumin ta ina zata fara sanar da mace an sace mata miji, amma dai gwara ita ta fad'a mata dataji a wani wajen, tana shiga gidan koh bi takan kofar yan uwan ta batayi ba,cikin kofar sumayya tayi tana kwala sallama. Sumayya dake tsaka da bacci ne, ta farka jin sallama ake, Amsa wa tayi, ta sauka a kujeran a hankali tana dingishi don yanzun dai Jikin da sauki tunda, ta shiga ruwan zafi. "Laaa goggo sannu da zuwa, bismillah goggo ki shigo" Ah ah sumayya kedai bari zan zauna a wajen, ban kujera kawai. Kitchen sumayya ta shiga zata d'aukowa goggo kujera, da ido gaggo ta bita koh ita yarinya ne ta fahimce meke faruwa. Hawaye ne ya shikawa goggo ido, duk yanda taso daurewa kasawa tayi. Sumayya kam sosai jikin ta ke rawa, wanda batasan dalili ba, tana ajewa goggo kujeran itama a bakin dakali ta zauna tayi shuru. Sumayya!! "Na'am goggo" Kin dai san a rayuwar d'an Adam tana tafiya ne, tare da jarabawa koh? "Kwarai kuwa Goggo" tace tana kara gyara zaman ta, don tasan tabbas akwai abinda ke faruwa Sumayya ina so ki kwantar da hankalin ki, kuma ki rungume kaddara a yanda tazo miki, ina son kiyi hakuri da abinda zan sanar dake sumayya, ki kwantar da hankalin ki addu'a kad'ai ya dace kiyi. "Meya farune goggo"? Sumayya ki kwantar da hankalin ki, tace ganin sumayya harta mike tsaye jiki na rawa tana kallon ta. " goggo meya same shi?tabbas nasan abune ya faru dashi, tun d'azun wallahi zuciya ta tsinkewa take"ta karasa maganar da fashewa da kuka. Sumayya kiyi hakuri wasu da bamu san suwaye ba, suka zo suka tafi dashi,ki kwantar da hankalin ki in ma masu garkuwa ne zamu jira kiransu, insha Allah babu abinda zai f....... Goggo bata karasa magana ba, dalilin ganim sumayya ta zube tim akasa,da gudu tayi kanta tana girgizata tana kuka. Jin kuka akofar sumayya yasa inna asabe lekowa, wanake gani kamar Amina meya samu MATAR MAKAHO kuma? Wallahi inna muhammad aka sace, shine na sanar da ita kinga sai kawai ta yanke jiki ta fad'i. Toh ai saiki kamata muje asibiti, ashe abinda modi ya sanar dani gaskiya ne, wai an kama MAKAHO banda haukan kidnopas ina su ina kama nakashashe?koh d'an kudi da aka ga yad'an samune oho. Inna ki taimaka mini bara na zuba mata ruwa, da gudu goggo tayi d'aki,ruwa ta ibo a firij tazo ta watsa mata, amma sumayya bata tashi ba, cicibarta sukayi ita da inna asabe zasu fitar da ita waje sai ga khadija. Innalilahi inna meke faruwa? Khadija jeki rufe musu kofa kizo mu tafi asibitin kiyi sauri. Toh goggo tana kuka ta nufi kofar yayan ta, rufewa sumayya d'aki tayi da kofa tabi bayan su goggo. FMC suka kai sumayya, suna zuwa aka bata gado,khadija shagon yayan ta ta wuce saboda rashin kudi a hannun su, shagari dubu 10k ya baiwa khadija, yace na cinikin da yayi yaune. Ta bangaren kamila, bayan yan uwan babanta sunzo aka kaisu sukaga kamila, sosai suka tausaya mata ba kad'an ba, masu magani aka nema kowa yazo ya gwada, abu ba sauki kadangaru fa sunki barin kamila. Harira taso koma wa jalingo, Amma sam baban kamila yaki, mijin ta yayita kira tun tana masa karya harya gaji yazo da kansa, yaji ba'asin zaman ta a kauye. Sosai yasha mamaki lokacin da baban kamila ya masa bayanin abinda matar sa ta jawowa yarsu, baice kome ba ya juya ya koma jala. Bayan maman kamila ta farka, tace atafau sai an maida kamila gun nakan dutse, suje su basa hakuri in ma kudi za'a basa a basa, ya bar musu yarinya ta huta. Anyi yanda za'ayi aja kamila amma an kasa saboda kadangaru sunki daga an tinkaro ta zasu hayayyako ma mutum. da aka ga haka sai aka samo bulala ana kora kamila dashi kamar saniya ana mata barazana tana gudu, in zatabi hanyar da bashi suke soba sai wasu su tarota, a haka gwanin tausayi akayi gun nakan dutse da ita, Amma ina suna zuwa aka ga koh kokon sa yau babu filine shatt ba kome. Haka suna ji suna gani kamila tayi ta fama da kadangaru, ga watan azumi gashi sun rasa ya zasuyi su dawo da ita jalingo. Karshe dai motar akori kura, aka samu aka kora kamila tahau baya, da kadangarun ta mammanne a jikin ta, Aka ja motar sai jalingo. Sai ayau Harira ta samu dawowa gidan ta, jikin ta har rawa yake ta shigo gidan, da mamaki ganin mijin ta zaune da yaranta, suna bud'a bakin azumi. Assalamu Alaikum Ba tare da ya d'ago ba ya amsa mata, wa'alaikumu salam. Rikice wa tayi ta rasa ma me zatayi ta zauna a falon ne, koh ta shiga d'aki, tashi tayi ta shiga d'akin ganin kallon banza da mijin ke mata. Tana shiga d'akin ya taso ya bita, kee Harira sai yau kika dawo? Eh sai yau wallahi aka samu aka fitoh da ita. Yayi kyau karbi wannan,yace yana mika mata takardan dake kan mirrow ta. Jiki na rawa tace menene wannan baban Amir? Takandar sakin kine, kije bazan iyya zama dake ba, yanzun ma jira nake ayi sallah aure zanyi. Saki, aure? Kwarai ma kuwa na baki nan da awa biyu ki tattara kayan ki kibar mini gida now now... Don Allah kayi kahuri, baban Amir kayi hakuri na tuba, wallahi bazan sake bin koh mai tofi, kayi hakuri karka sake ni wallahi bazan iyya koma wa gida a yanzun ba . Au nan in gidan ubanki ne da bazaki iyya koma wa ba? Sosai harira tasha mamaki, yau mijin tane ke zagin ubanta, mutumin da koh d'aga ido bayayi ya kalli tsakar idon baban ta tsaban kunyan sa dayake ji. Koh bazaki fita bane? yace cikin tsawa. Mikewa tayi ta fara tattara kayan ta, tanayi tana kuka tana dana sanin sanin kamila, gashe a dalilin neman mata auren wani gata ta kashe auren ta .. Kamila kam har akayi sallah tana fama da kadangaru, yan unguwan su ba wanda baiji abinda ya faru ba, wasu suzo gulma wasu suzo musu jaje, mamar ta haukane kawai batayi ba, duk malamin da aka samo abu yaki sam har akayi sallah jiki yaki sauki kadangaru kam basu barta ba. Ta bangaren muhammad kam, tunda suka sasa a mota sai had'asu da Allah yake, su taimaka su barsa matar sa ba lafiya yanzun ma magani yaje sai mata, sumai hakuri, amma ba wanda ya kulasa, da suka ga surutun sa yayi yawa, gam suka likawa bakinsa. Shidai yana zaune yanaji sai tafiya ake dashi sosai, kafun yaji motar ta tsaya, d'aya daga cikin sune ya bude masa baki, suka jasa waje aka fitar dashi daga motar, ajesa sukayi a kasa, suka aje masa plate a gaba, kai muhammad d'auke abincin gaban kan nan kaci, tafiya ne a gaban mu. Don Allah kuyi hakuri ku maidani, wallahi matata bata da lafiya na barta koh karyawa batayi ba. Kai muahmmad banace kaci abincin gaban kaba, koh bakaji bane? Ai da sauri ya fara cin abincin, jikinsa na bari. Kasan me mukeso dakai muhammad? Ah ah sai kun fad'a ya basu amsa abinci cike a bakin sa, don ya tsorata ainun, tura abinci kawai yake. An bamu kwangilar kashe ka, Amma mu bazamu iyya kashe ka ba, don shekarun baya mune tsilar makantar ka, wanan karon bazamu iyya d'aukar ranka ba, bakaji ba, baka gani ba, ana buwayan rayuwar ka. Innalilahi kune daman wa'inda kuka zubamin abu a fuska, na makance? Ba zuba maka abin bane ya makantar dakai muhammad, tafiya mukai dakai a wancan karon ma. Toh me nai muku kuma, waya saku?yana maganar yana kuka. Kai mana shuru,abinda muke so dakai yanzun shine xamu fitar dakai daga NIGERIA, Bama son ka kara taka kafar ka a wannan kasar, kaje can kayi rayuwar ka, yafi maka Alkhari sama da zaman ka a kasar nan. Toh don Allah ku bari na d'auki matata da kanwa ta, saimu tafi tare wallahi na muku Alkawari bazamu sake taka nigeria ba. Kaiiii kana wasa da ranka koh? ana maka gata kana kokarin sa kanka a matsala, an gaya maka koma warka gida yanzun baka bata mana aiki bane, don haka barin kasar nan dakai ya zama dole mundin kana son rayuwa mai tsawo Don Allah ranka ya d.... Bai bari ya karasa ba yace, rufemin baki wawan banza kawai, kome mata mata ai akwai mata da yawa a duniya, in sake jin ka am bace Hakuri anan saina sumar dakai nosense. Shuru muhammad yayi, agun suka kwana washe gari suka kama hanya, wanda shi ba gani yake ba bai san ma ina ake jansa ba. Lokacin da aka zo tsallaka border da muhammad ana tsallaka nigeria wani irin ihu ya sake yana birgima a cikin motar, ji yake kamar ruwan zafi aka watsa masa, sosai yake salati yana kuka jin jikinsa na tafarfasa. Abin mamaki mutanen basu wani damu ba, kuma abin bai basu mamaki ba, d'aya daga cikin sune ya masa Allauran bacci a take jikin sa ya sake. Ta bangaren sumayya sai da ta kwana biyu kafun ta dawo hayyacin ta, tunda ta farka sunan muhammad kawai take kira sai kuka, zaune take akan gadon asibiti An d'aura mata sabon ruwa a hannu, inka ga sumayya saika tausaya mata tsabar rama da tayi, Likita ce ta shigo d'akin, sumayya ta kalla ta sake kallon goggo dake zaune a gefe, ga khadija ma zaune tayi tagumi gabaki d'ayan su wujiga wujiga suka koma, abin tausayi. Sannun ku yamai jikin? Da sauki likita, goggo ta Amsa mata. Masha Allah, sumayya kam tana da mijine? Eh likita tana da miji. Ok koh zan iyya ganinsa? Kuka sumayya ta sake mai tsanani, tana dafa kirjinta jin zafin da yake mata. Subhanallah sumayya ki kula da lafiyar kifa, kina kokarin d'aurawa kanki wani ciwon kuma akan wanda kike dashi. Dole nayi kuka Dr mijina aka sace shikaran jiya da safe. Amma kun kai report wajen yan sanda kuwa? Ah ah waye muke dashi, da zai kai mana report, yan sandan ma in kaje sai sun nemi wani abu agun ka, mu ina muka ga abinda zamu basu. Duk da haka gwara kukai report yafi, sannan ina son kuban waje zanyi magana da sumayya? Ba kome likita, goggo tace tana fita, khadija ma tashi tayi tabi goggo har lokacin bata daina kuka ba inta tuna yayan ta. Sumayya hawan jini kika samu ya kamata, ki nutsu kisa tawakkali a ranki kiyi hakuri insha Allah mijin ki zai dawo. Dole nayi kuka Dr mijina shine kad'ai farin cikina daya saura mini, sannan a waye gari ban gansa ba dole na shiga damuwa. Kiyi hakuri, sannan ya kamata kima mahaifiyar ki magana ta ringa xuwa miki da ruwan zafi, kina zama a ciki saboda yanayin jikin ki kinji Allah ya sauwaka. Ameeen nagode likita, sumayya tace tana kallon likitar bazata wuce sa'arta ba koh ta bata yan tsiraran shekaru. Ta bangaren muhammad Sai da sukayi sati suna tafiya a motar, kafun suka iso kasar da suka shirya kaisa. Suna shiga kasar da suka yanke zasu aje sa, d'aya daga cikinsu ne ya kalli ogansa, oga anya wannan yaron, bazaice zai dawo kasa ba kuwa, ka sansa akwai fahimta ni inso samune mai zai hana a masa yanda zai manta da kome, na d'an wani lokaci. Bazai yuba hakkin yaron nan ya mana yawa, mu barsa haka wannan karon bazan sake cutar da yaron nan ba. Shikenan oga amma naga hakan ma, taimakon sa muke son yi, don mun masa hakan ba kome bane. Gaskiya ne oga, d'aya daga cikin su yace Kai ban Amince ba ku aje yaron nan mubar kasar nan, kar a kamamu jirgi ma zamu bi, bada mota zamu koma kamar zuwa ba. Haka suka aje muhammad suka kara gaba. Kamar Awa d'aya da tafiyar su muhammad ya farka, A hankali ya motsa hannunsa sai kuma ya fara kokarin bude idanusa a hankali, ya bude su yana kallon sararin samaniya, ai da sauri ya mike zaune, mafarki yake koh gaske jikin sa har rawa yake yasa hannu ya murza idon sa da kyau don kara tabbatar wa kansa abinda yake gani, gaskiya ne koh A mafarki yake...............🍀🍀🍀🍀🍀 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya Ibrahim* 🍃 ✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwa 👌 Free book🤧 Page6⃣4⃣&6⃣5⃣ Mafarki yake koh gaske, da idanun sa yake kallon duniya, wanda rabon sa daya gani yanzun ana neman shekara 13, Allahu Akbar Tsarki ya tabbata ga Allah, Alhamdulilah Alhamdulilah, shine abinda yake maimaitawa Mikewa yayi da sauri yana bin koh ida da kallo, kamar wani dolo, shi ganin abin yake kamar mafarki ne, an jima zaici gaba da ganin duhu,sai bin wajen yake kamar daji, haka ya ringa takawa a hankali yana tafiya cike da Al'ajabin abinda ke faruwa yau dashi, shine da kallo? Hango gonaki yayi a shimfide, gwanin sha'awa na kayan labbu, ga kogi babba yana gudana da gudu yayi saitin kogin da saurinsa ya shiga ruwan, don wallahi azababben kishi yake ji, ai yana shiga kogin ya tsoma hannun sa cikin ruwan ya iba yasha, ya sake tsoma wa ya iba yasha, kamar wasa yaji ruwa yana jansa daga bakin gaba, har tsakiya sai kokari yake ya fitoh amma ina abin yaci tura, salati ya fara yana innalilahi, wasa wasa ruwa ya fara nitsar dashi sai kokowa yake da ruwan, duk kokarin sa na fita, abu ya gagara, daman shi ba ruwa ya iyya ba, ina makaho ina rafi, koh lokacin tasowar sa baiyi yayin bin yara kogi ba. Sosai ruwa ya hadiye sa har wuya, sai kokari yake Amma ruwan yafi karfinsa, zuwa wani lokaci, shuuuuuuuu yaji ya burme cikin ruwa, da sauri yayi tsalle yafitar da kansa, sai kuma yaji ya sake komawa, kamar wasa Al'ameen ya fara shan ruwa, sannu sannu har yaji ruwan yaci karfinsa, tun yana gani dishi dishi har yaji bayanan , Gid'ado ne tsaye da shanun sa, daya koro bakin gaba susha ruwa, kamar wasa yaga shanukan sa, na kuka a bakin gaba, Alamu dai wani abin suka gani. Da sauri ya karaso wajen don yayi tunanin kada ne, koh wani mugun abu, tsayawa yayi turus yana bin abinda yake gani shida dabbobin sa, mutum ne, kwance baya motse kamar gawa, da sauri ya kad'a shanunsa har ya juya zai tafi don gudu rigima, daman ba shiri suke da manoma ba kar ace shiya kashesa, ya shiga uku. Sai kuma ya sake dawowa, haka kawai yaji hankalin sa bai kwanta da tafiya yabar gawan ba, nade kafar fantalelen wandon sa, na kiwo yayi ya shiga ruwan, jawo Al'ameen yayi, kiiiiiiiiii ya fitar dashi a ruwan, ajesa yayi a kan tabon bakin kogi. Kurawa fuskar Al'ameen ido gid'ado yayi tabbas wannan ba kabila bane, duk da fuskar tayi irin na fulani,Amma ba fulani husul bane, kyaun sanan akwai mix,ganin Hakan yasaka sa ciccibar Al'ameen, ya d'aura a bayan wuyansa yayi Rugan su dashi. Tun daga mahadin rugan su ake binsa da kallo, ganinsa d'auke da gawa a wuya, kowa ya tare sa, cemai yake shima a ruwa ya gansa, sosai wasu ke zagin sa meye na kawo musu gawa salon ya jaza musu bala'i, Amma shi sam bai damu ba tafiyar sa kawai yake. Isarsa gida ya tarar da mahaifinsa zaune a gindin bishiyar tsada a tsakar gidan su, sai innar sa dake gindin murhu tana girki. Assalamu Alaikum Waalaikum.......sai kuma ta dakata, bata ma karasa amsa sallamar ba, hadde yan boni, gid'ado dun dume, miyiyata do ha bahoma?(me nake ganin nan a bayan ka) Shuru yayi yana kallon ta, ganin yanda gabaki d'aya tabi ta gigice, bappan sa dake zaune a gindin bishiya ne, yayi saurin tasowa jin abinda inna kece wa. Gid'ado d'obo?bappan sa ya tambaya, yana nuna Al'ameen dake kafadar gidado. Bappa, kuyi hakuri bara na sauke sa sai in muku bayani, duk cikin fulanci suke maganar. Wani irin mu kwantar da hankali?kawai ka ciccibo mutum baya motse a kafad'ar ka, ka shigo mana ruga akan me? Don Allah inna a wad'a muyal, nima ganin sa nayi a bakin gaba, alamu dai ruwane ya jasa, koh aka yardashi, gidado yace yana kallon matarsa data fitoh daga d'aki, d'auke da tsohon ciki tana nufosu. Kwantar dashi gid'ado, in yaso koh sallah Amasa tunda naga kamar musulmi ne, bappa yace. Sauke sa gidado yayi, sosai bappa ya kurawa fuskar muhammad ido, yana nazari sai kuma ya d'aga ido yakalli gidado, Ai ohmayai(ai bai mutu ba)suma yayi. Da sauri gidado ya kara maimaitawa suma bappa? eh, yi sauri ka d'auko mini kwaryar magani a bukka, yana maganar yana dukawa kusa da muhammad, danne masa ciki ya farayi, take ruwa ya fara fita, ta bakin sa duk da baiyi motse ba, amma dai ruwan na fita sosai, bappa ya mammatse masa ciki. Matar gidado kam kujera ta samu ta zauna a hankali daker, sai ga gid'ado ya fitoh bukan bappa, da sauri ya ajewa bappa magani a gefe, bappa da lenki mai. Maganin bappa ya d'auka a kwarya, yana shashafa ma Al'ameen a fuska, da wuya yana masa Tofi,yana gamawa ya d'aga ido ya kalli gidado, husumo ayara ha sudu(ka daukesa ka kaisa d'aki) Wai bappan gidado ban gane a d'auke sa akai sa d'aki ba, yadaga ganin mutum bamusan daga ina ba, mugune koh nagari?kawai mu d'auko mu aje a cikin gidan mu, ni gaskiya ban yarda ba. Talatu kena bani mamaki wallahi, yanzun ace mutun baya cikin hayyacin sa, ina kikeso mu kaisa? Koma ina a kaisa, amma dai gaskiya banda cikin gidan nan, taima ma mugune. Koh mugune, mu Allah zai dubi zuciyar mu, insha allah bazai basa ikon cutar damu ba, bare ma wannan yaro baiyi kama da mugu ba, daga ka gansa kasan akwai jinin fulani a jikin sa. Lantana matar gidado kam, mikewa tayi ta shiga d'aki ganin fad'an bappa da inna baya karewa in gari ya waye . Kai gidado d'auke sa ka kaisa d'akin kusa da gindin murhu. Toh bappa, yace yana ciccibar sa yakai d'aki, shanu kansa dake binsa a baya tunda ya d'auko Al'ameen har gida, suya kama ya d'ad'aure a turke....... ************************** Ta bangaren sumayya yau satin ta d'aya a Hospital, har da kwana d'aya, Amma jikin dai za'ace Alhamdulilah, da sauki kad'an duk da baiyi kwari ba, sosai likitoti ke kula da ita, hatta Dr tana iyya bakin kokarin ta, ganin sumayya ta samu lafiya, Amma taki kwantar da hankalin ta sam. Khadija ma yau sati guda, rabon ta da makaranta,suna faman jinyan sumayya, Goggo ke zama a asibiti, ita kuma ke musu girki a gida ta kawo musu, duk da sumayya baci take ba, sai yan aikace aikacen gida duk ita keyi. Kamar yau ma, khadija ce ta kammala girki a kofar sumayya, zuzzubawa tayi a kula, tasa a kwando ga flask a hannun ta, ta fitoh gidan Adara, tsallaka titi tayi ta nufi shagon yayan ta, shagari ta samu zaune yayi tagumi gabaki d'aya yaron ya shiga damuwa ainu na b'atan Al'ameen, duk da shike kula da shagon yanzun, amma sai yanajin shagon kwata kwata baya masa dadi. Assalamu alaikum. Wa'alaikumu salam, khadija zaki wuce hospital in kenan harkin shirya? Eh na gama girki. Ok yace yana mikewa, laida ya d'auko ya zuzzuba ayaba da kankana mai yawa, ya rufe shagon, kwandon hanun khadija ya kamar ba, ya bar mata flask in yana rike da laidan kayan marmarin a d'aya hannun, suka kama hanyar FMC da kafa, don shagari duk da muhammad baya nan, amma baya masa Almubazza ranci da kudi, asalima tattalin sa na yanzun yafi nada, hatta kudin asibiti duk Abinda aka bukata shiyake biya, ya hana sumayya kashe koh sisi. Sunzo sharan kwanan doruwa, kawai suka ga anyi packing moter a gabansu, khadija kam koh duban motar batayi ba, kokarin kaucewa take ta gefe, ta wuce abinta, dayake shagari bai wani waye Ammar ba, yasa bai ma saurare saba yabi bayan khadija. Ke yar kauye, mai tafiya bata kallon gaban ta. Da sauri khadija ta d'ago jin muryar Ammar,ina kwana?tace. Kin Amsawa yayi ya dubeta, ina zaku kuma da abinci haka. Asibiti, ta basa Amsa. Waye ba lafiya? Aunty sumayya . Subhanallah, yayan naki nacan ne?nima yau na dawo da asuba, shine nace bara na biyo gunsa. Shuru khadija tayi bata basa Amsa ba, sai kaucewa da tayi taci gaba da tafiya. Da sauri ya fitoh a motar, yabi bayan ta, keee ba magana nake miki bane?kina tafiya? Kala batace ba, tana ta tafiyar ta. Hannun ta Ammar ya rike, da sauri ta juyo tana kallon sa, sakemin hannu? Naki na saken, ina miki magana kina manna mini hauka, ina wasa dake? Kuka khadija ta sake masa da karfi, ai da sauri Ammar ya sake mata hannu, ya juya yana kallon shagari, dake tsaye yana kallon su, fuskar sa A hade, haka kawai yaji ya tsani Ammar, ganin yanda ya wani rikewa khadija hannu. Kai meke faruwa ne?Ammar ya tambaye sa. Fuska a hade yace, An sace oga ne shiyasa daka mata maganar, ina yayan ta, take kuka. Sai a lokacin Ammar ya gane shagari, watoh shine wanda muhammad yace zai d'auko su zauna a shago, abu na biyu daya basa mamaki kuma wai an sace muhammad, sai kace kaza, ban gane an sace saba? Eh an sace sa, haka kawai wasu a mota sukazo suka d'auke sa, a bakin titi Tsabar razana har tuntube yayi, yau kwana nawa kenan? Sati d'aya. Amma har sati d'aya, police basu d'auki wani kakkauran mataki ba?mutum ya bata kamar wani kaza koh d'uriyan sa babu? Koh report bamu shigar ba, Shagari ya basa Amsa. What?? ba'a kai kara ba, akan me? Sumayya na asibiti, ni kuma tsoro nake ji, shiyasa ba wanda yakai. Amma ai koh baku kaiba, nasan labari zaije wa yan sanda, tunda kuna kusa da station, yaci su subibiye Lamarin. Shuru suka, masa. Ku shiga muje asibitin, yace yana karban flask in da khadija ta dongorar, yasa a mota. Shagari ma shiga yayi ya zauna a gaba, har lokaci tana tsungune a kasa, hannu kawai Ammar yasa ya fizgota, ya jefa a bayan motar, ya zagaya driver sit ya zauna, yaja motar suka nufi Hospital. Suna shiga hospital in, dashi da shagari ne suka d'auko kula da flask, harda laidan, khadija kam an kaikaya mata inda yake mata kaikayi, kuka har lokacin yinsa take, duk yanda shagari keta bata baki tayi shuru, amma ina. Keeee wallahi in na sake jin koh tarinki, a asibitin nan saina saba miki, banason shirme tun d'azun, sai cika min kunne kike nayi shuru, yanzun mun shigo asibitin ma bazaki rufe bakin bane? saikin tara mana jama'a. Shuru khadija tayi, harga Allah wannan Ammar in kamar mai Aljanu haka yake, zafi zafi sanyi sanyi. Shagari kam gaba ya kara, dayake yasan d'akin da sumayya take, bai saurare tahowar suba, yayi tafiyar sa, yana maijin haushi a ransa. Shiya fara shigowa d'akin, da sallama. Amsa masa sumayya tayi, wance ke zaune daga ita sai dogon rigan kanti, kanta koh d'ankwali babu, tana zaune a bakin gadon, rike da wayarta, hawaye nabin kumatun ta. Ina wuni Aunty, ya jiki? Kai kawai ta d'aga masa, ta mika hannu ta d'auki d'an kwalinta, dake gefen gadon ta yafa a kanta. Zama shagari yayi yana bin d'akin da kallo, ganin baiga goggo ba. Assalamu alaikum, Ammar ne yayi sallama a bakin kofar d'akin. Amsa masa shagari yayi, ba tare da ya d'ago yaga bakin kofar ba. itama sumayya bata d'ago ba, sanin wake sallamar, don ta shaida mai muryar. Shigowa Ammar yayi, idanun sa ya sauka akan sumaya, dake zaune gabaki d'aya ta chanja, ta rame sosai sai haske data kara a yan kwanakin nan, har yayi yawa,tayi fari kamar ka tabata jini ya fitoh. A hankali ya tako har inda take, hannu yasa ya amshe wayar, sai a lokacin sumayya ta d'ago ta dube sa, hade da mika masa hannu, Alamun ya bata wayar ta. Matsawa yayi gefe, ya kurawa screen in wayar ta ido, hoton tane da suka d'auka, ita da muhammad ranan sallah a gidan su. Sumayya ya kamata kima kanki fad'a, wannan abinda kike kara cutar dakan ki kike, kuka bashi ne magani ba, koh mafita, kin zauna kina kuka, gaki ba lafiya bane dake, ki dubi yanda kika koma fisabililahi. Gaya mata kam D'an nan, haka nake fama da ita, bansan me take gani a wayar nan ba, ta tura khadija ta d'auko mata, shikenan tamai dashi madubi, tana kallo tana kuka, goggo data fitoh a toilet na d'akin ne take maganar. Hoton mijin tane a ciki mama, Ammar yace yana latsa wayar sumayya, dake hannun sa. Au shiyasa take kuka?/lalle sumayya baki jiran kanki, kiga yanda kika zama gabaki d'aya kin koma, kashi da rai sai haske da kike tayi kamar mai ciwon far d'aya. Kyaleta mama, hotunan duka zan goge. Kuka sumayya ta sake, jin abinda Ammar yace wai zai goge hoton muhammad a wayar ta"ka bani wayata karka goge na rokeka don Allah" Ah ah bafa zan baki ba, in gaya miki, tunda zaki tasa wayar a gaba kina kallo kina kuka. "Allah nayi Alkawari zan daina" tana magana tana kuka Toh yanzun me kike in ba kukar ba? Don Allah ka bata wayar ta, sai kuka take tana maka magiya, kana wani ja mata rai, khadija ce tayi maganar cikin jin haushi ganin iyayin da yake ma Auntin ta. Wani kallo Ammar ya watsa mata, jin maganar da take masa kamar sa'arta. Bata sake magana ba, aje abincin tayi tana kallon sumayya, in zuba miki Aunty? "Ah ah banaci" Wani irin bakici?sumayya yau kwanan mu tara a asibiti, abinci kirki baki ciba ya za'ayi kiyi lafiya. Shuru sumayya tayi, ta koma ta kwanta bata kara magana ba, don ta fahimci bazasu gane abinda ke damun ta ba. Ammar kam kallon khadija yayi ya sake kallon, Goggo,meke damunta , sukace mama? Damuwa ce d'an nan, hawan jinine ya kamata, maimakon ta nutsu ta samu lafiya, Amma ina sai kara kwantar dakan ta take A gado. Allah ya bata lafiya, in ba damuwa mama, ina so zan fara bincike akan case in batar Al'ameen, in muna bukatar cikekken bayani zan tuntube ku. Ba kome yaro mun gode, Allah ya saka sai dai ban gane kaba? Abokin muhammad ne. Au koh dai kaine Ammar, da yake sanar dani ka bude masa shago?ai munga abin Arziki Allah ya biya ka. Ameeen mama. Sai a lokacin shagari da khadija, suka san Ammar ne ya bude ma Al'ameen shago. Fita Ammar yayi bai bawa sumayya wayar taba, ita ma bata sake magana ba. Ta bangaren Al'ameen kam har dare bai dawo hayyacin sa ba, gidado yayi ta zuwa dubasa yafi a kirga Amma shuru. sai da gari ya waye, ya farka jujjuyawa yayi sai kuma ya bude idanun sa, da sauri ya koma baya da mamaki, ganin yarinya budurwa zaune a gaban sa kyakky.................🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya Ibrahim* 🍃 Page6⃣6⃣&6⃣7⃣ Kyakkyawa tana sanye da kayan fulani, ga wani kitso manya manya a kanta, ta kura masa ido, da sauri ya mike zaune keee lafiya?ya tambaye ta cikin Al'ajabi. Wallun hakkiloma, tace masa tana murmushi. Da mamaki yake kallon ta, kafun ma yayi magana yaga wani saurayi da bazai wuce shekara 21 ba ya shigo d'akin, baki ne kamar yarinyar sai dai yarinyar ta fisa kyau sosai, duk da shima ba mummuna bane. laaa ka tashi?yace da sauri yana karaso wa kusa da Al'ameeen. Al'ameen kam ya cika da mamaki wai inane nan? gashinan a cikin wani daki kamar akurkin kaza, haka yake kallon d'akin, sai dai jin fulatanci a bakin su yasa sa gane fulanine su, duk da gidan Adara fulani ne sai dai sam basa magana da harshen su, da hausa suke magana sai dai koh yaya ne indai mutum ya zauna a jalingo, zaiji fullaci koh bai iyya maida martani ba bare shida yake zaune a unguwan fulani, shima cikin fullaci yake tambayar su nan inane yake. Murmushi yaga saurayi yayi, sai kuma ya juya ya kalli yarinyar, indo wai har yanzun baki tafi tallah ba?kinsan in inna tazo ta samu baki wuce ba ranki zai baci koh,fita ki d'auki nonon ki kitafi. Ba musu ta mike duk da ranta baiso ba, ta fita a d'akin, juyawa gidado yayi yana kallon Al'ameen, sunnu ya jikin naka?duk da fulatanci yake magana. Sosai Al'ameen yake mamakin wannan Al'amarin, wai garin yayane ma yazo inda yake nan, yanaji gidado nata masa magana amma kala baice ba. Ganin yaki magana yasa gidado tashi yabar dakin,cikin gida ya shiga yaje ya sanar da bappan sa bakon ya farka, amma baya magana don shi ya d'auka koh wata matsala ce, ya hana muhammad magana. Al'ameen na zaune kamar gunki yana tunani abubuwan da suka faru dashi, a yan kwana kin nan, sai kuma tunanin sumayya ya fado masa, koh yanzun a wani hali take?lumshe idanunsa yayi yana kiyastata amma yagagara hasko kaman nin ta, yaso ace itace mutum na farko da zai fara gani, bayan dawowar idanun sa. Gidado da bappa da suka dade da shigowa, sai magana suke amma Al'ameen baisan ma sunayi ba, dafasa gidado yayi, da sauri ya zabura sai kuma ya d'aga ido yana kallon dattijon dake kusa dashi, ya zuba masa ido, sunkuyar da kansa yayi Amma baiyi magana ba. Akwai inda yake maka ciwo ne? A hankali y dago kai ya kalli mutumin, sai kuma ya basa amsa cikin fulatanci kamar yanda yamasa magana, babu abinda yake mini ciwo. tashi ka fitoh kayi Alwala ka biya sallan da ake binka, gidado zai kawo maka kaya ka saka da abinci kaci. Toh kawai Al'ameen yace, yana mikewa tsaye da taimakon gidado ya fitoh a d'akin, kasance war dakin a hanyar kofar gidane , yasa yana fita yaga inna zaune tana gyaran zogale a tsakar gida, ina kwana? Mtswww kawai inna Talatu tayi, tacigaba da abinda take ba tare da tabi takan gaisuwar saba. Sanin halinta yasa gidado d'aukowa Al'ameen buta ya mika masa,shima Al'ameen dayake ya saba ganin abinda yafi na inna yasa bai wani damu ba, don duk Abinda zata masa lafilane in an had'a da rashin mutuncin gidan Adara. gidado dakinsa ya shiga, kaya ya d'auko kala uku na fulani, sai nono da matar sa ta dama,ya had'a da dambu ya kaima Al'ameen a d'aki. Bayan muhammad ya idar da sallah, wanka yayi bayan gidado ya iba masa ruwa a rijiya, ya chanja kaya, abincin ya bude kasa cin dambu yayi, nono kawai yasha, kad'an duk yabi ya shiga damuwa halinda sumayya da kanwar sa zasu shiga a rashin sa. Sai bayan muhammad ya gama kimtsawa, kafun ya mike a hankali ya fitoh a d'akin bappa ne da gidado zaune a gindin bishiya, sai inna dake zaune a gefen su rike da fifita, karasowa yayi kusa dasu bappa a hankali, ya zauna a gefen su,duk da bansan tayaya nazo nan ba, amma dai nasan taimako na kukayi, nagode Allah ya saka da Alkhar, yace musu. Ameeen,bappa da gidado har suna had'a baki suka amsa masa, sai kuma bappa ya kara tambayar sa, yaro garin yaya babba dakai har ruwa ya jaka?koh wani abinne ya faru dakai? Shiga ruwan nayi zan sha, shine yajani, ya bashi Amsa. Kai bako ne hala koh?don ruwan mu bayason bako. Eh ni ban taba zuwa kauyen nan ba, baba A ina kake? Jalingo. Jalingo kuma?inane haka, nidai bantaba jin sunan wannan gari ba, gidado yace da mamaki. Bappa ma kara tambayar sa yayi inane jalingo kuma? Muhammad kam sai yanzun ya tuma ashe bafa a kasar NIGERIA yake ba, yanzun toh Amma a ina yake haka, gadai mutane kamar na kasan sa fulanine musujin yare, wani kasane wannan, dan uwa?yayi maganar yana kallon gidado. Gidado ya juya ya kalli bappa, shima bappan gidadon ya kalla suka had'a ido, sannan suka sake maida kallonsa kan muhammad, Cameroun. A hankali yace musu ba'a kasar nan nake ba. Kamar ya ba'a kasar nan kake ba? Eh baba ba'a nan nake ba, a nigeria nake. Nigeria, a ta ina kasar take? gidado ya tambaya da mamaki, don shikam baisan wata kasa nigeria ba, murmuahi bappa yayi yana kallon gidado, nigeria ai na sha zuwa, lokacin da muke cikin ganiyar kuruciya, har kasar muke zuwa kiwo tun daga Cameroun, har nigeria. Wai bappa kasan kasar ne?inji gidado Sosai ma nasan jahohin kasar, kai yaro a wani jaha kake?ya tambaye muhammad. Taraba, ya basa Amsa yana kallon inna dake ta zabga masa harara tun daga inda take. Allah sarki ai naje jaharma dashi, da gombe harda Adamawa, amma tunda kace a taraba kake kenan ta Gimbu ka shigo kasar cameroun? Nima ban sani ba baba kawoni akayi. Kamar ya yaro aka kawo ka, ban gane ba? Shuru muahmmad yayi yama rasa ta ina zai fara. Dafasa bappa yayi, kaga yaro ka fad'amin gaskiya, mu bazamu cutar dakai ba sannan haka muke fata agunka. A hankali muhammad ya gyara zaman sa, ya fara bawa bappa da gidado labarin sa, har Auren sa da sumayya, da batar mahaifin su , har zuwa sanadin zuwarsa kasar nan, ya kara dacewa, sannan baba ina so na koma kasata koh don ganin halinda na tafi nabar mai d'akina a ciki. A hankali bappa ya d'aga ido yakalli muhammad da kyau, ya sunan ka? Muhammad Amma anfi sanina da Al'ameen. Ashe sunan baba nane dakai, Zan fad'a maka gaskiya, akwai asiri a jikin ka har yanzun, sanan bakai aka ma asirin ba, an ma wasu asirin ne a jikin ka, anyi amfani da tauraren ka anyi asiri da kai, dole kana bukatar ka zauna ka nutsu, komawar ka gida yanzun matsala ne duba da abinda mutanen da suka kawo ka sukace, zaka bata musu aiki sanan kwangilar kisan kai aka basu, watoh kaga yanzun an daina Amfani da boka, da zahiri ake son ganin bayanka, ka zauna anan zan maka jinya da izinin Allah duk asirin dake jikin ka zai karye, wa'inda akama asirin ma zasu dawo hayyacin su, sannan zan taimaka maka da maganin kariya babu wani asiri da zai sake cinka bi'izinillah,kaima ka dage da Addu'oin neman tsari a wajen Allah, don yawan ibadan ka shiyasa har yanzun basu gama cin nasara akanka ba. Shuru muhammad yayi amma sam ransa baiso ba, baiso hakan ba, yaso ace ayau innan ya koma gare ta, yaje yaga halinda take ciki ya kalleta da idanun sa, yaga wani irin farin ciki zatayi yau idan taga yana kallo, amma babu hali, sannan maganar mutumin nan bai kwanta masa ba, don shi ba mutum bane mai bin maganganu irin wannan na magani magani, aa tsari tsarin nan sam basu ransa. Ka kwantar da hankalin ka babana, ni magani zan baka don nema maka lafiya, sannan mu sama ma wasu lafiya, domin samun lafiyar ka, warakan wasu ne, karkaji kokonto ni bana aiki da Aljanu koh wani shirka, magani nake bayarwa wanda Alllah ya hure mini sani akan ganyen itatuwa da sassaken su, tunda na ganka nasan Akwai sihiri a jikin ka, Amma inga sarkan da mahaifinka ya baka. Hannu yasa ya kunce sarkan ya mikawa bappa, kurawa sarkan ido yayi nad'an wani lokaci sai kuma ya mike ya dauko ruwa a kwarya ya saka sarkan, ya zuba magani kad'awa yayi sai kawai ruwan maganin ya zama fari tas, wannan sarka d'ayan biyu ne Amma bazance maka kome ba Akansa, bappa yace. Shuru Al'ameen yayi sai kuma ya gyada kai a hankali alamun ya amince,ya karbi sarkan ya makala, kamar kwana nawa ne zamuyi baba? Murmushi bappa yayi sai kuma yace,ka kirani da bappa haka yarana ke kirana, sannan maganin ka bana kwana bane, na wata ne. Kamar wata nawa kenan bappa? Kamar wata uku, kuma kasan inka gama magani dole sai kunje cikin cameroun asai da shanu mu baka kudin mota. Shuru muhammad yayi kamar ya fashe da kuka, yanzun har wata uku yana zaune a wannan kauyen, ba tare da sumayya ba ai sai kewan ta ya kashe sa, tun lokacin sa baiyi ba, toh nagode bappa Allah ya saka,mikewa yayi a hankali ya nufi kofar da yake hango fili ta waje , alamu dai kofar gida kenan. ina zaka?Gidado daya mike yake tambayar sa don ya d'auka tafiya zaiyi Waje nake son fita, ya basa Amsa. Kanason zaga gari ne? Eh ina so, yace cikin ransa yana dariya wai wannan kauye ne gari. Toh jirani barana kunce shanu mu fita kiwo, saina nununa maka wajaje, yace yana tafiya tirkensu domin kunce shanun. Da sauri Al'ameen ya biyo sa wai zai tayasa kuncewa, ai yana saka hannu a kafar shanun da sauri yaja baya, ganin yanda shanun ta hafto kamar zata tunkudesa da kahon sa. Dariya gidado yayi, kai kaja baya fa shanun nan saimu, yana maganar yana kunce su . Matsawa muhammad yayi gefe yana kallon gidado yagama kunce su yana kad'asu yayi waje bayan ya karbi guzirin sa a wajen matar sa, muhammad na binsa a baya yana mamaki wai d'an yaron nan ne da mata. A haka suke tafiya gidado sai hira yake masa, duk inda suka wuce saiya ringa masa bayani, ga gonan wane, ga shanun su wane, ga kogin kaza a haka har suka nausa daji, wuni sukayi suna yawo sosai Al'ameen ya gaji bayan gidado ya kunce boronsa daya rataya, abinci ne a ciki sai goran ruwa, bayan sunci ne suka kamo hanyar gida basu suka iso ba sai goshin mangari ba, suna isa suka samu har an kira mangariba da sauri sauri gidado ya d'aure shanun suka tafi masallaci. Sosai jama'ar garin suke bin muhammad da kallo, ganinsa ras dashi kamar ba gawan jiya ba, gashi kyakkyawar bafulatani, suna idar da sallah, gida suka koma suna shiga muhammad yaga yarinyar d'azun da safe zaune a gefe tana cin tuwo, kai koh d'an kwali babu. d'aga ido tayi ta kalli Al'ameen da sauri kuma ta mike, cikin fullaci tace, laa bako kaine ka tashi, ya jikin naka yau sai sauri nake nono na ya kare na dawo gida, Amma bai kare da wuri ba. Shuru Al'ameen yayi baiyi magana ba, yana nazarin yarinyar kenan khadijar sa zatafi yarinyar nan a yanzun, Allah sarki yaci burin ganin su duk da bai taba tunanin ganin sa zai dawo ba, Amma yaso ganin sa na farko yafara dasu, ganin yanda ta bata fuska alamu dai bataji dadin shurun da ya mata ba, gashi gidado na kusa dashi, yasa a hankali yace eh na tashi. Washe baki tayi sai kuma da sauri tace, nakai maka abincin ka d'aki bappa yace na kai. Kai ya fahimce yarinyar nan yar damuwace, fadi ba'a tambaye taba, kamar ya sata, rijiyar dake tsakar gidan ya nufa jan ruwa yayi a kwalla ya wuce bandaki, bayan ya d'auko kayan da zaisa, bai wani jimaba ya fitoh Alwalan isha yayi jin ana kiran sallah ya wuce masallaci. Bayan an idar da sallan gida ya nufa a hankali ya shige dakin da aka ware masa, zama yayi akan gadon kaba da aka saka A dakin, ya buga tagumi abin duniya ya dame sa, tunanin matarsa kawai yake, adaidai wannan lokacin ne suke cin abinci, shin itama abincin take cine koh me take yanzun? Gidado ne ya shigo dakin da sallama. Amsa masa muhammad yayi, tare da gyara zaman sa. Har yanxun bakaci abincin ba tsoho? Da mamaki muhammad ke kallon sa, tsoho kuma? Eh man tunda ka haifi bappa aikai tsohone, yace yana aje agushin hannunsa. Murmushi muhammad yayi sai yanzun ya tuna, ashe fa bappa yace sunan baban sa garesa. Abinci na kawo mu had'a muci, yace yana bubude agushi. Hannu kawai muhammad yasa a kwanon bawai don yana kwadayin cin abinda ke ciki ba, loma uku yayi ya tsame hannun sa, da mamaki gidado ke kallon sa, wai harka koshine koh me? Wallahi gidado bazan iyya ciba, gabaki daya na saba ci da mata na, muna ci muna hira gabaki d'aya yau dai ina jina wani iri. Hhh dayake kabar hannun wa'inda suka kamaka ba har kana zancen kewa . Dariya shima muhamad yayi yana kallon gidado, wai ni ya akai nazo gidan kune? Nine na tsintoka a ruwa, na kawo ka gida. D'agani kayi koh shanunka ne ya kawo ni? Nina d'agaka, mana. Da mamaki Al'ameen yace, kaika d'agani fa kace, yana mamakin yaron nan ne ya dagasa. Hh ka raina karfina kenan koh? Shuru yayi sai kuma ya girgiza kai Toh kaci abincin mana, in bazaka ciba sai nasa indo ta kawo maka nono. Kai na koshi, nagode gidado Haka gidado yaci sauran abincin, bayan sun fita waje muhammad ya wanke hannunsa yana kokarin koma wa daki don sam zaman gidan baimai ba, bayason zama a gidan da akwai mata, haka shi kuma yana tsakiyarsu gashi ba'a kewaye dakin sa akayi ba, babana!!!!yaji bappa ya kirasa. Na'am ya amsa yana nufo bappa, bayan ya zauna ne bappa ya mika masa maganguna, wannan na hayaki ne wannan na wanka, yanxun zaka d'auki kwalla ka jika zuwa safiya, zaka fara amfani sai wannan gadaline zaka, shiga daki da kanka zaka nika da duste zansa gidado ya kawo maka, ga mai saika zuba gadalin a ciki, kana shafawa safe da rana, sosai bappa ya had'awa muhammad magani karba yayi, yayi godiya. Kamar yanda bappa yace haka yayi, ya jika maganin ya had'a nasha, yana gamawa ya shiga ya kwanta abinsa, sai kuma kewar sumayya duk yabi ya cikasa ji yake kamar yayi tsuntsu ya gamsa a nigeria, koh hankalin sa zai kwanta sosai yake kewan gadon su, kewan jikin ta, abincin ta, fadar su,kamshin ta kome nata kewan sa yake, a haka daker bacci ya d'auke sa. ********************* sumayya fa jiki ya fara sauki kad'an duk da ba kwari yayi ba, Amma da sauki, sosai take samun kulawa a wajen mutanen nan guda uku, goggo Ammar da khadija duk da ba kula Ammar take ba, amma kullum sai yazo kuma inzai zo haka zai kawo mata abubuwa, su tsire koh kaza, sai dai su khadija suci, itakam bata iyya ci sam. Makwanta dayan unguwa, harda yan gidan Adara, sunzo dubata sosai ta cika da mamaki, haka customers nata ma sunzozzo kuma sosai suke rike wani abu in zasuzo, lallai sana'ar mutun nasa aga kimarsa,tunda lokacin da bata sana'a babu wanda ya lekota a asibiti, Amma yanzun kowa zuwa yake yana mata ya jiki, da jajen batar mijin ta, gashi yau satin ta biyu a gado, amma haryau zuwa ake, iyayen Ammar ma sunzo da kannen sa, baban sa ne kawai baizo ba. Kamar kullum yauma hakan take, da sallama ya shigo d'akin, hannunsa d'auke da laida jikin laidan duk raba da alamu dai wani abin mai sanyi ne. Khadija dake gefe ne ta Amsa masa tana tashi daga kan kujeran da take, ta koma gefen gadon ta zauna. Sumayya dake kwance, koh d'ago kai batayi ta dubesa ba, don tun akan wayanta ta daina bi takan sa. Sannu hajiya ya jikin? Shuru ta masa taki magana, sai khadija dake gefen tane takece masa jikin da sauki. Bude laidan da yazo dashi yayi, goran kunun ayane mai sanyi harda raba a jiki, gashi fari tass, ya mikawa khadija, gashi ki bata koh zata sha? Kaidai yaya Ammar baka gajiya wallahi, kullum ka kawo abu baci take ba, amma koh yaushe sai ka saya. Mom ina cefa tayi kunu, shine nece ta zubamin a gora guda biyar, zan kawowa sumayya tun jiya na aje a firij. Karba khadija tayi tana kallon sumayya dake kwance tana jinsu, Amma har lokacin bata d'ago ba, Aunty ga kunun aya mai sanyi. Shuru tayi sai kuma taji tana jin kwad'ayin sha, mikewa tayi a hankali ta karbi goran. Tsaya ta tsiyaye miki a kofi, Ammar yace ganin tana kokarin bude marfin. Koh magana sumayya batayi masa ba, tana bude goron a hankali tasa hancin ta mai tsayi a bakin goron tana tsuntsuna kunun, tare da lumshe ido, kunun sosai yake mata wani irin masifeffen kamshi, dake fita a ciki na aya da dabino. Habba sumayya menene haka?abinci kike tsuntsunawa hakan bai dace ba, babu kyau fa, yace yana mamakin abinda tayi kamar wata tababbiya. Kafa goran tayi da bismillah, ta fara sha shatake kamar yar kokowa da sauri sauri, tunda ta kafa goran sai da yayi rabi ta cire a bakinta tana hutawa,kafun ta sake kafa bakin ta akai sai gora ya rage babu kunu. Ammar da khadija tsakake sukayi suna kallon sumayya, ita da tafi sati biyu ana binta taci abinci, taki sai d'aura mata ruwa ake, duk an bubula mata jiki, Amma yau ba lallama ba banbaki, da kanta tasha kunu har goran faro medium. Sumayya kam ta kammala da gora d'aya, rike take da gora empty a hannu, tayi shuru amma fa har ranta kari take so, saidai tanajin kunyar tambayar wani,ganin Ammar in baibar d'akin ba. Bude laidan Ammar yayi ya fitar da wani goran kunu, tashi yayi da kansa ya mika mata, hade da karban empty na goran, ba tare da yayi magana ba ya koma ya zauna. Ba kunya sumayya ta bude goron ta kama sha, wannan karon kam a hankali take sha tana kurba kad'an kad'an har tayi rabin goran, kafun ta aje sauran a hankali ta koma ta kwanta. Ammar mikewa yayi ya kalli khadija, ke tashi muje waje zanyi magana dake, yana maganar yana fita waje. Tashi khadija tayi tabi bayansa, samunsa tayi tsaye a baranda yana jiran ta, karasowa tayi ta tsaya a gefen sa fuska ba walwala, kamar yanda taga yayi. Shin yayan ki nada abokan hammaya ne? Babu yayana baida wani abokin fad'a, asali ma yanda na tashi ban taba ganin yayana yayi koda cacan baki bane da wani. Ok toh akwai wanda yake nuna masa kii koh kyama haka? Gaskiya babu. Ok shikenan kawai, yace yana barin wajen ya nufi packing space, khadija ma cikin d'akin ta koma . Sumayya kam da tafiyan Ammar koh minutes 30 batayi ba, ta sake mikewa da sauri ta d'auki sauran kunun ayan ta shanye wanda ta rege a gora, kafun dare sumayya ta gama da gora biyar innan tas sai fitsari da take akai akai. Goggo data dawo karan kanta tasha mamakin kunun da yau sumayya tasha, amma batace kome ba. Da misalin karfe 2 sumayya ta farka da sauri ta mike zaune, jin wani irin azabebben yunwan kunun aya daya farkar da ita, sauka tayi a gadon ta nufi wajen empty in gorunan, bubudesu tayi tana kale a marfi tana sha, tsaban yanda take ji kamar bazata iyya bacci ba in bata sha ba. Da yake asibitin ba'a barin mutane fiye da d'aya da mara lafiya, yasa goggo barin khadija da sumayya a dakin ita ta koma wajen block in ta shimfida taburma ta kwanta, kamar yanda sauran yan uwan majinyata keyi, shiyasa buruntun sumayya, khadija ya tayar mikewa tayi a hankali tana kallon sumayya, Aunty lafiya? "Khadija kunun ayannan nake so, kuma ya kare" toh kiyi hakuri Aunty, zuwa da safe sai inje in sai miki, kinga yanzun dare yayi. Sumayya kam ji take yanzun in bata sha kunun nan ba zata mutu, mikewa tayi ta d'au hijab tanufi kofa. Aunty ina zaki kuma? "Neman kunu, ta bata amsa" A daren nan ina zamu samu wani kunu , don allah ki dawo bara nafita ni naje na saya miki. Dawowa sumayya tayi ta zauna a bakin gadon, ta d'auki goran kunu tana shinshinawa. Fita khadija tayi tun sumayya na tsammanin ganin ta har ta fara gajiya, ta jira kusan awa d'aya bata dawo ba, mikewa kawai tayi ta fita a dakin,ba tare da ta damu ba don yanzun damuwar ta kunu ne, ba dare ba,bakin get ta nufa daga ida sai hijab, data d'aura akan zanin ta sai takalmi koh kudin kunu ma bata d'auka ba a hakan ta nufi get. Security ne suka tare ta da mamaki, ganin zata fita da uwar daren nan, duk yanda taso su barta, ki sukayi itama taki koma wa ciki, tana tsaye a bakin get in harta gaji ta koma gefe ta zauna, ta had'a kai da gwuwa. Tsayawar mutun taji a kanta, da sauri ta d'ago ta dubesa sai kuma ta mike da sauri cikin mamakin ganinsa a wannan lokacin.................🍀🍀🍀 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya Ibrahim* 🍃 Page6⃣8⃣&6⃣9⃣ Da mamaki take kallonsa"kaine da daren nan? Kala Ammar baice ba, mika mata goran dake hannunsa d'auke da kunun aya. Da sauri sumayya ta karba, ta fara kokarin budewa jikin ta har rawa yake. Sumayya ki tashi ki tafi daki mana, yanzun fa 3:30 na asuba amma kinzo nan kin wani zauna kamar turmin tsakar gida, kina wani bude gora, sha zakiyi anan?don Allah tashi muje na rakaki ciki. Shuru sumayya tayi taki tashi kafa goran tayi a baki zata sha, da sauri ya fizge goran, kinsan Allah in bazaki bi abinda nake so ba, in ban koma da kunun nan ba. Da sauri ta mike tsaye, sai kuma ta juya tana kallon sa "toh ka bani mana"? Mika mata yayi, yayi gaba tana binsa a baya har suka iso block in da take, goggo ne da khadija tsaye a kofar d'akin sun zuba musu ido, juyawa Ammar yayi zaima sumayya magana, kawai ya ganta tsaye da gora a hannu babu kunu, da mamaki yace kuttt ke sumayya tafiya kike kina sha koh me naga gora ba kome? Shuru tayi sai kuma ta bata fuska, guda d'aya fa ka kawo mini, ina ma laifin takwas. Takwas???goggo da Ammar harda khadija suka hada baki wajen tambayar ta. Sumayya kinsan gora d'ayan nan ma, a ina na samosa bayan likita ya kirani yace khadija taje ta same sa, akan kinason kunu? Kunya nema ya kama sumayya, a hankali ta wuce d'akin goggo da ido ta bita tana kintsima abu a ranta . D'akin sumayya ta shiga rike da goran, ajewa tayi ta kwanta abinta a take bacci ya d'auke ta. Ammar ma tafiyar sa yayi, khadija da goggo ma duk komawa sukayi suka kwanta. Da asuba bayan sunyi sallah, sosai sumayya ta uzura ma khadija Akan kunun aya, haka khadija tun asuba taje bakin get ta zauna har saida masu tallah suka fara fitowa, bata samu kunu ba sai 8:00 na safe, ta sayawa sumayya gora uku. Tana shigowa ta samu sumayya zaune a bakin d'akin, koh magani takisha duk yanda nurse sukayi da ita taki, koh ruwa tace an daina saka mata kenan Alamu dai yau da rigima ta tashi. Tun daga nesa sumayya ta hango khadija mikewa tayi da sauri ta nufeta, "habba khadija zuwa sayan kunun ne, saikije ki zauna"? Yi hakuri Aunty wallahi masu kunun ne basu bude ba saida na jirasu. Karban kunun sumayya tayi ta nufi d'akin zama tayi, takama sha. Khadija kam.kwanuka ta tsina da kayan sumayya masu datti, zata koma gida. "khadija inkin koma gida kibi wajen shagari, ya baki dabino, da kudi kisai min aya rabin kwano, da sugar da kwakwa flavour kimin kunun aya, kisa a firij in zaki taho saiki zomin dashi" Tab Aradu Aunty ban iyya kunun aya ba. "Baki iyya bafa kikace khadija"?sumayya tace tana kallon goggo, dake ta binta da kallo tunda gari ya waye. Kauda kai tayi tama khadija bayanin yanda zata had'a kunun, dayake baida wahala yasa khadija ganewa. Tana zuwa kamar yanda sumayya tace hakan tayi shagari dubu biyu ya bata, taje tayiwa sumayya sayaya har change ya rage, kunun ta dama mata tasa a firij kafun la'asar yayi sanyi haka ta jidi kunun a gora kusan 6 ta kaima sumayya hospital sauran ta barsu a firij. Yau sosai jikin sumayya yayi sauki kamar ba ita ba, da yamma da Ammar yazo likita ya basu discharge,Ammar da khadija ne suke tattara kayayyaki suna kaiwa mota. Sumayya ce tsaye a jikin motar Ammar, sanyi take da riga da siket na atamfa sai hijab mai corona, sosai kayan ya karbeta gashi tayi wani irin fari tayi fresh sosai, idanun nan nata sun kara fitowa sosai saboda kumburin da kasan idon yayi kamar mai ciwon ido, saidai kwayar idon ya kara haske, rike take da goran kunun ta da ya rage kuda d'aya a hannu duk da basha take ba a lokacin. Tun daga nesa yake kare mata kallo, shikaran kansa ya rasa wani irin ciwo ne haka, duk wanda ya santa, ramar da tayi ne kad'ai shaidan bata da lafiya. Ganin ta d'ago yasa sa kauda fuska, kamar ba ita yake kallo ba, boot ya bude ya saka akwatin hannun sa, ya tsaya yana jiran khadija ta karaso da tata jakar, tana zuwa ya rufe boot in . Shiga baya sumayya da goggo sukayi, dole tasa khadija shiga gaba, Amma yaja motar suka cillah. Gidan mai Ammar ya shiga zaisha mai yayi packing,ana loda masa mai A hankali ya sace kallo sumayya, gani yayi gabaki d'aya ta maida hankalin ta gefen glass inda take, alamu dai wani abin take kallo. Juyawa yayi yaga wata yar Christian ne zaune a tsallaken titi tana gashin masara, bayan an gama zuba masa mai jan motar yayi daidai wajen mai masara gasheshen, ya mika mata 500, ta saka masa. Da sauri mai masara ta mike daman ta gaggasasu suna zaune, jimbo ta d'auko tazo ta zuba musu masara guda goma, Hamsin hamsin ne, karba yayi ya aje a mota. Suna shiga sintali gidan goggo suka bi ya ajeta, masara ya d'auko kuda hudu ya bata Amma taki karba. Gida ya wuce dasu sumayya, dayake goggo tace khadija tabi sumayya gidan ta tana ibe mata kewa. Yana packing sumayya kam fita tayi, tayi cikin gida, tana bude kofar su a hankali ta zubawa kofar ido, hawaye na cika mata ido"nayi kewanka yanda ya kamata mijina, nayi kewanka so tarin yawa, don Allah ka dawo, kamin Alkawari bazaka taba barina ba, saidai in nine na gaji da zama da kai, gashi sun rabamu, bansan halinda kake ciki ba, "tana maganar tana hawaye sosai taji kewar mijinta. Toh Allah yayi dare gari ya waye, Ammar daya shigo da akwati a hannunsa da laida yace. Matsa masa sumayya tayi ta zauna akan dakali tayi tagumi, mika mata laidan masara Ammar yayi Ba musu sumayya ta karba, a Hankali kamar wance aka sakata dole tace "thank you for everything" tace tana zaro guda d'aya ta b'amb'are tana ci, Da mamaki Ammar ke kallon ta jin yau ta masa godiya, amma dai baice kome ba ya juya yayi waje. d'aga ido tayi tana kallon Ammar ganin ya dawo, don a zatonta yawuce kenan, da sauri ta mike tsaye tana murmushi har hakoran makkar ta suka bayyana tare da fararen hakoran ta, ganin manyan elagement in hoton su, da Ammar ya fitar a boro. "Wow masha Allah, kamar kasan abinda ke raina akan hoton nan kenan, ka kwashe mini waya" tayi maganar tana karban hotunan a hannun sa tana kallo. Hotuna ne guda biyar, d'aya ita da mijinta, sai kuma d'ayan ita kad'ai, d'ayan shima shi kad'ai, sai d'aya kuma shi da ita da khadija, d'ayan kuma su da kannen Ammar ne, sosai hotunan yayi kyau, abinka da hotuna daukar iphone da background. Yanzun kam kin daina jin haushina kenan koh? "Eh na daina jin haushin ka, tunda har kamin wannan"tana magana tana nuna hotunan. Hannu yasa a Aljuhunsa, ya fitar da wayar ta zai mika mata, Amma wayam yaga bata. Sumayya kam ganin khadija ta bude kofar d'akin yasa ta saurin shiga, wai zata bubbuga hotunan a jikin gini, sake fitowa tayi tunawa da tayi bata da kusa. Sumayya ga wayar ki, yace yana mika mata wayar, kimin Alkawarin mundin kika manna wannan hotunan duk lokacin da kika gani Addu'a zaki masa Allah ya kubutar dashi ba kuka ba. " insha Allah"tace tana karban wayan. Kallon khadija Ammar yayi, kee muje na samo kusa na baki ki kawo mata. Murgud'a baki khadija tayi, wallahi ta tsane yace mata kee innan , haka dai ta bishi a baya. Ba'a jima ba khadija ta dawowa da sumayya da kusa, bubuga hotunan tayi a d'akin ta. Har dare sumayya masaran nan ta ringa ci inta shake tasha kunu a firij, Abinci ma khadija daidai bakinta ta dafa, sumayya kwance take akan gado hannunta rike da masara tana b'amb'ara tanaci, suna kallo da khadija dake zaune akan kujera. A haka sumayya tayi bacci da masara a hannu, tsakar dare ma data farka wanke baki kawai tayi ta gwaguye masara ta koma ta kwanta. Washe gari khadija ta koma makaranta, ganin jikin sumayya da sauki sosai, ta mata wanke wanke da shara, breakfask ma taliya ta dafa laida d'aya taci ta rufe sauran, don sumayya tun asuba ta karya da masara..... ***************** Washe gari kamar yanda bappa ya fad'a haka muhammad yayi maganin sa, yana gamawa ya fitoh kenan ya samu matar gidado ta fitoh zatayi wanke wanke da tsohon ciki, hanata yayi da kansa ya wanke kwanukar ya jido musu ruwa ya ciccika randuna. Suna karyawa yabi gidado kiwo, basu dawo ba sai yamma, kayan sa kala biyu da jallabiyar da yazo dashi da wanda gidado ya basa, ya had'a ya wanke, ya shanya, wanka yayi ya fitoh wajen kofar gidan ya zauna yana bin garin da kallo. Tun daga nesa data sauko a machine ta hangosa kara sauri tayi, bako.. bako...bakon nigeria, tun bata karaso ba take kwala masa kira, sai washe baki take irin dai yanda mutanen kauye kiye in sunga bako(mutanen kauye akwai d'aukaka bako kam) Yajita sarai Amma ya mata banza, harta karaso inda yake d'auke da robobin nonon ta, bako ina kwana?au ina wuni. Lafiya yace yana basar wa don Wallahi yarinyar ta fara isarsa. Kasan me bako? Bata jira amsar saba tacigaba, ai in gaya maka ina zuwa birni nayi kawa yar gayu, harna mata tadin ka, gashi tace tana mika masa abu. Juyawa yayi kawai ya kalleta, ya sake kauda fuska, jin tace masa gashi, menene wannan? Uhmm abune na saya maka, ka bude ka gani. Ba musu ya bude abin, ai baisan sanda dariya ya kwace masa ba, bread ne wani yanka kamar na ashirin, gaskiya karbi kayanki ni baxanci ba babu ruwa na, tunda kudin nonon inna kika saya dashi. Don Allah kai hakuri kaci, in ba haka ba inna dukata zatayi na kashe mata kudi. Gaskiya bazanci ba sai dai na aje miki, in zaki fita kizo ki Amsa. Shikenan in zanje kallon shadi gobe saina karba Shadi? Gobe bazakije tallah bane? Eh gobe a........ Bata karasa ba taji dundu a bayanta mai masifar zafi dimmmm, saida ta wantsala gefe, daga muhammad har indo zaro ido sukayi sai kuma suka dubi wanda yayi wa indo dundu.......... 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 Kuyi manage na page innan wallahi yau typing nayi by mistake ya goge😥😥da yamma. 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya Ibrahim* 🍃 Page7⃣0⃣&7⃣1⃣ Inna Talatu ce tsaye, sai huci take cikin masifa, Wallahi indo in baki fita harkar yaron nan ba, saina saba miki mena fad'a miki akan sa? Don Allah inna kiyi hakuri, bazan kara ba, tace tana mikewa tsaye. Uban me kike mika masa a laida? Inna aikana yayi fa. Shige nace, tayi maganar tana hankad'a indo cikin gida. Al'ameen kam da ido ya bisu, watoh a rayuwa koh baka ma mutum kome ba, in kaje waje sai kaga masoyi da makiyi, zaka ga ka burge wani, wani kuma haushi kake basa. Tsoho kai kad'ai kake zaune ne?gidado daya fitoh gida yace. Eh gidado, yace yana matsama gidadon ya zauna. Gobe fa babu zuwa kiwo. Meyasa? Akwai shadi ne. Ina da yamma ne,?muhammad ya tambaya. Au harma kana da labari kenan? Eh indoce take sanar dani wai bazata tallah ba. Eh gaskiya gobe za'ayi wasa da yamma. Chap sai kuma ya hanaka kiwo?basai muje mu dawo da wuri ba, itama indo taje tallan tah ta dawo da wuri ba. Gaskiya ne, Amma mudai anan in za'ayi shadi duka yan kauye basa zuwa koh ina a ranan. Ok kana nufin kaima kafun kayi aure saida aka farfasa maka baya? kamar yanda nake jin Labari, don mu an daina a garin mu. Eh nima kafun na aure matata, duka akamin Hamsin, yace yana cire rigansa ya nunawa muhammad bayansa. Zare ido Al'ameen yayi ganin wasu bulalu kwance a bayansa rututu duk da sun warke amma tabon su na nan, yanzun kana ji kana gani gidado aka maka wannan? Eh yanzun kai yanda kake kaunar sumayya bazaka iyya tsayawa a bulale ka, don ka mallake ta ba? Zan iyya harma yafi wannan, indai akan tane. Toh baka gani ba, nima zan iyya jurewa. Gaskiya ne Allah yabar kauna, Al'ameen yayi maganar yana kallon gidado. Haka rayuwa yake tafiya, A hankali A hankali har muhammad ya saba da rugar su gidado, yanzun ya waye a kiwo, wata rana har raba shanu suke da gidado, kowa ya kama hanyar sa, tsakanin sa da yan gidan akwai mutun tawa da ganin darajan juna, duk yanda inna ke nuna masa kyama da masifa, bai taba koh d'aga ido ya kalle taba saboda darajan gidado da bappa. Jikinsa Alhamdulilah shi karan kansa yaji sanji a jikin sa, ba kamar da ba, haka tsakanin sa da indo akwai mutunci, duk da ba shiga tsafgarta yake ba, amma makale masa data ke, yasa yakan d'an rage mata wani abin. A sannu sannu gashi yanzun Muhammad na neman wata biyu, a ruga kuma yana cigaba da maganin sa. ********************** Sumayya ma tana nan da halinta nacin masara, sosai ta maida masara da kunun aya abinci, duk lokacin da Ammar zaizo dubata duk da ba shiga cikin gidan yake ba , a waje yake tsayuwa, saiya kawo mata masara koh kunu, sosai take ganin darajan sa kamar d'an uwan ta na jini, tunanin muhammad kam har gobe bata daina ba, saidai ta rage, Ashe haka b'atan d'a da miji yake? har gwara mutuwa wannan ka gama tabbatar wa kanka ya tafi kenan. Yau asabar babu makaranta, khadija ce ke wanke kayan ta a kofar sumayya, yayinda sumayya ke zaune a gefe tana latsa system nata, hannun ta rike da masara Assalamu Alaikum,wani yarone yayi sallama a bakin shashen su sumayya. Wa'alaikumu salam ta Amsa masa tana mikewa zaune, shigowa yayi da kwano a hannun sa ya mikawa sumayya, wai inji goggo Amina. Amsa sumayya tayi tace, yacewa goggo ta gode, budewa tayi gwaten shuwaka ne, yaji kyad'a da tsaki sosai, yawunta ya tsinke da sauri tamike ta d'auko shukali, ta faraci, "khadija ga gwate" Ah ah aunty kici nagode Kala sumayya batace ba, cigaba tayi dacin abinta, harta cinye tass, sai kuma taji bata son shan kunu aya sam, ruwa tasha sai kuma taji yawo ya cika mata baki. Haka sumayya ta wuni tana zubar da yawo, gashi ba yawo kad'an ba, karshe dai kunun nan rabawa yara tayi. Tun daga Ranan sumayya ta maida gwaten shuwaka da macikan zogale, sune abincin ta sai goruba haka ta maidasu abinci, masara duk sun zama tsohon yayi, haka Ammar ma ya maida ganye abin kawowar sa, sam baya gajiya da hidimar sumayya. Yau wata biyu kenan da batar Al'ameen, haka kawai taji a daren tana son cin tsire mai yajin bakuru, da cabbage, haka tasa khadija a gaba suka fita wajen mai nama tsallake sukaje suka saya, sunzo zasu tsallake titi kawai sukaga wani MAKAHO da d'an jagoran sa, zasu tsallake titi alamu dai dare ne ya musu wajen bara. Sosai sumayya tabisu da kallo hawaye na cika mata ido"ina suka kaimin mijina"? Don Allah aunty kiyi hakuri, kinga mun samu kin samu lafiya karki sake jajibo ma kanki ciwo don Allah. Shuru sumayya tayi suka tsallake titi, suna zuwa gida bayan sunci namar ta kwanta akan gado , khadija na kujera,Har khadija tayi bacci itakam ta kasa, , haka ta raba dare idanun ta biyu tunanin Rayuwar da mijinta ya shigane ya dameta. Da asuba da mugun ciwon kai ta tashi da zazzabi, khadija taso suje asibiti Amma haka ta ki zuwa, kafun azahar sosai cikin yayi tsamari Cikin ikon Allah Saiga Ammar yazo, shiya kaisu asibiti, bayan sunga likita ya mata tambayoyi, yace nurse ta bata roba tayi fitsari akai lab. Tunda sumayya taji haka, sam bata damu ba don ita ta d'auka koh ahone ire iren da aka mata, lokacin da hawan jini ya kwantar da ita. Bayan wasu hours, nurse ce ta dawo da result a hannun ta, mikawa likita tayi ta juya ta fita. a hankali likitar ya kalli Ammar ya kalli sumayya, harga Allah ya d'auka ma'aurata ne, Congratulation Aboki na matar ka na d'auke da cikin wata biyu da sati d'aya. Ammar kallon sumayya yayi, daidai lokacin itama ta kallesa sai kuma suka sake kallon likita har suna had'a baki, "ciki"?? Eh ciki wani abune, ya tambaya da mamaki ganinsu haka. Ah ah ba kome likita, Ammar yace yana kallon sumayya data d'aura hannu akan cikin ta, tanna hawaye na farin cikine?koh name oho baigane ba. Am bayan wannan akwai wani abin, ya kamata aboki kana kwantar mata da hankali a matsayin ta na iyalinka, ya kamata ka bata kulawa yanda ya kamata, yanzun juna biyu gareta Amma yanda take saka tunani a ranta, zaku iyya rasa baby ku, ciwon kannan nata tunani ne ya jaza mata, bp nata yahau, kuma bama son haka, a halinda take ciki yanzun nan. Insha Allah doctor za'a kiyaye, Ammar ya Amsa kawai, yana karban takardar magani da likita ya rubuta musu. Fita sukayi xuwa pharmacy, magani ya saya mata suka shiga mota, har lokacin hawaye sumayya take abin gwanin tausayi. Kinga sumayya yanzun fa Dr yaja miki kunne akan damuwar da kike sakawa kanki, waike wace irin mutunce? kukar ne zai dawo dashi kome? " na daina"kawai tace tana share hawayen ta. Me zan sai miki? Girgiza masa kai kawai tayi, Alamu batason kome. Tsayawa yayi a bakin asibiti yasai mata Alale, ya dawo motar ya mika mata Ba musu sumayya ta karba, ta rasa me yasa duk Abinda Ammar ya bata sai taji tanason ci. a haka Rayuwa yake ta tafiya yau farin ciki gobe akatsensa yanzun cikin sumayya nada wata uku cip, bata laulayi haka cikin yazo mata, kamar babyn yasan babu Dad a kusa, saici yanzun kam kome ta samu ci take kamar me, koh zabe batayi. Babu abinda ta nema ta rasa, Ammar na mata goma sha, shagari shike cefenen gidan ogansa, da duk abinda zata bukata shike bayar da kudi,asai mata, maganar lalle ma yanzun batayi sai make-up kawai shima Amare take ma, duk maiso tazo gida, a hakan take ta tara yan kud'aden ta, yanzun sunyi yawa a Account in khadija. Yau dai tunda ta tashi da safe takejin wani irin nishad'i wanda batasan dalili ba, tana tashi da safe dayake yanzun sam batason saka riga,don rigunan sun mata kad'an, sosai nonuwan ta suka cicciko, have vest da zani ta maida su kayan sawan ta, ko mai bata shafawa saboda wari yake mata, haka turare ma koh wani iri bata Amfani dasu. Zaune take a taburma ita kad'ai ta mimike kafa, don khadija ta tafi kasuwa, babu school yanzun suna hutun first time, kosai ne a gaban ta da kunun kyad'a tanaci, sosai sumayya tayi jiki tayi kiba, wuyanta har guru guru yayi, hips natan nan sun kara buduwa haka ma breast nata, daman akwaisu bare yanzun da dalili. Sallama akayi a tsakar gidan, na muryoyin mutane abin ya bata mamaki jin kamar muryar sani, bata gama shan mamaki ba saida taji suna gaisawa da y'an gidan Adara dake tsakar gida, suna tambayar su kofar sumayya. Mikewa tayi tsaye koh d'an kwali babu tsaban mamaki daga ita sai zani a kwankwaso da have vest, jin sun nufo kofar ta, kamar a mafarki Amma dai bara ta tsaya taga ikon Allah, bude kofar shashin ta akayi, da sallama Suman wucen gadi tayi, wallahi ita harta manta da wasu shugaba family, sai sa'i da lokaci take tunasu, cigaba tayi da tsayuwa tanabin wa'inda suka shigo da kallo. Dada ce a gaba sai matan uncles nata da yaransu harta surkunayen su momy ce kawai babu, ko wance cikin shiga ta Alfarma kana ganin su kaga inda naira ta samu matsunguni, murmushin yakene koh wance a fuskar ta, da kunya suma tsayen suke suna bin sumayya da kallo, kamar yanda itama ke binsu da kallo. Mamakine ya kamasu ganin yanda sumayya ta koma, sam bazaka taba cewa auren talaka take ba, sumayyar suce ta zama buhu haka? Takwarata bazaki bawa tsohowa wajen zama bane?gidan ki guda fa nazo, dada tace tana kara bin sumayya da kallon mamaki yar jikanta gabaki d'aya ta canja. "Ga taburma bismillan ku"tace tana shiga d'aki hijab ta saka ta d'auko babban dardumar ta, ta kara shimfid'awa a gefe, ganin taburmar bazai d'auke suba, dardumar ma bai gama d'aukar suba wasu a bakin dakali suka zazzauna. Zama sumayya tayi akan kujera tsugunu bayan ta d'auko sa a kitchen" ina kwanan ku"? Lafiya sumayya, ya maigidan naki? "Lafiya" kawai sumayya ta amsa kamar irin bata ganesu innan ba. Yar nan kice kika dawo haka gaskiya aure ya karbeki sosai wallahi, Hajjo matar babuji tace "Umm ikon Allah kenan ai hajiya, sai ya baka abinda wasu basu so ba"amsar da sumayya ta bata kenan tana cigaba dacin kosanta kamar irin taga sabbin fuskar nan. Jikin dada yayi sanyi, ganin halin koh in kula da sumayya ta nuna musu, da ace dane koh makaranta sumayya ta dawo inta ganta saita mata oyoyo ta rungume ta, suna wasa da tsokanar juna irin na jika da kaka, amma yau kallon banza sumayya ta mata, kawalli yaufa wuni muka zo miki, gabaki d'ayan mun nan munyi kewar ki yar mu. "eh dole kuzo mini jaje ai, tunda kunsace mijin hankalin ku ya kwanta, abinda ake so a gani dai insha Allah baza'a gansa ba, koh xaku mutu haka zaku ganni ku barni, don Mu Allah muka rike" tana magana tana shan kunun ta kamar ba ita ke magana va Miemie ce ta mike, habba sumayya wannan wani irin banzar magana ne, ya zaki bude baki kina fad'awa hajjo da dada irin wannan magana? "Keee mimi, ban kasa dake ba karki kuskura ki kwasa, dasu nake babu ruwan ki a maganar nan, kona karta miki layin rashin mutunci" Eyeeee lallai sumayya, yaushe kika koma mara kunya haka? "Kubra kenan rashin kunya ai dole na koya, koh kin manta gidan da nake ciki ne"?sumayya ta bata Amsa Habba sumayya wannan ba halinki bane, don Allah kiyi hakuri mu da kika gan munnan bamuzo don kara bata miki rai bane, munzo gyara abinda muka bata ne, aunty husna surkuwar uncle Abubukar tace. "Keee Husna karki kuskura kisa baki a maganar nan, ina ganin mutuncin ki, sannan kina maganar ku gyara abinda kuka bata, wani abin kuka bata da har xaku gyara?aini koh sanin ku banyi ba" Mamakine ya cikasu sumayya ta zama yar tasha, sun shiga uku, yarinyar da koh zagin yara bata iyya ba yau harda zagen manya haka. Sumayya dafa iyayen ki maza muka zo gidan nan suna waje. Kallon mammu sumayya tayi, jin abinda tace"meya kawo ku gida na kuma gayya guda haka"? Munzo ne akan auren ki da yaron nan MAKAHO, tundadaman baso kike ba mumuka miki dole, sam yanzun bamu lamunce ba takardan ki xai baki baziki zauna da misk................. ************* Muhammad dai yau shida indo , zasu cikin camaroon tallan nono, ta uzzura masa yau saiya rakata, dayake shima yana son zuwa cikin birni yasa sa binta, yau gidado ne kawai yaje kiwo, bappa da matar gidado wance cikin ta ya tsofa haihuwa yau koh gobe. Cikin Cameroon suka shiga, indo na tallan nono shikam sai kallon gari yake abinsa, basu dawo da wuri ba sai yamma lilis suka dawo. Bappa ne xaune a bakin masallaci yayi tagumi, su Al'ameen suka same sa, gaidashi sukayi suka wuce cikin gida. Da dare bayan isha'i Bappane da iyalansa zaune a tsakar gida harda Muhammad, hira ake sosai, tunda muhammad yazo gidan baitaba ganin sun zauna haka ana hira ba, harda inna da matar gidado lantana, Bappa bakajin dadi ne? Gidado lafiya ta klau, bansan meke faruwa ba tunda na tashi yau nakejin babu dadi a jikina. Toh Allah ya kyauta bappa, inna tace tana kallon sa don tun safe itama ta lura akwai abinda ke damun sa. Ameen Talatu. Amma bappa wani irin abune yake damunka haka? Gidado mubar zancen nan kawai bashi da Amfani. Kamo wani tadin akayi, sai hira ake muhammad nad'an saka baki kad'an kad'an in aka sakosa a zancen. Sosai yau gidan bappa aka sha hira sai chan dare, muhammad ya musu sallama, kwanciya yayi bayan yayi Alwala yayi addu'ar bacci, haka kawai yake jin kirjinsa na bugawa, kwanciya yayi, yayi likimo a gado,har bacci ya d'auke sa. Ta bangaren su bappa, sallama sukayi da juna bayan wucewar muhammad don shiya fara tashi, kowa yaje ya kwanta, Amma dai jikin su a sanyaye, yau dai indo taki kwana ita kadai a dakin ta, tace da innar ta zata kwana, dole tasa inna komawa d'akin indo tabar bappa a dakin sa. Da misalin karfe 1:14am agogon cameroon, Al'ameeen ya farka da salati jin ihu tako ta ina da salati, gari ya kaceme da hayaniya, karan yara da matane kota ina, ga ruwan bindigogi dake tashi, da sauri ya dirka daga kan gadon jin inna na salati da karfi tana wuta wuta jama'a cikin yaren fulatanci .................🍀🍀🍀🍀 Fan's🍋🥑 naga messenge inku ta PC nagode Allah yabar kauna wa'inda bamma reply ba sumin Afuwa abinne da yawa👌 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya Ibrahim* 🍃 Page7⃣2⃣&7⃣3⃣ Fita yayi a d'akin da gudu yayi waje, jikinsa rawa ya soma ganin An cinnawa gidan bappa wuta, ga sauran gidaje duk wuta ke tashi da karan mutane da guje guje. Gidado ne ya fitoh d'aki rike da matar sa, da tashin hankali yasa ta nakuda, ya kalli bappa dake xaune shuru, babu alamun tashin hankali a fuskar sa hakama babu alamun kwanciyar hankali. Inna ce ta mike da sauri ta isa garesa, hannun lantana ta kama wance ke kokarin faduwa,gaskiya haihuwace gadan gadan fa bappan gidado musan abinyi. Hanyar wajen gidado ya nufa hannunsa d'auke da wuka sharbebiya. Kai gidado ina zaka?koh bakajin abinda ke gudana a waje ne?muhammad yace cikin tsananin tashin hankali. Kaga ku zauna a ciki bara na fita, mu munfi karfin ana kashemu, muna buya sai dai a fito a gwabza, yana magana yana kokarin barin gidan. Kaiiii gidado, fitar da zakayi ba shine mafita ba, kanada tabbacin inka fita zaka dawo ka samemu a raye?wuta fa aka kunna wa gidan nan, mafita zamu nemawa kan mu, na fita a garin gabaki d'aya. Allah ya sauwaka, mugudu mubar mahaifan mu, da Arzikin mu. Gidado kabi abinda yaron nan ya fad'a, don yafika gaskiya nakuda matar ka take, kamata yayi ka fitar da ita, ga indo can sumar ta biyu,inna tace tana nuna indo dake zaune a gefe kamar ruwa ya cita. Shuru gidado yayi ya tsaya sosai jikinsa ke rawa , kowa yasan yanda ran fulani yake baci in an tabo musu dukiya ba sauki, gaskiya inna saidai kuzo kutafi da ita kaima muhammad ka bisu, mukam zamu kare shanukan mu, yayi maganar yana tsinka zanar bayan gidansu wanda wuta bai iso gunba. Soyayyar da ka iyya jure shadi akanta, da soyayyar tsakanin uwa da d'a, bazaka iyya sadaukar da arzkinka ba, gidado ku rayu tare? Mikewa inne tayi, gidado ya ciccibi matarsa da tiyo ya fashe ruwa yana zuba, da gudu indo ta rike hannun inna, muhammad ma binsu yayi a baya, har sun shiga bandaki kafun suka tuna da bappa yana bayansu, juyawa dukansu sukayi suna kallon sa har lokacin bai motsa ba. Inna ce ta dubesa, Bappan gidado yakana zaune kazo mu tafi baka ga halin da yarinyar nan take ciki bane? Kuje kawai Allah ya tsare hanya, ni bazan iyya gudu a rugan mu ba. Habba bappa yanzun kafison ka zauna azo a kashe ka, hakan bai dace ba koh a addinan ce, kana da damar kare kanka, ka bari a kashika, muhammad ya karasa maganar yana karasowa kusa da bappa. Don Allah bappa y'an dillo, indo tace tana kuka. Girgiza kai bappa yayi, kuyi hakuri bazan iyya zuwa ba. Muhammad ne ya dube gidado, kaga gidado ku tafi da inna, lantana da indo , ka fara fitar dasu, muna zuwa da bappa. Sanin taurin kai da kafiya irin na bappa, yasa gidado da inna suka fita ta zanan bayan gida, harda lantana data gama galabaita da indo. Zama muhammad yayi kusa da bappa sosai zuciyar sa ta tsinke, ganin yanda wuta yaci rabin gidan yanzun ma wani irin turiri da rad'adi yakeji a jikinsa ga hayaki, bappa don Allah badon niba kazo mu tafi a rugan nan, rayuwar ka tana da matukar Amfani wa Ahlinka, kasan wani irin hali zasu shiga in aka waye gari baka?akan iyya rasa dukiya, wata rana su dawo, Amma ba'a taba rasa uba wani ya maye gurbinsa har Abada, kama iyalinka adalci ka rayu dasu koh ba kome zasu walwala koh ba shanukai, akansu rayu bakai ba dukiya. Kuka bappa ya fashe dashi, babana bazaka gane bane yanda abin yake, akwai zafi azo a same ka har gidan ka a kwace maka dukiya, a kwace maka muhammali, asaka gudu kamar barawo ina sukeso muje, irin wa'innan mutane, sune sukayi sanadin iyaye na, shekara talatin baya, mu kullun cikin zulumi muke bamuda sakat? Kayi hakuri bappa, rayuwa tafi kome muhimmanci ita d'ayace, kayi hakuri mu fita anan, yana maganar yana kama hannun bappa ganin jikinsa yayi sanyi, kamasa yayi suka nufi bayan gidan, suka fita ta zanan gidan. Da ido bappa yake bin rugansu dashi, ganin gawawwakin fulani cikin jini manya da yara, kota ina hayaki ne. Tafiya suke kamar wasu barayi a hankali a hankali, suna bin ciyaye kamar a mafarki muhammad yaga yan ta'adan nan sanye da kakin sojoji ga bindigogi manya manya a hannunsu, kafun ma su buya tuni sun gansu, ai da gudu muhammad ya kama hannun bappa suka nausa daji, da gudun tsiya, suma suka rufa musu baya. Gudu muhammad yake da bappa suma suna binsu a baya, bappa ne yayi tuntube ya fadi tim, da sauri muhammad ya dakata kokarin tayar da bappa yake, Amma bappa ya kasa saboda ya buga kafarsa mai ciwo a dutse, ka tafi kawai yaron nan ni inaji lokacina yayi, Allah yamaka Albarka ya sadaka da ahlinka lafiya, sai wata rana.bappa yace. A karon farko muhammad ya sake kuka mai karfi, harga Allah a d'an zamansu da bappa jinsa yake kamar mahaifinsa, don Allah bappa karkace haka, bara na d'agaka, ciccibar bappa yayi, yana gudu kamar kiftawar walkiya yajisa a kasa dagashi har bappa, mummunan buguwa sukayi muhammad saida tsakiyar giransa ya tsage, saiga jini bappa ma gwuwarsa ta kwarzane sosai. Kafun ma ya mike tuni yan ta'adan nan sun kewaye su, d'aya daga cikin sune ya taka kafar muhammad saida yaci ta baki, jini ya balle masa, bindiga d'ayan yasa ya buga a kan bappa, kara bappa ya sake yana dukawa hade da rike kansa da karfi yana salati, jin wani irin azaba mai tarin yawa na bazata. Don Allah kuyi hakuri, karku cutar dashi don Allah, muhammad yana magana yana kuka. Kai ragon maza kaika san Allah ne?wani a cikinsu yace. Kuyi hakuri... Bamuda imani bare hakuri. Bappa dake duke har lokacin jikinsa sai rawa yake tsabar azaba, kamasa d'ayan yayi ya kwantar kaman rago yasa masa wuka a wuya. Ai muhammad na ganin haka yayi wani irin mikewa da karfi, ya bangaje mutumin da ya takasa, duk wani tsoro ya fitar masa a rai ganin tabbas abu biyune zai faru rayuwa koh mutuwa, rugawa yayi da gudu ya nufi bappa, kafun ma ya iso garesa tuni mutumin ya dirza wukar jini ya fantsama. Zuciyar muhammad ta riga ta kikashe yanzun, yaga mutuwar mahaifiyarsa, kaninsa, amma bai taba ganin mutuwar da ta mugu-mugun ratsasa ba irin wannan, sharbeben Adda dake rataye a jikin d'aya daga cikin yan Ta'adan ya zare da karfe, kafun giftawa da bismillah tuni muhammad ya shiga fad'a da mutanen nan, cikin bazata da rashin tsammani,Allah kad'ai yake kira, yakini kawai yasa a ransa koh yakashe koh a kashesa, suna da bindiga shikam wukane kawai, sosai suke..zuba alburusai yana kaucewa, cikin rashin sa'a wani yasake bullet, ya kuskure sa a hannun hagunsa, ihu yasa da karfi yayi kan mutumin, wukar hannunsa yasa ya fille masa kai,sosai jikin muhammad yake bari ganin yau da kansa ya kashe mutum shi muhammad, mutum hudu ya kwantar, daman su hudun suka bisu. Mikewa yayi ya sabe gawan bappa, sai kuma ya rasa ina zai nufa dashi, tunda fa ya fitoh baiga su inna ba, wani shawara ne ya fado masa, aje bappa yayi ya sabi bindiga da wuka ya koma cikin rugan su gidado. Tun daga nesa ya hango fulani da aka tara waje d'aya, cikinsu harda su gidado da wasu kattai suka danne sa, sai lantana dake kwance bata motse, sai jinjira a gefe tana cillara kara cikin jini koh cibi ba'a yanke mata ba, Alamu dai daga haihuwarta ta riski wannan masifa. Bin jikin ciyayi muhammad yayi ya saita mutanen da suka danne gidado, su biyar gabaki d'aya ya sakar musu bullet one by one, ai take yan ta'adan nan suka fusata suna sake ruwan harsashi ta saitin muhammad, da sauri ya kwanta a kasa. Wanna daman gidado ya samu da wasu matasan fulani suka d'auke wukake da adda aka fara aran gama. Inna dake gefe da sauri ta rarrafa zuwa wajen jaririyar, wuka ta karba a hannun wani ta yanke mata cibi, nadeta tayi a d'an kwallinta ta kama hannun indo, tare da wasu matan suka ruga a guje, sukayi daji kowa yayi takai takai, aka bar gawan lantana a wajen, don ta rai ake. Muhammad yau an zama zaratan maza sosai ake gomxa fad'a, duk wani tsoro nasa yau ya kau, yakini d'aya a ransa zaiyi rai koh ah ah, ganin yanda wasu dakarun barayin nan suka fara shigowa rugan, suna karuwa har sun fara ninkesu, gashi mata da yara da suka rage a raye sun dade da gudu, yasa muhammad d'aga murya da karfi, kowa yayi ta kansa karuwa suke aje-aje zasufi karfin mu. Ai yana maganar nan da gudu ya kama hannun gidado da wani saurayi zaiyi sa'an sa suka nausa daji da gudu, haka ma sauran mazan ana harbinsu suna gudu wasu na faduwa matantu, barayin suka mara musu baya, yayinda su kuma suka raba kawunan su, kashi-kashi. Muhammad gudu suke a daji koh gabansu basa gani, gudune irin na bakin Rai bakin fama, nausawa daji suke yan ta'andan nan na binsu, a hakan suka ringa gudu, (wani abu sai tashin Hankali kayi abinda koh da kudi aka had'aka bazaka iyya ba, sai kaga masifa)sosai sukayi nisan kiwo, gudu suke mutanen na binsu suna sake bullet, Allah ya tsare su, har suka isa wani baban ruwa fad'awa sukayi ciki, yaufa muhammad da kansa ya tsallake ruwa, suna tsallaka kogin har lokacin mutanen na binsu, sosai suka kara azama basu jima da gudu bayan tsallake kogi na biyu, suka hango wani kauyen, ganin Hakan ne yasa mutanen juyawa suka barsu. Faduwa muhammad yayi dasu gidado a kasa, ganin sun shigo cikin mutane, A raye basu mutu ba, karasawa sukayi cikin gari. Sun ma rasa ta ina zasu fara, fahimtar da sukayi garin kamar babu alamun musulunci, ganin yanda mutanen garin suke, buya Al'ameen sukayi basu bari hankalin yan kauyen ya dawo kansu ba, a hankali suke bin cikin gonaki har suka tsallake kauyen lokacin dare yayi sosai, don akiyasce zaikai 10:00 na dare, gindin wata bishiya suka samu suka zauna, kowa na maida numfashi koh bacci basuji yau, muhammad kam jingina yayi da jikin bishiyar ya lumshe idanunsa yana tunanin rayuwa, tunda ya tashi yake ganin jarabawa iri iri, Amma baitaba zata zaiga irin nayau ba, ace tun 2 na dare yana cikin tashin hankali har dare war haka, ada yayi tunanin zuwan sumayya da farin cikin da ya samu, baitaba tunanin akwai sauran wani damuwa ba, ya zauna da sumayya da zuciya d'aya, duk da an sanar dashi ita ba mutuniyar arziki bace, auren jingina za'a basa, hakan yaji A Ransa zai iyya zama da ita cikin aminci, baitaba sawa ransa, don sumayya tayi ciki zai gujeta ba. A Ranar daya samu tabbacin farin cikin sa, sumayyar sa budurwa ce, yaji dukkan wani damuwa kunci ya yaye, a lokacin rayuwa yake tuna musu mai dadi nan gaba,don ya tabbatar auren sa da sumayya akwai dalili, bai d'auka zaiga irin masifar yau ba, shine yayi kisa?kisan ma mutum d'aya ba, ba biyu ba, atake yaji aransa tabbas yanason zama SOJA don ya bawa kasarsa gudumawa, da maganin ire iren mutanen nan, indai da rai da lafiya koh kurtune inya koma gida zai nema, tunda ba ilimi mai zurfine dashi ba, insha Allah sumayyar sa sai tabar Amsa sunan MATAR MAKAHO zuwa MATAR SOJA........ ******************* Bazaki cigaba da zama da miskini ba yanzun sumayya, mahaifin kima yace gobe in Allah ya kaimu zaku wuce garin su mahaifiyar ki. "Kin gama, koh baki gama ba"? Na gama sumayya. "Toh bara kiji, ni a haka naga mijina kuma nake son zama dashi a miskinin, banga wanda ya'inda suka isa su rabani dashi ba, wallahi sai mutuwa karyar mutum" Sumayya Rashin kunyar da kika koya harya kai haka, bansani ba shige toh muje, su Abie na waje saikije ki kare musu tanadi bamu ba, aikoh me muka miki bamu shanshanci wannan iskancin ba. "Inje ina? mijina bayanan kuma baibani izinin fita waje inga kowa ba" sumayya tayi maganar tana tura kosanta a baki bibbiyu ma, take turawa irin na huce haushin nan. Innalilahi wa'inna'ilaihi raji'un na shiga uku ni sumayya,na lalace da'aka had'a baki dani aka aurar wa yan iskan Adarawan nan, yarinyar yarona ni sumayya na bonu, wi.. wi. wi dada ke kuka tana maganar nan gwanin tausayi Mimi ce ta mike tayi waje, wajen su Abie dake zaune a cikin manyan mototi a waje na Alfarma, gabaki daya yan unguwan sun maida hankalinsu kan mototin, atunanin su koh wani masifar yan gidan suka jajibo. Miemie na isa kuka ta fashe dashe a bakin motar da abie ke ciki. Da sauri dukansu suka fitoh a motar , magidanta ne sun d'an manyanta, su biyar harda abie sai samari hudu da masu aure biyu, abie da sauri ya fara tambayar mimi abinda yake faruwa, ina sumayyar?gabaki d'aya inka gansa sai ya baka tausayi. Tas mimi ta zayyana musu kwandon masifar da sumayya ta juye musu, kuma tace bazata fitoh ba mijinta bainan. Ita sumayyar ce ta fad'a miki haka?babuji yace yana rike baki. Eh babuji.... Ke kije cikin gidan kice ana sallama damai gidan, babuji yace wa mimi. Juyawa tayi ta shiga gidan, daidai lokacin Ammar ma yayi packing in motarsa, suka fitoh shida khadija a ciki, rage mata hanya yayi a bakin kasuwa. Karasowa yayi da sauri kusa da dasu, cikin sallama ganin su mutane ne ba raini, gaisawa sukayi, khadija ma ta gaidasu, tana mamakin meya kawos, don bata mantasu ba, sune iyayen sumayya, cikin gida ta shiga ta barsu a waje harda Ammar. Bayan d'aya daga cikin mazajen gidan adara ya fitoh, gaisawa sukayi dasu babuji, sannan suka nemi izinin shiga cikin gidan zasuyi magana da yarsu in ba damuwa. da mamaki mijin inno ke kallon su izini shi ai harma ya manta ana neman izini, kafun a shiga gidan wasu, suda gidansu ina yaga izinin shiga, amma dai ya maze yace su shigo. Ammar fa zare ido yake, wai meke faruwa ne haka, yasa sa binsu a baya suka shiga ciki. Sumayya na tsaka da cimar ta, taga shigowar Familin su maza, kwarjinin da suka mata yasata mikewa tsaye, haka kawai taji gwuwarta yayi sanyi, had'a ido da tayi da abienta dake binta da kallo, baitaba tsammanin xaiganta haka ba, daren jiya koh bacci baiyi ba, yana zullumin halinda xaizo ya risketa yau. Sannu sumayya tunda baxaki fita ba, mu munshigo munsame ki, uncle gaddafi yace. Tsunkuyar da kai, kawai sumayya tayi batace kala ba. Shige mu tafi, in mijin naki ya dawo saiya zo muna da magana dashi, wannan auren bamu yarda dashi ba, daman kudi muka biya sulaiman akan auren. "Kamar ya uncle bangane baku yarda da auren ba? Kuma ba wanda ya baiwa muhammad kudi, asalima cemai akai ciki ne dani" Eh Momcy gida zamu koma gaskiya bazaki cigaba da xama a gidan nan ba,ai daman mu muka sakaki auren sa, yanzun kuma munce bazaki zauna dashi ba, uncle nata d'aya yace. Hajjo ce ta kalli sumayya, kuma kaf mu innan babu wanda ya miki kazafin zina in karya muke a kira sulaiman in, don mu sulaiman in ma bamu sansa ba jinsa kawai muke a waliyin mijin da muka baki. "Ai uncle bakin Alkalami ya bushe, a da kunada iko dani Amma banda yanzun, ban shirya xama karamar baxawara ba, ina son mijina. Sumayya!! abie ya kirata da dukkan yakininsa, yau koh momcy baice ba sunan Dadansa guda ya Ambata, sumayya yau nayi miki Alkawarin cika miki burinki, zan kaiki kiga mahaifiyarki kiga danginta, zan dawo miki da aikin ki, ki Amince mu koma gida tare. Kara khadija ta sake da karfi, hade da kuka wayyo na shiga uku don Allah kuyi hakuri, wallahi yayana na sonta babu abinda baya mata, kuma ba mutumin banza bane, don Allah karku rabasu da Aunty, wallahi nima ina son zama da ita. "Kiyi shuru khadija koda Al'ameen bazai dawo ba, ni bazan taba barin gidan nan ba, koda na bari toh ba gidan shugaba zan koma ba, ku fita ku barmin gida banason ganin ku, nace ku fita"tayi maganar cikin karfi sai kuma ta sulale ta zube a kasa sumemmeya. After 6 hour's sumayya ce kwance a gado an d'aura mata ruwa a hannu, sai khadija dake gefen ta a zaune idanu jahur, sai Ammar dake gefe shima a zaune, cikin tashin hankali. A hankali sumayya takalli ammar " sun tafi"? Ah ah sumayya basu tafi ba tunda aka kawoki suke zaune a asibitin nan, yanzun ma sunso shiga likitane ya hana, kamar yanda kikace saboda yanayin bp ki, sumayya duk da bansan meke faruwa ba, nasan tabbas iyayen kine su, kuma iyaye darajane dasu baikama ta ki musu abinda kikayin nan ba, sannan abinda ya tsayamin a wuya, abin mamaki daman ba auren soyayya kukayi da Al'ameen ba? Don nasan sone kawai zaisa ke dashi ku kasance a karkashin inuwa d'aya, duba da duniyar mu ayau mai kudi sai mai kudi miskini sai miskini, talaka sai talaka Amma ke kullun sai na kwana da lamarin ku keda muhammad A raina, a yanda na ganku naga tsantsan kula da juna da soyayya, gaki kyakkyawa ruwan manya, kullun saina tambaye kaina taya kika aure muhammad?Amma Amsa d'aya nake samu soyayyace , don Allah yau ki fad'amin wani abu game dake koh muhammad, koh nima zansamu na kunce kullin dake damuna akanki. Hmm Ajiyar zuciya sumayya tayi, sannan a hankali ta bude baki"yau zan sanar dakai wacece sumayya Abdusalam Shugaba, ada kafun ta zamo MATAR MAKAHO...........🍀🍀🍀🍀 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya Ibrahim* 🍃 page7⃣4⃣&7⃣5⃣ Abdul'aziz wanda aka fi sani da shugaba, haifafen mambila plateau(Gembu) ne, Ainahin su fulanin gembu ne, acan aka haifi Abdul'aziz,duk da yana kauye hakan bai hana shugaba karatu ba, yayi karatun sa na secondary kafun yayi aure, matar sa ta farko fatima wance ake kira da fa'i, ita ma yar gembu ce, auren dangi aka musu, kafun daga baya ya aure sumayya (Dada), a kauyen su yake rayuwar sa da matan sa biyu,da yaransa maza biyar, yaran fa'i uku, Abdul'aziz mai sunan babansa(babuji)sai Abubakar da gaddafi,sumayya(dada)nada maza biyu itama, Usmanu sai Abdulsalam(Abie)shine autar gidan su, akwai kyakkyawar fahimta da zaman lafiya agidan, shugaba(Abdul'aziz)hakan ya samu asaline daga zaman lafiyar da matan keyi, zamane na kwatance a kauyen su, kaf kauyen babu gidan da zaka shiga kayi mamakin zaman kishiyoyi iri na gidan shugaba, sosai abin ke bawa wasu mazan sha'awa, don shugaba adaline a gidan sa, duk da auren soyayya sukayi da sumayya hakan baisa ya nunawa fa'i banbanci ba. bayan wasu shekaru an samu fad'an kabilanci a gembu sosai,tsakanin mambilawa da fulani wanda yazamo sanadin mutuwar fatima uwargidan shugaba, da mahaifiyar shugaba, daman mahaifinsa ya jima da rasuwa, wasu da dama a yan uwansa sun rasa ransu, a rikicin da ya afku. Bayan kome ya daidaita, shugaba ya saida duk wani kadara nasa na kauye wanda mahaifinsa ya mutu ya bar masa, don shikad'ai babansa ya haifa namiji sauran matane kuma duk sunyi aure, ya dandanka musu nasu gadon. Jalingo babban birnin jahar Taraba, ya tattara iyalansa suka dawo jalingo, gida madaidaici shugaba ya saya, yasa yaransa a makaranta, dada tana kula dasu kamar y'ay'anta na cikin ta, sam bata nuna musu banbanci da nata duk d'aya ta d'auke su, wannan abin shiya kara dasa soyayyar ta, a zuciyar mijinta. Bayan wasu shekaru kudi sosai ya fara zama a Aljuhun shugaba, don business yake na manya manyan shaguna zanunuwa a kasuwa yana order daga kano, aje aje yakoma na mototi, Arziki kullum gaba gaba yake ga yaransa na makaranta, duk wanda ya gama secondary, kwasar waje yake turasa karatu. Lokacin da yaransa suka fara nisa a boko , hakan yasa ya sakar musu wasu kud'ad'e su gwada tasu kasuwar, babuji da Abubakar sune suka fara kammala karatu, suka fad'a business abinka da yan boko, kuma kwararu a bangaren business, kankace kome kudine ya zauna company suka kafa mai zaman kansa, tare da haden gwuwar junan su, sosai arzikin su ya fantsama. Babuji da Abubakar a rana d'aya sukayi aure , wasu yaran jalingo suka aura wa'inda suka hadu a makaranta, bayan auren su, saida suka haifi yara bibbiyu, kafun gaddafi da Usman sukayi aure. Abdulsalam ya kammala karatunsa Amma sam yaki aure kaman yan uwansa, duk yanda iyayen sa sukaso yayi sai abin yaki, dada har magani take saka masa a abinci koh Aljanane ta aura mata yaro, Amma ina shuru abu yaki kowa aka nuna masa yace baya so, bata masa ba hardai su gaddafi suma suka hayayyafa sosai , a lokacin yaran babuji biyar, na Abubakar uku, yaran gaddafi biyu, na usman hudu. Bayan wasu yan shekaru shugaba ya kwanta ciwo, baiyi wani dogon jinya ba Allah ya karbi rayuwansa, gadon da aka raba musu shi suka had'a suka gina katafaren gida a unguwan specialist, gabaki d'ayan su suka tattaro kan iyalansu suka dawo cikin gidan da zama, don a lokacin Babuji da Abubakar suna da company kansu har biyu, yayinda gaddafi yake aikin goverment, usmanu d'an siyasa ne, Auta Abdulsalam shi ma'aikacin Bank ne(Accounter)kasance warsu rikankun yan boko ga naira ga kyau, kowa yasan yanda fulanin gembu keda tsananin kyau. Rayuwa ake a cikin shugaba family house mai kyau, daban sha'awa, mazan basu bawa matansu daman da zasu kawo musu tashin hankali ba sam, koh kara kika kaiwa mijinki matar wansa ta miki kaxa, had'a meeting ake a kira kowa, ku maida maganar hakan yasa matan sam suka daina fad'awa mazajen su, saidai ayi iyya mata da mata kasa kasa. Auren Abdulsalam ne yaxo musu da sabon salo, saboda yarinyar da ya kawo akan ita zai aura, yar maiduguri ne Amma tana karatu a TSU, tazo bank inda yake aiki cire kudi, Allah ya had'asu kanuri ce, hakan yasa dada tace ita sam bata yarda da auren nan ba, bazasu aure babarbariya ba, abinda ya xamo cecekuce a gidan kenan, duk yanda Abdulsalam yaso fahimtar da ita son da yake ma yarinyar, abu yaci tura sam taki Amince wa katafau tace bata yarda ba, shikuma Abdilsalam yace muddin ya rabu da Hafsa toh shikam bazaiyi aure ba. Aijin haka yad'agawa dada hankali don tasan sarai halin Abdulsalam, akwai kafiya kamar me, tayaya ma aka samu ya samo hafsar kullum yace yakusa aure shuru baiyi ba, bare yanzu yace bazaiyi ba ai magana ta lalace. Babu yanda ta iyya da banbakin su babuji ta Amince da auren hafsa, har maiduguri akaje da zancen auren. su karan kansu iyayen ta sunso gardama amma ganin sannanen family ne, yasasu karbansu da hannu bibbiyu, tare da kafa sharadin yarsu zata cigaba da karatu insun amince, zasu basu ita? Amincewa kam sunyi saboda kaf gidan shugaba yan boko ne, hatta matan gidan na zuwa aiki, rainon yara ma dada keyi da masu aiki. BAYAN AURE Hafsa fa ta fara fuskan tan banbancin launi a gidan su Abdulsalam, kasancewar ta baka kuma kanuri, sabanin yan gidan shugaba farare ne, daga matansu har maza da yara gasu fulani kyawawa, don Abdulsalam baza'ace kyaune ya rud'asa akan hafsa ba, ah ah sonta ne kawai Allah ya diga masa a zuciyar sa yaji baya ganin kyaun kowace mace sai nata, sosai ake nuna mata banbanci kuma ba wanda ya fara asasa hakan sai dada, haka zasu zauna suna hira daga sun ganta zasu koma yi da yare basa janta a jiki, inta matso garesu basa sonta rabesu sam, kansu a hade Amma ita sun ware ta. Hakan dasuke, yama hafsa zafi, yasata watsar da kowa na gidan, ta kama karatunta daga ta dawo makaranta ta shiga kitchen tayi girkinta, zata haura upstair's, ta shiga d'aki bata fita sai mijinta ya dawo. Abdulsalam yasha had'a meeting da korafi akan abinda akema matar sa, duk da bata fad'a masa ba, yaga alama yayunsa mazane kad'ai ke sonta. A haka fa abu yaki chanjawa abubuwa sai cigaba suke a haka, hafsa zaman hakuri take a gidan, babu zagi babu duka, Amma ana nuna mata mugun hali kam, a hakan cikin hukuncin Allah ta samu ciki, wanda kaf gidan babu mai farin ciki sai ita da mijin ta da yan uwan mijinta, amma babu ruwan matan dasu dada da ita, gashe cikin yazo mata da laulayi, bata iyya aikin kome, kuma babu mai taimakon ta, karshe dai Abdulsalam d'aukar hutu yayi a bank ya zauna a gida yana kula da matar sa, amma abu yaki karshe dai kiran iyayen ta yayi aka turo masa kanwar hafsa, tazo ta zauna da ita har cikin ya tsufa bata koma ba. Wata ranan Alhamis hafsa ta tashi da nakuda tsakar dare, Abdulsalam da kanwar hafsa ne, suka kaita asibiti don baiko sanar da yan gidan tana nakuda ba, hospital aka kaita kafun asuba Ta santalo yarta kyakkaywa fara tas, jinin gembu mai tsananin kama da zuriyar gidansu, koh kama da hafsa batayi kome na babanta ne. Sosai Abdul yayi farin cikin samun wannan baby, ga wani irin sonta daya ke sosai yaji son babyn sa, washe gari ne yan gidan suka tashi sukejin labarin haihuwar a bakin mazajen su, Dada da matan sunje asibiti bada son ransu ba, saidai ganin yanda Abdulsalam yahad'a wa kowa fuska, gaisuwa ma dada kawai ya gaishar, ya shiga yad'auko kayan baby ya fita, hakan yasan su zuwa duba baby. Ba karamin dadi sukaji ba ganin yarinya kamar su ta biyo, bama kamar dada a murna, zama tayi a asibitin taki tafiya ita kema yarinya wanka, duk da yar uwar hafsa tazo washe gari Amma dada ta karbi kome na baby, harsuka koma gida dada fa na leke da yarinya, ranan suna yarinya taci sunan dada sumayya ana kiranta da momcy, haihuwar sumayya shine musababin zaman lafiyar hafsa, sosai taga change agun dada haka ma matan gidan, sosai suka koma damawa da ita, itama bata rikesu a rai ba, a sannu sannu har itama ta fara jin fulatanci duk ta maida martani na bata wuya, amma babu abinda zaka fad'a da fulatanci bata sani ba, dayake gidan sosai suka rike yarensu, suna hausa Amma ba sosai ba. Sumayya(momcy) tana da shekara hudu Abie inta ya shigar da ita makaranta, lokacin hafsa(ummi)ta kammala karatunta na jami'a ta fannin koyarwa, taso kara gaba Amma abie ya hana, aiki yasama mata na koyarwa a makarantar secondary, wannan kenan. Sumayya na cika shekara biyar kanin Dada Allah ya masa rasuwa a gembu, dukansu sukaje taziya, bayan sadakan bakwai dada ta d'auko yarsa daya haifa guda d'aya, mai suna safina(momy), bayan dawowar safina family shugaba, sai abubuwa suka fara bullowa saboda tunda safina ta shigo gidan shikenan ta fara likewa Abdulsalam(abie)duk wani iyayinta abie baya kulata, asalima sai ya daina zaman falo kwata kwata koh abinci ne saidai suci da ummi a d'aki, abin har yakai ga dada ta lura da hakan, sosai ta nuna masa bacin ranta akan yana nunawa safina mugun hali don tana zaune a gidansu. Zama ya fara rashin dadi lokacin da safina ta fitoh karara tace ita abie take so, sam abi yaki zancen kuma ya nuna bazaiyu ba, ummi karan kanta a lokacin ba karamin bakin ciki taji ba, don gwara tayi kishi da kowa akan safina, irin yaran nan ne shegun kauye masu shiga idon mutane, gashi batada kunya sam. Dada fa ta tuntube abie akan zancen ya nuna bazaiyu ba, hakan yasa dada bata tilasta masa ba ta watsar da xancen, abinda ya konawa safina rai kenan, kaf gidan babu mai supporting nata, kowa ya nuna baya goyon baya akan zancen, harda matan babuji basa sonta. Safina makaranta aka saka ta na islamiyya, don sam taki zuwa boko duk yanda akayi bazata ba islamiyyar ma daker ta fara zuwa, zuwan ta islamiyya shiya had'ata da kawa nafisat, nafisa irin yaranan ne watsansu marasa jin magana, haduwar su da safina, yasa nafisa nunawa safina abubuwa da yawa, ta kara kangarar mata da kai, bata tsoron uban kowa. Abin yayi matukar d'agawa dada hankali duk yanda taso rabata da safina abin ya gagara, gashi a lokacin nafisa bazawarace harda y'a d'aya take dashi, hakan yasa dada mawa safina barazanan zata maidata kauye, amma safina koh a jikin ta, ta nunawa dada koh ta maidata kauye tasan hanya, duniya da fad'i. Bayan wata uku da haduwar safina da nafisa, lokacin sumayya nada shekara 6 a duniya, hafsa ta fara ganin change a zaman su, sam yanzun zaman ba dadi tsakanin ta da mijinta, kullum cikin rikici suke wanda itama karan kanta batasan dalili ba, sosai abin ke damunta, wasu lokacin har Abdulsalam na dukanta, Amma bata taba fad'awa iyayen ta ba, koh wani nata saboda tanason mijinta, sai kawarta wance suke karantar wa a makaranta d'aya, don lokacin kanwar ta da aka kawo mata lokacin cikin sumayya tayi aure, batada wani nata kusa. Yau an waye gari da wani masifa a gidan shugaba, amma dada satan sarkan gwal inta, sosai tayita masifa tana zagin yan aikin gidan wance ke mata gyaran d'aki kamma koranta akayi, koh sati ba'a kara ba aka sake ma hajjo(matar babuji) sata, ba'a kama barawon ba, haka aka ringa sace sace kusan wata har rashin yarda ya shiga tsakanin juna, kowa na zargin d'an uwansa, ba yan aiki kad'ai ba. Kamar yau aka sacewa Matar abubakar agogonta na demond, yau kam masifa aka sake akan sai anbi d'aki d'aki anyi bincike, sai an fitar da barawon don kaf gidan tunda safe babu bakon daya shigo koh ya fita, kuma kowa na gida ranan don weekend ne. Bincike aka ringayi har akazo d'akin hafsa, kamar a mafarki aka ga agogo da wasu sarkoki na dada a cikin wardrop na ummi abinda ya kawo cece kuce dacin mutuncin hafsa a gidan. Daman mai hakuri bai iyya fushi ba don ita da iyya gaskiyar ta, bata d'auki kome ba yama za'ace a iyya tsawon zamansu bata taba sata ba? sai yau sannan ita aitafi karfin sata tunda bayar matsiyata bace ita, sosai ta fara maida martani kowa ya gaya mata bakar magan fad'a masa take ita ma, ana cikin haka abie ya dawo daidai lokacin dada ke zagin hafsa, ita kuma ta gaya mata bakar magana, daman tun asali bata son zaman ta da d'anta, shiyasa ta had'a baki aka lika mata sata. Abie babu tambayar ba'asi yaja ummi d'aki ya rufe, duk da sumayya yarinya ce, amma a ranan tasan gidan shugaba sunyi ma mahaifiyar ta ba daidai ba, duka abie yama ummi kamar zai kasheta daker aka kwaceta. Cikin kuka ummi ta kira kawar ta a waya don ta tsorata lokacin, ganin jini nabin kafafunta, bayan zuwan kawarta, asibiti ta kaita ashe karamin cikine da ita wanda likitoti suka tabbatar daya zube, ga rauni kota ina a jikinta, wayar hafsa kawarta ta d'auka ta kira iyayenta, ta fad'a musu duk abinda ke faruwa tun zaman hafsa a gidan, kamar yanda hafsar ta taba fad'a mata. A ranan mutanen borno suka diro Taraba, cikin tsananin bacin rai, direct hospital suka dosa, duk da isan dare sukayi, ganin halinda hafsa take ciki abin yayi matikar musu ciwo sosai, kotu suka maka abie Amma ina abin ya gaggara saboda iko da kudi da abie suka fisu dashi a jalingo, hakan yasa shari'a taki bima hafsa hakkinta, karshe dai mahaifinta yayi rantsuwa hafsa bazata zauna da Abdul ba, saiya sakar masa da yarinyarsa, ba jinkiri agun abie ya saketa, ya basu takarda a hannu, wannan ciwon yasa mahaifin hafsa yace koh bayan ransa baiyarda hafsa ta kuskura ta sake taka gidan shugaba koh da wasa ne babu ita babu sumayya, ta manta ma ta taba haifar y'a, yajama abie kunne mundin ya taka kafa a gidansa koh sumayya , zai nuna masa ikonsu a maiduguri. Wannan shine dalili koh ince musababin rabuwar sumayya da hafsa, su karan kansu yan gidan basuso sakin hafsa ba duk da abubuwan da ta sace musu, Amma bakin Alkalami ya bushe. Bayan tafiyar hafsa sosai sumayya ke kewar mahaifiyarta, kullum haka zatayi ta kuka a kaita wajen ummin ta, duk yanda dada zatayi rarrashe ki take, karshe da abie yagaji bulala yake mata kafun tayi shuru, a haka haka ta fara cire abin a ranta, soyayya sosai ake gwada mata a gidan baga dada ba wanda ita ke kula da ita yanzun, d'akinsu d'aya haka matan gidan na mugun sonta da mazan, wannan karon harda safina amasu nuna mata so, ba kamar daba inta ganta kamar ta cinnnta a wuta, sosai yanzun sumayya ke wa yara lalle na wasa, daman tunda haka ta tashi da abin abien ta na kara mata karfin gwuwa, duk da kananun shekarunta don lokacin tana neman shekara 7. A wannan lokacin ne safina ta sake yad'a manufarta nason auren abie, kamar wanshan karon ma abie yaki amince wa, amma dada ta murza ido tace bata yarda ba aure dole koh yaso koh yaki, haka abie yana ji yana gani aka D'aura masa aure da safina, batare da son ransa ba, sam sam yarinyar batayi masa ba yaji baya kaunar ta. Tirkashi dada batasan wannan aure shine ummul'kaba'isin kome ba..............🍀🍀🍀🍀🍀 Anya gobe akwai update kuwa🤔🤔 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya* *Ibrahim* 🍃 Page7⃣6⃣&7⃣7⃣ Bayan Auren abie da safina, a lokacin safina tafito da duk wani mugun halinta a gidan, ta buwayi kowa, har dada bata ragarwa ba, shikuma abie daman ba sonta yake ba, shiyasa sam koh ana meeting, safina naci musu mutunci baya saka bakinsa a maganar, tunda su suka kakkaba masa ita, badason rasa ba. A lokacin safina tasaka sumayya a gaba da duka zagi, sai da dada ta sanar da abie, ranan da yasan abinda safina ke aikata wa yarinyar sa in baya nan, baraxanan sakin ta yayi ya zazzage ta, kai ranan anyi kwanan bacin rai a gidan. safina ganin auren ta zai iyya mutuwa yasa ta shafawa kanta lafiya, bata koh ga maciji da sumayya, daman ba'a hannunta take ba, a hannun Dada ne. Lokacin da sumayya takai shekara 12, har lokacin safina(momy)bata haihuba, kuma abie bai wani damuba, tunda yana da sumayya, duk wani soyayya da kulawa sumayya na samu a gidan, baga bappanayen taba, ba dada ba ga abien ta, momy ce kawai bata kaunar ta, har lokacin safina na tare da nafisa, duk da nafisar ta koma gidan tsohon mijinta, lokacin. Haka kawai sumayya ta waye gari duk yan gidansu basa kaunar ta, daga su babuji har matan su, dada karan kanta bata shiga tsabgarta sai in babu mutane a wajen, ga tsoron momy da suke, da bin umurnin ta kome tace jiki na bari zasuyi inka cire abie, sosai sumayya ta shiga wani irin mawuyacin hali, abie inta ne kawai ke tsaya mata akan kome, baya taba yarda a cutar da ita, kuma duk wanda yama yarsa abu a ranan zaiga bacin ransa, ana hakan ne fa momy rana tsaka ta dake sumayya, wai ta b'ata mata labulen d'aki da lalle, a ranan abie saki d'aya ya mata ya korata. Amma safina taki tafiya, dada tace sayya maidata d'akin ta, ganin matsaloli da sumayya keta fuskarta a lokacin, ga kananun shekaru, abin harya fara tayar mata da kewar mahaifiyarta, yasa abie saka a FGGC boarding school, ta cigaba da rayuwan ta a hostel, shikad'ai ne gatan ta, sai wata rana Dada tana zuwa mata visiting a boye, kuma tace mata karta fad'awa kowa tazo wajen ta, sumayya koh marmarin komawa gidansu hutu batayi, amma hakan take komawa in anyi hutu tana Allah Allah a dawo hutu. Sumayya lokacin da ta cika budurwa, ta tashi da wani irin hali, akwai jijida kai da ganin tafi kowa, kasancewar ta mai kyau, ga Arzikin gidan su, ga rashin sabo da mutanen gidan, ga rashin mafadi don har lokacin xaman hostel take. Sumayya inta dawo hutu duk yanda saurayi zai biyota, saita raina masa arziki gani take kamar tafi karfin sa, in kuma yakasan ce mai kudi sosai, sai taga kamar zata samu wanda ya fisa, in mai kyaune sai taga kamar nan gaba zata samu wanda ya fisa kyau, sumayya nada kawaye, koh saurayin kawarta ta gani ta ringa dariya kenan, tana kushe sa mummuna talaka kaza kazan, wasu Friends inta da dama in auren su ya tashi basa gayyatanta, saboda rainin wayo da take zuwa ta musu a wajen biki. Lokacin da sumayya tayi candy, taci jamb A lokacin tana da shekara 18, aka shiga university sai abin ya d'ara na da, ganin yanda ake tururin sonta, babu ranan da zata fita ba'a biyo taba, hatta cikin gidan su Abdul(wanda lokacin da sukaje gida, bayan aure aka mata wulakanci, yace zai rage musu hanya ita da khadija)da kaninsa sunsha dambe akanta, Amma haka ta murza ido tace basu mata ba, karshe dai Abdul aure yayi, harda yaransa biyu ya fita harkar sumayya. Sumayya bata gane kuranta ba, sai lokacin da takai shekara 23 lokacin ta kammala digree inta har tayi service, zuwa lokacin duk samarin ta sunja jiki da ita, kowa yana baya baya koh hira suke ta sako musu zancen aure, sai su kama kaucewa wasu kamma gudu suke, rabin kawayen ta duk sunyi aure, sai d'aid'aikune suka rage. Bayan dawowar ta gida lokacin yaran gidansu sun d'ara nada, a yawa wasu sunyi aure wasu na aiki, itama rashin miji yasa abie nema mata aiki a bank nasu dayake aiki , dayake statistic ta karanta, tana aikinta tana samun Albashin ta, Amma maganar samari fa babu yanzun, ita karan kanta aure take so Amma babu mazan, ga kyau ga aiki ga kudi, mijine kawai matsalar ta. Shekara 2 sumayya tana aiki a bank lokacin tana da shekara 25 a duniya, ganin haka yasa dada nema mata maganin farin jini, amma ina tayi tayi abin shuru, karshe dai dada ta nemi kanin abdul ya dawo su daidaita da sumayya, amma ba kunya a idon abie yace shi bazai aure sumayya ba, yarinya yar 15 xai nema ya aura ba rikekkeyaba abinnan yama abie zafi matuka, hakan yasa sa zagin kanin Abdul sosai abin ya zama babban magana. Wannan dalili yasa babuji rantsuwa sai sumayya ta fitoh da mijin aure nan da wata uku, tunda dai zaman ta a gida fad'a zata had'a a tsakanin su, kamar yanda momy ta kitsa musu, don Abie indai akan sumayya ne baya ganin kowa da gashi, jin abinda akace ma sumayya yace sam bai yarda ba, ga yaransu su kubra da miemie sun girmi sumayya ba'a saka musu ka'ida ba sai yarsa. Kuka dada tasa akan abie zai nuna musu iko da sumayya, abinda ya sa abie yarda kenan, sumayya har wata uku ya shige bata samu miji ba, su babuji sukace aikin da take shiya hanata aure, hakan yasa sukasa abie dakatar da aikinta. Sumayya kam ganin an rabata da aikin ta da tafi so, don lagon sumayya kenan, kace zaka kaita garin su mamanta, koh kace makaranta, hakan yasata d'aukar takardun ta, ta tafi asibiti neman aiki babu wanda ya sani. Dayake result nata nada kyau, yasata samun aiki a pharmacy tana musu lissafin kudin magani. Kullum take fita aiki, ba tare da aisan ina take zuwa ba, abie bincike yayi ya gano aiki take zuwa, wannan ne dalilin kwace mata ducument da yan uwan mahaifinta sukayi, sannan suka rabata da aikin ta. Ta dawo zaman gida, daga baya taga bazata iyya ba, tanemi shagon make-up tana zuwa training, daman ta iyya lalle, da sukaga ba sarki sai Allah, yasasu barinta tana zuwa koyon make-up in, basu hanata ba. Sumayya ta cigaba da koyon make-up, har ta iyya aka sallame ta, taso abie ya bude mata nata shagon, Amma yaki karshe dai kawaye da yan gidansu, in sun tashi aure koh yan unguwansu take ma, ana hakan ne lokacin Aikin hajji yayi, kamar koda yaushe daman duka gidan ake tafiya hajji koh wani shekara, amma bana sunce baxasu ba, sumayya da abie suje. Ba musu sumayya suka tafi aikin hajji, wanda zuwa lokacin bazata iyya kirga sau nawa taje ziyaran d'akin kaba ba, bayan sallah abie ya dawo, sumayyya kam daman akwai yar babuji dake aure a saudi, kin dawowa tayi ta zauna agunta har sai da tayi wata 7,lokacin ta cika shekara 26 ta dawo, kamar wasa tana dawowa yan gidan sukace sun mata miji, akwai wanda ya ganta yana so, hankalin sumayya ya tashi a lokacin, amma abie ya kwantar mata da hankali, akan zaiyi bincike akan mijin. Duk yanda abie yaso yan uwansa su sanar dashi waye ne mijin, sunki Amsa d'aya suke basa, shine sun isa da yarsa, haka ba yanda ya iyya dagashi har sumayya suka zubawa sarautan Allah ido, sumayya duk azanta wani shararen mai kudi za'a aura mata, koh d'aya daga cikin samarin gidan. Abu kamar da wasa, ya zama gaske don maganar auren sumayya babu inda baije ba, sai shirye shirye ake duk da ba auren soyayya bane, sumayya ta kwantar da hankalin ta koh banza tasan mijin classic za'a bata koh ajeboter. RANAR D'AURIN AURE Sai da sumayya ta tuno da mahaifiyar ta, haka kawai ranan tunda ta tashi sai kuka take, shi karan kansa abie a zullumin rabuwa da yarsa yake, yasan ba'a kyauta mata ba sam. A waje kofar gidan shugaba, ake shirye shiryen d'aurin aure, sumayya dake d'aki da kawayen ta Ansha kwalliya kamar me, za'a aure classic kanta sai wani kara fashewa yake yanzun kam koh kukan ta daina, ji kawai sukayi Ana Alhamdulilahi An d'aura auren sumayya Abdulsalam shugaba, tare da Angon ta Muhammad Al'ameen yusuf, akan sadaki naira dubu 20, da mamaki sumayya tace "dubu ishirin kuma?wani irin mijine haka dubu ishiri ai mu tunda muke aure a gidan nan ba'a taba biyan sadaki haka ba" Kawarta ce ta kalleta, kai sumayya sadaki fa Albarkansa ake nema, ba yawa ba kika sani koh mijin Alu-sunnah ne, irin samarin nan ne ustaxai, ga gemu ga d'angalalen wando kinsan fa irin su sunfi dadi love. Gabaki d'aya kawayen dake d'akin dariya suka saka da shewa, don harga Allah sun d'auka mai zafi sumayya zata aura, sanin da suka ma halinta na rainako, ke ina ga fa irin samarin nan ne yan 20 something zuwa 30. "Allah ya sauka bakin ki ya sare guntun kashi, habba 30 ai nima na fara jin kamshin, 30 ina laifin 35 irin ya bani shekara 9 nan" sumayya ta bata amsa Duka suka kwashe da dariya, ana ta nishadi, kamar daga sama suka fara jin hayani yana tashi a babban falon gidan, muryar abie ne yake cewa bai yarda da auren nan ba, bazai yafe ba arasa wa za'a aurawa yarsa sai miskini, saboda babuji yaga ba yar gaddafi bane koh Abubakar shiyasa har ya iyya had'ata da yaron nan, yau sai an raba auren bai yarda ba, jin haka yasa sumayya da kawayen ta rugawa da gudu suka shigo falon don jin ba'asi. MAKAHO ne ya ganta yana so, ba sai a basa ba tunda ba manemi bane da ita, babuji yace. Kafun abie yayi magana sukaji timmmm sumayya ta yanke jiki ta fad'i jin wai MAKAHO aka aura mata ita sumayya. *********** Bayan sumayya ta farfado duk borinta da masifar abie, dada tace a yau innan sai ankai sumayya gidan mijin ta, koh ta d'aga masa nono, ba yanda abie ya iyya yana ji yana gani aka sabi yarsa a mota, tare da babban mota na kayan d'akin ta, dana gara wanda kome set uku aka mata gado uku kujeru uku firij uku kome uku uku aka mata hada kayan kitchen, kawayen ta fa sun samu abin yi, sai dariya suke suna yad'a mata bakar magana, especially wa'inda sukayi aure, sumayya a ranan tayi kuka har saida tayi Addu'a Allah ya d'auki ranta,saida wata yar uwar su na gembu ta mata wa'azi kar bacin rai yasa tayi sabo. Ai bata tashi ganin bacin rai ba, saida motar su tayi fakin a kofar gidan Adara, wani gidane irin na talakawa mai jan kasa sai kofar gidan da babu kofa, lulubi aka mata suka shiga gidan, amma kamar ba gidan da za'a kawowa amarya ba, babu wanda ya tarbesu asalima kowa harkar gabansa yake kamar ba'aga zuwansu ba, tambayar kofar amarya sukayi aka nuna musu, wani samurmurin d'aki koh kewaye sa ba'ayi ba, d'akine d'aya kankani wani rubebe dashi, ihu sumayya tasa ta tsunguna agun tana sakin kuka itakam tata ta sameta. Ga auren MAKAHO ga talauci dame zataji, Allah ya isa ta farama su babuji, tana sun cuceta, a hakan dai aka wuce d'akin, yar uwar dada ce ta tura rubebben kofar da koh sakata bazai zauna ba tsaban rubewarsa, suna bude dakin ba laifi a wanke yake sai dai babu kome sai cinyayen taburma da ghana must go na kaya kad'ai a d'akin, su karan kansu masu jeren ma sun rasa ta ina zasu fara, wanda aka kawowa set uku shine aka samu d'aki d'aya karami. Da gudu sumayya ta b'anbara ta bar gidan, kawai su dada na zaune sukaga amarya ta faso da gudu ta dawo gida"wallahi bazan xauna agidan shan ba"wannan shine abinda sumayya tace, kuma ba wanda yayi maagana. Wannan hajiya yar uwar dada ita tayi waya aka kira mata kafinta, a take yaxo shida abokan aikinsa uku,suka buga musu kofar daki, a ka cire tsohon dayake yammane, wasu daga cikin yan uwan, kwana sukayi washe gari kafintoti suka gama aikinsu, sun kewaye kofar da falange an mata band''aki a kofarta, an saka silif da kitchen da baranda, Amma fa kaya bai d'auka ba koh set d'aya basu samu shigaba, haka aka juya da sauran kayan. Abie da kansa a ranan da , dadare ya dawo da sumayya bisa umurnin dada,haka aka watse aka bar sumayya da halinta, wasu sun mata wa'azi wasu kam magana suka gaggaya mata. Sumayya tunda suka watse aka barta kuka take, gashi dare ne tana zaune akan gadon tana kuka cikin bakin cikin wannan al'amari, sai a ranan wani irin kewar mahaifiyarta ya kamata da ace mamarta na tare da ita da abubuwa zasu mata sauki. Duke take tana kuka baji ba gani wai itace da aure a irin wannan gida................. Tas sumayya ta sanar da Ammar duk irin wahalar da tasha, da burinda taci na ganin tayi wa muhammad wulakanci, harsai yaji a jikinsa kafun tanemi sakin ta, amma saboda kyawawan halinsa da hakurinsa don babu abinda sumayya bata masa ba, amma bai taba nunawa koh a fuska ba, bai taba riketa , da wani manufa a ransa ba, kullum kokarin faranta mata yake, wannan sune makamin da yayi tasiri wajen mallakar zuciyar sumayya, taji zata rayu dashi a haka, sannan ta d'auki auren su da Al'ameeen isharane Allah ya nuna mata, akan halinta, kuma ta karbe kaddarar ta, tazauna da mijinta.... cigaban labari......... "Sannan yau suce wai na rabu dashi akan me"? D'aga ido Ammar yayi ya kalli sumayya da khadija dake kuka, lokaci guda, sumayya!!ya kira sunan ta. "Na'am" Kukan ya isa haka abinda nakeso dake shine ki d'auki duk abinda ya faru a matsayin jarabawa, kamar yanda kikace, naji duk abinda iyayen ki suka miki, Amma ke me kika fahimta akan auren ku da muhammad, da gaske bashi yace yana sonki ba? Gyara xama sumayya tayi ta zayyana masa labarin muhammad, da irin wahalhalun da yasha. Tabbas Ammar ya tausayawa rayuwar su muhammad, kuma a cikin labarin sa da sumayya ya auna wasu abubuwa da dama akai, sai kuma abu na biyu, sumayya kina nufin mamar ki sunan ta hafsa sannan yar maiduguri ce? "Eh Amma bansan a ina take a maidugurin ba" Amma naji mahaifin ki yace zai kaiki wannan karon. "Ni yanzun bata maiduguri nake ba, ta mijina nake" Sumayya kiyi hakuri ki koma gidan naku, tunda naga iyayenki zama a gidan Adara ne basaso kiyi, in Allah yasa Al'ameen ya dawo, kinga shikenan sai ki dawo d'akinki, in ma basason zaman gidan ne, nizan nema muku wani gidan saiku koma, amma a halinda kike cikin nan ya kamata ki kula da kanki, juna biyu ne dake ga dp ki na hawa, koh kinaso ki rasa babyn nakune? "Ah ah yaya Ammar"sumayya ta amsa masa. Yauwa koh kefa kiyi hakuri ki koma gidan kinji?insha Allah auren ki da muhammad bazai mutu ba. Kuka sukaji da karfi a gefen su, khadija ce ke kuka. Kee lafiya menene haka? Kallonsa khadija tayi da haushi jin tambayar da ya mata, toh ba kai bane kake cewa Aunty ta tafi, toh ni kuma in zauna dawa? Da goggo mana zaki zauna, ba za'a bude makaranta gobe monday ba?saiki cigaba da zuwa kafun yayan ki ya dawo. Kuka khadija ta sake, shikenan aunty yanzun tafiya zakiyi ki barni. Toh koh zaki bita ne gidan nasu?koh taki bin umurnin iyayen ta akanki?khadija iyaye fa ba wasa bane?ammar yace cikin haushi Shuru ta masa, sai ga likita yazo ya basu sallama, don sumayyar ba wani jin jiki tayi ba, ruwan da aka saka mata ya kare. Suna Fitowa taga Ahlin gidansu tim a cike a haraban asibitin, kala batace musu ba Tana bin Ammar a baya, ga khadija a gefe. Tashi sukayi suka bisu a baya har packing space, sumayya motar Ammar tayi niyar shiga Amma dada tayi tsalle ta dire akan ba inda sumayya zata shiga, sai motar gidansu. "Kinsan Allah dada in kika matsamin saina fasa bin naku naga ta tsiya" sumayya tace. Yi hakuri kawalli jeki shiga na Abokin mijin naki. Shiga motar sumayya tayi ta kalli khadija dake tafiya a hankali kamar kwai ya fashe mata a ciki, daga ka ganta kasan tana cikin matsanan cin damuwa, "ya Ammar ka fad'a musu bazan koma yau ba sai gobe, sutura driver yazo ya d'auke ni inna shirya kayana" ba musu Ammar ya fita a motar daidai lokacin khadija ke kokarin shiga, yaje ya sanar dasu basu wani d'aga hankalisu ba sukace goben insha Allah abie da kansa zaizo d'aukar ta, in kayan sawane ma?ta bari kawai za'a saya mata sabbi. Amma sumayya tace ita sai ta kwana washe gari zata koma gidan su. Bayan isar su sumayya gida, Ammar tafiya yayi, khadija ta kalli Auntin ta, yanzun Aunty da gaske zaki tafi ki barni?shikenan ni babu yaya babu ke banida kowa yanzun sai goggo? "Khadija baxan barki ba koh babu yayan ki Zan kula dake, guduwa zamuyi daga jalingo, gobe goben nan da asuba zamu bar gari..............🍀🍀🍀 ✨Ruqeenjalal✨ 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya* *Ibrahim* 🍃 Page7⃣8⃣&7⃣9⃣ "Zamu bar garin" A matukar Mamaki khadija tace, barin gari kuma Aunty? "Eh khadija barin garin zamuyi don wallahi baxan iyya xama a gidan muba, yanzun kwata-kwata naji bana kaunar gidan, da zama a cikinsa, kinga yanzun ma tashi ki tafi wajen shagari kice masa karya rufe shago, bayan isha'i muna zuwa akwai maganar da zanyi dashi, kibi gidan goggo ki d'auko abubuwan ki masu Amfani harda takardun ki, kiyi sauri kizo mu shirga kaya" Aunty ban gane ba?wani irin abune haka ni gaskiya nama hakuri, ki koma gidan naku Allah ya dawo da yaya lafiya, yanzun in muka tafi yaya ya dawo bamu nan ba? Cikin jin haushi sumayya tace"sai dai ke ki zauna, koh zaki bini koh bazaki bini ba zaman garin nan bazan yisa ba kinji na fad'a miki" Shuru khadija tayi tana nazarin sumayya koh dai bata da lafiya ne? ace mutum lokaci d'aya ya birkice haka, Amma dai batayi magana ba tasa hijab nata zata fita. "Khadija" Na'am aunty. "Ban saki ki sanar da kowa maganar nan ba, koh goggo ban yarda ta sani ba, inta tambaye ki me zakiyi da abinda kika d'auko kice mata nina ce ki d'auko kayayakin ki, na nan yayi datti" Toh aunty kawai khadija tace ta fita. Bayan fitar khadija, akwatuna sumayya ta saukar, tana shirga kayan ta kama daga na sawa harna amfani, daman har yanzun akwai wa'inda bata dinka ba, hotonan su data lika a bango duk ta cire ta saka a akwati,da system inta, sauran kaya daya rage ta barsu a wardrop, kayan muhammad ne kawai bata taba ba, kome nata ta d'an tattara harda make-up ket nata, saida ta cika akwatuna hudu da kit da kaya, ta barwa khadija akwati d'aya tasa kayanta a ciki. Khadija na dawowa ta sata had'a kayanta a akwati d'aya, da dare ita da khadija suka shiga keke-napep da akwatunan kaya, ba tare da y'an unguwan su luraba shagon shagari ta kai ta ajeye, shikaran kansa yayi mamakin kuma ya tambaye ba'asi, amma sumayya tace ya bari gobe zata masa bayani yanzun dai karya sanar da kowa, gobe da asuba ya bude shago tana zuwa. Ba musu ya aje mata kayan, bayan sun koma gida waya sumayya ta d'auka ta kira principal nasu khadija, ta masa bayanin tafiyan gaggawa ya same su, suna bukatan transfer letter na khadija, ba musu yace gobe da safe tazo school ta karba. Karfe uku na asuba sumayya ta tashi, tafasa ruwan zafi tayi, tayi wanka tasa khadija wankan asuba suka shirya cikin hijabai manya da socks, saboda yanayin garin, zanin gadonta guda uku dake d'akin ta dauko ta lulube gado ta da d'aya, d'ayan kuma kujera ta lulubawa, d'ayan kuma wardrop, zaninta babba ta lulube TV dashi. Dayake sunyi Alwala sallah kawai sukayi taja kofar d'akin ta rufe da kwado, key ta aje a inda Al'ameen yake ajewa in basanan, fita sukayi ita da khadija kam sai binta take, ba halin magana babu kome a hannun sumayya sai purse nata, wanda waya da ATM ke ciki sai y'an changen da baza'a rasa ba, shagon shagari suka wuce kamar yanda sukayi Alkawari, haka take don shagari ya bude musu shagon, tattara akwatunan sumayya take don burinta kar gari ya waye tana sintali bata fita ba. Aunty sumayya wai don Allah meke faruwa ne? "Shagari zamu bar gari ne da khadija" Barin gari kuma Aunty, wani abin aka miki? "Ba kome shagari gida akeson na koma ni kuma yanzun bana kaunar komawa gida" Toh yanzun wani gari zaku tafi, gashi jiya na saro kaya, kwata-kwata dubu 100k ne a hannu na bara na d'auko muku? "Tsaya shagari daman Wannan kudi bana muhammad bane na Ammar ne, don haka kaci gaba da kasuwancin ka kamar da, duk ranan da Ammar ya nemi kudinsa saika basa, uwar kudin kuma saika kama kasuwa dashi nasan zuwa yanzun ka kusa ninka kudin biyu, abinda nake so dakai shine in muka tafi kayi Register n jamb in lokaci yayi, ka koma makaranta, har ka kammala da kudin da kake nema, tunda mai shagon baya nan babu Amfanin kana ta tara Arziki bakaci,kayi Amfani dashi Allah yasama kasuwar Albarka. Ameen Aunty nagode Allah ya bayyana oga, amma don Allah ki karbi kudin aunty sumayya karki ce ah ah. Ganin ya nace yasa sumayya karban 50k tabar masa sauran don yaro tausayi yake bata. in babu damuwa ki bani number ki duk lokacin da akaji labarin oga saina kiraki, yace yana kallon khadija dake rabe a gefe tana hawaye haka kawai yau take jin wani irin kewar sintali, yanzun tafiya zatayi tabar sintali harda garin gabaki d'aya. "Gashi " sumayya ta mika masa wayar sa daya bata tasa masa layin ta,shiya tare musu keke-napep da asuban nan ya loda musu kayansu, akwati shida rus a ciki mai keke yaja machine insa, a hankali khadija ta leko kanta tana d'agawa shagari hannu wanda hawaye ya cika masa ido, don shi harga Allah son khadija yake kawai kunyar fad'a mata yakeji ganin kankantar shekarun sa, dayasan irin wannan rana zaizo dako ba kome tasan da sonta a ransa, koh ina taje tasan tana ransa. Bayan su sumayya sun tafi road block da asuban nan, tama rasa wani gari zatace zata kuma gashi tana son barin khadija taje ta karbo mata transfer letter nata, na makaranta maganar karatunta karya koma baya, aje khadija tayi a gefen tashar ta kama hanyar science, ba ita ta samu ganin principal ba sai kusan 7:30, ya kaita wajen exam officer daker dai ta samu transfer letter in, tasha ta koma amma zuwa lokacin duk mototi sun tashi sai kalilan suka rage, wajen da khadija take ta nufa, har lokacin tana zaune da tulin akwatunan su a gaba, abin duniya ya dame ta. "Kee khadija tashi ga mota shan naga ya kusa cika muje muji na wani garine" Mikewa khadija tayi, aunty kin samu lettern ne? "Eh na samu khadija daker baki ga har gari ya waye mini ba"? Gaskiya ne muje toh aunty . Wajen motar suka nufa suka tambaye ta wace gari ne, akace musu motar Abuja ne saura mutum uku, babu wani shamaki sumayya suka shiga, dayake motar babban mota ne ba karami ba, akwai space, Alelen akwa sumayya ta sai musu na 200, da gyada na 100, ta had'a musu da goran faro biyu, sai masa na 150, suka shiga dashi motar, suna shiga koh, aka samu mutum d'aya ya shigo aka tada mota, lumshe ido khadija tayi hankalin ta a tashe yau za'a bar gari. Sumayya kam koh a jikinta, sai cin Alelen ta take tana had'awa da ruwa, koh a jikinta bata san inda zasu ba, bata da wanda ta sani a Abuja Amma koh a kwalar riganta. Haka khadija da sumayya suka wuni a mota, don an sauke su sun sake shiga wani, khadija ta kasa cin kome, amma banda sumayya kome ta gani in an saya a hanya, saya take taci abinta, har mangari ba suka isa Abuja aka sauke su a tasha saboda yanayin tafiyar su . Sumayya gabaki d'aya tayi laushi likis don ita ma ba wani tafiye tafiye take a mota ba, sai yanzun takejin gajiya ga karamin ciki, tama rasa ina zasu nufa gabaki d'aya gashi mangariba yayi, a gefen tasha ta samu suka zauna ga kayansu a gabansu tirim, gabaki d'aya ta galabaita a zaune suke har isha'i suna tasha, a zaune tama rasa wazata tambaya inda zasu samu wajen kwana, banda hotel. Kamar daga sama taga wata ta dafa mata kafad'a da sauri da d'ago"laaa laila kece"?sumayya tace cikin mamaki. Oh duniya nifa tun mangari ba danazo tashan nan, nake ta kallon kamar kece kamar bake ba, sumayya naga kinyi jiki gaki a tasha nasan kuma kinfi karfin tasha, wallahi har zan tafi daga baya kawai na fasa nace bara dai na sake tabbatar wa bake bace. "Wallahi nice laila" Amma sumayya meya ajeki har war haka a tashan nan, gaku mata kuma ba sana'a ne ya kawo kuba? "Wallahi laila bana da inda zan sauka zaman da nayi nan, ina tunanin ina zani kowa na tambaya sai yace wai sai dai hotel" Toh yanzun dai dare ne ki tashi muje mijina baya gari saiku kwana washe gari zamu tattauna ki dubi gabaki d'aya kin jirkita. Mikewa sumayya tayi a hankali laila da khadija ne suka tattara kayan zuwa cikin mota. Suna isa wani gidane d'an madaidaici mai kyau sosai irin gidajen hayan nanne na zamani, ba ruwan wani da wani, kowa sa sassan sa amma dai gidan ya had'u, sashen laila suka shiga, yana d'auke da two bedroom da falo da toilet a ciki sai daining Area, ga tiles kota ina, irin dai gidajen hayan Abuja nan, gashi a unguwa mai kyaune akwai gidajen manya a unguwan sosai. Bayan sun shiga kofar laila d'aya d'akin laila ta sauke sumayya, wanka sumayya tayi da khadija, laila ta kawo musu abinci sukaci, kwanciya sumayya da khadija sukayi a kan katifar dake cikin dakin, kayayyakin su a gefe, a haka bacci ya d'auke su tsabar gajiya. ************ Ta bangaren mutanen jalingo... Tun da safe Ammar ya shirya yazo gidan su sumayya, lokacin karfe 9 na safe, yana isa kofar Adara ya tura yaro ya kira masa sumayya, amma yaro ya dawo yace masa sumayya bata nan kofarta a rufe. A zaton Ammar koh su abie da sassafe suka zo suka tafi da sumayya, hakan yasa-sa wucewa gidan goggo ya aika yaro ya kira masa khadija, ba'a jima ba saiga goggo da yaron sunfitoh tare. Bayan sun gaisa goggo ke sanar dashi ai khadija na gidan sumayya agun ta koma da zama, da mamaki ammar yace ai gidan yaje ya tura yaro, yaro yace basanan. Da mamaki goggo ke kara maimaita basanan kuma?kamar ya don ita dai batasan wainar da aka toya ba jiya. Kadai san halin yara wani sa'in suna da iyya shege taima ma basu je kofar sumayyar ba suka dawo sukace maka bata nan, inba haka ba ina sumayya zata da safen nan? Ammar baiyi magana ba ya juya ya koma kofar gidan Adara, wannan karo da kansa ya shiga har kofar sumayya, turus yayi ganin kwado a makale a kofar abin Al'ajabi toh koh yan gidan nasu sun d'auke tane? gashi yan gidan Adara ba mutunci bane dasu bare ya Tambaye su. Fita yayi kofar gidan ya tsaya yama rasa me zaiyi don shi gabaki d'aya tunanin sa ya basa khadija tabi sumayya gidansu kenan, kuma me yasa basu ma goggo sallama ba,motar sa yake kokarin shiga saiga mototin su abie, dakata wa yayi yajira sukayi packing yana mamakin ganinsu. Matsawa yayi garesu suka gaisa, Anan nefa yakejin wai sunzo d'aukar sumayya, da mamaki yake sanar dasu ai sumayya bata nan kofar ta a rufe tun 9 yazo mata sallama amma bai ganta ba. Ai abie baisan lokacin da ya zauna a dakalin kofar gidan adara ba, ya dafe kansa shikam ya shiga uku, Anya sumayyar sa daya sani ne mai tsananin sonsa da masa biyayya Amma yau ya zana mata layi ta ketare, sai yanzun yake nadamar auren ta a gidan Adara, don shi duk ya ta'alaka rashin jin sumayya, da auren tan nan da suka mata, tunda har tasan tasa kafa ta gudu, don dada da kanta taje kofar sumayya ta sake lekawa taga a rufe, ga shagari dayazo wucewa ma ya musu bayanin tun asuba sumayya suka bar gari, waya Ammar ya fitar yayi ta kiran sumayya amma bata d'agawa, Abie ma yayita kira Amma ba'a picking karshe dai dukansu suka d'unguma har tasha, Amma koh maikama da su basu gani ba, kowa suka ma kwatance sai yace bai gansu ba. Haka abie suka dawo da sanyi jiki gabaki d'aya hankalin sa a tashe, yar yarinyar sa guda d'aya dayake da ita, tasa kafa ta shiga duniya ita da ba sanin kowa tayi ba ina ta shiga, Ammar karan kansa tafiyar sumayya ya d'aga masa hankali, wani irin abune haka sumayya ta aikata yanzun barin gari da tayi menene Amfanin sa, yau in muhammad ya dawo fa, me zaifad'a masa don Allah, gashi wani Al'amari mai girma dake zuciyar sa yana shirin fiddawa sumayya tasa kafa suka gudu da khadija shidai ya bonu. *********** Washe gari bayan sumayya sun tashi da asuba sunyi sallah wayar ta ta d'auko wanda tasa a silent ta bude ganin miss call na yan gidan su, da sabon number har da messenge yasa ta bude wayar ta zaro sim in dake ciki ta bude Aljuhun akwatinta ta saka sim in a ciki, sannan tama khadija gargadin karta fad'awa kowa gaskiyar abinda ya kawo su Abuja, koda kuwa laila ce ta bari da kanta zata mata bayani. Khadija ce tama laila shara da moping in tiles, sumayya kam bacci ta koma don har yanzun akwai gajiya a jikinta, sai kusan 10:00 suka karya su uku saboda yaran laila biyu ne kuma duk sun tafi makaranta abinsu. Laila ce ta kalli sumayya,sumayya gaskiya nayi mamakin ganin ki a tasha jiya, garin yaya zakizo gari bakisan kowa ba?gari ma irin Abuja sumayya wallahi jiya ban d'auka ke bace don rabon mu dake tunda muka gama school, ban sake saki a ido ba,dayake a lokacin bata mu ake ba manyan yara. Dariya kawai sumayya tayi tana kallon laila, Allah sarki rayuwa da laila ba karamin sonta take da kawance ba, amma kullun sai tayita wulakanta ta , gashi yau itace ta mata rana gaskiya ne da akace A rayuwa koh wani mutum yana da ranan sa"wallahi laila tafiyar gaggawa ce, bamma sa tsamanin Abuja zanyi ba" Bangane ba sumayya?gaki na ganki da ciki don nasan wannan jikin naki da biyu ne. "Hhhh kai laila ba halin nayi jiki kenan"?tayi maganar tana kallon khadija data mike ta koma d'akin da suka sauka, jin hiran nasu na manya ne. Ah ah sumayya wannan jikin yafi karfin jikin jin dadi, kinga yanda kirjinki ya ciko ga hips yafi kome cika kamar me, ga jikin ki ma yayi d'anye. "Ke abar zancen nan ni duk ba wannan ba, a ina xan samu gidan haya kamar nakun nan, na kama"? Ah ah sumayya baki bani Amsa ta ba tukunna?cikine dake koh ba ciki ba? " cikine laila" Ok Aure kikayi ne, kuma meya kawoki Abuja da yarinyar shan? "Aure nayi laila, dalilin zuwa na kuma mijina akayi kidnap insa shiyasa nima na gudo daga Taraba na dawo nan" Baki da gidan iyaye ne? naga dai ke yar masu haline baza'a rasa tsaro a gidan kuba ai? "Kinga laila rabu dani bana sha'awar komawa gidan mu kwata kwata wallahi, kawai in zaki nema mini mafita ki nema min tunda kikace mijinki yau zai dawo kinga bai dace mu zauna miki a gida ba" Kwantar da hankalin ki sumayya, in gidane zaki samu don wannan gidan ma za'a samu waje, Amma sumayya kinsan rayuwar Abuja ba d'aya bane da Taraba koh? gidan nan da nake ciki dubu dari biyar ne a shekara , haka mijina ke biya. "Karki damu indai kudin hayan ne zan biya laila ba damuwa, har school nake son ki taimaka naje na saka khadija" Sumayya kamar nawa kika shigo dashi abuja ne wai? "Million d'aya da dubu d'ari hudu" Hhh lallai sumayya don kunzo da wa'innan kudi kike tunanin zama a Abuja, nifa bawai na yarda dake da abinda kikace bane, na sanki sarai da zurfin ciki, Amma fa ki sani wallahi wa'innan kud'aden da kikazo dasu wallahi bazasu miki kome ba, saidai in kin shigo da result naki nasa mijina ya nema miki aiki koda a office insu ne? "Laila banzo da kome daya shafe karatuna ba, sannan ni ina da sana'a wanda nake saka tsammanin zan iyya neman na kaina da shi, kuma yarinyar nan kanwar mijina ce, marayu ne su biyu Iyayen su suka haifa,mijina bayanan shiyasa narike ta a hannu na, kuma karatun ta nada muhimmanci aguna" Toh wani sana'a kenan kike bayan Lalle sumayya? Ita khadijar bata da dangi ne? "Harda make-up kuma khadija ta iyya kitso inso samune shago nake so na kama sai mu fara muga yanda Allah zaiyi damu" Anya kuwa sumayya gaki da ciki in kika haihu d'awainiyar abinda kika haifa zai dawo kanki, ga khadija ga kudin haya ga kayan da zaki sawa d'akin da zaku kama, ga kudin makarantar ta anya abinnan zai hadu kuwa? "Insha Allah laila Allah zai dafa mana, yanzun dai so nake kimin hanyar da zansamu dakin gidan nan da kikace ya saura, don so nake kafun mijin naki ya dawo mun bar muku kofa, tunda kikace jiya ma kinje d'aukosa a tasha kika samu bai iso ba, motar su ta samu matsala" Ba kome tashi toh muje gidan, mai gidan yana tsallaken titi bara na kira mijina na fad'a masa. Ok sumayya tace suka wuce gidan mai gidan hayan, bayan laila ta nemi izinin mijinta a waya. Bayan sunje a take sumayya ta wuce bank dayake babu halin transfer, tunda ba sim a wayar ta, kudin hayan suka kawo wa mai gidan,bayan sun dawo kudi sumayya ta baiwa khadija da laila suka tafi kasuwa, ita kuma bude d'akin da suka kama tayi, sashen mai kyau two bedroom da falo ga daining area ga toilet a cikin koh wani daki, ga kitchen a ciki daki dai mai kyau dashi yasha tiles kamar d'akin laila, kome a ciki. Bayan su khadija sun dawo katifa suka sayo babba, da zanin gado sai hot plate mai kai biyu, da sandan moping sai bokati biyu, soson wanka dadai d'an abubuwan Amfani daidai talaka, bujuwan su biyu, khadijar ce ta ibi ruwa a panpon gidan ta wanke musu d'akunan tayi moping, yana bushewa suka shimfid'a katifar a falon, suka kai sauran kayan da suka saya kitchen, suka shigar da akwatuna su cikin d'ayan d'akin, suka kwanta a katifar su ita da khadija a falo sosai gidan ya musu d'adi ganin kowa na d'akinsa babu tsegumi kamar gidajen hayan da suka sani. *********** Ta bangaren Al'ameeen, suna zaune a gindin bishiyar ga gajiya ga yunwa, Gidado dake gefene ya fashe da kukan bakin ciki, Al'ameen da yaron fulanin nan sukayi wajen sa da sauri, duk da raunukar dake jikinsu, don gabaki d'aya kafafunsu kayoyi sun bula gashi hannun muhammad sai yanzu yake jin tsamin sa ga giransa dake ciwo, Gidado lafiya kuwa ?sukace har suna had'a baki. Kuka gidado ya sake da karfi, sai kuma ya bude baki Amma ya kasa magana, da hannu kawai ya nuna musu gefen jikin bishiyar da yake. A matukar kidime muhammad yace, innalilahi wa'inna'ilahi raji'un sarin ka yayine gid'ado............ 🍀 ✨Ruqeenjalal✨ [10/24, 2:18 PM] +234 903 356 9641: 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya* *Ibrahim* 🍃 Page 8⃣0⃣&8⃣1⃣ Maciji ne babba duk da darene amma macijin fatarsa na sheki, Girgiza kai gidado yayi Alamu dai ba sarinsa yayi ba, da gudu Muhammad ya jawo wani katon reshen itace babba, ya bugawa macijin da karfi akai, ya sake buga masa take kan macijin ya wargaje, mikewa muhammad yayi ya taimaka wa gidado suka mike, ganin maciji a wajen yasa su cigaba da tafiya duk da dare ne, saida suka isa wani wajen yashi kafun suka yad'a zango, agun suka kwanta. Basu suka farka ba sai washe gari, harma gari ya waye kafun suka farka, taimama sukayi, sukayi sallah zuwa lokacin hannun Muhammad yayi mugun kumbura sosai, badaru ne ya tsinko wani ganye ya mursuke yasaka masa a ciwon, mangoro suka tsinko mai yawa suka sha ga ruwan korama suka iba, sukaci gaba da tafiya. A haka su Al'ameen sukayi ta tafiya kusan sati biyu, suna fasa hanya saidai su shiga wannan dajin su fita suyi wannan, gabaki d'aya wahala ya canja su, hannun Muhammad yayi dan sauki, kafafunsu tun yana musu rad'adi har suka saba, ga giransa daya tsage, da ace a garine dinki za'a masa, Amma haka sukaci gaba da tafi giran na warke wa, amma fa fatar bai hade ba sai yayi kamar tsagun wuka wajen yayi, sai yayi matikar karawa fuskar tasa kyau. Saida su Al'ameen sukayi kusan wata biyu, suna tafiya a kafa bayan zama da sukad'anyi a wasu kauyuka, yaukam tsintar kansu sukayi a sahara mai zafin gaske, Allah yasa ma sunyi guzuri saboda kauyen da suka baro sun sanar dasu gabansu sahara ne, suna tsallake sa nijar zasu shiga. ********* Ta bangaren sumayya basu farka ba sai mangariba, Bathroom suka shiga sukayi Alwala, bayan sunyi sallah sumayya ta kalli khadija"ki shiga kitchen a cikin cefenen da kukayin nan ki d'auka ki dafa mana koh abu mara nauyi ne" Toh Aunty khadija tace ta wuce wa kitchen in, dayake duk a falo yake basai ta fita waje ba flat ne babba, khadija na shiga kitchen saiga yar laila mai shekara biyar ta shigo d'akin da sallama Amsa mata sumayya tayi ta karbi kulan da ke hannunta, ina kwana aunty, ta gaida sumayya. Murmushi sumayya tayi tace"Ina wuni dai baby" Ina wuni? "Lafiya munira, Dady ya dawa koh? Eh ya dawo gashi momy ta bani na kawo miki, tace tana mikawa sumayya kulan " wai gaskiya mungode wa momy kinji kice nama dady sannu da zuwa. Toh yarinyar tace tana fita a falon, kwalama khadija kira sumayya tayi, bayan ta fitoh ne sumayya kece mata, Laila ta kawo musu abinci tabar girkin, ta d'auko musu pure water biyu dake kitchen in, A plate d'aya sumayya ta zuba musu abincin, tuwo ne miyar shuwaka da kifi busheshe, sosai sukaci tuwon suka sha ruwa tashi khadija tayi tarufe musu kofar falon, tabar kee a jikin kofar wanka sukayi dayake Abuja akwai nepa yasa ta kunna AC dake makale a falo, don sunyi sa'a akwai Ac a falo, shiyasa sumayya tace susa katifa a falon in, kwanciya sukayi akatifarsu. Washe gari tie da kwai suka karya dashi khadija ta wanke musu d'an plate insu da kwanon laila,khadija ce ta maida mata kwanukan da safe, sumayya had'a laila tayi da khadija da zata fita aiki akan suje ta kai khadija makarantar da yaranta ke zuwa, tunda transfer ne ba sabon register zatayi ba. Khadija ta samu gurbin karatu a school in, sai dai fa kudin makaranta 50k ne duk team nan ma wai makaranta daidai gwargwado kenan,sai kudin school bus, a ranan suka bawa khadija uniform nata Daman tazo da kome na makarantan ta harda note book, shiyasa washe gari da safe tana karyawa ta sanya uniform nata, siket ne da riga sai necktie da baby hijab, bayan khadija ta tafi makaranta dayake school bus na jiranta a bakin titi, Karyawa sumayya tayi ta koma ta kwanta tama rasa me zata kama, ta gaji da zama waje d'aya tashi tayi ta shirya ta fita, da kwatance taje clinic don yanzun cikin na neman 4 months shiyasa takeson fara zuwa awo abinka da yar boko dakanta, ta gane asibitin, ta bude file a wajen sannan zatana zuwa clinic harta haihu, daga asibiti kasuwa ta wuce tad'an saisai musu kayan masarufi. Bayan ta dawo wanka tayi ta dafa musu abinci sai yamma khadija ta dawo, uniform nata ta wanke ta had'a da kayanda Auntin ta ta saka jiya, tayi moping tayi musu girkin dare, yayin da sumayya ke kwance akan katifa tana kallo a system nata. Bayan mangari ba saiga laila ta shigo lokacin sumayya da khadija nacin abinci a kasan tiles, sumayya na zaune akan filo saboda yanayin ta da ba'aso ta dabasu a kasa. Ah ah hajiya sumy haka ake makwantakan koh nokin babu. "Kai laila kin cika iyayi maigida ya dawo basai mu baku waje ku sarara ba, tukunna" Karasowa falon laila tayi, lallai ma sumayya wani irin bamu waje, kaman sabbin aure Ina kwana Maman munira? Lafiya khadija ya school in? Lafiya klau, tace tana iban abinci a wani plate ta wuce daki. "Kai laila ga abinci bismillah" Zama tayi a bakin katifar, sumayya nayi magana da baban munira yace min za'a samu shago, amma nidai gaskiya sumayya hankalina bai kama ki bude shago yanzun ba, duba da halinda kike ciki ba [10/24, 2:18 PM] +234 903 356 9641: 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya* *Ibrahim* 🍃 Page8⃣2⃣&8⃣3⃣ Mikewa Sukayi da sauri suka nufi kofar gidan, ba tare da wani tsoro ba suka zare sakatar, me zasu gani?bawan Allah nan ne aka d'ago rababe-rababe kamar kayan wanki, cikin hanzari suka bawa mutane biyu da suka d'agosa hanya suka shigo dashi cikin gidan, direct d'aki suka nufa dashi suka kwantar. Al'ameen dake binsu a bayane ya tambaye su meya faru dashi? Wani a cikin sune yake tsanar dashi wai ashe faduwa mutumin yayi a gidan da yake aiki, kafarsa ya karye shine aka kaisa asibiti aka d'aure kafar, amma yaki zaman asibiti wai sai dai a dawo dashi gida yayi jinya. Allah ya kiyaye na gaba Su Al'ameen sukace suna komawa d'akin mutumin. Kallon kafar da aka d'aure muhammad yayi, Sannu baba Allah ya kiyaye na gaba? Amsa masa yayi da, Ameen Al'ameen. Sannu baba, gidado da badaru sukace a tare, Amsa musu yayi a hankali, tashi Al'ameen yayi ya fita a d'akin, murhun inda ya gani na karfe d'an karami ga gaushi a ciki, nitsuwa yayi ya hura wutan ya d'aura butan shayi, atakaice dai shayi ya had'a a cikin butan ya had'a da kofi ya kaima mutumin, ba musu mutumin yasha kad'an, Al'ameen ya sake fita ya d'aura ruwan zafi, yana dumi ya d'auko a roba ya had'a da tsumma yazo ya gogewa mutumin jiki, ya shanja masa kaya, sosai mutumin yaji dadi yayita sama Muhammad Albarka. Da dadare ma su gidado sun koma dakin su, yayinda Al'ameen ya kwanta da mutumin a d'akinsa tare, tsakar dare mutumin ya farka da taimakon muhammad yayi fitsari ya sake dawo dashi ya kwantar, a hankali mutumin ya kalli muhammad sai kuma ya bude baki ya fara magana, Allah ya dubi halinda zan shiga ya aiko mini ku muhammad, da ace yau babuku a gidan nan bansan halinda zan tsinci kaina ba, bani da kowa gashi ba Aure nake dashi ba bare yara. Babu kome Baba fatan mudai Allah ya baka lafiya. Ameen muhammad, Akwai wani taimako da nakeso kamin, in babu damuwa d'an nan? Ba kome baba indai har baifi karfina ba, kuma bai sab'awa shariya ba, zan maka kome da kake bukata, kayi mana kome baba tunda ka bamu matsuguni a gidan ka. Muhammad a gidan da nake aiki tsawon shekararu a gidan, tun lokacin da mahaifina ke aikin a matsayin da nake yau, ina binsa muje tare har Allah ya d'auki Ransa, ni na cigaba da aikin kamar shi, a yanzun bani da kowa ba uwa ba uba ba yara ni kad'a nake rayuwa ta a gidan nan, sai yanzun da Allah ya turo mini ku, in ba damuwa so nake muhammad kaje a matsayina, kaci gaba da aikin da nake har Allah yasa na samu Lafiya, kaga bazanso ace aikin da nake tsawon shekaru, yau a samu wani ya karbe mini ba, tunda ciwon bana kwana biyu koh uku na warke bane?sai nayi jinya mai tsawo. Shuru muhammad yayi na d'an wani lokaci kafun yace, ba kome baba zanje nayi aikin har Allah ya baka lafiya, Amma wani irin aikine don ni baba banyi karatu mai zurfi ba? Murmushin karfin hali mutumin yayi, bafa aikin da ya shafi ilimi bane, aikin gidan sarauta ne, kuma nine sarkin shayi na gidan. Muhammad ne ya kalle sa da mamaki, Gidan sarauta kuma baba? Eh d'an nan zakaje ka zauna a matsayina tun jiya na sanar dasu zaka fara zuwa aiki gobe. Aini baba ban iyya dafa shayi irin naku ba, kadai ga yanda na had'a shayin d'azun baiyi irin wanda ka had'a mana ba. Karka damu muhammad akwai wa'inda zan turaka wajen su, 'yan gida nane suna taimaka mini wajen raraba shayi a gidan, Na sarki ne kawai nake kaiwa da kaina, kaima yanzun kaine zakana kai masa,sannan shayi kala uku ake, akwai na sarki shinasa dabanne, akwai na family akwai na bayi. Baba anya zan iyya aikin nan kuwa, gidan sarauta fa kace? Zaka iyya muhammad ka taimaka kaje kaji? Shikenan Allah ya kaimu goben lafiya, Amma baba wazai nuna mini gidan, don ni bako ne , bansan ina ne gidan sarkin garin nan ba? Karka damu muhammad akwai yaron makwantan mu gobe zan turaka gidan su saiya kaika. Shuru muhammad yayi ya kwanta, Amma ya kasa bacci haka kawai yaji yana fargaban zuwa gidan kodon bai taba zuwa bane oho. Washe gari muhammad ne yayi wa mutumin Alwala da ruwan zafi ya saita sa gabas, sukuma suka wuce masallaci. Bayan sun dawo kamar jiya suka kimtsa gidan yau harda karyawa suka had'a mai kyau, bayan muhammad yayi wanka, baba kaya ya sakasa ya d'auka irin na buzaye, wando kato da rigansa mai aiki a gaba sai rawanin su, muhammad kasa nad'a rawanin yayi, Amma haka mutumin nan a bashi da lafiya saida ya nad'awa muhammad, rufe masa fuska yayi da rawanin babu abinda ake gani a fuskar sa sai kwayar idanunsa, sosai Al'ameen yayi mamaki harya kasa hakuri yayi magana, baba basai an rufe fuskar duka ba? Ah ah muhammad ina son koh kaje gidan karka bude fuskar ka, ka barsa a haka, kuma kayi taka tsamtsam da kowa na gidan, karka yarda da kowa kayi abinda ya kaika ka dawo, ga wannan in kaje get sai kanuna, kafun a barka ka wuce ciki. Karba muhammad yayi yana karanta abinda baba ya basa, get pass ne d'auke da rubutun larabci, a jiki saidai bai gane me aka rubuta ba, kasancewa yare aka rubuta da harufan Larabci sai hoton zaki a bayan get pass in, Muhammad fita yayi bayan yama su gidado bayanin inda zashi, sosai suke da Zuzuta karbar da kayan ta masa kamar buzun gaske, bayan ya fita a gidan, gidan makwancin su ya wuce ya masa bayani kamar yanda baban yace masa, had'asa da yaron sa mutumin yayi, ya rakasa gidan da baba ke aiki. Tunda suka sauko a machine yakejin wani irin masifeffen bugun zuciya, ga wani irin fargaba dake cikin ransa ya rasa dalilin da yasa? ya tsinci kansa da tsoron zuwa gidan, tun daga nesa ya hango wani irin gini mai d'aukar hankali gini ne irin dogin nan masu masifar tsaho, ga wani fankamemen get fari mai d'auke da hoton zaki babba a jiki, gidane na Alfarma koh ince unguwa guda tun daga nesa zaka tambatar gidane na sarauta, masuji da mulki,yanda suke matsowa gidan haka bugun zuciyar Al'ameen ke kara yawaita, karasowa sukayi bakin get in, masu tsarone sanye da bakaken kaya hannunsu d'auke da manya manyan bindigogi cikin tsawa d'aya daga cikin su ya dakawa su muhammad da karfi cikin yare yake musu magana. Daskarewa muhammad yayi jin yanda mutumin ya hayayyako musu kamar zaicisu d'anye, gashi sai yare yake shikuma baji yake ba, Allah yasa yaron da suka zo tare yana gun shiya musu bayanin zuwansu cikin yare tare da sanar dasu muhammad d'an uwan Sarkin shayi ne, zaizo ya karbe sa daidai yaji sauki. Basu barsu sun shiga ba har saida Al'ameen ya nuna musu get pass da baba ya basa kafun suka barsu suka shiga ciki, mutuwar tsaye muhammad yayi lokacin da idanunsa suka sauka a compound na gidan, duniyace babba gida mai matukar girma, a haka suke taka tsakar gidan daidai sun iso tsakiyar gidan muhammad yaga gunkin zaki babba mai matukar girman gaske, An kawatashi a tsakar gidan a zaune kamar mai rai, wucewa wani shashe sukayi da yaron sai gasu a wani kayatancen falo mai masifar kyau da d'aukar hankali, kujerune na Alfarma a cikin su, zarce wa sukayi cikin wani kofa dake gefen falon, shidai muhammad idone nasa yake bin koh ina da kallo, har suka shiga cikin d'akin, wow shine abinda ya fitoh a bakin sa ganin wani irin kitcheen na Alfarma mai dauke da kayan Alatu na zamani, sai samari guda biyu dake kitchen in a tsaye suna aiki,jin motsen su muhammad da sallamar suce yasasu juyowa. Amsa sallamar sukayi, bayan sun gaisa da yaron yake musu bayanin Al'ameen ne zai karbi, sarkin shayi harya warke, sannan sarkin shayi yace su koya masa had'a shayi, sannan shi zaina kaiwa sarki shayi kullum, duk da yare yaron ke musu bayani. Muhammad kamfa ya shiga tsaka mai wuya don shi dai ba yare yake jiba, tayaya zai iyya zama da wa'innan mutane wai daman babu hausawa ne a nijar koh dai wannan garine baida hausawan oho?kuma gashi baba ya iyya hausa? Yaron ne yajuya zai fita a kitchen in da sauri muhamamd ya bisa a baya, da mamaki yaron ya juyo ya kalli muhammad cikin mamaki yake tambayar sa yaya kuma zaina binsa? Gaskiya nifa ban gane ba kowa a gidan nan sai yare yake mini, nifa baji nake ba. Dariya yaron yayi karka damu kaji, wasu a cikin su suna ji sai dai in an ganka za'ayi tunanin koh kanajin yarene shiyasa wasu ke maka yare, Amma in suka maka magana kana musu hausa kaji zasu maka suma. Toh nagode kawai muhammad yace, ya koma kitchen in, sosai suka sakasa aiki goge kofuna d'aura shayi saka wanshan ganye ah ah yi kaza sai kusan azahar, bayan sunyi sallah aka fara rabon shayi a gidan, shima wasu kofuna da buta na Alfarma masu shegen kyau da sheki ruwan Gold suka zuba shayin a butan, aka jera a karamin tire da shukali sai bolw na zuma, shima Golden colour da shukali biyu, mikama Al'ameen sukayi Hade da had'asa da wani a cikin ma'aikatan ya nuna masa flat na sarki. Duk abinda Al'ameen kiyi tsananin bugun zuciyar sa nayi, har wa yanzun da suke nufar sashen sarki, hannunsa d'auke da tiren kayan shayin, suna isa kofar shiga falon, ma'aikacin ya koma ya bar muhammad tare da nuna masa kofar da hannu alamu dai nan zai shiga, yafi minutes 2 yana tsaye ya kasa shiga zuciyarsa na matukar buga wa da sauri-sauri, ganin wani bawa zai wuce yasa muhamamd saurin sa hannu ya murd'a kofar falon bakinsa d'auke da sallama, Amma bai shiga ciki ba a bakin kofar ya tsaya. Amsa masa sallamar akayi saiga wata mata ta fitoh, sanye da kayan da bayin gidan ke sanyawa, hade da masa iso zuwa cikin falon, shigowa Al'ameen yayi yana bin bayanta har suka karaso cikin falon, falone babba mai girman gaske da kawatuwa irin falon nan na sarakuna, masu ji da lokacin su, wuce falon sukayi suka nufi wani kofa daban, nan ma falone Amma baikai wanda suka wuce girma ba Da kayatuwa, kara nausawa sukayi cikin wani kofar, saigasu a wajen shakatawa mai d'auke da shuke shuke na flowers mai ban sha'awa da kamshi, jefa kafa kawai muhammad yake don yayi matukar gajiya da tafiyar nan, da yake daman bai gama sauke gudun hijiran da sukayi ba, ga matsanan cin bugun zuciyrsa kiyi da karfi, lokacin da idanunsa suka sauka akan mutanen dake zaune su biyu cikin shiga na Alfarma wanda koh ba'a fad'a ba kasan sarkine tare da matarsa dake sanye da Alkimba mai masifar kyau da d'aukar ido, farace tas kyakkyawa da ita, yayinda sarkin ke sanye da rawanin buzaye a kansa ya rufe fuskar sa luf banda idanunsa babu abinda mutun zai hanga don koh kafar sa da hannunsa boye yake a cikin suturansa, shuru sarauniyar tayi ganin su Al'ameen da Alamu dai magana take da mijinta Da sallama a bakin su Al'ameen suka karaso inda suke, da sauri sarkin ya dafe daidai saitin zuciyarsa yana Ambatun sunan Allah a zuciyar sa, yayin da muhamamd suka tsunguna a kan gwuwuwinsu A hankali ya d'aura tiren akan table inda ke gabansu, hannunsa sai rawa yake wanda baisan dalilin hakan ba, tsiyaye shayin ya fara a kofi yana had'awa da zuma. Sarauniya ita ta kula da halin da mijin ta ke ciki da sauri ta matso garesa Ranka ya dade lafiya meke faruwa zuciyar ce? Shuru ya mata, itama bata damu ba don tasan halin mijin ta zata masa magana sau dubu ba Samun Amsa zatayi ba, yasha yarfata a gaban bayinta Amma tun yana damunta yanzun koh a jikinta, kara tambayar sa tayi zuciyar sa na ciwo ne? Girgiza mata kai kawai yayi baiyi magana ba, jingina yayi da jikin kujeran da yake zaune akai ya lumshe ido yana maimaita innalilahi..... Al'ameen na gama had'a shayin ya mike abinsa ya fita a lambun, sai a lokacin sarkin ya zare hannunsa daga kan kirjinsa yayinda idanunsa sunyi matukar kaduwa zuwa ja, sosai jikinsa ke rawa, ganin hakan yasa sarauniya mikewa da sauri ta fita a lambun ba'a jima ba saiga ta, ta dawo da wata tsohowar mata cikin shiga ta Alfarma kyakkyawa da ita fara, ta karaso garesa hannunta d'auke da magani, da saurin ta balla hade da karban kofin ruwan dake hannun sarauniya ta kafa masa a baki, ba musu ya karba yasha maganin, ka tashi ka koma ciki kaji?tsohowar tace Girgiza mata kai kawai yayi vaiyi magana ba, Alamu dai yafison zaman nan in, ba musu daga matar tasa, har tsohowar suka basa waje don haka yake indai ta shine yafi kaunar a basa waje ya zauna shi kad'ai sau dubu akan ya zauna da mutane. Al'ameen kam yana komawa kitchen in abinci aka kawo musu na rana, mai rai da lafiya harda kaji sukaci, zama sukayi a falon da kitchen in ke cikinsa suka kwanta a kan kujerun dake wajen alamu dai daman falon donsu akama,(ma'aikatan shayi) sai la'asar suka sake dafa sabon shaye wannan karon Al'ameen ne ya d'auka shi kad'an sa, ba tare da rakiyar jakadiya ba ya shigo falon, yarane zaune a tsakar falo su uku, biyu suna zaune a kasan cafet dake shimfid'e a tsakiyar falon, suna rubutu a takarda dukansu mata ne d'ayan zata kai shekara goma sha biyar, d'ayan kuma zata kai shekara Goma, Lokacin da yaran suka d'ago suka kallesa baisan lokacin da tiren shayin dake hannun sa ya tsubuce a hannunsa ba, a take kome ya tarwatse a wajen, suma yaran zare ido sukayi ganin barnan da muhammad ya musu a falo, d'aya yarinya ta ukun dake zaune akan kujera tana danna waya bazata wuce shekara 20 ba, ta mike cikin masifa da izza, kai wani irin wawane koh ince dolo kana da hankali kuwa zaka shigo mana falo kazo ka zubar da abu, sannan ka tsaya kana kallon mu, jira kake mu kwashe maka koh me? Habba Nabila baikamata kima mutum babba kamar wannan irin zagin nan va, baikama taba gaskiya ki gyara halinki, d'aya daga cikin yaran da ke zaune a kasan cafet in tace ma nabilar. Kinga muhibbat babu ruwan ki dani ki daina mini irin wannan abin da kike mini, niba sa'arki bace Amma na fahimci kina mini shishigi a lamurana be careful, takarasa maganar da barin falon tana hararan sa. Muhibbat ce ta kallesa kaga malam tattara abinda ka fasan nan ka tafi store a baka wasu kayi sauri ka kawowa Abba shayi?duk da Turanci suke magana. Muhammad kam mutuwar tsaye yayi yana kallon yarinyar, koh dai mafarki yake ne yarinyar kamar khadijar sa haka yake jin muryar ta, yanda khadija ke magana ba R haka ita ke magana, kaman ninta kome nata yana masa irin na yar uwarsa,duk da khadija na yarinya ya makance amma hakan bazai hanasa gane taba, a gaskiya abinnan ya basa mamaki matuka da kuma tsoro gasu su biyu masu tsananin kama da juna, koh yace masu kama dasu, jin ta sake masa magana cikin yanayin mamaki ya tsunguna ya kwashe fashashun kofunan ya fita a falon da sauri. ***************** Sumayya fa yanzun ci yafi nada ga bacci babu aikin da take yanzun kome khadija kiyi in taga aikin yama khadija yawa saita, sata ta musu take Away kawai, don khadija na kokari ga zuwa school har yamma take dawowa ga aikin gida ga masu kitso, amma Alhmdulilah baza'ace aikin mai yawa ba tunda sharane kawai sai girkin abinda zasuci don yanzun cin sumayya yafi nada gashi cikin yayi girma sosai ya kara hurata, jiki tayi bana wasa ba kafafunta haka suka cika tim,An hanata cin gishiri ma A hospital yanzun ganin irin huruwar da tayi. Yau weekend babu school khadija ce zaune a baranda tana ma mutane kitso, yayinda wasu ke zazzaune suna jiran layi yazo kansu, sumayya ce ta fito cikin shiga ta Alfarma zanine less da hijab nata mai hannu medium size, sai jakan sakalawa a kafad'a da waya a hannunta sosai tayi kyau, hannu tasa ta maida kofar falon ta rufe, "khadija lailar ta fitoh ne"? Ah ah Aunty bata fitoh ba koh na dubo miki itane? "Ah ah khadija ki bari kawai bara naje flat natan sai mu wuce" Toh Aunty saikun dawo Tana sauka a kan barandan tace"Yauwa khadija" au na manta me zan dafa ne na rana? "Kibari kawai khadija naga yau akwai layin kitso sosai in muka shiga kasuwa zanbi restaurant nai mana take Away" Ok toh Aunty adawo lafiya "Allah yasa khadija"wucewa compound in gidan tayi ta nufi sashen laila, harta haura dakalin d'akin ta saigata ta fitoh cikin shirin fita, ah ah sumayya harkin shiryane? "Bazan shirya ba laila so fa nake mu dawo kafun Azahar don wannan zafin ranan ba lafiya bane" Gaskiya kam bare ku masu ciki. "Kinga laila don Allah ki shige muje bana son yawan tsayuwar nan habba" Yi hakuri hajiya muje, kawai laila tace suka kama hanya da sumayya. Kasuwa laila da sumayya sukaje da taimakon laila sukayi sayayyan kayan baby, dana haihuwa kama daga baf gadon yara kayan sawa feda kome daya dangance baby da sumayya wanda zatayi Amfani dashi lokacin haihuwa da bayan haihuwa ita da babyn ta duk sumayya ta saya, kaya niki niki haka suka zuba a Texi, har sun shiga mota sumayya ta hangi mai mangoro, take tunanin mijin ta daya zamo mata jiki ya fado mata, sai kuma taji tanason sha, hakuri ta baiwa mai motar ta sauka, da sauri ta nufi wajen mai mongoron bata saurare maganar da laila kece mata ba,tana kokarin bude jakar hannunta, gabaki d'aya hankalin ta na kan jakan, bata koh ganin gabanta. Ji kawai tayi an bangajeta da karfi tayi baya tagal tagal zata fadi............🍀🍀 ✨Ruqeenjalal✨ 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya* *Ibrahim* 🍃 Page8⃣4⃣&8⃣5⃣ Tagal-tagal tayi zata fadi gabaki d'aya ta gama sadakar wa itakam yau saita Allah, rumtsa ido tayi tana Ambatun illahilahi, saiji kawai tayi an tarota cikin zafin nama ta sauka a hannunsa. Subhanallahi baiwar Allah bi a hankali baki ga halinda kike ciki ba, haka kuke saiku d'auko ciki rududu rududu ku shigo kasuwa tsabar neman fitana da salon jawa mutan masifa. jin abinda mutumin da ya bangaje sumayya yace, yasa yaron da ya tarota ya taimaka mata ta zauna a bakin wani shago, da sauri ya nufi guy in, wanka masa mari yayi, ya cakumo wuyarsa cikin bacin rai yake magana, kai wani irin dabbane wawa kawai baka dubi halinda take ciki ba, ka tashi ka bangaje ta batare da ka dubi halinda zata shiga ba, kazo kana gayawa mutane maganar banza. Hannu guy in ya d'aga zai rama marin sa, da sauri yaron daya taro sumayya ya kama hannunsa, wasa wasa fa dambe ya kaure a tsakanin su, yayinda sumayya ke gefe gabaki d'aya jikin ta rawa yake, don ita d'auka tayi ma yau innan dai sai abinda Allah yayi. Da sauri jama'a suka shiga raba fad'ar, don gudun kada abin yakai ga yan sanda kuma ya zama babban magana, daker aka samu yaron ya hakura, guy in ya tafi, da sauri ya dawo wajen da sumayya ke zaune, sannu Aunty badai binda ke damunki koh? Girgiza kai sumayya tayi a hankali, tana kallon laila data gaji da jiranta tabiyo baya, don ita bata ga abinda ya faru ba. Kalamu-wahid!!!!!Daga nesa aka kwalama yaron kira da sauri ya juya, yana kallon mai kiran nasa,Na'am babayo ina zuwa pls. Babayo dake tinkaro inda su sumayya suke, bakine kamar Kalamu-wahid sai dai kalamu ya fisa kyau, duk da shima ba tayan baya bane, kuma babayo nada zanen kanuri a fuskar sa, sabanin kalamu da baida zane sam. Ke sumayya lafiya sayan mangoron ne, kika zo kika zauna?bata jira Amsar sumayya ba ta kalli kalamu, malam lafiya ka saya mata a kai? Sumayya ce ta bata amsa, "Lafiya laila taimako na yayi, saura kad'an yau nasha kasa" Sumayya dakin kashe kanki, shiyasa nake ta miki magana Ki tsaya na sayo miki, amma kememmen kika ki saurarata. Yi hakuri Aunty laila ba laifinta bane, kalamu yace, yana tattara wa sumayya jakanta daya watse a kasa. Kalamu lafiya mayya tsayar da kai kuma, ka barni a mota tun d'azun? Yi hakuri babayo bara mu sauke wa'innan a gida. "Ah ah ka bari kawai mun tare taxi harna saka kayana a ciki" Ah ah aunty sumayya muje dai na kaiku, kuyi hakuri wallahi da zuciya d'aya nake son d'aukarku. Shuru sumayya tayi tana kallon yaron da mamaki, bazai wuce shekara 19 zuwa da 20 ba, daga hadu d'aya har ya shiga jikinta ga Aunty sama Aunty kasa"toh shikenan sai muje ku d'auko kayan mu dake mota" Ok toh muje ku shiga mota gashi shan, yace yana nuna wani had'aden mota dake tsallaken titi, babu musu sumayya ta mike da sauri ya karbi jakan nata, laila na binsu a baya sukayi wajen motar, baya sumayya da laila suka shiga, yayinda babayo da kalamu-wahid suke gaba, babayo ne mai tukawa kalamu na gefe, da nuniya sumayya suka nuna musu taxi in, tattara mata kayanta sukayi shida babayo suka zuba a boot, wasu kuma a baya don kayan yawane dashi, shiga sukayi hade da tambayar su unguwan da suke. Da mamaki kalamu yace laaa ai unguwan mu d'aya daku wallahi, jin unguwar da laila tace. Laila ce ta kallesa Au da gaske, ku a wani gida kuke kenan? Muna kusa da gidan hayan Malam sale uba? "Kai aimu a gidan hayan muke "sumayya ta basa Amsa. Babayo ne yace, Ah lallai kam rashin ziyara ne babu, ace unguwan ku d'aya har ginin gidan ku a manne bakusan juna ba. "Gaskiya kam"kawai sumayya tace tayi shuru ganin sun iso get na gidan su, sauka sukayi kalamu ya sauke musu kayansu, tare da bawa babayo umurni daya shiga gida, shi zai shigar wa da sumayya kaya, duk yanda sumayya ta hanasa kiyayi, haka ya kinkimi kaya shida laila sukayi cikin gidan su sumayya, yayinda ita kuma ke binsu a baya. Khadija dake zaune a falo tana cin abinci, sannan ga laptop a cinyarta tana kallo,sai munira da kaninta a gefe, suma tasa musu abinci daban a plate, da sauri ta d'ago jin muryan namiji na sallama a bakin falon su, kafun ma ta Amsa har an turo kofar an shiga. Laa Aunty kun dawo?sai yanzu, da sauri yaran laila suka mike sukayi wajen mamansu suna mata oyoyo. Sai yanzu khadija sayayyar ce da yawa, yauwa kalamu aje mana kayan a falo. Aje kayan kalamu yayi, laila ma ta aje nata, juyawa yayi zai fita yana musu sallama. "Ah ah kalamu dawo ka zauna, ke khadija kawo masa sallaya, falon namu Empty ne ba kome sai katifa" Kai Aunty dama kin bari wallahi nagode Da sauri sumayya tace"Ah ah kalamu kadai zauna ta kawo maka abinci kaci don Allah karkace ah ah" Gaskiya ne kalamu ka zauna mana kaci abinci, nima khadija ibomin abincin nan yunwa nakeji, kinsan na fita gida banci kome ba, laila tace tana nufar kitchen in sumayya, karban abincin kawai tayi a plate ta fita. Zama kalamu yayi yayinda sumayya ta wuce d'aki abinta, zata watsa ruwa sosai taji dadin girkin da khadija tayi, don ita tama manta tace zata musu take Away. Kawowa kalamu Abinci khadija tayi da ruwa ta aje masa a gaba, komawa tayi inda ta tashi taci gaba da cin abincin ta, shukali kalamu yasa ya ibi abinci sai kuma ya kalli khadija da mamaki ganin tunda yazo falon koh gaidashi batayi ba, sai wani cin magani take kamar bata ga bako ba, damuwar ka da bawa kenan bai iyya samun yanci ba saiya zage. Jin abinda yace yasa khadija gane kanuri ne, cikin dariya tace eh tsabar rashin yancin wasu koh gangan tarihi basu dashi a fada. Kutt ke wallahi karyane kune bayi, kauyawa in banda kauyanci mutun yaga bako yaki gaidashi? Baki ma ai iri-iri ne, akwai kalan gaisuwa akwai kalan kori. Da mamaki yake kallon khadija, kutturu amma yarinyar nan ta iyya bakar magana, waike anya ba makarantan harshe kike ba? Ah ah na kutare nake Shuru kalamu yayi jin abinda tace masa, yaci gaba dacin abincin sa. "Waini maganar me nake jine tun d'azun ina bathroom"? Wallahi Aunty bakon kine da iyayi, harda zai gayawa fulani magana. "Ke kuma sai kikayi me"? Saina fad'a masa ba sugari, mudasu waza'a kira bayi. Jin abinda khadija tace da sauri kalamu yace, kune dai bayin. Wallahi badai muba. "ke khadija ya isa haka, banason zagewa da yawa kinsan dai ummina kanuri ce koh?toh ki sassauta musu" Dariya kalamu ya sake, shikenan Allah ya kamaku duka Itama sumayyar dariya tayi," babu wani Allah ya kamamu nadai kwace ka kawai yaro" Kai Aunty yaro kuma a gaban wannan yar rainin wayon? kai wallahi ya isheka karka sake cemin yar rainin wayo, ni bance maka ba sai kai zaka fad'a mini. Kunga ni surutun nan ya isheni haka, ibo mini abinci naci yunwa nake ji, habba kedai kullum fad'a da mutane ga kalamu yazo zai karbi Ammar. Kai Aunty Allah suke shiga idona, tana maganar tana shiga kitchen Zama sumayya tayi akan katifar ta, bayan khadija ta kawo mata abinci, cin abinta take koh a jikinta ta rasa me yasa ta sake jiki da kalamu sai hiransu suke da khadija, tana sa musu baki jifa-jifa in taga khadija na k'wararsa a magana, don daga gani ba sabo yayi da surutu ba, kawai yau saka kansa yayi, har suka gama cin abinci kalamu bai tafi ba sai da azahar yayi ya musu sallama ya wuce. Yana fita bayan su sumayya sunyi sallah kayan sayayyan tasa khadija d'aukowa suka duduba, sosai khadija tayita yaba kayan don yayi matikar kawatuwa, kuma an kashe kudi kam ba karya. Washe gari da safe principal insu khadija ya kira sumayya, akan baza'a zo d'aukar khadija ba, saboda drivern school buss insu ba lafiya, dole tasa yau khadija da kanta zata makaranta dayake yanzun tana da kudi, karywa kawai tayi tama sumayya sallama ta fita. Takai minutes 20 a tsaye bata samu abun hawa ba, tun 7:00 ta fitoh gashi yanzun har 7:20 bata samu mota ba, gabaki d'aya ranta ya gama baci, gashi suna jarabawan second team, gani kawai tayi mota yayi packing a gaban ta, da sauri ta d'ago tana kallon wa'inda ke cikin motar, kalamu dake sanye da fararen uniform na nurses, yana zaune a kusa dame tuki, sai students na makarantan su, dake baya su biyune namiji da mace, dukansu fuskar su d'auke da zanen kanuri,sabanin kalamu da babu, murmushi tayi ta gaida mai tukin. Amsawa yayi. ba tare da ta kalli kalamu sau biyu ba, tajuya zata ci gaba da tafiyar ta. In ance ma mutum bakauye yaji haushi, Amma bazai daina kauyancin ba, kinga mun tsaya a gaban ki, aikin san d'aukar ki zamuyi shine zaki wani juya kamar ana sarrafaki da remote. Ba karamin haushi khadija taji ba, jin rashin mutunci da kalamu ya mata. Kiyi hakuri kanwa ta, kizo mu wuce munyi late karki kulasa, mai tukin yace. Babu wani karta kulani babayo, gaskiya dai na fad'a kalamu yace yana danna wayar sa kamar bashi yayi maganar ba. Wallahi badon ana exam ba, yau da babu abinda zaisa taje makarantar ma gabaki d'aya, bare hawa motar su, amma ba yanda zatayi haka ta bude back seat ta shiga. Kalamu suka fara saukewa a school of nurse, kafun aka sauke su khadija, babayo ya wuce aiki. Wasa wasa shakuwa ya fara shiga tsakanin khadija da kalamu-wahid a boye don a gaban sumayya kam fad'a suke, don yanzun duk lokacin da yaso yake zuwa kofar sumayya, suyi hira ya tafi, duk da sumayya bata kawo kome a ranta ba, ganin cewa in yazo har falo yake shiga, kuma in suka zauna da khadija ma fad'a suke akai-akai. Kamar yau khadija sun gama jarabawa tun Friday, zaune take a falo ita da sumayya, sai ga Kalamu yayi sallama a kofar falon su mikewa khadija tayi ta mikawa sumayya hijab nata kafun suka basa izinin shigowa, sosai sukasha hira yauma, dayazo tafiya bayan sunyi sallama da sumayya tsayawa yayi a waje get, kamar minutes 5 da fitar sa khadija ta mike zata fita a falon. "Ina zaki kuma khadija"? Aunty zan tattaro shanya nane naga garin da hadiri? "Ah ah kidai tattaro shanyar, Amma garin nan kam ba hadiri bayan yanzun damuna ta wuce" Jin Abinda sumayya tace yasa khadija sunkuyar da kai, ta fice a falon da sauri ta nufi igiya ta dauko hijab nata, tayi get, tana bude get in aiko kamar yanda ta zata inne Kalamu na tsaye, kai lafiya tun a falo sai ketket-ta mini ido kake? Wallahi khadija magana nake so nayi dake daman. Da mamaki da kallesa au yau kuma kunyar Aunty kake ji kome? Ah ah ba haka bane kinsan next week zamu fara exam? so bazan samu daman shigowa ba shiyasa na kawo miki wannan, yace yana mika mata bakin laidar dake hannunsa. Ba musu khadija ta karba hade da tambayar sa menene a ciki? Wayace harda sim, na miki register sai muna gaisawa daidai na samu zama, don zan kwana biyu gaskiya bazan leko ba? Kaga karbi abinka wallahi babu ruwana? Kamar yaya ba ruwanki khadija? Kamar yanda nace maka, so kake Aunty taga rashin kyauta wata gareta? tayi mini dukkan kyautatawa baika mata na nuna mata rashin godiyan Allah ba. Yanzun khadija karbar wayar ce rashin godiyan Allah? Kayi hakuri Amma bazan iyya karba ba sai dai in zaka kaiwa Aunty da kanka ka bata? Babu damuwa muje na batan. Ah ah wallahi ka fara zuwa dai kaikad'ai kar tace mun had'a baki, tana maganar ta koma cikin compound in tana tattara shanyar ta. Ba musu Kalamu ya koma kofar sumayya, da mamaki take tambayar sa lafiya kuwa ya dawo?bayani ya mata akan waya ya baiwa khadija taki karba shine ya kawo mata koh khadijan zata yarda ta karba? Da mamaki sumayya ta karbi wayar ta bude, wayane sumsung Galaxy S9+" Kalamu nima karan kaina nayi tunanin saya wa khadija waya, Amma nafi son saita kammala secondary ta mallaki hankalin kanta" Aunty yanzun ma khadija tayi hankali fa, shekara 19 take nema wasu a shekarun tan nan ma, suna jami'a don Allah aunty ki barta ta rike wannan in? "Au haka ta fad'a maka kenan bazan barta ta rike ba, kuka had'a baki kazo waje na koh"? Ah ah aunty kawai dai na fahimci khadija nada biyayya ne. "Shikenan Allah ya sanya Albarka, harda shekarunta ta fad'a maka kenan"? Ameen Aunty Amma nidai kiyastawa nayi bata fad'a mini ba, yace cikin murna ya fita ganin Aunty ta karbi wayar, yana fita a falo yakusa cin karo da khadija dake makale a kofar falo tana sauraron su, cikin murna tace Aunty ta yarda? Kai kawai ya d'aga mata ya wuce get ya fita, Khadija kam kasa komawa cikin falon tayi, taci gaba da tsayuwa a bakin kofa. Sumayya dake jiran Khadija ta shigo, shuru shuru bata shigo ba, yasata mikewa fuska a had'e ta nufi kofar falon....... ************* Jikin muhammad sai rawa yake yaje ya karbo wasu kayan, ya karbo sabon shayi, ya sake shigowa falon wannan karon tsohowar ce da yara biyun, wanda d'ayan bai manta sunan taba muhibbat sai karamar , gaida tsohowar yayi ya wuce falon sarki, Wannan karo sarkin baya falo yana ciki, aje masa shayin yayi a table ya tsaya a gefe, kusan 30 minutes kafun ya fitoh yauma kamar kullum fuska a rufe,, a take gaban Al'ameen ya soma bugawa da karfin gaske, zama sarkin yayi a hankali akan d'aya daga cikin kujerun falon, da sauri Al'ameen ya dukar da kansa a hankali ya matso da table in ya siyaye masa shayi hade da gaidashi, hannu kawai sarki ya d'aga masa ba tare da yayi magana ba. Yana gama had'a shayin, ya fita a falon, direct kitchen in shayi ya koma, yama abokan aikin sa sallama duk da lokacin tashi baiyi ba, ya kama hanyar gida, cikin hanzari yake tafiya har ya iso bakin titi tare abin hawa yayi. Yana isa gidan cikin hanzari ya bude kofa bakin sa d'auke da sallama, baikara saba sallamar ya makale masa a wuya, ganin baba tsaye akan kafafunsa........... ✨Ruqeenjalal✨ 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya* *Ibrahim* 🍃 Page8⃣4⃣&8⃣5⃣ Tagal-tagal tayi zata fadi gabaki d'aya ta gama sadakar wa itakam yau saita Allah, rumtsa ido tayi tana Ambatun illahilahi, saiji kawai tayi an tarota cikin zafin nama ta sauka a hannunsa. Subhanallahi baiwar Allah bi a hankali baki ga halinda kike ciki ba, haka kuke saiku d'auko ciki rududu rududu ku shigo kasuwa tsabar neman fitana da salon jawa mutan masifa. jin abinda mutumin da ya bangaje sumayya yace, yasa yaron da ya tarota ya taimaka mata ta zauna a bakin wani shago, da sauri ya nufi guy in, wanka masa mari yayi, ya cakumo wuyarsa cikin bacin rai yake magana, kai wani irin dabbane wawa kawai baka dubi halinda take ciki ba, ka tashi ka bangaje ta batare da ka dubi halinda zata shiga ba, kazo kana gayawa mutane maganar banza. Hannu guy in ya d'aga zai rama marin sa, da sauri yaron daya taro sumayya ya kama hannunsa, wasa wasa fa dambe ya kaure a tsakanin su, yayinda sumayya ke gefe gabaki d'aya jikin ta rawa yake, don ita d'auka tayi ma yau innan dai sai abinda Allah yayi. Da sauri jama'a suka shiga raba fad'ar, don gudun kada abin yakai ga yan sanda kuma ya zama babban magana, daker aka samu yaron ya hakura, guy in ya tafi, da sauri ya dawo wajen da sumayya ke zaune, sannu Aunty badai binda ke damunki koh? Girgiza kai sumayya tayi a hankali, tana kallon laila data gaji da jiranta tabiyo baya, don ita bata ga abinda ya faru ba. Kalamu-wahid!!!!!Daga nesa aka kwalama yaron kira da sauri ya juya, yana kallon mai kiran nasa,Na'am babayo ina zuwa pls. Babayo dake tinkaro inda su sumayya suke, bakine kamar Kalamu-wahid sai dai kalamu ya fisa kyau, duk da shima ba tayan baya bane, kuma babayo nada zanen kanuri a fuskar sa, sabanin kalamu da baida zane sam. Ke sumayya lafiya sayan mangoron ne, kika zo kika zauna?bata jira Amsar sumayya ba ta kalli kalamu, malam lafiya ka saya mata a kai? Sumayya ce ta bata amsa, "Lafiya laila taimako na yayi, saura kad'an yau nasha kasa" Sumayya dakin kashe kanki, shiyasa nake ta miki magana Ki tsaya na sayo miki, amma kememmen kika ki saurarata. Yi hakuri Aunty laila ba laifinta bane, kalamu yace, yana tattara wa sumayya jakanta daya watse a kasa. Kalamu lafiya mayya tsayar da kai kuma, ka barni a mota tun d'azun? Yi hakuri babayo bara mu sauke wa'innan a gida. "Ah ah ka bari kawai mun tare taxi harna saka kayana a ciki" Ah ah aunty sumayya muje dai na kaiku, kuyi hakuri wallahi da zuciya d'aya nake son d'aukarku. Shuru sumayya tayi tana kallon yaron da mamaki, bazai wuce shekara 19 zuwa da 20 ba, daga hadu d'aya har ya shiga jikinta ga Aunty sama Aunty kasa"toh shikenan sai muje ku d'auko kayan mu dake mota" Ok toh muje ku shiga mota gashi shan, yace yana nuna wani had'aden mota dake tsallaken titi, babu musu sumayya ta mike da sauri ya karbi jakan nata, laila na binsu a baya sukayi wajen motar, baya sumayya da laila suka shiga, yayinda babayo da kalamu-wahid suke gaba, babayo ne mai tukawa kalamu na gefe, da nuniya sumayya suka nuna musu taxi in, tattara mata kayanta sukayi shida babayo suka zuba a boot, wasu kuma a baya don kayan yawane dashi, shiga sukayi hade da tambayar su unguwan da suke. Da mamaki kalamu yace laaa ai unguwan mu d'aya daku wallahi, jin unguwar da laila tace. Laila ce ta kallesa Au da gaske, ku a wani gida kuke kenan? Muna kusa da gidan hayan Malam sale uba? "Kai aimu a gidan hayan muke "sumayya ta basa Amsa. Babayo ne yace, Ah lallai kam rashin ziyara ne babu, ace unguwan ku d'aya har ginin gidan ku a manne bakusan juna ba. "Gaskiya kam"kawai sumayya tace tayi shuru ganin sun iso get na gidan su, sauka sukayi kalamu ya sauke musu kayansu, tare da bawa babayo umurni daya shiga gida, shi zai shigar wa da sumayya kaya, duk yanda sumayya ta hanasa kiyayi, haka ya kinkimi kaya shida laila sukayi cikin gidan su sumayya, yayinda ita kuma ke binsu a baya. Khadija dake zaune a falo tana cin abinci, sannan ga laptop a cinyarta tana kallo,sai munira da kaninta a gefe, suma tasa musu abinci daban a plate, da sauri ta d'ago jin muryan namiji na sallama a bakin falon su, kafun ma ta Amsa har an turo kofar an shiga. Laa Aunty kun dawo?sai yanzu, da sauri yaran laila suka mike sukayi wajen mamansu suna mata oyoyo. Sai yanzu khadija sayayyar ce da yawa, yauwa kalamu aje mana kayan a falo. Aje kayan kalamu yayi, laila ma ta aje nata, juyawa yayi zai fita yana musu sallama. "Ah ah kalamu dawo ka zauna, ke khadija kawo masa sallaya, falon namu Empty ne ba kome sai katifa" Kai Aunty dama kin bari wallahi nagode Da sauri sumayya tace"Ah ah kalamu kadai zauna ta kawo maka abinci kaci don Allah karkace ah ah" Gaskiya ne kalamu ka zauna mana kaci abinci, nima khadija ibomin abincin nan yunwa nakeji, kinsan na fita gida banci kome ba, laila tace tana nufar kitchen in sumayya, karban abincin kawai tayi a plate ta fita. Zama kalamu yayi yayinda sumayya ta wuce d'aki abinta, zata watsa ruwa sosai taji dadin girkin da khadija tayi, don ita tama manta tace zata musu take Away. Kawowa kalamu Abinci khadija tayi da ruwa ta aje masa a gaba, komawa tayi inda ta tashi taci gaba da cin abincin ta, shukali kalamu yasa ya ibi abinci sai kuma ya kalli khadija da mamaki ganin tunda yazo falon koh gaidashi batayi ba, sai wani cin magani take kamar bata ga bako ba, damuwar ka da bawa kenan bai iyya samun yanci ba saiya zage. Jin abinda yace yasa khadija gane kanuri ne, cikin dariya tace eh tsabar rashin yancin wasu koh gangan tarihi basu dashi a fada. Kutt ke wallahi karyane kune bayi, kauyawa in banda kauyanci mutun yaga bako yaki gaidashi? Baki ma ai iri-iri ne, akwai kalan gaisuwa akwai kalan kori. Da mamaki yake kallon khadija, kutturu amma yarinyar nan ta iyya bakar magana, waike anya ba makarantan harshe kike ba? Ah ah na kutare nake Shuru kalamu yayi jin abinda tace masa, yaci gaba dacin abincin sa. "Waini maganar me nake jine tun d'azun ina bathroom"? Wallahi Aunty bakon kine da iyayi, harda zai gayawa fulani magana. "Ke kuma sai kikayi me"? Saina fad'a masa ba sugari, mudasu waza'a kira bayi. Jin abinda khadija tace da sauri kalamu yace, kune dai bayin. Wallahi badai muba. "ke khadija ya isa haka, banason zagewa da yawa kinsan dai ummina kanuri ce koh?toh ki sassauta musu" Dariya kalamu ya sake, shikenan Allah ya kamaku duka Itama sumayyar dariya tayi," babu wani Allah ya kamamu nadai kwace ka kawai yaro" Kai Aunty yaro kuma a gaban wannan yar rainin wayon? kai wallahi ya isheka karka sake cemin yar rainin wayo, ni bance maka ba sai kai zaka fad'a mini. Kunga ni surutun nan ya isheni haka, ibo mini abinci naci yunwa nake ji, habba kedai kullum fad'a da mutane ga kalamu yazo zai karbi Ammar. Kai Aunty Allah suke shiga idona, tana maganar tana shiga kitchen Zama sumayya tayi akan katifar ta, bayan khadija ta kawo mata abinci, cin abinta take koh a jikinta ta rasa me yasa ta sake jiki da kalamu sai hiransu suke da khadija, tana sa musu baki jifa-jifa in taga khadija na k'wararsa a magana, don daga gani ba sabo yayi da surutu ba, kawai yau saka kansa yayi, har suka gama cin abinci kalamu bai tafi ba sai da azahar yayi ya musu sallama ya wuce. Yana fita bayan su sumayya sunyi sallah kayan sayayyan tasa khadija d'aukowa suka duduba, sosai khadija tayita yaba kayan don yayi matikar kawatuwa, kuma an kashe kudi kam ba karya. Washe gari da safe principal insu khadija ya kira sumayya, akan baza'a zo d'aukar khadija ba, saboda drivern school buss insu ba lafiya, dole tasa yau khadija da kanta zata makaranta dayake yanzun tana da kudi, karywa kawai tayi tama sumayya sallama ta fita. Takai minutes 20 a tsaye bata samu abun hawa ba, tun 7:00 ta fitoh gashi yanzun har 7:20 bata samu mota ba, gabaki d'aya ranta ya gama baci, gashi suna jarabawan second team, gani kawai tayi mota yayi packing a gaban ta, da sauri ta d'ago tana kallon wa'inda ke cikin motar, kalamu dake sanye da fararen uniform na nurses, yana zaune a kusa dame tuki, sai students na makarantan su, dake baya su biyune namiji da mace, dukansu fuskar su d'auke da zanen kanuri,sabanin kalamu da babu, murmushi tayi ta gaida mai tukin. Amsawa yayi. ba tare da ta kalli kalamu sau biyu ba, tajuya zata ci gaba da tafiyar ta. In ance ma mutum bakauye yaji haushi, Amma bazai daina kauyancin ba, kinga mun tsaya a gaban ki, aikin san d'aukar ki zamuyi shine zaki wani juya kamar ana sarrafaki da remote. Ba karamin haushi khadija taji ba, jin rashin mutunci da kalamu ya mata. Kiyi hakuri kanwa ta, kizo mu wuce munyi late karki kulasa, mai tukin yace. Babu wani karta kulani babayo, gaskiya dai na fad'a kalamu yace yana danna wayar sa kamar bashi yayi maganar ba. Wallahi badon ana exam ba, yau da babu abinda zaisa taje makarantar ma gabaki d'aya, bare hawa motar su, amma ba yanda zatayi haka ta bude back seat ta shiga. Kalamu suka fara saukewa a school of nurse, kafun aka sauke su khadija, babayo ya wuce aiki. Wasa wasa shakuwa ya fara shiga tsakanin khadija da kalamu-wahid a boye don a gaban sumayya kam fad'a suke, don yanzun duk lokacin da yaso yake zuwa kofar sumayya, suyi hira ya tafi, duk da sumayya bata kawo kome a ranta ba, ganin cewa in yazo har falo yake shiga, kuma in suka zauna da khadija ma fad'a suke akai-akai. Kamar yau khadija sun gama jarabawa tun Friday, zaune take a falo ita da sumayya, sai ga Kalamu yayi sallama a kofar falon su mikewa khadija tayi ta mikawa sumayya hijab nata kafun suka basa izinin shigowa, sosai sukasha hira yauma, dayazo tafiya bayan sunyi sallama da sumayya tsayawa yayi a waje get, kamar minutes 5 da fitar sa khadija ta mike zata fita a falon. "Ina zaki kuma khadija"? Aunty zan tattaro shanya nane naga garin da hadiri? "Ah ah kidai tattaro shanyar, Amma garin nan kam ba hadiri bayan yanzun damuna ta wuce" Jin Abinda sumayya tace yasa khadija sunkuyar da kai, ta fice a falon da sauri ta nufi igiya ta dauko hijab nata, tayi get, tana bude get in aiko kamar yanda ta zata inne Kalamu na tsaye, kai lafiya tun a falo sai ketket-ta mini ido kake? Wallahi khadija magana nake so nayi dake daman. Da mamaki da kallesa au yau kuma kunyar Aunty kake ji kome? Ah ah ba haka bane kinsan next week zamu fara exam? so bazan samu daman shigowa ba shiyasa na kawo miki wannan, yace yana mika mata bakin laidar dake hannunsa. Ba musu khadija ta karba hade da tambayar sa menene a ciki? Wayace harda sim, na miki register sai muna gaisawa daidai na samu zama, don zan kwana biyu gaskiya bazan leko ba? Kaga karbi abinka wallahi babu ruwana? Kamar yaya ba ruwanki khadija? Kamar yanda nace maka, so kake Aunty taga rashin kyauta wata gareta? tayi mini dukkan kyautatawa baika mata na nuna mata rashin godiyan Allah ba. Yanzun khadija karbar wayar ce rashin godiyan Allah? Kayi hakuri Amma bazan iyya karba ba sai dai in zaka kaiwa Aunty da kanka ka bata? Babu damuwa muje na batan. Ah ah wallahi ka fara zuwa dai kaikad'ai kar tace mun had'a baki, tana maganar ta koma cikin compound in tana tattara shanyar ta. Ba musu Kalamu ya koma kofar sumayya, da mamaki take tambayar sa lafiya kuwa ya dawo?bayani ya mata akan waya ya baiwa khadija taki karba shine ya kawo mata koh khadijan zata yarda ta karba? Da mamaki sumayya ta karbi wayar ta bude, wayane sumsung Galaxy S9+" Kalamu nima karan kaina nayi tunanin saya wa khadija waya, Amma nafi son saita kammala secondary ta mallaki hankalin kanta" Aunty yanzun ma khadija tayi hankali fa, shekara 19 take nema wasu a shekarun tan nan ma, suna jami'a don Allah aunty ki barta ta rike wannan in? "Au haka ta fad'a maka kenan bazan barta ta rike ba, kuka had'a baki kazo waje na koh"? Ah ah aunty kawai dai na fahimci khadija nada biyayya ne. "Shikenan Allah ya sanya Albarka, harda shekarunta ta fad'a maka kenan"? Ameen Aunty Amma nidai kiyastawa nayi bata fad'a mini ba, yace cikin murna ya fita ganin Aunty ta karbi wayar, yana fita a falo yakusa cin karo da khadija dake makale a kofar falo tana sauraron su, cikin murna tace Aunty ta yarda? Kai kawai ya d'aga mata ya wuce get ya fita, Khadija kam kasa komawa cikin falon tayi, taci gaba da tsayuwa a bakin kofa. Sumayya dake jiran Khadija ta shigo, shuru shuru bata shigo ba, yasata mikewa fuska a had'e ta nufi kofar falon....... ************* Jikin muhammad sai rawa yake yaje ya karbo wasu kayan, ya karbo sabon shayi, ya sake shigowa falon wannan karon tsohowar ce da yara biyun, wanda d'ayan bai manta sunan taba muhibbat sai karamar , gaida tsohowar yayi ya wuce falon sarki, Wannan karo sarkin baya falo yana ciki, aje masa shayin yayi a table ya tsaya a gefe, kusan 30 minutes kafun ya fitoh yauma kamar kullum fuska a rufe,, a take gaban Al'ameen ya soma bugawa da karfin gaske, zama sarkin yayi a hankali akan d'aya daga cikin kujerun falon, da sauri Al'ameen ya dukar da kansa a hankali ya matso da table in ya siyaye masa shayi hade da gaidashi, hannu kawai sarki ya d'aga masa ba tare da yayi magana ba. Yana gama had'a shayin, ya fita a falon, direct kitchen in shayi ya koma, yama abokan aikin sa sallama duk da lokacin tashi baiyi ba, ya kama hanyar gida, cikin hanzari yake tafiya har ya iso bakin titi tare abin hawa yayi. Yana isa gidan cikin hanzari ya bude kofa bakin sa d'auke da sallama, baikara saba sallamar ya makale masa a wuya, ganin baba tsaye akan kafafunsa........... ✨Ruqeenjalal✨ [10/24, 2:18 PM] +234 903 356 9641: 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya* *Ibrahim* 🍃 Page8⃣6⃣&8⃣7⃣ Babane tsaye akan kafarsa yana gyara yayin dake kan bukkar sa, da mamaki Al'ameen yace ikon Allah baba menake ganin nan? Da sauri baba ya juya da mamakin ganin Muhammad ya dawo daidai lokacin nan, Alhalin ba lokacin ake tashi aiki ba, lafiya ka dawo yanzun? Kai zan tambaya dai baba, na ganka tsaye akan kafafunka, kaida ka karye? Zoka zauna muhammad muyi magana?yace yana zama akan taburma. Ba musu Al'ameen ya zauna a kusa da baban. Muhammad ina fatan kaga abinda nake so ka gani koh? Da sauri Al'ameen ya warware rawanin sa, kamar ya baba kuma me kakeso na gani? Muhammad Abinda yasani yin haka badon kome bane, illah don naga kaje da kanka gidan sarkin nan, tunda na ganka jikina ya bani wani abu, kamar dake tsakanin ka da muhibbat da muwaddat ya baci sosai, haka sarki ma duk da rabona dana ga fuskar sa, bazan iyya tuna ranan ba Saboda dadewar da nayi bana gani, Amma fa ka sani nasan sarki tunkan yahau mulki, yanda kaga fuskar ka, haka fuskar sa yake sai dai ka nuna masa yaranta? Me kake nufi baba bangane ba, wai sarkin da naga fuskar sa a rufe kana nufin yana kama da yara biyu dana gani innan? Kwarai muhammad duk da dai akan samu mutum, ya samu mai kamar sa a duniya Amma kaman ku dasu Akwai alamun jini. Baba ni bani da kowa a nijar fa bansan kowa a nan ba. Toh Amma kaman nin ku, ku hudun nan yayi yawa muhammad? Bamu hudu bane mu biyar ne, da kanwa ta. Muhammad niba yaro bane, Amma tunda kace haka shikenan, amma dai zaka cigaba da zuwa aiki har lokacin da na yanke akan zancen kafata, tunda ba kariyar gaske nayi ba baikamata na koma ba yanzun? Shikenan baba zan cigaba da zuwan,har randa zaka koma aikin, ina su gidado ne tunda na shigo ban gansu ba? Sunje kasuwa yi mana sayayyan kayan abinci. Tashi muhammad yayi ya ibi ruwa ya shiga band'aki wanka yayi ya shige d'aki ya kwanta, tunanin duniya ya dame sa, duk sanda ya lumshe idanunsa yaran nan yake gani wanda baba yace masa muwaddat da muhibbat wai suna kama da sarki, kenan suna kama dashi, kai shikam bai gane kan Al'amarin nan ba, wani zuciyar na kawo masa wani tunani, amma kokarin tunkude sa yake don yasan abune da kamar wuya. Yana kwance har gidado da badaru suka dawo kasuwa, yana jinsu suna ta girki da jido ruwa Amma bai koh fita ba. Har suka kammala aikin dare abinka da gidan gauraye, bayan sunci abinci suka wuce masallaci. Daren nan sukutum muhammad baiyi bacci ba, sai kusan asuba bacci ya d'auke sa. Washe gari muhammad yaje aiki kamar jiya bayan sun gama shayin safe, yaukam had'a masa akayi da yawa a tire, ya wuce dashi falon , da sallama ya tura kofar falon ba kowa a falon sai kamshin turare dake tashi aka tsakar falon, wucewa falon maimartaba yayi a hankali ya tura kofar da sallama. Sarauniya ce cikin Alkimba a zaune akan kujera hannunta dauke da kumshen lalle ja abinka da farar fata sosai yayi kyau, sai sarki dake kujeran sa na special kamar kullum fuskar sa a rufe, sai muwaddat da muhibbat dake zaune akasan kushin sai tsohowar nan dake zaune a kujera tana magana da nabila, ke nabila nafa fahimci babu wanda ya bata ku sai lawiza(sarauniya) ace mutum ya dage sai yayi turanci abinda bama amfani muke dashi anan ba? Kai mahmah karfa ki manta a abroad nake karatu kuma ashan basu san wani abu wai French koh buzanci ba, da turanci kawai ake Amfani kinga kuma nan gaba muwaddat da muhibbat suna gama secondary suma chan zasu, shiyasa nake saba musu tun a gida mahmah, nabila tace. Murmushi sarauniya lawiza tayi tana kallon mijinta da kwata kwata hankalinsa baya wajen su, hankinsa bama a wajen su yake ba, hawaye ne ya cika mata ido, ta rasa yaushe ne ita da yaranta zasu samu lokacin sa? abu tsawon shekaru abu d'aya, tun yaransa na kanana suke korafi har yanzun sun girma har yabi jikinsu, Abban muwaddat......bata karasa ba sukaji sallamar muhammad. Amsa masa mahmah tayi, ya karaso cikin falon yana gaidasu da turanci lawiza da su muwaddat ne suka amsa sarki kam koh d'ago kansa baiyi ba bare Amsa gaisuwa, mahmah kam baki ta kama sai kuma tayi shuru batace kome ba. a kan table ya aje shayin ya siyaye a kofuna yazo ya aje musu, yana kokarin tashi saiga wasu zaratan maza sun shigo falon cikin sallama, maza ne guda biyu d'ayan zaikai shekara 40 d'ayan kuma zaikai 33 zama sukayi akan kujerun falon suna gaida mah mah da buzanci bayan ta amsa suka juya wajen sarki sauka gaidashi hannu kawai ya d'aga musu. uncle Ango, nabila tace tana dariya Hararan ta mai shekara 33 yayi ke wallahi bana wasa dake? zan saba miki fa. Dariya muwaddat ta sake kai uncle jiya mafa aunty Amarya tazo school namu, ta kawo mana special Anko in mu na yaran Ango. Ganin bakin yasa muhammad siyaye musu shayi suma, don shidai duk hiran da suke baji yake ba, kasancewar da yare suke magana, yazo ya jera musu a gaba, har zai mike kawai kafarsa ya taka na nabila, ai da sauri ta mike cikin masifa, kai wallahi kaji na rantse maka ka fita idanuna, kai wani irin masifa ne,haka kawai kabi ka sani a gaba da fitina tunda ka fara aiki a gidan na kake takalata tun jiya? Kiyi hakuri don Allah bada sanina bane, muhammad yace da sauri yana matsawa gefe duk da sumayya ta masa rashin mutunci a farkon zamansu, Amma bata taba masa a cikin mutane ba, koh zata masa masifa sai insun kasance su biyu, amma wannan a gaban sarki take masa zagi haka bataji kunyar mulki ba? a take yaji wani irin tsanar yarinyar. Ke nabila matsalata dake kenan rashin hakuri da rashin kunya, d'aya daga cikin mazan ya fad'a yana mamakin rashin kunyar nabila Gaskiya nabila halinki sai Allah ace ke a rayuwar ki rashin kunya ne baya baki kunya a gaban Abba kike irin wannan tsewar kamar ba sarki bane a gaban ki? Kunya ne ya kamata da sauri ta sunkuyar da kanta kasa, cikin sanyin jiki ta fita a falon, muhammad ma hakuri ya kara basu ya fita, yana fita yaga nabila tsaye alamu dai shi take jira. Wallahi wallahi in baka fita idanuna ba zan maka rashin mutuncin da ba'a taba maka ba, matsiyaci kawai shashasha duk cikin turanci take maganar. Kala muhammad baice mata ba ya nufi kofa, sai masifa take Amma shi koh juyowa baiyi ya kara ganinta ba, yana gaba tana baya har suka fitoh a flat in sarki ta shiga nasu, muhammad kuma ya wuce sashen shayi. ***************** Sumayya na bude kofar falon khadija ta gani tsaye da kaya a hannu, da mamaki tace"tsayuwar me kikayi a nan kuma, kika kasa shigowa koh rashin gaskiya ne"? Ah ah aunty yanzun nake kokarin shigowa. "Aiko kwara ki shigo inkam" tace tana koma ta zauna a kan katifa. A hankali khadija ta karaso falon kayan dake hannunta ta kai d'aki, sai kuma ta makale taki fitowa gabaki d'aya fargaba ne a Ranta, ganin fuskar sumayya a hade. "Khadija wai tsayuwar me kike a bakin kofar nan ne da bazaki shigo falon ba"? A hankali ta shigo falon tana rabe-rabe a jikin falo a nesa da sumayya ta tsaya. "Waike khadija meye haka? zama zakizo kiyi muyi magana" Kiyi hakuri Aunty wallahi ni bansan da maganar wayar nan ba, kawai sai naga ya bani shine fa danaki karba ya shigo falo. "Nidai bance kome ba nace kizo ki zauna muyi magana" A hankali ta matso ta zauna a bakin katifar. Kallonta sumayya tayi "menene tsakanin ki da kalamu-wahid"? Wallahi Aunty babu kome a tsakanin mu dashi kawai fa mutunci muke, kuma aunty koh soyayya zanyi sai nayi da d'an yaron nan? "Oh yaro koh lalle kam waya gaya miki ba'a auren yaro ai da ba'ayi da bazan aure yayanki ba" Kai Aunty yayana fa ya baki shekaru 4 rus fa, Amma kalamu bazai girmeni da 2 years bama. "Kwadaiji dashi wallahi ina nan ina zuba ido, kuma ga wayar taki saiki rike, tace tana mika mata kwalin wayar" Amsa khadija tayi da sauri ta ruga d'aki da gudu tana murmushi don wallahi ba karamin son waya take ba. "Khadija dawo nan" Jin abinda sumayya tace yasa khadija dawowa ta zauna. Kinga khadija waya a zamanin nan cikin kaso goma ya kwashe kaso 7 na hanyar lalacewar yara, sauran 3 nan sune ake amfanuwa, ki kula da wayar nan ban baki ita don kiyi abinda ranki yake so ba, kinga waya sirrin mutum ne wani bazaka taba tunanin koh yatsa aka saka masa a baki zai tauna ba, Amma in aka amshe wayarsa abinda za'a gani bamai kyau bane?na barki ki rike wayar nan ne saboda kalamu Amma ki rufamin asiri ki ji tsoron Allah ki kiyaye shiga inda bai dace ba" Insha Allah aunty zan kiyaye. "Yauwa sannan zaki iyya hawa online Amma ban yarda ki d'aura hoton ki ba sam banaso" in Allah ya yarda Aunty "Toh tashi ki tafi d'akin" D'akin khadija ta shiga ta had'a wayarta daman oready ya saka mata wayar a cherge, ya saka mata sim suka, tana kunna wayar aiko ta shiga latsawa, ya sauke mata facebook whatsApp da instagram harda telegram duk ya bubbude mata account, call ne ya shigo wayar da sauri tayi picking ganin rubuta daya bayyana Nurul-Qalbi a screen in, tana d'agawa taji yayi sallama hade da kiranta da kanwar sa. da masifa ta fara magana, Allah ya sauwaka ka zamo yayana wallahi wane kai kaji na fad'a maka. Shuru yayi bai mata magana ba, jin baiyi magana ba yasa ta dawowa hayyacinta cikin kunya ta Amsa sallamar, tana masa godiyan waya daya bata. baiyi magana ba har lokacin, ita ma shuru tayi kamar yanda yayi,sai da yayi minti biyu yace mata ta hau whatsApp ya mata messenge. Kashe call in tayi ta hau whatsApp ganin akwai enough card a wayar. Khadija kamfa gabaki d'aya yau waya ya d'auke mata hankali sosai, tana gama girkin ta, ta nuke a d'aki sai hira suke da kalamu, Abin har yaso bawa sumayya dariya daga zaran khadija taji motsen zata shigo d'akin saita kifa wayar ta kama baccin karya, Amma batace mata kome ba tunda yanzun hutun makaranta suke, sai kalamun yazo zata masa fad'a maganar karatunsa karya biye shashanci. Ranan fa khadija a d'aki tayi shimfida a kasan tiles ta kwanta da waya a hannu, sumayya ita kad'ai ta kwana a falo. *************** Yau kwanar muhammad 25 yana zuwa aiki gidan sarauta, zuwa yanzun ya fara fahimtar Halin mutanen gidan sosai, especially nabila ba karamin haushin yarinyar yake jib, bad'an kad'an ba, yau tun Asuba yayi wanka yabar gidansu, kasancewar yaune za'a fara bikin kanin sarki(Ramadan) kamar yanda yaji ana fad'a, shiyasa tun asuba zasu tafi aiki, don shirya shayi mai yawa da zai d'auke mutanen biki zasu wuni sha, duk lokacin da aka nemi shayi a samu kar ya kasance babu, aiko hakance tun safe da sukaje basu zauna ba daman har yanzun ba'a sakar ma muhammad hannu ya girka shayi shi kad'ai ba, anfi sashi ya rarrabawa mutane. yau haka ya wuni aiki saiya kaiwa flat innan yana dawowa a bugo telephone in kitchen ace yakai shayi, gabaki d'aya yayi mugun gajiya. Haka muhammad sukayi ta fama da aiki har na tsawon kwana 4, sai yau aka d'aura aure, da misalin karfe 4 na yamma liyafa aka had'a a tsakar farfajiyar gidan, manyan sarakuna da manyan kasa ne makil a ciki, masu kudi da shuni, tunda aka fara bikin sarki bai hallaci koh wani liyafa ba sai d'aurin aure da wanda yanzun ake, muhammad ne ya karaso filin yana raba shayi koh wani table yana aje musu nasu dayake taron na mazane da mata, kuma tarone na manya yasa Al'ameen yake bin kome sannu sannu karyayi kuskure koh laifi, kwala masa kira nabila tayi ganin ya wuce table nata da suke xaune da kawayen ta, bai aje musu shayi ba zai tafi next table, kai malam bazaka kawo mana namu shayin ba!! Cikin haushi yazo zai dongora mata shayin a gaban table inda suke, by mistake kafarsa ta harde da cafet inda aka shimfid'a a kasa, kawai shayin ya watsale sai jikin kawar nabila, ihu kawar ta saka wanda yaja hankalin jama'a, ai nabila na ganin haka batayi wata-wata ba ta tsinke muhammad da mari. Kafun ta sauke hannunta muhammad ya bata wasu tagwayen mari hagu da dama, masu masifar zafi ihu da sake cikin azaba don a tsawon rayuwar ta bazata iyya tuna lokacin da aka bugeta da wayon taba. Yayan nabila dake gefen su ne ya mike cikin zafin nama ya d'aga hannu zai wanke Al'ameen da mari, da sauri Al'ameen ya cafke hannunsa cikin matsanannin cin bacin rai ya nuna mustapha da yatsa, jikinsa har rawa yake cikin kakkauran murya yace karka kuskura ka tabani.. Ai bai karasa maganar ba Ramadan(Ango)daya karaso wajen don abin sosai yajawo hankalin jama'a ganin mai aikin gidan sarauta ya mare yar gidan, cakumo kwalar muhammad yayi cikin zafin nama hade da kai masa naushe a fuska, da sauri Muhammad ya kauce a zafafe wanda yayi sanadin yagewar kwalar rigansa da ramadan yake rike dashi. A take Ramadan ya ja da bawa tare da kwalo ido waje, jikinsa har rawa yake yana nuna wuyan Al'ameen, sai kuma cikin sauri yasa hannu akan rawanin fuskar sa zai............ ✨Ruqeenjalal✨ [10/24, 2:18 PM] +234 903 356 9641: 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya* *Ibrahim* 🍃 Page8⃣8⃣&8⃣9⃣ Da sauri muhammad ya damke rawanin sa, ya hana Ramadan bude masa fuska, menene haka? banaso karka kuskura ka bude mini fuska. Har lokacin jikin Ango rawa yake cikin mamaki yace a ina ka samu sarkan nan, waya baka wanene kai?da karfi yace security. Jama'an gurin duk sun mike banda sarki dake zaune akan kujera duk rikicin da ake baiko d'ago kansa ba bare yasan abinda ke faruwa. Mustapha ne yayi magana a rude wallahi sarkan ne, sarkan magadan masarauta ne, a ina ka samo sarkan nan?yana maganar yana kai hannunsa wuyan Al'ameen zai duba sarkan. Da sauri Al'ameen ya buge hannunsa, Shuru yayi yana kokarin barin filin, da sauri Ramadan ya jawo sa baya yana kwalawa Yayansa kira, da sauri sarki ya juyo yana kallon Ramadan da mamakin kiran gona da yake masa? Yaya sarkan magada ne a wuyan wannan me kawo shayin, kuma yaki bari aga fuskar sa, bamu yarda dashiba suspect ne? Ai kafun ma ya gama magana saiga sarki ya sauko a kujera da hanzari ya nufi inda suke tsaye, daga isarsa hannu yasa a kamo sarkan yana kallo sai kuma jikinsa ya fara rawa ya kamo rawanin fuskar muhammad. Da sauri muhammad ya dafe Hannun sarki dake kan fuskar sa yana girgiza masa kai, alamun rashin son hakan. Shima sarkin girgiza kai yayi, hakan yasa muhammad sauke Hannunsa akan na sarki. A Hankali yake warware Rawanin kansa, tsaf gashinsa ya bayyana mai masifar tsawo da sheki, a hankali ya warware na fuskar sa, da sauri ya dafe kirjinsa cikin tsananin mamaki da sauri yace muhammad!!!!!bai karasa ba kawai hancin sa ya fara tsiyayo da jini a hankali ya fara lumshe ido sai kuma ya yanke jiki zai fadi, da azama muhammad ya taro mahaifinsa da sauri ya rungumi abinsa cikin matsanan ciyar mamaki jin sarkin ya Ambace sunan sa. Zuwa fadawa sukayi aka kewaye sarki muhammad ne ya ciccibi sarki har cikin flat nasa, atake gida ya rude da koke koke, ga masu tsananin mamakin muhammad da abinda ya had'asu da sarki harya Ambace sunan sa? Bayan Ankai sarki d'aki likita da abokan aikinsa suka rufu a kansa, yayinda Ahlin gidan ke make a babban falon fada, daga maza har mata harda wa'inda muhammad bai taba ganinsu ba, mikewa yayi zai fita a falon da sauri Mahmah ta riko hannunsa, ina zaka yaron nan? Gidan mu mana ba aiki bane ya kawoni mama?yace yana kallon nabila dake rakube a jikin kujera fuska jajjawur ga jini ya taru a idanunta da gani dai ta maru. Wani irin ka tafi kuma kaje ina baka ga Halinda d'ana yake ciki ba? kuma na tabbata yana farfadowa kai zai nemi gani.da gorancen hausar ta take magana. Toh ni kuma so nake na tafi gida ranki ya dade, in Allah ya kaimu gobe ai zanzo aiki duk maganar da zamuyi sai muyishi? Ramadan ne ya mike,Hala nan dajine da bazaka iyya kwana a cikiba? Ban saba kwana gida irin wannan ba, kasa bacci zanyi, yace yana fita a falon babu wanda yayi yunkurin hanasa, sai rakasa da ido sukayi. Muhammad na zuwa gida gabaki d'aya abin duniya ya damesa, amma baicewa baba kome ba, shima baiyi magana ba duk da yaga sarkan wuyan Al'ameen Amma baice kala ba. Yau koh abincin dare kasa ci yayi, badaru da gidado ne sukaci gabaki d'aya jikinsa yau A sanyaye yaki kome yanayi a sake kamar mai ciwon fata. Har dare bai rumtsa ba, tunani kawai yake a ransa, donshi dai bai gane inda abinnan ya dosa ba, menene Alakansa da mutanen nan shi zaman kasar ma ya isheshi kuma ya rasa hanyar da zaibi yabar kasar gabaki d'aya, yau wani irin kewar iyalinsa yame dason jin duminta, ba irin tambayar duniya dasu gidado basu masa ba Amma bakome yake ce musu. Da misalin karfe 2:30 sukaji ana bugun kofar gidan, babane ya fita zai duba koh lafiya yayinda muhammad ke kwance duk da idanunsa biyu Amma bai mike ba. Baba bai jima da fita ba sai gasa ya shigo d'akin su muhammad, mikewa yayi yana kallon baba. Muhammad ka fitoh ana sallama dakai? Da mamaki yace dani kuma baba, sallamar ma tsakar dare? Ka tashi daga gidan sarautane. Gaskiya baba kace musu su bari sai gobe, koma menene in gari ya waye sai ayi bawai a tadani tsakar dare ba kamar tashin duniya. Muhammad yaushe ka koma mara kunya ban sani ba? Kayi hakuri baba Tashi kawai kaje kaji da wani sako aka turosa? Mikewa yayi kawai ya sanya kayansa ya fitoh a d'akin, kallon mutumin da aka aiko wajen sa yayi, lafiya malam? Lafiya muhammad ana neman ka a fada. Tsakani da Allah in Ana son ganin mutum sai azo tsakar dare ya kirasa ai naga gari zai waye? Babane ya kallesa, muhammad ka iyye bakinka banason irin wa'innan kalami, bai dace da kai ba, don haka ka bisa kuje bakasan menene dalilin kiranka ba, ya kamata kaje kaji. Baiyi magana ba kawai ya nufi hanyar kofar gidan, binsa a baya mutumin yayi daman da mota yazo ba musu muhammad ya shiga suka wuce. Daga isarsu masarauta gidan kaman rana koh ta ina fitilune haske kaman farin wata, ga mutane a tsatsaye kamar rana bakin dake gidan duk basu tafi ba, Al'ameen na fita a motar gabaki d'aya aka ringa binsa da ido har suka ratsa babban falon sarki, suna shiga mahmah da lawixa harda su ramadan muwaddat nabila duk suna cike a falon wasu kamma kuka suke fuskar lawiza da mahmah jazir alamu kuka sukasha, da sallama ya shigo falon amsa masa sukayi suna mikewa tsaye gabaki d'ayansu, binsu yayi da ido sai kuma ya nufi kofar d'aya falon, ya shiga yana shiga duka suka rufa masa baya zuwa ciki, tunda ya tinkare kofar bedroom yake jin salati ga sunan sa da ake kira da sauri ya cusa kansa adakin. Sarkine kwance akan gado yana tari jini na biyo bakinsa yana Ambatun sunan muhammad, ai Al'ameen baisan lokacin da yayi super ba ya isa garesa koh tsawon shekaru nawane bazai taba manta wannan fuska ba bare shekarun da baiwuce a kirgasu ba, hawaye ne ya cika masa ido ganin halinda mahaifinsa abin sonsa ke ciki, duk da ya rayu da takaicin gudunsu dayayi Ya kuma sha Alwashin duk randa ya gansa zai basa mamaki shima, amma bai d'auka zai gansa a irin wannan halin ba, karasawa yayi garesa a hankali ya kamo hannayensa dake dafe a kirjinsa cikin kuka yace Abbajoooo!!!me nake gani haka ka rufa mana asiri kar maraicin ya mana yawa? Ai jin muryar sa da sauri yusuf ya mike ya rungume d'ansa a zaune, tunda ya hau karagan mulki ba'a kara ganin hawayen saba sai yau, hawaye ne yake siyaya a idanunsa, ganin haka yasa muhammad fashewa da kuka mai matukar karfi yana banbare Abbajon sa a jikinsa, tare da kallon doctor dake gefe, habba bawan Allah jini nefa kebin bakinsa kun barsa haka? Kayi hakuri yallaboi wallahi tun da ya farfado anyi anyi ya tsaya a basa taimako yaki gashi ciwonsa baison damuwa Amma yaki ya saida hankalinsa. Jin haka yasa muhammad kokarin mikewa tsaye,Ai da sauri yusuf ya rikosa da karfi tamkar uwar da za'a rabata da jaririnta, fuskar muhammad ya rike sai kuma ya soma magana a hankali, tabbas jini yafi ruwa kauri, babu tantama wannan jini nane muhammad nane koh babu sarka a wuyanka akwai alamun jini muhammad ku yafe mini. Ah ah Abbajo ka rufa mini asiri karkace haka kayi hakuri ka rayu damu yana magana yana kuka. A hankali sarki yace muhammad dukkan mai Rai mamaci ne in lokaci yayi dole mu amsa kiran mahalincin mu. Don Allah Abbajo kabar irin wa'inan magana, likita kazo ka taimaka masa, da sauri likitan ya maso da taimakon muhammad suka gogi masa jinin dake bakinsa ya taimaka masa ya shiga toilet ya shanja kayan daya baci, daidai ya fitoh har muhammad ya sauya zanin gado. Yana fitowa ya kwanta likitan ya d'aura masa ruwa da Allurai ya fita, a hankali yusuf ya kama hannun d'ansa sosai ya zurawa muhammad ido yana kara tasbihi a zuciyar sa yaushe yabar muhammad yaro karami d'an shekara 13 Yau shine ya zama cikeken mutun tamkar shi a lokacin da ya barsu muhammad?badon shekaru ba koh yau duk wanda yaga muhammad zaice shine. Na'am Abbajo. Ya Aishan Adara? Jin tambayar da ya masa sai da gaban sa ya fadi, a halinda mahaifin sa yake cikin nan bai kamata ya kara d'aga masa hankali ba, cikin sanyin jiki yace, Tana Lafiya Abbajo. Murmushi yusuf yayi cikin karfin hali, nasan xuwa yanzun ta rage masifa koh? nama san itama ta tsufa kamar ni? Hhh bata tsufaba tana nan da kyawun ta daka sani, kuma yanzun sam bata fad'a da kowa. Ah ah muhammad fadi gaskiya dai nasan maman ku, saidai in ba'a bata mata rai ba? Dafa gaske nake. Ta yafe mini? Babu abinda ka mata abbajo asalima ita ke neman yafiyar ka, don gaskiya yayi halinsa bayan bakai, meyasa Abbajo kayi fushi ka tafi ka barmu, kana rayuwan ka cikin mulki da kudi mukuma baka damu da kalar rayuwar da muke ba? Girgiza kai kawai yusuf yayi baibawa muhammad Amsa ba, ya sake jefo masa wani tambayar, ya jikin salim nasan zuwa yanzun kam yagirma don zai fika jiki kasan jikin mamanku garesa? Kwarai ma kuwa abbajo salim ya warke sosai sai godiyan Allah. Su lawiza da suka jima a bakin kofa suna kallon ikon Allah wai me yusuf yake nufi da yaron nan ne basu gane ba, kasa magana sukayi ganin kamar ma basu san da zaman suba sai hira suke, hakan yasasu juyawa suka fita a d'akin ganin lokaci d'aya jikin yusuf yayi sauki gashi sam ba hausa suke ji sosai ba, duk da su mazan suna hausa tsabanin mata da kwata kwata bayi suke sosai ba sai jifa jifa, Haka yusuf da muhammad suka ringa hira na yaushe gamo, Amma sam muhammad bai fad'awa yusuf mutuwar Aisha ba koh salim, sai asuba da sukayi sallah doctor yazo ya cirewa yusuf laidan ruwan, suka kwanta tare a Royel bed na sarki bacci ya d'auke su. ************** Sumayya ciki ya shiga wata bakwai yanzun sosai tayi wani irin kumbura, har yakai yanzun bata iyya tashi da kanta sai khadija ta kama hannunta ta jata da karfi saboda nauyin cikin, abincin ma yanzun bataci daga ruwan zafi sai tie koh nama. Kalamu-wahid da khadija yanzun kam an dinke sosai suka shaku kalamu na zuwa gidan sumayya akai-akai gashi yanzun har kwaryan tuwo yake dashi akofar sumayya na rana,kamar yau sumayya ta gaji da kwanciyar da khafija keyi a kasan tiles hakan yasa ta kiran ta hade da mika mata kudi taje ta sai karamin katifa, Amsan kudin tayi tace bari tayi wanka. Tana shiga d'aki messenge ta turawa kalamu akan zata fita, kafun ta shiga wanka. Tana fitowa shiryawa tayi ta fita da niyar tafiya kasuwa, tana nufar get ta bude da murmushi a fuskar ta ganin kalamu tsaye sanye da jamfa wando da riga yayi matukar masa kyau abinka da bakin mutun sanye da farin kaya, mota ya bude mata ta shiga shima ya zagaya ya shiga yaza suka cillah kasuwa. Duk yanda yaso ya saya mata katifa da kudinsa taki yarda, yace zai cikimata ta d'auki babba, amma taki tace aunty zatayi hulo itakam babu ruwan ta. Tare suka dawo kasuwa ya sauketa a get nasu, ta shiga da katifar ta da kanta don tace karya shigo kar aunty ta mata fad'a, sunje kasuwa dashi bada izininta ba, ba musu shima ya shige gidansu bai matsa mata ba. Bayan isha'i sumayya ne kwance a falo, yayinda khadija na cikin daki suna hira da kalamu a waya, kamar a mafarki taji sallamar sa a bakin kofar falon su, da sauri ta mike zaune tana mamakin sa na rashin fad'a mata yana zuwa Alhalin kuma waya suke da juna yanzun, kalamu!!!! Ta cikin wayar taji yace ke don Allah fitoh ki bude mini kofa. Ba musu ta fitoh a d'akin kallon sumayya dake falo a kwance, tana bude kofar ya shigo gaida sumayya yayi ta Amsa masa sama-sama don yanzun koh yawan magana bata so. Aunty daman wajen ki nazo? "Khadija basa wajen zama" Zama yayi akan kushin da khadija ta aje masa, itama ta koma gefe ta zauna. Aunty daman nace mezai hana khadija ta shiga islamiyyar mu ?nayi magana da ita tace nini tun saukar ta na farko bata kara komawa tushi ba. "Gaskiya ne kalamu koni ina son khadija ta koma islamiyya, nama laila magana akan koh akwai islamiyya a kusa, shine tacemin yaranta babansu ke koyar dasu, ni kuma bana son khadija taje wajen sa d'aukar karatu" Gaskiya ne Aunty kinga kuma zuwan weekend ne aje 3 adawo 5 ? "Shikenan kalamu sai Allah ya kaimu next week sai na had'aku ka kaita don ni ba iyya taka kafar nake sosai ba" Eh aunty daman na kammala mata kome yanzun ma uniform na kawo mata da form sai a cika mata sati mai zuwa ta fara zuwa. "Lallai ma kalamu toh Allah dai biya ka" Ameen ya Amsa yana kallon khadija dake murmushi a boye. "Yauwa kalamu daman akwai abinda nake son na fad'a muku kaida khadija"? Zuciyar suce a tare ya buga da sauri suka kalli juna sai kuma suka juya suka kalli sumayya har suna had'a baki, Aunty Allah dai yasa lafiya?? "eh daman akan kune, ba kome bane illah abu d'aya zuwa biyu, ina so daga yau.............. ✨Ruqeenjalal✨ [10/24, 2:18 PM] +234 903 356 9641: 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya* *Ibrahim* 🍃 Page9⃣0⃣&9⃣1⃣ "Daga yau banason kara gani koh jin ka kira khadija a waya yafi sau biyu a rana, na gaji da halinku kunce ba soyayya kuke va ?sannan kai bakada aiki sai kiranta karfa ka manta kai d'alibin kiwon lafiya ne, bai kamata kana wasa da karatu ba"? Insha Allah Aunty za'a kiyaye. "Sannan ke kuma khadija kinga dai kokarin shiga ss 2 kike, kuma niyata in kika dage saina miki registration in waec next year, amma tunda wasa zaki saka a ranki bismillah zakiyita zama har 21 years a secondary" Shap wayaga maman aji, kalamu yace yana dariya. "Kaga banason shashanci kalamu, ina muku fad'a kana sako wasa" Sorry Aunty zamu kiyaye yace yana kallon khadija, ke akwai sauran shinkafa ki zubamin yau nanne na tuwo ta dafa? Babu kawai khadija tace tana mikewa ta shiga daki. "Kaga kalamu tashi akwai macaroni data dafa a tukunya kaje ka iba tunda kitchen in ba bakon ka bane, karku dameni da surutu kaina ciwo yake". Mikewa yayi ya shiga kitchen in ya ibo makaroni da miyar kifin gesha, yana ci yana latsa wayarsa don yanzun sumayya bata surutu kamar da. ************* Muhammad basu farka ba kuma ba'a tadasu ba sai kusan 10 na safe suka farka don kansu, wanka sarki yayi sosai yaji sauki jikinsa yayi karfi, kaya ya saka muhammad ma wanka yayi yasha jumfa da aka kawo masa mai masifar kyau da tsada, abincin karyawa aka jera musu a daining tare suka karya su biyu suna hira gwanin sha'awa, a hankali sarki yace muhammad wai nikam ban tambaye ka kaninku ba? Wanne kenan Abbajo? Kanin salim mana. Ai macece khadija tananan. Allah sarki yanzun fa shekarun ta 18 da wata 9 ta kusa 19?nasan itama yanzun ta kusa nabila koh? Eh Abbajo ta girma abinta. Allah ya raya mini ku ta farkin islama? Ameeen, haka suna ci suna hira har suka gama yusuf ya gyara rawanin sa yana rike da hannun muhammad sukayi fada. Ana bude musu kofa suna shiga saida gaban muhammad ya fad'i, ganin wasu jajayen buzaye, cikin su harda baba da gidado da badaru a zazzaune, sosai fadar ta cika makil da manya da yara alamu dai yusuf yasan da taron, sake hannun muhammad yayi ya zauna a kujeransa yama muhammad nuni da kasan cafen. Ba musu muhammad ya zauna a hankali, yayinda mutane kibinsa da kallo na mamaki sosai. a hankali yusuf yasa hannu ya ja rawanin fuskar sa, take fuskar nan mai kamala da dattako ya bayyana koh yaransa basu samun ganinta a araha irin na yau, kowa na kasa yusuf ne kawai a kujera. Gyaran murya yusuf yayi, Asslamu Alaikum warahamatullahi wabarkatuhu. Gabaki d'aya jama'an dake falon suka amsa masa sallamar. Na gode Allah daya nuna mini wannan rana, wanda ban taba tsammanin ganinsa nan kusa ba, koh ince ban taba sa ran ganinsa ba,Ayau xan sanar daku yan uwana don duk fadar nan yan uwana ne in aka cire mutane uku,ayau xan sanar daku abinda nasan dayawan cikin ku zasuyi mamaki, muhammad Al'ameen, d'aya daga cikin masu aikin gidan nan D'anane, kuma shine a gabana. Gabaki d'aya falon ya d'auki surutan mutane, daker aka samu ya lafa, yaci gaba da magana, nasan dole jama'a zasuyi mamaki Amma banda mahmah mahaifiyata, don ita tana d'aya daga cikin mutanen da suka san da wannan magana,mahmah ya kira sunan mahaifiyar sa dake xaune a gefe. Na'am . A taushashe yace, Mahmah ina son ki sanar dasu Asalin abinda ya faru shekarun baya da suka wuce, bani da koshin lafiya sosai kuma inbabu damuwa ina son kiyi da hausa wa'inda basa ji, Ramadan yana fassara musu. Gyara zama mahmah tayi ta fara magana kamar haka. *SHEKARUN BAYA DA SUKA WUCE* Masarautar karfe shine cikekken sunan masarautar gidan nan, wanda ke d'auke da tambarin zaki ya samo asaline tun bayan shekaru da suka shude, ka'idar masarautar ne duk yarima mai jiran gaso za'a makala masa sarka na magajin masarauta, sarkane daya samo asali daga makafan masarauta, duk wanda ya d'aura sarkan badai tsafi jifa koh tsibbo ya kamasa ba saida ikon Allah. mutallaf shine cikekken sunan mahaifin yusuf, a lokacin sarki ne yana da matarsa ta farko mai suna Hauwa-kulu sai dai Allah bai basu haihuwa ba har girma ya soma kama mutallaf don a lokacin harya haura shekara 50, hakan yasa kasa kara aure ya auro Hajara cikin ikon Allah shekara na zagayo wa hajara ta haifa masa yarinya mace, duk da yaso d'a namiji Amma hakan bai hanasa murnan samun mace ba, aka saka mata sunan hauwa-kulu yama uwar gidan sa takwara, haka hajara tayi ta haihuwar mata har hudu rus, sosai tsoro ya shiga zuciyar mutallaf, koh baida rabon d'a namjine kasancewar su a zuriyarsu ana yawan haihuwar mata, sama da maza gashi yana son magaji ga girma ya kamasa, Amma daga baya saiya maida lamuransa ga Allah, yaran nan kaf a wajen hauwa suke ita ke kula dasu kasancewar ta bata taba haihuwa ba kuma zaman lafiya suke da hajara. Hajara ta sake samun ciki sam wannan karon mutallaf bai kwallafawa ransa namiji zai haifa ba sam, cikin ikon Allah hajara ta haifi d'a namiji yaro yaci suna yusuf, tunda aka haifi yusuf mutallaf ya d'auki son duniya ya d'aura masa bama shi kad'ai ba duk wani masoyinsa nason yusuf, kuma aka d'aura masa sarkan magajin masarauta, saida hajara ta haifi yusuf daga shi bata kara haihuwa ba. Yar kaninta hauwa ta d'auko tana riko mai suna zahra, lokacin yusuf nada shekara goma sha biyar, sosai zarah keson yusuf ganin saukin kansa babu izzah koh nuna isa mutum ne na mutane, bai d'auki son mulki ya sakawa ransa ba wannan yasa zahra keson maganar sa. A lokacin da yusuf ya cika shekara 20 yayi haddan Alkur'ani mai girma da haddisai, yana cigaba da karatunsa na gaba da secondary, hauwa ta kwanta ciwo wanda kafun ta mutu saida ta nemi Alfarman mutallaf daya had'a aure tsakanin yar d'an uwanta zahra da yusuf, koh bayan ranta za'a tuna da ita a masarautan karfe, kuma zuriya vai kare tsakanin ta da mutallaf ba, babu wani shamaki mutallaf ya Amince mata. Bayan mutuwar hauwa mutallaf ya tada maganar auren yusuf da zahra, daman zahra nason yusuf wanda kowa ya sani sai dai shi yusuf inne bayayinta a lokacin, yaso gardama da nuna shifa Aure ba yanzun ba sai ya girma, Amma mahaifinsa ya murza ido akan lalle lalle auren Addanayen sa da za'ayi guda biyu Kafshatu da maisara tare za'a had'a da nasa, yusuf yayi iyya yinsa akan bayason zahra, abasa dama ya nemo wance zai aura Amma ina mutallaf yace bazai Aminta ba. Rana bata karya Saidai uwar deya taji kunya, a ranan da aka zartar amatsayin ranan d'auren auren yusuf da yan uwansa ya cika, Amma abin takaici an waye gari babu yusuf a gidan Sarauta. Sarki ya shiga tashin hankali Amma daga baya saiyayi zuciya akan duk inda yusuf yaje wata rana zai juyo gida, in ma bai dawo ba yama kansa, haka aka d'aura auren zahra da wani d'an uwanta. Tunda sarki ya rasa yusuf ya shiga wani irin matsanancin damuwa, ganin an share shekara goma babu yusuf babu a lamansa a lokacin hajara ta sake haihuwar na miji zulkiflu, sosai sarki yayi murna ya samu wani d'a na miji, sai dai ganin girma ya fara kamasa gashi shekaru naja yana sonyin murabas Amma babu magajiiiii. Shekaru sunja Amma shuru babu yusuf babu labarin sa, har hajara ta sake haihuwar wani d'a na mijin (Ramadan)dayake daman ita akwai kuruciya a tare da ita, Yusuf kam bai dawo ba shekaru sai tafiya suke har mahaifin sa ya kwanta ciwon ajali mai tsanani, a lokacin zulkiflu ya girma yakai saurayi, ga yan uwansa mata duk sunyi aure su hudu gashi mazajen su manya ne a kasa wasu kuma sarakuna. Hade Hannu sukayi aka bazama neman yusuf kasa da kasa Amma ina ba'aga yusuf ba gashi jikin mutallaf sai kara tsanani yake, baida magana saina d'ansa yusuf yana son ganin d'ansa kafun numfashinsa na karshe. Rana tsaka saiga shi an gano yusuf yana NIGERIA Kuma a ranan aka samu labarin An kaisa prison, bai kwana ba aka cirosa washe gari sai gasu a NIGER Har gaban mahafinsa dake kwance aka dukar dashi. Ganin halinda yusuf yaga mahaifinsa a take kuka ya kamasa tare da neman yafiyar mahaifinsa, sai a lokacin nadama tazo masa ganin yanda uban ya tsufa matuka, shekaru sunja, da ba'a d'aukosa ba da shikenan daker ya sake ganinsa sai wani ikon Allah. Mutallaf dake kwance cikin ciwo yace bazai taba yafe masa ba har sai ya masa Alkawari? Ba musu Yusuf yace ya Amince a take mutallaf yace koh bayan ransa bai yarda ya sake taka nigeria ba, koma menene zai kaisa baiyarda ba sannan ya masa Alkawarin zai auri lawiza(kanwar zahra) don cikawa hauwa burinta na had'a jini da zuriyar su. A take yusuf yasa kuka yana sanar da mahaifinsa cewa yana da mata da yara a nageria, a basa dama ya d'auko su kuma ya Amince da auren lawiza. Kin Yarda mutallaf yayi ganin haka yasa yusuf D'aukar wannan Alkawari, shi kuma mutallf ya yafe masa duniya da lahira tare da sakamasa Albarka, anyi haka washe gari aka d'aura auren yusuf da lawiza sati mai zuwa aka nad'a yusuf a matsayin sarkin masarautar karfe, a wannan rana mutallaf yabar duniya. Tunda yusuf ya zama sarki shikenan Rayuwar sa ta sauya bashida aiki sai tunani gabaki d'aya ya kwallafa ransa akan nigeria, yaso tura mutane aje a duba rayuwar da iyalansa keyi Amma hajara ta gargadesa akan rashin biyayya ga mahaifinsa da karya Alkawari, sannan tace bata son kowa yasan da maganar. Yusuf rayuwa suke da matar sa lawiza za'ace sai a hankali, batasan wan abu wai dadin aure ba, asalima yusuf ya samu ciwon zuciya wanda kullum gaba gaba yake duk wani abinda za'ayi don ganin yusuf ya dawo da walwalarsa anyi Amma abin yaci tura. Hatta yan uwansa da dangi ya shanja musu ba kamar yusuf da aka sani daba. Bayan wasu shekaru lawiza ta haifi yara biyu mata muwaddat da muhibbat, sai nabila yar kafshatu ce wance hajara ke riko a gidan sarauta. An dawo labari.......... Tabbas yusuf nada yara ni shaidace mahmah tace tana hawaye. Jama'a da dama dake fadan sunsha mamakin abinda ya faru wai yusuf nada iyali, Amma ba'a sanar da kowa ba acikin zuriyar su, sannan wasu suna ganin rashin kyautawar abinda aka ma yusuf, lawiza kam kuka ta sake yanzun daman yusuf nada wasu yaran kamar muhammad, amma tana matsayin matarsa a kasa sanar da ita, mikewa tayi zata bar falon, alamu yusuf ya mata data koma ta zauna, ba musu ta koma ta zauna. Al'ameen ne ya dubi mahmah yanzun kina nufin kice mini kece mahaifiyar abbajo? Kwarai nice hajara kakar ka uwar yusuf... Yanzun kun kyauta kenan abinda kuka ma mahaifina ace mutum an yanke masa alaka da yaransa duk wani hakkin su daya rataya a wuyansa ? kai koh ashariya wannan ba daidai bane, mijinki bai kyauta wa mahaifina ba. Ya kyauta masa muhammad, nine ban kyauta ma mahaifinka ba, a Ranar da aka nad'a yusuf kafun mutallaf ya bar duniya munyi wani magana dashi akan yusuf............... ✨Ruqeenjalal✨ [10/24, 9:42 PM] +234 806 618 5035: 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya* *Ibrahim* 🍃 Page9⃣2⃣&9⃣3⃣ A ranan da aka nad'a yusuf a ranan mahaifinsa yake sanar dani, akan na fad'awa yusuf ya d'auko iyalansa, ya masa hakan ne don yaga zai masa biyayya koh zai bijire masa, Amma tunda ya yarda da auren lawiza kuma ya hau karagan mulki ya yafe masa duniya da lahira. A hankali yusuf ya kalli mahaifiyarsa, mahmah meyasa kika hanani? Kayi hakuri yusuf nayi hakan ne don banason kayi nisa dani, nayi tunanin koh inna sanar dakai hakan zaka iyya bijire wa mulki. Ramadan ne ya kalleta Amma wallahi mama baki kyauta ba, duk irin ciwon da yaya yake Amma mahmah baki tausaya ma d'anki ba?kowa yasan dalilin ciwon yaya yusuf Amma ga magani a hannunki mahmah kika kasa basa habba mama mulki yafi lafiya ne? Kuka mahmah ta sake tana nuna Alhininta. Kaga ramadan ya isa haka mahmah uwatace har abada babu wanda yakai uwa son d'anta don haka ni mama bata mini kome ba. Jin abinda yusuf yace sosai jikin wasu yayi sanyi, Al'ameen hannu yasa a wuyansa ya zaro sarkan tare da mikawa mahaifinsa, Abbajo ga sarkanku a sawa wanda ya dace? Kallonsa zulkiflu yayi, akan me zaka cire, wayace maka baka dace da magaji ba? Ah ah uncle kai ya dace kasa koh uncle Ramadan nikam banida sha'awar sarauta so nake nayi karatu mai zurfi na zama soja mai mukami. Kowa dake wajen da kallo yabi muhammad jin abinda ya fad'a, murmushi sarki yayi hade da cewa yan uwansa, bazan tilasta muhammad ba daman na basa sarkane badon na shaida shine magaji ba, na basane don na gane sa aduk shekaru da zai gabato duk da Akwai kamar jini, Amma zan aje shaida don haka Za'a d'aurawa zulkiflu. Da sauri zulkiflu yace Ah ah wallahi yaya nikam banaso gaskiya, amini afuwa adai bawa Ramadan. Ba musu aka d'aura wa Ramadan sarkan magajin masarauta, sannan a mana booking in fly next week zamu shige nageria. Jin Abinda sarki yace yasa zuciyar muhamamd rawa, ganin wani rawan jiki da mahaifinsa keyi zashi nageria duk zatonsa matarsa na raye, Abbajo nace dukan mu zamu wuce ne? Ah ah muhamamd bazamu wuce mu biyar ba, tunda in muka d'auko su dawowa zamuyi nan? Shuru muhammad yayi yana kallon Mahaifinsa, ya sake juyawa ya kalli mama kamar hadin baki suka had'a ido da nabila kauda fuskar sa yayi. Waini muhammad baka bamu labarin abubuwan da suka shafeka ba, da Alakar ka da sarkin shayi da yaran nan?, zulkiflu yace yana nuna su gidado. Da sauri muwaddat tace eh hakane Akki. Kasa magana yayi yana kallon yusuf, gyad'a masa kai yusuf yayi Alamun yayi maganar sa, A hankali ya fara basu labarin abubuwan da suka faru bayan tafiyar yusuf da wahalar da suka sha da abubuwan da suka faru da ubangari da zainab, da mutuwar Maminsa da kaninsa harda Aurensa da sumayya, sai dai bai fad'a musu dalilin da yasa aka aura masa ita ba, don baidace yace dangin ta sunyi mata kazafi ba, har kawo zuwansa cameroon. Muhammad na bayani mutane wasu na kuka wasu na salati wasu najin haushin zainab da mahmah data hana a d'auko yaran yusuf, kuka itama mahmah ta sake tana cewa su muhammad su yafeta ta cutar dasu. Yusuf kam zaune yake akan karagan mulkinsa sosai fuska tayi zahur, jijiyoyin fuskarsa ya mike alamu dai ran maza ya baci, gashi a fada yake dole ya matse irin na sarakun, abin tsoro koh bacin rai da tausayi baya bayyana a fuskarsu mundin suma gaban jama'arsu. A take aka matso da tafiya zuwa jibi in Allah ya kaimu da rai da lafiya sai NIGERIA!!!!!! Mikewa yusuf yayi ya koma falonsa kafun kowa ya mike ya fita, nabila kam jiki yayi sanyi saibin mahmah take a baya, yayinda muwaddat da muhibbat suka likewa d'an uwansu sai hira suke masa da tambayarsa labarin khadija, sosai yaji wani irin farin ciki ganin yan kannensa, lawiza ma tashi tayi batama kowa magana ba tayi flat nata, da fari tad'au abin da zafi Amma jin irin wahalar da su muhamamd sukasha da mutuwar Aisha sai taji jikinta yayi sanyi. *************** Sumayya ce zaune a kitchen tana girka pepper chicken zallah, don ita yanzun nama kawai takeci sai shayi, yanzun ma khdija taje islamiyya ne shiyasa ta shiga kitchen da rarrafe zata girka abinci. Sai karfe 5:21 khadija ta shigo falon da sallama, sanye take da riga da wando sai hijab babba na islamiyya, hannunta d'auke da jaka. Amsa mata sumayya tayi tana binta da kallo ta rasa meke damun khadija a kwana biyun nan, gabaki d'aya ta shanja bata da nutsuwa sam, kullum ta zauna shuru koh aiki ta sata bata gamawa akan lokaci, shiyasa wasu aikin take lallabawa tayi duk da nauyin cikinta, don yanzun saidai ta ja ta shiga d'aki indai khadija bata nan"khadija zonan"? Ba musu ta kwabe hijab nata tazo ta zauna kusa da sumayya, Aunty gani. "Khadija meke damunki"? Babu Aunty "Wani irin babu kome, ki dubi halinda kike ciki duk kinsa rayuwar ki a garari, sai kinzo kin samu ciwone a koma ana sayan magani koh yaya"? Babu kome fa Aunty "Bankai ki fad'amin damuwarki ba koh"? Sunkuyar da kai khadina tayi bata iyya cewa sumayya kome ba, tana wasa da yatsarta. "kunyi fad'a da kalamu ne kwana uku yau baizo ba" Wallahi Aunty bansan meke faruwa ba yau kwana uku bai kirani ba, inna kirasa wayar sa a kashe. "Ok abinda ke damunki kenan?amma meyasa baki tambaye kannensa ba tunda islamiyyar ku d'aya kuma boko ma d'aya" Wallahi Aunty kunya nake ji, karsuce da wani abu. "Kunya?lallai khadija bakisan inda ke miki ciwo ba, yaro kullum sai yazo wajen ki kwana uku bakisa sa a idanunki ba, bazaki iyya shigiyarsa ba? Sai gobe innaje school saina tambaye falmata(kanwarsa) " ohon miki" Tashi khadija tayi jin amsar da Auntin ta ta bata. Washe gari bayan khadija ta dawo gida take sanar da sumayya ai kalamu ba lafiya yana hospital, kasancewar sumayya tayi nauyi, khadija ce tayi girki mai rai da lafiya, kawarta ta rakata suka je asibiti wajen kalamu, sosai suka samu jikin nasa yad'anyi sauki, kuma taji dadin tarbar da aka mata maman sa nada kirki sosai, haka ma babansa, wanda ke d'auke da zanen kanuri a fuska, amma mamansa bata dashi, haka kannensa sukayita tsokanarta wai budurwan kalamu ne, sosai tayita jin kunya. ************ Kwana biyu da muhammad yayi a gidan sarauta, da ace zasu hadu da wanda yasansa a baya indai ba farin sani ba, bazai ganesa ba, ya samu gata kota ina bana wasa ba yayi kyau ya kara fresh yana cin mai kyau yana shan mai kyau, ya kwanta a maikyau baida buri daya wuce yadawo yaga matarsa abar sonsa, sannan yana iyya bakin kokarinsa wajen ganin mahaifinsa bai saka damuwar rashin Aisha da salim ba, sosai yake kula dashi baya barinsa shi kad'ai mundin yabar fada, toh zasu kasance tare haka yan uwan babansa na sonsa, kannensa ma duk ya shaku dasu, nabila ce kawai bata samu fuska a wajen saba duk da mahmah tasata ta basa hakuri kome ya wuce, kuma ya nuna ya hakura Amma bata ganin fuska koh hira yake tazo wajen sai yayi shuru abinsa koh ya tashi. Su gidado da sarkin shayi duk sun dawo gidan da zama. Waya mai tsada zulkiflu ya saya masa da kayayyakin sawa masu yawa, wanda zaina sawa. Kamar yanda Aka saka rana yaune za'a diro nigeria, maimartaba ne da mahmah sai muhamamd da zulkiflu Adda maisara, dayake su muwaddat na jarabawa an barsu da lawiza a gida, karfe 2 na rana jirginsu ya d'aga zuwa Kasarmu ta gado!!!!! Sun sauka lafiya, suna fita a jirgi dayake sarki yasan da zuwansu yasa suka samu tarba na musamman direct gidan sarki suka nufa, duk da muhammad yaso ya fara zarcewa sintali sai dai ba dama. Bayan sunyi wanka sunci abinci,kasa hakuri yayi ya ce zaije sintali ramadan ya rakasa a mota tare da driver. Tunda suka shigo sintali yake bin koh ina da kallo yana tuna abubuwan da suka shude watan nin baya, har kofar gidan Adara akayi packing in motar,jikinsa har rawa yake yana Allah Allah ya fitoh, saura kad'an ya buge kafarsa saban sauri ya bude motar ya fita, gashi daman yammane ana shirye shiryen kiran mangariba, abin mamaki yana fita babu wanda ma ya zaci shine, harya ratsa mutane sai binsa ake da kallo ganin babbar motar da ya sauka a ciki. Shiga gidan adara yayi kamar yanda ya tsammani hakan ce ta faru, wato jama'ar gidan na tsakar gida, duk juyawa sukayi suna kallonsa harya karaso tsakar gidan, gaidasu yayi da sauri gabaki d'ayansu suka Amsa hade da shiga shock, indai ba gizau ba Al'ameen ne, duk gatan da ya samu bazai hana su kasa gane saba. Da sauri iro ya mike bura uba wanake ganin nan kamar muhammad ina ka shiga? Bai samu daman basu amsa ba, kofar su kawai ya nufa cikin sauri ya bude kofar shashen, da mamaki yakebin kofar ganin duk datti, Alamu dai an dade ba'a share ba da sauri ya karaso kofar, yana bin koh ina da kallo,da sauri ya shiga kitchen insu ga mamakinsa kome a zaune yayi kura, da sauri ya fitoh a kofar, daidai lokacin Ramadan ya shigo gidan, da sauri muhammad ke tambayar yan gidan da har yanzun suke a tsaye sun maidashi madubi,tambayar su yayi ya yaga kofar sumayya a kulle? Inna asabe ce take sanar dashi ai ba'aga sumayya ba, kama kai kawai yayi yana salati, da sauri ya fita a gidan da kafa ya taka har gidan goggo, yayinda su iro ke mara masa baya, duk inda suka wuce saisu cewa mutane ga MAKAHO ya dawo ga makaho, har gidan goggo va tare da wani neman izini ba ya shiga gidan. Goggo dake zaune a gindin bishiya, gabaki d'aya ta rame ta zama abin tausayi zaune take tayi tagumi, jin sallamar muhammad yasa ta mike da sauri, wanake ganin nan kaman muhamamd?Allahu Akbar Allah mungode maka sai kuma ta fashe da kuka tana rungumar Al'ameen. Saida tayi kukanta mai isarta kafun Suka gaisa na yaushe rabo, hade da karama mujammad karin bayani akan batan su sumayya, wanda shagari ya sanar dasu guduwa sukayi bawai sacesu akayi ba, sosai muhammad yaji wani irin ciwo na abinda dangin sumayya sukayi bayan rabuwar su, taya zasuce ya rabu da matarsa akan wani dalili, anan yake sanar da goggo abubuwan da suka faru sannan yace mata yana son zuwa gidan su sumayya don ganawa da iyayenta, koh Allah yasa sunsan inda sumayya zata iyya zuwa. Ba karamin mamaki Goggo tasha ba jin wai yusuf sarkine yanzun, Allah sarki duniya, mikewa gogho tayi tad'au hijabinta suka fita gidan da Al'ameen, ai suna fita kofar gida, me zasu gani mutane ne makil a kofar gidan, sunzo kallon Al'ameen don lokaci d'aya labari ya samesu makaho ya dawo yayi kudi, goggo ma a take ta kara musu da wani ai yanzun d'an sarki ne babansa yana mulkin wani gari, a nijar, muhamamd in ma kudi ya ciro a Aljuhunsa ya rarraba musu dubu bibbiyu. Yana gama raba musu kowa ya watse yana saka masa Albarka, harya juya zasu shiga mota,don driver yajawo ramadan dake ciki har kofar gidan goggo, yana shiga tun daga nesa ya fara jin ana kwala masa kira oga oga oga!!!! Shagari ne ya iso wajen da gudu, da ido muhammad ke binsa koh ba'a fad'a ba yasan shagari ne daga muryarsa ya gane sa. Oga sannu da dawowa ka dawo lafiya, yanzun Abdu ra'uf kece mini wai ka dawo. Murmushi muhammad yayi, lafiya Alhamdulilah shagari. Da sauri shagari yace munyi kewarka oga shagon mu ya bunkasa nima, yanzun ina makaranta bara na kira Ammar na sanar dashi daman ina da number sa? Ah ah basai ka kiraba ka bani number sa zan kirasa. Kallon ramadan da goggo dake mota shagari yayi sai kuma ahankali yace oga tafiya zakayi ne? Ah ah shagari ina Taraba har sai anga sumayya. Number Ammar ya basa sukayi sallama suka tafi, dayake shugaba family house sanannen gidane kuma driven dan garine, yasa da kwatance suka gane gidan, goggo ramadan da muhamamd suka shiga gidan,ganin zubinsu yasa mai gadin basu hanya suka wuce cikin compound, ya shiga gidan don musu sallama da mai gidan, ba'a jima ba saiga Uncle Abubakar ya fitoh suka gaisawa, sannan suka gabatar masa da kansu, kuma suna son magana da mahaifin sumayya, da rawan jiki Abubakar ya musu iso zuwa cikin gidan, da gaggawa ya hado kan mutanen gidan a falo, kowa na zazzaune don su daman ba farin sani sukayiwa muhammad sosai ba, a d'auren aure suka fara ganinsa hakan yasa basu wani ganesa ba, gashi ba'a makaho yake ba yau. Bayan sun zazzauna wannan zaman ma ba momy a ciki, a nitse goggo ta musu bayanin ga mijin sumayya ga kuma bappansa ta nuna Ramadan, da mamaki suke tambayarta ba'ance mijin sumayya makaho bane kuma ya bata. Ramadan ne ya musu bayanin kome a take jikinsu yayi mugun sanyi, sannan suke sanar dashi rashin ganin sumayya anyi iyya bincike Amma shuru, duk inda ake tsammanin zataje ba'a ganta ba, abie har wani ya samu ya tura unguwan su Hafsa a maiduguri a dubo masa koh sumayya ta gane gidan kakan ninta shan taje, amma an samu tabbacin banan sumayya taje ba, Asali ma hafsa tayi aure bata maiduguri yanzun. Hankalin muhammad ba karamin tashi yayi ba, fiye da hankalin yan gidan duk da abie ya shiga damuwa don har rama yayi mai tsanani, suna tsaka da maida zancen sukaji an turo kofar falon koh sallama babu. Gabaki d'aya suka juyo suna duban falon, safina ce ta shigo Alamu dai daga unguwa take, duk suka bita da kallo itama, d'aga ido tayi ta kalli jama'an falon da karfi ta kwala kara ta zube a kasa sumammeya.. Da sauri dada tayi kanta, sabanin Abie da sauran yan gidan dako a jikinsu alamu dai ba karamin tsanarta sukayi ba, muhammad ma mikewa yayi shida ramadan suka nufi kan momy, da taimakon su aka kaita asibiti don anyita watsa ruwa bata farfado ba, gashi yan gidan koh a jikinsu, sune suka d'auketa har asibiti suka biya kudin kome suka tafi suka barta da dada, gida suka koma bayan isha'i suke sanar dasu yusuf abubuwan da ya faru da batar da sumayya tayi,sosai suka nuna Alhininsu da damuwa sosai muhamamd ya basu tausayi yaro tun yana karami yasan wahalan duniya, har tashinsa ma yayi gwagwarmaya. Washe gari da sassafe saiga Ammar a gidan sarauta, daya samu aka barsa ya shiga ya tura wani dogari yace ana sallama da muhamamd bakin Niger, ba'a jima ba sai ga muhammad ya fitoh, tun daga nesa yake kallon muhamamd kamar bashi ba gabaki d'aya rayuwa ta sauya, sanye yake da jallabiya yar saudi sai hula taba kaji hadisi, sosai yayi kyau saidai fuskar sa a tamke take alamu baya cikin walwalarsa, yana karasowa da sallama a bakinsa, amsa masa Ammar yayi ai yana jim muryar Ammar da sauri ya rungume sa, cikin farin ciki suka hau hira har cikin gida muhammad ya shigar da Ammar suka gaisa da yan uwansa da mahaifinsa, sai a lokacin yake sanar dashi ai shagarine ya kirasa yake sanar sashi muhamamd ya dawo, yana gidan sarki kuma ya basa number Amma shuru Al'ameen bai kirasa ba shiyasa yabuga sammako yazo ya gansa. Abinci aka kawowa Ammar, suna zaune a d'akin da aka sauke muhammad ana hira da labarun abubuwan da suka faru a baya harda Ramadan, kawai saijin muryar jama'a sukayi a sashen sarki, dayake window d'akin da aka sauke muhammad yana saitin sashen. Mikewa sukayi gabaki d'ayansu suka zagaya zuwa falon sarki,family shugaba ne, suka gaishe dasu abie, aka daura zancen batan sumayya kowa na kawo shawaran sa, karshe dai akace za'a dage da rokon Allah da sadaka sannan za'a zuba jami'an tsaro a bincike su, kafun kowa ya watse, daman yan gidan su sumayya gaida yusuf sukazo da mahaifiyar sa tare da bada hakuri akan abinda ya faru kuma ba laifi sun nuna musu bakome, kome ya wuce Allah ya kiyaye na gaba. Satin yan nijar biyu a taraba ba'aga sumayya ba, gashi kaf gidan su an duba hotonan ta duka ba'a gani ba, hatta dakin su muhammad ya koma yayi bincike sap baiga wani hoto ba, don sumayya ta tafi da hotunan su, gashi na wayar maimuna kanwar Ammar ma, wayar ta lalace harma ta saida ta, bare su samu hotunan su, da yake yanzun zamani ya sauya ba kamar daba, mutun ya bata a gari ma ba'a ganesa sai da rabo bare a kasa sukutum, dole tasa Yusuf komawa dasu ramadan aka bar mahmah da muhammad, kafun su tafi saida aka sai musu gida mai shegen kyau a Amazon suka koma ciki su uku harda goggo, kasancewar mijinta ya rasu bayan tafiyar sumayya hakan yasa muhammad d'aukar ta suka koma gidan su suna zaune tare da mahmah. Wasa wasa saida muhamamd suka share wata biyu a jalingo Ana kan bincike har yanzun shuru ba'aji duriyar sumayya ba, koh khadija sosai abin ya dame muhammad koh abinci baya iyyaci sosai, ba irin tunanin da baiyi ba don shi gani yake saceta akayi tunda makiyansa suka iyya saka a kashesa, Amma ammar na yawan kwantar masa da hankali ba kad'an ba. Ta bangaren safina dai tunda ta farfado a gadon asibiti ta makance bata gani kwata kwata haka magana ma bata iyyawa saboda bakinta daya koma gefe, fuska ya karkace ya murd'u ya wainu wanda likitoti sun tabbatar hawan jinine daya hau lokaci d'aya, daya bugar da ita ta fadin nan, shine ya kaushar mata da fuska, sai dai makantar ne basu gano sila ba, kuma kaf gidan babu wanda ya damu da lamuranta sai dada ita ke jinya amma hatta abie yaji ya tsaneta hakama y'an gidan wanda basu san dalili ba, dada ma daurewa take Amma ba kaunar safinan take ba yanzun. Ammar ne zaune a falon gidan su shida kannen sa, abinci yake ci gabaki d'aya hankalin sa nakan TV, yayinda iyayen sa ke hiran batar sumayya da dawowar Al'ameen wanda Ammar ke kawo musu zancen, don iyayen sama sunje har gidan muhammad, suka masa jaje, kaninsa ne kawai baya falon. Kwala masa kira yaji kaninsa yayi daga d'aki sai gasa ya fitoh da gudu hannunsa d'auke da waya yana zuwa baiyi magana ba, kawai ya mikawa Ammar wayan. Kallon wayan yayi hotunane akayi posted nasu a instagram guda uku, Khadija ce sanye da uniform ita da wani bakin yaro wanda zaiyi sa'ar ta koh ya fita da kad'an shima da uniform in nurse suka d'auki hoto a unguwa mai kyau, sai na biyun tana sanye da uniform in islamilayya nan ma su biyu sai na ukun ita da yaron suna sanye da kayan hausa atamfa da shadda. Jikin Ammar na rawa yake tambayar Abdul wanene yaron nan? Aboki nane kalamu-wahid, school namu d'aya dashi a abuja naga yayi post kuma naga kamar khadija? Ba kama bane Abdul itace, yanzun kasan inda yaron yake takamamme a Abuja? Eh na sani yaya don inban manta ba kafun mu dawo hutu yayi ciwo danaje asibiti dubasa na samu an sallamo sa, so yamin kwatancen gidan su naje. Waya kawai Ammar ya fitar a Aljuhunsa yana lalubar numban muhammad gabaki d'aya yabi ya gigice. ******************* Kalamu yaji sauki har ya dawo da normal life nasa, a haka sukaci gaba da rayuwa abinsu cikin farin ciki duk da basa rasa kalubalen rayuwa. Sumayya ciki ya shiga wata tara duk rashin tausayin mutun inya ganta sayya tausaya mata, cikine yayi kato matuka yayi tsayi ga nauyi don yanzun koh tafiya bata iyyawa sai dai rarrafe abin tausayi bata fita koh ina daga falo sai toilet khadija ke kome wani sa'in kalamu zaizo ya tattara wankin ta ya kai mata dana khadija, wani sa'in har girki yake zuwa ya taya khadija in ayyuka sun mata yawa, sumayya kam yanzun sai a hankali, koh riga bata iyya sawa sai wasu manya manyan vest na gwanjo da zani shine kayanta, sosai laila ke tausaya mata. Yau laila da mijinta harda yaranta sunyi tafiya zuwa Adamawa wajen dangin mijinta, bayan isha'i kalamu yazo ya kawowa sumayya balankun nama, amma ta kasa ci saboda ciwon kanda ke damunta, suka sha hira da khadija suna cin nama, bai koma gida ba sai kusan 9 ya ma khadija sallama ya wuce, don zuwa lokacin sumayya ta dade da kwanciya. Da misalin karfe 1 na dare sumayya ta farka jin wani irin matsetsen fitsari daya kamata, mikewa tayi zaune a hankali jin fitsari ya cika mata mara, gashi dare ne batason shiga hakkin khadija, yasa ta rarrafawa ta shiga bedroom da rarrafe har cikin bandaki, tsungunawa tayi, tayi fitsari ai tana gamawa taji bayan ta ya kama ga wani irin c................ ✨Ruqeenjalal✨ 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya* *Ibrahim* 🍃 Page9⃣4⃣&9⃣5⃣ Bayan ta ya rike sosai ga wani irin ciwo da taji a maranta lokaci d'aya ta gigice tana salata tunda take bata taba jin ciwo irin na yau ba, Ambaton Allah kawai take a ranta gabaki d'aya ta had'a gumi, jin wani abu na zuba babu control ya sata tsorata ruwa ne yake dundula, salati ta sake hade da kwalawa khadija kira. Khadija dake bacci kamar a mafarki taji muryar sumayya mikewa tayi ta nufi ban d'akin da sauri ta bude wazata gani? sumayya ce duke jikinta sai rawa yake gabaki d'aya ta had'a gumi a tsorace take tambayar ta haihuwa ne? sumayya bata samu Amsan bata ba, nuni kawai ta mata ta kira mata mota su tafi asibiti, ba musu khadija tad'au hijab tasa akan kayan baccin jikinta, ta ruga da gudu ta fita a falon, sakatan get in ta zare ta fita bakin kwalta, abinka da dare koh tsuntsu bata samu ba koh ina shuru, kuka ta sa da gudu ta dawo cikin gidan, kofar d'aya makwanciyar su ta wuce tana buga wa, amma basu bude ba gashi kaf gidan babu mai mota koh mijin laila ma ba motar bane dashi. Haka da dawo sashen su, tana shiga zuwa lokacin jikin sumayya ya kara tsanani sosai koh zama ta kasa har lokacin tana tsungune. Da sauri ta d'auki wayar ta layin kalamu ta kira, sai da ta masa kusan 4 miss call kafun ya d'aga cikin muryar bacci yake tambayar ta lafiya? Ai tana sanar dashi da sauri ya mike ya zura jallabiyar sa ya fitoh a d'akin sa, harya tura kofar falon su zai fita saiga nannen sa ta fitoh daga dakin ta, tambayar sa tayi ina zaije a daren nan? Sanar da ita yayi Auntin khadija ba lafiya tana labour, tambayar sa tayi mijin tafa,Amsa ya bata shidai bai taba ganin mijinta ba, yama ga alamu bata da miji, jin haka yasa nanne d'aukar hijab nata ta sanar da mijinta zasukai sumayya asibiti, suka fitoh tare dashi mota kalamu ya fitar suka shiga sai get insu sumayya, fita nanne dashi sukayi zuwa ciki. Zuwa lokacin sumayya tayi laushi sosai koh gane wake kanta bazata iyya ba, dayake dare ne nanne da khadija ne suka ririketa yayinda kalamu ya diauki akwatin ta, data jima da shiryashi a zaune, rufe musu kofar yayi suka tafi asibitin da sumayya ke awo. Suna zuwa aka karbesu nanne na zaune a waje ita da khadija, kalamu keta hidima na sayyan abubuwan da aka bukata koh zama bai samu, har 4 na asuba sumayya haihuwa ya gagara, gabaki d'aya karfin ta ya gama karewa sai da aka kira Assalatu kafun haihuwa yazo gadan gadan, cikin hukunci Allah sumayya ta haifi yaran ta guda biyu wanda koh sanin wani iri ta haifa bata sani ba, tsabar wahalar da tasha, tadai san ta haihu sau biyu, Alluran hutu aka mata bayan an kimtsata a take bacci ya d'auke ta. ****************** Bugu d'aya Al'ameen ya d'auka a take Ammar ke sanar dashi anga wajen da khadija take, suna Abuja. Ai muhammad baisan lokacin da ya wantsalo daga kan kujeran falo, a take yayi sujjada akan tiles yana wa Allah kirari, goggo da mahmah dake zaune a kasan falo suna cin abinci da sauri suka mike suna tambayar sa lafiya?ai da sauri ya mike ya rungumi mahmah cikin farin ciki yake sanar da ita anga sumayya anga sumayya tana Abuja. Ai sosai suka nuna farin cikin su goggo harda kuka, a take Muhammad ya fitar da waya ya kira abie ya sanar dashi akan yanzun nan zai tafi gidan su Ammar zasu wuce abuja. Hanasa Abie yayi yace ya bari sai da safe sai subi fly zai sa a nema musu ticket sai su tafi tare da abie, ai a take goggo ma tace zata mahmah ma tace ita ma, dada dake kusa da abie tace itama baza'ayi ba ita ba, duk yanda abie da muhammad sukayi da tsofinnan su zauna a Taraba, su zasuje su dawo da sumayya amma kememen sukace kafar su kafar su abie, haka ba yanda abie ya iyya duka aka musu booking in fly tare da kiraye kirayen waya har nijar aka sanar dasu an samu wajen da suke, suma sun sanar dasu a cikin satin nan suna zuwa gabaki d'ayan su. Washe gari tun sassafe suka bar Taraba muhammad koh bacci jiya kasawa yayi, dada ma haka ta watsar da safina tace sai taje taga jikallen ta, Ammar ma tasa Abdul yayi a gaba tare zasu ya nuna musu gidan su kalamu. Karfe 9 su muhammad suka dira a Abuja, dayake yana da aboki, tun a taraba ya kirasa akan suna zuwa, tarba suka samu daga wajen abokin abie shiyazo ya d'aukesu a Airport, direct gidan su kalamu suka wuce, Amma abin haushi basu sami kowa ba wai Suna asibiti, haka mai ganin ya sanar dasu Alfarman ganin baban kalamu abie ya nema ba musu, mai gadi ya shiga ga sanar dashi, aiko sai gasa bayan sun gaisa ne sukace masa suna son sanin asibitin da kalamu sukaje in ba damuwa. Ganin girman su da kudin su, gashi kamar ba lafiya ba, hakan yasa baban kalamu yace musu bara ya bisu asibitin, shiga mototi sukayi ya kira nanne ya tambaye ta asibitin da number room nasu, da mamaki yake tambayar ta koh lafiya jin muryar ta ya dishe-dishe alamu dai ba lafiya ba, koh tayi kuka, ya tambaye ta lafiya tace masa ba kome, kashe wayar yayi ya sanar dasu abie ga asibitin da suke. Suna isa asibitin muhammad da gudu ya ruga bayan sanar dashi block inda suke koh kunyan su abie baiji ba da gudu yayi block in mutane sai kallonsa suke, da sauri sauri ya shiga d'akunan one by one yana dubasu, ana ukun ne ya shiga koh sallama babu ganin mace kwance akan gado ga yara sa'o'in juna zaune rike da jinjiraye a hannayen su, da sauri suma suka juyo jin mutun a d'akin babu sallama. Ai da sauri khadija ta mike ta kwala ihu yaya!!!!!!!! Da sauri kalamu dake kusa da ita rike da d'ayar babyn da sauri ya cafke wance ke hannun khadija, don saura kad'an ta buga jinjira, da gudu khadija tayi wajen muhammad batayi wata wata ba ta rungumi d'an uwanta tana fashewa da kuka yaya, kaine koh mafarki nake? Khadija nine nine khadija ina Aunty ki? Allahu akbar yaya kalli nan tace tana nuna masa kan gadon da sumayya ke kwance har yanzun tana bacci. Da sauri ya ware idanun sa yana kallon sumayya sai kuma ya juya ya kalli kalamu, ya sake kallon khadija? Gyada masa kai tayi tana murmushi, shima murmushin yayi sai kuma ga hawaye, tare da matsawa kusa da gadon da sumayya take kwance, dukawa yayi akan gwuwar sa hannu yasa a hankali yana shafa fuskar sumayya, dake kwance sanye da kayan asibiti, tayi kyau tayi fresh irin na masujego, wannan ce sumayyar tawa ashe haka take da kyau masha Allah? Itace yaya kaga wa'innan jarirai nakane. Da sauri ya juya yana kallon kalamu da sauri ya mike tsaye hannu yasa ya Amshi babies in yana kallon su, yarane mata masu tsananin kama da junan su tamkar An raba kunu a kofi, gasu masu tsananin kama dashi kome nashine a fuskar yaran, gasu farare tass, rungumarsu yayi ya fashe da kuka. Toh ragon maza baka da aiki sai kuka, mahmah da suka shigo cikin d'akin tun d'azun, amma basu ma san da su ba. Da sauri ya nufi mahmah yana ce mata, mahmah kalli yaran nan, wai yarana ne kallesu fa ga sumayya mahmah kyakkyawa fa sosai? . Sunkuyar da kai abie yayi yana mamakin surkin nan nasa yau koh dai ya mantasa a wajen ne, shima da sauri ya nufi wajen da yarsa ke kwance, zama yayi a bakin gadon yana shafa gashin kanta daya hargitse koh ribon babu. Mahmah ce ta karbi baby d'aya dada ma ta karbi d'aya goggo kam baki kawai ta sake tana bin kowa da ido, kalamu kallon babansa yayi dake gefe, ya gaidashi, amsawa yayi yana tambayar sa mai jiki. Matsawa kusa da abie muhammad yayi ganin sumayya ta fara motse, a hankali ta bude idanunta dalilin kukan da yaranta suka sake dukan su biyu. Tana bude idanunta bata sauke sa akan kowa ba sai muhamamd dake kanta a tsaye, kamar a mafarki haka ta kalli abin da sauri ta mike zaune har tana kokarin zamowa kasa, da sauri ya tarota, bi a hankali sumayya jikin ki ba kirfi. Ai jin abinda yace da sauri ta riko hannunsa gam tana kwalama khadija kira, Amsawa khadija tayi da sauri ta karaso wajen"khadija yayanki ke mini gizau na kamasa " Aunty ba gizau bane yayane "Yaya kuma khadija mijina fa baya gani yau kuma naga wannan na gani"? Aunty ya warke ne. Ai sumayya najin haka ta sake dariya cikin farin ciki koh damuwa da jikinta batayi ba ta rungume mijinta, don ita sam hankalin ta vaikai wajen mutanen d'akin ba. Mikewa abie yayi dasu mahmah zasu fita a dakin su basu waje don sukam kunya ne zai kashe su. Nanne dake toilet tana wanke kayayyakin sumayya daya baci, tun d'azun take jin surutai a d'akin mikewa tayi tsaye da boket na kaya a hannunta ta bude kofar toilet ta fitoh, Wai khadija da kalamu anya kuna da hankali kuwa mara lafiya na bacci kuke surutai da wa......bata karasa ba tayi turus ganin jama'ar dake shirin fita a d'akin dasuka juyo suna kallonta. Dada ce ta kama salati tana tafa hanneye, wanake ganin nan? Abie ma da sauri yace Hafsa?? Nanne kam bata wani nuna reaction ba, dayake tun daren jiya data gane sumayya tasan tabbas zata ga su abie, duk da saurin da take tabar asibitin kafun suzo don ita batasan sumayya gudu tayi ba, haka ma batasan itace Aunty khadija ba sai daren jiya. Nanne bata wani Amsa ba bare ma ta nuna tasan abie, sai tsayuwar da tayi tana kallon sumayya data sake muhamamd tana kallonta sosai irin kallon nan na kewa da soyayya, cikin kuka tace" ummi"? Sai a wannan karo nanne tayi magana, Na'am momcy? Da sauri sumayya ta sauka akan gadon tana takawa a hankali cikin dauriya tayi wajen mahaifiyarta fad'awa tayi jikinta tana kuka yau kam ta rasa ina zata sa kanta, murnan samun babies koh murnan ganin mahaifiyarta koh mijinta dole tayi kuka, ummi karan kanta hawaye ne ya cika a idanunta tana shafa kan sumayya ya isa haka momcy yi shuru kinga ba lafiya bane dake koma ki kwanta, tana maganar tana rike da hannun sumayya har ta kaita bakin gadon ta aje ta. Waini yau hafsa nake gani ne koh gizau idanuna kemin koh mafarki nake ne? Itace dada Abie yace yana dafe kansa cikin takaici da bakin cikin abubuwan da suka faru a baya. Mijin hafsa ne yace, Hafsa kin sansu ne daman nina d'auka koh iyayen yarinyar nan ce? Baban kalamu ne da kakarsa wannan kuma Addansa ce ta nuna sumayya. Daga sumayya har kalamu da Abie a tare suka jefowa Hafsa tambaya lokaci guda, baban kalamu wani kalamun? Da sauri abie yace hafsa ban gane ba wanene kalamu. Nuna masa kalamu tayi dake tsaye cikin shock na abinda nanne tace, yanzun wai sumayya Addansa, ta yaya kamar ya?baigane ba? "Ummi kina nufin kalamu d'an uwa nane"? Hafsa kina nufin wannan yaro, yaro nane? Kallon sumayya da abie hafsa tayi jin tambayar da suka jefo mata, eh kawai tace tana kama hanyar kofa zata fita tare da kallon mijin ta, yauwa Alan guburo mutafi naga dangin ta sunzo zasu zauna a gunta. Ah ah hafsa zuwan mu bazaisa ki daina hidima da yarki ba. Ah ah dada zan tafi , Allah ya sauwaka momcy. "Ameeen ummi in zaki dawo a kawo mini sabulun wanka" Toh momcy muje kalamu koh zaka zauna ne? Ah ah nanne muje yace yana kallon abie da mamaki wai wannan ne babansa, shi abin ma yajisa wani banbara kwai. Kokarin fita a dakin suke a hankali abie ya kama hannun kalamu daya wucesa zai fita a d'akin, kalamu bazaka ma abie magana bane? Murmushi kalamu yayi sai kuma yaji hawaye ya taro masa, abie ashe kanason na maka magana, shine zaka kyamace ni ka kyautata rayuwar yar uwata, amma ka wofantar da nawa rayuwar ka barwa uwata ni, na zauna a matsayin agola a gidan da, bana ubana ba ya maye gurbinka ina Amfani da sunan sa koh a makaranta, bai taba nunawa duniya bashi ya haifeni ba koni bansan bashine mahaifina ba, sai yau akan me zan maka magana ni bansan wani uba ba sai ........ "bai karasa ba sumayya ta mike ta wanke sa da mari cikin bacin rai ta soma magana, karka kuskura ka fara abinda zai dame ka wallahi kayi kad'an ka zagar min uba na barka,ni a haka nake son abina koma me zaimin bazan taba kinsa ba" sai kuma ta kama kuka. Da sauri nurses dake falo suka shigo d'akin, akan surutun dake tashi, hakuri aka basu akan za'a kiyaye magana ne mai muhimmanci ake, ganin kalarsu yasa su barinsu a dakin. Daker aka samu suka sassanta nanne ta koma gida dasu goggo yayinda mazan kuma suka koma hotel sumayya ma ita da dada kadai aka bari a hospital. Washe gari aka sallame ta saboda kyaun da jikinta yayi, don haihuwar duk da yazo da gardama amma tana haihuwa shikenan. Gidan nanne aka maidata bata koma gidan hayansu ba,sosai ake kula da ita muhamamd a rana sai yazo sama da sau hudu, sai da sumayya ta kwana hudu da haihuwa kafun suka koma shirye shiryen dawowa jalingo don anan ake son yin taron suna gashi yan nijar ma sunce suna shirin zuwa, duk yanda sukayi ta rokon nanne ta biyosu taki tace bazataki bin umurnin mahaifinta ba na raba kanta da zuriyar shugaba, saida mijinta ya nuna bacin ransa da nuna mata yaranta nada hakki akan ta, sannan kalamu bazaiji dadin hakan ba tunda shima so yake yaje yaga dangin babansa, daker dai ta Amince washe gari da sumayya ta cika kwanan biyar sukabi jirgi saijalingo. Muhammad murza idanunsa yayi yace a gidan sa da babansa ya sai masa a Amazon sumayya zata sauka, ba musu duk da abie yaso ta koma gida Amma ganin hafsa da Al'ameen basason hakan. Gidan sumayya ta sauka dayake babban gidane ga d'akuna shiyasa gidan ya d'auke su, duka harda su hafsa falmata su babayo muhamamd goggo dasu mahmah, kalamu kam shugaba family house ya sauka kuma ba karamin farin cikin ganinsa sukayi ba. Babu inda haihuwar sumayya bai bazu ba jama'a sai tururuwan zuwa dubata suke harda yan Abuja laila ma daga adamawa ta gangaro, a ranan yan nijar suka diro nageria gabaki d'aya yan uwan yusuf ne harda shi karan kansa ma, wannan zuwa harda lawiza da nabila, sosai gidan ya dad'a cika da yan uwa kota ina yan gidan shugaba ma tun a washe gari suna matan suka diro, yusuf a gidan sarki ya sauka dayake suma ana gobe suna suka zo, kai sumayya taga jama'a iyya jama'a ga wani irin lalle da aka watsa mata mai masifar kyau da ketson suna duka. Yau take suna yara sunci suna NA'IMA da NA'IFA , tun Asuba yan gidan Adara suka diro su inna asabe inna lami Ana gindin murhu a sauke wanshan a d'aura wanshan, shanu uku aka yanka da rago biyu, duk suna ta kan gyaran nama, ga abinci kala kala, gashi koh ina ka leka zakaga group group na mata kowa da angon su mai zafi, wanda abie ya d'auki nauyi duka, yan nijar nasu da ban haka dangin adara, yan shugaba family house ga yan gembu, ashan gefe naga MATAR MAKAHO FAN'S ansha anko na Atamfa mai ratsen flower green ana zazzaune ana dirkan shinkafa a manyan tireruka hhhhh. Sumayya dake sanye da wani hadedden material gown wanda yasha dinki ga sarka na d'anyen gwal da sarki ya bada aka kawo mata, sarkane da dankunne sai warwaro ga agogo mai zafi na mata duka, tasha heavy make-up sai d'aukan hotuna suke da kannen Ammar dake sanye da Ankon su, khadija da kalamu dake zaune a gefe suna cin shinkafa. Muhammad da Ammar harda su ramadan zulkiflu gidado badaru duk yanzun sun chanja kamar basu ba, suna zazzaune a kofar gida a rumfar da aka kakkafa abinci suke ci mairai da lafiya. Tun daga nesa suke jin ihun yara da mutane suna rugawa a guje, da sauri suka mike gabaki d'ayansu suna kallon abinda ke faruwa. Mutum suka gani kamar mace ne koh na miji bazasu gane ba, kadangaru manne a jikin sa tana gudu suna binsa wasu na jikin ginin unguwan suna rugowa suna binta sosai kota ina kadangaru ga wasu runduna na binta a baya, sai wata mata dake gefenta rike da sharbebeyar bulala tana kad'a mai kadangarun suna tafiya a haka. Da sauri su muhammad suka ruga cikin gida da gudu har ana rige rige, ganin wajen da suke suka nufo. Suna shiga suka rufe kofar gidan da karfi suna ji sai bugawa matar take akan don Allah abude mata, kiri kiri su muhammad sukaki budewa har abin yaja hankalin matan dake compound sosai, dada dake rike da jinjira zata kaiwa kawayen ta dake falo a zaune ssga dayar, itace taji hayaniya aje jinjiran tayi ta fitoh compound, ganin su muahmamd da jama'ar tsakar gidan a tsaye yasata karasawa bakin get in tana tambayar dalili, kafun ma su muhammad suyi mata bayani tuni tasa hannu ta zare sakatar get in, ihu Ramadan ya sake tsabar rikita yare ma ya fara. Dada na budewa idanunta ya sauka akan matar dake rike da bulala kwalalo ido tayi cikin mamaki tace wanake gani anan kamar Nafi............. kafun ma ta karasa maganar ta idanunta ya sauka akan wance ke tsaye mammanne da kadangaru ga bataliya a kasa, ai ihu dada tasa ta ruga ciki da gudu, da sauri inna lami tazo zata rufe get aida sauri wannan matar ta banke kofar ta kora mai kadangaru ta shigo, itama shigowa tayi, ai ana ganinta, ihu ne yake tashi abinka da mata atake masu Aljanu Aljanunsu ya soma tashi, gidan suna gabaki d'aya ya rikice ya zama gidan tsere kowa gudu yake yana burmuwa falo wasu kitchen masu Aljanu kam sun zuzzube.............. ✨Ruqeenjalal✨ 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya* *Ibrahim* 🍃 Page9⃣6⃣&9⃣7⃣ Duk masu Aljanu sun zuzzube a kasa, muhammad da gudu yayi falon cikin gidan duk da yaga tashin hankali a cameroon Amma wannan tashin hankalin tabanne koh mutum baida Aljanu indai yaga kamila sai tsikar jikinsa ya mike, yana shiga falon yaga an watsar masa da jinjiraye akan kujera, kawayen dada tuni sun ruga daki da sauri ya ciccibi yaransa ya manna a kirjinsa yanemi gefen daining ya tsaya yana jijigasu. Ta gefen sumayya kam bayan d'akunan gidan suka nufa mahmah dake dana da jiki, gudu take kamar kazan Agric irin sunyi naman nan, kowa fa gudu yake abin dariya abin tausayi a take ramadan ya kira yusuf ya sanar dashi, Ammar ma abie ya kira don su harga Allah abin ya basu tsoro especially ganin yanda kadangarun makwanta ke biyowa ta gini da gudu suzo wajen kamila, gasu bataliya guda. Ba'a d'auki lokaci ba saiga Abie ya shigo shikaran kansa abin ya masa tsoro, Amma sai yayi ta maza ganin nafisa, babban get in ya wangale galala gabaki d'aya ana kallon cikin gidan, nuni yama nafisa dasu fita waje su tsaya, ba musu ganin get a bude ta kora mai kadangaru suka fitoh bakin get suka tsaya suna hangen cikin gidan. Daidai lokacin yusuf da mijin nafisa suka iso a tare, don shima wani abokinsa dake unguwan ne ya kirasa akan yaga kamila da nafisa sai gudunsu mutane kiyi. A get yusuf ya sauka suka nufo inda abie ke tsaye, yana ma nafisa masifa akan sun shigo sun dagawa jama'a hankali, ita kuma sai hakuri take basa akan tazo tana son ganin muhammadsumayya da hafsa taji labarin duk suna gidan nan. Daker aka shawo kan abie da wasu mazajen unguwan akan yayi hakuri aji meke tafe dasu, rukiya yusuf yayi ma masu Aljanun suka farfado, matan da suka gugudu ma duk aka tarkatosu, sumayya kam d'ankwali ya fadi koh takalmi babu, muhammad har lokacin yaransa na hannunsa,shimfid'a manyan taburmaye akayi a gefe guda hudu, gefen maza daban na mata daban kowa aka ajesa, wasu da dama kam sun gudu gida wasu kuma na cikin d'akuna, sun rantse bazasu kara yarda su kara kallon kamila ba, haka masu Aljanu duk an hanasu fita. Zama akayi sarki kam kujera aka kawo masa ya zauna, yasa aka shigo da nafisa kamila kam a wajen get akace ta zauna saboda kadangarun ta. Yusuf ne ya kalli nafisa, baiwar Allah lafiya kikazo kika d'agawa mutane hankali da wanshan abin? Kuka nafisa tasa a hankali ta kalli mijinta, sam bataso yau ta sanar da sirrin ta a gabansa ba tsoron kar auren ta ya mutu gashi batasan inda zata shiga ba. Wai ba magana ake miki bane kinsan waye a gabanki kuwa, sarkine da kansa ki kama kanki baya magana biyu? Kayi hakuri nasan yau koh naki koh naso sai gaskiya tayi halinta, shiyasa na gwammaci kunyar duniya data lahira, gwara na nemi yafiyar su koh Alhaki zai barni. Shuru kowa yayi ya zubawa nafisa ido don jin me tazo dashi. Abubuwan da suka faru a shekarun baya da suka wuce, nidai sunanan nafisa Abdullahi kamar yanda wasu suka sani macece maison abin duniya gabin bokaye, bayan nayi aure da mijina saboda halayena ya rabu dani, lokacin na haifi yarinyata kwalli d'aya da Allah ya bamu mai suna kamila, duk yanda naso na koma gidan mijina sam yaki amince wa hakan yasa na shiga islamiyya saboda a lokacin bana zuwa boko sam, mun hadu da safina ne A makarantar islamiyya muka kulla kawance, a lokacin don ance hali sai yazo d'aya ake abota, kawancen mu yayi karfi a lokacin safina ke sanar dani bata da buri saina auren Abdulsalam Amma goggon ta(dada) bata bata goyi baya ba. Ni kuma jin haka yasa na bata shawara muje gun wani malami danaji labarin sa, nima so nake na koma gidan mijina ba musu safina ta samo kudi muka kama hanya har Ardo-kwala wajen wani hanshakin boka. Bayan munje da bukatan mu yake sanar damu Auren safisa da Abdul bazai taba yuwa ba, mundin yana tare da hafsa don soyayyar su na daban ne kuma mai karfi, dole rabasu shine zai iyya taimakawa ta samu Abdul salam. Babu musu mukace mun Amince a rabasu, nima na shaida masa bukatana nason komawa gidan mijina aiko cikin sati d'aya baban kamila ya dawo yace shi kaf duniya saini, na koma gidan mijina aiki yayi kyau sai dai aikin safina shuru baici ba, haka muka koma wajen bokan nan yake sanar damu saimun kawo idanun jariri, kafun mu iyya dishar da soyayyar dake tsakanin su,yaji kwata-kwata baya ganin farin hafsa sai bakinta, sannan bazai iyya rabasu ba sai safina ta had'a da kirsa. Babu musu na samo wasu rikakakun yan daba muka biyasu suka sato mana jinjiri, haka ba tausayi aka kwakule idanunsa a take ya mutu koh shurawa baiyi ba, muka kaiwa boka ido yayi aiki aiko koh sati ba'ayi ba rashin zaman lafiya ya wanzu a tsakanin ma'auratan nan, yayinda na baiwa safina shawara ta shiga sacewa mutanen gidan Abubuwa daga karshe ta likawa hafsa. Aiko shawarata taci don cikin wata d'aya akayi hakan kuma aiki yayi Abdul ya sake hafsa. Bayan nan muka koma wajen boka ya mana wasu aikin gabaki d'aya ya rikitar da dada da yan uwanta akan sai Abdul ya Aure safina kuma duka aikin bokane. Bayan auren kuma safina tazo da bukata akan tanason a raba sumayya da Abdul don ta fahimci yana tsananin son yarsa, shawara na bata akan basai mun koma wajen boka ba ita ta d'auki mataki da kanta, amma abin mamaki har Kashe mata aure dukan sumayya yajawo wannan dalili yasata tayi sanyi ganin babu yanda ta iyya da sumayya. A lokacin da sumayya takai shekara 14 sai gabaki d'aya hankalin safina ya tashi ganin irin kyaun data tashi dashi, gashi koh a gidan su farin jinine da ita gashi kowa na dangi baida magana sai sumayya, kome sumayya hakan yasa safina fara kishi da sumayyar. Kasa hakuri tayi muka koma wajen boka akan a raba tsakanin sumayya da ubanta, dayan gidan su suji sun tsaneta yanda zatayi rayuwa cikin kaskanci, Amma boka yace hakan bazaiyu ba sai an diga magani a idanun yaro matashi mai tashen balaga kuma ya kasance tauraren sa nada karfi, wannan zance da mukaji yamatukar d'agawa safina hankali don ita tana da tsoro ba kamar ni ba. Nikam jin haka sai wani tunani ya fado mini na Al'ameen dake likewa yarinya ta, kwata kwata bana sonsa da yarinyana,gashi nayi iyya kokari na babanta ya rabasu yaki itama duk irin lallama da dabara da zan mata ta rabu dashi Amma taki, hakan yasa na kirawo wa'innan yan daban da suka taba sato mana jinjiri na basu hoton muhammad dake wajen kamila na d'auka, na musu kwatancen makarantan su a ranan suka kama muhammad bayan sun bugar dashi suka daukesa har Ardo-kwala wajen boka, sai da akayi sati baya cikin hayyacinsa, ana masa wankan magani da digawa a ido, kafun aka mayar dashi bayan gari aka jefar. Wannan shine dalilin makantan Al'ameee, ta karasa maganar tana kuka, jama'ar dake wajen salati suka buga, Muhammad kam gabaki d'aya jijiyoyin kansa su mike bacin raine karara a fuskarsa wanda kallo d'aya zaka masa kasan ran maza ya baci, mikewa dada tayi tsaye habba nafisa mai muka miki? yanzun da haden bakin safina aka aikata wannan mummunan aiki, Sai kuma ta fashe da kuka take surutai ya fara tashi kowa yana furta Albarkacin bakinsa. D'aga hannu sarki yayi tare da bada umurni kowa yayi shuru, aiko shurun akayi ya bawa nafisa dake kuka damar ci gaba da bayaninta. Bayan an gama aiki kuma yaci, sai dai sam bai kama Abdul ba iyya yan gidan ne sukaji basa kyaunar sumayya sam, sai kuma Abdul ya d'agata ya maidata hostel wanda hakan ya rage musguna mata da ake, kuma hakan baiwa safina Dadi ba, taso abar sumayya a gida taci kwakwa. Duk yanda mukayi babanta ya rabu da ita abin ya gagara karshe dai haka mukayi hakuri aka cigaba da rayuwa, kamila ma taki muhammad a lokacin ganin ya makance. Lokacin da sumayya ta zama cikekkeyar budurwa hankalin safina ya tashi hassada take da sumayya karta samu mijin dayafi ubanta kudi, koh wani mai mulki kwata kwata so take taga sumayya ta kaskanta a rayuwa wannan dalili yasa muka koma wajen boka daman sumayya nada wani hali na raina wa mutun ArZiki, aiko da halin nan nata aka samo mafita wajen mata magani yanda samari zasuji basa sonta kwata kwata wanda majority zasuce halinta ne ya ja mata. Bayan nan sumayya ta rasa manemi sai dai ba'anan gizo ke saka ba, sumayya na samun kudi sama da safina don tana aiki, ga kaunar da mahaifinta ke mata, shawara na bata muje wajen wani bokan aiko munsamu wannan aiki da wanshan ya kasa wannan yace zai mana amma da sharadi, shine sai an nemi makahon yaron da mukama asiri, mu had'asa aure da sumayya wannan ne zaisa ta fita a zuciyar Abie,yanda mukasa muhammad yana kallon baki, haka su dada ke kallon bakin sumayya, kuma duk adadin sex da zasuyi, haka aiki zai kara karfi tamkar muna bawa shuki ruw, tsanar ta a zukatansu zai karu, amma aiki zai lalace mundin aka rabasu misali d'aya na wani kasa d'ayan na wani kasa aiki zai karye. Ba musu muka abince daman safina ta shanye kowa a gidan, kowa tsoron ta yake sai abie kawai baya shayin ta, wannan dalili yasa ta samu su babuji da dada ta tilastasu akan aurar da sumayya kuma ita ta sama mata miji ba musu suka amince jiki na bari. Mu muka nemi mamman dayaje ya samu muhamamd akan shine uban sumayya, zai basa auren ta amma dayake Al'ameen nada tunani sai yaki Amince wa, karshe dai wajen Bappa suleman akaje don munji labarin yanada son kudi, mamman ya sake masa kudi masu yawa akan zance, wanda gaskiya lamari sharri muka ma suamyya akan tayi ciki saurayin da zata aura ya fasa, a taimaka a had'ata da muhamamd ba musu ya amince da zancen. Bayan auren sumayyya da muhammad magani yaci Abdul ya tsane yarsa, duniya kaf babu wanda yaki jini irinta, muma sosai muka sakawa rayuwar sumayya ido duk wani motsenta muna sane dashi. A lokacin An jima da sakar mini yata kamila wance ta koma makaranta tana ci gaba da karatunta da bata samu tayi ba, kusam ta dawo rayuwar muahmamd wanda bansan da labarin ba saida taje gidan Adara aka mata duka, a lokacin raina ya baci kuma na jama kamila kunne akan ta rabu da rayuwar yaron nan in tanason kanta da lafiya, amma bata daddara ba ita da kawarta suka je mutum biyu wajen boka.............................................har sanadin haka ta samu wannan matsala na kadangaru wanda na tabbata Alhakine yake bibiyata. Munyi neman duniya wa bokan nan don mu biyasa koh mu basa hakuri ya rabu da ita, Amma ina bamu gansa ba duk malaman da muka kira shuru ba sauki, a lokacin na shiga tashin hankali ita kuma safina a lokacin take jin dadin ta, naje wajen ta akan ta taimaka mini akan zancen kamila koh da kudine don kaf abinda muka tara ya kare a wajen jinya amma haka safina ta murza ido bata tuna irin hallaci dana mata ba ta hanani koh biyar, ni kuma abin yayi matukar bata mini rai hakan ne yasa na d'auki kayan dakina na sayar na biya yan dabanda suke mini aiki tsawon shekaru, akan su kashe mini muhamamd yanda aikin safina zai lalace sannan nima na huce takaicina akansa, tunda ata dalilinsa rayuwar yata ya shiga garari, don haka kowa ma ya rasa. Aiko yan ta'andan nan sun bani tabbacin batar muhamamd wanda zancen yaje har kunnen safina, kuma ta zargi nice wanda har gida tazo mukayi fad'a kasha kasha, ta tafi ban sake bi takanta ba, sai kawai labarin rashin lafiyar safina ya riskeni, da kuma dawowar muhammad gida. Shine nazo neman yafiyar ku don Allah ku yafe mini sharrin shaid'an ne? Ai kece shaid'aniyar in kam, munafuka wallahi bazan taba yafe miki ba har abada kin cuceni kin rabani da matata kin muzguna ma rayuwar yata, Allah ya isa tsakanina daku kuma bala'i yanzun kika fara gani. Jin abinda abie yace yasa dada mikewa tsaye da hannu tayi pointing in mutanen gembu, maza maza su tashi su tafi gidan shugaba su tattari safina a yau innan su maidata wajen dangin uwarta babu ita babu safina har Abada, ita tana ta bauta mata ashe shaid'aniya ce. Baban kamila mikewa yayi yanzun nafisa har kisan kai kike? toh kiji daga yau bani bake kuma bara kiji na sakeki saki biyu daman babu igiya d'aya a tsakanin mu, ki tattara yarki ku kara gaba koh gidana karki koma don bakizo da kome ba, bazan iyya zama daku ba, kuka nafisa tasa da sauri ta rike kafar baban kamila tana neman yafiyar sa tunkudeta yayi ya kama gabansa. Duk yanda yusuf yaso wajen yayi shuru abu ya gagara ganin yan gidan Adara sun rufarwa nafina da duka, waya Ammar yayi wa ofishin yan sanda cikin kankanin lokaci sukazo daker aka kwace nafisa anso tafiya da ita, Amma yusuf ya hana yace a barta kodon Albarkacin kamila dake d'auke da wannan matsala taje duniyace, haka ta mike daker tana koran kamila suka bar unguwan gwanin tausayi. Hafsa a ranan kuka tasha bana wasa ba kuma itama ta basu labarin, bayan rabuwarsu akan cikin bai zube ba, jinine ya zuba kuma mahaifinta yace sai an zubar da cikin Abdul salam, baza'a haifa masa a gida ba ganin yanda ransa ya baci yasa kanwar mamarta d'aukar ta ashan ta haifi kalamu bayan haihuwar sa ne matar cousin nata kabeer ta rasu, bayan shekara d'aya da mutuwarta sai ya nemi ya auri hafsa kuma ba musu findon ta amince dayake kowa yasan halin ta macece mai nutsuwa, kuma bayan auren su ta rike yaran kabeer hannu bibbiyu, wannan dalili yasa sa rike d'anta itama kamar nasa hatta su babayo basa nuna wa kalamu ba yan uwansu bane harya girma, bayan kalamu ta haifi yara uku shamsiyya(tayi aure a maiduguri) falmata da musa (auta) duk yaran hafsa ne da suka haifa da kabeer. Sosai abie ya nuna nadamar sa kuma ya nemi yafiyarta tare da sanar da ita insha Allah gobe gobe xasu je maiduguri har wajen mahaifinta ya nemi yafiyarsa wannan umurnin yusuf ne kuma hardashi zasu. Washe gari haka aka tattaru duka aka wuce maiduguri duk yanda akayi sumayya ta zauna saboda yanayinta amma ina tace da ita za'aje taga kakan ninta da kanwarta shamsiyya, ba yanda aka iyya haka aka tattaru harda Ammar suka wuce maiduguri. Da isarsu suka sauka a gidan sarki yayinda Ammar ya nemi Alfarmar su muhammad su bisa gidan Uncle nasa su kwana, bazasuji dadi ba in sukasan yazo Maiduguri ya kwana a wani wajen, ba musu ramadan da muhamamd suka bisa jin yace musu babu kowa a gidan daga uncle nasa sai matarsa da yarsu babba. Unguwane mai kyau suka shiga cikin wani gida madaidaici mai kyau,sunyita sallama Amma shuru ba'a amsa ba, hakan yasa Ammar nufar kofar falon ganin kamar a bude, aiko yana turawa yaga kofar ta bude, bismillah yama su muhammad ba musu suka shiga da sallama, amma shuru. Macece zata kai shekara 44 zaune akan sallaya a falo ta fuskanci gabar rabin fuskar ta kawai suke iyya hanga zaune take tayi tagumi kana ganinta kasan tayi zurfi a tunani. Girgiza kai Ammar yyi saboda wannan abin ba sabo bane agunsa, abune da ya saba da ganinta a haka, da sauri ya nufi wajen da take ya tabata Aunty!!!!! Da sauri ta dawo hayyacinta, ta dubesa a dakile tace Ammar yaushe kazo? Yanzun nazo kina sana'ar taki ina zakisan na shigo? Shuru ta masa alamu dai batada yawan magana, koh ince damuwa ya maidata haka. Ganin ta masa shuru yasa sa tambayar ta, aunty ina mom? Basanan Ammar kai kad'aine? Ah ah Aunti babba nida abokai nane, yace yana nuna mata su Ramadan dake tsaye, yayinda shi kuma muhammad ya zuba ma fuskar matar ido yana kallonta, kallo irin na tsana, koh shekara dubune bazai manta da wannan fuskar ba. Ai tana kallonsa jikinta ya soma rawa da sauri ta mike tsaye sanye da hijab, tana nunasa da hannu sai kuma ta yanke jiki zata fad.............. .. ✨Ruqeenjalal✨ 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya* *Ibrahim* 🍃 Page 9⃣8⃣&9⃣9⃣ Zata fadi da sauri Ammar ya tarota cikin tashin hanki Ramadan ya bude firij inda ya gani a falon ya ibo ruwa watsa mata sukayi ta farfado cikin kidima take magana ina yake na tabbata d'an yusuf ne, don Allah ku taimaka ku kaini wajen sa na nemi yafiyarsa na tabbata muhammad ne, don salim baya kama da yusuf. Da mamaki suka juya baya don yima Muhammad magana, sai kawai sukaga wayam babu shi ga kuma mamakin ina matan nan ta sansu. Kuka take tana rokonsu su taimaka su kaita wajen muhammad, kwantar mata da hankali sukayi akan tayi hakuri ya koma inda suka sauka ne, kuma tare da yusuf suka zo, ai tana jin haka ta mike da sauri ta tsaya takalmi ta saka ta nufi kofar gida. Ganin haka yasa su Ammar binta suna tambayarta ina zata? Amsa ta basu akan gidan sarki zata wajen dasu yusuf suka sauka, jin haka yasa su binta a baya suna had'ata da Allah ta tsaya yanzun dai yana hutawa, amma ina bude get tayi zata fita daidai lokacin Alhaji suka dawo tsayawa yayi da motar sa yana tambyar zainab in zata? da mamaki don sam inba dalili mai karfi ba zainab sai tafi wata uku bata leka kofar gida ba. Tambayarta yayi ina zata Amma ina ta kasa basa Amsa shuru tayi ta tsunkuyar da kai, Ammar dake gefenta shiyake sanar da uncle insa ga inda zata, sata yayi ta koma amma kememmen Zainab taki komawa sai hawaye dayake bin fuskar ta, daka mata tsawa Alhaji yayi akan ta wuce ta koma ba musu ta juya tana kuka ta koma cikin gida, Ammar kam dariya abin ya basa watoh duk girman mace in batayi aure ba saikaga wani yaranta a tare da ita yanzun kamar Aunty zee ke kuka don ance bazata wani wajen ba. Komawa ciki sukayi dukansu harda uncle in Ammar da mom, shiga falon sukayi duka suka tsinci zainab na kuka a zaune zama sukayi baban ya fara rarrashinta don abin na zainab tsawa baya gyarasa. Tambayar Ammar yayi cikekken bayani, Ba musu Ammar ya zayyana masa kome dayafaru da labarin su yusuf kuka zainab tasa tana sambatu akan kome ya faru dasu yusuf itace ummulkaba'isin kome daya same su. Ajesu Alhaji yayi akan su zauna gobe daga shi harsu in saisu tafi wajen yusuf in tare. Aiko washe gari da sassafe suka wuce gidan sarki Amma basuyi sa'a ba duk basanan sunje gidan su hafsa, waya Ramadan ya d'auka ya kira zulkifilu akan ya tambaya musu sunan unguwan da suke. Bayan sun isa gidan da sallama suka shiga falon bayan an musu ido, zainab sai boye fuska take ganin sun had'a ido da yusuf dake mamakin ganinta da ubangari. Zama ubangari yayi suka gaggaisa da juna anan ne ubangari ke neman yafiyar yusuf tare da rokonsa daya yafe ma zainab, duniya ta koya mata Hankali, duk da sun dawo Maiduguri Amma har yanzun batayi aure ba, kowa yazo wajenta sai tace bata so gashi yau tana da shekara 44 harta fara tsufa Amma shuru kullum cikin istigifari dake da nadamar abinda ta Aikata, ga mutuwar khairat daya shiga jikinta sosai don Allah yusuf da muhammad su yafe musu. Daker aka samu muhammad ya yafe don yusuf kam a take ya yafe mata tare da neman izinin Aurenta, don zainab ta basa tausayi matuka tsawon shekara 44 ace batayi aure ba, yasan sonsa ke wahalar da ita duk da tsufa yaxo, Amma xuciyarta bai tsufa ba, ba musu Aka daidaita kome baban hafsa ma ya yafe ma abie, abin gwanin sha'awa su muhammad basu bar maiduguri ba saida aka saka sartin auren yusuf aka biya sadaki, Amma auren sai yusuf yaje nijar zasu dawo d'auren aure, duk wanda yaga fuskar zainab a lokacin zaisan lallai so ba karya bane don ta kasa boye farin cikinta. Daga maiduguri Hafsa da kalamu dasu falmata suka wuce Abuja,saboda karatunsu, muhammad da Sumayya suka wuce Taraba harda mahmah dasu dahdah, yusuf dasu ramadan sun wuce nijar daga Maiduguri. Bayan komawar sumayya dasu Abie jalingo sukaci gaba da kula da jariransu yayinda muhammad ya kai khadija wajen hafsa tacigaba da zuwa makaranta daidai su tashi tafiya nijar in sumayya ta gama jego. Kudi yusuf y sakarwa Al'ameeen a account ba kad'an ba, kamar yau suna zaune a falo su uku dashi da sumayya sai mahmah dake bawa na'ima madara gaggo na sallah a d'aki, hira suke anan ne muhammad ya kalli sumayya, ina so ki bani shawara matata cikin fulatanci yayi maganar sanin mahmah bataji. Murmushi sumayya tayi tana kallon mijinta sai kuma ta basa amsa da hausa gudun kar su ware mahmah, "ina jinka dear" Jin haka yasa mahmah mikewa ta basu waje. Yauwa don Allah ki tayani nazari in sama wa yan uwana mafita don nayi nazari Abinda ke damun Adara abu biyu ne, akwai jalinci akwai bin jini na gado, akan halinsu shiyasa nake son na shawo kan lamarin nan kuma na rasa mafita ta ina zan fara? "Gaskiya naji dadi daka ji a ranka Adara yan uwanka ne, baka kullace su a rai ba akan abinda suka maka ba, har kana nema musu tsira"? Taya zan gujesu sumayya bayan dangin mahaifiyata ne, da kinsu ake da Abbajo bai yarda ya auri mami ba. "Gaskiya ne ni a nawa shawaran abu na farko da zaka fara shine ka tarasu, kayi musu magana akan duk wanda yake da wance yake so koh wance take da saurayi tsayaye zaka aurar dasu, babu koh sisin iyayen su sannan ka gyara musu gidan tunda akwai fili saika ma samarukan d'akuna room and falo, suyi aure a ciki ka nema musu jari matan kuma asasu a islamiyya yara a had'a musu da boko, su kuma su inna ka basu jarin 50k ga kowance su kama san'a, sai maganar shagari kaje ka sanar dashi akan ka basa shagon halak malak kaga zaifi samun natsuwa akan ya zauna da tantama tunda Ammar yace ya baka kyautane" Gaskiya sumayya ngode matar Aljana Allah ya barmin ke baby, amma ya zanyi dasu bappa sulaiman? "Ameeen dear, ni a ganina kamar daman ai suna da sana'arsu kadai taimaka wa mata da yara matasan zaifi in yaso daga baya saika basu abinda kaga ya dace" Haka koh akayi washe gari muhammad yaje gidan adara kuma ya sanar da shagari ya barmasa shagon kyauta, yaron har kuka yayi gwanin tausayi, sannan yanzun yasan khadija tafi karfinsa shiyasa ya fara kula wata yarinyar school nasu dake matsa masa. Takardun makarantan sa muhammad kawai ya d'auka a dakinsu, sauran kayan d'akin ya baiwa matan gidan Adara kyauta harda na kitchen. Kafun wata d'aya duk samarin gidan adara da suka kai aure duk sun fitar da mata, haka ma matan don daman suna son auren, rashin kudine kawai, mazan ma wa'inda basu da budurwa jin auren bati da za'a musu yasa su neman yan mata cikin lokaci kankani, gashi ansa yara a boko ansa mata a islamiyya harda mazan ma. Anyi bikin gidan Adara na gani na fad'a wanda ya samu hallartar jama'a da yawa kowa na tofa Albarkacin bakinsa, akan muhammad da Halakcin daya musu. Sumayya ta kammala wankan jegon ta sati d'aya kenan, yau tun safe daga ita har muhammad in suna cikin farin ciki,adalilin khadija da kalamu da zasu zo yau don anyi hutun makaranta Khadija an kammala ss 1 zasu tafi 2, gashi yau daga ita har kalamu zasu zo Taraba tun asuba suke sanar dasu akan zasu bi fly, wanka sumayya tayi goggo tama yaranta wanka suka shirya cikin shiga ta Alfarma harda muhammad zasu je gaida maman Ammar, daga nan zasu bi Airport d'auko su Kalamu 4:00 na yamma. Dayake yanzun muhammad ya iyya tuki shiya d'aukesu a motar zuwa Gidan su Ammar, suna fita a motar dayake zuwan bazata sukayi basu sanar da Ammar zasuzo ba, tsayawa muhammad yayi a tsakar gidan yayinda sumayya ta wuce ciki rike da na'ima ta bar masa na'ifa da sallama ta shigo falon Amma babu kowa shuru kakeji,zama tayi koh masu gidan zasu fitoh Amma har minutes biyu bataga kowa ba, gashi Al'ameen sai kiranta yake akan yajita shuru saboda shi baya shiga gidan mutane ba tare da neman izini ba. Mikewa tayi ta nufi wani kofar dake gefen falon don a tunaninta koh dakin su maimuna ne a falon harta kama handle in kofar zata bude sai kuma ta dakata jin maganar dake tashi a d'akin. Muryar hajiyar Ammar ke magana, yanzun Ammar kanada wance ta fini ne ka zauna kana cutar da kanka ni bangane kanka ba gabaki d'aya ka chanja yau ciwo gobe lafiya? Ammar ne ya bata Amsa, Mom babu fa abinda ke damuwa kawai dai banajin dadi ne. Wani irin bakajin dadi, abinda ke damunka harda tunani da damuwa ba haka kake ba Ammar nice fa na haifeka? Mom daman wallahi na jima ina son khadija sai kuma yayi shuru bai karasa ba Wace khadijar? Kanwar Al'ameen Toh sai akayi yaya cewa tayi bata sonka? Ah ah mama ban fad'a mata ba,daman naso na sanar da sumayya maganar sai kuma bakina yayi nauyi kar tace daman da wani manufa nake taimakon su, gashi banason yarinyar ta rainani. Gyara zama mom tayi yana kara kallon Ammar tun ba yauba tasam d'an nata akwai son girma. Toh shine ita da Auntin nata suka gudu Abuja ba tare da na zayyana mata abinda ke raina ba, kuma yanzun kawai saina ganta da yaron nan kalamu kanin sumayya, kinga yanzun ai babu halin nace mata ina sonta tunda yanzun soyayya suke koma na fahimci tana son yaron. Ammar ka bani mamaki wallahi ita tace maka soyayya suke? Hamma mom kowa yagansu yasan masoya ne kuma nasan koh da ba sonsa khadija take ba Albarkacin sumayya zata yarda ta aure kalamun bare ma tana sonsa. Kaga Ammar kafito ka sanar da yarinyar nan kana sonta bakasan me Allah zaiyi a lamarin nan naku ba, ka kwantar da Hankalinka kaji inso samune ma ka shirya kaje abujan? Mom muhammad ya sanar dani khadija na zuwa. Toh maza ka tashi ka shirya samun ta ganka tsaf dakai kabi yayanta Airport gobe kuma sai kaje gidan su ku gaisa kaga saika sanar da ita Amma ka dubi yanda duk kabi ka rame........ Jin abinda suke cewa yasa sumayya sauri tabar bakin kofar, jin alamun mom zata iyya fitowa da sauri ta bude kofar falo ta fita waje, muhammad dake tsaye a rumfa har yanzun rike da babyn sa, dan yanzun sunyi wayo sosai,ya tambaye ta Lafiya tun d'azun Ammar bai fito ba? "Muje kawai ba kowa a gidan" Da gaske? "Don Allah ka shiga mu tafi gidan mu pls nace maka basa nan" Ba musu muhammamd ya shiga motar yaja suka wuce gidan su sumayya. Yad'an jima a gidan kafun kiran Ammar ya shigo wayarsa, sallama yama su dada ya wuce, bayan fitar Muhamamd ne dada ke sanar da sumayya akan ta kara ma abie magana akan Amina(goggo)ya aureta don ita hankalin matar ya burge ta, Amma duk yanda dada tayi akan ya yarda Ya nemi Amina tunda dai bata tsufa ba, da yarantanta Amma yaki Amince wa. Sumayya karan kanta taji dadin Abin don babu shakka goggo macece ta gari duba da zaman da suke da ita yanzun a gida d'aya sam bata da dumuwa. Sumayya ta samu Abie akan maganar daker saida takai ruwa rana kafun ya Amince da zancen, A ranan dada ta sasa dole sai ya wuce gidan su Al'ameen sun daidaita da goggo tunda yanzun yaran basa gida sai mahmah ne kawai. Muhammad da Ammar su sukaje suka d'auko su khadija a Airport gidan su Abie suka sauka daman sumayya na gidan sosai suka musu tarba ta musamman, Sannan a nan suke xancen Abie ya tafi zance gun goggo, aiko muhamamd yaji dadi don daman tunanin da yake kenan in ya tafi karatu abroad kamar yanda uncle zulkiflu yace masa next month zasu tafi America an sama masa gurbin karatu harda sumayya da yaransu don gida yusuf ya kama musu ashan haya, yanzun ma bikin Abbajo suke jira. Lokacin da abie ya dawo sosai yayi farin cikin isowar d'an nasa hira ne ya kara barkewa a tsakaninsu sai dare su sumayya suka tashi tafiya, kiran kalamu tayi da Khadija a compound ta tambayesu shin soyayya suke kuma su fad'a mata tsakanin su da Allah? Dariya suka sake a tare sannan khadija tace wa sumayya ai tsakaninta da kalamu babu zancen soyayya asali ma Abota ce kawai da shakuwa don kalamu kamma yana da budurwa yar school nasu sunsha gaisawa da khadija a wayar Kalamu. Hakan sosai yama sumayya dadi sallama sukayi da yan uwanta. Sun isa gida muhammad kam kwanciya yayi ya barsu da khadija anan sumayya ke sanar da ita Zancen sonda Ammar ke mata, da kuma bata shawarwari da tuna mata irin Alkharin Ammar a karesu ya cancanci ta sosa koh Albarkacin Halakcin sa, saida ta tabbatar jikin khadija ya mutu murus kafun ta mata sallama ta wuce d'akin mijinta khadija kam tare da mahmah zasu kwanta. Washe gari da safe bayan sun karya Al'ameen ke tambayar ta dalilin sasa su bar gidan su Ammar bayan kuma Ammar yace masa suna nan,sumayya ke sanar da muhammad zancen Ammar da abinda ta jiyo suna tattaunawa sosai muhammad yayi murna ba d'an kadan ba, haka mahmah khadija kam kunyane kamar zai kasheta, especially jin muhamamd ya shirya ya fita wai kar Ammar yazo ya samesa a gidan tunda wajen khadija zaizo. Sumayya da khadija kitchen suka shiga bayan matsawa khadija datayi kafun ta yarda, suna aikin girki yayinda mahmah da goggo ke falo suna rirrike da yaran sumayya. Wayar mahmah ne yayi kara a d'aki mikewa tayi da na'ima a hannunta ta shiga dakin ta d'auko wayar, ganin nabila ne yasata d'auka da sauri. Ta bangaren nabila jin mahmah ta dauka jiki a sanyaye tace hello Kedai nabila anyi yar banza, sallamar ma bazakiyi ba sai wani d'an banzan hello wai gaki baturiya koh? Yi hakuri mahmah Assalamu alaikum Amsawa mahmah tayi tana tambayar nabila lafiya?jin muryarta cike da damuwa Dada kewarku nake yaushe akki (muhammada)zai dawo? Toh watoh shi kike kewa kenan banda ni? Yi hakuri harda kene mahmah Toh make damunki nabila in baki fad'amin ba wa zaki fadawa? Mahmah wallahi nifa son Akki nake don Allah kisa baki a maganar nan ki sanar da abba kice ke kikeso a had'amu ki taimaka mini mahmah......... ✨Ruqeenjalal✨ 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 ~ Na ~ 🍃 *Rukayya* *Ibrahim* 🍃 ✨Tsokaci A ranan 30/8/2021 na fara rubuta Wannan novel na matar makaho, gashi A yau 28/10/2021 na kammala cikin Yardan Allah kuskuren danayi a ciki Ubangaji ka yafe mini🤲🤲🤲🤲🤲🤲🤲🤲🤲🤲🤲 Free book🤧 😥END😥 Page1⃣0⃣0⃣ Wani irin magana ne haka nabila?toh nidai baza'ayi wannan haukar dani ba, kinji na fad'a miki taya yaro da matarsa koh sanin dadin aure basuyi ba, gani tsohowar banza nazo nasa bakina a sha'aninsu salon nayi bakin jini a wajen baiwar Allah, yarinya na ganin girmana najawa kaina raini wallahi da sakel ki barni na mutu da mutunci na. Kuka nabila ta sake cikin maganar shagwaba tace, ni shikenan babu inda zanje naji dadi, dedena naje mata da zancen zagina tayi kema shine xaki mini haka? Jin abinda tace yasa mahmah kashe wayar ta aje ta fita a d'akin. Ammar yazo sun gaisa da khadija kuma ba laifi ta sake jiki dashi kad'an, kuma yana samun hankalinta, Amma ba karamin kunyar muhammad yake jiba duk lokacin da zaizo sai ya tambaye khadija a waya yayan ta na nan intace eh tofa ba zuwan zaiyi ba. Bayan sati uku Ayau ne dubun Al'umma suka shaida d'aurin auren sarki yusuf mutallaf tare da Amaryar sa zainab Rabi'u ubangari sai kuma Abdulsalam Abdul'Aziz shugaba da Amaryar sa Amina Ahmad Adara, d'auren auren da ya samu halaktan manyan mutane daga nijar har nigeri'a tabbas yan uwan zainab sun nuna mata gata a bikinta. Bayan d'auren Auren ne mahafin Ammar ke wa yusuf zancen khadija, wanda yace sai dai aje nijar ayi batun Auren tunda canne mahaifarsu kar yan uwa suga ana musu wariya. Su sumayya da muhammad harda khadija ayau sukabi gida gidan yan uwa domen musu sallama, washe gari taje abuja tama mahaifiyarta sallama zasu tafi nijar wajen dangin mijinta, kuma daga wajen zasu wuce America. Ayau ne sumayyya dasu khadija da mahmah tare da tawagar sarki da Amaryar sa,suka nufi nijar, sun samu kyakkyawar tarba, saidai fa sumayya ta fuskanci sauyi a wajen nabila wanda hakan yasata shawa nabila mur, ganin duk lokacin da taga Al'ameeen zatana wani kwarkwasa shikam baima nuna yasan tanayi ba, ga lawiza da kishi ke cinta, Amma dai ta kwantar da hankalinta ganin yanzun tana samun kulawa a wajen mijinta fiye da da. Nabila tayita nacewa mahmah akan zancen ta da muhammad, wanda abin yasa mahmah tarar yusuf da zancen, kai tsaye yace mata, mahmah banki bin umurnin kiba amma mama inkin duba duk abubuwan da suka faru Nine na fata ballo ruwan, da ace nayi biyayya ga mahaifina da duk abinnan bai faruwa ba, duk da bawa baya wuce kaddararsa mama bazan iyyama muhammad wannan zancen ba,A tausayawa yaron nan yasha wahala A rayuwar sa yanzun lokacine daya kamata Ya huta, duba da irin halakcin da yarinyar nan ta masa bata cancanci haka ba, in shine ya taso da zancen aure bazan hanasa ba, Amma mama bazan iyya tikasta masa ba kiyi hakuri bawai don yana d'ana ba, zaki iyya tuntubarsa duk Abinda ya yanke shikenan. Jikin mahmah yayi sanyi kuma taji shawaran da d'anta ya bata don/a dalilin Auren dole yusuf yasha wahala, hakan yasa bata ma tinkare muhammad da zancen ba. Gidado da badaru dayake ba boko sukayi ba, kuma yanzun sun wuce shiga makaranta, yasa sarki bada umurnin a sasu a islamiyya, da kuma yaki da jahilci koh karatun hausane da turanci su iyya,ya bude musu manyan shaguna a kasuwa,in sunje boko sun dawo sai kuma su tafi shago, asabar da lahadi suje islamiyya. A kasuwa gidado ya hadu da indo kanwarsa na bara, cikin wani irin yanayi ya tisata har inda suke da zama, aiko suna zuwa saida yayi hawaye ganin wani kazamin waje kusa da bola innarsa ke rayuwa gata a kwance ba lafiya ga yarsa cikin datti ,sai abinda indo tayi bara ta sama musu, d'aukar su yayi wanda a lokacin inna koh sanin wake kanta batayi ba. Sarki a washe garin ya tura su saudiya da inna,saboda ciwonta ya kazanta blood Cancer ne, yayinda indo ke zaune a gidan sarki tare da lantana karama. Muhammad da sumayya sun wuce America tare da yaransu suna mai kewar kasarsu da yan uwansu. Bayan tafiyar su akayi auren Gidado da nabila sai badaru da wata yarinya yar tsohowar unguwansu, sarkin shayi ma Yusuf ya had'asa da wata bazawara an had'asu aure. Jikin inna yayi sauki inda sarki yasai musu gida ita da indo da yar gidado , d'aya shashin kuma gidado ne da nabila, dataga ba sarki sai Allah ta aure sa abinta. Su sumayya basu dawo ba saida sukayi shekara d'aya, lokacin auren khadija da Ammar sukazo, khadija tayi weac dayake har lokacin tana Nigeria a abuja wajen hafsa, yayin da yaran sumayya suka cika shekara 1 da watanni a lokacin kowa yaga sumayya da muhammad sai sun basu sha'awa, gaskiya ne mahakurci mawadace, mai hakuri yana tare da riba, sannan duk mai biyayya ga iyaye zaiga Amfaninsa wata rana. Ana bikin Ammar da khadija suka koma wajen aikin Ammar a maiduguri bayan aure ya maidata makaranta, don result nata yayi kyau sosai, su sumayya sun koma America bayan biki. *************** Bayan wasu shekaru......... Wani matashin magidanci ne tsaye a wani hadedden compound mai d'auke da shuke shuke mai ban sha'awa, sanye yake da kakin sojoji a jikinsa wandone da riga, kansa ba hula sai gashinsa dake kwance baki kirim yana sheki, yayi farine tas yayin da idanunsa ke d'auke da bakin glass, dukar da kansa yayi yana kallon agogon sa mai masifar tsada, dake hannunsa d'an yamutsa fuska yayi hade da dan sakin tsiririn tsaki,ganin 7:21pm Amma har yanzun gimbiyar tasa bata fitoh ba bare yaransa, jin karan bude kofar falonsu da akayi yasa sa saurin d'agowa. Sanye take da siket baki mai kauri yana nan kamar pencil Amma ba'a tsaga baya ba,sai takalmi mai tsini a kafarta dake d'auke da socks baki, shirt ne a jikinta white mai botur da dogon hannu, wanda tayi stokin dashi, Have sunnah ne a wuyanta baki, da agogo fari a d'aure a farin tsintsiyar hannunta, sai jakan office dake rataye a hannunta d'aya Tabar daya hannun na lilo, fuskar nan nata yayi fayau babu kwalliya alamu dai jin dadi ya samu waje, rike take da wani kyakkyawan yaro fari yana sanye da uniform na primary bazai wuce shekara 5 ba, ga wani yaron na binta a baya zaikai 7 shima yana sanye da uniform hannunsa d'auke da jaka d'aya hannun kuma lunch-box nasa. Da sauri ta kara hanzartawa ganin fuskar mijin nata a hade, don tasan tabbas sun sasa jira don yau dai sun makara. Yanzun ke kullum in zamu tafi aiki da safe sai kin sani lettin kike jin dadi, ki duba yanzun minutes 30 ina tsaye ina jiranku? "Don Allah kayi hakuri dear wallahi neman socks in na'ima nake wai bataga d'aya ba" Toh surutun ma ai ya cinye lokacin daya saura manan, yace yana kamo yaron dake hannunta ya bude seat back ya ajesa, kallon mai shekara bakwan yayi, Au kaima salim(takwaran salim marigayi, muhammad ya hana a masa inkiya yace a barsa da sunan sa)so kake na d'aga kane koh me? kana tsaye. Washe fararen hakoransa yayi cikin dariya ganin yau ran baban nasu a bace, yace, sorry Dady. Shiga gaba sumayya tayi ta aje jakanta akan cinyarta da mamaki Al'ameen yake kallonta, wai sumayya ina sauran yaran ne? "Au wai basu shiga bane tare fa muke futowa dasu" Kinsan Allah sumayya yau in kikayi tsiya sai kija mota da kanki tunda dai naga kowa nada shi, ya fad'a a hankali yanda yaran bazasu ji ba. "Kayi hakuri toh" kawai tace tana fita a motar daidai lokacin wasu yaran mata da zasukai shekara 10 masu tsananin kama da juna, gasu kyawawa sanye suke da uniform suna gudu da school back a hannu d'aya nabin d'ayar da gudu. Da sauri sumayya ta kalli wance ake binta da gudun, tazo ta makale a bayan Dadynsu,"Na'ima mekika mata"? Momy wallahi babu abinda na mata. Kallon na'ifa dake hawaye a gefenta tayi, tana tsaye batabi na'ima bayan dadyn sun ba" meta miki kika biyo ta"? Wallahi momy colour nata d'auka guda hudu, kum drewing zanyi dashi fa. Ke na'ima ina naki colour da zaki d'auka mata nata? Dady toh banga nawan bane bafa. Da sauri sumayya ta karbi maganan jin Amsar data bawa muhammad"Daman ke haka kike kome naki ba'a gani, kina ganin da safen nan harkin batar da socks naki daker na gane inda kika aje, kome naki baya lastic wannan biro in aka saima yar uwarki sai yayi 1 month tana amfani dashi, amma ke koh kwana bayayi sai kice ba pen ah ah pen ya bata, don haka oya bata colourn ta koh na saba miki"? Ba musu ta bude jakanta ta mikawa na'ifa abinta, sai kuma ta fashe da kuka. Muhammad dake tsaye ne ya dubeta, toh wai kukan na menene? Dady kuma fa bangama drewing ba gashi uncle yace duk wanda baida colour waje zai korasa bazai masa makin ba. Ina dai akan colour ne?muhammad ya tambaye ta. D'aga masa kai tayi alamun eh. Toh muje a hanya saina sai miki sabo koh?yanzun ku shiga mu wuce mun kusa makara. Dady nimafa bani da calculator? "Da sauri sumayya ta dubi yaron ta, kaji tsoron Allah khaleefa(yusuf) ba jiya naga calculator a jakan ka ba" Momy Abokina kullun sai uncle ya bugesa wai bayida calculator, shine na tambayesa mai yasa ba'a saya masa ba, wai Auntin sa(step mother)in dadynsa ya basa kudin saita kwace, shine na basa kyautan nawa jiya. "Masha Allah yaron kirki haka nakeso Allah ya muku Albarka" Gabaki d'ayansu suka Amsa da Ameeen . Jan motan muhammad yayi mai gadi ya walgale musu makeken get nasu suka fice. Sai da suka bi ta bookshop ya sai musu abinda suke bukata, yaran ya fara saukewa a school, kafun ya kama hanyar bank da sumayya, tun a hanya ta makala ID card nata a wuya, suna isa bank ta sabi jakanta sukayi sallama ya wuce wajen aikin sa. Misalin karfe 4:30 na yamma muhammad ne zaune a office yana aiki, yaji ring na wayan sa kamar bazai d'auka ba don aiki yake mai muhimmanci,d'auka yayi yana kallon mai kiran nasa da sauri yayi picking yasa a kunne,Assalamu Alaikum Ta d'aya bangaren Ammar ya Amsa wa'alaikumu salam, Captain muna fa Airport azo ya d'auke mu. Da sauri muhammad ya mike cikin mamaki yace What? kana nufin kun shigo Lagos koh note's babu? Surprise muke son muku. Amma gaskiya ka kyauta gamunan zuwa, suna yanke wayar neman wayar sumayya yayi ya kirata sumayya dake zauce akan kantan customer care tana aiki taji wayanta na ringing d'agawa tayi tasa a kunne ganin sunan maikiran nata, "Hello Rabin Raina" Hello sweetheart kin koma gidane? "No Rabin Rai yanzun nake kokarin fita, musa driver na haraban bank yana jirana" Ok kice masa ya wuce dasu salim, ke ki jirani ina zuwa? "Lafiya dai naga kace mini yau sai 6 zaka dawo kana da aiki"? Lafiya yanzun Ammar yake sanar dani sun shigo lagos suna Airport. Ok saika zo tace tana yanke wayar, number musa driver ta kira ta shaida masa ya wuce kawai gida, sannan yacewa bahbah(tsohowar mai Aikinsu)ta kara wasu abubuwan cin zasuyi baki. Ba'a jima ba da wucewar musa saiga muhammad jakanta kawai ta d'auka ta shiga motarsa suka wuce Airport, suna isa Jakanta sumayya ta bude ta zaro Abayan ta sakawa tayi daman akwai have sunnah a jikinta dukansu suka sauka a motar waya Al'ameen ya d'aga ya kira Ammar. Tsaye suke suna duduba masu fitowa, daga nesa sumayya ta hango Khadija da katon cikinta a gaba tayi kyau kamar ba khadin goggo ba hutu dajin dadi sun ratsa ta, sai Ammar dake rike da hannun yaran su biyu mace da namiji,macen baka kamar babanta sabanin na mijin dayake fari, da sauri sumayya ta dagawa Khadija hannu da sauri suka karaso garesu da gudu, yaran suka rungumi muhammad suna masa oyoyo uncle da murna suka tattaru sai gida. Suna isa gida suka samu yaransu a tsakar gida, bahbah ta musu wanka, suna zazzaune a gaban malamin su dake can gefen flowern tsakar gidan, ai lokacin da suka gu momynsu ta sauko a mota da Ummi(khadija)gasu Amira(Aisha) da mukaddas yasasu rugawa da gudu suka nufesu da gudu, duk irin kwala musu kira da ustax keyi, ina sunyi gunsu da gudu da sauri suka rungume yaran suna murna. Koran su sumayya tayi hardasu Ameer suka wuce wajen karatu, tace sai ustax ya tadasu sai su shigo duka. Suna shiga cikin part daban sumayya ta sauke su khadija da mijinta, ta basu waje su kimtsa itama d'aki ta shiga ita da muhammad. Bayan mangariba zaune suke akan daining dukansu suna cin Abinci, Ga yaransu a zazzaune Suma ana ci dasu, hira ake na yaushe gamo, kallon sumayya khadija tayi. Aunty Gaskiya shagunan ki sun habbaka last months munje jalingo, nida maimuna mukaje shagon gaskiya nasha mamaki ganin harda saloon ga gyaran jiki duka? "Wallahi kuwa khadija kinsan yanzun shago hudu nake running Na make-up saloon gyaran jiki, lalle kuma gaskiya Alhamdulilh matar shagari na iyya kokarinta yarinyar ta burgeni akwai Amana" Gaskiya ne Aunty nima na yaba da nutsuwar Rufaida. "Ai shiyasa na bar mata kula da shagunan a hannunta sannan ita ke iban ma'aikata da masu training". Toh Allah ya kara budi. "Ameen khadija waini ina labarin kamila ne"? wallahi aunty tadaiji sauki yanzun ba kadangarun sai daifa Abin ya taba kwakwalwanta. "Toh Allah ya sauwaka,Yajikan momy(safina)da rahama" Ameen suka amsa dukan su,bayan sun gama cin abinci Yaran suka wuce ciki yayinda su sumayya ke hira falo, sallan isha'i sukayi sukaci gaba da zaman falo ana hira. Da gudu Na'ifa take saukowa daga upstair hannunta d'auke da system in sumayya tana kwala mata kira ga sauran yaran na binsu baya. Da mamaki sumayya ta kalleta ganin vedio call suke da mutanen nijar, karban system in tayi ta aje musu akan center table dake falon, duk suna zazzauna akan kujeran da take gaisawa suke da su nabila indo Aunty zainab da nana(Aisha takwaran mamansu muhammad)sai muwaddat dake rike da sabuwar jaririya a hannunta, gaggaisawa suke tare da mata barkar haihuwa akan basu samu zuwa ba cikin khadija wata 8 amma insha Allah zasu zo auren muhibbat. Bawa su muhammad da Ammar system in sukayi suma suka gaisa da yusuf dake cikin iyalansa cikin farin ciki don yara biyu zainab ta haifa masa Aisha da muhin, sosai akayita hira harda mahmah data kara tsufa sosai ga lawiza duka don yau akayi sunan muwaddat duk suna hade. Sai kusan 9 sukayi sallama khadija da mijinta sukayi part da suke sauka in sunzo, dayake yaransu dasu Na'ima zasu kwana, had'a kansu sumayya tayi har bedroom na maza wanka ta musu dukansu tasa musu kayan bacci ta kwantar dasu, tufa masu Addu'a tayi taja musu kofa, d'akinsu na'ima ta shiga ta samu har suma sunyi wanka dasu Amira dayake duk zasu iyya ma kansu, Addu'a tasasu sukayi ta rufe musu kofa bayan ta tabbatar sun kwanta. D'akin ta ta shiga, wanka tayi ta sanya wani d'an iskan kayan bacci riga da wando jikinta sai kamshi yake ta wuce d'akin mijinta, tura kofar tayi da sallama ta shiga. Zaune yake akan gado yana aiki a laptop ganinta yasa sa kashewa ya aje akan drowern gado ya zuba mata ido ganin irin kyaun da ta masa. Da sauri sumayya ta karaso garesa faduwa tayi a kansa wanda yasa dole ya koma kan gadon suka kwanta, yayinda yake kasa tana samansa fuskar su ya hade waje d'aya Cikin kasa kasa da murya yake mata magana, wai Rabin Raina menene sirrin ne kullum dad'a kyau kike kamar yau Aka kawo mini ke?yana maganar yana mammatsa mata jiki. Murmushi sumayya tayi sai kuma ta tuno wani abu cikin dariya tace,kai menene haka? Dariya ya sake tuna masa da ranan su na farko, shima Amsa ya bata, yi hakuri gado nake nema zan kwanta ne? Itama ta sake basa Amsa, wallahi bazan kwanta dakai gado d'aya ba gadai kujera acan jeka kwanta. Gabaki d'ayansu dariya suka sake a tare cike da farin ciki suke romancing na juna, hannu muhammad yasa ya kamo blanket in ya lulubesu. *Alhamdulil!!!!!Alhamdulilah!!!!!!!! Alhamdulilh!!!!! nagode Allah daya nuna mini wannan rana cikin koshin lafiya, harna kawo karshen labarin matar makaho, duk wanda nama ba daidai ba ina neman afuwarsa* *MATAR MAKAHO FAN'S INA MATUKAR ALFAHARI DAKU, DON DA KARFAFAWARKU NA TAKA WANNAN STEPS DANAKE KAI AYAU, WA'INDA NAGA COMMENTS NAKU DA WA'INDA BANGANI BA WA'INDA NAMA REPLY DA WA'INDA BANMA WA BA, ALLAH YABAR KAUNA INA GODIYA*😃 *SANNAN INA MAI MUKU ALBISHIR HADE DA SANAR DAKU SABON LABARI NA DAKE TAFE MAI SUNA* 🏵 *ALKAWARIN MASOYA* 🏵 *WANDA NAKE DA TABBACI HADE DA YAKININ ZAI MATUKAR KAYATAR DAKU INSHA ALLAH*😎 ✨Ruqeenjalal ke muku sallama✨ Compilied By Abubakar Saleh AlQuyraemey Whatsapp Number 08138873799 Visit www.rumbunlabarai.com For More Complete Documents