********************** ⬇ ************************** ************* Ai Hausa Novels **************** *************************⬆ ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ⬇ ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ⬆ ************************** Gargaɗi ban yarda wani ko wata su juyamin wannan labari ta kowani siga ba, ko kuma a karantashi a youtube channel. Labarin Tsohuwar Soyayya hakkin mallakar Azizat Hamza ne. *TSOHUWAR💖 SOYAYYA* *©Azizat* Wattpad @000Azee *BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM* Free page *Shimfiɗa* A duk lokacin da soyayya ta zamo tsakani da Allah to haƙiƙa ta na nan har ƙarshen rayuwa. Yanayi zai iya chanjawa, mutane za su iya chanjawa amma soyayya ta na nan a zuciya. Soyayyan da ake yanzu yawanci soyayya ce da ke zuwa da buri da ado da ƙyale-ƙyale. Kuɗi,kyau, su suka fi zama jagora a soyayyar yanzu. Ɗan maikuɗi sai 'yar maikuɗi. Ɗan mai mulki sai 'yar mulki shi ne abinda mu ka samu tun zamanin kaka da kakanni. Bature shi ne wanda ya fara watsar da wannan al'ada ta yanda indai soyayyace ta asali to ba ruwansa da kuɗi ko sarauta. Misalai na nan da dama kamar auren Prince William da Kathrine, prince Harry da Meghan. Ku duba auren Mark Zuckerberge da Priscilla chan, Bill Gates da Melinda.  Aure ne da su ke yi saboda soyayyar asali. Amma idan ka garzayo ƙasar mu Nigeria maimakon abin ya ragu to abin ƙaruwa ya ke. Duk min kyan ki/ka idan zuri'ar ku ba naira to fa sai dai ki auri mutum mai dama-dama amma asalin ƙusosin ƙasa masu kuɗin kuɗi, sai dai ki gansu ko ka gansu a talabijin ko jarida da kuma yanar gizo. Haka nan masu dama-dama ɗin ma ba son raɓan talaka su ke ba kowa ya na son upgrade. Wannan labari ƙagagge ne idan yai kama da rayuwar wani/wata/wasu to anyi shi dan a faɗakar. Ba wanda ya fi ƙarfin ƙaddara da kuma hukuncin Allah. So whatever happens it's destined already. I promised you, this story will make you smile,laugh, cry but most importantly it will make you ponder. And you wont regret investing your time, strenght and money in to this journey. *Follow me as i take you on a journey, a journey of true love.....* 0️⃣1️⃣ It's 2018 Wajen liyafar ya cika da mutane musamman ma'aikatan BBC Hausa harda ma na sashen BBC English. Familyn Bulama su na nan a wajen 'ya'ya da jikoki. Musamman wanda dama su na London a wannan lokaci ko kusa da London ɗin. Wanda su ke nesa ma sun zo, saboda Mom Aaliyah ta kowa ce. Ta na zaune aka kira sunan ta *Aaliyah Badamasi Bulama* ta taso ta na murmushi wanda ya ke ƙara sanyawa fiskarta alhini. Ta je wajen podium ɗin ta ƙarɓi award da aka bata sannan ta amsa mic ta yi jawabin godiya da Hausa sannan cikin turancin ta na ƙwarewa ta ɗaga award ɗin ta ce "this is for my husband Ahmad may his soul rest in Jannah Amin" Hawaye ne su ka ciko a idon ta ta yi saurin sa hannu ta goge tareda barin wajen, tana saukowa aka sa tafi. Da sauri Zaid ya nufo ta ya rungumeta yayinda sauran 'yan uwa su ka fara zuwa ɗaya bayan ɗaya su na ma ta congratulations... Wata budurwace da ba za ta fi shekara ashirin ba ta ƙaraso wajen da Aaliyah ke magana da wasu turawa. "Excuse me, can i take a picture with you ma'am?" Aaliyah ta yi murmushi  ta ce "sure"  selfie ta mu su kusan guda uku sannan ta ce "thank you" Kai tsaye wajen da Zaid ke zaune ya na magana da wasu 'yan uwan sa ta je. Neman izinin magana ta yi da Zaid wanda ko kallo ba ta ishe shi ba. A hankali ta ce "plz Zaid ka taimaka ka bani minti ɗaya naka, abinda zan gaya ma ka is very important" "Zaid ka saurareta ma na" inji Hafiz. Ko ɗagowa bai yi ba balle ya amsa ya cigaba da danna waya. Ta fito da wayarta daga cikin purse ta danna kira. Sai ga wayar Zaid ta na ringing, ganin baƙuwar number ya sa shi yin tsaƙi sannan ya ɗauka " Hello" "Hello Aaliyah ce" Sai a lokacin ya ɗago ya kalleta. Kallon a ina ki ka samu special number na. Murmushi ta ma sa sannan ta ce " na san za kuje Nigeria cikin satin nan so i will be waiting for you there" ta wuce ta barshi da mamaki. "And who the hell is she?" ya faɗa da ƙarfi Hafiz ya ce "kai zamu tambaya ai" Tsaki yai dan ya san irin matan nan ne ma su bibiyar sa. "Kai amma fa tanada kyau" inji Rabi'u da ke gefen su. Yarinyar na fitowa daga ɗakin taron kai tsaye taxi ta shiga sai airport. Tun acikin taxi ɗin ta kira Abban ta ta sanar ma sa jirgin su ƙarfe goma sha biyu na dare zai tashi, ya ma ta addu'an Allah ya kawosu lafiya. Tana cikin jirgin ma selfie da su ka ɗauka da Aaliyah Badamasi ta ke kallo. A hankali ta furta ' its now or never' .... Wanka ta yi sannan ta gabatar da shafa'i da wutri, da ta idar ta na jan carbi aka ƙwanƙwasa ƙofar ɗakin. "Come in" ta bashi umurni. Sanye ya ke da silk pyjamas baƙi. Murmushi ta yi ganin ƙwan na ta ɗaya a duniya. "Ba ka yi bacci ba?" Zama yai gefen ta ya riƙe ɗaya hannun da babu carbin ya ce "are you Ok Mom?" Ta ajiye carbin ta sa hannu ta na shafa gashin kan sa mai tsantsi da yalwa. "I'm Ok son, thank you" "Kin missing Daddy ko?" Ta ɗaga kai alamar eh. "I miss him too" ya jima a ɗakin kafin daga baya ya ma ta sai da safe. Ta jima ta na addu'o'i kafin daga bisani ta je ta kwanta. Kwantawanta ke da wuya maganganun Ahmad ya fara dawo ma ta, daren rasuwar shi. *"Na zalinceki Aaliyah, na hukunta ki da horo mafi tsanani ta hanyar rabaki da ɗan ki na tsawon lokaci, ki yafemin. Dont be lonely after my death ki..."* Ta yi saurin toshe kunnuwanta saboda yadda maganar ke tuno ma ta da abin da ta daɗe da binnewa a zuciyarta. "Na yafe ma ka Ahmad, haka ƙaddara ta ta zo" ta faɗi a hankali... .................................... Bayan yai waya da Aaliyah ya ci gaba da kallon program ɗin har sai da aka gama. Ta rame ma sa, haka nan kaman ba ta da lafiya ya ke gani. Zulumin rashin ta da zai yi ya ke. Shekara ashirin da biyar bai taɓa fashin jin shirye-shiryen ta ba tun ta na yi a BBC english har ta koma na Hausa haka nan kuwa a duk lokacin da kewarta ya addabeshi toh programs ɗin ta su ke ɗebe ma sa kewa ya na da record na programs ɗin ta tun daga 1993 zuwa last program da ta yi a farkon shekaran 2018. "I pray you have peace idan ki ka dawo Nigeria Aaliyah" ........................................ "Abba, Abba...." Muryar 'yar ta sa ya doki kunnen sa. Yanzu ya ke shirin fita ya je ya ɗauko ta. Ya fito daga ɗaki da sauri, a stairs su ka haɗu saboda yadda ta shigo gidan da gudu. Ta rungumeshi ta na faɗin "i miss you Abba nah" "Yanzu ke da na ke shirin zuwa na ɗauko ki, sai ga ki" Ta kissing goshin sa ta ce "what's important is that im home now" Ya ɗan ja kunnen ta ya ce  "na hanaki gudun nan ba kya ji ko" "Sorry Abba" ta faɗi ta na murmushi. Kai tsaye ɗaki ta shiga ta yi wanka sannan ta fito a dining ta ga ƙannenta na breakfast sai a lokacin su ka ganta saboda Lokacin da ta shigo gidan ba su tashi a barci ba. Ta joining ɗin su su ka karya tare, su na ci ta na basu labarin bikin da ta je a London... Gaba ɗaya ta gama haɗa kayan ta tun jiya, ita da London yanzu kam sai dai ziyara wanda ba ta tunanin za ta yi shi nan kusa, amma ba dai zama ba. Ta yi murmushi lokacin da ta tuna farkon zuwanta gidan nan. Rayuwa kenan komai yai farko zai yi ƙarshe. Gashi yanzu ƙarshen zaman ta a London ya zo ƙarshen kasancewarta matar Ahmad ya zo. "Mom an gama fitar da kayan?" Zaid da ya leƙo ɗakin ya ke tambaya. "Yes son nima ina saukowa yanzu" Ok ya faɗi sannan ya tafi. A hankali ta ƙarasa wajen  dressing mirror ɗin ta, ta ɗan tura shi ƙasa sai ga wani safe a jikin bango. Ta danna number kamar haka 0108 sai gashi safe ɗin ya buɗe. Wata ƙaramar jaka ce acikin safe ɗin. Ta fito da jakar tareda rungumeta ta na hawaye. Muryan Zaid da ta jiyo ya na bawa ma su aikin gidan umarni ya sa ta yi saurin ɗaukan jakar ta sa acikin handbag ɗin ta, da shi ke handbag ɗin babba ne sannan ba komai a ciki, ya sa jakar da ta cusa ciki ya zauna daɓas. Ta yi saurin goge hawayen ta sannan ta ɗau jakar ta fito. Har su ka isa airport zuciyar ta bai bar bugawa da ƙarfi ba. Haka kawai gaban ta ke faɗuwa. Tun rasuwan Ahmad rabonta da Nigeria wannan kaɗai ya isa ya sa ma ta fargaba musamman idan ta tuno rabuwar ta da Hajiya Inna. Hannunta saƙale da na ɗan ta Lokacin da su ke fitowa daga jirgin. Da mamakin su har lokacin ba su ga wani ya zo tarban su ba. Cikin ɓacin rai Zaid ya fara kiran 'yan gidan na su  saboda rashin mutunci bayan ya riga ya shaida mu su yau zasu taho amma ba wanda ya zo ɗaukan su bayan har Lokacin da za su sauka ya faɗa. "Zaid Ahmad Wamako" ya ji wata siririyar murya ta kirashi Murmushi ta ke mu su har ta iso. Kamar dai ya taɓa ganin ta amma ba zai iya tunawa ba dan 'yan matan da ya gani cikin satin nan kaɗai sun fi ashirin. Ta ƙaraso ta rungume mom, "i'm so happy na same ku da ban san ya zan yi ba." "And who are you?" Zaid ya tambaya da ƙarfi. Ta maida kallon ta ga mom ta ce " mom ni die hard Fan ɗin ki ce, saboda ke na je bikin retirement na ki a london" ta fito da wayarta ta na nuna ma ta selfie da su ka yi ranan. "Ayya, 'yata ya sunan ki?" mommy ta tambaya. "Aaliyah" "Ashe ke takwarata ce,na gode" " mom da alama ma su zuwa ɗaukan ku ba su ƙaraso ba, ki min alfarma na kaiku gida" "Kar ki damu 'yata za su ƙaraso nan ba da jimawa ba" "Plz mom do this for me, ko dan son da na ke mi ki" Mom ta ce " Ok dear" ta kalli Zaid ta ce "mu tafi" "But mom you dont even know h..........." ya katse maganar lokacin da ya ga mom ta fara tafiya da Aaliyah, Aaliyar ce ma ta ke jan akwatin ta. Bayadda ya iya dole dai bin bayansu yai.  Wata haɗaɗɗiyar mota su ka nufa wanda driver ke tsaye a wajen ya na jiran su. Sai da ya ƙaraso wajen ya hango motar gidan su na shirin tsayawa ya cewa Mom da ke shirin shiga motar Aaliyah "Mom ga driver ya zo, barin bi shi" Ta ɗaga masa kai. Har su Aaliyah su ka bar airport ɗin bai shiga motan ba yana tsaye yana zubawa driver masifa. Sun yi nisa da tafiya Aaliyah ta ce "Mom bari ki ji wani surprise" ta bawa driver wayarta ya haɗa da radio ta fara playing wasu recordings. Muryan ta Mom taji a cikin recording ɗin, ba za ta iya tuna shekarar da ta yi wannan program ɗin ba amma ta san ya jima ƙila tun farkon shekaran da ta fara aiki a sashen BBC Hausa ne. Ta sake tabbatar da hasashen ta lokacin da ta ji muryarta na kiran *"shiri ne wanda ni Aaliyah Badamasi Bulama zan gabatar"* Aaliyah ta katse record ɗin ta kalli Mom da idon ta ya cicciko da hawaye ta ce "you are surprised ko?" "A ina kika sami wannan?, inada tabbacin sanda na ke gabatar da shirin nan ba a haifeki ba" Aaliyah ta yi dariya. "Gaskiya ne Mom, sai dai kamar yadda na faɗa mi ki ni  Fan ɗin ki ce tun ina ƙarama. Na taso da soyayyar ki da son sanin ke ɗin wace ce" Mom ta zaro ido "Dont be surprise mom idan na ce mi ki inada records na duka shirye-shiryen ki tun lokacin da ki ka fara aiki har zuwa ƙarshen program ɗin ki a gidan radio" ta yi wani ƙayataccen murmushi ta ci gaba " ku masu aikin gidan radio ai farin jini gareku. Zazzaƙar muryarki mai sanyaya zuciya. Kar ki sha mamaki idan na ce mi ki takanas saboda ke aka sa min suna Aaliyah" "Wow! I'm speechless dear" Aaliyah ta cigaba da kunna ma ta records ɗin  wanda Mom ce ta buƙaci hakan. Ta na ji ta na tuna Lokacin ƙuruciyar ta a wajen aiki da kuma girman ta. Muryar dai idan ba ka lura ba ka iya cewa bai chanja ba iya waɗannan shekaru sai dai fa ita ma'abociyar muryar ta chanja sosai girma ya kamata, shekaru ashirin da biyar ba wasa ba ne, shekaru biyar a sashen Turanci sai shekaru ishirin a sashen Hausa. *Tsohuwar soyayya labari ne mai ɗaukan hankali cike da darussa na rayuwa. Labari ne da ba za ku so ya wuce ku ba. It's a different journey entirely, different from mutum mugu ne, duk kyan namiji da sauransu. Labari ne da ya zo da salo na daban wanda sai wanda ya karanta zai san the journey is worth investing in.* *ga mai son cigaban labarin zai biya #200 kacal ta wannan account ɗin 3099546325 Azizat Hamza, firstbank. Idan kuma credit card ne to MTN card na 200 za a turo wa wannan numbar 08137311900. Sannan za turo shaidar biya (screenshot) na kuɗin zuwa numbar nan still 08137311900. Ko kuma ka biya #300 ka samu labarai guda biyu wato tsohuwar soyayya da sakatariya ta* *TSOHUWAR💖SOYAYYA* *©Azizat* Wattpad @000Azee *BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM* Free page 0️⃣2️⃣ find the diary Har su ka iso tangamemen gidan, Aaliyah ba ta bar yiwa Mom magana akan aikin ta ba tareda ba ta wasu bayanai a kan ta, wanda ba kowa bane ya sani. Like makarantan da ta yi tun daga primary har masters na ta. Like exact date and day da ta yi aure har kalar kayan da ta sa ranar da aka yi wushe-wushen ta a Maiduguri thirty years ago. "Who are you Aaliyah?" Mom ta faɗi lokacin da motar ta tsaya a farfajiyan gidan. "Kamar yadda na gaya mi ki i'm your biggest fan Mom. Ina son ki, ina son komai na ki. Infact idan kin bani dama i want to be a daughter to you" "Ina ganin dole mu zauna mu yi magana" Mom ta faɗa sannan ta fita daga motar. Ganin Aaliyah ba ta fito ba ya sa ta ce " 'yata ki shigo ma na" Aaliyah ta yi murmushi ta ce " na san da gajiya a jikin ki, zan zo gobe idan kin huta" "Thank you dear" ta faɗi tareda maida duban ta ga gate saboda buɗewa da akayi. Motar da ta ɗauko Zaid ne dan haka ta tsaya saboda su shiga gidan tare. Sai da Zaid ya fito daga motar sannan Aaliyah ta fito da sauri ta ce "Mom idan ba za ki damu ba barin yi magana da Wamako" "No problem dear" Ta ƙarasa wajen Zaid da ya haɗe rai ganin ta nufo shi. "Plz Wamako give me two minutes" "Na san maganar ba za ta wuce barar soyayyata ba. Kar ki ɓata bakin ki dan ba za ki samu ba" "You guessed wrong, Zaid ka taimaka ka bani lokaci mu yi magana, there's something you need to know about your mother" " rubbish"  ya faɗi tareda barin wurin. Murmushi Aaliyah ta yi sannan ta wuce wajen motar ta saboda Mom ta bar wajen. "My prince mi daughter ke ce ma ka ne na ga ka haɗa rai?" " she's just like the rest, she's crushing on me" "Amma kamar ba haka na ke gani ba" Ya kama hannun Mom ya haɗa da na shi ya ce " manta da zancen ta, she's a nobody"... Kamar yadda ta tsammanta hakan ne ta faru kallon kirki ba ta samu a wajen Hajiya Fatimah ba balle ta samu tarba mai kyau. Sashen Hajiya Inna da su ka shiga ma abu ɗaya ne nan kam maimakon shiru Inna sai da ta zageta tatas kamar yadda ta saba. Zaid da ya ke ƙoƙarin kare Mom ɗin ne ya sa abin yai sauƙi. Ɓangarenta na nan yadda ya ke ba abinda aka chanja. Gyara shi kawai aka yi saboda ƙura. Ta zauna gefen gado maganganun Hajiya Inna na ma ta yawo a ka. *" ashe za ki iya takowa gidan nan, ai na ɗauka daga chan gidan ku za ki wuce tunda Ahmad ya rasu, alaƙa ta yanke. Tsabar sheɗanci yaushe Ahmad ya rasu amma za ki gama aiki wai har wani dinner ki ka haɗa ki na wani bubbuɗa haƙora irin ga ki bazawara ko. To wallahi indai zawarci za ki yi ba anan gidan ba kije chan cikin dangin ki ki yi...."* "Mom are you Ok?" Muryan Zaid ya dawo da ita. Murmushi ta ma sa. Ya ƙaraso ya durƙusa a gabanta ya riƙe hannunta biyu. "Mom kar ki damu da maganganun Inna. She's old and crazy" "Kakar ta kan" ta faɗi tana dariya. "Yeah she's crazy" Dukkan su biyu su ka sa dariya... ................................... Aaliyah na komawa gida ta turawa Zaid text kamar haka: *dan Allah ka bani dama mu haɗu gobe, we really need to talk. Aaliyah* Ta na gama tura text ɗin Abba ya leƙo ya ce "princess zan fita, ba zan dawo da wuri ba kar a yi lunch da ni" "Ok Abba" Ta na tsammanin reply ɗin Zaid amma har yamma shiru. Ta sake tura ma sa wani text ɗin amma still bai yi reply ba. Ta kirashi ya ƙi ɗauka. Ta na zaune ta na karatun ƙur'ani Nusrat ta shigo ɗakin da gudu. Ta na zuwa ta faɗa jikin Mom. "My Mom ashe kin dawo, mun kalle ki a Tv ni da su Inna da Mummy ranan. I miss you" "Oh I miss you too dear" Kallon yarinyar ta ke yi wanda kamannin Ahmad gareta. "Mom ina Yaya?" "Ina ga yana part ɗin sa ki duba shi acan" "Mom kar ki gayawa Mummy na gaya mi ki, ranan Inna ta ce kar kowa ya shigo wajen ki, wai idan ki ka gaji za ki tafi. Mom ina ba za ki tafi ba ko?" Ta girgiza ma ta kai. Sai da Nusrat ta fita sannan ta sauke nannauyan ajiyar zuciya. Abin ya kai haka ta faɗi a zuciyar ta. Saboda Zaid za ta zauna anan, saboda shi za ta shanye ko me za a ma ta... Sai da ta shirya za ta kwanta text ya shigo wayarta ta duba baƙuwar number ce ta karanta text ɗin, saƙon bangajiya ne sai daga ƙarshe aka rubuta yours Aaliyah. Ta yi murmushi sannan ta kira numbar su ka sake gaisawa da Aaliyar. Ta rasa dalilin da ya sa lokaci guda yarinyar ta shiga ran ta... *"a duk inda ki ke, a ko wani lokaci, a ko wani hali, duk min rintsi, ina son ki Aaliyah, har ƙarshen rayuwa ta, har ƙarshen numfashi na a doron ƙasa. I will forever love you Aaliyah"* Waɗannan kalmomi su ne abu na ƙarshe da ta tuna kafin ta yi bacci. Washe gari ba abinda ya chanja ba wanda ya zo wajen ta ita ce dai ta je ta gaida Inna sannan ta duba Zaid a part ɗin sa wanda bai jima da tashi daga bacci ba. Gaisawa su ka yi sannan ta wuce ɓangarenta. Kitchen ta shiga dan ta nemi abinda za ta ci saboda jiya haka ta wuni da yunwa sai dai ba kayan abinci a store ba komai a kitchen ɗin sai kitchen utensils. Ta fito ta zauna a falo ta na tunani. Wayar ta ya shiga ringing a ɗaki ta yi sauri ta je ta ɗauko ta ga numbar Aaliyah ce kafin ta ɗauka wayar ta katse. Ta yi saurin kiran ta "Hello Mom ina cikin gidan ku ki aiko a shigar da ni" " tsaya zan zo da kai na"  ta faɗi sannan ta shiga ta sa hijab ta fito. Motar jiya ne ta kawota. Aaliyah na ganin mom ta fito ta yi saurin fitowa daga motar ta na murmushi. Ta ɗauko basket a cikin mota sannan ta nufi wajen Mom. Da murna ta tareta su ka shige cikin gidan. Kai tsaye falo su ka zauna. "Sai ga ki da safe na ɗauka sai yamma za ki zo ai" "Mom wallahi Abba ne yai ma na breakfast shi ne na ce dole sai na kawo kin ci kin ji girkin Abban mu" "Kai kai Aaliyah da rigima, shine tun daga gida ki ka taho da shi" "Yes Mom i have to. Kin san Abba na shi ne number one fan ɗin ki in this whole world" "Kayya, to na gode" "Hope ba dai kin karya ba dan dayawa na kawo saboda mu ci mu ƙoshi" Mom ta yi murmushi. "Mom ina ne kitchen na ɗauko ma na plate da cups" Mom ta tashi ta ce "barin ɗauko" A falon su ka baza kolin sinasir da miyar taushe da su ke ci wanda miyan ya ji nama. Sai da Mom ta kurɓi shayin da Aaliyah ta kawo ta ji wani abu ya tokareta. Aaliyah ta ce "you dont like it?" "No, shayin nan kamar..." sai kuma ta yi shiru "Abba ya iya haɗa shayi, this is his favourite recipe, he calls it Aaliyah's tea. He'd being making it for more than 30yrs now" "Aaliyah mi ye sunan Abban ki?" Mom ta tambaya. Aaliyah ta san anzo wajen but this is not the right time dan haka ta ce " Sani, Aaliyah Sani suna na" Ajiyar zuciya ta yi sannan ta ce "Oh that's nice, ki ce wa Abba ya iya haɗa shayi" Su na cikin cin abinci ya shigo falon da sallama. Mom ce ta amsa ma sa yayinda Aaliyah ta shagala da kallon sa. Sanye ya ke da baƙin jeans three quarter da farar vest, gashin kan sa a kwance lub-lub sai sheƙi ya ke yi. "And what are you doing here? Ba dai a nan gidan ki ka kwana ba?" Sai a lokacin Aaliyah ta yi firgigit da kallon sa. "Mom i dont like this, daga haɗuwa da yarinya kin shigo da ita gida har kuna cin abinci tare. What if she's a spy" Mom murmushi ta yi ta ce " kai da za ka tayani murna na samu daughter sai ka hau fishi, haka ake yi" Ya harari Aaliyah ya ce "yarinya ƙarama da ke sai shegen shige-shige" "Eliza,Eliza" ya fara kira da ƙarfi. Mom ta kalleshi ta ce " Son lafiyar ka kuwa, wace Elizan kuma ka ke nema?" "Mai aikin ki ma na, ko ta fita ne?" Hmmm kawai Mom ta ce ta ci gaba da ƙurɓan shayin ta. Aaliyah ta kalli Zaid da ke rarraba ido ya na kallon Mom ta ce " ni da Mom ne kawai a wajen nan tun ɗazu ba wadda ta shigo" "This people are trying my patience abi" ya faɗi tareda yin hanyar waje. Aaliyah na jin shi ya na kiran sunan ma'aikatan gidan. A tsakiyar main parlour ya tsaya ya na masifa. "Dan Ubanki Eliza jiya ban ce ke za ki dinga kula da ɓangaren Mom ba. What the hell are you still doing here?" "Oga...." sai kuma ta yi shiru "Talk" ya daka ma ta tsawa. "Ni ne nan na ce kar wanda ya shiga wajen Aaliyah" muryan Inna ya doki kunnen sa. Ya juyo a fusace ya ce "Inna mi hakan ke nufi?" " hakan na nufin idan ta na son mai aiki, ta kawo na ta, amma wanda su ke nan ba wanda zai yi ma ta bauta" " interesting" ya kalli Eliza ya ce " je ki ɗakin Inna ki haɗa ma ta kayan ta she's leaving this house" "Zaid kana da hankali kuwa" Hajiya Fatima da fitowar ta kenan ta faɗi. " listen old woman, gidan mijin ki ya na Sokoto Idan bai mi ki ba akwai wani gidan sa a Wamako ki je chan ki zauna ki yi iko yadda ki ke so. But this house is my fathers and he built it for my Mom so ba ki da hurumin aiwatar da doka a gidan nan. Idan ba tsofin zamani ba ma da shegen son duniya ke da ɗanki ya mutu mi ya kamata ki yi banda ki koma ƙuryar ɗaki ki na nema ma sa gafara tareda ke kan ki amma banda tada fitina ba abin da ki ke yi a nan. Look ni Zaid ba zan lamunci cin mutunci daga wajen kowa ba, duk wanda ba zai kyautatawa mahaifiyata ba to zai iya tattara kayan sa ya bar gidan nan. And that includes you Anty" yai maganar ya na kallon Hajiya Fatima. "Innalillahi, yanzu ni Zaidu za ka ciwa mutunci. Abinda Aaliyah ta ce ka ma na kenan?" ta ƙarasa maganar tana goge hawaye. Zaid ya ƙaraso wajen ta ya ce " ki yi kuka yadda ki ke so ɗanki ya mutu. Ni tawa uwar ta na nan da ran ta and i will always protect her. Idan wani ya yi ƙoƙarin ƙuntata ma ta i promise, ko waye sai na yi maganin sa" " ka san dai ba kai kaɗai ke da dukiyar ba, na ga da shi ka ke taƙama" Anty ta faɗi Dariyar rainin hankali yai sannan ya ce " to waye matsiyaci anan. Aaliyah Badamasi Bulama dai ko da ba ta auri Ahmad Wamako ba ta gaji arziƙi idan ba ki san tarihi ba Inna ta sanar da ke" "Zaid ni ka ke cewa matsiyaciya, kai Allah ya jiƙan rai" ta fashe da kuka. Kallon ma su aikin da su ka tsaya cirko-cirko a wajen yai ya ce "Eliza ke da wannan ku wuce wajen Mom and, idan ku ka ƙara barin wajen ta. I will deal with you mercilessly. Now get the hell out of here!" Gaba ɗaya su ka fita da gudu. Ya kalli Anty ya ce " na yadda ba ni kaɗai ke da dukiya ba, amma ki sani this particular house is my mothers, infact zaman alfarma ku ke yi domin a ko wani lokaci tana da ikon koran ku. You can ask Dad's lawyer if you want" ya na faɗin haka ya haye sama. Kwalin taba ya ɗauka ya ciro ɗaya ya sa ta a baki ya ɗau lighter ya kunna. Sai da ya zuƙeta sau uku sannan ya ɗau wayar sa da ke ringing. Yawan kira da kuma text da ta ke mi shi ya sa ya gane numbar. Kamar ba zai ɗauka ba sai kuma ya ɗauka ya na furzar da iskan taban. Shiru yai ya na sauraron mi za ta ce sai dai kuma kafin ma ta ce wani abu ya jiyo muryan Inna ta na faɗa. "Wamako plz come, Mom is crying...." da sauri ya cillar da wayar sannan ya jefa tabar a ƙasa ya take ta ya fita daga ɗakin da gudu... Aaliyah kam yau ta tabbatar da maganar da ake cewa *'the rich also cry'* sai yaushe Mom za ta samu farin ciki, Ahmad Wamako ya rasu amma kuma iyalen sa ba su bar tozarta Mom ba sai yaushe za ta bar wannan ahali wanda ba su san darajar ta ba. " har Zaid zai ce nan ba gida na bane na koma Wamako ko Sokoto. Gidan Ahmad ɗin, gidan ɗa na!. To ki sani, wallahi wani batun Ahmad ya mi ki kyautan gida duk shirme ne. Ke ce za ki bar gidan nan ba mu ba" Kamar wani Mahaukacin zaki haka ya shigo falon. Kallon Mom yai da hawaye ke zirya a idonta. Bai yi wani tunani ba ya kaiwa Inna mari wanda Aaliyah ta yi saurin riƙe hannunsa. Mamaki ƙarara a fiskar Inna da Anty. "Zaid plz dont" Mom ta faɗi a hankali. "Mare ni Zaidu, mare ni, sai na san ka cika tantagaryan ɗan iska" Huci ya ke yi kamar wani mayunwacin Zaki da kakkausar murya ya ce " i swear Inna if you ever insult my Mom again, i will forget the fact ke Kaka ta ce.  Zan mi ki abinda har ki mutu ba za ki manta ba" Ya kalli Anty ya ce " duk ranan da ki ka shigo wannan waje ba tareda izinin Mom ba wallahi a ranan za ki bar gidan nan. Now get out!" "Zaid please, iyayen ka ne" " Ahmad ma kin shanye shi kin juya shi yadda ki ke so balle kuma ɗan da ki ka haifa. Mu na nan da ke Aaliyah" Inna ta faɗi sannan ta juya su ka fita. Mom ta dafe ƙirjin ta da ke ma ta zafi. Mom ya faɗi tareda ƙarasawa wajen ta da sauri. "Mom are you Ok?"  Murmushin ƙarfin hali ta yi sannan ta ce " Zaid dan Allah ka dena ɗaga mu su hankali, they deserve your respect. Bai kamata ka treating na su kamar wasu yaran ka ba" " kafin su samu respect ɗi na sai sun fara respecting na ki Mom" "Ba rin shiga ɗaki i'm having headache"  shi da kan shi ya taimaka ma ta ta shiga ɗaki sai da ta kwanta ya ja ma ta bargo sannan ya fito bayan ya kissing goshin ta. Ya na fitowa ya ga su Eliza su na shiga da kayan abinci kitchen ɗin. Wato tsabar mugunta kayan abincin wajen ma kwashe su a kayi. Kujera ya samu ya zauna ya miƙar da ƙafar sa ya na kallon ceiling. Maganganun Daddy na yawo a ƙwaƙwalwarsa. " Zaid take care of your mother. Iya rayuwar auren mu ban kula da ita ba. I hurted her so much not only me even my family too, ni na raba ta da kai for my own selfish gain. Plz dont let her ever cry again......" "Wamako, Wamako" muryar Aaliyah ya dawo da shi a hankali ya saukar da idon sa a kan ta. Tsugunne ta ke kusa da shi. "Plz ka bani 10 minutes na ka mu yi wata magana mai muhimmanci. Its about Mom" "Minene?" Ya faɗi a hankali "Can we go to somewhere private plz" Ido ya ƙura ma ta wanda ya sanya ta yi saurin janye idon ta daga kallon sa da ta ke saboda tasirin da kallon sa ke yi ajikin ta. " it better be important" ya faɗi tareda tashi tsaye ya ce " follow me" Ba mu su ta tashi ta bi bayan sa. Wajen swimming pool ɗin gidan su ka je. Sai da ya kunna taba ya zuƙa sannan ya ce " i'm listening" Ta fito da wani envelop mai ɗan girma ta miƙa ma sa. "Miye wannan?" "Just look at it"  ta faɗi. Ya buɗe envelop ɗin ya fito da hotunan da ke ciki. hotunan Mom da Dad ne lokacin bikin su wani a wajen dinner wani a wajen wushe-wushe. Shi wasu hotunan ma bai taɓa kallon su ba sai yanzu. "What does this mean?" Ya tambaya ya na kallon ta. Ta miƙa ma sa wani envelop ɗin. Ya karɓa tareda buɗewa hotuna huɗu ne a ciki. Still hotunan Mom ne ta na budurwa amma ta ɗau hoton da wani saurayi wanda da gani kasan hoton masoya ne. Zaid ya ɗago ido ya kalli Aaliyah ya ce " explain" Aaliyah ta nisa ta ce " idan ka lura da hotunan farko za ka ga babu murmushi a fiskar Mom idan ma akwai ba genuine smile ba ne. Amma ɗaya hoton she's completely happy." "And so?" "Zaid, i need to know the complete story, i need to know if Mom still loves that man" "This is bullshit, abinda ya sa ki ke damina da kira ke nan?" "Zaid, ina son ka min wata alfarma. Your Mom has a diary plz find it" "You must be crazy. Personal diary na Mom zan ɗauka in baki saboda kin sha ƙwaya. See, duk wani stupid idea da ki ke da shi you better drop it. Infact kar ki sake shigowa gidan nan" "Zaid, na rantse da Allah akwai babban al'amari da ba ka sani ba a rayuwar Mom, and you really need to know. Ba zan iya gaya ma ka komai ba yanzu saboda ba ni da cikakkan labari amma with the diary we'll know everything" "Aaliyah ki ke ko waye. Tashi ki bar nan" "Plz Wamako find the diary" ta faɗi sannan ta ɗau jakar ta ta bar wajen ba tareda ta ƙarɓi hotunan a wajen shi ba... *Tsohuwar soyayya labari ne mai ɗaukan hankali cike da darussa na rayuwa. Labari ne da ba za ku so ya wuce ku ba. It's a different journey entirely, different from mutum mugu ne, duk kyan namiji da sauransu. Labari ne da ya zo da salo na daban wanda sai wanda ya karanta zai san the journey is worth investing in.* *ga mai son cigaban labarin zai biya #200 kacal ta wannan account ɗin 3099546325 Azizat Hamza, firstbank. Idan kuma credit card ne to MTN card na 200 za a turo wa wannan numbar 08137311900. Sannan za turo shaidar biya (screenshot) na kuɗin zuwa numbar nan still 08137311900. Ko kuma mutum ya biya #300 ya samu labarai biyu wato Tsohuwar soyayya da kuma sakatariya ta* *TSOHUWAR💖SOYAYYA* *©Azizat* Wattpad @000Azee *BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM* Free page 0️⃣3️⃣ Aaliyah and Saeed's diary Tun tafiyar Aaliyah ya ke kallon hotunan, yana yi ya na zuƙar tabar sa. Tabbas ya san Mom da Dad arrange marriage a ka mu su. To dama haka ake yi ai, rich girl for a rich boy. But for thirty years Mom would've fall inlove with Dad ai. Zuciyar sa ya raya ma sa. Amma kuma idan ya tuna maganganun Dad sai ya ga kamar har ya rasu babu soyayya tsakanin su. Anya kuwa? Good 30yrs fah. Ya maida hotunan tareda cigaba da tuno rayuwar su kafin Dad ya ɗauke shi a London. Duk da yana da ƙarancin shekaru amma yana iya tuno wasu events da su ka faru. Ƙarar wayar sa ne ya fargar da shi. Ya amsa kiran ganin wanda ya bugo. "Zaid mi ya faru ne, Fatima ta kira ni tana kuka wai dole a raba gado. What is happening?" Sai da ya zuƙi taba wanda itace ta uku da ya ke sha ya ce " Uncle, abinda ta ga ya fi ma ta kenan. And i'm Ok with it" "A'a Zaid, Ahmad ba zai so haka ba, ka san yaran Fatima mata ne kai ne Ubansu yanzu. Responsibilities na su na hannunka har su yi aure.  Zan zo ranan Friday sai mu zauna a tattauna matsalar" "Ok Uncle" Sai daya ajiye wayar sannan ya tuna ko breakfast bai yi ba. Dama breakfast ɗin zai je yi a wajen Mom ya tarar da badaƙalar da su Inna su ka shiryawa Mom... .................................. Kwana biyu da tafiyan Aaliyah amma kuma ya kasa cire maganganunta a ran shi, musamman idan ya kalli Mom sai ya ga kamar tana cikin damuwa. Idan ya tambayeta kuma ta ce ma sa ba matsala. Yau ma su na cin abincin dare tare amma ya lura a takure ta ke kamar ba ta jin daɗin abincin duk da kuwa ita da kanta ta bada order abinda su Eliza za su girka. "Mom is there something you are hiding from me?" "Ofcourse not son, mi ka gani?" "Mom kamar akwai abinda ke damunki, you always look disturbed. Like you are hiding something very important...." "Zaid" ta katse shi "I'm fine son, yes i look worried saboda yanzu ba da bane, but nothing else" "Mom that night, twenty years ago...." "Zaid!"  Ta faɗa da ƙarfi. "Shikenan tunda bakyason maganan" Ajiye cokali ta yi ta ce " I've lost my appetite" Sai da ta shige ɗaki ya sauke ajiyar zuciya. Ba zai manta abinda ya faru shekara ashirin da su ka wuce ba. He was only eight amma ya na iya tuno komai. Lokacin da Dad ya ɗauke shi daga London kullum sai ya tuna kukan Mom a daren ranar. The screaming, the cries, everything. Maganan Aaliyah ya tuno da ta ce akwai babban al'amari a rayuwar Mom that he needs to know about. "Could it be related to what happened 20yrs ago?" Ya tambayi kan sa. He was only eight years lokacin da ya rabu da Mom and ba ta taɓa neman sa ba.  She stays in London all the while. Ya tuna lokacin da ta zo Nigeria ya ƙi ya je wajen ta. How she kneel and cried.  Hawaye su ka gangaro ma sa. Lallai ne dole ya nemo diary ɗin Mom atleast he will find some answers there... Ta ya Zaid zai tuno ma ta da abinda ta ke ƙoƙarin ɓoyewa iya tsawon rayuwar ta. This is too much for her. Ta sa key ta buɗe drawer, ta fidda jakar da ta jima tana adanawa. "If only you came Saeed, if only you came that day"  ta faɗi hawaye na zirya a idon ta. *"Ke ce zuciya ta Aaliyah, idan na rasa ki na rasa zuciya ta gaba ɗaya" *  ta tuna maganganun sa lokacin da ya sanya ma ta zobe a hannun ta. Ta kalli yatsarta da ke ɗauke da tabon ƙuna. Ko ba zoben a wajen akwai shaidar zaman zoben a yatsar. Gani ta ke kamar yau ne komai ya faru. Da saka zoben da kuma cire shi. "Makhtub" abinda mai duban ya faɗa kenan lokacin da ta tambayeshi. "Zan auri Saeed?" Tambayar da ba za ta taɓa mantawa ba kenan. "Makhtub yarinya, rubutacce ne, ko sama da ƙasa za su haɗu sai kunyi aure. Sai dai....." Ƙaran wayarta ya fargar da ita ta yi murmushi lokacin da ta ga Aaliyah ce. Ta ɗauka wayar ta na murmushi, lokaci guda Allah ya haɗata da yarinyar nan amma ba ƙaramin shiga ranta ta yi ba. ........................... Mom ba ta wajen aka yi zaman saboda Zaid bai ma sanar da ita ba. Idon Hajiya Fatima yai zuru-zuru lokacin da lawyer ya gama bayanin sa. "Wannan gidan da ku ke ciki na Aaliyah ce. Aaliyah, Ahmad ya bawa gidan nan" Gidan da Aaliyah ba ta zauna a ciki na cikakken shekara ba. Ta ya Ahmad zai ma ta haka? Fatima ta tambayi kanta "Hajiya Fatima, ina so ku daure ku yi zaman lafiya tsakanin ku. Idan ki ka cire wannan gida da Ahmad yai wa Aaliyah kyautar sa Aaliyah ta yafe gadon Ahmad. Daga ke, 'ya'yan ki sai Zaid ku kuke da wannan dukiya, kuma idan aka ce a raba kowa yai na sa waje ba za ku ji daɗi ba. Zaid shi kaɗai ne ɗa namiji dan haka ki bashi haɗin kai ya kula da ƙannen sa"  lawyer ya faɗi ya na harhaɗa takardun da ya nunawa su Hajiyar. Da Hajiya Fatima da Inna duk ba wanda ya ce wani abu har Zaid da lawyer su ka fita a falon. ........................... Sai da aka yi sati biyu da dawowar su sannan Mom ta shirya ta tafi Maiduguri. A wannan lokacin Zaid ya samu damar bincika ɗakin Mom. Ya jima ya na dube-dube a ɗakin amma shiru bai ga diary ba. Ya zauna akan gadon ta ya na haki. "Kodai Mom ta tafi da shi Maiduguri ne ko kuma Mom ba ta da diary?" Zuciyar sa ne ya tuno ma sa ɗaya daga cikin drawers ɗin a kulle ya ke da key. Ya tashi da sauri. Ya nemi key ɗin wajen bai gani ba. It's obvious duk sauran wajen ba a sa key ba sai last drawer ɗin definitely akwai abu mai muhimmanci a ciki. Ganin neman key ɗin zai ɓata ma sa lokaci ya sa ya fita dan ya nemo guduma ya kwaɗe, ya san duk rintsi kafin Mom ta dawo zai sa a gyara ba za ta ma ganeba... To his surprise wata jaka ya gani a cikin drawer ɗin. Tsohuwar jaka ce wanda aka yi yayinsu a irin 80's ɗin nan. Ya sa hannu ya ɗau ko jakar tsaftsaf ta ke ba ƙura ko dauɗa a jiki. Sai da ya zauna da kyau a tsakiyar ɗakin sannan ya buɗe jakar. Diary guda biyu ne a ciki sai album. Album ɗin ya fara buɗewa yana ganin hotunan da ke ciki. Hoton farko na Mom ne lokacin tana jaririya sai da ya jima yana kallon hoton kafin ya cigaba da kallon sauran, cikin hotunan da ya ke dubawa ya ga harda wanda Aaliyah ta bashi. Sai daya gama kallon hotunan sannan ya jawo ɗaya daga cikin diary ɗin ya buɗe date ya gani a sama sannan aka rubuta *The beginning* Rufe diary ɗin yai ya kwashe komai ya maida cikin jakan sannan ya ɗau jakar ya fita daga ɗakin... Tana kitchen tareda Abba su na girki ƙaninta Abdul ya shigo ɗauke da wayarta da ke ringing. "Z Wamako na kiran ki Anty" "Abdul ka maida wayar ka ga aiki mu ke zan kira daga baya" ta faɗi tana ƙoƙarin saita nitsuwarta. "Tun ɗazu fa ake kira" Abdul ya faɗi yana miƙa ma ta wayar. Tana amsar wayar kiran ya kuma shigowa. Abba ya ce " ki je ki amsa wayar ki" Haɗiye miyau ta yi ta amsa wayar tareda ficewa daga kitchen ɗin da sauri. Minti biyar sai ga ta ta dawo fiskarta ɗauke da farin ciki. Abba ya kalleta ya ce " waye *Z Wamako*?" "Ehm. Abba ƙawata ce da mukayi makaranta ɗaya. Zainab....Zainab Wamako sunan ta" Kamar faɗin Wamako ya tsikareshi lokaci guda ya furta *Wamako* "Abba ka san wani mai irin sunan ne?" Ya jima bai ce komai ba, hankalinsa ma ba ya wajenta. Sunan Wamako ya taɓo ma sa wani tabo da ke zuciyansa tsawon shekaru. "Abba are you Ok?"' Yai firgigit ya ce " yes, yes princess"... .............................. Ba ta sha mamaki ba da Abba ya amince da tafiyarta amma da sharaɗin  za ta dawo kafin ƙarfe shida na yamma. Ko ba komai za ta samu ta yi abinda za ta yi kafin nan. Driver ne ya kaita har gidan su Nawal. Kamar yadda ta tsara. Da dreban su ya tafi sai ta kira Nawal ta fito da motar ta su ka fita. Har cikin compound ɗin gidan su Zaid Wamako ta shiga da ita, su ka rabu akan za ta kirata. Kiran Zaid ta yi akan ta iso ya ce ta shigo ɓangaren Mom. A zaune ta sameshi yana karanta jarida. "Wamako da gaske ka samu diary ɗin?" Hararanta yai ya ce "idan ban samu ba zan kira ki ne" "Oh. Ina diary ɗin? Ka karanta?" "Aaliyah ki ke ko wace, I dont trust you. Ki faɗamin miyasa ki ke bibiyar Mom ɗina" Ba ta bashi amsa ba sai ta buɗe jakarta ta fitar da wani diary daga ciki ta ce "wannan diary ɗin shi ya sa na san wacece Mom kuma shine dalilin da ya sa na ke bibiyarta" Kallonta yai na wasu daƙiƙai sannan ya ce biyoni. Ɗakin Mom su ka shiga inda ya fito da jakar da ya gani a drawer. Lokacin da ya fitar da abinda ke ciki Aaliyah harda ɗan ihunta. Zaid ya ce "lafiyar ki kuwa" Aaliyah ta ɗan yi gyaran murya ta ce "duk farin ciki ne ya jawo haka"... A ƙasa su ka zauna bayansu na jingine da gado. Nan su ka fara karanta diary ɗin Mom... *TSOHUWAR💖SOYAYYA* *©Azizat* Wattpad @000Azee *BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM* Free page 0️⃣4️⃣ *...........AALIYAH.............* The begining Suna na *Aaliyah Badamasi Bulama*. A faɗin garin Maiduguri suna Bulama suna ne da yai ƙaurin suna,  gida ne da ya gaji dukiya da arziƙi tun Iyaye da Kakanni. Mahaifina Alhaji Badamasi Aliyu Bulama ya fito daga wannan gida mai daraja, ya fito gidan kuɗi kuma ya nemi kuɗi ya samu. A wannan lokaci Alhaji Badamasi yana ɗaya daga cikin wanda su ka ƙara ɗaukaka sunan gidan su saboda yadda Allah ya buɗa ma sa arziƙinsa ya haɓaka sosai. Mahaifina matan sa biyu, da farko ya auri 'yar dangi wato Hajiya Yana sai daga baya ya auri Mariyatou. A lokacin da ya auri Mariyatou yaran su huɗu da Hajiya Yana. Akwai  Bukar, Falmata, Aliyu sai Sanah wacce ta ke 'yar shekara ɗaya a lokacin. Mariyatou wadda kowa ke kira da Amma ƙanwa ce ga Alhaji Aliyu Sise Idrissa wanda ya kasance hamshaƙin mai kuɗi a garin Agadez da ke ƙasar Niger, asalin su Buzaye ne. A yadda labari ya zo mana Mahaifina ya je Niger biki ya haɗu da mahaifiya ta. Kyawunta ne ya ja hankalinsa farat ɗaya. Wadda a take ya sa a nema ma sa ko ita wacece. Kasancewarta ƙanwa ga Alhaji Sise sai abin ya zo ma sa da sauƙi saboda Alhaji Sise abokin sa ne. Wata goma da auren Mariyatou aka haifeni. Kyau da farin fata ta duk daga mahaifiya ta ce. Tun da aka haifeni kuwa Amma ba ta sake haihuwa ba sai dana shekara biyar kafin ta haifi ƙanina Muhammad sannan Usman, Yahya da Musa su ka biyo baya. Mu shabiyu ne a wajen Mahaifinmu. Hajiya Yana na da 'ya'ya bakwai Amma na kuma biyar. Tun tasowata na ke cikin gata, daga wajen Amma har zuwa wajen Baba. Yadda na ke da kyau ya sa kowa ke son ɗauka ta, haka nan koyaushe akayi baƙi Baba zai sa a kawo ni, ina maƙale da shi. Yawan surutu da tambayoyi su ne ɗabi'un da su ka bayyana min tun a ƙarancin shekaruna. Ba na taɓa gani na yi shiru. Hajiya da Amma su na zaune lafiya, Hajiya ta riƙe girmanta a matsayinta na babba hakan ya sa Amma ta kwantar da kai su ke zaman su lafiya tamkar ya da ƙanwa. Babban gida Baban mu ya gina a Maiduguri. A lokacin gidan mu na ɗaya daga cikin gidajen da ake kwatance da su saboda girma da kyau. An wadata cikin gidan da kayan alatu na more rayuwa kuma tsarin ginin gini ne mai tafiya da zamani saboda wasu ƙwararrun turawa ne su ka zana gidan. Parts huɗu ne a gidan na mu, akwai ɓangaren Baba wanda ya fi ko'ina girma, yana amfani da ƙasa wajen ƙarɓan baƙinsa wanda ke ƙunshe da falo biyu  da ɗakuna uku, akwai babban dining room da ke ɗaukan kujeru ashirin, sai sama inda ya ke kwana falo da ɗakuna biyu da ɗakin karatu. Akwai ɓangaren Hajiya da ke ɗauke da falo da ɗakuna huɗu da kitchen, dining da store sai na Amma na ma haka. Bangaren ƙarshe kuma na yara maza ne falo ne da ɗakuna huɗu shima. Chan ta bayan gidan kuma an gina quaters na ma su aiki, sannan akwai garden a gidan wanda aka wadata da rumfuna guda huɗu domin zaman shaƙatawa. Lokacin da aka haifeni da 'yan watanni kaɗan Amma na ta koma makaranta dan haka rainona kwacokam ya koma hannun Jijiɗo matar ɗaya daga cikin masu gadin gidan mu. Jiji kamar yadda na ke kiranta ita ta raine ni kuma ita na fi gani a matsayin uwa, saboda na taso na ga ita ke min duk wata ɗawainiya da uwa ke wa ɗiyar ta. Sabo mai tsanani ne ya shiga tsakanina da wannan salihar mata.  Lokacin da aka yayeni kam daina damuwa ma na yi da Amma na, domin hatta 'yan gidan mu kirana su ke da 'yar gidan Jiji. Lokacin da aka sa ni a makaranta kuwa, a kullum idan na tashi Jiji ce za ta zo ta shirya ni ta bani abinci sannan ta ɗauke ni ta kaini wajen mota inda direba ke jiran mu. Da na dawo kuwa ita za ta cire min kaya ta min wanka ta bani abinci, wani lokaci idan na dawo ban ganta a ɓangaren mu ba to gidan su zan wuce da gudu kamar yadda na ke kiran quarters ɗin su. Ba na taɓa yarda na dawo wani ya min hidima idan ba Jiji ba, duk ranan da Amma ta yi yunƙurin kula da ni sai na fara kuka, wani lokaci har da birgima akan dole Jiji ce za ta cire min kaya ko Jiji ce za ta min wanka ko bani abinci, randa na ishi Amma kuwa har mangareni ta ke yi. Akwai wani lokaci ina shekara shida Jiji ta tafi ƙauyensu lokacin za a yi bikin 'yarta Nana, sati biyu su ka yi achan ba su dawo ba. Cikin sati biyun nan kuwa sai da nayi rashin lafiya mai tsanani, ta kai sai da na kwana uku ma a asibiti. Harta Baba da bai cika zama a gida ba saboda yawan tafiye-tafiye sai da yai kwana biyar a gida yana kula da ni, hakan ya rage min kewar Jiji. Ranan da Jiji su ka dawo kuwa ai a  gidan su na kwana na ƙi komawa ɓangaren Amma na.  Jiji Allah bai ba ta yawan haihuwa ba, yaranta  mata biyu.  Lokacin da aka aurar da 'yarta ta fari ba ni da wayo gaskiya, dan Jiji ta ce lokacin ina shekara uku ne. Ina shekara shida kuma aka aurar da autar ta Nana. Abinka da fulani auren wuri duk aka mu su. Asma'u tana shekara shabiyu aka aurar da ita Nana kuma shauku, duk cikin su ba wanda yai makarantar boko. Bayan bikin 'ya'yanta sai ya zamana ni ne kaɗai 'ya a wajen Jiji, tana sona sosai kamar 'yar da ta haifa a cikinta, hakanan nima ina sonta sosai. ..................... Bazan taɓa mantawa da wannan rana a tarihin rayuwata ba, wata ranar jumu'ah a shekarar 1975 lokacin ina shekara bakwai a duniya. Na dawo daga makaranta ko cire uniform ban yi ba na yiwo gidan su Jiji saboda ban ga Jiji a sashen mu ba. Ina shiga falon su na fara ƙwala sunan Jiji. Sai ganin wani yaro na yi ya fito daga ɗakin su Jijin ɗauke da radion Baffa Manu. Na ƙwalla ƙara na fara cewa "ɓayawo, ɓayawo,...Jiji ɓayawo a gidan ku" na fita da gudu na yi hanyar gate, ban tsaya ko ina ba sai gaban Baffa Manu. Ina haki na fara ce ma sa ga wani yaro ya shiga gidan su ya sace mu su radio. Da farko Baffa Manu bai gane ba sai daga baya ya gane ya fara dariya. Ina cikin yi ma sa bayani sai ga yaron yana tahowa inda mu ke. Na nuna shi da yatsa na ce "Baffa ga ɓayawon nan, ga shi chan da radiyon ka Baffa" Baffa ya kalleshi yai dariya ya ce " ba ɓarawo bane Aaliyah, ɗa na ne" "Ƙarya ne Baffa, ɓayawon radio ne fa" Sai da Baffa ya jima yana min bayani kafin na gamsu ba ɓayawo ba ne musamman ma da na ga wannan yaron da ya zo  miƙawa Baffa Radiyon ya yi. Abinda ban sani ba alokacin shine, wannan yaron ba radiyo ya zo sata ba, ba kuma wani abin daban zai sace ba illa zuciyar Aaliyah. Wannan fari dogo siriri kuma yanƙwanannen yaron ba radiyo ya zo sata ba illa Zuciya ta.... *..............SA'EED...........* Fulani boy Ƙauyen Durum shi ne asalina. Inda aka haife ni, iyaye da kuma Kakanni na. Baffa na ya rasu ina shekara biyu a duniya hakan ya sa lokacin da Inna ta ta sake wani auren aka maidani gaban kaka na Modibbo. Suna na Sa'eed Aliyu Modibbo amma kasancewar sunan Harɗon ƙauyen mu ne da ni shi ya sa ake kirana da Harɗo ko kuma Lamiɗo, yawanci ma anfi kira na da Lamiɗon. Mahaifiyata ba a Durum ta sake aure ba, a Lame mijin da ta aura ya ke, shi ya sa na tashi ba uba ba uwa sai kakanni. A shekarar 1975 Kakana Modibbo ya rasu lokacin ina da shekaru shabiyu a duniya. Kaka na bai haihu dayawa ba, yaran sa biyar, biyu maza uku mata. Baffa Manu shi ne ɗan fari sai Goggo Ma'u, Baffa na sannan Goggo Sadiya da Goggo Aminah. Da farko an shirya zan koma wajen Inna ta a Lame sai kuma Dadda wato Kakata ta nuna hakan bai dace ba kasancewa Innata ba ishashshen lafiya gareta ba, dan tunda ta yi haihuwarta na uku ta ke jinya. Ƙarshe Baffa Manu ya zo ya ɗauke ni ya tafi da ni Maiduguri inda ya ke aiki a chan. Baffa Manu bai da niyyar yin nisa da Durum, sai dai auren sa da Hafsatu (Jijiɗo) shi ya sa ya tattara iyalinsa yai nisa da gida. Baffa Manu ya taso gida ɗaya da 'yar ƙanwar Dadda wacce ake kira da Hebbini. Hebbini ta so Baffa Manu sosai hakanan Dadda ma ta nuna ita ta ke so ya aura. Sai dai shi kam ya jima da fara son Hafsatu kuma baida niyyar auren wata ba ita ba.  Da ƙyar da siɗin goshi Dadda ta amince ya auri Hafsatu, sai dai tunda ta shigo gidan Dadda ta ke takura ma ta. Zagi da habaici ga uwa uba mugunta Dadda ke wa Hafsatu, wanda ko lokacin da ta fara samun ciki sai da ta yi ɓari saboda rashin kwanciyar hankali. Cikin shekara ɗaya da auren Jijiɗo sai da ta yi ɓari sau biyu. Nan Dadda ta fara ƙorafi akan dole Baffa Manu ya auri Hebbini. Shi kam harga Allah ba zai iya ba dan yana son Hafsatun sa sosai. Daga ƙarshe da takura yai yawa ya nemi izini a wajen Modibbo ya ɗauki Hafsatu su ka bar Durum, bai tsaya a Jama'a ba ko Toro ko Bauchi sai ya lula har Maiduguri. Tunda ya tafi sai da ya shekara uku kafin ya zo gida lokacin Baffa na zai yi aure. Da farko Dadda ta yi fishi da shi ta ƙi ma sa magana amma daga baya ta haƙura dan zuri'a ta shiga tsakaninsa da Jijiɗo dan 'yar su tana shekara biyu a lokacin... .................. Wata Ranan Jumu'ah a shekarar 1975 kwana na ɗaya a garin Maiduguri ina zaune akan benchi kusa da Baffa Manu aka yi horn da mota, Baffa ya tashi ya je ya buɗe gate, motar ta shigo farfajiyar gidan. Ina zaune ina bin motar da kallo har ta tsaya. Ba ta gama tsayawa ma da kyau ba aka buɗe ƙofa wata ƙaramar yarinya 'yar shekara bakwai ta fito daga cikin motar da gudu tana dariya, kayan makaranta ne a jikinta ta riƙe ɗankwalin kayan a hannu tana gudu iska yana kaɗa ɗankwalin saboda ba ta riƙe shi da kyau ba. Dariyar da ta ke yi ya bayyana fararan haƙoran ta, haka nan gashin kanta baƙi mai yalwa ya ƙara haskaka fiskarta. "Aaliyah ki tsaya" abinda ɗaya baƙar yarinyar da ta biyo bayan ta ke faɗi kenan sai dai inaaa, yarinyar ko waiwayowa ba ta yi ba gudu kawai ta ke fanfalawa tanayi tana dariya. Haka na bi yarinyar da kallo har ta shige gida. "Lamiɗo je ka ɗauko min radiyo na" Muryan Baffa Manu ta katse ni daga nisan da na yi wajen kallon waɗannan yara... *TSOHUWAR💖SOYAYYA* *©Azizat* Wattpad @000Azee *BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM* Free page 0️⃣5️⃣ *..............Aaliyah.............* A friend "Ai sunum?" na ce da shi lokacin da na matsa ku sa da shi. Kallona kawai ya ke ba tareda ya ce komai ba. "Mi ye sunan ka?" Na maimaita tambayar da Hausa "Aaliyah, Aaliyah ki zo in ji Baba" Muryan Sanah ya doki kunnena. Idan akwai wanda na fi so bayan Jiji to Baba na ne, duk da ba wai muna ganin shi kullum ba ne amma duk lokacin da ya ke nan to ina son kasancewa da shi. Haka na ruga da gudu ba tareda wannan ɗan fulanin ya gayamin sunan sa ba. Lokacin da na shiga gida sai da kowa ya san da labarin ɓayawon radio. Jiji ma da ke goge-goge a kitchen sai da na bi ta na bata labari, ta yi ta dariya. Kamar yadda Baffa Manu ya ce mini ba ɓarawon radio ba ne haka ma Jiji ta ce min. Na ce "to waye shi? Miyasa ya shiga gidan ku?" Buɗan bakin Jiji ta ce "Hamman ki ne ya zo Aaliyah" Zamana da Jiji na koyi yaren fillanci duk da harshe na a lokacin ya fi ƙwarewa a Hausa da Kanuri harta yaren Amma na da ta ke min ba wani ji na ke ba kamar yadda na ke jin fillanci saboda sabo da Jiji. Ita Amma ma munfi yin Hausa da ita. "Hamma na kuma?" na sake tambaya. "Ko ba kya son shi?" Jiji ta tambayeni Ba tareda na san cikakkiyar ma'anar kalmar so ba, ba tareda na san sarƙaƙiya da ke tattare da kalmar so ba na furta " Ina son shi Jiji"... Da yamma da Jiji ta gama ayyukan ta ta ɗaukeni mu ka wuce gidan su. Anan na sa ke ganin yamutsatstsen yaron nan yana zaune a ƙofar gida yana kallon su John da Shina yaran dreban mu da gardener su na wasa. Na zauna kusa da shi na ce " wai kai Hamma na ne?" Bai min magana ba sai ma kallona da ya ke yi. Ganin kallon yai yawa ya sa na kai hannuna na tsokale ma sa ido, na tashi da gudu na shige gida ina dariya. Abinda na tsammanta shine ya biyoni ya dakeni kaman yadda yayuna Bukar da Aliyu su ke idan na tsokale su amma wannan yaron ba abinda yai, bai biyoni ba kuma bai min magana ba. Haka na dinga fitowa ina jan koɗaɗɗiyar rigarsa sai na shige gida da gudu amma ko ajikinsa. Ina cikin haka na ci tuntuɓe na faɗi ƙasa, baki na ya bugi sumunti sai jini. Nan take na fashe da kuka, a wannan lokaci ya taso da sauri ya ɗaga ni yana karkaɗe min jiki na yana faɗin "shannu, shannu ka ji" da gurɓacacciyar Hausar sa. Jin maganan sa a karo na farko ya sa na dena kuka na zuba ma sa ido saboda rashin maganar sa run farkon ganin shi ya sa na ɗauka ko baya magana ne. Jin kuka na ya sa Jiji ta fito da sauri ta ɗaukeni ta shige da ni ciki tana mini sannu. Tun daga wannan rana na samu sabon abokin wasa duk lokacin da na je gidan Jiji. Maimakon da da nake maƙalewa Jiji yanzu wajen Hamma na ke maƙalewa. Ba ya damuwa idan na tsokale shi haka nan ko sau goma zan ce ya goyeni ko ya min doki baya min mu su. Cikin ƙanƙanin lokaci sunan Jiji ya fara ɓacewa a bakina, yanzu taɗi na baya wuce Hamma na Hamma na. Hamma bai cika magana ba amma duk lokacin da na takura shi akan ya bani labari sai yai ta bani labarin shanun su da labarin gona, ko ya bani labarin Rafin da su ke zuwa su yi wanka. Ina son labaran sa, ba na gajiya da su haka nan shi ma ba ya gajiya da maimaitamin labaran a duk lokacin da na buƙata. Duk da ƙarancin shekaruna a wannan lokacin bai jima ba na fahimci Hamma ba ya zuwa makaranta. Duk da kuwa ya ce min a chan ƙauyen su yana zuwa makaranta idan hantsi yai kuma ya wuce kiwo. Nan na fara takura Jiji akan a saka Hamma a makarantar mu. Jiji ta kan ce mini za a sashi amma sai maganarta ya zama ƙanzon kurege. Sai na koma damun Amma na. Hmm ita kan rana na biyu da na kawo maganar da faɗa ta ce min na samu Baba na ba ta son shirme. Haka na fita da gudu ina kuka na wuce sashen Baba amma bayanan, na yi ta zaman jiran shi ƙarshe anan falon sa bacci ya ɗaukeni. Cikin bacci Baba ya shigo falon ya ɗaukeni zai maidani wajen Amma na ya ji na ce "Baba a sa Hamma na a makaranta" Sai da ya kai ni ya ke tambayar Amma na waye Hamma dan shi ya manta wa na ke kira da Hamma. "Ɗan ƙanin mijin Jijiɗo ne da ya ke zama a wajen su" Ta bashi labarin yadda muka yi kafin na je falon sa. Ya ce zai wa Manu maigadi magana akan ya sa Hamma a makaranta. Sai dai abu da ɗan kasuwa zuwa wayewar gari har ya manta wani maganan Hamma. Ni kam maganan na rai na da shi na kwana da shi na tashi. Da safe ma sai da na yiwa Amma magana, ta ce min Baba na ya ce za a sa shi, nan ta ke na fara murna. Sai dai kwana biyu shiru ba maganan makaranta... Da gudu na faɗo falon Baba inda ya ke ƙarɓan baƙin sa ma su mahimmanci. "Baba ba a sa Hamma a makaranta ba" abinda na faɗi kenan lokacin da na ƙaraso wajen sa ba tareda na yi la'akari da baƙin da ke wajen ba. "Je ki Aaliyah za a sashi" "In in" na girgiza kai tareda fara bubbuga ƙafa ina cewa. "Ai haka Amma ta ce, amma ba ka sa shi ba" "Aaliyah!" Ya daka min tsawa nan ni kuma na ɓarke da kuka. "Zo nan 'ya ta" ɗaya daga cikin baƙin ya faɗi. Na kalleshi sosai, ban taɓa ganin sa ba amma kuma murmushin da ke fiskar sa ya sa na ji zuciyana ta yadda da shi. Na yi saurin ƙarasawa wajensa ina goge hawaye ina shan majina. Ya ɗaukeni ya ɗaura ni akan cinyar sa ya ce " wa ki ke so a sa a makaranta" Na ce "Hamma" "Waye Hamma?" "Hamma ɗan gidan Jiji mana" "Alhaji Wamako ka ƙyale wannan mai surutun, rigimarta ya fi ƙarfin ta" Baba ya faɗi. Shi kam sai murmushi ya ke yi yana faɗin " 'yata ba ta da rigima, ka bari na ji damuwarta" Ya kalleni ya ce " yanzu mi za ayi miki" "A sa shi a makaranta" Ya shafa kaina ya ce " gobe-gobe za a sashi a makaranta" "Idan ba a sashi ba fa?" Na tambaya cike da damuwa "Ni da kai na zan zo na kai shi"... Daga wannan rana kuka na ya ƙare aka saka Hamma a makaranta sai dai ba makarantar mu ba, sannan ba da mu ya ke zuwa ba, mu ana kai mu a mota shi yana tafiya a ƙafa. Wannan ma na yi ƙorafi akan dole sai ana kai shi tareda mu. Sai dai ban san ya aka yi ba tunda Hamma ya ce shi ba ya son shiga mota sai na dena ƙorafi. *..............Sa'eed...........* The rich girl versus the poor boy Ban san ya aka yi ba shaƙuwa mai ƙarfi ta shiga tsakanina da Aaliyah sai dai al'amari na Allah rubutacce ne kuma tsararre. Tun ba na iya ma ta magana sosai har na fara yi, tun ban fahimtar ta sosai har na fara yi. Duk da shekaru biyar cur da na ba ta rata, hakan bai hana mun zama tamkar abokai ba. Aaliyah to koremin zaman kaɗaici da rashin sabo da na ke yi farkon zuwa na. Mu kan ci abin ci tare mu yi wasa tare sannan mu yi karatu tare. Yayinda sauran yara tsarana su ke ball a ƙofar gida ni ina chan garden ina yiwa Aaliyah do ki ko goyo. Dalilin Aaliyah aka sani makaranta. Ita ta dinga kuka tana birgima har sai da aka sani a makaranta. Wata rana ina zaune ina yin Homework (aikin gida) sai ga Aaliyah da kaya a hannunta. Tana zuwa ta watsa min ta ce "gashi Hamma, kai ma ka sa kaya ma su kyau" Na tsorata matuƙa da wannan kaya saboda irin kayan da su Aliyu ke sawa kenan. Na ce "Aaliyah wa ya baki kayan nan" Sai ta fashe da dariya tana yi tana rufe baki. Na ce " ta Aliyu ce ko?" Saboda Aliyu shi ne tsarana ko da na girmeshi ba zai fi da shekara ɗaya ba. Maimakon ta ɗau kayan sai ta koma da gudu tana faɗin " barin je na ɗauko ma wasu" Kafin na ma ta magana ta yi nisa. Na ɗau kayan na shiga na nunawa Jijiɗo, ai kuwa ta tisani a gaba muka wuce sashen Hajia. Jijiɗo ta nunawa Hajia kaya tana ba da haƙuri. Hajia ta ce ba komai mu tafi da kayan wanda riga biyu ne da wando ɗaya. Ana haka sai ga Aliyu ya shigo ɗauke da Aaliyah, ya direta gaban Hajia. "Mama idan na daki Aaliyah ki ce na cika mugunta. To ga ta nan na kama ta tana ɗauka min kaya wai za ta kai wa Sa'eed" "Ni a Hamma zan kaiwa" Ta katse shi da ƙarfi. Hajia ta ce " yanzu dai ka yi haƙuri, ka ga Aaliyah yarinya ce" Ta ɗauki Aaliyah ta ce " 'yar fara ba a ɗaukan abin mutane sai an tambaye su kin ji" "Mama ai shine ya ce wai a John zai ba wa kaya, wai ba zai ba wa Hamma ba" Hajia ta ce maza ya je ya ɗauko kayan sa da su ka tsufa ya kawomin. Aliyu ya fita yana ƙunƙuni. A ranan saboda Aaliyah sai da na samu kaya kala takwas da takalma biyu. A wajen Aliyu tsofaffin kaya ne amma a wajena kaya ne ma su kyau, domin kaya ne na yayi. Tun daga ranan maimakon su John da ake bawa tsofaffin kayan Aliyu sai ya zama ni ake bawa waɗannan kaya... Cikin shekaru biyu na gama primary saboda aji huɗu aka sakani lokacin, saboda na iya karatu da rubutu. A makarantar mu ta ƙauye ina aji shida na taho Maiduguri sai dai gwaji da su ka min lokacin da za a sa ni a makarantar ya sa dole su ka maida ni aji huɗu. A shekaru na goma shahuɗu na fara aji ɗaya a sakandare yayinda su Aliyu da su John sa'annina su ka min fintinkau. Cikin shekaru biyu na gane banbanci tsakanin ni da Aaliyah. Aaliyah 'ya ce a gidan Bulama sunan da ke sa a kalleka da daraja a kuma mutuntaka. Ni Sa'eed kuma ɗan Baffa Manu maigadi ne. Wannan banbanci da kuma ƙara girma da na yi ya sa na ke ƙoƙarin ja baya da Aaliyah, sai dai a wajen Aaliyah ba ta bani daman yin hakan ba saboda tana ƙara girma da wayo tana ƙara shaƙuwa da kusanci da ni. Jijiɗo da Baffa na koyaushe suna ƙara nusar da ni akan Aaliyah musamman da ya ke ni na fita wayo sai dai abinda ba su sani ba shine Aaliyah ta jima da zama jinin jiki na. Aaliyah ta jima da mamaye ruhina. *TSOHUWAR💖SOYAYYA* *©Azizat* Wattpad @000Azee *BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM* Free page 0️⃣6️⃣ *..........Aaliyah.........* A girl, A woman Abubuwa dayawa sun faru a tsakanin shekaru uku da zuwan Hamma Sa'eed gidan mu. Hamma Sa'eed ya zamo tamkar wani ɓangare na jikina wanda idan babu shi ba zan rayu ba. A gidan mu na koma daga Aaliyan Jiji zuwa Aaliyan Sa'eed. Banida ɗanuwa ko ƙawa dana shaƙu da su sama da Hamma Sa'eed. Sanah da muke kusan kai ɗaya, ita ce kaɗai ƙawata ta kusa dani bayan Hamma. Mukan je ya koya mana karatu domin Allah ya bashi ƙwaƙwalwa, daga ƙauye ya zo amma ya ɗara mutane dayawa da su ka yi karatu a birni. Watarana ina shekara goma muna ɗakin Hamma yana koya mana karatu, da ke ni da Sanah ajinmu ɗaya, duk da kuwa ta girmeni. Abunda Hamma ke koya mana na riga na gane tuntuni shiyasa ya maida hankalinsa kan Sanah domin itama ta gane. Cewa yai na koma gefe na dinga practicing wasu lissafi da ya bani. Ina cikin yi na hangoshi da Sanah su na dariya. Hamma ya kan yi raha da barkwanci lokacin kowa mana karatu musamman darasi na Maths. A ƙarancin shekaruna sai na ji wani kishi ya mamaye ni, na ji ba abun da na ke ji sai haushin Sanah. Ji na ke za ta ƙwacemin Hamma Sa'eed ne. Na taso da sauri na zo na ture Sanah. Sanah ta kalleni "Aaliyah ba na son tsokala kinga muna karatu" "Ki dena zuwa karatu wajen Hamma. Hamma na ne ni kaɗai" ban san maganar da na yi a ranan magana ce da ta ƙunshi abubuwa dayawa ba. Ba ranan ne muka fara karatu a wajen Hamma tare ba, kusan shekara biyu kenan. "Aaliyah ba yayar ki ba ce" Sa'eed ya ɗan daka mini tsawa. "Ta tashi ta tafi, ba ta iya komai ba dama" Sanah ta fusata fuuuu ta tashi ta fita. Sai da na zauna ya kalleni ya ce "tunda kin koreta ke ma tafiya za ki yi angama karatun yau ɗin" Na yi-na yi da shi amma ya ƙi kulani ya ce sai dai na je na bawa Sanah haƙuri, cikin fushi na kwashi littattafaina na tafi. Maimakon na tafi gida sai na wuce garden na je na zauna ina wasa. Kusan awa ɗaya da rabi ina cikin wasa sai ga jini ya biyo ƙafata na tsorata da ganin jinin nan sai na fashe da kuka dan na ɗauka ciwo na ji a cinyata duk da kuwa ba wai ina jin zafi bane. Ban je cikin gida ba domin na kai kuka na wa Amma ko wa Jiji wanda na san tabbas tana kitchen tana haɗa mana abincin dare, ban je wajen Sanah ba wanda ba mu jima da yin faɗa ba. Ban je wajen Hajia ba wanda ta ke so na, ta ke son surutu na. Sai na wuce wajen Hamma Sa'eed wanda na san ina fushi da shi amma kuma shi kaɗai zan nunawa ciwo na. Hamma Sa'eed yana zaune yana karatun wani littafi na faɗo ɗakinsa. Ɗaki ne da kafin zuwan Hamma 'ya'yan Jiji ke kwana amma kuma tun zuwan sa ɗakin ya juye ya koma na shi yayinda Jiji da Baffa ke amfani da ɗaya ɗakin. Ina kuka na fara ɗaga skirt ɗina ina nuna ma sa pant ɗina da ya jiƙe da jini. "Hamma jini, Hamma ciwo na ji" A shekarunsa shabiyar ba zan ce ga takamaimai inda ya samu ilimi gameda jinin haila ba. Amma bayan ya duba sai ya gane ba ciwo bane. Abinda ya fara ce min shine "ki dena kuka, ba ciwo bane" "To minene?" Na tambaya cike da wasu tambayoyin a cikin ƙwaƙwalwata. "Bari mu je wajen Jiji" Akwai wani mayafi da ya ke rufuwa da shi sai ya ɗauko ya ɗaura mini ya ce muje wajen Jiji. "Idan na yi tafiya jinina zai ƙare Hamma" Bai ce komai ba sai ya tsugunna, ni kuwa na hau bayanshi. Ta ƙofar kitchen mu ka shiga inda mu ka tarar da Jiji tana yin farfesun kaza. Yana direni Jiji ta haushi da faɗa " Lamiɗo ba na hanaka goyon Aaliyah ba, kai ba ka jin magana ko" Bai ce komai ba saboda shi dama ba mai yawan magana bane balle kuma duk lokacin da babba ke magana to za ka ga Hamma Sa'eed ya yi shiru idon sa a ƙasa. "Jiji jini a jikina, ki zo ki min wanka" "Jini kuma?" A wannan shekaru babu irin gurɓacewar zamani inda ake yawan faɗe musamman har acikin yara saffa. Jiji ba ta kawo wannan a ranta ba sai dai ta tsammanta ciwo na ji. Ta kama hannuna mu ka bar kitchen ɗin. A wannan rana Jiji ta zaunar da ni tamin bayani gameda jinin haila cikin ɗan iliminta na gargajiyanci. Ni dai a lokacin ko kashi goma ban ɗauka ba cikin kashi ɗari na abubuwan da ta faɗa min. Sai ma ƙara dulmiyar dani da ta yi musamman yadda ta yi ta jajanta min wai na girma, ta dinga karanto min farillai da mustahabban mu'amala da Hamma Sa'eed wanda jinsu kawai na ke amma yadda su ke shiga haka su ke fita ta ɗaya kunne na. Abu da mai surutu babu wanda bai san labarin jini na ba, sati uku kenan Baba ba ya gida ranan da ya dawo tare su ka dawo da abokinshi Alhaji Wamako wanda ya zamo tamkar Baba na, duk lokacin da ya zo gidan mu sai ya taho min da tsaraba, sannan ko da su na meeting ne to Baban Lagos kaman yadda na ke kiranshi zai ɗaukeni a cinyar sa ko kuma ya barni na yi ta wasa a wajen. "Baban Lagos na fara jini" abinda na faɗa kenan lokacin da ya ɗaukeni bayan na ma sa oyoyo. Baba na da shi Alhaji Wamakon su ka tsaya kallon-kallo Baba ya ce "Aaliyah shekarun ki nawa?" Na ɗan ɓata fuska na ce " Baba har ka manta. Ba na yi birthday ba ranan" Na ɗan ɗaga murya na ce " i am 10yrs 7months now" Haka na zauna na basu labarin jini na tirtiryan tun daga faɗan mu da Sanah har zuwa yadda na ga jinin. Alhaji Wamako ya ce " Masha Allah, ashe ɗiyata ta zama 'yan mata, sai a fara haɗa kayan gado" Baba ya ce "wannan ɗin. Allah ya kaimu lokacin" Alhaji Wamako ya ce " 'ya ta ai sai ɗa na, wagga kyau da kwanya ai sai gida na" A wannan lokacin ya min tambayan da na yi da na sanin ba da amsarta. "Za ki auri ɗa na ko Aaliyah?" Ta ya zai min wannan tambaya a wannan lokaci, ta ya zai sa na yankewa kaina hukunci bisa abin da ban da ilimi a kai. Na gyaɗa kai na alamar e ba tare da na san me tambayar ke nufi ba. Abinda ban sani ba shine wannan amsa tun daga wannan lokaci ta ɗaureni gaba ɗaya ta hanani sakat ta hana na samu abinda zuciya na ke so... Al'amari na gidajen ma su kuɗi sai addu'a. Na fara al'ada da ƙarancin shekaru amma ba ni da wani ilimi mai inganci akan sa. Amma ta was busy da harkokin kasuwancinta, ta sadaukar da ragamar tarbiyata wajen Jiji, Jiji tana iya ƙoƙarinta a kaina amma ita kuma ba ta da wani ilimi mai zurfi, yawanci bayanan ta sunfi kama da gargajiyanci. Hajia na ta shirye-shiryen bikin 'yarta Falmata. Aje nan aje chan duk dan ana so ayi bikin da duniya za ta shaida. Baba harkokinsa ba sa bari ma ya zauna a gida na cikakken sati biyu ba tareda ya yi tafiya ba. Mukan je makarantar Allo daga baya ni da Sanah mu ka watsar. Aka ɗauka mana malami yana zuwa yana koya ma na karatu. Kuɗin gidan mu ya sa malamin ba ya iya aiwatar da abinda ya kamata. Ba zai iya ma na tsawa ko ya bulale mu ba, mun iya ba mu iyaba a haka dai ake ta tafiyar, wata rana ma ya zo mu ƙi fita. Hamma ya na koyamin ƙur'ani wasu lokutan saboda tun kafin ya zo yai sauka ta tartil hakanan tun farkon zuwan sa Baffa Manu ya kaishi wata makaranta yana hadda yana karatu. Na tafka ƙwaɓa dayawa farkon balaga ta. Musamman saboda ƙarancin shekaruna da kuma rashin fahimtar abin. Babban ƙwaɓar da na fara tafkawa shi ne sallah cikin jini. Jiji ta ce min ba'a sallah idan ana al'ada amma ni kam ina yi wani lokaci ma sai na tada sallar sai in tuna maganar Jiji amma sai na dake na ce ai Hamma ya ce ba kyau a bar sallah. A wata na uku da fara jini na, wata rana ina ɗakin Hamma muna karatu, saboda ko da baya koyamin karatun makaranta haka za ka ga mun samu littafin labarai na turanci muna karantawa. Sai aka kira Sallah, akwai masallaci a ƙofar gidan mu dan haka sai Hamma ya fita, idan akwai babban abinda zan shaidi Hamma da shi a iya tarihin rayuwar mu tare to sallah ne. Yayyena su Bukar da Aliyu ba su damu da sallah ba a wannan shekaru na ƙuruciyar su, banda kiɗa da kallo da zuwa party ba abin da su ka fi bawa amanna. Bayan Hamma ya tafi na cigaba da karanta labarin saboda na ji daɗin sa, chan na tuna idan Hamma ya dawo ya tadda ban yi sallah ba zai min faɗa. Sai na tashi na je banɗakin su na yi alwala duk da kuwa na san ina cikin jini. Na zo na tada sallah, ina raka'an ƙarshe Hamma ya shigo. "Aaliyah sallan mi ki ke yi?" Na yi gyaran murya. "Ki katse sallan nan" Ban katse ba sai dai na yi dungure-dungure na ƙarasa a gurguje. Dama sallar ta wa ya aka ƙare dan ma Hamma na ƙoƙarin gyara mini. "Waya ce mi ki ana Sallah idan ana al'ada?" "Ba ka ce wanda baya sallah ɗan wuta ba ne" Sai da ya sa na zauna kusa da shi sannan ya fara min bayani bayanin da ya shigeni farat ɗaya saboda Hamma na ne ke min su. Tambayoyi kam ya sha su wassu ya amsa wassu ya ce bai sani ba amma zai tambaya. Tambaya ta ƙarshe da na ma sa shi ne " Hamma wai inji Jiji idan ka taɓani zan yi ciki, da gaske ne?"... Sai da na shekara ɗaya da fara al'ada kafin Sanah ta fara. Da ke tun lokacin dana fara ana cewa na girma sai abin ya shige ni, sai na dinga tsokalarta ai na rigata girma. Wata rana da na isheta sai ta ce "ai nono na sun fi na ki" Ranan na wuni gaban madubi ina duba kai na ina ganin 'yan ƙananun nono na wanda na san tabbas ba su kai na Sanah girma ba. *TSOHUWAR💖SOYAYYA* *©Azizat* Wattpad @000Azee *BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM* Free page 0️⃣7️⃣ *...........Sa'eed.........* Feelings Shekaru bakwai kenan da zuwa na Maiduguri. Wannan gari mai Albarka ya zame mun tamkar asalina. Ina jin daɗin garin, ina kuma son garin sosai. A shekaru bakwai ɗin nan sau uku na je ƙauyen mu, na farko lokacin da Inna ta ta rasu shekara ɗaya bayan na zo Maiduguri mu ka je ta'aziya tareda Jijiɗo. Na biyu mu ka je da Baffa Manu lokacin da mahaifiyar sa ta rasu, sai na uku wanda ya zamo min wani tarihi mai muhimmanci a rayuwa ta. Ina shekara shatakwas, lokacin ina aji biyar a sakandare mijin babbar 'yar Jijiɗo ya rasu, lokacin ana hutu sai ya zama na tare mu ka tafi. Ban sanar da Aaliyah ba saboda sun tafi Lagos bikin wata cousin ɗin su. Su na dawowa daga tafiyar su, ko cikin gida ba ta shiga ba ta yiwo wajen mu da gudu. Kwana biyar kenan ba sa gida. Da ta zo ta samu ɓangaren mu a garƙame da kwaɗo. Ta shiga wajen su Mama John ta tambayi ina mu ka je. Mama John ta ce mun tafi ƙauye an ma na rasuwa. Daga wajen ta fara kuka ta shige gida da kuka. Kai tsaye ta je ta fara haɗa kayanta, da ta gama ta fito da jaka ta samu Amma a ɗaki tana baccin huce gajiya. Yadda ta ke ƙwala sunan ta ya sa tun kafin ta shigo ɗakin Amma ta farka. " Aaliyah ki na so na zane ki ko? Yaushe mu ka dawo za ki fara damuna da shirmen ki" Cikin kuka ta ce "Amma wai Hamma da Jiji sun tafi ƙauye, zan bi su" Takaici ya sa Amma ta ce " Allah ya kiyaye" Aaliyah ta fito da jaka ta nufi gate. Ma su gadi sun tafi Sallah, Ɗaya Maigadin da baya sallah kuwa ya kwanta a kan benchi yana hutawa bacci ya tafi da shi.  Ta je ta buɗe ƙaramar ƙofa ta fita. Taxi ɗin da ta tsare tace da shi ƙauyen Durum zai kai ta. Ganin kayan jikin ta ya san 'yar gidan manya ce. Ƙarancin shekarunta da rashin wayo da ya bayyana a fuskar ta ya sa ya gane ƙila guduwa za ta yi. Ya ce ta shigo. Su na tafiya ya fara ma ta tambayoyi akan mi za ta je yi a Durum, shi da ko sunan ƙauyen ma bai taɓa ji ba sai lokacin. "Zan je ganin Hamma da Jiji ne" "Ayya 'yan mata, Ashe ki na son Hamma da Jijin na kin nan sosai. Amma ban ga kin ɗauka mu su tsaraba ba, na ga kamar jakar kaya ne a hannun ki" Aaliyah ta dafe kai "oops ai na manta. Mu koma gida sai na ɗauko mu su tsaraban Lagos" Dama abinda mai taxi ɗin ke so kenan. Lokacin da ta ce gidan Alhaji Badamasi Bulama zai kai ta sai da yai mamaki. A ƙofar gate  ɗin gidan ya tsaya ta fita da gudu ta fara buga gate ɗin. Mr Francis ya leƙo ta ɗan ƙaramar ƙofa da akayi ajikin gate ɗin sai ya ga Aaliyah.  Da sauri ya buɗe ma ta ƙaramar ƙofa ta shigo, yana ma ta magana ma ita kan ko ajikin ta tsarabar Hamma da Jiji ne a gaban ta. Lokacin da ta fita daga taxi yai dai-dai da karyowar kwanar motar Alhaji Badamasi. Tsayawa su ka yi dreban sa ya fita ya je ya kirawo mai taxi ɗin. Mai taxi ya zo jikin window jikin sa na rawa duk da kuwa shi niyyar sa da Aaliyah ta shiga sai ya miƙawa ma su gadi jakarta ya kuma gaya mu su abin da ta ke niyyar yi. Sai dai abinka da ma su kuɗi yanzu sai a fassaraka da wani manufar. Bayan yai wa Alhaji Badamasi bayani Alhaji ya fito da kuɗi ya bashi sannan ya ce dreban sa ya ɗauko jakar Aaliyah... Aaliyah tana chan tana haɗa tsaraba ba ta san mi ake ciki ba sai da ta fito falon su ta ga Alhaji zaune ga jakarta a falon. "Kiramin Amman ki" "Baba zan je wajen Hamma da.." "Je ki kiramin ita na ce" ya daka ma ta tsawa. Ta juya da gudu ta tafi. Lokacin da Amma ta fito faɗa ya fara ma ta akan tana ina Aaliyah ta haɗa kaya har ta fita daga gidan nan wai za ta je ƙauye ba ta sani ba. "Alhaji na ɗauka shirme ta ke yi ai" "Shirme? Idan da wani abu ya sameta nan za ki gane shirme. Ba na son irin  wannan sakacin Mariya. Aaliyah ta fara girma ki sa ido akan ta" daga haka ya fita, haƙurin da Amma ke ba shi ma bai saurara ba. Wannan ranan Aaliyah har mari sai da ta sha a wajen Amma. Aaliyah ta ƙauracewa cin abinci, ranan farko Amma ba ta damu ba ta ce idan yunwa ya cita za ta nemi abinci da kan ta. Rana na biyu da yamma mai'aiki ta samu Amma da cewa har yanzu Aaliyah ba ta ci abinci ba kuma ta ki buɗe ƙofa. "Yarinyar nan ba za ta kashe ni ba, ni kam ko Jijiɗo mayya ce wannan abu da mi yai kama" Extra key ta nemo ta buɗe ƙofar ɗakin Aaliyah, anan ta ga Aaliyah na kwance zazzaɓi ya rufeta. Ranan Aaliyah sai kwanan asibiti. Amma ta yi faɗan har ta gaji amma Aaliyah ta ƙi cin abinci, sai da aka kira Alhaji Badamasi wanda ba ya gari ma lokacin. Aka bawa Aaliyah wayar tarho su ka yi magana da Baban na ta, ya ma ta alkawari da ta ci abinci ta warke za a kaita wajen Jiji. Hakan kuwa aka yi. Duk da Alhaji yana da 'ya'ya mata amma Aaliyah yarinya ce mai shiga rai, ta kasance 'yar gaban goshin Baban ta. Kwana uku da murmurewan ta Alhaji ya sa aka tsara ma ta tafiyar.  Dreba aka sa ya kawo su Bauchi zuwa Toro zuwa ƙauyen mu Durum. Ita da Sanah, saboda itama ta ce za ta je. Ina zaune kan wani dutse kusa da rafi ina karatu kamar daga sama na fara jiyo muryan Aaliyah "Hamma Sa'eed, Hamma Sa'eed" Na ɗan girgiza kai na, dan a ganina kunnena ke min ƙarya.  Ta ya zan ji muryan Aaliyah a nan, bayan Aaliyah ta min nisa. Sai dai wannan kira sai ƙara kusantoni ya ke. Na ɗaga ido  sai na hango Aaliyah tana gudu, hular ta a hannu tana sanye da doguwar riga irin ta turawa  wanda aka fi kira da 'yar kanti a lokacin, rigan ya tsaya iya silangarin ƙafarta. Iska na kaɗa dogon gashin ta tana dariya. Na tsaya kawai ina kallon ta, sai ya zama kaman ranan ne na fara ganin ta lokacin tana shekara bakwai, sai dai yanzu wannan yarinya ta zama budurwa she's  now 13. Ban motsa a wajen ba ban kuma ɗauke ido na akan ta ba har ta iso. "Hamma ta ya ka hau dutsen nan? ya yi tsayi dayawa" ta faɗa tana haki. "Tsaya barin hauro da ke"  na faɗa ina mamakin ganin ta. Ina saukowa daga dutsen domin na hauro da ita kawai sai ta faɗa jiki na. A da duk lokacin da ta rungumeni ba na jin komai ko dan akwai ƙarancin shekaru ne, ko dan kuma da ɗin bana jin abinda na ke ji gameda Aaliyah yanzu. "Hamma i miss you, shi ne ka tafi ka bar ni ko" ta faɗa tana ƙara shigewa jikina. A lokacin ji na yi na shiga wani hali na daban, wani yanayi wanda ke da wuyar fassarawa. Ban san ya akayi kalmomin su ka fito a baki na ba " I miss you more Aaliyah" Mu ka zauna a saman dutse  tana bani labarin yadda akayi har aka bari ta zo. Tana cikin labari na karɓi hular hannunta na sa ma ta aka na ce "Aaliyah ba na hana ki barin gashi a buɗe ba" Ta turo baki " Hamma ni kam" Mu ka zauna a saman dutse kusan awa ɗaya da 'yan kai muna hira. Da magriba ta gabato mu ka koma gida. Sati ɗaya Aaliyah ta yi a ƙauyen mu. Kullum mu na fita na nuna ma ta yadda ƙauyen mu ya ke, mu je gona, mu je kiwo tare, mu je rafi. Aaliyah was so excited and fascinated with my village, ni kuma na fi kowa farin ciki da zuwan ta. Da su ka yi sati dreba ya dawo ɗaukan su saboda makaranta da za a koma. Mu ma albarkacin Aaliyah mu ka shiga mota aka tafi da mu. Wannan rikici da Aaliyah ta yi kafin a barta ta zo ƙauyen mu shi ya jawo Jiji ta fara ja baya da Aaliyah hakanan ni ma ta min faɗa akan na rage mu'amala da Aaliyah saboda yanzu ba yarinya ba ce. Sai dai Aaliyah idan tana son abu ba mai hanata. Duk wani hannunka mai sanda da Jiji ko ni ke ma ta kamar ba ta san ma munayi ba, sai ma ƙara shige ma na da fa ke yi. Ni kam na shiga wani hali domin kuwa zuciyata ta na jin wassu sabbin shauƙi gameda Aaliyah, zuciya ta tana raya min wani al'amari mai daɗi gameda Aaliyah wannan al'amari da ya ke da kamar wuya. Amma ko da mafarkine to zan so na cigaba da yin wannan mafarki har ƙarshen rayuwa ta... Kasancewa jarrabawata ta yi kyau sai aka awarding nawa scholarship karatu a Cambridge da ke ƙasar England. Har falon Baba Aaliyah ta raka ni na nuna ma sa admission ɗin. Ya ji daɗi kuma ya sa min albarka. A wajen Aaliyah ta ce "Baba ni ma Cambridge za ka kai ni ko?" Baba ya ce "duk inda ki ke so 'ya ta"... A hankali ina ta shirye-shiryen tafiya har ya zama rana ta zo, gobe da safe zan tafi. Kullum sai Aaliyah ta min ƙorafin zan tafi na barta ita ba ta so na tafi, wai na bari itama ta ƙare sakandare sai mu tafi tare. Ni kam kawai dariya na ke yi dan nima ba ta san ya na ke ji gameda rabuwa da za mu yi ba. Da yamma ta zo muka  wuni a ɗakina da maghriba ta wuce cikin gida.  Ban ɗauka za ta dawo ba shiya sa nima ban dawo daga masallaci da wuri ba.  Wajen ƙarfe goma na shigo ɗakina sai na tarar da Aaliyah tana zaune tana jirana. "Aaliyah dare ya yi, mi ki ka dawo yi?" "Anan zan kwana" abinda ta faɗa kenan kai tsaye. Na sani ta kan yi baccin rana a ɗakina, hakanan lokacin ba ta kai haka ba bacci kan ɗauketa a ɗakina da dare in ɗauketa in mai da ta gida ko Jijiɗo ta maidata. Amma yanzu Aaliyah budurwace she's 14. Duk yadda na yi da ita ta tafi ta ƙi. I have no choice haka mu ka kwanta tare a gado ɗaya tun ina tunane-tunane har bacci mai daɗi ya tafi dani. The best sleep i ever had. Washe gari Jiji ta ga Aaliyah ta fito daga ɗakina, Nan ta fara faɗa.  Ba dan tafiya zan yi ba da ban san irin masifar da Jijiɗo za ta min ba. Dreban gidan Aaliyah ta sa ya kaini airport wanda tun cikin motan Aaliyah ke hawaye har muka isa. Nima daurewa kawai na yi amma ina jin yadda ta ke ji a ranta, ina jin ma fiyeda yadda ta ke ji.... *TSOHUWAR💖SOYAYYA* *©Azizat* Wattpad @000Azee *BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM* Free page 0️⃣8️⃣ *.............Aaliyah.............* Confession Lokacin da Hamma Sa'eed ya tafi Cambridge, sai ya zamo kamar ya tafi da rabin jiki na ne sauran rabin kuma yana Maiduguri. Duk su Jiji sun ɗauka rashin ganin Hamma  zai sa na dena damuwa da shi amma abin bai zamo haka ba. Kullum na dawo daga makaranta ɗakin sa na ke tarewa wani lokaci na yi ta kuka, wani lokaci  na zauna na wuni ina kallon hotunan sa. Abin ta kai har kwana na ke a ɗakin sa duk da kuwa Jiji ta hana ni amma na ƙi ji. Itakam Amma ta yi faɗan har ta gaji ta sallama ni. Lokacin da Yaya na Bukar ya tafi Oxford karatu mu kan yi waya da shi lokaci zuwa lokaci, amma Hamma tun ina irga kwanaki har na fara irga watanni ƙarshen shekara na baza ido ko zan ga Hamma kamar yadda Ya Bukar kai zuwa duk ƙarshen shekara amma ba Hamma ba dalilin sa. Safiyar wata Lahdi ina karatu a ɗakin Hamma, Jiji ta shigo da murnan ta. Ta miƙamin wani envelope mai ɗan girma ta ce yanzu Baffa Manu ya kawo, an aiko daga post office wai na karanta mu su daga Sa'eed ne. Ai da sauri na farke envelope ɗin na fiddo da abinda ke ciki. Akwai wani envelope madaidaici wanda  ke ɗauke da sunana a jiki. Ban san lokacin da na kissing envelope ɗin ba ina shaƙar ƙanshin jiki.  A gurguje na karanta ma ta abinda ya rubuto mu su. Gaisuwa ne da kuma bayanin yadda za su rinƙa amsan kuɗin da zai dinga turowa. Ina gama karanta ma ta na yi waje da gudu. Ban tsaya sauraron wasu tambayoyin ta ba balle na amsa su. Ina zuwa na faɗa kan gado na ina maida numfashi. Finally Hamma Sa'eed ya turomin saƙo. Kenan bai manta da ni ba, kamar yadda ni ma kullum ya ke rai na. Sai da na samu na nitsu sannan na buɗe envelope ɗin na fiddo da takardu goma shabiyu da ke ciki. Na fara karantawa ɗaya bayan ɗaya saboda ya sa number a jiki. Taƙaitattun bayanai ne akan yadda shekara ɗayan nan ta kasance ma sa a Cambridge ba tareda ni ko su Jiji ba. Duk inda ya rubuta *i miss you Aaliyah* sai na bi wajen da kiss. Haka na sa letters ɗin nan a gaba ina karantasu ina sake maimaitawa... Shekara na biyu ya zo min da sauƙi saboda mun yi musayar letters har sau shida. A wannan shekara na yi jarrabawar Waec ina aji biyar. Babban abinda ya fi sa ni farin ciki da kammala jarrabawar nan bai fi tunanin tafiya Cambridge da zan yi ba. Ina tunanin zan kasance tareda Hamma na. Sanah Oxford ta zaɓa ni kuma na zaɓi Cambridge duk da ma dai Baba ya so mu tafi waje ɗaya tunda tare mu ka taso amma kowa da ra'ayin sa. Ita Sanah tuntuni Oxford ta ke son zuwa ni kuma tun lokacin da Hamma ya samu scholarship a Cambridge na sa wa raina Cambridge zan je. Abu ne na 'ya'yan ma su kuɗi. Ko ina za ka je indai ana zuwa to ba matsala ba ce a wajen ma su arziƙi. Baba ya sa aka fara ma na shirye-shiryen tafiya. Ni excitement ɗi na ba na makarantar da zan je bane sai dan ganin Hamma da zan yi after 2yrs da ba ma tare. Cikin ƙanƙanin lokaci aka  sama mana admission aka arranging ma na komai hatta wajen da zan zauna an shirya komai. Ranan tafiya ta zo, Baba da kan sa ya raka ni airport abunka da shalele, da ke ba tare za mu tafi da Sanah ba ita sai nan da sati uku. Ban sha wahalar komai ba saboda an riga an shirya wanda zai ɗauke ni tundaga airport ya kaini gidan da zauna. Gidan flat ne ɗaki ɗaya da falo sai kitchen. Ba abinda ke raina illa na ga Hamma, ko ya ya ƙara girma yanzu oho. Mun riga mun tsara inda za mu haɗu a cikin makaranta idan na zo. Ba tareda hutawa ba na ce da wanda ya kawoni gida akan ya kaini makaranta. Baturen Mr Wallace ya nuna na huta yau gobe sai muje ya nuna min yadda zan ƙarasa registration. Na mai fau-fau akan dole sai mun je makarantar. Ba mu su ya amince, tunda kuɗi aka biya shi ya kula da ni... Kaman yadda na haddace sunan Hamma Sa'eed haka na haddace sunan address ɗin garden ɗin da za mu haɗu. Ba tareda ɓata lokaci ba Mr Wallace ya kaini wajen. Dai-dai wajen fountain ɗin da ya ce zai zauna ya jira ni dai-dai nan na tsaya amma banga Hamma ba. Na tsaya a wajen ina irga saukar numfashina, wanda ke sauka da sunan Hamma Sa'eed. Ban fi minti goma da zuwa ba amma gani na ke kamar na fi awa ɗaya.  Tun ina sa ran zan ganshi har na fara jin ko dai ya manta ne, ko dai baya son ganina ne ko dai... hawaye su ka fara sauko wa daga ido na. Ina zaune sanyin ruwan da ke ɓulɓula daga fountain ɗin yana ratsa ni amma ni zafi na ke ji. Daga ta baya na aka sa hannu aka rufe min ido, na sa hannu na taɓa hannun da ya rufe min ido, nan ta ke farin ciki ya mamaye ni. Shekara biyu amma ban manta yadda ɗumin hannunsa ya ke ba. "Hamma" na faɗa ina ƙoƙarin cire hannunshi da ga fiska ta. "Miye na kukan kuma?, kwata-kwata minti shabiyar ki ka yi a nan har kin gaji da jira" Na juyo da sauri and there he is. Hamma Sa'eed ɗina, sai dai wannan ya ƙara ƙiba ya kuma ajiye gemu. Murmushin sa mai rikitata tunani na shi ne shimfiɗe a fiskar sa. Kallon sa na ke yi ido cikin ido duk da yanzu ina jin wani abu na tasowa daga chan ƙasan zuciyata lokacin da na ke kallon sa. Ban sani ba ko tunda ɗin akwai wannan abun ko kuma yanzu ne da na girma na ke jin wannan abin ko kuma saboda munyi shekara biyu da wata huɗu ba tareda mun ga juna ba ne. A hankali na tashi ina cigaba da kallon sa, gani na yi ya ƙara min tsayi, sai na ganni 'yar guntuwa a kusa da shi duk da kuwa a cikin shekaru biyun nan nima na ƙara tsayi.  Hannu na sa na shafa fiskar sa ina ƙara tabbatarwa kai na finally Hamma ne a gaba na. Har lokacin bai dena murmushi ba. A hankali na shiga jikin sa ina dariya. Shima ya sa hannu ya ƙara jawoni jikinsa sosai ya ɗan ranƙwafo kan sa ya ce " finally" Mun jima a haka har ban san adadin lokacin da mu ka tsaya a wajen a haka ba, har cikin raina so na ke mu cigaba da kasancewa haka. Lokacin da za mu bar wajen bayan Mr Wallace ya zo akan yana so ya maidani gida cewa na yi dole Hamma ya goyeni ya kai ni wajen da aka yi parking motar. "Aaliyah yanzu kin girma fa" Na tuɓure na ce ban san wannan ba ni dai dole ya goye ni. Ban san miyasa Hamma ba ya son musu ba, ko dan tun asalin sa ba wai yawar magana ba. Haka a wajen nan ya tsugunna ni kuma na hau bayan sa, abin ya burge Mr Wallace har ya sa ya je ya karɓo wani camera a wajen wa su masoya da su ke ɗaukan hoto a gefen mu. Ya ɗauke mu hoto ina bayan Hamma yana dariya ina dariya. Wajen da aka ajiye motar ba ƙaramin nisa ne da shi ba amma haka Hamma ya jure ya kaini har wajen. Abinka da ƙasar waje ba wanda ya damu balle a tsaya a muku magana. Kallon mun burge sosai ma ake ma na... Ba zan iya tuna rana ɗaya da ba mu haɗu da Hamma ba tun daga wannan rana duk da kuwa abin da mu ke karanta ba ɗaya ba ne, kuma wajajen ɗaukan karatun mu ba sa kusa. Idan ba mu haɗu a makaranta ba to dole zai zo gidana, duk yadda na dameshi akan ya tattaro ya dawo gidana sai ya ce min a'a tun ina fushi akan haka har na dena. Wata rana maƙociyata Cassandra wadda ake kira da Cassy ta gayyaceni birthday party ɗin saurayin ta. Da ke bayan Hamma, Cassy ita ce wadda na shaƙu da ita tun zuwana Cambridge. Na bar wa Hamma saƙo akan idan ya zo na fita tareda Cassy da ke ya san inda na ke ajiye ma sa key. Ƙarfe bakwai na yamma mu ka fita daga gida amma kafin mu isa wajen da ake party ɗin ma sai tara saura domin chan bayan gari ne wajen ruwa. Mata da Maza ne a wajen kowa da shigar sa ta wajen beach. Mata da bikini Maza da gajerun wanduna. Dayawa mu baƙaƙen fata idan munje ƙasar waje mu ka ga ana abu to fa ba ma so a barmu a baya, ba ma so a mana kallon mu 'yan ƙauye ne. Haka ta ke tun 80's haka ta ke kuma har yau. Cassy ta dinga damuna a kan ni ma na cire kayan jikina, dan idan na fito a haka za a dinga min dariya.  Da farko ban yadda ba amma daga baya na amince na cire doguwar rigan da na sa wanda itama doguwar rigan dama guntuwa ce, to wa ya damu, fashion ɗin lokacin kenan. Na ajiye kayan a motar Cassy na fito daga mota ina ɗan ɗari-ɗari saboda ban taɓa fita haka ba, daga ni sai bra da pant kamar sauran matan wajen. Ba ma maganar ɗankwali dan tun asalina ba na son sawa sai kuma ya haɗe da zuwa turai na ma watsar da batun rufe gashi, yana ɗaya daga cikin abinda ya ke sa Hamma ke min faɗa a mafi yawancin lokuta. Na ƙarasa wajen party ɗin da ƙyar. Ana ta rawa amma ni na kasa yi, Cassy ta miƙomin wani abu a kofi na girgiza kai na ƙi na karɓa. Ban ankara ba wani bature ya kama ni ta baya yana rawa yana shafa jiki na. Ina ƙoƙarin ture shi amma shi ina bai ma jin mai na ke faɗa saboda kiɗa da ke tashi. Hankalina ya tashi saboda duk da ba wannan karan ne na fara zuwa party ba amma ban taɓa zuwa irin wannan partyn ba. Da ƙyar na ƙwaci kai na a wajen baturen na koma gefe na takure ina danasanin biyo Cassy da na yi. Hamma ya je gidana ya tarar da saƙon da na bar mi shi, kasancewa ba na ɓoyewa Hamma komai hakan ya sa na rubuta ma sa address ɗin inda za a yi party ɗin incase zai zo. Tunda ya ga address ɗin hankalin sa ya tashi ya nemi wani abokin sa mai mota ya aro mota ya taho. Zuwa na yi dan na gayawa Cassy akan zan tafi gida sai  wani Matt wanda mu ke aji ɗaya ya ganni, ya kamo hannuna yana cewa mu yi rawa. "Plz Matt leave me" na faɗa ina ƙoƙarin cire hannuna daga cikin na shi. Ban san daga ina ya fito ba sai saukan mari da na gani a fiskar Matt. Matt ya riƙe ƙuncin sa yana kallon Hamma da ke tsaye fiskar sa kamar garwashin wuta. Hamma ya cire jacket da ke jikin sa ya matso ya samun wanda tsabar tsoro na ka sa cewa komai. Ya ja hannuna mu ka bar wajen. Har ya kai ni gida bai yi min magana ba, lokacin da ya buɗe min ƙofa kasa shiga na yi na tsaya bakina na rawa na ce "Hamma" "Kar ki ƙara kiran suna na. Party girl ko" Ya rufe ƙofar ya juya ya tafi. Ranan haka na kwana da zazzaɓi, ina sauraren Hamma ko zai zo ya duba ni amma bai zo ba. Idan na kira shi ba ya ɗauka. Lokaci guda Hamma ya ƙaurace min. Duk inda mu ke haɗuwa da Hamma ya dena zuwa, har ajin su na je amma ya shareni. Cikin kwana uku na shiga tashin hankali da ban taɓa shiga ba a lokacin. Ba abinda ke damuna irin Hamma ya gujeni, Hamma na ya guje ni. A kwana na biyar sai da aka kwantar da ni a asibiti, ina nan ma duk halin da na ke ciki babban burina shine na ga Hamma, amma bai zo ba sai washegari. Ina kwance ya shigo lokacin ina ƙara tambayar Cassy ko ta sanar da Hamma cewa banda lafiya. Ina ganin sa na yi yunƙurin tashi duk da ruwan da aka ɗaura min. "Hamma i'm sorry, wallahi ba zan kuma ba, dan Allah kar ka gujeni" na fara faɗa ina kuka tun ma kafin ya ce wani abu. Hannuna ya kamo ya ce "ba komai, get well soon" Kwana ɗaya na ƙara a asibitin su ka sallameni. Tare mu ka dawo da Hamma gida, ya shiga kitchen ɗina ya min lafiyayyen girki, duk da bana jin daɗin baki na amma haka na daure na ci sosai. Sai chan dare tukunna ya tashi zai tafi. "Hamma ka kwana anan" girgiza kai kawai yai ya nufi ƙofa. " ki sha maganin ki akan lokaci zan zo gobe da rana" Daga inda na ke zaune gani na ke idan ya tafi ba zai kuma dawowa ba. "Hamma" Ya juyo ya kalle ni. Na tashi na ƙaraso wajen da ya ke tsaye. Idon sa na kalla na furta abinda ya jima ya na damuna, wanda ban gane ba sai a 'yan kwanakin nan da Hamma yai fushi da ni. "I love you Hamma Sa'eed, i love you so much. Dan Allah kar ka kujeni, ina son ka da dukkan bugun zuciya ta, Ina son ka da kowanne fitar numfashi na, ina son ka da duk wani jijiyar jikina. Ina son ka..." Yatsun sa biyu ya sa ya toshe bakina ya ce "shhhhhhhh"... *TSOHUWAR💖SOYAYYA* *©Azizat* Wattpad @000Azee *BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM* 0️⃣9️⃣ Free page *................Sa'eed..............*   Love Tafiya na ke akan titi amma ji na nake kamar a kan gajimare na ke tafiya. Farin cikin da ya mamayeni a wannan lokacin ba zai bayyanu ba. Ji na nake a sama, ban ƙi na dinga tiƙar rawa a wajen ba dan na nuna yadda na ke cikin tsananin farin ciki. Duk nisan gidan Aaliyah da Hostel ɗin mu ban gani ba, a haka na tafi a ƙafa, ina tafiya ina ji kamar kar wannan dare ya ƙare, wannan dare mai tarin albarka, wannan dare da na iya amayar da abinda na jima ina ƙunshe da shi a zuciyata. Idan na tuna yadda idon ta ya bayyana shauƙi da farinciki lokacin da na bayyana ma ta sirrin zuciyata, sai na ga kamar na fi kowa sa'a a rayuwa... Kamo hannunta na yi na kai dai-dai ƙirjina da ke bugawa da ƙarfi-ƙarfi na ce *"Kin ji yadda ƙirjina ke bugawa ko? Zuciyata ta jima tana bugawa domin ki Aaliyah. Ba zan taɓa gudun ki ba, har ƙarshen rayuwata haka zuciyata za ta cigaba da bugawa domin ki. I have always love you, and will always love you till my last breath on earth. Ke ce zuciyata Aaliyah, ke ce farin ciki na"* Na tallafo fiskanta da ya riga ya jiƙe da hawaye na manna ma ta light kiss a bakin ta. Ta shige jikina tana kukan farin ciki, nima ɗin sai na ji hawaye na zubowa a idanuna. Ban son rabuwa da ita, ina son kasancewa da ita har washegari, har ma ƙarshen rayuwata amma.... "Are you crazy!" ihun wani mai mota ya dawo da ni daga duniyar tunani. Ashe na kai tsakiyar titi ban sani ba, na matsa da gudu ina bashi haƙuri. Idan ina tunanin Aaliyah mantawa na ke da komai... ............................. Baccin daɗi na yi daren ranan, baccin da na jima ban yi irin sa ba. Na tashi da niyyar shimfiɗa  sabon rayuwa, rayuwa mai daɗi tareda masoyiyata Aaliyah... Shaƙuwa tsakanina da Aaliyah ba abinda ya ragu sai ma ƙaruwa da yai. Kullum muna maƙale da juna. Ko a makaranta ko a gida, ko kuma a shagon da na ke aiki. Ina haɗa coffee, tea, capuccino, frapuccino da sauran su a shagon. Tun shekarana na farko na fara aiki a wajen saboda samun kuɗin shiga da kuma 'yan chanjin da zan dinga turawa su Baffa Manu. Cikin ƙanƙanin lokaci na yi fice a shagon, ta kasance duk wanda ya zo za ka ga ni ya ke buƙatan na haɗa ma sa order ɗin sa, duk da kuwa ba koyaushe na ke aikin ba na kan yi da yamma ne ko dare idan ba ni da class. Ranan ina tsaka da haɗa coffee wa wani customer sai ga Oga na ya zo. "Seed" ya kira ni kamar yadda ya saba saboda bai iya kiran Sa'eed ba. Na juya ina kallon sa. Da mamakina sai ga Aaliyah a gefen sa tana murmushi tana sanye da T-shirt mai ɗauke da sunan shagon. Ya nuna min Aaliyah a matsayin sabuwar ma'aikaciya tareda cewa na koya ma ta aiki har ta iya. Na amsa da to ina aikawa Aaliyah kallon za ki gamu da ni... Ƙarfe shaɗaya na dare na gama aiki na na ranan, na fito daga shagon ina yin biris da Aaliyah da ke ta kiran suna na. "Hamma dan Allah ka jira ni, Hamma please ka rage sauri" Ban kulata ba na cigaba da tafiya. Ganin idan na cigaba da tafiya a haka zan ma ta fintinkau ya sa ta kama gudu. Da ta isoni ta tsaya gaba na tana haki. "Hamma Dan Allah na ce fa, ka yi haƙuri ba zan sake ba" Na tsaya da tafiya ina kallon ta ba tareda na ce komai ba. "Hamma ina son kasancewa tareda kai shiyasa na nemi aiki a wajen. Please forgive me" ta ƙarasa maganan tana haɗa hannunta biyu. Na sa hannu a haɓata kaman mai tunani na 'yan wasu daƙiƙu kafin na ce "zan yafe amma da sharaɗi" "Mi ye sharaɗin?" Ta tambaya tana kallona "Daga yau ba na so ki sake kirana da Hamma" Ta ƙwalalo ido waje saboda ba tun yau ba na ce ta dena kirana da hakan amma ta ƙi, ta ce ba za ta iya denawa ba. "Ni gaskiya ka chanja wani sharaɗin" ta faɗa da sakalci. "Wannan ne kaɗai sharaɗin" Ta fara buga ƙafa tana faɗin dole na chanja sharaɗi. Ni kuma na ce sam shi kaɗai ne sharaɗin. Da ta ga na doge dole ta haƙura ta faɗa. Ta rufe idonta kafin ta furta sunan a hankali "Sa'eed" Na ji abinda ta ce amma saboda yadda sunan yai daɗi a bakin ta ya sa na ce ma ta ni banji mi ta ce ba. "Sa'eed" ta sake maimaitawa. "Ni fa idan ba ki kalli ido na kin kira sunana ba ban san kina magana ba" "Kayya! that's not fair Hamma" "Shikenan barin tafi" na sa kai zan cigaba da tafiya ta yi saurin riƙe hannuna. Na juyo ina kallonta ina kuma jin yadda duk jijiyoyin jikina su ka amsa da riƙon da ta min. *"Sa'eed"* wannan karon ido cikin ido ta kira suna na, wannan karan da wani salo me haɗe da yauƙi ta kira suna na, wannan karan na fi jin daɗin suna na fiye da kowanne lokaci... So kenan, mai sa ka ji za ka iya yin komai domin masoyinka. Saɓanin ni da na ke aiki ake biyana Aaliyah na aiki ne dan kawai ta kasance tareda ni. Maƙudan kuɗi ta bawa mai shagon domin ya barta ta yi aiki sannan ya ƙara min albashi. Ban tashi sanin ƙarin albashi da na samu daga wajen Aaliyah ba ne sai da tafiya ta yi nisa... Mun kusa yin hutun ƙarshen shekara, yayinda mafiya yawanci ɗalibai da ba 'yan ƙasan ba ke ta murnan za su je gida, ni baƙin cikin rabuwa da Aaliyah na ke ji. A wannan lokacin da ba karatu na ke samun daman yin ayyuka dayawa domin samun kuɗi shiyasa ban damu na nemi kuɗin jirgi na dawo gida hutu ba. Kwana uku ya saura Aaliyah ta koma gida, mun fito daga wani cinema inda mu ka je mu ka yi kallo. Aaliyah ke sake roƙo na akan lallai na amince na koma Nigeria tareda ita za ta biya min kuɗin jirgi. Na nuna ma ta ba zan koma Nigeria koma Nigeria ba sai na gama karatu na. Hakan ya sa ta yi fushi ta fara tafiya ta bar ni tsaye a wajen. "Aaliyah wait..wait please" na bi bayanta da sauri... "Ni ka sake ni na tafi, dama ba ka damu da ni ba ai. Ka yi ta zamanka a nan har Mahdi ya zo..." Ganin ta ƙi yin shiru ya sa na rufe bakinta da nawa. Wannan ne karo na farko da na kissing ɗin ta properly, our first deep french kiss. Ta kwanta a ƙirjina tana murmushi. Na sa hannu a aljihu na ciro zoben da na jima ina tara kuɗi domin na siye shi, zoben zallan azurfa ne mai kyau. Na kamo hannunta na sa zoben a yatsar ta tareda kissing ɗin hannun ina faɗin *"ke ce zuciya ta Aaliyah, idan na rasa ki na rasa zuciya ta gaba ɗaya. A duk inda ki ke, a kowani lokaci, a kowani hali, duk min rintsi ina son ki Aaliyah, har ƙarshen rayuwata, har ƙarshen numfashina a doron ƙasa. I will forever love you Aaliyah"* *...........Aaliyah............* Fear Ina son Sa'eed sosai, kowacce rana kamar ƙara dasa min son shi a ke a zuciya ta. Sa'eed mutum ne mai karamci, tsaftacecciyar soyayya ya ke gwada min wanda ta ke babu ƙarya a cikin ta. Idan ka cire riƙe hannu ko runguma sau uku Sa'eed ya taɓa kissing ɗi na. Wani lokaci na kan nuna ma sa alamun ba matsala idan ma mun aikata abin da ya fi kiss amma sai ya dinga janye jiki da ni. Akwai lokacin da na fito fili na faɗa ma sa ni da shi ɗaya ne kuma zan mallaka ma sa kai na ba tareda wani tsoro ko fargaba ba. Yai murmushi kawai ya ce "Aaliyah ba jikin ki na ke so ba, haka nan akwai lokacin da za mu kasance tare har abada, ki yi haƙuri kafin nan"... Saura kwana ɗaya na tafi gida muna zaune da Sa'eed a gida na aka fara ƙwanƙwasa ƙofa. Muna zaune a kujera mu na shan tea ɗin da ya haɗa min wanda har yau na ka sa iya haɗawa kamar yadda ya ke haɗawa. Tunanina pizza da mu ka order ne aka kawo ma na, dan haka na tashi da sauri na je na buɗe ƙofa.  Ido na zaro ganin Amma na tsaye. Na faɗa jikin ta ina murna... Shigowar da ta yi ta ga Sa'eed ya sa ta haɗe rai tana yiwa Sa'eed kallon tuhuma. Da ƙyar ta amsa gaisuwar da Sa'eed ɗin ya ma ta. Shima ɗin sai na ga tsoro ya bayyana a fiskar sa. Suna gama gaisawa ya ce zai tafi, na nemi ya tsaya a kawo mana pizzar amma ya ce yana sauri ya tuna zai je ya amso saƙo. Sa'eed na tafiya Amma ta kalle ni cike da masifa ta ce " mi ya ke yi a nan?" "Amma ya zo tayani hira mana tunda ba makaranta" na faɗa ba tareda wani fargaba ba. "Na shiga uku, Aaliyah ba dai anan ya ke kwana ba?" Duk yadda na faɗawa Amma Sa'eed ba ya kwana a gidana haka nan bai taɓa kwana a gida na ba bata yarda ba sai da ta dudduba gidan ta ga babu kayansa ciki. "Amma wai miye haka ne? Sa'eed ɗan uwana ne, ko da ya kwana anan mi ye a ciki?" Amma ta fara min faɗa, ta inda ta ke shiga ba ta nan ta ke fita ba. Tun ban maida abin komai ba har tsoro ya fara shiga na saboda maganganun da ta ke faɗa. Ba abinda ya fi ɗaga min hankali irin abinda ta ce wai idan ma soyayya mu ke to mu dena dan ba inda zai kai mu. "Amma miye ne idan mun yi soyayyar? Sa'eed mutumin kirki ne" "Tsakanin ki da Sa'eed babu soyayya Aaliyah, idan kuma ki ka fara za ki sha baƙar wahala ne dan ba inda zai kai ku. Ki kama kan ki Aaliyah ko kuma na sa Baban ki ya chanja miki makaranta"... Har mu ka koma gida Nigeria ban ga Sa'eed ba gashi Amma ba ta bari na fita a gidan ba. Dama ta je ganin yayanta da ba lafiya ne ta biyo min akan mu wuce Nigeria tare tunda nima chan na nufa... Tundaga wannan lokaci na ji tsoro ya shiga rai na. Ina tsoron ka da kashedin Amma ya tabbata, ina tsoron kar wata rana a raba ni da Sa'eed... Har hutu na ya ƙare ban ji daɗin hutun ba saboda kewar Sa'eed da na ke yi. Sai da na koma Cambridge na samu nitsuwa. Kwanaki kaɗan da komawata na fara ganin chanji tattare da Sa'eed kamar ƙoƙarin ja baya ya ke da ni, gashi ya daina zuwa gidana. Da na tuhumeshi sai ya ce karatu ne ya ke riƙe shi wanda na san ba haka ba ne.  A hankali na gane Amma ce ta gargaɗe shi a kai na. Ranan na ma sa kuka sosai  na kuma nuna ma sa soyayyar sa ƙarya ne indai zai ji tsoron Amma. Abin ya ma sa ciwo, hakan ya sa ya dena baya-baya da ni ya kuma nuna mini duk rintsi muna tare. Muka cigaba da soyayyar mu kawai mu ka manta da komai... A shekara na biyu da na zo gida hutu na tuhumi Amma akan dalilin son rabani da Sa'eed da ta ke yi. Ranan ne  na ji tsanar gidan mu, na ji a raina ina ma ni ba 'ya ce a gidan Alhaji Badamasi Bulama ba, na ji inama ni 'yar wata maigadi ne ko dreba. Amma ƙiri-ƙiri ta faɗa mini babu aure tsakanina da Sa'eed idan ma zan bar shirmen da na ke yi to na bari. Domin makaranta kawai ake jira na ƙare amin aure domin an min miji. Ban san ya na ƙare satuttukan da na yi a Nigeria ba domin na kasance tamkar mara lafiya ba na fita ko'ina kuma ba na shiga cikin 'yan gidan mu. Jiji ma dana samu da maganar sai ta tabbatar min da maganar Amma, 'Yar mai kuɗi sai ɗan mai kuɗi... Ranan da na koma makaranta ina zuwa gida na kira Sa'eed akan ya zo ina neman sa. Tun a Nigeria na riga na yanke wa kai na shawara kuma ko sama da ƙasa za su haɗu ba zan fasa abinda na yi niyya ba... Yana zuwa na rungumeshi saboda ba ƙaramin missing ɗin sa na yi ba. "Sa'eed ka min ciki" abinda na faɗa ma sa kenan kuma har zuciya ta abinda na ke so kenan. Ya janye ni a jikin sa yana faɗin "ciki kuma? Why? Miya kawo wannan maganar?" "Amma ta ce ba za mu yi aure ba, Jiji ta ce ba za mu yi aure ba. Sun ce wai ba mu dace ba. Sa'eed idan na rasa ka mutuwa zan yi. Dan Allah ka sadu da ni na samu ciki ko za su bari mu yi aure" "Kwantar da hankalin ki Aaliyah, da sauran lokaci har yanzu saura miki shekara biyu ki ƙare ƙaratun ki. Kafin nan za su amince mana" Wannan karan cikin kuka na ce " ba za su taɓa amincewa ba Sa'eed. Amma ta ce ina gama karatu za su min aure, wai anriga an min miji" Na fara ƙoƙarin cire kayan jikina. "Aaliyah stop this nonsense, ki bar cire kayan nan" Ban saurareshi ba na yi tsirara gaban sa. Ya daka min tsawa akan na maida kaya na. Amma ba abinda na yi sai ma na fara ƙoƙarin cire ma sa belt ɗin wandon sa. "Ba ka sha'awata ne, kai ba namiji ba ne, ka yi duk abinda ka ga dama dani ni Aaliyah ta ka ce" "Stop Aaliyah" ya faɗa yana tureni amma ban daddara ba na sake matsowa kusa da shi zan cire ma sa riga. Saukar mari na ji a fiskata wanda ya sa na tsaya da abinda na ke shirin yi. "Ke mahaukaciya ce Aaliyah, i said akwai lokaci. Ba zan taɓa ɓata miki rayuwa saboda wani dalili marar kan gado ba. Yes I love you amma ba irin wannan soyayyar na ke miki ba, what i feel for you is beyond this" Har ya je ya ɗauko bargo ya zo ya rufa min ina tsaye ina zubda hawaye. "Ki je ki sa kayan Ki" ya faɗa a hankali... *TSOHUWAR💖SOYAYYA* *©Azizat* Wattpad @000Azee *BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM* 1️⃣0️⃣ Free page *za'a samu cigaban wannan labari a 200, idan kuma ka biya kuɗin Sakatariyata to 100 za ka biya. Domin ƙarin bayani 08137311900* Wayar Zaid da ke ringing ne ya katse shi daga karatun da ya ke yi. Ya ɗaga ido ya kalli Aaliyah da idon ta ya cicciko da hawaye. "Mi ya same ki kike kuka?" Ya tambaya yana ƙura ma ta idanun sa. Ta girgiza kai kawai tana matse hawaye da gefen gyalenta. Cigaba da kiran da aka yi ne ya sa yai tsaki tareda jawo wayar da ke kan gado. Kafin ya swiping ya ɗauka kiran ta ga sunan da ke jikin screen ɗin  *Zahra* babu tantama ta san Zahra MCcollins ce ke kiran sa. Waye bai san Zaid Ahmad Wamako da Zahra MCcollins su na soyayya ba. Zahran da ta ke da over 2million followers a instagram da twitter. Manyan mutane da 'ya'yan manya sun yi chaa a kanta amma ba wanda ta damu da shi kamar Zaid. Shekara ɗaya da ya wuce ta tabbatar da zargin da ake ma ta kan soyayyar su da Zaid ɗin, inda ta bi duk shafukan ta na sada zumunta ta posting hoton ta da Zaid da su ka yi a Dubai ta rubuta *my man* a ƙasan hoton. Ba dan rasuwan mahaifin Zaid ɗin bama ƙila da anyi auren Zaid da Zahra tuntuni... Arnold MCcollins shine kakan Zahra ta wajen Uba. Baturen ƙasar Ingila ne wanda ya zo Nigeria lokacin turawan mulkin mallaka. Kusan shekaran sa shabakwai  a Nigeria kafin Allah ya sa yana da rabon musulunci ya musulunta. Kasancewa matar sa Rebecca ta daɗe da mutuwa ya sa bayan musuluntar sa aka bashi mata a Niger state inda ya ke da zama. Hadiza Mamman Kankana 'ya ce  a gidan Alhaji Mamman Kankana ɗaya daga cikin masu kuɗi kuma jigajigan ƙasa 'yan asalin Minna. Auren Abubakar Arnold MCcollins da Hadiza Mamman Kankana sun haifi yara biyu, mace da namiji. Muhammad da Aisha. Shekaran su goma shabiyar da aure Abubakar ya rasu yana mai shekaru sittin da ɗaya. Muhammad da Aisha ba ƙaramin gado su ka samu ba saboda dukiyar da wannan baturen ya mutu ya bar mu su. Muhammad A.A MCcolllins fitaccen mutum ne a ƙasar Nigeria da ma duniya gaba ɗaya. Ya riƙe muƙamai da dama kafin ya koma aiki da United Nations. Matar sa ɗaya Hajiya Maryam Tambuwal wanda itama 'yar babban gida ce. Allah ya azurta su da yara uku. Hanifa Mccollins ita ce 'yar fari, wacce ta ke auren ɗan sarkin Sokoto. Sai Anwar MCcollins wanda ke auren 'yar shugaban ƙasa. Sai autar su Zahra wanda ta ke cin karenta ba babbaka a ciki da wajen ƙasar. A shekarunta ashirin da biyar ta na da kwalin degree uku a ɓangare daban-daban. Tana da Kamfani da ta buɗe shekaru uku da su ka wuce, Zahra MCcollins brand ce. Tana da kyau, kuɗi, asali da nagarta. Yarinya ce da ta ke da girman kai da jiji da kai,  ba da kowa ta ke harka ba, iya matsayin ka iya kusancin ka da ita. Za ta iya walaƙanta kowa indai ka shiga gabanta. Ta samu tayin soyayya da ga wajen 'ya'yan manya da dama, sai dai da mutum biyu ta taɓa soyayya ko kuma na ce ta amince da soyayyar su. Masoyinta na farko cousin ɗin ta ne Junaid, ɗa a wajen ƙanwar Baban ta wato Aisha MCcollins. Ba su jima tare ba su ka rabu dan yanzu haka shekarar sa uku da aure. Zahra na masifar son Zaid, duk girman kan ta ba ƙaramin walaƙanci ta sha a wajen Zaid ba kafin su ka zo su ka zama masoya... Bayan ya gama wayar da Zahra ya kashe wayar gaba ɗaya ya ajiyeta gefe. Sannan ya juyo ya kalli Aaliyah da har lokacin tana ƙoƙarin goge hawaye ya ce " a ina ki ka samu diary ɗin Sa'eed?" "Wamako mu cigaba da karatun za ka gane daga baya" Kallon ta yai na ɗan wasu daƙiƙu kafin ya buɗe diary ɗin Mom ya cigaba da karatu. *..........Aaliyah...........* Ahmad Wamako Tun daga ranan hankalina bai kwanta ba, amma Sa'eed bai wani nuna damuwa ba. Koyaushe ce mini ya ke na kwantar da hankalina na cigaba da addu'a komai zai zo da sauƙi. Sai da aka ɗau lokaci mai tsayi kafin na cire damuwa a raina na, koyaushe Sa'eed nuna min ya ke akwai nasara a tattare da soyayyar mu... Wata ranan Alhamis na dawo daga aji zan shiga gida sai na ji kamar ana kuka, na kasa kunne sosai sai na ji kaman daga ɓangaren Cassy maƙociyata ake kukan. Da farko na yi niyyar na share ta sai kuma na ga hakan bai dace ba, maimakon na shiga ɓangarena sai na je ɓangaren Cassy na fara buga ƙofar ta. Ba ta buɗe da wuri ba sai da na yi ta mata magiya kafin ta zo ta buɗe. Ganin yadda idon ta ya koma saboda kuka ya sa na shiga tambayarta miya faru. Da farko ma na ɗauka ko faɗa su ka yi da saurayin ta dan na san tana son Damien sosai. Sai da ta faɗa min asalin abinda ya faru sai jikina yai sanyi. Saurayin ta Damien yai hatsari ya mutu. Abinda ya ƙara ɗaga ma ta hankali shi ne sati biyu da su ka wuce wata ƙawarta ta ma ta kwatancen wani mai duba. Out of curiosity sai ta je, da ta je mutumin ya gaya ma ta Damien zai mutu. Ta harzuƙa da wannan zance ta zage shi tatas, ta kirashi da maƙaryaci. Sai ga shi da safiya aka kirata akan Damien yai hatsari, bai jima da kawoshi asibitin ba ya mutu. Ba shiga rarrashin Cassy ina nuna ma ta lokacin Damien ne yai... Bayan kwana huɗu da mutuwar Damien na je na samu Cassy akan ta kai ni wajen mai duban nan, ina so nima ya min duba. Da farko ta ƙi saboda tana tunanin kar na je a gaya min abinda zai ɗaga min hankali amma da na nuna ma ta koma minene zan jure ba zan tada hankali ba sai ta yarda... Mutumin da mu ka je irin sufi ɗin nan ne, yana yin sa da kuma turancin sa ya daɗa tabbatar min da ba zai wuce ɗan ƙasar India ba ne. Muna zuwa ya kalleni ya ce *Aashiƙan* yai murmushi wanda na rasa gane murmushin ko na minene. Tun kafin na ma sa bayanin mi ya kawo ni ya ce ya sani na zo ne akan maganar soyayya na gyaɗa ma sa kai ina sawa a raina wannan mutumin da gaske yana duba ɗin. Na miƙa ma sa hannun dama na bayan ya buƙaci hakan. Ya sa yatsar sa yana bin zanen hannuna kafin ya ce *Makhtub* ya cigaba da cewa "ko sama da ƙasa za su haɗu sai kun yi aure" ya kalli ƙwayar idon na ya ce "sai dai za ku yi shekaru talatin kuna kewar junan ku" ba tareda na gama gane ma'anar maganar sa ba na ce "ka ce ni da Sa'eed za mu yi aure?" Sai da yai dariya kafin ya ce "za ku yi aure" Kalmar za mu yi aure kaɗai ya wadatar da ni duk wani bayani da ya ɗaura akai duk shirme ne a waje na. Na ɗau maƙudan kuɗi na bashi sannan mu ka bar wajen sa zuciya ta cike da farin ciki. Tundaga wannan rana na sawa kai na salama domin ance ni da Sa'eed za mu yi aure. Ko gayawa Sa'eed ban yi ba dan na san zai mun faɗa. Na riƙe abin a raina ni kaɗai... Saboda ni Bayan Sa'eed ya kammala degree ɗin sa ya ɗora da masters domin mu samu mu gama makaranta tare. Wannan karan tun kafin ayi hutu na kira Baba na ce ba zan zo Nigeria ba saboda zan tsaya yin project ɗi na. Bai musa min ba ya amince kai tsaye. Da na kira Amma na gaya ma ta sai ta dinga mun faɗa domin ta san saboda Sa'eed ne na ƙi dawowa gida. Ni dai ban damu ba tunda Baba ya amince... Kwamci tashi har Allah ya kawo mu ƙarshen karatuna inda ni Aaliyah Badamasi Bulama na kammala degree ɗina yayinda shi kuma masoyina Sa'eed Aliyu Modibbo ya kammala masters na shi. Mun sa dogon buri a zukatan mu. Da mun dawo Nigeria kafin mu tafi bautar ƙasa zan sanar da Baba maganar Sa'eed saboda muna gamawa sai a mana aure. Kasancewa an tabbatar min ni da Sa'eed za mu yi aure sai ban sa a raina za a samu matsala ba musamman idan na tuna cewa Baba yana so na ba zai min auren dole ba sai dai... ........................ Cikin ikon Allah ba mu jima da dawowa ba aka tura Sa'eed bautar ƙasa chan Minna. Ni kuma Borno, ban ji daɗi ba dan ina so mu tafi bautar ƙasa tare. Na je na samu Baba a falon sa da letter ɗin da niyyar ya min hanya a maida ni Minna sai na tarar da wani zance marar daɗin ji. Baba shi ya sa aka posting nawa Maiduguri saboda yana so na zauna kusa da gida. "Baba na yi karatu a ƙasar waje ma balle kuma bautar ƙasa a chan wani state, za ku iya ganina duk lokacin da ku ke so fa" na faɗa da sigar sakalci. "Aaliyah ki zauna a gida, ba na son ƙananun maganganu da na ke ji ana faɗa a kan ki" "Baba wani magana kenan?" Na faɗa cike da tsoron tambayar da na yi da kuma amsar da zan iya samu. "Aaliyah ba na son kusancin ki da Sa'eed. Dan kun yi makaranta ɗaya ba yana nufin ɗaya ku ke ba. Ki riƙe matsayin ki shima ya riƙe na sa" Baki na rawa na ce " Baba ina son Sa'eed" Bai yi mamakin kalamai na ba dan ya san da hakan tuntuni. "Ko ma mi ki ke ji game da shi ki yakice shi. Na riga na miki miji" Na fashe da kuka ina bashi haƙuri amma ko saurarata bai yi ba ƙarshe ma ya tashi ya bar min falon... Kalmar an min miji yana da girma a wajena, hakan na nuna ba ni da 'yan ci kwata-kwata. Ya kuma nuna cewa banida ikon zaɓar mijin da na ke so sai dai a zaɓa min. Sa'eed yana Minna bai san miya ke faruwa ba ni kuma ina Maiduguri ina fama da ƙunci. Wasa-wasa fa Baba ya ɗauke min wuta, yai biris da lamarina ya nuna matuƙar na cigaba da maganar Sa'eed a gidan nan zai aurar da ni tun ma kafin na gama bautar ƙasa na. Babu wanda ya damu da halin da na ke ciki, kowa nuna min ya ke bamu da ce da Sa'eed ba. Harta Jiji abinda ta ke nanata min kullum kenan. Sanah ce kaɗai ta yarda da soyayyata ta kuma supporting ɗi na... Na turawa Sa'eed wasiƙa akan halin da na ke ciki amma har yau bai tura mini amsa ba. Ina kwance a ɗakina ina duba tsoffin wasiƙun Sa'eed Amma ta shigo ɗakina. Na ɗaga ido na kalleta na kau da kai. Ta ajiye min wassu kaya a gabana ta ce, "ki sa wannan anjima za ki yi baƙo" "Ba zan sa ba" na faɗa kai tsaye. Amma ta min kallon banza ta ce " idan kin isa ki ƙi sa kayan nan mu gani. Ni da ke a gidan nan" Yadda ta ajiye kayan nan haka ta dawo ta same su bayan awa ɗaya da rabi. Faɗa ta shiga min sosai wanda ni kam ko ajiki na. "Ki tashi ki sa kayan nan Aaliyah ko na sassaɓa mi ki" Na kalli cikin idon ta na ce ba zan sa ba, idan za ta kashe ni to ta kashe ni amma ba zan sa ba. Ina ganin yadda ɓacin rai ya mamaye fiskarta lokaci guda amma ni ko a jikina. Ba ta ce ƙala ba ta fita daga ɗakin. Minti takwas bayan fitar ta sai ga Baba ya shigo ɗakin ran sa a ɓace. Na ɗan tsorata da ganin sa amma na dake. "Ɗan gidan Alhaji Wamako ya zo ganin ki ki shirya ki je ki same shi a falon baƙi" Sai da ya juya zai tafi ya ce " umurni ba shawara ba Aaliyah" ya faɗa kafin ya sa kai ya fita... Ina kuka ina saka kayan, ina kuma zagin Alhaji Wamako a zuciyata domin duk ƙauna da so daya nuna min tun ina yarinya ashe akwai abinda ya ƙimtsa min ne na baƙin ciki. Kayan kawai na sa ko kwalliya ban yi ba na wuce sashen Baba. Yana zaune a falo lokacin da na shigo, an cika gaban sa da tarkacen ciye-ciye da shaye-shaye. Shiga ta alfarma yai, shigan 'yan ma su ji da naira. Ba wannan ne karo na farko dana fara ganin sa ba, na taɓa ganin sa a Sokoto shekaru biyar da su ka wuce lokacin da mu ka je bikin ƙanwar sa. Ahmad Ibrahim Wamako kenan, babban ɗa a wajen Alhaji Ibrahim Wamako. Kamar yadda mahaifina ke ji da arziƙi da dukiya haka Alhaji Wamako ke ji da kuɗi da dukiya, sunan sa ya shahara a Nigeria da Africa baki ɗaya. Ban ko zauna ba na kalleshi na ce " kar ka bawa kan ka wahala Malam. Ina da wanda na ke so kuma shi zan aura. Ka nemi wata matar a gaba" Sai dana gama maganar sannan ya ɗago ido ya kalleni ya kwashe da wata mahaukaciyar dariya. *TSOHUWAR💖SOYAYYA* *©Azizat* Wattpad @000Azee *BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM* 1️⃣1️⃣ Free page *za'a samu cigaban wannan labari a 200, idan kuma ka biya kuɗin Sakatariyata to 100 za ka biya. Domin ƙarin bayani 08137311900* *........Aaliyah.........* Engagement Da gudu na shiga ɗaki na ina kuka. Wai miyasa komai ya lalace min ne cikin ƙanƙanin lokaci haka? Abinda na ke ta tambayar kaina kenan. Maganganun Ahmad Wamako babu tausayi aciki. "Dole na aureki Aaliyah, ko dan na raba ki da girman kai da tsiwar ki ta banza. Ki na da wanda ki ke so ko? To kuma ba wanda za ki aura sai ni, gara tun wuri ki kwantar da hankalin ki"... Gado na fara birkitawa kafin na shiga wurgi da kayan ɗakin. Sai da na yi watsi da komai kafin na zube a ƙasa ina kuka ban damu da kwalban turaren da ya ke fashe a ƙasa ba, ban kuma damu da zafin da na ke ji ba saboda yadda kwalbar ta yaga min gefen gwiwa ba, zafin da na ke ji daga zuciya ta ke, zafin da na ke ji daga ruhi na ne. Sanah ce ta shigo ɗakin ta sameni ina kuka. Ta zo da gudu ta rungumeni, mun jima a haka kafin ta rarrasheni ta miƙar da ni wanda hakan ya sa ta ga jinin da ke ƙasa da kuma ciwon da na ji. Sai da ta kai ni bakin gado na zauna kafin ta fita da gudu dan ta ɗauko first aid box a ɗakin Amma... Kafin dare zazzaɓi mai zafi ya kama ni, bayan Sanah da Jiji babu wanda ya shigo ɗakina. Amma shareni ta yi duk da kuwa ina da tabbacin ta san sarai abinda ya sameni. Ba wannan ne ma yafi ɗaga mun hankali ba irin yadda Sa'eed ya shareni, babu ɗaya cikin wasiƙuna da ya amsa. Yana so ya ce duk kuka na duk roƙo da na yi cikin wasiƙun bai damu ba. Chan ƙarfe takwas Sanah ta shigo min da abinci, ta tisa ni a gaba dole sai da na ci kaɗan kuma na sha magani. "Sanah, Sa'eed ya gujeni" na faɗa ina hawaye. "Bai guje ki ba Aaliyah, yana tareda ke" "Aaliyah" ta kira suna na a hankali. Ganin ba ta ce komai ba ya sa na ɗago ido na kalleta. "Ki yi haƙuri dan Allah, na san ban kyauta miki ba" Ban yi magana ba ban kuma janye ido na daga kallon ta da na ke ba. "Duk wasiƙun da ki ke turawa Sa'eed ba sa isa gareshi" Na zaro ido ina jiran ta min sauran bayani. Domin hankalina bai kama maganar da ta yi ba. A ƙalla na aika wasiƙu sama da ishirin cikin wata uku kacal. "Tun da Sa'eed ya tafi Amma ta sa aka dena aika ma sa wasiƙar ki, haka shima ta shi wasiƙar an hana ma a turo ta nan" Hawayen da da su ka kafe da ne su ka cigaba da kwaranya a ido na. Duk zuwa post office a banza kenan, duk abinda na rubuta ya bi iska kenan tunda bai isa inda ake so ya je ba. Ta ya Amma za ta min haka? Ta ya Sanah za ta barni na yi ta wahalar banza. "Ki yi haƙuri Aaliyah, ni ma ban sani ba sai kwanaki da Amma ke hiran da Hajiya. Na so gaya mi ki amma ina tsoro" Muryan Sanah ya ƙatse ni daga dogon tunanin da na ke ciki. Na yi wuff na tashi domin na je na ji dalilin wannan rashin mutunci da Amma ta min amma Sanah ta riƙe hannuna. "Aaliyah ba abin da zai chanza idan ki ka je, ki tsaya mu nemi wata mafitar" Jikina rawa ya ke saboda yadda zuciya ke ci na. Ba dan girman Uwa ba da ba abinda zai hana a wannan dare na je na yiwa Amma rashin mutuncin da har ta koma ƙasa ba za ta taɓa mantawa ba... Washe gari Sanah ce ta tafi da doguwar wasiƙar da na rubutawa Sa'eed, inda na ke ma sa bayanin abinda ke faruwa. Na sani indai ni na kai ba za su aika ba shiyasa Sanah ta ce za ta kai wa wata ƙawarta ta aika da wasiƙar. Mai kuɗi kenan, kuɗi da suna da gidan mu ke da shi ya sa ake son raba tsakanin masoya amma ni Aaliyah ba zan yarda ba. Ko da zan rasa komai indai zan kasance da masoyina to babu komai... ............................. Kasancewa ban kuma ɗaga hankalina ba ya sa aka cigaba da shirye-shiryen biki. Ahmad Wamako bai kuma dawowa ba hakanan Amma ba ta tambayeni ya mu ka yi da shi ba. Dama mi za ta tambaya, abu ne da tun farko ba a nemi shawarana ba balle ya zama ina da abin faɗa cikin lamarin. Satin da ta zagayo Sanah ta amso min wasiƙar Sa'eed.  Hannu na rawa na warware takardar na fara karantawa. Ashe duka aka zalincemu, shima bai san wasiƙun sa ba sa isowa gare ni ba. Ina gama karanta takardar na cillar da ita na fashe da kuka. Taya Sa'eed zai ce na yi haƙuri na cigaba da addu'a, ta ya zai ce zai yi ƙoƙari ya zo idan ya samu dama. Sanah ta ɗau wasiƙar ta karanta kafin ta ƙaraso wajena ta zauna, dafa kafaɗuna ta yi kafin ta ce "Aaliyah maganar Sa'eed gaskiya ce, addu'a kawai za ki cigaba da yi nima kuma zan taya ki" Da wata durƙusashshiyar murya na ce "Sanah ba zan iya son wani namiji bayan Sa'eed ba, ba zan iya auren wani namiji idan ba Sa'eed ba. Idan aka takura ni mutuwa zan yi, mutuwa zan yi Sanah" na ƙarasa maganar ina sheshsheƙar kuka. Sanah ta rungumeni tana lallashina... A satin da ya zago aka sa mana rana. Ina zaune a ɗaki Sanah ta shigo, ni dama daga na dawo daga wajen PPA ɗina ina nan ƙunshe a ɗaki bana kuma fita sai washegari. Duk wanda ya zo cikin 'yan uwa na ɗaki zai shigo ya sameni, yawancin su haushi na ke basu, su yi ta zagina wai ina ƙyashin auren ɗan gidan Alhaji Wamako. Ba wanda na ke tankawa har su gama abinda za su yi su jajuɓa jiki su fita min daga ɗaki. "Aaliyah ƙarshen watan da za mu shiga aka sa bikin ki ya za kiyi?" Murmushi mai ciwo na yi sannan na ce "ba zan auri Ahmad Wamako ba" Sanah dai kallon da kamar wuya ta ke min ta rasa abin faɗa. Ni kuma na ƙudura a raina da na auri Ahmad Wamako gara na rasa rayuwata ko kuma na bi uwa duniya... Bayan Sanah ta fita a ɗakin na tashi na je ɗakin Amma inda na samu tana riƙe da wayar tarho, maganganunta ya tabbatar min da 'yan uwanta na Niger ta ke magana. Sai da ta gama ta ajiye kafin ta juyo ta kalleni, a ƙasa na tsugunna a gabanta, fiskana duk ta kumbura saboda yawan kuka da rashin barci. "Amma dan Allah indai ke ki ka haife ni, ki yi haƙuri ki yiwa Baba magana a fasa aurena da Ahmad Wamako. Ba na son shi, ba na son auren shi. Sa'eed kaɗai na ke so ba zan iya rayuwa babu shi ba" "Aaliyah kenan, dan ba kya son shi yanzu idan aka yi aure za ki so shi. Sa'eed ba tsaran ki ba ne, ba ta inda kuka dace, ki manta da shi ki rungumi ƙaddarar ki" Hawayen da su ka taru a idona su ka fara saukowa, ba zan iya tuna rana ta ƙarshe da na tashi na wuni har washe gari ban yi kuka ba. Ƙila tun a Cambridge lokacin muna tareda Sa'eed. "Amma, Sa'eed musulmine, mai ilimi, kyakykyawar zuciyar sa ya sa kyawawan halayen sa su ka bayyana. Sa'eed mutum ne na gari, babu wata mace a doron ƙasa da ba za ta yi alfahari da Sa'eed ba. Amma saboda shi maraya ne?, saboda shi talaka ne? Saboda shi ɗan fulanin ƙauyen Durum ne?" "Aaliyah" Amma ta kira sunana da ɗan ƙarfi, ban sani ba ko maganganun da na yi sun shigeta ne ban kuma sani ba ko dai mamakin maganganuna ta ke ba. "Amma, Sa'eed ya yi karatu, nan ba da jimawa ba zai samu aiki. Ba sai kun min komai ba na yafe komai na ku, rufin asirin sa da kwanciyar hankali da zan samu tattare da shi ya fi min komai. Amma ki ceci rayuwata ki sa Baba ya fasa auren nan" "Aaliyah ke wani irin taurin kai gareki ne. Maganar ki da ɗan gidan Alhaji Wamako an yi shi kusan shekaru goma da su ka wuce, babu yadda za ayi rana ɗaya a ɓata shirin da ake yi tun shekara da shekaru" da ƙarfi ta yi maganar cikin masifa. A hankali na furta " akwai Sanah, idan burin ku haɗa aure tsakanin iyalen Bulama da Wamako ne, akwai Sanah. Ku haɗa Sanah da Ahmad, za ta iya zama da shi. Ki tausaya min Amma zan iya mutuwa idan na rasa Sa'eed" Ban sani ba ko dan Amma ma auren haɗi aka ma ta ya sa ba ta damu da halin da na ke ciki ba, ban sani ba ko dai Amma ba ta san soyayya ba ne, ba ta san zaƙin soyayya da ɗacinta ba, ba ta san mi ake kira so ba. Abinda na sani shine ni Aaliyah na san so na kuma san zaƙin sa, ba zan bari na samu ɗacin ta ba saboda son zuciya irin ta iyayena... *TSOHUWAR💖SOYAYYA* *©Azizat* Wattpad @000Azee *BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM* 1️⃣2️⃣ Last free page *za'a samu cigaban wannan labari a 200, idan kuma ka biya kuɗin Sakatariyata to 100 za ka biya. Domin ƙarin bayani 08137311900* *The Plan* *........Sa'eed........* Na fara samun karaya ne gameda soyayyar mu lokacin da mu ka dawo daga Cambridge. Ina zaune a kan benchi kusa da Baffa Manu mu ka ji horn ɗin mota. Baffa yai sauri ya tashi zai je ya buɗe ƙofar na yi wuff na rigashi. Motar Alhaji Badamasi Bulama ne ta shigo cikin gidan. Ina gama rufe gate ɗin na ji muryan Baba Umar wanda ya ke tsohon dreban Alhaji Badamasi ne yana kirana. Na ƙarasa wajen sa da sauri ina gaida shi. " Alhaji ya ce ka sameshi a falon sa yanzu"  abinda ya faɗa min kenan. Ban kawo komai a raina ba na bi bayan Alhajin. Ina shiga falon sa na zauna ƙasan kujera ina ƙarewa falon kallo ganin yadda falon yai kyau saboda furnitures da aka sake. Shekaru shida kenan rabona da shiga falon, tun ranan da Aaliyah ta kawo ni na zo na nuna ma sa admission ɗina. Na yi aƙalla minti Ishirin zuwa ishirin da biyar a wajen kafin Alhaji ya sauƙo ƙasa, lokacin ya yi wanka ya chanja kaya zuwa jallabiya ta shaƙatawa. Daga inda na ke zaune na duƙa na gaida shi. Cikin fara'a ya amsa mini tareda jinjina mini bisa ƙoƙari da na yi a makaranta. "Sa'eed sai ina yanzu?" Ya sako tambayar bayan dogon shiru da ya karaɗe falon. "Bautar ƙasa Alhaji" na faɗa kaina a ƙasa. "Minna ko?" Ya tambaya bayan ina da tabbacin ya san amsar tambayan. Na amsa ma sa da eh "Ka na da ƙwazo da hankali, ga kuma tarbiyya" yai shiru yana nazarta na duk da ƙasa na ke kallo amma ina ji ajikina yadda idon sa ke yawo a kaina. "Sa'eed na yiwa Aaliyah miji" Da sauri na ɗago ido na kalleshi wanda hakan ne karo na farko a tarihin rayuwata da kalleshi ido cikin ido. "Ba sai na maka dogon bayani ba,na san ka fahimci abinda na ke nufi" A wahale na saukar da ido na ina jin maganar Alhaji na tsatstsafomin da wani zafi daga dukkan jijiyoyin jiki na. Abubuwa dayawa su ka fara yawo a kwanya ta.  Duk wani tsari, shiri, buri  ko mafarkina a kan Aaliyah su ka fara min yawo a ƙwaƙwalwa ta. Ina sane da banbancin da ke tsakanin mu, ina sane da cewa abu ne mai wuya na samu Aaliyah. Sai dai na watsar da komai saboda na yarda da soyayya ta kuma na yarda da Allah. Ban fito daga gida ma su arziƙi ba amma arziƙi na Allah ne hakanan ban cire rai da samun sa ba. A duk lokutan da na yi tunanin rana irin wannan, na kan yi ƙoƙarin janye tunanin da cewa Allah shi ne ke tsara komai, kuma duk abinda ya tsara wa Bawan sa ba makawa sai ta auku gareshi.  Soyayyar da na ke wa Aaliyah daga Allah ne haka nan kuma ko da mun rabu ma daga Allah ne. Tawakkali da na yi da wannan ya sa ban taɓa ɗaga hankalina ba sai ma na sawa kai na samun Aaliyah fiye da rashin samun ta. Sauran bayanan da Alhaji yai duk ba wanda ya wuce fatar kunnena balle har su shiga su samu mafaka a cikin ƙwaƙwalwata har ma na fahimci abinda ya faɗa... Ina son komawa wajen Baffa Manu amma kuma ba zan iya zuwa na sameshi a yanayin da na ke ciki ba. Na dinga takawa a hankali har na kai ɗakina, duhu na ga ɗakin ya mun lokacin da na shiga duk da kuwa hasken rana da ya karaɗe ɗakin. "Sa'eed na yiwa Aaliyah miji" maganan Alhaji ya dinga dawo min. Na tsugunna a tsakiyar ɗakin ina dafe da ƙirjina, farat ɗaya soyayyar Aaliyah ya shigeni ba tareda na shirya ba, gashi yanzu ma farat ɗaya ake son raba ni da ita. Na jima a durƙushe a wajen ba tareda na san minene mafita a gareni ba. Tabbas rashin Aaliyah a rayuwata tamkar rasa nawa rayuwar ne gaba ɗaya. Na dinga maimaita Innalillahi saboda na samu sauƙin ƙuncin da na ke ciki, ban iya barin wajen ba sai da Jiji ta shigo ta sameni a haka. Ganin yadda ta shiga ruɗu da yanayin da ta ganni ya sa na daure na tashi na yi murmushin da ko makaho ya san ba ta kai zuci ba. Masallaci na nufa bayan na nunawa Jiji lafiya na ƙalau kawai gajiya ce da kuma ciwon kai. Ban dawo gida ba sai ƙarfe goma na dare duk da kuwa na san Aaliyah za ta yi ta ziryar nema na. Ban ma tsaya a masallacin ƙofar gida ba saboda kar ma ta aiko a kirani. Masallacin da ke chan cikin anguwa na nufa ina mai neman samun nitsuwa idan na je chan. A ƙofar gida na samu Aaliyah da Baffa su na hira. Ganina ya sa ta miƙe tsaye tana faɗin " Sa'eed are you Ok? lafiya ka yi dare yau?" Na sani ba dan Baffa na wajen ba ba abinda zai hana ta rungumeni. Ina ganin tsantsar kewa da damuwa a ƙwayar idonta duk da kuwa hasken farin wata ne kaɗai ya haska wajen. "Lafiya Aaliyah, na tsaya karatu da wani malami ne" Na sani ba ta gamsu da bayani na ba, dan Aaliyah tana da saurin gane ƙarya musamman idan ni na faɗeta. A hankali ta furta "amma dai ka san zan jira ka ko" "Ki yi haƙuri Aaliyah, mantawa na yi" Fiskarta sam babu alamar yarda sai ma fushi, ta yiwa Baffa sai da safe ta wuce ɓangaren su. "Barka da dare Baffa" na faɗa ina ƙoƙarin shiga gida "Lamiɗo zo ka zauna" Ya faɗa yana nuna min gefen tabarma kusa da shi. Ban musa ba na ƙarisa wajen na zauna ina sauke ajiyar zuciya. "Ina son barin nan, ina son komawa cikin 'yan uwana, Shekaru sun jaa. Sabo da mutanen gidan nan ya sa na kai har iya tsawon wannan lokaci ban tafi ba. Amma idan mu na da rai ƙarshen shekaran nan zan koma gida" Har ya ƙarasa maganar sa ban ce ƙala ba domin ba abinda zan ce ɗin. "Lamiɗo" ya sake kira wannan karan da sigar jan hankali. "Na'am Baffa" na amsa ma sa tareda yaƙinin magana zai min makamancin na Alhaji. "Na san ka na son yarinyar nan sosai, amma ka yi haƙuri ka janye jiki daga gareta, ba na fata a samu matsala a iya zaman da ya rage min a ƙarƙashin Alhaji. Ka yi haƙuri Lamiɗo na" Hannuna da ke rawa Baffa ya kamo ya riƙe yana faɗin "ka cigaba da addu'a Lamiɗo, har Allah ya sawa zuciyar ka nitsuwa. Rashin masoyi akwai ciwo" Mun jima da Baffa a wannan dare yana lallashina. Kafin mu ka shiga ciki dan bacci, ni kam bacci ƙaurace mini yai gaba ɗaya. Ina son Aaliyah, ba na tunanin zan taɓa son wata bayan ta... Cikin kwanakin da na yi kafin na tafi bautar ƙasa zuciyata ta yi laushi. Ba zan iya furtawa Aaliyah halin da na ke ciki ba, ina so ko da na ƙarshe ne to na kasance da ita, ina kallon murmushin da ke shimfiɗe a kyakykyawar fiskarta, murmushin da domin Sa'eed kawai ta ke yin sa. Ban yi mamaki ba da na samu tafiya amma Aaliyah ba ta samu tafiya tareda ni ba, na san shirin Alhaji ne dan kar ma mu tafi tare. Lokacin da ta samu tafiya ma maimakon Minna da ta sa a farko sai a ka sa ta Maiduguri bayan kuma ba ta cika da Maiduguri ba. Ranan da zan tafi kallon ƙarshe na yiwa Aaliyah domin ni kam na san daga lokacin Aaliyah ta yi min nisa. "Sa'eed ka ga muna gama bautan ƙasa sai aure. Za mu fara zama a Durum kafin mu tafi duk inda aiki ya kai ka. Na missing ƙauyen ku" Yadda ta ke maganan hakanan na ke jin zafi a zuciyata. Ina ma nima wani ne ko kuma ɗan wani ne a ƙasar. Ina ma Aaliyah ba 'yar kowa ba ce. Ina ma muna duniyar da babu haramci tsakanin auren talaka da maikuɗi. "Beloved ba ka ce komai ba?" Ta katse tunanin da na ke yi. Na yi murmushin yaƙe na ce "duk abinda ki ke so haka za ayi" Da na ɗau jaka na zan tafi ta riƙe hannuna. " ba goodbye kiss ne?" Na yi seƙeƙe ina kallon ta, ba wai dan ba na son yi ba ne a'a sai dan ina gudun haƙurin da na ke ta yi na tsawon lokaci zai iya ƙarewa. Ta matso kusa da ni sosai ta    yi ɗegel da ƙafafuwanta saboda ta yi daidai da ni. Ta sa hannu ta shafa fiskata ta ce " na kusa zama mallakin ka duniya da lahira masoyina" ta yi murmushi sannan ta fara kissing ɗina.... Tunda na tafi na ke cikin ƙunci amma a hankali ina addu'a abin ya fara min sauƙi. Sai da na yi wata ɗaya kafin na rubutawa Aaliyah wasiƙa amma har wani watan babu amsa, na sake kai wani wasiƙan shima shiru. Da bincike na gano abinda ke faruwa, jin mahaifiyar Aaliyah ce ta hana kai wasiƙuna ya sa na haƙura na fawwalawa Allah lamarina ina neman ya taimaka min kafin rashin Aaliyah ya ja min matsala a ƙwaƙwalwata... Bayan mun samu mafitar aikawa juna wasiƙa Aaliyah ta aiko da wasiƙar da ta rikita ni. *Sa'eed ka zo gida, idan ba ka zo ba zan kashe kai na, Ba zan iya auren wani bayan kai ba* Iya abin da ta rubuta kenan. Na san halin Aaliyah na san za ta iya aikata abinda ta ce shiyasa tun farko na ɓoye ma ta abinda Alhaji ya faɗa. Ba ni da niyyar komawa Maiduguri har sai na ƙare bautar ƙasa ta amma wasiƙar Aaliyah ya chanja min ra'ayi. Ba ɓata lokaci na nemi a bani hutun kwana biyu amma hakan bai yiwu ba dole sai dai na haƙura zuwa ƙarshen sati... Ranan Jumu'ah da yamma na hau mota sai Maiduguri, ba mu isa ba sai ƙarfe huɗun Asuba. A park na kwana sai da safiya na nemi taxi na wuce gida. Baffa da Jiji sun yi mamakin ganina da sassafiya haka, na nuna mu  akwai abinda na zo yi ne kuma kwana biyu zan yi na koma. Baffa bai yi magana ba amma Jiji ta ritse ni a ɗaki tana neman tabbatar da zargin ta. "Saura kwana shatara auren Aaliyah. Lamiɗo Dan Allah duk abinda ka zo yi ka yi ka tafi ba tareda tashin hankali ba" Na kalli Jiji wanda ita ta zame min uwa a yanzu na ce "Insha Allahu ba tashin hankalin da zai faru"... Ban samu ganin Aaliyah ba sai bayan Azahar. Tana shigowa ɗakin ta faɗa jikina tana kuka. Tsikar jikina ya tashi saboda yadda wani ƙanshi ke fita a jikinta, duk da Aaliyah ma'abociyar ƙanshi ce amma wannan ƙanshin daban ya ke. "Sa'eed wai aure za'amin, wai ƙarshen wata aurena da Ahmad Wamako. Ka taimakeni Sa'eed ba zan iya auren sa ba, mutuwa zan yi" "Shhhhhh" na sa yatsata na rufe bakin ta. "Ban da zancen mutuwa Aaliyah, kin san hukuncin kisan kai kuwa?" Na faɗa ina ƙoƙarin danne duk wani raɗaɗi da na ke ji a zuciyata. "Laifin ka ne ai, da ka amince da ni tun a makaranta da yanzu babu yadda za'ayi su raba mu" Ina ƙoƙarin shawo kan ta amma ta ƙi saurarena. Ta riga ta tsarawa kan ta mafita wanda duk ciki babu mai daɗin ji. "Ka amince mu gudu mu je mu yi aure Sa'eed. Its the only way we can be together" "Aaliyah" na faɗa a hankali "Kar ka ce a'a, domin zan aikata abinda ba ka yi tsammani ba" "Please Aaliyah, mu yi haƙuri, Allah ya...." Dariyan da Aaliyah ta fashe da shi ya sa na kasa ƙarasa maganar da na ke yi. "Mu yi haƙuri fa ka ce. Sa'eed son da ka ke min har ya yi raunin da za ka sadaukar da ni ga wani banza. Har za ka iya rayuwa babu ni? Har za ka iya haƙura da ni a rayuwar ka? Ta ya zan fara zama da mutumin da bayan sunan sa ban san komai game da shi ba?. Ta ya zan manta da soyayyar ka da ta riga ta zama jinin jiki na?. Ta ya za ka ce Aaliyah ta sadaukar da farin cikin ta saboda son zuciya irin na iyaye na, ba su damu da ni ko farin ciki na ba, abinda aurena zai haifar su ke hangowa. Sa'eed ban shirya biyayya wa auren dole ba tunda addini ma ya hana hakan" Shiru na yi ina nazartar maganganunta. Nima daurewa na ke yi amma na san rashin Aaliyah zai iya jawo min matsala a sauran rayuwata. To ya zan yi? Ban taɓa burin na auri Aaliyah ba tareda yarda da amincewar iyayen ta ba. "Aaliyah albarkar iyaye ta fi komai" na faɗa murya na rawa saboda yadda hawayen Aaliyah su ka sa na ji jikina yai sanyi. "Ka zaɓa min halaka kenan Sa'eed?" Na zaro ido ina girgiza kai. "Idan ba ka amince mu gudu ba kashe kai na zan yi" Na cigaba da girgiza kai ina ƙoƙarin magana amma na kasa saboda wani abu daya toshe min maƙoshi. Ta ɗan ja baya kaɗan kafin ta ce " ka yanke shawara daga yanzu zuwa dare, duk abinda ka yanke shi zai tabbatar da rayuwa ta a duniya ko kuma mutuwa ta" "Aaliyah" Ta fice daga ɗakin da gudu tana hawaye. Nima ɗin hawayen baƙin ciki su ka samu damar zubowa daga ido na... Duk inda na je na dawo zancen ɗaya ne, na amince da buƙatar Aaliyah. Tsoro na ka da na ƙi amincewa Aaliyah ta kashe kan ta kamar yadda ta faɗa. Idan haka ta faru zan ƙarasa rayuwata cikin nadama da ƙunci ina dana sanin ƙin amincewa da buƙatar ta da na yi... Da dare ta zo jin abinda na yanke na kuma tabbatar ma ta na amince mu gudu amma da sharaɗi ba za mu yi aure ba har sai iyayen ta sun amince. "Ka na ganin ko shekara nawa na yi ban dawo gida ba idan na dawo Baba zai yarda ka aure ni?" "Ina da yaƙinin zai amince Aaliyah" na faɗa duk da kuwa na san da kamar wuya. Aaliyah ce ta shirya komai ita ta tsara tafiyar mu da inda za mu je. Lafiya zamu je, a nan za mu zauna har iyayenta su haƙura da maganar auren ta da Ahmad Wamako. Duk da kuwa ban taɓa zuwa garin ba amma na amince da hakan. Acikin rai na ina fatan idan mun je a hankali na nutsar da Aaliyah da maganar kisan kai da ta ke ta iƙirarin yi saboda yanzu na san tsoron auren ya ke sa ta ke wannan batu. Bayan tafiyar ta na yi alwala na yi sallah ina roƙon Allah ya kawo mana mafita ya kuma sa kar tafiyar da za mu yi ya jawo ma na sharri maimakon alkhairi da mu ke fata.. Washe gari da safe kusan ƙarfe goma ina zaune a ɗaki ina saƙe-saƙe a raina sai ga Musa ƙanin Aaliyah wanda su ke kira da Kalim ya shigo ɗakina. "Hamma Sa'eed wai ka je in ji Baba" ya faɗa lokacin da ya shigo ɗakin ba ko sallama. Na kalli yaron wanda shi ne autan Alhajin na ce " Baban yana ina?" "Yana Garden" ya faɗa yana cusa yatsar sa a hannu yana tsotsa. Na yi mamakin ya aka yi har Alhaji ya san ina gari bayan ko haɗuwa ba mu yi da shi ba, asalima ba kowa ya san ina gidan ba. Na tashi na sa rigata na bi bayan Kalim wanda ya fita daga ɗakin ba jimawa... *........Aaliyah.......* Tunda na samu Sa'eed ya amince an wuce wajen maganar ma idan mun je ba aure za mu yi ba jin sa na ke yi kawai. Idan har zan dawo gida to sai dai idan da auren Sa'eed zan zo. Na san halin Baba na, ba zai taɓa amincewa da aurena da Sa'eed ba kuma ko da ban auri Ahmad Wamako ba wani ɗan maikuɗin za a kuma jajuɓomin. Idan da auren Sa'eed akai na kuwa duk fushin sa ƙarshe haƙura zai yi ya bar ni na yi rayuwata da masoyina. Ko Sanah ban faɗawa shiri na ba saboda tsoron kada ta faɗa duk da kuwa na san za ta riƙe min amana amma Sanah tana da tsoro idan Amma ko Baba ta dage akan ta gaya mu su inda na ke za ta faɗa. Ba kasafai na ke fita ba saboda gyara da aka fara yi min. Idan na fita to na je wajen aiki ne. Kwantar da kai da na yi tun daga ranan da na yiwa Amma magana ya sa ta ɗan sake min ba kamar da ba. Ko da aka fara min gyara ban yi gardama ba, duk abinda aka bani na ci ci na keyi hakanan wa ni turara jiki da sauran shafe-shafe duk ina zama ana min. Ni kam duk tanadin nan Sa'eed na ke hangowa ba Ahmad Wamako ba. Safiyar ranan da za mu gudu na samu Amma a ɗaki akan zan je gidan ƙawata  Daula da ba ta da lafiya ba ta musa ba ta ce na je amma na dawo da wuri. Dreban ta ne ma ya kai ni gidan su Daula.  Zuwan da na yi kuwa rufa ido ne dan daga gidan na chanja kaya na fita ta ƙofar baya. Dreba na nemo na ma sa bayanin inda zai kai mu da kuma inda za mu haɗu da shi. Kuɗin da ya buƙata na ga sun yi kaɗan na ƙara ma sa ninkin sa tareda alƙawarin indai ya kai mu garin Lafiya zan bashi wani kuɗin adadin wancan. Dreban mai suna Bdliya yai godiya ya kuma nuna min lallai zai cika alƙawari. Na koma gidan su Daula daga nan Dreban Amma ya mai da ni gida... Kuɗi da hotuna da sarƙoƙi, ɗankunne da awarwaro na gwal kawai na saka a sabuwar Jaka ta, wanda daga Cambridge na taho da ita kuma ban taɓa amfani da ita ba. Kuɗin da na sa zai isa mu kama gida a chan sannan mu fara wani sana'a kafin abubuwa su dai-dai ta, idan ma kuɗin ba su isa ba za mu iya siyar da jewelries ɗi na. Bayan na haɗa komai na sa jakar a ƙarƙashin gado na cigaba da hidima ta... Ƙarfe shaɗaya da rabi na dare na fito daga ɗaki ɗauke da jaka ta. Amma ke da girki dan haka tana sashen Baba. Ta ƙofar kitchen na fice daga ɓangaren mu ina sauri har na tafi wajen katanga. Lokacin da Baba ya sawa yayana Aliyu dokar kulle ta baya wajen katangar gidan ya ke haurawa ya fita. Duk da katangar akwai tsayi amma ya riga ya yi rami ta inda zai taka ya hau. Da yamma sai da na zago ta wajen na tabbatar ramukan na nan ta yadda zan iya hawa... Jaka ta na fara jefawa kafin na diro ƙasa, sosai na bugu dan har ina tunanin gwiwowina sun kukkurje amma ba matsala ta ba ce, matsalata na bar gidan mu, matsalata na bar garin mu, matsalata na auri masoyina Sa'eed. Gudu- gudu sauri-sauri haka na dinga tafiya har na kai inda na ce Bdliya Dreba ya jirani. Da mamakina sai ban ga Sa'eed ba, tun a daren jiya na gaya ma sa plan ɗina, sannan yau da yamma da na je ɗakin sa na  ajiye ma sa wasiƙa mai ɗauke da ƙarin bayanin inda za mu haɗu da sunan dreban da kamannin sa. Dole ne idan har ya shiga ɗaki sai ya ga wasiƙar saboda na ajiye ne a ƙarƙashin pillow kuma muddin Sa'eed zai kwanta to dole sai ya gyara gado. Balle ma na gaya ma sa idan na zo ban same shi a ɗaki ba zan bar ma sa saƙo. Amma da ta sani a gaba tana nuna mi ni hotunan wa su kaya ya sa ban samu sararin sake zuwa na duba shi ba. Ina rungume da jaka a cikin mota ina jiran zuwan Sa'eed amma babu shi babu dalilin sa. Ba ni da agogo a tareda ni amma na yi hasashen a ƙalla zan kai minti talatin a wajen. Ina cikin mota sai ga wata mota ta hasko mu, na sa hannu na kare ido na saboda ƙarfin hasken. Motar ta yi parking  aka buɗe ƙofa, tunanina Sa'eed ne dan ban gani sosai saboda hasken fitilar motar da har yanzu ba a kashe ba. Sai da mutumin ya kusa isowa motar mu na ga ba Sa'eed ba ne. Maimakon Sa'eed yayana Bukar na gani. Na yi wuff na fito daga motar na ranta da gudu, shima ɗin ya bi bayana da gudu yana faɗin na tsaya.  Gudu na ke yi kamar rai na zai fita hakanan kuma shi ma Bukar bai bar bina ba daga ƙarshe ma maimakon gudun mutum ɗaya sai ji na yi kamar mutum biyu ke bina. Ina cikin gudu Bukar ya damƙoni ta baya. "Ka sake ni, ka sake ni in tafi"  inaaaa, duk ihu da kuka na Bukar bai sarara min ba haka ya saɓani a kafaɗa har lokacin ina damƙe da jaka ta ina kuka ina kiran Sa'eed. Haruna ne a gefen Bukar ɗin, shi ne wanda ya biyo Sanah wanda tsakanina da shi wata goma ne cur na bashi, amma saboda shi namiji ne yadda yai girma ka ce ya girmeni da shekara biyar ne. Motar su su ka sani ta ƙarfi,  gefen dama na Haruna gefen hagu kuma Bukar. Ina jin dreba ya ja mota na ƙara sautin kuka na ina kiran " SA'EED"... Anan na kawo ƙarshen free pages na Tsohuwar soyayya. *Shin ya labarin Aaliyah Badamasi Bulama bayan wannan dare?* *Ya rayuwa ta kasance wa Sa'eed Aliyu Modibbo bayan ya saɓa alƙawari* *wai ya za ta kasance tsakanin Zaid, Zarah da Aaliyah?* *ko kun yarda cewa kuɗi zalla ba sa saka farin ciki?* *shin dole ɗan maikuɗi sai 'yar maikuɗi* Za ku samu cigaban labarin idan kun biya 200 kacal ga wanda ya biya Sakatariya ta kuma zai biya 100. *13-The wedding* Wannan karan kuka Aaliyah ta ke yi sosai har da sheshsheƙa. Zaid ya ajiye diary ɗin a gefe ya zuba ma ta ido, yadda ka san 'yar yaye haka ta ke kuka, ko mutuwa aka mata albarka. "Idan ba ki dena kukan nan ba zan fasa karatun nan, and that will be all. Ke yarinyace da za ki dinga kuka kaman wanda aka zane ki?" ya faɗa yana hararanta dan ta bashi haushi. "I'm sorry" ta faɗa tana ƙoƙarin tsaida kukan ta... *A* Suna fitowa dani daga mota kai tsaye sashen Baba su ka nufa da ni, a lokacin na dena kuka kuma na dena kiran sunan Sa'eed. Ba abinda na ke hangowa kai na irin baƙar rayuwa da zan yi a gaba, rayuwa mai ƙunci rayuwar da babu farin ciki, tabbas na sani tunda na rasa damata yau, tawa ta ƙare kenan. Zaune mu ka samu Baba da Amma a falo dukkan su sanye da kayan bacci. Kallo ɗaya na mu su na ɗauke kai na daga gare su. Baba ya tako wajen da na ke tsaye rungume da jaka ina ƙyarma kamar wadda aka tsamo daga cikin ruwan sanyi. Wani wawan mari Baba ya saukemun sai da na faɗi ƙasa, na dafe gefen fiskata tareda ɗagowa da sauri ina kallon sa ido cikin ido. "Wallahi Wallahi idan ba ki nitsu an yi bikin nan lafiya ba. Sai na tabbatar miki da cewa ni na haifeki kuma ina da iko da ke" Ban ce ƙala ba sai ma cigaba da kallon sa da na ke yi, ina ganin son zuciya ƙarara a tareda shi. Ta yaya Uba zai yi watsi da farin cikin 'yar sa saboda wani buri na shi na duniya? Ta ya zai take abinda addini ya ce ya bi tsarin da 'yan Adam su ka shimfiɗa saboda cimma kan su wani alfanu na banza wanda aka shimfiɗa saboda zalunci da son zuciya. "Idan ka aura min Ahmad Wamako ka zalunce ni Baba, ba zan taɓa yafe ma ka ba" na faɗa ba tareda tsoro ko fargaba ba. Har zuciyata kuma abinda na faɗa ɗin haka ya ke. Baba ya kalleni da mamaki ya ce "ni Aaliyah ki ke faɗawa haka? Ni?" Ya jaddada maganar ta hanyar nuna kan sa. Ban cire ido na acikin na sa ba saboda zuciyata ta riga ta bushe. Ya juya ya kalli Amma ya ce "kin ga abinda 'yarki ke faɗi ko. To ki gaya ma ta ko mutuwa za ta yi sai an ɗaura auren nan" Ya kalli su Bukar ya ce " ku je ku kulleta a ɗakin ta" daga haka ya haura sama cikin fushi. Tsananin tashin hankali da ɓacin rai na gani a idanun Amma, wanda ya haɗu da tsoro da fargaba. Dama ita mace ce mai saurin rikicewa musamman idan akan Baba ne, tana tsoron Baba sosai abinda na fiskanta a yanayin zaman su kenan. To ba dole ta rinƙa tsoron sa ba, aure ne aka yi babu ɗigon soyayya ko ɗis aciki. Sai yanzu na ke ganin da gayya Amma ta ka sa goyon bayana akan soyayya ta da Sa'eed, itama auro ta aka yi saboda cimma wani buri. Haruna ne na ya ja ni muka bar falon. Sai da mu ka je tsakiyar ɗakina sannan ya tunkuɗani na faɗi ƙasa. "Kin cika taurin kai Aaliyah. Miyene aciki idan kin auri Ahmad Wamako? Mutum ga kyau ga kuɗi, mi kuma ki ke buƙata?" Na ɗaga ido na kalli Haruna wanda ya ke matsayin ƙanina amma ya ke gaya min magana kamar ƙanwar sa ko 'yar sa. "Kyau da kuɗi su ne buƙatun wanda bai mallake su ba Haruna, ga wanda ya ke da su kyakykyawar zuciya da kyawawan halaye su ne abu mafi soyuwa a gun sa" Tsaki ya ja ya ce " a littattafai kenan Aaliyah, gara ki rungumi ƙaddara ki sawa kan ki salama" Sai daya fita a ɗakin na fashe da kuka. Kukan abu ɗaya na ke, abu ɗaya da na ke so, abu ɗaya da ya ke ƙoƙarin gagarata, SA'EED na ke so... Ban san ya aka yi na kai gado ba balle na san ko bacci na yi ko kuma suma na yi. Na dai buɗe ido na washe gari na ganni a kan gado na, Sanah ce ke zaune gefe na idon ta yai ja alamar ta sha kuka. Na yi yunƙurin tashi sai na ji hannuna saƙale da wani abu na bi hannun nawa da kallo sai a lokacin na ga ashe ruwa aka ɗaura min. Na haɗiyi yawu mai ɗaci tareda ƙoƙarin tuno yadda aka yi aka sa min ruwa a hannu ban sani ba. Ni bayan fitan Haruna a ɗaki jiya da dare ba zan iya tuna komai ba kuma. "Ya jikin na ki?" Sanah ta faɗa tana ƙoƙarin gyara min pillow saboda na samu na kishingiɗa. "Ƙarfe nawa?" Na faɗa da dashashshiyar muryata. Ta ɗaga ido ta kalli agogon ɗakin ta ce min ƙarfe shabiyu da rabi. Na rintse ido na takaicin abinda ya faru daren jiya, da Sa'eed ya zo da yanzu mun jima da isa garin Lafiya ƙila ma har mun samu gida achan. "Sa'eed, Sa'eed ya zo nema na?" Na tambayi Sanah ina mai fatan amsar da za ta ban ya zamo mai daɗin ji a wajena. "Ban sani ba Aaliyah, ko ya zo ba zai samu damar shigowa ba saboda Amma" Na rintse ido na ina hawaye. Dama ina so ya zo ne ba dan komai ba dan ya gaya min dalilin da ya sa bai zo ba jiya. Idan ya gaya min bai gane kwatance na bane ko kuma bai ga wasiƙar da na bar ma sa ba, zan ma sa uzuri. Amma idan ya ce bai zo bane saboda tsoron Baba da Amma na ba zan yafe ma sa ba... Da yamma Jiji ta shigo gaida ni na tambayeta ina Sa'eed sai ta ce min Sa'eed ya koma Minna jiya da yamma. Ba zan iya bayyana kalar baƙin cikin dana shiga ba da jin wannan batu, wani ɓangare na zuciyata na son ƙaryata maganar amma mafi rinjaye na zuciyata ya aminta da maganar Jiji. "Sa'eed ya koma Minna" da zancen danake kwana nake tashi kenan. Sa'eed ɗina ya saɓa alkawari, Sa'eed ɗina ya zama rago kuma matsoraci, Sa'eed ɗina ya zama butulu maciyin amana. Sa'eed ya yaudari soyayya ta, ya munafurci yardar da na ma sa. Kwana biyu na yi jinya a ɗaki na warware, ban san ya akayi na saki raina ba da maganar biki da kuma maganar komawar Sa'eed Minna. Na sani chan ƙasar raina akwai soyayyar Sa'eed wadda ta ke ta gaskiya babu algus aciki amma kuma a fili na ka sa nuna ƙin auren dole da za amin. Cikin 'yan kwanaki 'yan uwan Amma na Niger da 'yan uwan Baba da su ke lungu da saƙo na duniya su ka fara cika gidan. Duk wani abubuwan al'ada an min, ban nuna damuwa ko rashin son auren kamar yadda na ke yi a da ba na saki raina ina shiga ana hidima da ni kamar kowacce amarya da za a mata auren so. A zahiri ne ake ganin wannan Aaliyar amma a cikin zuciyata na sani Aaliyah ta Sa'eed ce... Biki da buduri aka yi na sati guda, naira da dala sun yi kuka a wannan hidima. Nigeria da duniya sun shaida an ɗaura auren *Aaliyah Badamasi Bulama* da *Ahmad Ibrahim Wamako* Kafin ranan da za a kaini an riga an wuce da tirelolin da su ke ɗauke da kayana. Kayayyaki da aka haɗo daga sassa na duniya baki ɗaya. Yadda ake gulman kayana kace akaina Baba ya fara aurar da ɗiyar sa mace. 'Yan ubanni da wasu cikin 'yan uwa sun nuna baƙin cikin su ƙarara gameda dukiya da Baba ya narka mini. Sanah ce kawai ba ta damu da komai ba ta ma fi nuna damuwa da yadda na kwantar da kai aka yi hidiman biki na bayan ta san irin tsananin son da na ke yiwa Sa'eed. Ranan da za akai ni ta ke cewa "Aaliyah ina zargin Amma da Hajia Badariyya, akwai abinda na tsinkayi suna faɗa amma ban tabbatar ba saboda ban gama ji ba" Da na tambayi me ta ji sai ta ke ce min wai ta ji Hajia Badariyya wacce ta ke babbar ƙawar Amma tana faɗawa Amma akan akwai inda za ta je a rufe bakina na amince da auren da za a min. Ni kam dariya kawai na yi dan koma mi Amma da Hajia Badariyya su ka kitsa aikin gama ya gama domin an riga an ɗaura aurena. Ba nasihar da Amma ta min lokacin da aka kaini sallama wajen ta illa addu'a da kuka da ta dinga yi. Ni kam na riga na gama nawa koke-koken tun kafin ranan, dan haka ko ɗigon hawaye bai sauko min ba. Daga wajen ta sai wajen Baba wanda ya min wata guntuwar nasihar munafurci, wai na ji tsoron Allah na yiwa mijina biyayya. Har shi zai min maganar tsoron Allah bayan shi bai ji tsoron Allah ya haɗa ni da wanda na ke so ba. Ya gama addu'an da zai yi aka ɗauke ni sai wajen motocin da ke jirana za su raka ni airport... A cikin Sokoto zamu zauna, a danƙarren gidan da aka ce Alhaji Wamako ya ginawa babban ɗan sa da ya ke matuƙar so, dan haka Sokoto mu ka nufa, sai dai saboda abinka da ma su arziƙi ba mota za mu bi ba jirgi za mu bi. Motar mu na fita daga gate ɗin gidan mu na juya na kalli gate ɗin sai ga hawaye yana zubo min. Daga yau na rabu da gidan mu kenan, sai dai ziyara, daga yau na zama mallakin Ahmad ba Sa'eed ba, daga yau na rasa 'yancina na matsayin budurwa tunda na zama matar aure. Na kifa kaina na fara rera kuka... *14-Black night* S A garden na samu Alhaji yana zaune kan ɗaya daga cikin kujerun da aka ajiye dan shaƙatawa, Kayan marmari iri-iri da aka yanka ƙanana aka tula a gaban sa yana ci. Na tsugunna ɗan nesa da shi na gaishe shi. Bai amsa ba sai da ya cakwkwalo apple da fork ya kai bakin sa ya tauna sannan ya haɗiye kafin ya ce da ni "Lafiya Sa'eed" Yanayin fiskar sa bai nuna alamun da zan gane ko akwai wata matsala ba. Na sunkuyar da kaina gameda sauke nannauyan ajiyar zuciya. Ban ɗago na kalleshi ba amma na san kayan marmarin da ke gaban sa ya cigaba da ci. Bishiyoyin da ke wajen su ka cigaba da kaɗa iska mai daɗin ni'ima, ga ƙanshin furanni da ya sake sanya iskar ta zama da daɗin shaƙa. Idan ka cire bishishoyi da furanni da su ke kaɗawa a wajen to sai kuma ƙaran fork da ke gugar faffaɗan tray ɗin da aka zuba kayan marmarin da Alhaji ke ci. Babu wani motsi da ke nuna akwai halittar mutum a wajen. Shirun yai yawa har na ke tunanin ko dai Alhaji ya manta da ni ne. Ba zan iya tuna tsawon tsugunnon jira da na yi a wajen ba amma na san gaskiya na jima sosai, hatta ƙafafuwana sai da su ka yi tsami. Ban ce ƙala ba na cigaba da jiran tsammani. Ina tsugunne a wajen zuciyata cike da tunani kala-kala sai na ji sallama a bayana. Na ɗago fiskata na juya gefena inda mutumin da yai sallama ke tsaye ƙiƙam yana jira Alhaji ya bashi umurni. Maimakon Alhaji ya ma sa magana sai ya dube ni ya ce "Sa'eed ka bi Ubaidu, zai kai ka wajen da za ka min wani aiki" "Shikenan Ranka shi daɗe" na faɗa tareda miƙewa na bi bayan wanda aka kira da Ubaidu. A shekaru na san zan girme shi sosai amma da ke shi ɗin yana da girma da faɗin jiki sai ya zamana ka iya ɗauka ya girmeni sosai. Idan da faɗa zai shiga tsakaninmu na tabbata ba ƙaramin lallasani Ubaidu zai yi ba saboda yanayin sa kaɗai ya nuna ba ƙaramin motsa jiki da aikin ƙarfi ya ke ba. Zubin Ubaidu zubin sojoji ne ko bodyguard. Na yiwa Ubaidu sallama amma bai amsa mini ba kai ko kallona bai yi ba. "Malam Ubaidu ai ko ba komai ka amsa sallama" Jin bai kulani ba na ja baki na nayi shiru muka cigaba da tafiya. Chan wajen gate mu ka nufa inda wata mota ke jiran mu. Ni da Ubaidu mu ka shiga bayan motan yayinda gidan gaban ke ɗauke da wasu Maza biyu, na musu sallama lokacin da na shiga motar wannan karan na ci sa'a wanda ke zaune a mazaunin dreba ya amsa sallamata. Ban ce komai ba haka su ka tada mota mu ka fita daga gidan. Tafiya mu ke sosai har mun fara ficewa daga cikin gari, ban iya tambayar su inda za mu ba dan yanayin su bai bani damar tambaya ba. Tunda Alhaji ya ce aiki zan je na ma sa, to na san duk rintsi dai a cikin garin Maiduguri ne aikin. Tafiyar awa ɗaya da rabi ta kaimu gidan gonan Alhaji. Na taɓa zuwa gidan gonan, lokacin da Aaliyah ta yi birthday ɗin cika shekara shabiyu a duniya. Muna fita daga cikin motan Ubaidu ya ce na bi shi. Ba mu su na bi shi zuciyata cike da wasi-wasi. Chan ɓangaren gidajen ma'aikata mu ka je inda muka tsaya a bakin ƙofar ɗaya daga cikin flats ɗin da aka gina dan ma'aikata. Ubaidu ya ciro key ya buɗe gidan ya shiga ciki bayan ya ce na biyo shi. Falo mu ka tarar wanda ya sha ƙura saboda daɗewa da aka yi ba'a amfani da shi, ba komai a falon sai tsofin kujeru wanda datti da ƙura su ka jima da samun gindin zama a jikin su. "A nan za ka zauna har sai Alhaji ya neme ka. Idan ka kwantar da kai ba abinda za mu maka har ka tafi amma idan ka yi taurin kai wallahi umurni aka bamu mu bugeka son ran mu" Maganganun da Ubaidu ya faɗa kenan yana huhhura hanci. Mamaki, tsoro, fargaba, dana sani duk su ka haɗu su ka mamaye min zuciyata. "B B Ban gane ba? Ubaidu miyasa Alhaji zai sa a kawo ni nan" Na ma sa tambayar ina da yaƙinin ko dai ya amsa min da baƙar magana ko kuma yai banza dani, ya bar ni da amsa tambayar da kai na. "Za a kawo maka abinci sau uku a rana. Zan maimaita abinda na faɗa da farko, idan ka yi taurin kai girman ka ba zai hana mu buge ka ba" Daga haka ya fice daga falon ya barni tsaye baki buɗe. Ina ji yana kulle ƙofar gidan da key amma ba abinda na iya yi. Tausayin kai na da kuma Aaliyah na fara yi, idan har Alhaji ya sa aka kulleni kenan ya san da maganar shirin mu da Aaliyah kenan. Lokaci guda na furta "Aaliyah" a fili, ba abinda na ke tunowa irin halin da Aaliyah za ta shiga idan ta jira ni da dare ba ta ganni ba. Ganin ba mafita sai Allah ya sa na shiga kiran sunan sa dan ya kawo min ɗauki... Da dare da Ubaidu ya kawo min abinci na roƙi Alfarma akan ko da dai ba zai bar ni na fita ba ina so ya nemomin takarda da biro na rubuta saƙo. Ubaidu ya ja tsaki zai fita na riƙe ƙafarsa ina cigaba da roƙon sa. Buri na koda zan rasa Aaliyah ina so ta sani ba da gangan na karya alƙawarin da na yi ba, ba da gangan na yi watsi da shirinmu ba. Ubaidu ya tureni tareda faɗin idan na sake taɓa shi ba zan ji da daɗi ba. Sai da ya fita daga falon hawayen ƙunci da baƙin ciki su ka fara zubo min. Tsorona kar Aaliyah ta ce za ta kashe kan ta saboda na ƙi bayyana a wannan dare, tsorona kar Aaliyah ta gudu ita ɗaya ta shiga duniya kamar yadda ta ke yawan iƙirari. Kuka sosai na ke yi ina ambaton Allah ya taimakeni kar Aaliyah ta aiwatar da ɗaya daga cikin abu biyu da na ke tunani. Ban iya bacci ba a wannan baƙin dare. Ko ban auri Aaliyah ba bana so ta faɗa halaka saboda ni, wannan shine babban buri na a wannan baƙin dare... Kwana ɗaya biyu uku huɗu... haka kwanakin su ka yi ta wucewa ba tareda na samu hanyar fita daga gidan ba, ba tareda na san halin da Aaliyah ta ke ciki ba. Idan ka cire ruwa ba abinda na ke amfani da shi cikin abincin da su ke kawo mini. Banda sallah, addu'a da kuka ba abinda na ke a ɗan ƙaramin gidan nan, wanda falo ne da ɗakuna biyu sai banɗaki da kitchen. Ranan farko da na biyu na yi yunkurin neman wajen guduwa amma ba hali, haka na haƙura na fawwalawa Allah komai... Ina irga kwanaki har ya kai saura kwana ɗaya a ɗaura auren Aaliyah. Ina ji ajikina tana raye kuma tana gida, koda Ubaidu da sauran samarin nan ba su sanar da ni komai ba, zuciyata ta sanar da ni Aaliyah na raye kuma tana gida. Daren ranan da na kwanta na yi mafarkin ina tafiya acikin jeji sai na hango wata bukka a tsakiyar jejin. Na yi sauri na nufi bukkar saboda gajiya da ishirwa da ke damuna, ina tunkaran bukkar na fara jiyo ihun Aaliyah kuka ta ke tana kururuwa haɗe da roƙo da magiya. Na sa gudu sosai dan na gaggauta isa bukkar na ceci masoyiyata sai kawai na yi tuntuɓe da wani ƙaton dutse na faɗi ƙasa. Ina jin muryan Aaliyah tana kiran suna na amma na ka sa tashi, na kasa motsawa. Na miƙa hannuna ɗaya ina furta sunan ta a hankali "Aaliyah" ... Da sunan Aaliyah na farfaɗo daga bacci jikina na ƙyarma saboda tsoro.Duk yadda aka yi Aaliyah na cikin tashin hankali, na tashi da sauri duk da jikina da yai rauni saboda yunwa. Na fara neman yadda zan yi na bar gidan nan ina tunanin idan ban fita yau ba ƙila ni da Aaliyah sai a lahira. Tun da daren da na tashi na ke neman hanyar fita har rana ta fito. Akwai window na glass a banɗaki amma a rufe ya ke kirif da kwaɗo gashi na duba gidan kaf babu abunda zan samu na fasa shi. Abinda na samu na yi ta bugawa plate ɗin roba ne da aka kawo min abincin dare amma bai fashe ba. Na ji haushi na dunƙule hannu na fara nausan windown ko zai fashe, zafin da na ke ji bai dameni ba face zafin rashin Aaliyah, na cigaba da bugun glass ɗin. Glass ko alamar fashewa bai yi ba sai ma nawa hannun daya fashe yana jini amma still ban dena buga hannuna ba. Na jima ina bugawa kafin naji kaman daga sama an jawo ni ana kai min duka ta ko'ina. Bugun da na ke yi Ubaidu ya jiyo lokacin da zai kawomin abincin safe hakan ya tunzurashi ya sa ya shigo banɗakin a guje ya hau jibgata. Ko da ina da isashshen ƙarfi da ƙyar zan iya ƙwatan kaina a wajen Ubaidu balle yanzu rabon da na ci abinci har na manta. Tun ina iya jiyo zagi da tsinuwa da ya ke yi har na dena jin komai na fara ganin duhu ƙarshe na sume a wajen.... *15-Black night 2* *A* Mutane takwas ne kawai za su rakani Sokoto, sauran duk daga airport su ka juya. Ni da Sanah ne mu ka zauna kusa, idan akwai wanda zan iya bugan ƙirji na ce ta fahimci halin da na ke ciki a wannan lokaci to Sanah ce. Akwai yayar mu Falmata sai ƙannen Baba Hajiya Aisha da Hajiya Hafsatu sai yayar Amma wato Hajiya Rahima. Sauran ba zan iya cewa suwaye ba ne dan ƙuncin da na ke ciki ya fi gaban na tsaya duba su waye za su rakani. Lokacin da mu ka isa tuni motocin gidan Alhaji Wamako su na tsaye su na jiran mu. Tun da na fito wanda su ka zo taran mu su ka sa guɗa su na shewa da tafi. Duk wani shirmen su baya gaba na lissafina yadda kowani rana za ta kasance tareda mutumin da banda sunan sa ba abinda na sani game da shi. Akwai wata Inna Ɓodejo wanda ban san daga ina ta haɗu da dangina ba a chan Maiduguri kafin mu taho lokacin da na ke gaban Amma da 'yan uwanta a falo tana min addu'a. Ƙus-ƙus ɗin da ake yi na cewa ban yi kuka ba irin wanda Amare ke yi idan za a kai su gidan miji ya sa wasu ke cewa ai saboda ba na son mijin ne. Tashin wannan bagidajiyar mata ta ce " yo ai wannan ba dalili ba ne. Mu da zamanin mu haka ake kai mu gidajen miji ba tareda ko fiskar mijin mun taɓa gani ba. Ko yana da kyau ko mummuna ne sai dai idan an kai ki ɗaki ki ganshi. Kuma a hakan mu ke zama lafiya-lafiya. Aaliyah ki godewa Allah kawai domin kina da sa'a" Ban san lokacin da na ɗago fiskata na kalli fuskar matar ba, wanda gani ɗaya na mata na san wannan kalen dangi ce. Cike da ɓacin rai na ce "wani sa'a kenan Baaba?" Yadda na yi maganar ya sa aka yi chaa akan ta ana faɗin Inna Boɗejo ba ki kyauta ba wai yarinya na jumurin barin gida kina sake tunzurata. Kuɗi kenan wanda ke maida yaro babba, maimakon su min faɗa sai su ka yiwa tsohuwar nan chaa har sai da na ɗan ji tausayinta. Wannan rikici ya sa aka tarkatani aka wuce dani sashen Baba... Ban sake hannun Sanah ba dan haka dole mota ɗaya mu ka shiga aka wuce da mu gidan da zan zauna, gidan aure na. Babban gida ne sai dai bai kai namu girma ba. Tsarin ginin dai zan ce ya fi namu saboda gidan anginashi aƙalla ba zai fi shekaru biyar da su ka wuce ba, ba kaman namu da ginin ya fi shekara talatin ba, duk da gidan mu irin gida ne sa ke tafiya da zamani amma akwai wasu chanje-chanje na yayi wanda tsarin ginin gidan Alhaji Wamako ke da shi amma namu ba shi da shi. A Lagos Alhaji Wamako ke yawan kasuwancin sa shiyasa ya fi zama a chan, idan ya zo Sokoto kuwa to a garin Wamako ya ke sauka a nan yai ginin sa a kusa da gidan gadon su. Sai dai ko wani dalilin ne ya sa yai wani ginin acikin garin Sokoto ya dawo nan da zama Allah shi ne masani. Ɓangaren Alhaji Wamako aka wuce da ni wanda tsakanin gidan da gidan da ya ginawa ɗan sa Ahmad ba ko katanga a tsakani, sai dai gate ɗin gidan biyu ne, na ɓangaren sa da kuma na ɓangaren gidan Ahmad. Sashen Hajiya Inna wacce ta ke Uwargida kuma mahaifiyar Ahmad aka wuce da ni dan na gaisheta. Tsugunnon dole na yi a gaban matar da kallon arziƙi ni ko 'yan uwana ba mu samu a wajen ta ba. A wajen ta ke gayawa 'yan uwana magana wai ko iya kayan da aka turo tun shekaranjiya ne kawai kayana ko kuma akwai wanda za su zo daga baya? Dan wai ita ta yi mamakin ƙarancin kayan. Hajiya Hafsatu wanda kowa ya shaideta cikin familyn mu da zafi da faɗa ta maidawa Hajiya Inna da martani ta ce "Har wata Agola ce za ta cewa 'yar ma su gida kaya sun yi kaɗan?. Wani matsiyaci, tsatson talaucin ne zai ce tireloli goma sun yi kaɗan?. Wa ya taɓa aika 'yar sa da wannan a duk faɗin garin nan?" Ta ja dogon tsaki ta ce "daɗin abin ma shekaru uku da su ka wuce aka aurar da 'yar gidan nan kuma muna da tarihin da mi aka kaita ɗakin ta" Ni kaina sai a wajen na san trailer goma aka totsa da kayana su ka taho Sokoto. Na sani ba komai ya sa Baba wannan almabazzaranci ba fa ce kawai ya nuna cewa Bulama da Wamako akwai Banbanci, na sani shi a wajen sa kaman ya siya min girma da daraja ne, amma a wajena bai burge ba sai ma haushin sa da na ji. Hajiya Inna ta sha jinin jikinta dan ta gamu da gamonta. Dama ta kawo maganar ne dan ta ƙasƙantar da ni a gaban 'yan uwanta da 'yan uwan Mijin ta, sai kuma ta samu Hajiya Hafsatu Bulama ta fi ƙarfin gaban raini. Bayan dama tun asali na ji ana cewa ni Aaliyah zaɓin Alhaji Wamako ne, ita Hajiya Inna akwai zaɓin da ta so ɗan ta Ahmad ya aura. Wannan rana shine zan iya cewa ya fara rura wutar ƙiyayya da Hajiya Inna ta ke min... Fiskoki ba fara'a haka aka fito daga sashen Hajiya Inna aka wuce da ni sashen matar Alhaji Wamako ta biyu wato Alaja Barakat Atinuke. Wannan mata babbar 'yar kasuwa ce a garin Lagos, Mijinta na fari Alaji Ishola AbdulYaqeen ne ya mutu ya bar mata tarin dukiya, kasancewa 'yar su ɗaya da shi ya sa 'yan uwan sa su ka hau kan dukiyar su ka zauna, abinda su ka bata bai fi kaso goma cikin ɗari na abinda ya kamata ace ita da 'yarta Misturah sun samu ba. Da wannan ta fara kasuwanci tana kula da 'yar ta kuma cikin ƙanƙanin shekaru Allah ya albarkaci kasuwancin ta. Kasuwanci ne ya haɗa Alhaji Ibrahim Wamako da Alaja Atinuke wanda a hankali su ka fahimci junan su. Riƙon addini da kuma riƙo da gaskiyarta ya ja hankalin Alhaji Wamako akanta har yai sha'awar aurenta musamman dan ya kula da 'yarta marainiya 'yar shekara shauku a lokacin. Auren kusan a sirrance aka ce yai saboda tsoron Uwargidan sa Asma'u wanda ake kira da Hajiya Inna. Sai daga baya ya faɗa ma ta. So biyu yana aure tana fitinar matan suna guduwa sai akan wata Jamilah 'yar Zamfara ta kasa taɓuka komai akan ta. Abunka da matan manya ko a lokacin anyita cece-kuce akan maganin Jamilah ne ya fi nata ƙarfi shiyasa ta kasa koran ta. Jamilah ta zauna har ta haihu biyu a gidan duka mata sai a na ukun da ta zo haihuwa da ita da yaron su ka rasu. A gida ta fara naƙuda, kafin a kawota asibiti jikinta ya bircike ƙarshe ɗan bai gama fitowa ba ma Jamilah ta koma ga mahaliccinta, yaro kuma dama bai fito da rai ba. Sha'ani na ma su kuɗi da yadda ake kai mu su gulman 'yan uwan su ma su kuɗi da ɗumi-lumin sa, haka har falon Amma aka zo ana gulmata ma ta wai Hajiya Inna ce ta kashe Jamilah. Amma na ba mai yadda da irin waɗannan abubuwan ba ne shiyasa ina kwance kan kujera ina karatu a falon na ji Amma na gayawa matar da ta kawo gulman cewa Jamilah lokacin ta ne yai ba abinda Hajiya Inna ta mata. Duk da alokacin ina da ƙarancin shekaru ban fahimci maganganun su sosai ba dan ba zan wuce shekara tara ba a lokacin, amma na fahimci yadda ake ta gulmammakin Hajiya Inna to ba makawa matar ba ta kirki ba ce. Bayan Jamilah ta rasu Hajiya Inna ta kame gida ita ɗaya sai kwatsam ta ji zancen auren Alhaji Wamako da bazawaran Bayarabiya a sama. Ta ɗaga hankalinta matuƙa sai dai har yau ɗin ba yadda ta iya suna tare. Ba gida ɗaya su ka zauna ba a chan Lagos ɗin dan duk zuwan mu Lagos gaisheda Alhaji Wamako idan mun je ni da Amma a gidan Alaja Atinuke mu ke sauka. Matar ba ruwan ta tana da son jama'a ga ta da yawan kyauta da sadaka, duk Jumma'a aka ce ta ke sawa ayi sadakan abinci safe rana da dare. Alaja Atinuke ta haifawa Alhaji Wamako 'yan biyu maza amma ɗayan ya rasu tun yana jariri daga nan kuma ba ta sake haihuwa ba. Yaran Alhaji Wamako duk mata ne su ka fi yawa. Hajiya Innar ma bayan Ahmad ba ta da wani ɗa namijin. Ance immediate brother ɗin Ahmad namiji ne amma shima bai yi tsawon rai ba dan bai fi shekara biyu ba ya rasu. Hajiya Inna ta yi ta haihuwan amma still mata ne shiyasa aka ce tana ji da Ahmad kamar ranta... Tarɓa mai kyau mu ka samu a wajen Alaja Atinuke wanda ta dinga mana barkwanci da gurɓacecciyar Hausarta wanda har yau bai saitu ba. Ta nuna farin cikin ta da wannan aure tareda damƙawa 'yan uwana kyauta. Ban san mi ta ba su ba amma ko da sun san dai sun fi ƙarfin wani kyauta da za ta ba su. Dalilin karamcin da ya sa ta bada kyautan ne ya sa su ka amshi kyautan su ka yaba. Lokacin da aka wuce da ni gidan mu ba ƙaramin gajiya na ke ji ba ga kaina da ke wani irin sara mini. Abin mamaki bayan sun gama surutu da nasihohin su na boge su ka wuce su ka barni ni ɗaya. Har Sanah da na roƙa ta tsaya ba su barta ba, ita kam ma da kuka aka fitar da ita daga ɗakina. Sai da su ka tafi gidan yai tsit sannan damuwa ta sauka min. Ina ma Sa'eed na ke aure, da wannan dare ya zama dare mai cike da tarihi a rayuwata. A wajen hidindimun biki da mu ke haɗuwa da Ahmad ya kan raɗa min a kunne akan wannan dare sai ya kashe min duk wani rashin kunya da na ke ji. Na fara girgiza kai ina ƙoƙarin daurewa kar na yi kuka. Ga dai daren da Ahmad Wamako ke faɗi ga kuma daren da na yi mafarki na ci buri da alwashin mallakawa Sa'eed gangan jikina domin zuciya da ruhi na sun jima da zama ta shi... Ana kiraye-kirayen sallar Isha na tashi na shiga banɗakin da ke ɗakin na ɗauro alwala na fito na gabatar da sallolin da ake bina tareda zama a sallayar ina cigaba da kai wa Allah kuka na. Na jima ina zaune ina addu'a kafin aka buɗe ƙofar ɗakin aka shigo. Kallo ɗaya na ma sa na kauda kai na na cigaba da abinda na ke yi. Ina ji ya zauna a bakin gado tareda cewa "ki gama duk noƙe-noƙen ki yau daren na kuka ne da cizon leɓe". Ban yi kamar na ji shi ba na cigaba da gayawa Allah damuwa ta. Bai fi minti biyar da shigowar sa ba mu ka fara jin ƙaran telephone daga wani ɗaki kusa da nawa ya tashi da sauri ya fita. Yana gama amsa kiran wanda ya shigo ta wayar tarho ya fita daga gidan, shiru-shiru zai dawo bai dawo ba dan haka na tashi na hau kan gado na kwanta, ido na biyu ina sallamawa kaina na rasa 'yan ci na har abada daga yau, hakanan na rasa masoyina na gaskiya har abada. Ina cikin saƙe-saƙe ya banko ƙofa ya shigo. Da kakkausar murya ya ce "saboda dangin ki mahaukata ne shine za su zo har gida su zagi Inna ta. Inna ta ku ke cewa Agola 'yar matsiyata?" Ɗazu da 'yan uwana su ka kawo ni ɗakina da ake maida zancen abinda Hajiya Inna ta yi shine Hajiya Hafsatu ke bamu tarihin Hajiya Inna. Mahaifiyarta ce ta auri Alhaji Saminu babban ɗa ga wazirin garin Wamako, da Asma'u ta je agolanci wanda kyautatawa na Alhaji Saminu ya sa ya riƙe Asma'u tamkar 'yar sa ba ya banbanta ta da 'yayan sa na cikin sa. Ko kafin ya rasu sai da ya ba ta kyautar gona da shanaye saboda ba ta da gadon sa. Asalin mahaifinta ance Maharbi ne wanda ya mutu a jeji aka dawo da gawar sa gida. Kyau da ƙuruciyar Fatima mahaifiyar Asma'u ya sa tana gama Idda manema su ka ma ta chaa ƙarshe ta auri Alhaji Saminu ta je a matar sa ta uku. Tasowa a gidan arziƙi ya sa Asma'u ko na ce Hajiya Inna ta ɗauki rigan girman kai, faɗin rai, jiji da kai duk ta yaɓa wa kanta. Ance ko lokacin tana budurwa yauƙinta ya fi na asalin 'yan gidan. Tsaki na ja na juyar da kai dan damuwar da na ke ciki ya fi ƙarfin in tsaya ja in ja akan wata uwar miji marar mutunci. "A ni ki ke wa tsaki?" Ya faɗa yana nufoni da sauri. Ban ce komai ba sai ma wata tsakin da na ƙara yi. Ai kuwa ya jawoni daga inda na ke kwance kan gado ya cillani ƙasa, ba ƙaramin buguwa na yi ba amma kafin in gama samun nitsuwa na ji saukan mari a fiskata bai tsaya anan ba ya cigaba da naushina ta ko'ina, tun ina daurewa har na fara kuka ina faɗin Allah ya isa. Sai da ya ga na yi laushi na dena magana, kukan ma na dena sai sheshsheƙa sannan ya cire kayan sa ya afka mini kaman wata akuya. Kukan da na dena ne na tsala lokacin da ya fara shigata da ƙarfi, bai dena ba sai da ya shiga ciki sosai da ƙarfin tsiya, yana faɗin "na gaya miki sai na rufe bakin rashin kunyar ki, duk wani shirmen da ki ka zo da shi daga gida sai na raba ki da shi"... A wannan dare na tsinewa Baba, Amma, Sanah, Jiji sannan Sa'eed. Kai kowa ma da ya shafi rayuwata sai da na tsine ma sa. Ban san ya akayi mutuwa ta manta da ni ba lokacin da Ahmad ya hau kai na har ya gama abinda zai yi ban mutu ba. Bayan ya samu nitsuwa ko ya gaji ne oho, ya kwanta a gefe na yaraf yana maida numfashi. *"Sa'eed why?"* Abinda na iya faɗa kenan da dasashshiyar muryar da ba na tsammanin za a iya jin ta, kafin ido na ya rufe... 17-married to a beast A Yau Sanah ta tafi bayan ta yi kwana uku tana jinya na. Ba abinda zan ce mata ita da Alaja face Allah ya saka mu su da alkhairi domin su ne suka taimaka min, ban ɓoye mu su dukan da Ahmad ya mini ba saboda ganin tabon dukan da su ka yi a jikina. Inna uwar mijina ba ta leƙoni ba balle na tsammanci gaisuwa daga gareta bayan na san duk abinda ke faruwa ana kai ma ta gulman sa. Mairo da ke ma ta hidima ma ta hanata zuwa wajena. Ahmad kam tun safiyar da Mairo ta zo ban sake sashi a ido na ba. Alaja ce tace min ta roƙeshi akan ya barta ta yi jinyata shiyasa baya zuwa wajena. Alhamdulillah cikin kwana uku na ɗan ji ƙarfin jikina dan ina shiga  banɗaki na yi komai da kaina hakanan sallar asuba ta yau ma a tsaye na yi ta saɓanin kwana uku da na ke yin sallah a zaune. Daga sashen Alaja ake kawo mana abinci ko yau kafin Sanah ta tafi daga wajenta aka kawo mana lafiyayyiyar breakfast. Ina zaune akan gado ina tuno hiran mu da Sanah jiya da dare. Itama ɗin da alamu irin nawa za a mata nan ba da jimawaba. Sadiq ɗan gidan Alhaji Abbori ta ke so, a Oxford su ka haɗu. Amma kuma matsalar shine ba wanda bai san gabar da ke tsakanin Alhaji Bulama da Alhaji Abbori ba. Ta ke gayamin a hidiman bikina ta ji ana maganar haɗata da Alhaji Umar Bukarti. Mutumin da aƙalla idan bai yi hamsin ba to saura ƙiris hakanan matanshi biyu kuma dukkan su ba jituwa su ke ba hakan ne ma ya sa ya warewa kowa gidan ta. Idan aka aura mata Alhaji Bukarti ina ga da ni da ita ba zan iya faɗin wanda aka fi cuta ba. Na sani Sanah ba za ta tada hankali ba kamar ni, ba za ma ta iya buɗan baki ta ce Sadiq Abbori ta ke so ba balle ta san ko Baba zai iya chanza ra'ayi ko ba zai chanza ba. Turo ƙofar da aka yi ya sa na ɗaga ido na kalli ƙofar dan na san idan Alaja ce ko masu aikinta to da sallama za su shigo bayan sun nemi izinin shigowa. Ƙallo ɗaya na ma sa na kauda kai na, ina ƙara jin tsanarsa a zuciyata. "Haka aka miki tarbiya a gidan ku mijin ki ya shigo ki kauda kan ki gefe ba sannu da zuwa bare mi ka ke buƙata?" Ya faɗa yana huci. Ƙala ban ce ma sa ba dan idan na ce zan yi magana to ba lallai na faɗi maganar da za ta ma sa daɗi ba. "Ki shirya Alhaji na neman mu" ya faɗa yana mai ƙaremin kallo gameda lashe bakin sa. Har ya fita ko kallon sa ban yi ba balle na ma sa magana. Na dai tashi na nemi babban mayafi na saka na fito wanda tun kawoni gidan wannan ne karon farko dana fito daga ɗaki. Ko Sanah da za ta tafi hanani rakata ta yi wai ban gama warkewa ba. A falon da ke ƙasa na zauna ina jiran sa har kusan minti shabiyar kafin ya sauko. "Wato ba za ki gaisheni ba ko?" Na dunƙule hannuna biyu ina jin wani masifa na cina amma na daure na ce "Sannu" Ya ƙyalƙyale da wata shegiyar dariya ya ce "bayan na roƙi gaisuwan ma Sannu kawai zan samu?. Anyway bari mu gama da Alhaji tukunna"... Yana gaba ina bayan sa har mu ka je sashen Alhajin wanda mu ka sameshi a falo yana shan lemon kwalba ta cocacola. Na durƙusa har ƙasa na gaidashi duk da kuwa durƙuson da na yi ya sa na fama jinyar da na ke yi. Alhaji ya amsa gaisuwata yana faɗin na tashi na zauna. A kujerar da Ahmad ya zauna na zauna chan nesa da shi. Alhaji ya min ya jiki tareda faɗin Alaja ta gaya ma sa na yi zazzaɓi, na ce ma sa da sauƙi. Ahmad ya kwashe da dariya  yana faɗin "Alhaji ba a dai gaya ma ka gaskiya ba, ka ƙara bincike" Takaici ya kamani, shi wani irin daƙiƙi ne da ko kunya ba shi da shi. Alhaji ya kauda zancen da cewa "Allah ya ƙara miki lafiya 'yata" Ƙaramar nasiha ya mana sannan ya mana addu'ar samun zaman lafiya. Tareda shaida mana gobe zai yi tafiya zai je London wani kasuwanci kuma zai iya kaiwa wata ɗaya zuwa sati shida, na ma sa addu'ar sa'a tareda tsari. Yayinda Ahmad ke maganar kuɗin da Alhajin ya ma sa alƙawarin zai bashi. A take ya ciro check ya rubuta ma sa kuɗi ya miƙa ma sa, Ahmad ya karɓa ba ko godiya. Bayan mun fito ya ce mu je na gaida Inna na ce ma sa na gaji ƙafata ciwo ta ke, duk da gaskiyata na faɗa amma kuma ban son haɗuwa da Innar ne ya sa na faɗi hakan. Ya watsa min kallon banza ya ce "ko ki wuce mu je ko wallahi na miki rashin mutuncin da ya fi na ranan" Na yi ƙaramar tsaki a zuciyata na bi bayan sa. A hakimce mu ka sameta a falo tana cin gasashshen kaza. Yadda ta ke ci ka ce naman guduwa zai yi, gaskiya kwaɗayi na ga matsiyaci marar godiyan Allah. Duk da rigan arziƙi da ke jikin Inna har yanzu halayenta na matsiyata ne. Ban yi gigin tsugunnawa ba, a kujera na zauna tareda cewa Hajiya Barka da rana. "Ina zaune a kujera kema kina zaune" ta faɗa da tsawa. Na juya gefe na ina tunanin ko da wani ta ke. "Ba ki ji mi tace bane?" Ahmad ya faɗa yana kallona. "Au da ni ta ke?" "Bana son iskanci Aaliyah, ki shiga hankalinki" "Barta Ahmad, ta gama iskancin na ta na yau ne kawai" ta kalleni ta ce na tashi na fita. Ni kam bajau ɗina domin za ni ne ta tadda mu je, dan haka da sauri na tashi na bar falon na wuce sashen Alaja inda na samu tana ta kan shiri ita da Safiya ƙanwar Ahmad. Safiya 'yar marigayiya Jamilah ce, uƙubar da su ke sha a wajen Inna ya sa lokacin da Alhaji ya auri Alaja su ka gudu su ka koma wajenta, kuma ta riƙe su hannu bibbiyu. Ita ne ma ta aurar da Fadila yayar Safiyar shekaru huɗu da su ka wuce. Ita da mijinta su na chan ƙasar Malaysia. Ni na ma manta yau da safe Alaja ta ce min gobe za su koma Lagos dan dama bikin Ahmad ne ya sa ta zo Sokoto. Ba ta zama a Sokoto sai dai sallah ko biki ko wani uzuri. Ita da ɗanta da Safiya duk a chan su ke sai dai Alhaji ya je ya gan su, Inna kam tunda ta dawo Sokoto ko sau ɗaya ba ta koma chan ba. Na yi zamana a wajen su dan ba na son komawa gidan mu na haɗu da Ahmad.  Har dare ina wajen su, a nan ma na ci abinci, haka nan na yi amfani da tarho ɗin Alaja na kira layin gidan mu dan na ji ko Sanah ta sauka lafiya. Ta ce min ta kira tarho ɗin gidana ba a ɗauka ba na ce mata ina wajen Alaja ne. Haka ta labarta min cewa ta samu gida lafiya, ta haɗamin da cewa Hajiya Hafsatu da ta dawo ta samu Baba ta ma sa maganar abinda ya faru a gidana amma Baba ya banzatar da zancen tareda cewa wai gutsuri tsomin mata ne kawai amma Ahmad ba zai faɗi maganganun da ta yi iƙirarin Ahmad ɗin ya faɗa ba. Sosai Hajiya ta rinƙa faɗa ƙarshe ma ta ce inta sake taka gidan Aaliyah da Ahmad Allah ya tsine ma ta. Na yi dariya na ce lallai anyi drama kam dan faɗan Baba da ƙanwar sa da ke bi ma sa ba ƙaramin kallo ake sha ba. Haka mu ka yi hira sosai tareda ba ta shawaran ta faɗawa Hajiyarta maganar Sadiq ta ce min tsoron Hajiya ta ke yi na ce ma ta Allah ya shiryeta ta dinga dariya... Ban bar sashen Alaja ba sai ƙarfe tara da rabi na dare nan ma sai da ta min magana akan na koma gidana dare ya yi kafin na tafi. Ina zuwa na samu Ahmad a falo yana kallo ban ma sa magana ba na wuceshi zan haura sama ya ce "zo nan Aaliyah" Ba musu na dawo na tsaya ɗan nesa da shi. "Da izinin wa ki ka shiga sashen Alaja?" "Gaisheta na je yi kamar yadda na je gaida mahaifiyar ka" "You dont talk to me like that Aaliyah!" Ya faɗa da ƙarfi. Na haɗiye miyau ina jiran na ji saukan mari ko duka sai ya ce min "kin ci albarkacin Alhaji na nan, mu je ki bani hakkina tunda yanzu kin warke har kinada lafiyar zuwa gulma" Mamaki ya bani, saboda rashin imani tsantsa da ya ke son nuna min, shi idan aka ce ya kusanceni sai ya yi bayan ya san irin aika-aikan da ya min kwana huɗu da su ka wuce. A fusace na fara maida ma sa magana "Kai wani irin mutum ne dan Allah. Dan ina matarka ba shi zai sa ka min abinda ranka ya ke so ba, you raped me Ahmad. Maimakon ka barni na yi jinyar kaina hankali kwance shine ka ke maganar haƙƙi, nima inada hakki akan ka, dan haka banida lafiya" na faɗa ina hayewa sama da sauri. Ban gama rufe ƙofar ba ya banko ƙofar sai da na tsorata ya fara dariya yana faɗin "you like it rough huh?" Na fara ja da baya ina huci domin na tsorata da yadda ya ke "kin san miyasa na amince na aure ki bayan Hajiya ba ta so? saboda taurin kan ki, you're just perfect, ba za ki bani da kan ki ba sai dai na ƙwata ta ƙarfi, to ai shikenan cause I love it Wild"... Ban san beast aka aura min ba sai wannan dare, ashe na ranan soman taɓi ne ga wanda ya min yau da wanda yai ta yi a gaba. Ɗaure ni yai a kan gado, hannu da ƙafa. Bayan munyi kokawa da shi ya ci galaba akaina, to ina zan iya da ƙarfin sa. Ban fara kuka ba sai da ya ciro belt ɗin sa ya fara zabga min a cinyoyina, tsirara na ke akan gadon nan haka saukar belt ɗin nan ke sauka ajikina ba kakkautawa. Ina kuka yana dariya, shi ƙuncin da na ke ciki shi ne ke sa shi nishaɗi. Ba zan ce ban san akwai mutane irin haka ba amma ko da ya ke acikin litattafai na karanta gameda mutane da su ke da matsalar BDSM. Ni ban san akwai sadomasochist mutane a ƙasar Hausa ba sai akan Ahmad. Sai na tuna kuma Ahmad rainon turawa ne, primary school kawai aka ce yai a Nigeria gaba ɗaya karatunsa a turai yai. Idan ba sharrin bature ba ta ya ganin mutum cikin ƙunci da wahala zai saka farinciki har ya tada maka sha'awa ya kuma gamsar ma ka da sha'awarka. Yadda ya ke sucking breast ɗina gameda cizon su ka rantse zai ɓimcine min nipple ne. Ya ce he likes it wild amma shine wild, ɗin domin Ahmad kam na sadaƙar ba mutum bane wild Animal ne sanye da rigan mutane. Scracthes ɗin da ya min a kafaɗuna da cikina sai da su ka yi jini. Na jima da dena kuka ina tunanin ma suma na yi. Lokacin da na buɗe ido dai ya kunce ni, ya rungumeni yana bubbuga bayana a hankali yana faɗin wasu maganganu marasa kan gado. "You're too much Aaliyah, ciki da wajen ki duk daɗine. Dama haka matan Borno su ke? Ko ke ce daban?" Yai ta sunbatun sa wanda na rasa gane na dukan da ya min ne ko na rough sex ɗin... Da safe da ƙyar na tashi na shiga banɗaki na yi alwala bayan na yi wanka da ruwa zalla, tabon da ke jikina idan ya ji sabulu zafi zai sa min. A daddafe na sallaci sallar asuba ina yi ina hawaye saboda ni kam na san tawa ta ƙare domin inhar a kwana biyar da kawoni gidan Ahmad shine zai shiga ƙunci haka to na san lallai kafin sati biyar Ahmad ya kashe ni. Ban iya fita na yiwa su Alaja sallama ba kaman yadda na ce mu su zan je sai dai sun shigo sun min sallama har ɗaki. Ganina a kwance kan gado ya sa su ka ɗauka ko jikin ne, Alaja ta ce duk lokacin da banida lafiya ko na ke da matsala na kira Doctor Linda za ta zo har gida ta duba ni, na amsa ma ta da to... Kwana biyu kenan da tafiyar su Alaja da Alhaji ganin ba mai kawo min abinci ya sa na nemi kitchen na shiga na dafawa kaina abinci dan kar yunwa ya kasheni. Ahmad ma ban ji ɗuriyan sa ba tun safiyar ranan ɗin. Yau ina kitchen ina dafa jollof ɗin shinkafa sai na ji ana ƙwala min kira, muryan Inna ce dan haka na fito a hankali saboda har yanzu ba isashshen lafiya gareni ba. "Uban mi ki ke yi ba ki je kin gaida ni ba jiya da na dawo daga tafiya?" "Ni ba wanda ya ce min kin yi tafiya" na amsa a taƙaice. "Allah sarki ashe iyayen ki ba sa son ki haka. Ashe ba ki da wani gata. Na ji ance an dasa ki da Ɗana ne ko kasheki zai yi ba za ki iya rabuwa da shi ba" Ban gane maganarta ba dan haka na juya zan koma kitchen. Ta jawoni ta kifa min mari tana faɗa wai tana magana ina tafiya. Mi zan yi ban da ido ta gama faɗanta ta fita... Cikin sati uku salon zaman namu ya sauya. Inna ta maidani tamkar baiwarta, tun safe har dare ni ke ma ta hidima, ta hana ma su aikinta aiki wai tana da surukuwa mi za ta yi da 'yan aiki. A gida idan na yi wani aiki to ra'ayin kaina ne ba sani a ka yi ba. Girki ma dalilin Jiji ya sa na koya amma sai gashi ina yiwa uwar miji bautan da ko a mafarki ba zan yi a gidan mu ba. Mijina kam sai dai na ce Allah ya saka min da alkhairi domin sai ma abin da ya ƙaru. Tun da na ga Ahmad na shan giya na san duk abin da ya min ba komai ba ne tunda mashayi ne. Sex kuwa ni ban san daɗin sa ba. Idan bai dakeni ba kafin yai ko kuma yanayi yana zuba min belt ko bulala to shi baya samun gamsuwa. Randa 'yan mutuncin sa kenan kuma ba duka amma da zafi-zafi zai dinga yin komai maimakon na ji daɗi sai dai zafi. Kamar yadda Sanah ta faɗa kamar yadda Inna ta faɗa, iyayena sun min magani. Duk baƙincikin da na ke ji ban taɓa tunanin na gudu ko na gayawa iyayena ba banjin ma a raina zan iya rabuwa da Ahmad Wamako ko da kuwa zan ƙarasa rayuwata da shi cikin ƙunci... 18- A good father inlaw A Ina duba hannuna da su ka yi kanta saboda aiki telephone ɗin ɗaki ya fara ƙara na tashi da ƙyar na je na ɗauka. "Hello" na faɗa a sanyaye. Muryan mahaifiyata na ji, rabo na da ita tun ranan da za a kawo ni gidan Ahmad. Sau tari na kan yi tunanin na kira ta mu gaisa amma kuma idan na tuna yadda ta goyi baya wajen rabani da farinciki na sai na fasa. A duk gidan mu da Sanah kawai mu ke waya sai Baba da ya kirani sau ɗaya yana ja min kunne akan kada na kuskura na bari rigimar Hajia Hafsatu ya shafi tsakanina da mijina, na yiwa mijina biyayya. Addini da al'ada wani lokaci su kan sa akai mace ga halaka. Bayan anmin auren dole ba'a barni haka ba aka haɗa da yimin magani sannan kuma ake tsammani na yiwa mijina biyayya ta ko wani hali. Shin wani biyayya zan yi wa ɗan giya? Wani biyayya zan yiwa mutumin da ina da yaƙinin ba ya sallah sai ya ga dama? Shin wani biyayya zan yi wa mijin da ko ɗaya daga cikin haƙƙoƙin da Allah ya ɗaura ma sa nawa bai sauke ba. "Aure Ibada ne" wannan kalmar ana ma sa mummunan fassara a mafi yawancin lokuta, domin ana fassara shi bisa son zuciya. "Ki na lafiya? Ya gidan na ku?" Tambayoyin da Amma ta min kenan bayan mun gaisa na tambayi lafiyar ƙannena. Abin mamaki sai na fashe da dariya, dariya sosai kamar wata zautacciya. Tun Amma na jiran in ƙare dariyar na amsa tambayoyinta, har ta haƙora ta katse kiran bayan ta yi ta tambayan dalilin dariyana amma ban gaya ma ta ba. To mi zan ce mata? So ta ke na ce ma ta ina lafiya ko so ta ke na ce ma ta ba ni da lafiya. Kowanne na faɗa ciki ba abin da za ta iya yi akai illa ta ce Allah ya kyauta. Ban jima da zama ba Ahmad ya shigo ɗakin. Kallo ɗaya na ma sa na tabbatar a buge ya ke. Wani lokaci ina mamakin wani abu, wai shin kowane gidan ma su arziƙi ne ake samun fitsararren ɗa, ɓata gari kamar Ahmad? Aliyun gidan mu yana shaye-shaye ga satan kuɗin Baba da ya ke lokaci zuwa lokaci. Sosai ya ke bawa Baba ciwon kai kuma ikon Allah duk yaran gidan mu ya fi kowa kama da Baba, yadda ka san photocopy na shi haka ya ke. Bayan na gidan mu na san ɗaiɗaikun gidaje da na san su na da matsaloli irin haka sai dai wannan Ahmad ɗin kam na shi ya kai ƙalu Innalillahi. "Aaliyah yunwa na ke ji" ya faɗa yana jawo ni jikinsa. Na san mi ya ke buƙata amma na dake na ce " akwai abinci a dining room" Ya juyo da fiskata yana busa min iskar bakinsa mai haɗe da warin giya yana faɗin "kin san abincina Aaliyah. You know how i like it" Ƙoƙarin tuɓe min riga ya ke na fashe da kuka sosai. Wallahi a lokacin da Ahmad ya kusanceni kamar yadda ya saba inada tabbacin mutuwa zan yi. Ba wani ƙarfi ajikina, daga ɓangaren Inna na ke na gama wahala sosai, abincin safe na jera a dining zanci Inna ta aiko aka kirani tunda na fita kuwa sai bayan la'asar na dawo. Yunwan da na ke ji ta gama galabaitar da ni, wanka na yi na yi sallah shine ma kiran Amma ya shigo. Ban san ko giyan ce ta sanar da shi ya ƙyaleni ba amma sai na ga ya sake ni ya juya ya fita daga ɗakin. Sai da na tabbatar ba dawowa zai yi ba sannan na dena kuka na goge hawaye na je na kwanta akan gado. Cikina daya cigaba da murɗawa ya sa dole na fito dan na nemi abinda zan ci ko da kuwa tea ne. A stairs na samu Ahmad yana sharan bacci cikin aman da yai, na girgiza kai na wuce shi. Daren ranan kam Ahmad bai barni ba, har na jima da barci kusan ƙarfe shabiyu na ji gurnanin sa a gefena. Yanzu kam dan dole na fara sabawa da yanayin sa, bai dakeni ba amma na azabtu a wajen sa... Sati na biyar kenan a gidan, gaba ɗaya na fige na lalace, idan ka cire fiskata ba abin da ke da kyan gani ajikina yanzu. Wannan jiki da na yi lokacin da na je makaranta da wannan kyau da na ƙara kafin bikina da na sha gyara duk babu shi yanzu. Ina goge wa Hajiya dressing mirror ɗin ta cikin rashin sa'a na ture wani kwalban turarenta ya faɗi ƙasa ya fashe. Ba ta ɗakin dan haka na tsugunna da sauri ina ƙoƙarin tattarewa kafin ta shigo, da na duba da kyau sai na ga ina da irin turaren a ɗakina kuma ni ba amfani na ke da su ba. To awa zan yiwa kwalliyar?. Ina cikin tattarewa sai ga ta ta shigo, jin ƙaran buɗe ƙofa da na yi sai tsoro ya kamani har na yanke yatsata. "Wato da na ɗan kauce daga ɗaki ta'adin da ki ke min kenan ko? Kin san nawa turaren nan?" "Inna ba da gangan na fasa miki ba, amma akwai irin shi acikin kayana zan kawo miki" Inna ta fara tafa hannu tana salati wai ina ma ta gori. Ban san mi zan ce ma ta ba na kauda kai na daga kanta na cigaba da tattara kwalban. Lokacin da na gama ta riga ta fita a ɗakin, na fito domin na je na zubar na nemi tsintsiya na ƙara sharewa sosai sai na ga Inna da Ahmad tsaye a falo su na magana. Na kauda kai zan wuce Ahmad ya kirani, na ce ina zuwa. Niyyata na je na zubar da fasashshun kwalaben kafin na dawo amma sai ya daka min tsawa akan na zo yanzun. Na ƙarisa wajen su ina tunanin ko mi za su min. "Mi ki ka cewa Hajiya?" Ya tambaya da ƙarfi. "Mi zan ce ma ta, na fasa ma ta turare na ce zan kawo ma ta wani, mi na faɗa yai zafi anan?" "Ka ga matarka ko? Ka ji dai da kunnenka irin rashin kunyar da ta ke min ?" Inna ta faɗa tana nunani da yatsa. "Ki tsugunna ki bata haƙuri" ya faɗa yana kallon cikin ido na. Kallon sa na ke ina kuma kallon Innan lokaci guda. "Ba na son haƙurinta, hukuntata za ka yi ta yadda gaba ko ƙwayar ido na ba za ta so kallo ba" Kamar almara haka na ji kalmomin Inna da ta ke cewa wai Ahmad ya ɗau kwalba ya min zane a fiska. Shi kan sa Ahmad ɗin sai da ya kalli Inna da mamaki. "Ba ka ji mi na ce bane?" Ta daka ma sa tsawa "Hajiya amma..." "Ka san Allah idan ba ka yi ba sai na danneta a gaban ka na yayyaga mata fiska da kwalban nan. Shegen fiskar da ke sata girman kan idan na ɓata shi sai mu ga abinda za ta yi" Na fara ja da baya lokacin da na ga Ahmad na ƙoƙarin matsoni. "Please dont do this to me. Please" sai da na kai bango na tsaya har lokacin hannuna na riƙe da kwalban. Ganin da gaske idan na tsaya zai aikata abinda uwarsa ta sashi ya sa na watsa ma sa kwalban ajiki na fita da gudu sai dai ban kai ko'ina ba Inna ta riƙoni. Na fara kici-kici ɗin fincike kaina daga riƙonta Ahmad ya ƙariso wajen, sai da ya wanka min mari kafin na nitsu na tsaya domin na san ƙoƙarin gudu ma ɓatawa kai na lokaci ne. "Miƙo min kwalban Ahmad, ni da kaina zan yayyaga ma ta fiskar" Inna ta ƙarɓi kwalba tana shirin yanka min fiska shi kuma Ahmad ya riƙe hannayena duka biyu. "Asma'u!" Muryan Alhaji ya tsayar da ita daga mummunan aniyarta. "Innalillahi, Asma'u ashe bakida Imani?" Yana zuwa ya wankawa Ahmad mari yana faɗin "wallahi na yi asaran Haihuwar ka Ahmad, har da kai za a ci mutuncin matarka saboda ba ka da hankali" ni dai na ji ƙaran mari uku dan ban buɗe idona ba tun lokacin da Inna ta ƙarɓi kwalban hannun Ahmad na rufe ido na domin na sadaƙar. "Allah ya shiryaku, Asma'u wallahi ki ji tsoron Allah" haka Alhaji yai ta faɗa, maimakon ta yi shiru ko ta ba da haƙuri sai ta ce. "Nan ka ce ka yiwa Ahmad Mata na ce ma ka sai dai Baiwa dan na riga na ma sa amma ka bi son ran ka, ban ga abinda zai sa ka ɗaga jijiyar wuya yanzu ba." Alhaji ya shiga ƙwalawa Mairo kira ba tareda ya amsawa Inna ba. Da ta zo ya ce ta kaini gida ta gyarani. Mairo ta kama hannuna mu ka fita a falon... Da dare Alhaji ya zo gidan mu, ina ɗaki Mairo ta shigo ta ce na fito Alhaji na ƙasa. Na sa mayafi na sauka. Ina kallon tsantsan damuwa a ransa. "Tun kina yarinya ki ke burgeni shiyasa na kwaɗaitawa ɗana ke, a lokacin na bayyanawa Mahaifinki burina kuma ya amince min. Na yi son zuciya Aaliyah domin na san ɗana ya lalace a ƙasar waje, ina da sanin Ahmad na shaye-shaye kuma na yi iya ƙoƙarina a kan sa. Da farko na so janye batuna lokacin da kika dawo daga makaranta amma mahaifinki ya nuna min ba matsala domin kun riga kun saisaita kan ku da Ahmad ɗin. Wallahil Azim ba zan bari a zalince ki ba, idan har ba kya son zama da Ahmad zan sa ya sawwaƙe mi ki yanzun nan. Ban taɓa tsanar abinda Amma ta sa aka min ba sai wannan lokaci. Ba na son Ahmad kuma ba na son auren shi amma ba zan iya rabuwa da shi ba haka na ke ji a raina. Wannan dama da na samu haka ya wuce ni domin cewa na yi zan zauna da Ahmad ina da yaƙinin zai gyaru watarana. Alhaji ya min godiya tareda addu'a ya kuma sanar da ni ya ɗau mataki akan Inna ba za ta sake min mugunta ba. Da ya tambayeni ko ina da abin da na ke buƙata sai na ma sa maganar Sanah. Na roƙeshi akan yai wa Baba magana ko zai amince Sanah ta auri Sadiq Abbori. Ya min alƙawarin zai yi iyaka ƙoƙarin sa ya ga ya sasanta Baba da Alhaji Abbori ko za su amince su zama sirikai.... Baban miji na yai min gata, domin kuwa washe gari aka kawo min 'yan aiki guda biyu Salamatu da Uwale, sannan Alhaji ya ce idan ya wuce gaisuwa bai yadda na yiwa Inna wani bauta ba. Ahmad kam ina ga faɗan da aka ma sa ya sa ya ji haushi ya bar gidan, domin bai dawo ba sai da yai sati biyu cur. Waɗannan sati biyun ba ƙaramin murmurewa na yi ba, ba inda na ke fita daga ɗaki sai falo. Ma su aikina kuma su na da kirki, mu kan zauna mu yi taɗi sosai da su, tun suna ɗari-ɗari da ni har su ka saki jiki da ni. Mutane rahama ne, ka zauna da wani ku yi hira shima yana ƙarawa mutum annashuwa da farinciki. Hiran da ban taɓa samu a wajen mijina ba kenan. Inna ma ganin Alhaji na gari ya sa ta fita harkata, ba ta zo wajena ba bata kuma aiko an kirani ba... Tun da na ji muryan sa a falo raina ya jagule saboda na san baccin daɗi da na ke yi kwana biyu sun wuce ni kenan. Na ƙi fitowa ƙasa kamar yadda na saba, ina zaune a kan gado ya shigo ɗakin. "Sannu da zuwa" na faɗa a hankali dan na san idan ban faɗa ba ma sai ya tambaya. Ya jawoni jikin sa ya ce " kin yi missing ɗina kuwa? Ni kan na yi missing ɗin ki sosai, matan Lagos duk fanko ne. Ba ta inda su ka kamo ƙafarki, idan zan yi tafiya dole na dinga tafiya da ke" Banji haushin neman matansa ba kamar yadda na ji haushin yadda ya maida ni sex object ɗin sa, wato ni ban da wani amfani sai wajen sex. Na daure na ce " ni ma idan an kwana biyu zan koma fanko kamar su" "Never, never" ya faɗa ya na ɗakar bayana daga nan kuma ya shiga sarrafani kamar yadda ya saba... Na samu sauƙin wahalar aiki amma ban samu na kwanciyar aure ba domin duk daɗin da Ahmad ke magana akai shi kaɗai ya ke jin kayansa ni kan wahala kawai na sani. Ranan da safe Alhaji ya kirani dana je ya min maganar aiki na ce ma sa ai ban ma gama bautar ƙasa na ba, ya nuna min ba matsala zai yi wani abu a kai. Ashema tuntuni Baba ya sa an maidani Sokoto amma kuma ba na zuwa ko'ina. Sati ɗaya da maganar mu da Alhaji na fara fita aiki a wani gidan jarida. Maganar sasanta Baba da Alhaji Abbori kam bai yiwuba dan maganar ne ma ya sa Baba ya speeding maganar auren Alhaji Bukarti da Sanah. Duk inda Alhaji Wamako ya fito waɗannan maƙiya sun ƙi sauke girman kai su rungumi soyayyar 'ya'yan su. Wata uku aka sanya bikin Sanah wanda da ƙyar Baba ya sa shi da nisa domin shi ya so ayi bikin nan kusa a wuce wajen kawai. Sai dai Hajiya Yana ta nuna a bari sai wata uku saboda bikin zai yi kusa da na wasu cousins ɗin mu biyu da za ayi. Yadda bikina yai fice yai suna a family ita ma haka ta ke son bikin 'yarta yai, dan haka aka sa shi wata uku... Ranan wata Jumma'a Alhaji yai baƙuwa a office ɗin sa. Wata tsohuwar 'yar aikin marigayiya matar sa Jamilah ce. Magaret ta zo gaban Alhaji tana kuka tana neman yafiyarsa bisa mummunan laifin da ta yi ma sa, da ya nemi jin laifin sai ta ce ma sa Inna ce ta ba ta magani ta sawa Jamilah a abinci, da farko ta ƙi amma Innar ta yi barazanar kasheta idan har ba ta aikata abin da ta sa ta ba. Magaret ta ce abincin nan da ta ci ne ya sa ta kama ciwon ciki daga nan sai naƙuda gadan-gadan wanda ƙarshe ta mutu wajen haihuwa. Alhaji ya shiga tashin hankali yana kuka yana neman tsari daga muguwar matar sa Hajiya Inna. Cikin tashin hankali ya baro office ya taho gida, dreban sa ya shigo da shi nima na shigo da motata saboda dawowata kenan daga wajen aiki. Na ce barin gaisa da shi kafin na wuce gidana sai kuma na ga Alhaji ya fito daga mota fuuu hankalin sa a tashe. Na bi bayan sa da sauri ina tunanin ko lafiya. A falo ya samu Inna tana yiwa ma su aikinta faɗa, tana ganin yanayinsa ta sallamesu tana tambayar sa ko lafiya. "Asma'u akan me? Me ta miki kika sa a kasheta?" Inna ta zaro ido ta ce "wa kenan?" Tari ya fara sannan ya ce "JJJJamilah" Ta ja tsaki ta ce " na ɗauka ma Aaliyah ka ke magana dan ina gab da kasheta." "Asma..." Alhaji ya riƙe ƙirji yana tarin jini. "Jamilah tsohuwar gawa ce ai, kuma saboda kai na kasheta. Ta haifi ɗaya biyu duk bai isheta ba sai ta ƙara, gara ta je ta haifa a lahira idan ana haihuwan a can" "Inna Alhaji" na faɗa ina yin kan Alhajin da gudu wanda ya faɗi yijib a wajen... Wasu matan duniya da dukiya sun rufe mu su ido kuma za su iya yin komai saboda su gaje gidan mijin su. A hannuna Alhaji ya ƙarasa cikawa wanda hakan ya gigitani. Yadda na shiga tashin hankali ita da mijinta ya rasu ba ta wani nuna damuwarta akai ba... Lokacin da mu ka je asibiti aka tabbatar mana ya riga ya cika, dama Alhaji yana da hawan jini kuma shock ne ya kasheshi ni kuma na ce Inna ce ta kashe shi. Mutuwar Alhaji Ibrahim Wamako ya zo da sauye-sauye dayawa wasu na daɗi wasu ba daɗi. A rana ta biyu da rasuwan Alaja da sauran 'ya'yansa su ka zo. Na yi mamaki da na ga Ahmad ya yi kuka lokacin da ya zo ya samemu a asibiti na ɗauka shima ɗin kamar Inna zai yi farin ciki ne amma sai na ga saɓanin haka. Baba ma wannan mutuwar ce ta sashi ya risina har ta kai ya gaisa da Alhaji Abbori a wajen ta'aziya... Sati biyu da rasuwan Alhaji Wamako, Alhaji Abbori ya samu Baba akan maganar auren Sadiq da Sanah. Cikin Ikon Allah ya sa mutuwar Alhaji ya sa Baba ya risina musamman da ya tuna yadda Alhaji Wamako yai ƙoƙarin sasanta tsakaninsu kafin rasuwar sa. Baba ya amince da maganar auren bayan ya nemi Alhaji Bukarti ya janya neman, dama shima yana fama da matansa da su ka tisa shi a gaba saboda auren da ya ce zai yi... Sanah ta taki sa'a ba kamar ni ba. Yau ina tareda Alaja a falo lawyer ɗin Alhaji ya shigo. Bayan sun gaisa da Alaja ya faɗi abinda ya kawo shi, wai Inna ce ta ke so a raba gado. Ni da Alaja mu ka kalli juna cikin mamaki domin yau ne kwana goma shatara da mutuwar Alhajin. Dole ta ce a raba gado mana tunda ita ke da 'ya'ya dayawa, ɗa namiji guda da 'ya'ya mata shida. Alaja ta kalli lawyer ta ce ciki gareta dan haka maganar gado sai ta haihu. Ni kaina sai da ta yi maganan cikin na tabbatar da zargin da na ke ma ta tun kafin ma ta tafi Lagos. Fitan Lawyer daga falon ko minti biyar bai yi ba Inna ta shigo falon tana masifa wai ba za ta yadda da wannan ƙaryan ba. Idan ma wani salon yaudaran ne gara ta dena dan ba zai yiwu ba. Alaja ta miƙe tsaye ta ce "Asma'u ke gado ya dama ba ni ba, amma ki sani sai na haihu ayi batun gado domin cikina yana wata na biyar ne yanzu, kuma zai zo duniya da yardar Allah" daga haka ta bar wajen. Inna ta sa ihu tana zage zage har da kiran Alaja da Ashawo. Ni kam na riƙe baki ina ganin yadda Inna ta maida kanta mahaukaciya saboda dukiya, dukiyar da shi Alhajin ma haka ya mutu ya barshi ba tareda ya ɗau komai ya tafi da shi makwancinsa ba... 19-The new bride A Abu ƙarami sai ga shi ya zama babba, Alaja da Inna da ya kamata su zauna su yiwa Alhaji takaba cikin kwanciyar hankali sai ya zama kullum cikin case ake yi a gidan. Abu ta kai har manyan mutane sai da su ka shiga ciki. Dama duk cikin 'yan uwan Alhaji ba wanda Inna ke shakka, da akwai wani yayansa Alhaji Abbas da ta ke mugun tsoronsa amma Allah ya ma sa rasuwa kusan shekaru goma da su ka wuce. Ƙarshe da na ga abin ya zama haka sai na bawa Alaja shawara akan ta janye ƙudirinta ta bari a raba gado idan ya so sai a bar kaso biyu wanda za a ajiyewa jariri ko jaririyarta. Ni tsorona kar Inna ta sa a kashe Alaja tunda da kunnena na ji tace saboda gado ta kashe Jamilah matar Alhaji. Alaja ba wai gadon ne ya dameta ba kawai dai ba ta so ta ragewa Inna abin da ya ke hakkinta ne da na 'ya'yanta. Ganin ba ta fahimceni ba ya sa na fito ma ta da gaskiyar abin da na ke tsoro da kuma abin da na ji ranan da Alhaji ya rasu. Duk haƙurin Alaja wannan information da ta ji ya sa ta tunzura sosai, ta ɗau alƙawarin maka Inna a kotu a bi hakkin Jamilah da Alhaji. Ni da na faɗa mata dan ta saduda ta haƙura da komai sai ya zamana na jawo wani masifan ne. Alaja ta fara bincike sosai har ta gano inda Magaret ta ke, har da ni mu ka je muka haɗu da Magaret wanda ta zayyane mana komai tareda alƙawarin za ta ba da shaida a kotu saboda gaskiya ta tuba tana son samun ceton Yesu dan haka za ta faɗi gaskiya a ko'ina. Ni dai tunda Alaja ta fara bincike na ke jin tsoro amma na daure na cigaba da tayata da addu'a. Ranan ina zaune a ɗaki ina haɗa report sai ga Ahmad ya shigo, yana zuwa ya jawoni daga kan gado ya fara dukana ta ko'ina bugu ya ke yi zagin da ya ke min da maganganun da ya ke faɗa ya sa na gane ba wai dukan sha'awa ya ke min ba. Sai da ya ga na daina motsi ya fita daga ɗakin. A ƙalla na kai kusan awa uku kafin Salamatu ta shigo ɗakina ta ganni kwance a haka. Ta fara salati tana ƙwalawa Uwale kira, suna shirin kaini asibiti na ce su barni. Su ka taimakamin na kwanta akan gado zazzaɓi mai zafi ya rufeni. Daga baya da Alaja ta zo ta ga halin da na ke ciki ta ce yanzu kam bayan Inna har Ahmad za ta yi ƙara saboda abin da ya ke min. Na dinga roƙonta akan kar ta yi ƙaran Ahmad, mutane za su zargeta. Da ƙyar ta haƙura da maganar. Ban gaya mata saboda ita Ahmad ya dakeni ba, domin an kai wa Inna takardar sammaci daga kotu shine ya zo ya sauke haushinsa a kaina wai har da ni acikin wannan munafurcin. Da na san maganar nan shi zai yi sanadiyar ajalin Alaja da ban yi ba... Bayan Ahmad Inna ma ta zo gida ta min tatas tareda min alƙawarin idan ta gama da Alaja za ta dawo kaina... Da ƙaton ciki haka Alaja ta je kotu ranan da aka yi zaman farko, cikinta ya shiga watansa na tara kenan haihuwa ko yau ko gobe. Ba na wajen saboda Ahmad ya hanani fita, tun wancan dukan da ya min ma ya hanani fita ko'ina, har wajen aiki na dena zuwa. Bayan an gama zaman kotu na ranan aka ɗaga zama zuwa sati biyu ma su zuwa saboda a ƙara bayyana shaidu. Lafiya-lafiya Alaja da ƙanwarta da ke zama tareda ita Madam AdeKumbi su ka shiga mota, da ke family ɗin su mix ne ita cousin ɗinta Kumbi christian ce.  Dreba ya wuce da su gida. Ba su jima da barin kotun ba motar su ta yi hatsari ta kama da wuta. Dreban da Madam Kumbi a take su ka mutu amma ita Alaja sai da aka kaita asibiti da kusan awa ɗaya kafin ta cika. Ana ƙoƙarin shiga da ita theater room a ciro ɗaya yaronta da ke motsi amma da aka sake scanning aka ga shima ɗin babu rai. Haka Alaja Barakat Atinuke ta mutu da ita da 'yan biyunta. Nikam da labarin mutuwar Alaja ya riskeni sai da na suma saboda gigicewa da na yi. Kafin yamma an kai dreba da Alaja makwancin su yayinda 'yar uwarta Madam Kumbi kuma aka kai mortuary saboda a Lagos 'yan uwanta ke son bisine ta. Kwana biyu ban gane kaina ba. Wannan mutuwar sai ta fi girgizani fiye da lokacin mutuwar Alhaji. Satin da aka yi rasuwan sati na gaba ne bikin 'yar uwata Sanah sai dai har bikin ya zo ban je ba. Na farko saboda mutuwar Alaja da bai sakeni ba har ya sani jinya. Na biyu kuma saboda Ahmad ya hana, yadda gidan ya rikice tun mutuwar Alaja ya sa ba ya son na je ko'ina. 'Yan jarida su ka yi ta yin zirya a gidan ƙarshe dai magana ya wuce kamar ba a taɓa yi ba. Wata guda da mutuwar Alaja kotu ta wanke sunan Hajiya Inna. Maganan gado kam kamar Inna ce ta yi kason domin ɗan Alaja mai suna AbdulWahab bai samu komai ba. Tun rasuwar mahaifiyarsa ma da 'yan uwanta su ka tafi da shi bai sake zuwa ba hakanan ba su waiwayi 'yan uwan mahaifinsa da maganan gado ba. Safiya ma ɗin Lagos ta koma idan ta zo Sokoto ba ta taka gidan Ubanta sai dai ta je gidan 'yan uwan Babanta a Wamako. Babu Alhaji ba Alaja duniya sabuwa a wajen Inna. Ta shiga nan ta fita chan, ita da ɗanta kawai su ke sha'anin su. Inaga ma sun manta da ni a rayuwar su. Ahmad ba ya nemana sai ya bushi iska ita kuwa Inna dama she's too busy ne yanzu. A shekaran ta sake zuwa Hajji ta renewing haƙorin da ta sa. Ma su aikina tuni Inna ta fatattakesu ni kaɗai ke hidima ta a gidan. Kwatsam wata rana Inna ta shigo da masu aiki ta ce su fitar min da kayana su maida ɗakin da ke ƙasa ban ce komai ba na zuba musu ido kawai. Inna ta ce idan an gama kwashe min kaya zan koma ɗakin ƙasa domin an kusa kawo amarya. Na ce Allah ya kawota lafiya. Idan da adalci ɗakuna huɗu ne a sama ɗaya nawa ɗaya na Ahmad sauran biyun ba wanda ke amfani da shi. Amma ni kan daɗina ma tunda amarya za ta zo wahala na za ta ragu musamman wajen Ahmad. Sati biyu da wannan chanjin aka kawo amarya. Duk wani hidima da bidiri a ciki duk babu ni aciki ban ma san yaushe ne auren ba sai a bakin ma su aikin Inna. Aka yi biki aka ƙare, aka kawo amarya. Ranan sai ga kiran Amma tana ban haƙuri tareda yi min nasiha, da ta ƙare hiranta na ce na gode amma ta adana maganganunta domin ba na buƙatar su. Amma ta tsorata da amsata ta fara tambayana ko ƙalau na ke na ce ma ta ta gaida gida na ajiye wayar. Watana goma da kwana shaɗaya a gidan Ahmad ya ƙara aure... Amarya Bilkisu 'ya ce guda a gidan Alhaji Ɗan iya, wani attajiri kuma hamshaƙin mai kuɗi a garin Bauchi. Bayan arziƙi har da sarauta domin shine Tafidan Bauchi. Yadda ka san ƙwai haka Inna ke lallaɓa Bilkisu, daga gidan su ma da ma su aiki uku aka haɗota ga Inna da ta ƙara mata biyu. Sati ɗaya da biki ita da Ahmad su ka wuce honeymoon ƙasar waje. A yadda ma su aikinta ke gaya min sai sun yi wata biyu kafin su dawo amma idan har lissafina yayi dai-dai to satin su biyu su ka dawo. Bayan sun dawo kuwa rikici ya ɓalle a gidan, ban san miya haɗasu ba amma kuma a ɗan ƙus-ƙus da na ke ji halin Ahmad ne ya isheta ya sa ta dawo. Ranan ina ɗakina na ji faɗan Inna da Ahmad akan Bilkisun. Wai Bilkisu ta kawo ƙara akan yadda ya ke mata ba ta jin daɗi. Ina ji yana faɗin " ita Aaliyah ba Mutum ba ce? Duk yadda na je mata ba ta taɓa complain ba amma wannan duk abinda mu ka yi sai ta kwashe ta gaya miki" "Ahmad, Dole mu lallaɓa Bilkisu domin ba dan Mahaifinta ba da ban kai matakin da na ke yanzu ba" "I dont care. Ta ce ba ta son duka na dena, ta ce na dinga mata a hankali ina yi. Mi kuma take so? Ban sameta a budurwa ba did i complain? Sai ita ce za ta buɗi baki ta kai ƙarana. To hell with her, idan ba za ta iya daniba ta tafi dama ke kikace na aureta ba ni na ce ina son aure ba" Ganin ɗanta ya birkice mata ya sa ta shiga lallashinsa daga ƙarshe ya fita ya bar mata gidan. Nikam na ce tukunna ma. Bayan kwana biyu abubuwa su ka lafa amma ni kam ba abinda ya chanja min yadda Inna ke sani aiki haka Amarya za ta sani aiki duk da tanada ma su mata aiki a gidan. Ni kam i've accepted my fate shiyasa na ke bin komai a hankali, ɗaga ƙafar da na samu daga Ahmad ya min daɗi. Bilkisu ta san banida daraja agidan walau a wajen Ahmad ko mahaifiyar sa. Amma duk da haka kishi ta ke dani, ƙiri da ƙiri ta ce kishin kyauna ta ke yi, wai da tanada rabin kyauna da ba abinda zai sa ta tsaya da Ahmad, wai Ahmad ya yi kaɗan. Nikam sai dai kawai na girgiza kai kawai dan ba abin da zan ce... Ranan da Ahmad ya zo wajena bayan ya gama lallasani na yi ƙoƙari na tambayeshi ina son zuwa gida. Sanah da mijinta za su koma Ƙasar Canada kuma rabona da ita tun lokacin mutuwar Alhaji. Rashin zuwa bikinta da na yi ya sa take fushi dani har da ta yi aurema ta ƙauracewa gidana. "Mu ma za mu koma London Aaliyah, akwai gidan Alhaji achan kuma yanada hannun jari dayawa anan. Ina son barin ƙasar nan, this country sucks" Wannan ne karo na farko da Ahmad ya faɗa min wani abu mai muhimmanci a tarihin auren mu Na ce ma sa Allah ya kaimu... Ina wanke-wanke ina murna saboda zanje gida for the first time bayan shekara ɗaya da aure na. Gobe ne tafiyar kuma Ahmad ya ce na yi sati ɗaya a chan. Hajijiya na fara ji wanda ya sa na dafe sink ɗin kitchen ɗin da sauri ina ƙoƙarin saita kaina amma duk da haka sai da na kai ƙasa. Na jima ina zaune har Mairo ta shigo ta sameni, ita ta taimaka min na tashi tace na koma gida za ta ƙarasa aikin tunda Inna ba ta nan. Na mata godiya na tafi. Ina zuwa na bi lafiyar gado na kwanta. Haka ranan ta wuce mani a ɗaki domin gaba ɗaya wani kasala na ke ji, na kan ji hakan 'yan kwanakin nan amma kuma na danganta hakan da yawan ayyukan da na ke yi... Da dare Ahmad ya zo wai zai min sallama. Dama tunda Bilkisu ta yi tafiya ya koma min. Ce ma sa ma banida lafiya ma ɓata baki ne dan haka na barshi.  Ya hau kaina ya fara riding ɗina kamar yadda ya saba, wani azaba na fara ji wanda ya jima ban ji haka ba idan yana sex dani tun ina jurewa har na fara kuka ina roƙon sa ya tashi a kaina. Da ƙyar ya haƙura ya tashi, ganin jini a ƙasa na ya sa shi tambayar ko lafiya. Dama dokar Ahmad ne ba a kashe wuta idan yana abunsa. "Aaliyah kin fara period ne?" Ban kulashi ba dan tuni na suma. Ganin ban tashi ba ya sa ya ɗan ruɗe ya shiga jijjiga ni daga ƙarshe ya sa jallabiya ya naɗoni a bargo ya fito dani sai mota... A asibiti na buɗe ido na ganni. Ahmad na gefe na fiskar sa da fara'a. "Sannu Aaliyah, ina ke miki ciwo?" Na girgiza ma sa kai. "Sannu kin ji. Barin kira Doctor ya duba ki" Da Dr Munnir ya zo ne ya shaida min abinda ya faru kuma a nan na gane silar murmushin Ahmad ɗin. Wai ƙaramin ciki gareni kuma jiya ɗin na zubar da jini amma cikin bai fita ba yana nan. Dr Munnir ya ba da shawaran Ahmad ya rage sex da ni har sai cikin ya yi ƙwari. Da mamakina sai na ji Ahmad ya ce " ai idan ka ce na barta sai ta haihu ma zan barta, for my son xan iya yin komai" Haka Ahmad yai ta nan nan da ni a dole wai dan inada ciki. Ya sanar da Inna amma ba ta zo ba haka na yi kwana biyu a asibiti su ka sallameni. Da na dawo gida Inna ba ta yi murnan wai ina da ciki ba sai ma kwaɗayinta da ta nuna akaina. Wai dalilin barina da ta yi da Ahmad dan gadon da zan samu ne idan Baba na ya mutu. Ikon Allah ita ba mutuwarta ta ke hangowa ba sai na wasu. 20- London A A kwana na uku da dawowata Ahmad da kansa ya kai ni airport na shiga jirgi na wuce Maiduguri.  Da ke na gayawa Amma ina zuwa shiyasa aka aiko da dreba daga gida ya zo ya ɗaukeni. Tun a hanya na ke ganin chanje-chanje, sai ya ke min kaman shekara goma na yi ban zo gida ba. Gidan mu dai bai chanja ba, na dai ga sabon fenti inaga a lokacin bikin Sanah aka yi. Kai tsaye sashen Amma na shiga ina ƙoƙarin yaɓawa kaina murmushin dole. Ƙannena Yahya da Musa na samu a falo suna kallo, su na ganina su ka fara murna suka zo suka rungumeni. Sai na ga duk sun chanja mani sun ƙara girma sosai. Musa Kalim Auta ma ya yi tsayi sosai. Muna cikin hira da su Amma ta fito daga ɗaki. Kallon-kallo mu ka tsaya yi da ni da ita. Ita tana min kallon na rame na lalace ni kuma ina ma ta kallon ƙiba da wani haske da ta yi. "Amma na same ku lafiya?" Na faɗa bayan na janye Ido na daga cikin na ta. Maimakon ta amsa sai ta jefo min da tambaya "Aaliyah ba ki da lafiya ne? Kin ganki kuwa?" Na yi murmushi ina murza yatsuna da su ka koma daga laushi zuwa tauri... Ranan kowa ya ganni sai ya yi maganan da Amma ta yi. Dan a tunaninsu rashin lafiya ne kawai zai sa nayi wannan mummunan chanjawar.  Da yamma lis na je gidan Sanah. Kwanciyar hankali da farinciki na tarar a gidanta, itama na da ƙaramin ciki shiyasa sirikarta ke lailayata kamar ƙwai. A wajen Mama uwar mijinta, Sadiq ne ɗan fari dan haka tana ji dashi, soyayyar da ta ke wa ɗanta shi ya raɓi Sanah. Saura sati ɗaya su bar ƙasar zuwa Canada dan a nan Sadiq ya samu aiki. Duk wani faɗan da Sanah ta tanada min da ta ganni sai ta ji ta huce. Tausayina ya kamata, da na zo muna cin abinci ta ga yadda  hannuna ya koma sai da ta yi kuka. "Aaliyah ki rabu da Ahmad dan Allah, zai kashe ki" ta faɗa cikin kuka. "Ina da ciki" na furta a hankali Ta ɗago ido ta kalleni ta rasa farinciki za ta yi da labarin da na bata ko baƙin ciki. "May be its too late for everything dear Sister. I'm  carrying his child" na ƙarasa faɗa lokacin da na haɗiyi lomar abincin da na sa a bakina Ta riƙe hannuna ta ce "ki duba hannunki Aaliyah. Haka za ki cigaba da rayuwa da shi kenan?" Na yi murmushi tareda ce mata Ahmad na son cikin jikina kuma ya ce za mu koma London da zama, idan na yi nisa da Inna zan samu sauƙin wasu abubuwan. And who knows Ahmad might change... Ban bar gidan Sanah ba sai ƙarfe tara na dare. Ita da mijinta su ka dawo da ni gida. Kai tsaye ɗakina na wuce na shiga banɗaki na yi wanka ina fitowa ɗaure da towel na tsaya gaban mirror ina ƙara kallon kaina. Na yi haske sosai, inaga saboda cikin jikina ne amma kuma ba ƙaramin rama na yi ba.  Na sa hannu na fara shafa fiskata zuwa wuya na. ********************** ⬇ ************************** ************* Ai Hausa Novels **************** *************************⬆ ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ⬇ ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ⬆ ************************** Amma ta ƙwanƙwasa ƙofar ɗakin ta shigo tana faɗin "Aaliyah ga tea na kawo miki, garin akwai sanyi yau" ta tsaida maganarta lokacin da ta ga kafaɗuna zuwa bayan wuyana. Innalillahi ta fara maimaitawa ta ƙariso wajena da sauri bayan tea ɗin da ta ɗauko ya ɓare a hannunta. "Aaliyah miye wannan? Mi ya sameki anan? kaman tabon duka na ke gani" ta faɗa tana kai hannunta wuyana. Towel ɗin na kunce na jashi ya faɗi ƙasa. Amma ta kama baki haɗeda zaro ido ganin raunukan da ke bayana, ɗuwawuna zuwa ƙafafuwana. "Wa su sun warke, wa su suna kan warkewa wa su kuma sabbin raunuka ne ko?" Na faɗa gameda juyowa ina kallonta. "Subnallahi, Aaliyah ba dai Ahmad ne ya miki wannan ba?" Ta faɗa cikin rawar murya Murmushin takaici na yi na ce " Amma akwai raunin da ya fi kowanne daɗewa ajikina, tun ranan farko da aka kaini Sokoto na sameshi. Ya jima da warkewa sai dai tabo da ya bari a wajen bai bar wajen ba har yau. An dakeni lokacin saduwa, an dakeni saboda maganar baki, an dakeni saboda uwar miji, an dakeni saboda na goyi bayan  gaskiya. Ban san daɗin aure ba Amma, duka da wahala kawai na sani. Ban san farinciki da kwanciyar hankalin aure ba Amma, fargaba, tsoro da baƙin ciki kawai na sani. Ban..." Na tsaya da maganar lokacin da na ga Amma ta yi zaman dirshan a gabana tana rusa kuka. Na ɗau towel ɗin da ke ƙasa na ɗaura shi jikina na ce "ina fata dai alfanun da kuke nema da ku ka haɗani aure da Ahmad kun sameshi?" na shige banɗaki da sauri saboda kuka da ke cin ƙarfi na. Na rufe baki ina kuka, kukan abubuwa dayawa na ke yi amma alokacin kukan da ya fi damuna shine kukan ɗan da ke cikina. Ɗan da aka sameshi lokacin da na ke tsaka da Allah ya isa wa Ubansa, ɗan da zai fito ya ganni cikin baƙin ciki da tsanar uban sa. Ɗan da kullum na kalleshi zan so inama bai fito ta satson uban sa ba... Amma ta jima tana kuka a ɗakina kafin daga baya ta ja ƙafafuwanta ta bar ɗakin. Sai da na ji fitanta sannan na fito daga banɗaki na sa kayan bacci na bi lafiyar gado. Ban jima ba baccin gajiya ya tafi da ni... Washe gari Amma ko kallona ba ta iya yiba. Da na gaidata da ƙyar ta amsa min, muryanta ya dashe hakanan idonta duk sun kumbura. Tun bakwai ta fita gidan Hajia Badariyya sai dai ko da ta je aka ce ma ta Hajiyar ba ta ƙasar ta tafi Dubai siyayya. Haka Amma ta dawo jiki a sanyaye. Da ta dawo ina zaune a falo ina kallo, a zahiri kallon na ke yi amma chan zuciyata wani ƙunci na ke ji. Gidan su Jiji na je dan mu gaisa na samu sabbin fiska a cikin gidan da na tambaya sai aka ce wai su Jiji sun jima da tashi. Wani zafi na ke ji yana mamaye duk ilahirin jikina duk da kuwa sanyi da ake yi a garin. A kowani rana sai na tuna da wani abu na rayuwar da mu ka yi da Sa'eed, duk iya ƙoƙarina na ganin na yaƙice hakan a raina na kasa musamman idan na kalli yatsata na ga zoben da Sa'eed ya sa min a wajen. Sanin akwai auren Ahmad a kaina ya sa na ke yaƙi a kullum dan na dena tunanin sa amma still duk a banza. Halayyan Ahmad su suka sa na kasa mantawa da mutumin da na ke tsananin so a duniya... Amma ta zauna gefena tana  faɗin "ki yafeni 'yata. Ni ne nan na cuceki, ba abinda zai sa ki zauna da Ahmad yana zaluntar ki face abinda na sa aka miki da ke riƙe ki" Hannuna ta kamo tana kallon yadda su ka koma. "Ranan da ki ka yi ƙoƙarin guduwa abin ya bani tsoro. Na san taurin kan ki, na sani ko bayan an ɗaura auren ki da Ahmad za ki iya guduwa. Ina gudun ki jawo mana abin kunya, ina gudun ki yi abinda har ki koma ga Allah za a dinga zagin ki da shi, shiyasa da Hajia Badariyya ta bani shawara na amince. Wajen Malami ta je aka rufe min bakinki ba za ki taɓa neman saki da bakin ki ba a wajen Ahmad. Ba anan abin ya tsaya ba,  ba za ki taɓa guduwa daga gareshi ba kai ko shi ya sakeki bisa ra'ayin kan sa ba za ki bar gidan sa ba har sai an warware abinda aka miki. Niyyata idan kunyi aure kin zauna da shi kin kwantar da kan ki sai na sa a warware abin da aka miki. Na yi wauta Aaliyah ki yafeni" ta ƙarasa maganar tana kuka mai tsuma zuciya. Inna was right all along shiyasa ta ke min abinda ta ga dama saboda ta san ba zan iya rabuwa da ɗanta ba. Na miƙe tsaye na kalli Amma da ke kuka na ce "ko da abinda ki ka min ya fi wannan ni mai yafe miki ne saboda ke kika haifeni. Zamana a gidan Ahmad na koyi darasin rayuwa, na gani muraratan yadda mace ke iya zama hatsabibiya sheɗaniya saboda dukiya. Na ga yadda kwaɗayin duniya ke sa mutum ya zama marar imani marar tausayi. Na gane cewa kuɗi ko kaɗan ba su ke jawo farin ciki ba kuma ba za su iya siyan farin ciki ba. Kuɗi kuke tunanin zai sani farinciki shiyasa ku ka ƙi Sa'eed kuka zaɓi Ahmad" Na share hawayen da su ka cika min ido na ce "Na yafe miki Amma kuma nima ina so ki yafe min. Ko da na mutu a gidan Ahmad na amince addarata ce ta zo da hakan ku dai kawai kun zo a sababin kaini gidan sa ne" Na wuce ɗaki na bar Amma tana cigaba da kuka... Cikin kwana biyu Amma kamar za ta zauce, neman numbar Hajiya Badariyya kawai ta ke yi saboda ta samu a warware duk wani ƙullin da aka min. Baba da baya ƙasar ma sai da ta kira shi ta ce ya dawo ya ga yadda na koma, tun a waya ta ce ma sa idan ya zo dolene a raba aurena da Ahmad. Da ke bai san mi ya ke faruwa ba ya dai kwantar ma ta hankali akan dole zai dawo Monday ya gani da idonsa koma minene ta ke magana a kai. Monday ɗin ya kamata na koma Sokoto sai dai yadda Amma ta takura ya sa na ce zan bari Baban ya dawo kafin na tafi.  Ranan Jumu'ah da misalin ƙarfe uku ina zaune a ɗaki ina karanta wani littafi mai suna Gone with the wind wanda Sa'eed ne ya siya min lokacin muna Cambridge sai  ga Kalim ya shigo ɗakin da gudu. Ce min yai wai Ahmad ya zo yana falo, na zaro ido cikin mamaki ko dai dan dawo yau ɗin ba ne ya biyo bayana. Na yi saurin ɗaukan gyale na yafa na fito falon. Ɗan nesa da shi na tsaya ina kallon sa na rasa ma mi zan ce ma sa. "Tunda ban samu gaisuwaba ni ba rin gaisa da baby na. Fatan kina kular min da shi?" "Sannu da zuwa, ya hanya?"  Na faɗa ina ƙoƙarin haɗiye miyau. "Na baki minti ishirin ki shirya ki fito tafiya za mu yi" Dama na san sai dai hakan. Na daure na ce Amma ba ta gida ka ɗan ƙara min lokaci ta dawo sai mu yi sallama. Ya miƙe tsaye ya ce " minti talatin" ƙarasowa yai gabana yai zai shafa ciki na, da na ga ya kawo hannu sai da hanjin cikina su ka kaɗa dan na ɗauka duka zai kai min. Yana ajiye hannun sa a ƙasan cikina ina sauke ajiyar zuciya nima. Ya kalleni ya ce " na gaya miki har ki haifi baby na ba abinda zan miki" Har ya fita ban bar kallon ƙofa ba, shikenan zan koma gidan tashin hankali. Na koma ɗaki dan na tattara kayana tunda na san halin sa ba haƙura zai yi ba. Na gama shirya jaka ta na ɗauko na fito bayan na rubutawa Amma ƙaramar takarda kan na tafi Ahmad ne ya zo. Ina fitowa falon Amma na shigowa, ganina da jaka ya sa ta ƙariso da sauri tana tambayar ko lafiya. Na ce tafiya zan yi Ahmad ne ya zo ɗauka na. "Ba inda za ki je, ba za ki koma gidan sa ba. Duk abinda zai je ya dawo ba zan bari ki koma ba" ta faɗa da ƙarfi. Na girgiza kai a hankali na furta "its too late" "Its not late Aaliyah. Babanki zai dawo ranan litinin, Badariya ma ta ce za ta dawo ranan laraba kinga komai zai zo ƙarshe kenan. Alhamdulillah ma da rabo bai ratsa tsakanin ku ba, a rashin sani ina chan ina addu'ar Allah ya baki ciki ashe da mugu ki ke tare. Allah na gode da ba ka amsa addu'a ta ba" ta faɗa tana ɗaga hannunta biyu sama kamar mai addu'a. Murmushin da na yi ne ya yi sanadiyar suɓutowar hawayen da su ka taru a idona. "Allah ya amshi addu'ar ki, akwai rabo tsakanina da Ahmad" Amma ta yi taga-taga kamar za ta faɗi na yi saurin riƙota. "Duk da haka Aaliyah ba za ki koma ba, ba za ki koma ba" ta ƙarisa maganar cikin kuka... Dreban na mu gudu kawai ya ke fanfalawa a titi. Na dai ga ba hanyar Sokoto mu ka nufa ba amma na yi shiru, lokaci zuwa lokaci Ahmad na sa hannu a cikina yai ta sunbatun sa, a dole yana yiwa ɗan sa hira. Sau uku ina bacci ina farkawa amma tafiya ta ƙi ƙarewa mun tsaya sau biyu dan cin abinci da kuma sallah bayan na lura tun da mu ka taso bamu yi sallar la'asar ba balle magariba da Isha. "Ba za ki tambayi inda za mu je ba?" Ya faɗa lokacin da ya ga ina ƙoƙarin sake komawa bacci. "Koma ina zamuje Allah ya sauke mu lafiya" Dariya yai ya ce "Aaliyah kenan, har yanzu kina da girman kai. Da ki tambaye ni gara kin jira har mu isa inda za mu je ki gani da idon ki kenan. Shikenan Maman baby" ya ƙarisa maganar yana dariya ƙasa-ƙasa... Lagos mu ka je, ni kaina ban san dalilin zuwan mu ba sai daga baya. Ahmad ya saki Bilkisu kuma sun yi kaca-kaca da Inna shiyasa ma ya zo ya ɗaukeni akan mu zauna a Lagos kafin visan mu ya zama ready. A gidan Alhaji da ke Lagos mu ke zaune, ni dai ban taɓa tambayanshi abinda ya faru ba, a hankali ya dinga gaya min da bakin sa musamman ranan da ya bugu. Anan na ke jin asalin gaskiyar sa. Ranan da na bar Sokoto ranan shima ya tafi Kano yai kwana biyu a chan. Kasancewa shi dama tafiyar sa da dawowar sa duk ba a sani shiyasa a rana ta uku ya dira a gidan bagtatan inda ya je ya kama Bilkisu da kwartonta, abin haushin ma ɗaya daga cikin abokan sa ne. Abu da ɗan giya haka ya hau jibgarta ita da kwarton, kwarton ya tsira da ƙyar itama kuma ihun da ta ke yi ya ja hankalin ma su aikinta su ka je su ka sanar da Inna. Inna ta taho da gudunta ta ceci Bilkisu da ƙyar a hannunsa gaba ɗaya ta galabaita ga jini a baki da hanci. Inna ta fara ma sa faɗa shi ko ya nuna ga abinda ya kamata tana yi, Inna ta ce ai ba komai bane jiba da irin tarbiyan da aka yiwa Bilkisun. Uwa da ɗa su ka shiga yaɓawa junansu magana suna zage-zage ƙarshe ya fita ya bar mata gidan bayan ya rubutawa Bilkisu saki uku. Ba akai Bilkisu asibiti ba likita Inna ta kira ya zo har gida ya dubata. Inna ta dinga bawa Bilkisu haƙuri kan abinda Ahmad yai, ita ba ma ta abinda Bilkisun ta aikata ta ke ba, tsoron abinda Alhaji Ɗan Iya zai yi idan har ya ji labarin dukan da Ahmad yai wa 'yar sa ta ke ji. Inna ta shiga lallamin Bilkisu tareda yi mata alƙawarin Ahmad zai tsugunna har ƙasa ya bata haƙuri. Ahmad ya dawo chan dare ya samu Inna na jinyar Bilkisu abin ya bashi mamaki. Duk dukan da zai min Inna ba ta taɓa hanashi ba sai ma tace madallah amma kuma sai gashi ya kama Bilkisu da kwarto amma har tana iya zaman jinyarta. Tana fara ma sa maganar Dawo da Bilkisu da kuma ba ta haƙuri ya haukace ma ta a daren ya shiga fizgar da kayan Bilkisu waje yana faɗin idan ba ta bar ma sa gida ba zai kasheta. Inna kanta sai da ta tsorata da yanayinsa ta ja Bilkisu su ka fita su ka koma na ta gidan. A chan kuwa Bilkisu ta juyewa Inna da masifa tana zagi tana tsine ma ta. Inna sai haƙuri ta ke bata amma da Bilkisun ta gaya ma ta kalmar da ta fi tsana a duniya hakan ya sa Inna ta riƙiɗe ta fara maidawa Bilkisu martanin maganganunta. Haka Bilkisu ta bar gidan a daren tana tafiya tana zagin Inna da 'yar matsiyata 'yar talakawa, zuciyar Inna kaman zai fito dan baƙin ciki. Washegari tun asuba Ahmad ya tattaro kayan sa ya taho Maiduguri... Kwanan mu tara a Lagos mu ka wuce London. Haɗaɗɗen Mansion Alhaji ya siya, ni kaina gidan ya burgeni saboda tsarin ginin. Sati na ɗaya kafin na samu na kira Amma na gaya ma ta ina London. Da muryan kuka ta ke min magana, tun ranan da na je gida Amma ta ke dana sanin abinda ta aikata da wanda ta bari aka aikata a kaina. Cemin ta yi Malamin da yai wa Hajia Badariyya aiki ya rasu, yanzu haka sun nemi wani malami ya ce zai iya karya alkadarin. Ni kam tabbatar ma ta da cewa na yi da abinda su ka min ya karye da bai karye ba idan ba Ahmad ne ya sake ni da ra'ayin kan sa ba zan cigaba da zama da shi duk rintsi. Amma kam cewa tayi ba zai yiwu ba dole ne na rabu da Ahmad. Ni 'yar gata ce gaba da baya, ban cancanci miji kamar Ahmad ba, ni kam na ce daga baya kenan. Baba ya kirani sau ɗaya inda ya ke neman na gaya ma sa gaskiyar abinda ke faruwa tsakanina da Ahmad, shima dai yana maganar ne cike da tarin nadama duk da girman kai bai bari ya yarda da hakan ba. Ba abinda ya sa ya aminta da zancen Amma face lokacin da ya kira Ahmad tun muna Lagos akan ya zo ya sameshi za su tattauna sai Ahmad ya ce ba shi da lokacin sa. Wannan kalmar ta shocking ɗin Baba matuƙa. Ni ban ma san anyi haka ba Amma ke gayamin komai. Ga Inna a gefe da dama tun batun rabon gadon Alhaji Wamako su ka ɓata da Baba, da Baba ya san a gaba Ahmad zai ma sa fiye da baƙar magana ina ga da tuntuni ya zo ya tafi dani ko da ta ƙarfi ne, amma aka ce rashin sani ya fi dare duhu... Zama a London ya zo min da sauyi da dama a rayuwata. Har wa yau ban yi dana sanin zuwa garin ba, akwai ranakun baƙin ciki akwai kuma na farin ciki. A London na ga wani ɓangare na Ahmad wanda ban san da shi ba a zaman da mu ka yi na Shekara ɗaya a Sokoto. *21- The casino* *A* Wata ɗaya da mu ka fara yi ya zo min da kwanciyar hankali, na farko dai banda yawan bacci da cin abinci da cikin jikina ke sani ba ni da wani damuwa. Ina samun isashshen hutu domin ba na wani aiki, aikin wahala da na yi ya ƙare a gidan Inna. Inada mai aiki wata Black American Mrs Payne wanda a ƙalla za ta kai shekaru hamsin a lokacin. Ita ke yin aikin komai ko na ɗan shiga kitchen domin na yi wani abun idan Ahmad ya zo ya gani zai fara faɗa wai zan wahalar da ɗan sa, hakan ya sa na daina komai. Kamar yadda yai alkawari kuwa ya daina nemana hakan ya ƙara kwantar min da hankali. Na fara sakin raina da gidan kwatsam sai ga Ahmad da wata karuwa wata yammaci ina zaune a terrace na gidan ina shan iska. Daga yanayin yarinyar ya sa na san irin matan da Ahmad ke so kenan, irin macen da yai ƙoƙarin mai da ni kenan. Yarinyar na sanye da wani lether mini skirt babu riga ajikinta sai wa su chains da ta sa dayawa wanda ya ɗan rufe gefen nonuwanta. Akwai rings a hancinta biyu da gefen bakinta har a nonuwanta akwai rings da ta piercing ajiki. Kallo ɗaya na mata na ɗauke kaina dan ƙyama ma ta bani. Ina gani su ka shiga gidan na cigaba da zama a inda na ke domin daɗin zaman wajen da na ke ji. Bai fi minti biyar da shigan su ba na fara jin ihun yarinyar tareda ƙaran duka. Na sauke ajiyar zuciya ina ƙoƙarin ɗauke hankalina daga abin da na ke ji. Amma ina ihun yai yawa na tashi dan na shiga ɗakina na nemi ko littafine nai karatu. Yadda na ke jin ihun yai yawa ne ya sa na sauko dan na tabbatar da zargi na. A tsakiyar stairs na tsaya ina banin yadda Ahmad ya ɗaure yarinyar nan tsaye yana jibgarta yana saduwa da ita. Na juya ciki ina yi ma sa addu'ar Allah ya shirya shi. Daga Wannan rana baturiyar nan mai suna Cataliya ta zama regular a gidan mu. Tun ina damuwa har na watsar da su na cigaba da renon cikina hankali kwance, idan su ka dameni da ihu kuma idan ba da dare bane fita na ke na je ta baya wajen lambu na zauna. Ko da a auren so ne akwai lokacin da idan miji ya shareka ya dena saka ka cikin lamuran sa kai ma za ka ajiye shi gefe ka zuba ma sa ido. Balle ni da na ke auren mutumin da ban taɓa so ba ban taɓa ƙauna ba. Idan ba ya zo yiwa ɗan sa hira ba bana gaban sa Cataliya ce komai na sa. Wata biyu da introducing Cataliya a rayuwar mu su ka yi aure. Ahmad Wamako ya auri Cataliya Santiago a kotu. Asalin su Cataliya 'yan mexico ne amma ita a London aka haifeta. Ban san dalilinsa na auren ta ba amma kuma na danganta hakan da business ɗin da ya ke yi wanda ban san komai gameda shi ba. A hankali ranaku su ka shige har ta kai cikina ya shiga wata takwas a lokacin ne kuma ciwukan da ban yi lokacin cikin yana ƙarami ba sai yanzun da ya girma ya fara. Daga ciwon ƙafa, ciwon baya sai rashin kuzari da ciwon kai mai tsanani a mafiya yawan lokuta. Ga rashin son cin abinci duk wani ci da na yi ta yi a baya sai na dena sai na wuni bai fi na ci abinci sau ɗaya ba. Duk halin da na ke ciki ban taɓa cewa Ahmad ya kaini asibiti ba. Shi yanzu ma sai yai kwana ɗaya biyu baya gidan. Ranan da na shiga wani hali har zazzaɓi ya turnuke ni na kasa fitowa tun safe ya sa dole Mrs Payne ta kira Ahmad amma ya dinga ma ta faɗa ƙarshe dai ta kashe wayan ta kira ambulance aka zo aka ɗaukeni. Kwana na uku a asibitin tukunna aka sallamoni cikin ranakun nan ko mai kaman Ahmad ban gani ba. Cewa su ka yi ina da hawan jini kuma sun na dena sa damuwa a raina idan ba haka ba zan samu matsala wajen haihuwa, su ka bani shawaran na dinga motsa jiki sosai hakan zai kawo min sauƙi wajen haihuwa. Na amshi dukkan shawarwarin su ina ƙoƙarin motsa jiki, wani lokacin Mrs Payne ne za ta raka ni mu fita strolling. Na yi mamakin da 'yan gidan mu ba su neme ni ba musamman da su ka san ina gab da haihuwa. Na yi ƙoƙarin kiran su amma ba ya tafiya, haka ya sa na haƙura na cigaba da addu'ar Allah ya saukeni lafiya ya kuma shiryar da abin da zan haifa kada ya ɗauko halin Uban sa. Sati ɗaya da dawowana daga asibiti amma ba Ahmad ba dalilin sa. A lokacin ne na tuno da alƙawurran Sa'eed. *"zan kasance da ke ako wani hali, idan ba ki da lafiya zan zauna na yi jinyar ki har ki warke. Idan kina da ciki da ni da ke za mu raini cikin, idan za ki haihu zan kasance tareda ke, na riƙe hannun ki na riƙa tofa miki addu'a har ki haihu lafiya"* Na share ƙwallan da ke zubo min ina ƙoƙarin danne duk wani shauƙin Sa'eed da na ke ji da shi a wannan lokaci. Ina cikin haka Mrs Payne ta shigo ɗakina da sauri tana faɗamin akwai wa su mutane suna nemana, yadda ta ke maganar ya sa na gane ba lafiya ba. Na tashi da ƙyar na bita mu ka fito. Wani mutum ne zaune akan kujera da ka ganshi ka san irin Mafia Boss ɗin nan ne. Bodyguards ɗin sa guda huɗu su na tsaye kowanne da bindiga a hannun sa. Na yi addu'a a raina sannan na tambayi mutumin dalilin zuwan sa bayan na zauna a kujeran da ke saitin sa. Ya kalleni da kyau sannan ya fara min bayani. Gidan da mu ke zaune na shi ne kuma yana so mu tashi zuwa gobe. Da mamaki na fara tambayar sa yaushe gidan ya zama na shi. Ya ƙyalƙyale da dariya kafin ya tambayeni yaushe rabon na kalli news na ce ma sa ba zan iya tunawa ba dan na jima. Ya ce to zai ban labarin abin da ke faruwa har wanda media ba su san da shi ba. Don Pedro Santiago wani Mafia Boss ne da yai ƙaurin suna a ƙasar sa Mexico zuwa America, UK da ma Russia. Yanada manya-manyan 'yan gwamnati da ke take ma sa baya shiyasa ya ke tsula tsiyarsa yadda ya ga dama. Yana da wani babban casino a tsakiyar birnin London inda ake gudanar da illegal business da dama. Watannin baya da su ka wuce Ahmad ya zama regular a Casino ɗin inda ya ke buga chacha kuma ba ƙaramin sa'a ya ke sosai ba duk lokacin da yai. Wannan sa'ar da ya ke samu ya sa har aka kai maganar sa wajen Don Pedro wanda yai niyyar hallaka Ahmad a lokacin daga baya zuciyar sa ya raya ma sa yai chacha da Ahmad ɗin. A lokacin ya sa aka ma sa binciken ko waye Ahmad da kuma abinda ya ke da shi. Nan aka gane Ahmad wani wawan ɗan Nigeria ne wanda uban sa ya bar wa kuɗi dayawa. Don Pedro ya fara buga game da rayuwar Ahmad. Cataliya 'yar Don Pedro ce, taƙadariyar 'yar ƙwaya ce kuma masochist. Ta jima da barin wajen Ubanta a shekararta sha tara ta zama fitsararriya ta ƙarshe. Uba da 'ya su ka haɗewa Ahmad wanda wauta ya hana shi ganewa domin bai san alaƙar Cataliya da Don Pedro ba. Cataliya ta shiga rayuwar sa har ta kai sun yi aure, ita ta dinga tunzura Ahmad ya dinga buga chacha da duk wani abu mallakin sa. Daga ƙarshe bayan an cinye duk abinda ya tara har bashi sai da aka bishi. Gidan da mu ke ciki ma Casinon Don Pedro ta cinye. Yanzu haka wasu maƙudan kuɗi ake binsa bashi har an rufe shi a prison saboda ba shi da halin biya. Innalillahi kawai na ke ta maimaitawa a raina dan Ahmad ya wuce tunani na. A yadda Don Pedro ya ke bayani duk wani kuɗi da kadara da na san Ahmad ya mallaka duk sun tafi a chacha. Allah ya tsinewa bature, Allah ya tsinewa wanda ya ƙirƙiro chacha a duniya na faɗa a raina. Ajiyar zuciya kawai na ke yi na rasa abin faɗa. Don Pedro ya miƙe tsaye yana faɗin saboda halin da ya sameni ya bani kwana uku na bar gidan idan ba haka ba za a zo a watsar da ni waje. Yana son buɗe branch na Casino ɗin sa da gidan na mu dan shi baya wasa da kuɗi. Mrs Payne ta kawo min ruwa na sha tana kwantar min da hankali. Zama na da ita ta fahimci irin auren mu shiyasa ta ke tausaya mun. Ta kan ce min mijinta Colins lokacin yana raye ba ƙaramin rayuwar daɗi da farin ciki su ka yi ba. Sai dai shekarar su sha biyar da aure ya mutu gashi ba su taɓa haihuwa ba. Bayan mutuwar sa ne ta adopting wani yaro tana kula da shi, to shima sickler ne bai jima ba ya mutu, daga haka ta cigaba da rayuwa ita ɗaya. Kwana na farko ni da Mrs Payne mu ka fita neman ko a wani prison aka rufe Ahmad amma ba labari, mun dai samu labarin cewa da gaske ne an rufe shi ɗin amma ba a London ba. Rana na biyu Mrs Payne ta sameni akan na bar gidan kafin Don Pedro ya dawo ya sa a mana koran walaƙanci. Na kalleta na ce ina zan je? Ina na ke da shi da zan je?. Ina da passport amma ban da kuɗin jirgi idan ba a titi zan dinga kwana ba to ba ni da wajen zuwa. Ta ce idan ba damuwa na bi ta mu je garin Watford akwai ƙaninta a nan. Ba yadda zan yi haka na ɗau jaka na sa kayana da na san nawa ne da passport ɗina na bi Mrs Payne mu ka bar London. Ƙaninta mai suna Riley yana zaune da matar sa da 'ya'yan sa maza guda biyu, ɗan shekara shabiyar da ɗan shekara shaɗaya. Ɗakin yaran aka bamu saboda gidan ƙaramine ɗakuna biyu ne aciki yayinda yaran su ka koma kwana a falo. Buri na na haihu lafiya idan ya so na nemi yadda zan yi na koma Nigeria tunda ban san inda Ahmad ya ke ba... S- I Miss her Shekara ɗaya abubuwa su na ta bunƙasa mini, hankalina ya kwanta sosai saboda cigaban da na kawo a ƙauyen mu, idan ka cire koyarwa da na ke wa 'yan primary ba aikin da na ke yi daya wuce noma da kiwo. Ganin na samu nitsuwa ya sa Baffa da Jiji su ka fara kawomin maganar aure da farko wasa na ɗauka sai da su ka dage sosai ya sa na fahimci abin na su ba na wasa ba ne. Jiji har 'yan mata ta ke nuna min na zaɓa, yaran 'yan uwa da na maƙota, su kan nuna min duk ƙauyen ba wanda mu ka taso tare da bai ajiye mace ɗaya ko biyu ba. I was only 26yrs amma gani su ke na yi shekaru arba'in ban yi aure ba. Ganin maganar ta yi yawa ya sa na shirya tafiya ƙaro karatu a hankali na samu gurbi a Jami'ar Oxford, na ƙi Cambridge ne saboda Aaliyah. Cikin ikon Allah na kammala duk wani shirye-shirye na tafiya kuma Alhamdulillah duk wani hidima da gumi na nayi shi. Ana saura sati uku na tafi na yiwa su Baffa maganar tafiyar wanda ƙarara su ka nuna min fushin su domin sun fi so duk inda zan tafi to na tafi tare da mata. Ranan da zan bar Durum zuwa Kano haka Jiji ta dinga kuka tana faɗin "Lamiɗo ka haƙura da Aaliyah, dan Allah kar ka guje mu. Dan Allah ka dawo da wuri ko ba za ka yi aure a Ƙauye ba ka nemi mata ka aura" Na yi ta lallashinta da ƙyar ta dena kuka ta min addu'a sannan na tafi... With everyday that goes by I Miss her. I miss her so much. Karatu ba wahala dan mafiyanci duk research ne. Wata rana wani abokina da mu ke karatu tare ya rasa iyalen sa a hatsarin mota. Musulmi ne ɗan ƙasar Chad, a Birmingham su ka haɗu da matar sa wanda ta hanunsa ta ƙarɓi musulunci. Joey 'yar gudun hijira ce daga Somalia tana aikin karuwanci a Birmingham kafin dalilin abokina Muzaffar ta bar karuwanci sannan ta ƙarɓi musulunci. Aisha Joey da ɗan sa AbdulShakur duka su ka rasu a hatsarin mota. Ni da shi mu ka wuce Watford inda iyalen sa su ke kafin mutuwar na su. Aisha Joey tana da ƙaramin grocery store da Muzaffar ya buɗe ma ta take zama. Shekarun su bakwai da aure ta rasu. Dama Joey ba ta da 'yan uwa sai dai abokai kuma gaskiya an mata shaida mai kyau. Yadda Muzaffar ya rikice da ya ga gawar matar sa da ɗan sa ba ƙaramin tausayin sa na ji ba. Ba ƙaramin so Muzaffar ke wa matar sa ba, sai wanda ke yin soyayya tsakani da Allah zai iya auren tsohuwar karuwa. Na zauna da Muzaffar na kwana uku kafin na shirya komawa dan kar abubuwa su min yawa. BookStore ɗin da na shiga na ke duba littafi na ɗaga Ido na hango ta. Tana tafiya gefenta wata mata tana riƙe da ita. Ina gani su ka tambayi wani littafi inda aka je aka kawo mu su, baƙar matar ta fitar da kuɗi ta biya sannan su ka fita daga shagon. Ina son zuwa na ma ta magana amma ba ni da dalilin hakan. Ga tulelen cikinta da ta ke tafiya da shi da ƙyar ya ƙara tabbatar min da yanzu ba da bane. Na cigaba da duba littafin amma hankalina bai kwanta ba domin ta rame ta lalace, na jingina hakan da cikin da ta ke da shi amma kuma zuciyata ta ƙaryata hakan. Her eyes bears a deep pain, cheerful Aaliyah da na sani ba ita ba ne wannan. Duk yadda na so na daure na kasa haka na fita daga shagon na bi bayan su da sauri dan sun jima da tafiya. Da ke a hankali su ke tafiyar ba a jima ba na iso su. Ina bin su a baya a hankali cike da tausayinta. Komai nata ya chanja har tafiyar ta. Wani garden su ka je inda baƙar matar nan ta taimaka ma ta ta zauna a kujera. Littafin da su ka siya ta fito da shi tana karantawa, tana yi tana shafa cikinta. A nan na ƙyalla ido na kalli zoben da na bata yana nan a hannunta. Abubuwa dayawa su ka fara min yawo a ƙwaƙwalwata, hawaye ma su zafi su ka fara zarya a ido na. Komai da ya faru na dinga gani Aaliyah 'yar ƙaramar yarinyar da na dinga goya a bayana, Aaliyah 'yan mata da muryan ta kaɗai na ji ina shiga wani hali. Yanzu kuma ga Aaliyah matar Ahmad ɗauke da tsohon cikin sa. Ina shirin juyawa ta ɗago kai ta kalle saitin inda na ke, muna haɗa ido ta miƙe zumɓur tana nuna ni, na yi saurin barin wajen ina sawa a raina bai dace ba, kallon matar wani bai dace ba musamman irin kallon da na ke wa Aaliyah. Addinin mu ya hana, Al'adar mu ya hana. Gudu Aaliyah ta fara tana kira suna na amma ban waiwaya ba na cigaba da yin sauri. Ihunta na ji lokacin da ta tsugunna ƙasa tana nishi da ƙyar. Na juya na hangota durƙushe a ƙasa tana kuka. Ba zan iya ganin Aaliyah acikin halin ƙunci na ƙyaleta ba shiyasa na koma da baya. Kafin na isa wajen Matar nan ta Isa gareta tana ƙoƙarin ɗaga ta. Ina zuwa ta kama hannuna ta ce "Hamma Sa'eed" daga nan kuma ta suma... Ni da Mrs Doris Payne mu ka kaita asibiti inda ba a jima ba likitocin su ka ce ina mijinta ya sa hannu dan ba za ta iya haihuwa da kan ta ba. Mrs Doris na kalla ina so ta bada bayani tunda tare na gansu da Aaliyah dole ta san wani abu... Ina hawaye na saka hannu a takardar bayan Mrs Doris ta bayyana min halin da ake ciki. Fatana bai wuce Allah ya sa Aaliyah ta haihu lafiya ba... *22- Baby Zaid* *S* Ina zaune ina addu'a har aka fito mana da jariri, its a boy nurse ɗin ta faɗa. Na ƙarɓi jaririn ina kallon sa, ya ɗauko farin Aaliyah da ƙaramin bakin ta, sai yatsun sa da na ke ganin suma irin na ta ne. Na yiwa yaron huɗuba da Muhammad. Bayan na tabbatar an maida Aaliyah ɗakin hutu sannan na baiwa Mrs Payne yaron na je store na siyo mu su abin buƙata. Har na dawo ba ta farfaɗo ba dan haka na tafi domin nema ma ta mafita, ba zai yiwu ace ta haihu a ƙasar da ba nata ba ace kuma ba kowa na ta a kusa. Numbar Alhaji na nema na kira bai ɗauka ba sai a kira na uku. Ban nuna ma sa ko ni wanene ba na dai sanar da shi halin da Aaliyah ta ke ciki. Ashe Alhajin ma ba lafiya gareshi ba bai jima da dawowa daga ƙasar Egypt ba inda ya kwanta jinya kusan wata ɗaya. Numbar gidan Ahmad sun kira sau iyaka amma ba ta tafiya, jinyar Alhajin ne ma ya sa Amma ba ta taho London ba. Ya min godiya yana tambayar ko ni wanene na kashe kiran ba tareda na bashi amsa ba. Da tsakar dare na koma asibitin inda aka ce min Aaliyah ta farfaɗo amma an mata allurar bacci saboda rikicewa da ta yi. Mrs Payne ta sanar da ni tunda Aaliyah ta farfaɗo ta ke kiran suna na. Na riga na gaya ma ta indai har Aaliyah ta farfaɗo ta tambayeni to tace ba ni ta gani ba wani bature ne ya taimaketa ba ni ba. Washe gari Iyalen Alhaji Tasi'u Wambai su ka zo daga London. Dama sai abu ya tashi ake tuna zumunci. Alhaji Wambai abokin Alhaji Bulama ne tun su na yara kuma a London ya ke da zama. Ganin Aaliyah na hannu mai kyau ya sa na bar garin Watford bayan na yiwa Aaliyah ganin ƙarshe a Asibiti wannan karan ba tareda ta ganni ba... *A* Gaba ɗaya su ka maida ni mahaukaciya lokacin da na ce mu su Sa'eed ne ya kawoni asibiti, Har Mrs Payne ma ƙaryata kwatance na ta yi ta dinga faɗin wani bature ne ba Sa'eed ba. Ta ya zan manta da Sa'eed? Ta ya zan manta da mutumin da na taso da son shi. Ganin sun ƙi kulani hakan ya sa na yi shiru ina ganin su kawai. Kwana na goma na koma Nigeria , Amma ce ta zo min daga Nigeria ita ta zauna da ni a kwana na uku da haihuwa. A Nigeria kowa Allah wadaran ya ke da Ahmad ganin yadda na ƙara lalacewa fiye da da. Baba kam bai iya ce min komai ba, ya jiki kawai ya iya min, kunyata ya ke ji yanzu. Kwana na ishirin da haihuwa aka yi taron suna domin na samu lafiya sosai, yaro na yaci sunan ZAID, Baba ne ya zaɓi sunan saboda sunan ɗan sa na fari kenan da ya rasu a ranan sunan sa, ni ban san da labarin ba ma sai a ranan dan na ɗauka Yaya Bukar ne ɗan fari. Amma da sauran 'yan uwa na kowa ƙoƙarin sa ni farin ciki ya ke. Wata na ɗaya da haihuwa Sanah ta haihu ta samu ɗa namiji, a chan Canada aka yi sunan inda ɗanta ya ci sunan HAFIZ. Ashe su na da labarin an sake Ahmad amma ba su gayamin ba domin Baba ya riga ya rantse Ahmad na fitowa zai sa ya sakeni. A ƙoƙarin Baba na ganin ya raba aurena da Ahmad ne ma ya sa ya biya maƙudan kuɗin da ake bin Ahmad bashi. Ba ƙaramin asara Ahmad yai ba a chachan nan. Hauka ne kawai Hajiya Inna ba ta yi ba lokacin da aka sanar mata abinda Ahmad yai domin abin bai tsaya a kadarorin Alhaji Wamako na ƙasar waje ba har da na gida Nigeria, gashi dama danne hakkin marayu da Inna ta yi ya sa abubuwa sun lalace ma ta, ga uwa uba kuma chachan da Ahmad yai da dukiyar ta su. Idan za ka kasa dukiyar Alhaji Wamako kashi ɗari to kaso tamanin sun tafi a chacha. Ahmad na fita daga prison da ya dawo Nigeria gidan mu ya zo ya fara nema na. Dan ya san zuwa yanzu dole na haihu. Da ya zo hanashi shigowa aka yi amma ya tsaya a compound yana mu su hauka a haka Baba ya shigo gidan ya same shi. Yana fitowa daga mota Ahmad ya nufe shi yana faɗin Baba ya fito ma sa da matar sa da ɗan sa. Baba ya tsinke shi da mari yana faɗin ya bar ma sa gida kafin nan kuma ya ajiye takardar saki na. Ahmad ya ce ba abinda zai yi, shi dai kawai a fito ma sa da matar sa da ɗan sa. Baba ya ma sa tuni da alƙawarin da ya ɗauka kafin a fitar da shi daga prison. Ahmad ya ce bai san zance ba. Takaici ya kama Baba ya sa masu gadi su ka fitar da shi. Baba ya ɗauka abin ya ƙare daga haka, inda ya bari a kan sai Ahmad ya huce takaici na kwana biyu tukunna kafin ya sake waiwayansa da zancen saki na, kwatsam sai ga sammaci daga kotu wai Ahmad na ƙaran Baba. Rashin kunyar Ahmad ta kai yai ƙaran Baba bayan irin halaccin da Baban ya ma sa. Ba wannan ba ma harda maganar wa su kuɗaɗe na Alhaji Wamako da su ke iƙirarin Baba ya cinye. Ranan da aka kawo takardan sai da ciwon Baba ya tashi. Aka kaishi asibiti da gaggawa. A asibitin Ahmad ya zo yana yiwa Baba maganar shi ba komai ya ke so ba irin Matar sa da ɗan sa idan har ya maidoni wajen sa to zai janye ƙaran dama ɗaya tuhumar Inna ce ke yin sa ba shi ba. Baba garin mai da wa Ahmad maganan sa ya ƙara rikicewa da ƙyar aka samu aka stabilizing na shi. Ina zaune a ɗaki ina shayar da Zaid Haruna ya shigo ɗakin yana min masifa akan na san yadda zan yi da Ahmad kafin shi da kan sa ya kashe shi. Duniya kenan shekaru biyu da su ka wuce a ɗakin ya sameni yana zagina kan na ƙi auren Ahmad Wamako sai gashi yau yana maganar zai kashe Ahmad ɗin. Ina shafa kan yaro na na ce " mi yai zafi Haruna? Ka manta Ahmad kyakykyawa ne ɗan Babban gida kuma mai kuɗi?" Shiru yai na wasu daɗiƙai kafin ya ce " ki san yadda za ki yi da mijin ki" Bayan na ji labarin duk abinda ke faruwa ba tareda shawaran kowa ba na shirya kayana da na ɗana na fita. Amma na asibiti shiyasa ban samu matsala ba, dreban gidan mu na samu na ce ya kaini tasha. Kai tsaye Sokoto na nufa duk da kuwa na san yanzu ba asiri ajikina Amma ta ce an warware komai hakanan na daina jin wannan attachment ɗin da na ke ji gameda Ahmad a da. Yanzu zan koma wajen sa ne for peace to reign, ka da dalilina a ci mutuncin Baba. Tausayinsa na ke ji yanzu da ba shi da lafiya, tsoro na ke ji kar baƙin ciki ya kashe shi kamar yadda ya kashe Alhaji Wamako... Gidan dai yana nan yadda ya ke iya ka ci da na shiga ɓangaren mu na samu wasu mutane a ciki ashe Inna ce ta sa 'yan haya. Na ta gidan na je inda ɓangaren Marigayiwa Alaja Atinuke ma an sa 'yan haya a ciki. Lallai Inna ta ga bone. Na ta sashen ma gashinan ga kamarsa, mai aiki ɗaya gareta wata tsohuwa wanda ban san ta a da ba. Tsohuwar ce ta ce min Inna ba ta nan, na ce Ahmad fa ta ce ba ta sani ba amma za ta duba min. Na zauna a falon ina jira yayinda ta fita zuwa sashen Alhaji na da. Zaid na kwance a baya na wanda yai kuka ya gaji acikin mota yai bacci. Har lokacin baccin wahala ya ke yi, ina kallon ɗana wanda tun ranan da na buɗe ido aka nuna min shi na ke jin tsananin son sa, ban damu da tsananin kaman sa da Ahmad ba buri na shine halinsa ya banbanta da na uban sa. Na ɗau alkawarin ɗaura shi a akan tarbiyya mai kyau, zan koya ma sa daraja mace, zan koya ma sa ibada da kuma riƙo da gaskiya. Na tabbata kaso saba'in cikin halayen Ahmad sun samo asali daga Inna ce saboda mummunan tarbiyan da ta ɗaura shi akai. Kaman jira ya ke na kawo shi gidan uban sa kawai ya farka ya fara kuka, na ɗauke shi na sa shi a kafaɗa na ina jijjiga shi dan na bashi nono kafin yai bacci ɗazu a mota. Kamar mahaukaci ya shigo falon a birkice yana ihu. Ya karɓi ɗan sa a hannuna yana jijjiga shi. Na zuba ma sa ido ina ganin yadda ya koma, a zama na da shi ban taɓa ƙare ma sa kallo kamar yau ba. Ahmad ya fige yai wani fayau da shi, jajayen idon sa sun ƙara zama ja. Lallai wahala ba ta yi ba musamman ga wanda ya saba da jin daɗi. " Zaid sunan sa ba" ya faɗa yana kallona Na haɗiye miyau na ce "idan ba ka so sai a chanja" Ya girgiza kai yana faɗin "duk sunan da ki ka sa ina so. Aaliyah ki ga yadda ya ke ta murmushi ya ganni" Ya fara kissing goshin sa yana faɗin "Son ka ga Baban ka ko? I'm sorry ba na nan lokacin da ka zo duniya. Na maka alkawarin zan ba ka duk wani gata a duniya, ba za ka taɓa neman abu ka rasa ba" Ina tunanin ko a ina gatan zai zo ga wanda ya riga ya lalata rayuwar sa. Bayan Zaid ya koma da bacci ya jani zuwa sashen Alhaji shima sashen fayau ya ke abubuwan ƙyaleƙyale da ke gidan a da yanzu duk babu shi ina da yaƙinin siyar wa aka yi. Yana ɗaura Zaid akan gado ya shiga sarrafani yadda ya ke so, jikin sa har rawa ya ke, ƙoƙari ya ke kar ya ga ya min mugunta kamar yadda ya saba amma still sai da na ji zafi, ban sani ba ko dan na riga na sawa raina akan zan ji zafin ne. A ƙasa mu ka yada zango inda na tuna da daren farko na da shi yadda ya raping ɗina a ƙasa wannan ɗin ma duk sammakal tunda ba wai ina so ba ne. Ganin hawaye a ido na ya sa ya rikice yana tambayan dalilin kuka na. "Saboda Baba ki ke kuka ko? Dan Allah ki bar kuka zan janye ƙaran gobe-goben nan. Dama saboda ke ne ya sa na shigar da ƙaran. Wai ki ji Baban ki ya sa na sa hannu akan idan ya fitar da ni a prison zan sake ki. Ta ya zan sake ki? Ta ya zan rabu da ke? Ke kaɗai ce ki ke zaune da ni babu munafurci, ni da ke mutu ka raba" Na rufe ido na ina cigaba da kukan zuci "ni da Ahmad mutu ka raba" abin da ya ce kenan kuma abinda ya farun kenan... *23-Father's death* *A* Sai da na yi kwana biyu tukunna Inna ta dawo, ita ma ta chanja amma ba kamar Ahmad ba. Na ɗauka ganin Zaid zai sa na yi daraja a wajen Inna amma abin ba haka bane. Sam yaron ba ya gabanta, yana kwance a gado ta leƙa shi ta ce "ba ri mu ga ko ɗan shege a kawo mana" Ta ƙura ma sa ido sosai sannan ta ce " saura ka ɗauko farar ƙafar uwarka, dan tunda aka aurota komai ya lalace mana" Ta kalleni ta ce "ke kuma ki gayawa Ubanki ya fitar da kuɗin da ya cinye idan ba haka ba yadda aka kulle Ahmad haka zan sa a kulle ki" Ban yi magana ba sai da na bari ta kusa fita daga ɗakin sai na ce " Alhaji Bulama ba ɗan chacha ba ne, kuma bai ta ke hakkin marayu ba balle bala'i da masifa ta afku ma sa kamar yadda ta afko ga wa su Iyalai marasa tsoron Allah" "Ni Aaliyah ki ke gayawa magana dan Uban ki" Na juyar da kai na gefe. Ta fara zage-zage kamar za ta ci kan ta ko uffan ban ce ba haka ta gama ta fita... Sati na ɗaya a gidan, Ahmad ya zo da murnan sa yana gaya min wai ya janye ƙarar Baba da ya ke yi. A ganinsa yayi abin gwaninta kenan... Amma fushi ta yi dani lokacin da ta dawo ta samu ba na gida, ta kirani ta dinga faɗa tana faɗamin idan na yi haƙuri za a ci galaba akan Ahmad. May be na gaji da komai ne, may be kuma na rufe samun farin ciki a rayuwata shiyasa na dawo ga Uban ɗana. Zaman mu da chanji sosai compared to da, ni da Inna ba ma ga maciji, bayan gaisuwa wanda idan na yi ba ta amsawa, shikenan. She's so busy bin manyan mutane da neman yadda za su farfaɗo daga karayar arziki da ta samesu. Yadda ta ke marar tausayi haka yaranta duka su ka tashi ba sa tausayinta. 'Ya 'Yanta mata duk manyan mutane su ka aura amma kuma duk sun fita harkanta musamman da aka gama batun rabon gado su ka ga tsananin son kai a ciki. Ni na ke shiga kitchen na yiwa kai na girki, ga ɗawainiyar ɗana. Wani lokaci Baaba Gambo mai aikin Hajia na shigowa wajena ta tayani ba ni na sata ba ita ta saka kanta. Tsakanina da 'yan gidan mu sai dai waya amma ba mai zuwa mini kuma ba na zuwa gida. Wata na biyu a gidan Ahmad ya samu aiki, shige da ficen Inna ne yai tasiri sai dai ba a Sokoto ba ne a Abuja ne, dan haka Ahmad ya tattara mu muka koma Abuja da zama. Ahmad ya rage shan giya, dan bai taɓa zuwa gida a buge ba sai dai na kan ji warinta a jikinsa lokaci zuwa lokaci. Duk wata idan aka ma sa albashi haka zai je kasuwa yai ta siyowa Zaid kayan sawa da kayan wasa. Wa su kayan ma ƙila sai ya kai shekara goma kafin ya fara amfani da su amma ba ruwansa haka zai yi ta jibgo su, ban taɓa yi ma sa magana ba na dai zuba ma sa ido. Shekaran mu ɗaya a Abuja Jikin Baba ya tsananta daga Egypt an wuce da shi India daga nan aka miƙa shi ƙasar Germany, rabona da Baba tun da na dawo gidan Ahmad tun lokacin kuma bai sake lafiya ba daga gida sai asibiti haka ake fama da shi duk wasu business ɗin sa Bukar da Haruna ke kula da shi dan Aliyu kam ya zama zauna gari banza karatun ma ya watsar tuntuni. Amma ce ta kirani akan maza-maza na zo gida domin Baba na nemana. Yadda ta ke magana ya sa na san ba lafiya ba dan haka da Ahmad ya zo na ce ma sa zan je gida Baba ba lafiya. "Ni ba na son ki je gidan nan Aaliyah, Baban ki so ya ke ya rabani da ke" Rai na a ɓace na ce "ka san yanada ikon rabani da kai ta ƙarfi idan yana so. I stayed here because i choose to. Ko da ka cigaba da ƙaran Baba a lokacin nan ba galaba za ka ci a kansa ba, ya haƙura ne saboda ni. Idan ba ka barni na tafi ta daɗi ba zan tafi da ƙarfin tsiya and idan na tafi ba zan sake dawowa ba, and there's nothing you can do about it. Ko a da Aaliyah Badamasi Bulama ta fi ƙarfin Ahmad Wamako ƙaddara ne kawai ta riga fata" Yadda na ke maganar sai da ya tsorata, ya jima bai ganni a asalin Aaliyah ta ba. "Kin san dai na chanja ko, duk abinda bakyaso na dena. Idan kika gujeni Hauka zan yi Aaliyah dan sai na yi faɗa da duk wanda ya ke ƙoƙarin raba mu even if it's your father. Ki je gida amma kar ki wuce sati ɗaya" Yana gama faɗin haka ya fita. Na sauke ajiyar zuciya ina kallon Zaid da ke wasa a tsakiyar falon. Buri na Zaid ya banbanta da Uban sa idan ba haka ba na yi asaran haihuwar sa... Ranan da na je gida sosai na yi kuka yadda na ga Baba na ya koma kamar wani miskini. A keke ake turashi baya iya tashi yai tafiya da kan sa. Abu biyu Allah ya sa wa masu kuɗi fargaban sa. Kowa na tsoron rashin lafiya da mutuwa amma attajirai da ma su muƙami sun fi kowa tsoron mutuwa da rashin lafiya. Abu ne da kuɗi ko matsayin mutum ba sa siyan shi. Gashi dai Baba na da kuɗin amma bai iya siyawa kan sa lafiya ba. An je manya-manyan asibitoti da ake ji da su a duniya amma kuma lafiyar ta ƙi samuwa. Jallah Jalaluhu kenan, ya hallaka Fir'auna da ƙaruna wanda har yau tarihi ba ta manta da mulki da dukiya da su ke da shi ba a zamanin su, ƙarfin ikon su bai sa sun kuɓuta daga halaka ba. Likewise Baba ma kuɗin sa bai siya ma sa lafiya ba. Wannan kaɗai ya isa ya nuna mana cewa dukkan mu ɗaya muke a wajen Allah amma har wayau maikuɗi gani ya ke ya fi talaka. Zaid na ɗaura wa Baba a hannunsa bayan ya buƙaci hakan. Yaron sai dariya ya ke lokacin da Baba ke ma sa wasa. "He smiles just like you Aaliyah. Allah ya ma sa albarka" na amsa da amin. "Dr Sa'eed da Baffan sa sun zo sun gaisheni" na ɗago ido na kalleshi yana shafa kan Zaid idon sa ɗauke da dana sani bisa ƙaddara da ta riga fata. Ya cigaba "ya kammala Phd ɗin sa a Oxford kwanakin baya. He's going to be a successful man. Ban taɓa ɗauka soyayyar da na ke miki shi zai sa na tura ki ga rayuwar ƙunci ba. Allah ya jiƙan rai Alhaji Wamako mutumin ƙwarai ne, yana ɗaya daga cikin mutanen da zan iya rantsewa akan iya tsawon rayuwar su ba su yi neme-nemen mata ba kuma ba sa shan barasa. na ɗauka haɗa zuri'a da shi zai ƙarfafa zumuncin mu sannan ya haɗe kan mu har ƙarshen rayuwar mu, na ɗauka dukiyoyin mu za su haɓaka sunan mu zai sake bazuwa a duniya. A yau son zuciya ta sa ni a jirgin da na sani, Aaliyah ki yi haƙuri ki yafe min"... hawaye ya fara zubo ma sa. It was the first and last time dana ga hawaye a idon Baba. Nima ɗin kuka na ke yi domin ambaton Sa'eed da yai ya taɓomin da wani tsohon ciwo a zuciyata... Sati ɗaya da na yi kullum ina tare da Baba, ya kan yawan faɗamin na yafe ma sa bayan na riga na yafe ma sa har zuciyata. Nawa mijin ko kiran Baba ya gaisheshi bai yi ba balle ya zo. Jikin Baba da ɗan sauƙi amma kuma ba ya fita. Ranan da zan koma a jirgi aka maida ni Abuja wanda Baba ne ya biya. Ina cikin jirgi ina riƙe da ɗana yayinda maganganun Baba na ƙarshe su ke min kama da wasiyya. Takardu ya damƙa mini sannan ya bayyana mini kyauta ce ya min tun lokacin da na haihu. Shares ne na wani kamfani a ƙasar waje, yadda Ahmad yai wasa da dukiyar Uban sa ya salwantar da shi a chacha shiyasa Baba yai gudun samun matsala idan baya nan. Duk da akwai zaman lafiya tsakanin Hajia da Amma sai dai abinda ba a rasa ba amma kuma sha'ani na gado sai a hankali. "Ban kai ki gidan da za ki ji daɗi ba amma kuma ba zan bari ki tsiyace ba saboda Ahmad. Aaliyah ke 'yar gata ce" i wish 'yar gatan da ya ke faɗi ba kuɗi ba ne, i wish 'yar gatan da ya ke nufi shine amincewa da soyayyar Sa'eed a lokacin da na nuna duk duniya babu wanda na ke so kamar sa. Ban so karɓar wani abu na shi ba amma ya nuna idan ban karɓa ba kamar ban yafe ma sa bane... Tunda na koma Abuja kullum sai na kira Baba mun gaisa, wani lokaci har ya ce na bawa Zaid su gaisa. Zaid yai ta ma sa shirmensa na yara. Sati uku da dawowa na Muhammad ƙanina ya kirani yana kuka yana sanar da ni Baba ya rasu. Shock ɗin da ya kama ni haka na sake tarho ɗin ta faɗi ƙasa .... Ahmad baya nan dan haka na ɗau ɗana mu ka wuce Maiduguri a ranan. Mai gadi na barwa saƙo ya ajiyewa Ahmad idan ya dawo. Wato matsalar gado musamman ga mai arziƙi masifa ce. Duk wani haɗin kai da zaman lafiya maganar gado ta wargaza komai. Ana sadakan bakwai aka fara batun rabon gado. Abin da ya sa na tuna da rasuwan Alhaji Wamako kenan. Mu biyar ne a wajen Amma kuma ni kaɗai ce mace. Hajia na da 'ya 'ya bakwai mata uku maza huɗu ban ga abin tashin hankali ba amma da aka fara ƙananun maganganu akan dukiya abin bai tsaya anan ba sai da aka fara batun maganar hannun jari da Baba ya siya min. Haruna da Anty Falmata su suka fara maganar wai dole a raba gado da shi tunda dai Baba ya rasu. Ni ban san ya aka yi su ka san da zancen ba ma. Magana ta kai aka kira lawyer da malamai wanda su ka tabbatar wannan hannun jari ba ya cikin gado. Fiye da shekara ɗaya da ya wuce ya sayi shares ɗin kuma da sunana ya siya, sannan kuma kyautar sa ya min tun alokacin. A duk tarin dukiyar Baba bai isa ba sai an sa ido a kyautar da ya min. Gani su ke tamkar rabin dukiyar sa ya raba ya bani bayan ba haka bane. Idan ka cire Sanah da Aliyu wanda shaye-shaye ne gaban sa duk sauran haushi na su ke ji. Ganin abin zai zama matsala na cire kai na a cikin gado na ce na yafe. Ai kuwa nan ma ban tsira ba haka aka fara zargin wai bayan hannun jarin da Baba ya siya akwai wasu kyautan da na ke ɓoyewa ne. Sati na biyu a gida na koma Abuja yadda maganar gado ke kawo kace- nace ne ya sa na bar gidan na dawo gidan Ahmad. Ahmad ya san da mutuwar Baba amma kuma bai zo ba haka bai kira ya gaishe ni ba. He's too busy da sabon party da su ka buɗe. Inna ce ta tunzura shi ya shiga harkan siyasa. Ni dai na zuba mu su ido, tunda dukkan su biyu ba su yiwa kan su karatun ta nitsu ba... *24- Unrequited love* Zaid na shekara ɗaya da rabi na yayeshi. Kullum addu'ata shine Allah ya inganta rayuwar sa ya rabashi da munanan hali irin na uban sa. While Ahmad is busy ni kam na samu kwanciyar hankali ba zan ce farin ciki ba sai dai kwanciyar hankali tunda duk abinda ke ɗaga min hankali a da kusan kaso saba'in babu su yanzu. Zaman gidan ya isheni, kullum ba inda na ke zuwa daga gida sai gida, ni da ɗana mu ke rayuwar mu mai daɗi. Ahmad bai cika zaman gida ba ƙoƙarin ɗabbaka partyn su su ke. Watarana Zaid na shekara biyu da rabi Ahmad ya fara maganar sa shi a makaranta. Alhamdulillah yaron nawa Allah ya bashi kwanya, yadda na dedicating dukkan lokacina gareshi ya sa ƙwaƙwalwarsa ta ƙara buɗewa da sauri. Maganar ƙasar waje Ahmad ya min wanda ya sa na kalleshi da mamaki. "So ka ke na tura yarona chan wata duniya yai rayuwa shi kaɗai?" Dariya yai ya kamo hannuna ya ce "haba Mommyn Zaid ai ko hauka na ke ba zan bar Zaid yai rayuwar kaɗaici ba. You see, Na yiwa Zaid alƙawarin inganta rayuwar sa so dole na fara ta ɓangaren Ilimi. Dukkan mu za mu koma amma ni zan dinga sintiri tsakanin Nigeria da London" Na zaro ido na ce "London?" "Yes Aaliyah, a inda aka ɓata min suna haka zalika a nan zan gyara sunana. I will exact revenge on Pedro Santiago" Ni dai kawai na buɗe baki ina binsa da kallo saboda rashin hankali ƙarara da na gani a wajen Ahmad. Wato abinda Don Pedro ya ma sa bai daddara ba. Abinda ban sani ba shine Ahmad ya yi nisa. Inna ta shigar da shi inda zai kaishi ga halaka, a lokacin revenge ne kawai a ransa shiyasa bai damu da abinda ka iya biyowa ba. For the second time mu ka tattare mu ka koma London, gidan da ya siya bai kai gidan Alhaji na da ba amma shima ba laifi yana da kyau. A ka saka Zaid a kindergarten yayinda ni kuma na koma abinda na saba wato zaman gida. Wata rana mu ka yi waya da Sanah ta ke gayamin ta fara masters na ta a chan Canada na tayata murna sai alokacin ta ce mi zai hana nima na koma karatu ko kuma na nemi aiki. Na yi shiru dan ban san ya Ahmad zai ɗauki maganar ba. Bayan mun gama maganar na zauna ina juya maganar a raina tabbas makaranta ko aiki zai rage min kaɗaici. Amma Ahmad zai yadda?... Bayan kwana uku da Ahmad ya zo na jarraba yi ma sa maganar to my surprise sai ya ce " idan aiki ki ke so za ki samu idan ma kuma makaranta ne za ki samu, Ahmad ɗin yanzu ba na da bane" Ya kissing goshina ya ce " ba abinda ba zan iya yi miki ba. I love you Aaliyah, daga yanzu komai ki ke so shi zan yi" Wani lokaci Allah ya kan jarrabci mutum da son wani abu da ada ya ƙi shi. Allah ya jarrabci Ahmad da so na, a da bai fahimta ba amma yanzu ya gane cewa xuciyar sa na tsananin son Aaliyah... Bamu yi sati uku da maganar ba ya sama min aiki a BBC sashen turanci. Aiki ya sa duk wani depression da ke tareda ni ya warware. Ni ina fama da aiki shi kuma Ahmad yana ƙara cusa kan sa cikin baƙar rayuwa. Da ƙarfin tsafi Ahmad ya ga bayan Don Pedro, bayan ya ƙwace ragamar harkokinsa. Ahmad was now a Mafia Boss, sai yai wata ɗaya biyu bai zo ya ganmu ba amma kuma kullum sai ya kira musamman dan ya gaisa da ɗan sa. Within one year sunan Ahmad Wamako yai tashe a duniya. Haka kuma rayuwarmu ta koma cikin hatsari. Bodyguards ke tsarona da kuma ɗa na. Gida da wajen aiki duk sai bodyguards sun rakani. Tun ina tsoro har na haƙura na koma addu'a kawai. Ina jin maganganu dayawa akan Ahmad kuma nima ina karanta labaransa a gidan radio, amma ya zan yi Ahmad ya fi ƙarfi na. Shekaru huɗu mu ka yi Ahmad na cin karensa ba babbaka until komai ya fara lalacewa. Mu baƙaƙen fata mu kan ɗauka turawa ba sa asiri ko magani to ƙarya ne. Alberto ƙanin Don Pedro da Ahmad yai sanadiyar mutuwar sa da kuma Cataliya 'yar sa, cikin shekarun nan sun shiga sun fita domin su ga bayan Ahmad and they took away everything da ya building a shekarun nan. Not only that sun attempting kashe shi amma ya tsira da ƙyar, bullet biyu aka ma sa but he survives it. Ni ne na fara jinyar sa da ga baya Inna ta taho daga Nigeria, ganin zaman mu ba zai yiwu ba na bar ma ta jinyar sa na koma bakin aikina. Ranan daga office da na dawo gida sai ga Cataliya a gidan mu. Yanzu ba mu da bodyguards tunda ta ƙarewa Ahmad. Kashe ni ta zo yi da ni da Zaid saboda ta huce takaicin Ahmad amma ba ta iya yin komai ba. Ƙwayoyin da ta ke sha sun gaya ma ta dai-dai. "I wanted to kill you" ta yi dariya tana bubbuga bindiga a kanta. "But then i pity you. Your more miserable than i am" "Why didnt you leave him?" "Please dont hurt my son" na faɗa a hankali. Ta tako wajena ta sa bindiga a goshina tana shirin harbi sai kuma ta fasa tana dariya ta ce "you're a good person i like you" tundaga wannan rana Cataliya ta fita daga rayuwar mu. Bayan an sallami Ahmad Inna ta ce sai dai ya koma Nigeria. Ba shi da wani abin kirki duk abinda ya samu sanadiyar Don Pedro babu shi dama da dukiyar sa ya ke burga dukiyar chacha dukiyar da aka samu ta hanyoyi marasa kyau. Na fara jin daɗin aikina dan haka ban shirya tafiya ba na ce wa Ahmad ba zan koma Nigeria ba. Inna ta kalleshi tana jiran ya min magana sai ya ce " duk abinda ki ke so shi na ke so Aaliyah" Inna ta zaro ido ta ce "na shiga uku yaushe kika shanye ɗana?"... Na cigaba da aiki da BBC English daga baya sashen BBC Hausa su ka nemi na dawo wajen su na kuma amince. Ban san wata tsiyar Ahmad da mahaifiyar sa ke kimtsawa a Nigeria ba tunda ba sa taredani ban damu ba. Tafiyar su da wata uku aka buƙaci kuɗin makarantan Zaid inda sai a nan na san ba ƙaramin maƙudan kuɗi Ahmad ke biya ma sa. Albashina da na ke tarawa dana cire na biya sai ga shi abin da ya rage ba wani auki gashi yanzu ni ke ciyar da mu. A sannan ne na tuna da hannun jari na wanda tun lokacin ban taɓa waiwayansa ba. Da na contacting kamfanin kan maganar kuɗaɗe na sai gashi su na min maganan miliyoyin dollars. A America kamfanin ya ke kuma a shekaru shida kamfanin ta bunƙasa sosai. Na buƙaci cikin kuɗin su turamin rabi zuwa account ɗina. Hutun da na samu ƙarshen shekara na ɗau Zaid mu ka wuce Nigeria. A Abuja Ahmad ya ke yamzu har ma da Inna, ƙoƙarin tada ɗan nata ta ke ta kowanni hanya. Ranan da na zo gidan kamar ya zuba ruwa a ƙasa ya sha saboda farin ciki. He's been depressed saboda yadda al'amura su ka juya ma sa... Da dare na nemi jarrabashi for the last time ko akwai gyara a lamarin sa. "Ahmad dan Allah ka haƙura da neman kuɗi ta mummunan hanya. Bala'i ka ke jawowa kan ka. Ba na so Allah ya jarrabi Zaid dalilin haƙƙin mutane da ka ke ɗauka" " i want to give you a good life ba na so ki dinga cewa Aaliyah ta fi ƙarfin Ahmad ɗin nan. I know i fucked up but please dont leave me. Zan iya yin komai a kan ki Aaliyah, yanzu haka an bani appointment kin san ɗaya daga cikin party member na mu ya zama Minister" "Ahmad kasuwanci ka karanta and ka fita da first class. Lokacin da ka shugabanci Casinon Don Pedro ka bunƙasa shi sosai saboda ka na da ilimin kasuwanci. Ka yi amfani da iliminka ka yi kasuwanci ta halal sai ka ga Allah ya albarkace shi" Yai shiru yana nazarin maganganuna. Ni na san Ahmad ya fara chanjawa amma Inna ce remote control ɗin sa, duk lokacin da ka ga ya chanja Inna ce ta juya shi. "Ba mu da komai Aaliyah, everything is gone. Duk abinda ki ke gani yanzu ko dai bashi ne ko kuma Hajia ce ta yi roƙo ta samu" "Idan na baka jari za ka yi kasuwanci na halal?" "Idan ki ka yi alkawarin ba za ki rabu da ni ba" ... *** Ahmad start a fresh, kuɗin da na bashi ya fara jujjuyawa and things were Improving, i stayed in London with my son. Ni na ke mana komai saboda bayan albashina ina amfani da kuɗin da na ke samu ta hannun jarin da Baba ya siya min. Ahmad na zuwa duba mu duk bayan wata biyu hakan ya sa na samu kwanciyar hankali sosai. Two years bayan na bashi kuɗi abubuwa su ka fara haɓaka ma sa na sake zuba jari a kamfanin da ya buɗe dan na taimaka ma sa kamfanin ta bunƙasa. Abu ɗaya da ke damuna shine yadda duk lokacin da Ahmad ya zo London ya ke takurani, shi a dole nuna min so ya ke, haka zai kai ni date akan date ko kuma mu je cinema kallo, ko wajen shaƙatawa. Da dare kuma ya daddage akan sai ya sanyani farinciki. Yes ya dena yi min da ƙarfi, yes ya dena duka na amma kuma ban iya sake jiki da shi ba. Duk abinda ya ke yi Allah Allah na ke yi ya gama ya tashi shi kuma duk abinda ake yi mace ta ji daɗi haka zai daddage ya dinga mini. Ko gizau ba zan yi ba, baya gane ina jin daɗi ne ko ba na jin daɗi. Wani lokaci kuma sai dai na fara hawaye, all the years of not enjoying sex ba zai tafi ba lokaci guda. Wani dare daya gama abinda zai yi ya tashi sai ya ce "Allah ya sa ajiyana ta zauna. Its high time Zaid ya samu ƙani ko ƙanwa. Kai na ma fi son Mace domin ta ɗauko irin kyaun ki, i'm going to treat her like a princess" Ganin na yi shiru ya sa ya kalleni ya ce "idan namiji ki ke so its ok nima ina so"... Wannan karan maimakon Sati ɗaya da ya ke yi sati biyu yai tare da mu duk wai dan na samu ciki... Inna ganin abubuwa sun fara zama ma sa ya sa ta bijiro ma sa da zancen ƙara aure. Yai ma ta biris akan ba zai yi ba, ganin Ahmad ya yi nisa a soyayyata ya sa ta shiga haɗa mu. Ta dinga zuga shi akan ba na son shi shiyasa na zaɓi zaman London akan zama kusa da shi da ta ga abin bai shigeshi ba sai ta fara zuga shi akan ya duba Zaid ya kusa cika shekara takwas amma kuma na ƙi haihuwa ta dinga rantse ma sa akan ni ne na tsaida haihuwan dan ba na son shi, wannan maganar ne ta shige shi ba shiri ya taho wajen mu. Da dare ya shigo London, lokacin da ya shigo gida na jima da bacci ba. Yau na karanta labari akan Dr Sa'eed Aliyu Modibbo, tun a studio yanayina ya chanja domin ya taɓomin da tabon da ke zuciyata. Na dawo gida na rasa gane kai na, ranan kuma Zaid yai ta damuna akan maganar birthday party da na yi alƙawarin zan haɗa ma sa. Da ƙyar na lallaɓashi har yai bacci. Da na shiga ɗaki na ɗauko jakar da na jima ina adana ta saboda mahimmancinta a rayuwata. Hotunan mu na ɗauko ina kallo, zuciyata kamar za ta fito saboda tuna baya da na yi. Kuka na saka ina godewa Allah bisa ni'imominsa gareni. Ina kwance ina hawaye bacci ya sace ni ban far ka sai da na ji ƙaran fashewar glass. Na tashi a firgice, Ahmad na gani tsaye yana huci. Jakar da ke gefena yai wulli da ita ta bugi mirror da ke ɗakin shine mirror ɗin ya fashe. "Ahmad lafiya?" " ina son ki Aaliyah, i've changed because of you. Inna was right after all ba kya so na shiyasa ba kya son haihuwa da ni. You're planning to leave me ko?" Ya faɗa yana jawo gashina da ƙarfi. "Miyasa ba za ki manta da shi ba? Miyasa ba za ki soni ba?" "Ahmad you're hurting me" na faɗa da ƙarfi. A ƙoƙarin da na ke na ƙwace kai na daga riƙon da ya mini idon sa ya kai ga zoben da ke hannuna. Wani mahaukacin dariya ya saka sannan ya fizgo hannuna ya ce "wannan ma shi ya baki ko?" Na girgiza kai ina hawaye na ma rasa abin faɗa. "Kina da hotunan sa kina sanye da zobensa all this years kin maidani mahaukaci kenan. Is that why duk ƙoƙarina a kan ki ba kya gani? Is that why duk yadda zan jajirce na gamsar da ke ba kya jin daɗi na?" Ya fara ƙoƙarin cire zoben a hannuna amma ya ƙi fita. "Sai ka fita dan Uban ka" ya faɗa yana jawo ni daga kan gado. Jana ya dinga yi har kitchen, na ɗauka sabulu zai nema ya sa min a hannu but ba haka ba ne. Gas ya kunna ya sa wuƙa a wuta ta yi ja. "Ahmad ka bari na sa sabulu zai fita, please" Ahmad bai ji magiya na ba, all he knows shine da auren sa na ke dakon son wani namiji. Haka ya sa wuƙan nan akan zoben hannuna sai da ta rabe ta sama ya sa ta ƙasan ma sai ga zoben ya faɗi ƙasa. Bai damu da ƙunar da yatsana ta yi ba ya jani muka koma ɗaki. Hotunan mu ni da Sa'eed da kuma Jakar nan ya ɗauka zai je ya ƙona na riƙe ƙafar sa ina kuka. "Ahmad please kar ka ƙona, na yi alƙawarin indai kana nan ba zan sake dubawa ba but please kar ka ƙona" ya tureni gefe ya fita. Na dinga kiran sa ina kuka amma bai kulani ba. Mace kenan, rana ɗaya da na tuna da masoyina ya ɗaga ma sa hankali, ya manta da shi lokutan da ya ke harka da matan sa na banza. Amma shi namiji ne Its OK... Washegari Ahmad ya ɗau Zaid yai tafiyar sa ban san inda ya kai min ɗana ba. Na yi kiran na yi roƙon amma ba ruwan sa cewa yai kafin ya dawo min da Zaid sai dai idan wani cikin na samu. Ahmad bai min da wasa ba domin kusan wata huɗu ba Zaid ba dalilinsa na yi neman duniyan nan na rasa inda ya kai shi ƙarshe na haƙura na fara nemawa kaina mafita. Asibiti na je su ka duba ni kan maganar haihuwa su ka tabbatar min da lafiyana ƙalau zan iya ɗaukan ciki a kowani lokaci. Dukkan asibitin da na je zancen ɗaya ne ina da lafiya. Wannan fushi da Ahmad yai ya sa Inna ta samu kan sa yai aure. Shi anashi tsarin gana ganin idan ya ƙara aure zan ji haushi na lallaɓeshi na so shi kamar yadda ya ke buƙata, amma ni babban damuwana ɗana ne. Shekara ɗaya na yi ina kewar ɗana ba tareda na ganshi ba. Bikin ƙanina ya taso inda abin mamaki Ahmad da kan sa ya ce na halarci bikin. Na shirya na je dan dama na kwana biyu rabona da Nigeria. Ranan ɗaurin aure bayan an taso daga wajen ɗaurin aure sai ga Kalim ya shigo sashen mu riƙe da Zaid. Ina ɗaki na jiyo muryan Salma wata cousin ɗina tana tambayar Zaid ko shi da wa ya zo ya ce da shi da Dad ɗin sa. Ina jin muryan ɗana na fito daga ɗaki da gudu. "Zaid" na faɗa ina nufo wajen shi yaro na ya koma bayan Kalim yana ɓuya. "Zaid come to Mommy" na faɗa muryata a raunace. "Stay away from me" ɗa na ɗan shekara tara ya faɗa da ƙarfi. Na tsugunna a wajen ina magiya kamar ƙaramar yarinya Kalim da Salma na cewa ya zo wajena ya girgiza kai ya fice daga falon da gudu. Na san sharrin Ahmad ne shi ya ke son ɗasa ƙiyayyata a zuciyar ɗana. Ba shiri na bi bayan Zaid amma ban ganshi ba, a taƙaice haka Ahmad ya koma da Zaid ba tareda na sake saka shi a ido ba. Daga Maiduguri Abuja na wuce dan na sake bawa Ahmad haƙuri a nan na ga Amarya Fatima na zaune da tsohon cikinta. Inna kuma tana nan ta ƙara murjewa saboda yanzu Ahmad ya samu dukiya gashi jam'iyyar da su ka kafa ta yi suna ana damawa da su a gwamnati. Zancen dai ɗaya ne, na ajiye aikina na dawo Nigeria na zauna da shi na samu ciki na haihu. Ban shirya zama da Inna ba, ban shirya wani kayan takaicin ba shiyasa na zaɓi komawa London after all na san ko ba daɗe ko ba jima zan gano ƙasar da ya kai min ɗana... *** *S- a wife* Bayan na ƙare Phd ɗina Jami'ar Oxford su ka bani aikin koyarwa, saboda ba na son komawa Nigeria ya sa na karɓi aikin. Tunda na rabu da Aaliyah a asibiti na ke ƙoƙarin yaƙi da zuciyata akan ma manta da soyayyarta amma abin bai yiwu ba. A hankali na dinga bibiyar rayuwarta dan na tabbatar tana cikin kwanciyar hankali. Na san komai gameda komawarta gidan Ahmad zuwa rasuwan mahaifinta har ta kai ga sun koma London a karo na biyu. Ranan da na samu nitsuwa a raina shine ranan da aka fara ɗaura shirinta a gidan radiyon BBC. Ina jin muryan na gane Aaliyah ce da ke na zo na tarar an yi nisa da shirin. Na baza kunne har ta kai ƙarshen shirin na ta inda ta bayyana sunanta cikin muryanta mai zaƙi. Tun daga ranan shirin da Aaliyah ke yi bai taɓa wuce ni ba. For years wannan murya ke sani nishaɗi sau ɗaya na ke zuwa Nigeria na yi sati biyu kuma koyaushe na je da fushin Jiji zan dawo akan na ƙi aure. Kullum haƙuri na ke badawa ina ganin lokaci ne bai yi ba. Wasa-wasa har shekaru su ka ja. Zuwana gida a ƙarshen shekara kaman yadda na saba na tarar da Baffa yana kwance yana jinya. Baffa ya dinga magiyar akan na yi aure saboda kar ya mutu Allah ya tambayeshi hakkina da ke kan shi. Duk yadda na so bijire ma abin ban iya ba dole na amince da maganar Baffa. Kafin sati aka aura min aure da 'yar uwata Halimatus Sadiya, sai dai yarinya ce dan shekaranta sha shida a lokacin. Saboda jinyar Baffa sai da na ƙara sati kafin na koma UK bayan na ga jikin Baffa ya fara sauƙi. A hankali na sa aka fara yiwa Halima visa dan idan na dawo wani zuwan sai na tafi da ita. Watana biyu da barin Nigeria Allah yaiwa Baffa Manu rasuwa. Rasuwan nan ta girgiza ni matuƙa ba shiri na sake zuwa Nigeria. Nasihohin Baffa kafin ya rasu da ya min gameda Halima ya sa na speeding process ɗin Visan ta. Ko da dai ba na sonta yanzu, zan yi ƙoƙari na koyawa kai na sonta a matsayinta na matata. Ban koma UK ba sai da Halimah inda a nan ne na angonce da ita bayan ta cika shekara goma shabakwai a duniya kuma watanmu bakwai kenan da aure. Halimah yarinya ce, akwai ƙuruciya a tattare da ita ta yi primary sannan ta zana JCE daga nan ba ta cigaba ba saboda yadda ba a damu da karatun mace a Ƙauye ba. Biyayyar da ta ke min ya sa na ke yawan jin tausayinta na ke kuma ƙoƙarin sauke hakkokinta da ke kaina... *25-Senator Ahmad Wamako* *A* Duk wani musulmi na ƙwarai ya yarda da cewa yiwa Iyaye biyayya shi ne zai zama ma tsani zuwa Aljannah. Amma yadda ake samun ƙangararrun 'ya'ya haka ma akwai iyaye da su ke tantirai 'yan duniya. Ahmad bai yi sa'ar uwa ta gari ba. Bai gane hakan ba sai da ya ɓata tsawon rayuwar sa yana yiwa ƙiɗanta rawa. Ahmad yana so na sosai na sani, kuma nima shekaru da su ka ja da kuma umurnin Allah ya sa na danne duk wani son Sa'eed da na ke na rufe shi a chan ƙasar zuciyata, na dinga ƙoƙarin sauke ma sa hakkin sa da ke kaina. Shekara ɗaya biyu uku... shiru ba haihuwa, tun ina neman haihuwan saboda na samu Ahmad ya dawo min da Zaid har na koma ina nema ne saboda ina son samun wasu 'ya'yan, musamman 'ya mace. Sai dai Allah ya riga ya rubuta ɗa ɗaya zan haifa a rayuwata. Ganin ko ɓatan wata ban taɓa yi ba ya sa na haƙura da maganar haihuwa na cigaba da yiwa Zaid addu'a saboda yai rayuwa mai albarka ya kuma tsira da duniya lafiya. Afterall Allah ya bani ɗa ɗaya, wasu ido rufe su ke neman haihuwan amma har su koma ga mahaliccin su ba za su taɓa haihuwa ba. Jalla Jalaluhu kenan wanda ya ce zai ba wa su 'ya'ya maza zalla wasu kuma mata zallah sannan wasu ya basu maza da mata, wa su kuma ya jarrabesu da rashin haihuwa. Alhamdulillah tunda atleast ina da Zaid kuma yana nan cikin ƙoshin lafiya... Bayan na bawa Ahmad Jari duk wani kadara da dukiya da na mallaka na maida shi sunan ɗana Zaid. A cikin 'ya 'yan Baban mu wanda su ka wawuri gado lokacin da aka raba dukansu ba wanda zai nuna min wani abu domin Allah ya sa albarka a kasuwancina. Duk inda na zuba hannun jari sai ka ga kasuwancin wajen yana haɓaka. Ƙanina Muhammad shi ne ya ke min wakilci a dukkan harkokin kasuwanci na. Ni kam Aaliyah Badamasi Bulama ma'akaciyar gidan radiyo ce, aikine da na ke jin daɗin sa ya ke ɗebe min kewa. Ni da aka dinga yiwa gori a baya sai na zama a duk familyn mu su na mugun respecting ɗina saboda ban taɓa tambayar wani kuɗi ko wani alfarma ba. Duk cikin 'ya'yan Hajia Yana babu wanda ban taimakawa ba one way or the other. Lokacin da business ɗin Anty Falmata ya durƙushe aka yi family meetimg ana neman gudumawa. Duk cikin 'yan uwanta da su ke uwa ɗaya babu wanda ya ma ta kyautar da na mata. Miliyan Goma na tura ma ta wanda duk gudumawan da aka haɗa mata bai kai miliyan uku ba. Haka ta kirani tana kuka tana godiya saboda lokacin da ake maganar rabon gado tana cikin wanda su ka dinga ɗaga jijiyar wuya akan kyautar da Baba ya min. Kowani gida da nashi matsalar. Yayinda nima na ke fama da Ahmad ita Anty Falmata mijinta shekarun baya gwamnatin Nigeria ta kama shi dumu-dumu da almundahana da kuma illegal business ciki harda human trafficking, ana tattare yara mata ana siyar da su a ƙasashen waje karuwanci ko aikatau. Da aka fara sintirin case ɗin ne zuciyar mijinta Alhaji Musa ya buga ya mutu ya barsu da takaici. Duk dukiyar sa aka kwashe aka bar iyalensa da cizon yatsa. Matansa uku kuma Anty Falmata ce ta biyu tana da yara biyar, business ɗin da ta ke yi shima abubuwa su ka kwaɓe ma ta bayan an damfareta maƙudan kuɗaɗe. A 'ya'yan Alhaji Badamasi Bulama na zamo tauraruwa. Ba zan iya irga iya 'yan uwana nawa na taimakawa ba. Na sponsoring karatun dayawa daga cikin 'ya'yan yayuna da cousins ɗina... *** Ina kitchen ina yanka cabbage a chopping board na ji ƙanshin turaren Ahmad. Dama ba ya sanar da ni idan zai zo sai dai kawai na ganshi, watarana ma studio zai je ya jirani ina fitowa sai dai kawai na ganshi. "Sannu da zuwa, ya hanya" na faɗa ba tareda na juya ba. Ya ƙariso ya rungumeni ta baya ya ce "yaushe za ki yi ƙiba ne wai Aaliyah. Kinga Fatima yadda ta dawo yanzu kuwa, ko a haihuwan Nusrat sai da ta sha wahala" "Ashe an samu ƙaruwa, Allah ya raya Amin" Ya matseni jikinsa sosai yana faɗin " ba ke ƙin ki haihuwa da ni ba" Hawaye ne ya fara zubo min, wai na ƙi haihuwa. Why is the world so cruel? A duk lokacin da aka samu ma'aurata biyu suna zaune Allah bai ba su haihuwa ba to laifin na macen ne. Haka za a dinga cewa har yanzu shiru kamar ita ke rabon 'ya 'ya. Kafin a fara zargin mijin sai dai idan ita macen ta taɓa haihuwa a wani wajen ne amma ko sau dubu malaman asibiti za su ce macen ba ta da matsala to duniya ba za ta yarda ba, ita ɗin dai za a ɗaurawa laifi. Na zare jikina daga nashi na juyo na kalli ƙwayar idon sa na ce "Zaid is the only thing that is keeping this marriage Ahmad. Ka sani back then da ban samu cikin Zaid ba da ba abinda zai hana na rabu da kai especially when my parents supported me. Tunda na samu cikin Zaid to this day, i tolerated everything for him. But what did you do? ka raba ni da ɗana for good 10yrs. Ba na jin muryan sa ba na ganin sa. Duk burina na bashi tarbiyya mai kyau ka ruguza min shi, ka san yadda na ke ji a raina? Ka sani? Ka san yadda na ke kwana in tashi da kewar sa a raina? Ka san yadda na ke ji cewa ina raye amma ban san inda ɗana ya ke ba? Ka san yadda na ji alokacin bikin Munnirah da na ga an ɗaura hoton Zaid a wajen biki a Facebook, ka san awa nawa na yi ina kallon hoton ɗa na a ranan? Ka san na bi Zaid a facebook na faɗa ma sa ko ni wacece ya blocking ɗina?, ka san an turomin numban Zaid na kirashi ya ce kar na ƙara kiran sa ya tsaneni, ɗan da na yi ɗawainiya da shi tun yana ciki har ya fito ya ke cewa ya tsaneni. Wani irin punishment ne Ahmad za ka raba ni da ɗana?. Ahmad da ni na ke bawa kaina haihuwa da tuni na haihu dan ka dawo min da Zaid. I am alone here and you took the only Joy i have in this world. You took everything from me, everything Ahmad" Na dafe ƙirjina da ke zafi yana bugawa kamar zai fito ina haki. Idan na cigaba da magana zuciyata za ta fashe. Ahmad ya tsaya a wajen kaman gunki, hannun sa na rawa ya dafa kafaɗa na. Muryarsa na rawa ya ce "ina cikin ƙunci Aaliyah, rayuwata tana cikin ƙunci. Ina son ki sosai, ina tsananin kishin ki, koyaushe na tuna ba na cikin zuciyar ki sai na ji gara na ƙunsa miki baƙin ciki ko za ki daina tunawa da shi. May be ban san yadda ake soyayya ba amma kin sani ina son ki sosai kuma da kin bani wani matsayi a zuciyar ki ko da kaɗan ne da zan ji daɗi sosai. But it hurts me to always think that ba ni da matsayi a wajen ki daya wuce uban ɗan ki. Na sani taking Zaid away from you was selfish but hankalina ya kwanta knowing tunanin Zaid za ki dinga yi ba na wani namijin ba" Maganganunsa ya sa na ji kaina ya fara sarawa. Na ture hannunsa daga jikina zan fice daga kitchen ɗin ya riƙe hannuna. "I'm sorry Aaliyah. I'm really sorry. Dama na zo na kai ki wajen Zaid ne, jibi ne convocation na su. Your son is a graduate" "Allah ya ma sa albarka Amin" na faɗa na fice daga kitchen ɗin Ina shiga ɗaki Ahmad ya shigo, har ƙasa ya tsugunna yana bani haƙuri. Ni mace ce, I'm not supposed to be angry with my husband, ko na yi fushin ma, ba abinda zai chanja, auren shekara ashirin da ɗaya ba wasa bane... Washe gari jirgin mu ya tashi sai ƙasar Prague, a nan Zaid ya ƙare degree ɗin sa. Farko Ahmad Switzerland ya kai shi kafin daga nan Zaid ɗin da kan sa ya choosing Prague inda ya ƙare karatun sa a nan. Lokacin da Zaid ya zo tarar mu a airport haka na buɗe ido baki hanci ina kallon sa yadda ya zama saurayi, kamanninsa da Ubansa ya ƙara fitowa, farin fatana kawai ya banbantashi da Uban sa. Yana ganina ya juyar da kai gefe, na taune leɓena dan kar na yi kuka a wajen. Sai da Ahmad ya ce ya gaisheni kafin ya iya buɗa baki ya ce ya hanya? "Son you are handsome" na faɗa ina murmushi kamar wata wawuya. Bai ce komai ba ya kama hannun uban sa yai gaba. Na bi bayan su a hankali ina ƙarewa ɗa na kallo, duk tsayin Ahmad sai na ga Zaid ya fishi. Gidan da Ahmad ya siya mi shi mu ka sauka. Duk wani haba-haba da ya ke da uban sa ni ban samu ba. But Its ok tunda gani ga ɗa na ai shikenan. Da ke da dare mu ka isa ba mu wani jima ba kowa ya wuce ɗaki dan bacci. Ni kam bacci ƙauracemin yai saboda tsananin farin ciki. Washegari mu ka shirya zuwa makarantar su Zaid inda ya ƙarɓi kyauta har sau biyar a wajen convocation ɗin. A wajen ɗaukan hoto ma da ƙyar Zaid ya tsaya mu ka ɗau hoto mu biyu. Kwana uku mu ka yi mu ka dawo London. Bayan mun yi weekend ranan Monday mu ka wuce Nigeria. Ban san mi Ahmad ya gayawa Zaid ba amma ya dena gudu na, yana gaisheni sai dai ya kasa sake jiki da ni. Gidan Ahmad ɗin nan ne da na sani bai chanja ba. Kwana na ɗaya Ahmad ya ɗaukeni zuwa Maitama inda ya kaini wani ƙaton gida da ya gina. Lungu da saƙo na gidan ya kaini na gani. "Do you like it?" Ya tambaya bayan mun gama duba gidan. "Yayi kyau" na faɗa a hankali ina ganin ƙaton hoton bikinmu da aka manna a falon. Briefcase ɗin sa ya buɗe ya fito da takardu ya miƙo min. Whats this? Na faɗa bayan na amshi takardun Open it ya faɗa tana murmushi. Takardun gidan ne ɗauke da suna na. "Ahmad..." "Shhhhh, kar ki ce komai. Ƙaramar kyauta ce na miki ba zan taɓa biyan ki abinda ki ka min ba, but daga yau na miki alƙawarin har ƙarshen rayuwata zan dinga ƙoƙarin faranta miki rai kuma duk abinda ki ke so shi zan yi" Na yi shiru ina kallon takardun. Ba abinda gida zai min, farin ciki na Zaid ne. If i have my son nothing else matters. "Ke da Zaid za ku zauna a nan gidan. Akwai gidan da zan siya Fatima da Hajia sai su koma chan. Idan akwai wani abu da ki ke so please feel free to ask me" ya faɗa yana wasa da ɗaya hannuna. Mun ɗau lokaci ba wanda yai magana kafin na ce ina neman alfarman abu uku a wajen ka. Da fara'a a fiskarsa ya ce "go ahead minene?" Na sauke ajiyar zuciya sannan na ce " na farko ka cewa Zaid ya rakani Hajjin da za ayi bana. Na biyu ka amince dukkan mu mu zauna a gidan nan. Wannan gidan ya ishemu zama ba sai ka raba mana gida ba. Na uku shine ka nemi yafiyar ƙannenka ɗan Alaja da su Safiya, idan da hali ka maida mu su dukiyar su da ka cinye" "An gama gimbiyata, anything else?" "Ka amince min na cigaba da aiki na." Na faɗa a hankali kaina a ƙasa. Nannauyan ajiyar zuciya ya sauke kafin ya ce "ina son ki kasance kusa da ni amma tunda kin fi son chan shikenan. Duk abinda Aaliyah ke so shi Ahmad zai yi... Na yi zaman sati bayan gaba ɗayan mu mun dawo gidan. Inna ce ta zaɓi Inda za ta zauna da inda Fatima za ta zauna. Ni ba damuwana ba ne tunda ba wai zama zan yi tareda su ba. Tare da Zaid mu ka koma London a hankali a hankali soyayyar ɗa da uwa ta fara dawowa tsakanin mu. Da lokacin Hajji ya zo na biya mana Hajji mu ka je ni da ɗana. Fiye da rabin addu'a na akan ɗana ne ina nema ma sa shiriya musamman da na karanci al'adar bature ta fara zama a jikin sa. Bayan 'yan watanni Zaid ya koma yin masters na shi wannan karan a America yai inda duk lokacin da ya samu dama yana zuwa wajena yai kwanaki kafin ya koma... A Nigeria kuma Ahmad ya maida hankalinsa kan siyasa inda aka fitar da shi a matsayin ɗan takara da ke neman kujeran senator. Da zaɓe ta zo ya ci zaɓe. Na je na ma sa sati biyu a Nigeria domin na taya shi murna a nan na ga yadda Inna ke ƙara dulmiya da sha'anin duniya ko kaɗan tsufanta ba ya gabanta. Yadda yanzu ake damawa da Ahmad a harkokin siyasa ya sa ta ke sake baza ƙafa tana tsula tsiyarta yadda ta ke so. Idan ka zo gidan ka ga yadda Inna ke zuba mulki ka ɗauka ita ce matar gidan. Ni kam yanzu hankalina kacokam na ga ɗana Zaid ba na sa damuwar komai a raina balle takaici ya hanani bacci. Da ke yanzu Ahmad na senator shiyasa ba ya samun zuwa wajena akai akai kamar da. *** Bayan Ahmad ya gama tenure na shi na farko yana son tafiya na biyu Inna ta ma sa kwaɗayin ya nemi kujerar Gwamna da farko bai amince ba daga baya ya amince. Innar ce ta haɗashi da wanda su ka kaishi gaban Shugaba. Shugaba ya riƙe hannun Ahmad yana duba tafin hannunsa chan ya ce mutane uku ka ke tsananin so a duniya yanzu. Mahaifiyar ka, matar ka da kuma ɗan ka. Mahaifiyarka ta riga ta zaɓi wanda za ayi amfani dashi a maka aiki saura ka ƙarasa aikin ne kawai. Shugaba ya bashi wani ƙaho ya fito da wata ƙwarya wanda ba komai a ciki ya ajiye a gaban Ahmad ya ce ka kira sunan ta sau uku sunanta da na mahaifiyarta za ka kira. Za ka ce Aaliyah 'yar Mariyatu har sau uku. Idan hoton ta ya bayyana ka daɓa ma ta ƙahon nan ka bar shi a jiki. Za ka hau kujerar gwamna hakanan matarka za ta dinga rashin lafiya, ba za ta taɓa samun sauƙi ba har sai idan an cire ƙahon nan daga jikin ta. Yadda ba za ta taɓa tashi ba haka za ka zauna akujeran nan sai ka yi shekaru takwas ɗin nan rus. Ahmad riƙe da ƙaho ya fara girgiza kai yana faɗin " No,never. I will never hurt Aaliyah, I will never hurt my wife" Shugaba ya bushe da dariya sannan ya ce "wa ka ke tunanin ya sa ka ci zaɓen farko da aka yi. Ka tambayi mahaifiyarka jinin da aka zubar aka ma ka aiki da shi" Ahmad ya miƙe tareda cillar da ƙawon hannunsa yana faɗin " ba zai yiwu ba. Ba zai taɓa yiwua ba" yana magana kamar wani zararre haka ya fice daga gidan Shugaba. *26- The widower* *S* Cikin Halima na wata bakwai na sa aka yiwa Jiji visa ta taho UK. Ba na so Halima ta sha wahala kamar yadda Aaliyah ta sha, although ina samun lokaci amma kuma a condition ɗin da ta ke tana buƙatar mutum kusa da it 24/7. Da ikon Allah wataranan Alhamis ina office Aka kirani daga asibiti akan matana ta haihu. Da gudu na figi motata sai asibiti. And there she was, my beautiful Princess is born. Allah na gani ina son 'ya mace, alƙawari na yiwa kaina idan na samu 'ya mace zan bata kulawa da tarbiya. Za ta yi karatu a inda ta ke so za ta karanta abinda ta ke so za ta auri duk wanda ta ke so matuƙar ba kafiri ba ne. Da ke ba wata matsala a ranan aka sallamemu mu ka koma gida inda Jiji ke kula da Princess da mamanta. Ranan suna na sawa jewel ɗina *Aaliyah*, dama tun a asibiti na ma ta huɗuba da sunan. Idan ban samu Aaliyah ba a matsayin mata Allah ya bani ita a matsayin 'ya. Ina riƙe da Aaliyah a hannuna ranan suna da daddare Halima ta ce "Hamma sunan ta kenan ko?" "Ba kya son sunan ne?" Na tambaya ina kallonta. Ta yi saurin girgiza kai tana faɗin "dama so na ke ka ma ta mai suna" ta faɗa a hankali. Tausayi ta bani domin tanada haƙuri, ta sani har yanzu gurbin Aaliyah yana nan a zuciyata amma ba ta taɓa ƙorafi ko ta nuna damuwa ba. "Ki yi haƙuri Halima, Insha Allah zan ƙara ƙoƙari" "Ba komai Hamma na, na san 'yar nan za ta samu kulawa fiye da mai sunan ta" ta ƙarisa maganar tana murmushi... Yayinda Halima ke yiwa Aaliyah kunyar Fulani a matsayinta na 'yar fari ni ban san wannan ba. Indai ina gida to ina maƙale da princess da tana cika wata biyu na fara fita da ita. Like idan zan je strolling haka zan sa ta a kekenta mu je tare wani lokaci kuma goyonta na ke yi da babycarrier. Da ta kai wata shida kam har class na ke zuwa da ita. Haihuwar Princess ya ɗauke min hankali akan Aaliyah dan na daina saka ta a raina kamar da, sai dai har yau babu shirinta guda da na taɓa missing, sauraron shirye-shiryenta ya riga ya zame min jiki. Aaliyah na shekara uku aka haifi Usman wanda mu ke kira Ameer sai Aliyu Haidar sannan AbulRazaq. Allah ya wadata mu da buɗi zaman lafiya da kwanciyar hankali. Aikin koyarwa na ke amma dukkan wani arziƙi da na samu dalilin noma da arziƙi ne. Abdul na da shekara biyu Halima ta sake samun wani cikin a hankali ta ke rainon cikinta, wannan karan yana ba ta wahala sosai dan tun yana ƙarami ta ke laulayi mai zafi. Cikin yana wata bakwai na tafi Yale University dan gudanar da wani conference, dama tunda na zama professor abubuwa su ka fara min yawa domin ina yawan samun gayyata zuwa ƙasashe daban-daban. A wannan lokacin ne kuma Allah yai wa matata Halima rasuwa wajen haihuwa. It was one of the saddest day of my life. Ashe ma ɗan cikinta ya mutu kwana biyu kafin ta fara naƙudar. Mutuwar iyali akwai ciwo sosai, sai bayan Halima ta rasu na gane cewa mace rufin asiri ce ga namiji... Kafin ni da 'ya'ya na mu saba da rashinta sai da abin ya fi shekara. Jiji ta min maganan aure amma na nuna mata banda ra'ayin yin wani auren kuma Alhamdulillah dalilin Jiji duk yaran ba su rasa gatan uwa ba, dama tun Halima na da rai yaran sun fi sabawa da Jiji a kanta. Allah ya jiƙan Halima da rahama, mace ce ta gari, mace ce mai biyayya, matar ƙwarai ce. Ta amsheni da weakness ɗina ta amsheni da broken soul ɗina. Bayan rasuwanta things were not the same again, ta tafi ta bar giɓi a rayuwata, giɓin da bana tunanin akwai wata mace da za ta cika shi. Three years bayan rasuwanta na dawo Nigeria gaba ɗaya. A Bauchi na ke son setteling saboda kusancinsa da ƙauyenmu. Sai dai na samu gurbin koyarwa a UniAbuja, BUK, Mautech da kuma Unimaid na dawo Abuja bayan Princess ta zaɓa min Abuja, so i settled in Abuja. Though na kan je visiting lectures a BUK. Aaliyah ta ƙare degree ɗinta at 19yrs. Bai jima ba ta joining namu a Nigeria. I have high hopes for her amma kuma ba zan taɓa ma ta dole ba, she's free to choose her path and as long as I'm alive Aaliyah will always be happy. Thats a Promise... *** *A* Ahmad ya dawo gida a rikice Inna ba ta nan. A lokacin ya kirani yana tambayata ko ina lafiya na ce ma sa lafiyata ƙalau. Kafin ya kashe wayar ya ce ina fara jin wani chanji a jikina to na kirashi. Na ce ma sa na ji. Yadda ya ke maganar a wayan na san ba lafiya ba amma kuma tunda bai gayamim komai ba nima ba zan tambayeshi ba. Da Inna ta dawo ta taradda Ahmad a rikice. Faɗa ta fara ma sa kan ƙin bin umurnin Shugaba da yai. "Ahmad mi ye aciki idan Aaliyah ta yi jinya na shekara huɗu zuwa takwas ba fa mutuwa aka ce za ta yi ba kuma..." Ta tsaida maganar saboda bindiga da Ahmad ya ciro daga aljihunsa. "Na yi danasanin kasancewar ki uwata. I curse the day you gave birth to me. Bayan duk irin walaƙancin da mu ka yiwa Aaliyah you want me to hurt her" Bindigar hannunsa ya saita daidai goshinta ya ce "idan ki ka yiwa Aaliyah wani abu. Na rantse da Allah kashe ki zan yi. Enough Inna, Enough. Na haƙura da mulkin, na haƙura da komai. Leave Aaliyah alone, please" ya ƙarisa maganar yana hawaye. Inna da ta gama tsurewa kasa motsi ta yi har ya fice daga ɗakin. Kira yai akan a booking ma sa flight zuwa London aka tabbatar ma sa weekend ne. Bai kwana a gidan ba ranan, saboda baƙin ciki. Little did he know that everything that goes around comes around. Washe gari Inna ta kirashi a waya tana ma sa magiya akan ya dawo gida domin akwai matsala. Lokacin da ya dawo ta ke sanar da shi sharuɗɗan shugaba, idan ba zai ba da ni ba to tabbas shi ma ba zai zauna lafiya ba. Inna har ƙasa ta tsugunna tana roƙonsa akan yai abinda Shugaba ya ce dan ba za ta juri rashin sa ba. Ina maka burin ka zama shugaban ƙasa bayan ka yi gwamna. Ina da burin zama uwar shugaban ƙasa. Ya kalli greedy uwar sa ya ce "what about her, ba ki da wani buri akan ta na alkhairi sai na sharri? Aaliyah ita ce Ahmad Wamako. Na farfaɗo da ƙafata ne saboda ita, without her may be yanzu ina jail ko psychiatric. Dont you ever wish her well? Ita ce fa uwar jikan ki Zaid" "Ahmad ta riga ta shanye ka, idan ba dan na tashi tsaye a kanka ba da Allah ne kaɗai ya san ya za ta maida kai. Ban taɓa sonta ba kuma ba zan so ta ba, tunda ta zo gidan nan komai ya lalace mana. Farar ƙafa gareta ta, ta hana na juyaka yadda na ke so" Da rinannun idon sa ya kalli Inna ya ce "gara na mutu da wani abu ya samu Aaliyah" Inna ta sa kuka tana magiya amma Ahmad bai saurareta ba... Ahmad na shiga ɗakinsa ya faɗi. Ƙarshen tsayuwarsa a duniya kenan. Washegari ne iyalen gidan su ka fahimci halin da ya ke ciki. Inna ce ta fi kowa damuwa da halin da Ahmad ya shiga saboda tasan inda cutarsa ta samo asali. A Nigeria aka fara jinyar sa amma ba wani cigaba. Ba ya iya yin komai a kwance ya ke, ba zai iya koda ɗaga hannu ba sai an taimaka ma sa, magana ma da ƙyar ya ke yi. Inna ta shiga ta fita amma zancen ɗaya ne Ahmad ya ba da ni. Ita da tanada iko ba abinda zai hana ta zo ta kasheni a inda na ke, amma Shugaba ya ce sai dai Ahmad ɗin ne zai iya sacrificing ɗina tunda shi ke so na. Ana ƙoƙarin fita da shi waje ya ce baya so a kai shi wajena kawai. Inna ta hana, ta ce ba zai je wajena ba. Duk gidan tsoron Inna su ke shiyasa su ka haƙura, sai da Zaid ya je Nigeria tukunna ya yi faɗa da Inna ya taho da shi London. Seeing him in his vulnerable state ya sa na ji tsananin tausayinsa. Lallai ɗan Adam ba komai ba ne... Haka na zauna da shi ina jinyar sa. Shi da bakinsa ya gayamin jinyar sa ba ta asibiti ba ce sakamakon aikin da ya aikata a ƙuruciyar sa da ma girman sa ya ke ci tun yanzu. Daga baya ya gaya min komai. Gaskiya mutum mugu ne. After all what Inna did to me bai isheta ba sai ta haɗa da son hallakani. While Inna was busy neman taimako a wajen malaman tsubbu da ma su tsafi. Ni na duƙufa wajen yi ma sa addu'a da sadaka hakanan na fara nema ma sa maganin Musulunci. Ƙanin sa AbdulWahab sau biyu yana zuwa gaisheshi, Safiya da Fadila ma sun zo cikin ƙannensa 'ya'yan Inna ɗaya ce kawai ta zo London ta gaida shi kuma dukkan su suna da halin zuwa. Wata biyu da kawoshi London ƙafafuwansa su ka ruɓe, dama a kumbure su ke tun lokacin. Ana ta kan kula da shi ta waje ashe ƙafarsa ta ciki na ta kan ruɓewa. Likitoci su ka ce sai dai a yanke ƙafafun idan ba haka ba haka zai ta ci har ya kawo cinyar sa. Su kan su ba su san takamaimai miya jawo ruɓewar ƙafar ba kame-kame kawai su ke tunda aka kawoshi. Ashe da Ahmad ya bayar da ni haka zan ta ruɓewa har na mutu. Inna babu ɗanɗanon imani ko kaɗan a ranta. Hatsabibiyace da tai nisa. Kuma fa a cikin duniyar nan akwai ire-irenta bila adadin. Ta ya Allah ba zai jarrabemu ba bayan ga mugayen mutane da su ka yi yawa acikinmu su na tafka fasadi a ƙasa. Gobe za a ma sa aikin ina tareda shi ina goge ma sa jiki ya kira suna na a hankali ya ce*"Na zalinceki Aaliyah, na hukunta ki da horo mafi tsanani ta hanyar rabaki da ɗan ki na tsawon lokaci, ki yafemin. Dont be lonely after my death ki je ki aure shi. Ba za ki taɓa samun cikakken farin ciki ba sai kina tareda shi"* "Ka daina irin wannan maganan dan Allah, daga za a maka aiki sai ka fara kiran mutuwa. Rashin ƙafa ba mutuwa ba ne" "Ina ma tun farko Allah ya dasa min son ki a zuciyata. Da yanzu na san na shafe gurbin sa a zuciyar ki. Ina ma zan iya maida hannun agogo baya, da na gwada miki soyayya ranan da aka kawoki gidana da ban miki ƙarfi ba da ban dake ki ba da ban..." Na sa hannu na rufe ma sa baki "ya wuce Ahmad ka daina tuna baya, ya wuce" Murmushi mai ciwo yai sannan ya ce " ki min wata alfarma dan Allah" Na kalleshi na ce minene? "Tunda mu ka yi aure ba ki cewa kina sona ba. Please ko da bai kai zuciyar ki ba ki ce kina sona" Kuka ne ya kufce min, he was right. 29yrs of marriage amma ban taɓa ce ma sa ina son shi ba, ban taɓa kiransa da suna mai daɗi ba balle na ma sa maganar soyayya. Na riƙe hannun sa na ce " Darling Ahmad I love you, please forgive me" Shima ɗin hawaye ne fal a idonsa ya ce " ki ɗan sake faɗamin dan Allah" "My darling husband I love you, Allah ya baka lafiya mijina" Dariya ya fara marar sauti yanayi yana lumshe ido. And that was the last laughter he had in this world... Da asuba da na tashi na yi ƙoƙarin tashin sa amma inaa rai yayi halin sa. Allah ya sa mutuwa ce hutu gareshi. Da rabon zai mutu da ƙafafuwan sa shiyasa ya rasu kafin ayi ma sa aiki. It wasnt easy loosing a husband ko da kuwa mijin da ba ka so ne. Miji rufin asiri ne ga mace. A ranan aka shirya gawan Ahmad aka maida shi Nigeria. Mutuwar Ahmad ta girgiza ni, i was hospitalised for two weeks. Rashin zuwana Nigeria shi ya ƙara sa mun baƙin jini a wajen Inna. Jini na ne ya hau ranan da aka wuce da gawarsa Nigeria sai da aka min alluran bacci tukun aka stabilizing ɗina. Hawan jini na dama ya riga ya zamemun ciwon zuciya. A London na yi takabar Ahmad wanda duka cikin jinya na yi shi. Sai yanzu na ke dana sani, i should've shown him love lokacin da ya quitting halayensa na banza. Ahmad didnt have a great life infact sai towards the end of his life ne ya quitting shan giya completely. Neman mata kam inaga tun lokacin Cataliya ya dena. But in the end Allah Gafurun Rahimun ne. Bayan na ƙare takaba na ajiye aikina gaba ɗaya. Ina son komawa ƙasata ina son kasancewa kusa da gida kusa da 'yan uwa na, and idan Zaid yai aure i will live close to him.... *** paging da ya buɗe na gaba an rubuta Nigeria amma ba a fara rubutu a ciki ba. Ya kalli Aaliyah da ke ta sheshsheƙar kuka ya jawota jikinsa yana ɗan bubbuga bayanta. a hankali. Shi ɗinma kukan ne bai yi ba amma idanunsa sun ciko da hawaye, he has no idea cewa Mom was in pains all these years. And ba za ka taɓa gani a idonta ba domin kullum fiskanta ɗauke da murmushi ya ke. "Hey ki dena kuka kin ji, Its over now. Thats in the past now from now on i'll make sure ta samu farin cikinta" Ya jima yana lallaɓa Aaliyah kafin ta yi shiru ta dena kuka. Sun jima zaune a haka kafin ta ɗago daga jikinsa ta ce "Wamako zan tafi gida" "You cant go like this, ki huta tukunna or else kowa ya ganki zai yi tunanin something is wrong" Ya taimaka mata ta kwanta a gado. Fitowa falo yai ya zauna yanajin zuciyarsa na ma sa zafi. Chan ya fito da sigari ya kunna ya fara zuƙa but then Mom ta hanashi sha, he has to respect her every wish from now on. Ya jefar da sigarin ya take ta. Lokacin da ya shiga ɗakin, Aaliyah har ta yi bacci. Zuwa yai ya rufeta da bargo kafin ya fita daga ɗakin a karo na biyu... *27-The Plan 2* Da sauri ta sauko daga kan gadon bayan ta ga agogon da ke ɗakin ya clocking ƙarfe bakwai da kwata na dare. "Oh no! Abba will be worried" Ta fara neman wayan ta a inda su ka zauna amma ba ta gani ba. Gyara zaman gyalenta ta yi sannan ta fito daga ɗakin. Tana cikin duba wayarta a falon Zaid ya shigo. Ta juyo ta kalleshi ta ce "Wamako why didnt you wake me up? Abba ya ce na dawo before 6pm and its past 7pm now" "Relax, kin yi sallah?" Ta girgiza kai "To je kiyi sallah" "Wamako ba za ka gane ba Abba..." "Shhhhhhh, just do as i say" ya faɗa yana nuna ma ta hanyar ɗaki. He's right sallah shi ne gaba da komai. Ta juya ta shige ɗakin Mom. Alwala ta yi ta gabatar da sallar la'asar da maghriba. Addu'a ta ke a ranta Allah ya sa kar Abba yai fushi. Tana fitowa ta sameshi a falo yana danna waya. Ganin wayanta akan center table ya sa ta yi saurin ɗauka tana dubawa. Missed calls ne na Abba, Nawal da kuma Ameer. "Na shiga uku...Abba!" "Relax, na yi magana da Nawal, kar ki damu" Hararan sa ta yi ta ce "dole ka ce kar na damu tunda kai a gida ka ke" Tasowa yai gabanta ya ranƙwashi kan ta "Ah!, mi na maka?" Ta faɗa tana sosa wajen. "Ba na son raini, ni ba sa'an ki bane" Ta turo baki tana haɗe rai, ya kai hannu zai sake ranƙwashinta ta kauce. "Lets go" ya faɗa yana wucewa gaba. Ta yi sauri ta koma ɗakin ta ɗauko jakarta wanda tuni ta maida dairy ɗin Abba ciki... Ba wanda ya ke magana tunda su ka shiga motan kowa da abinda ya ke tunani. "Wamako mi Nawal ta ce?" Aaliyah ta katse shirun. "Abba na nemanki" "Innalillahi! Mi ta ce ma sa" "Mi za ta ce kuwa. Ban da kin ma sa ƙarya kin zo wajen namiji" "Wamako please" ta faɗa kaman za ta yi kuka. 'Yar dariya yai kafin ya ce "bulala ɗari awaits you baby" "Lie, ba abinda Abba zai min" Ok ya faɗa yana maida hankalinsa ga driving da ya ke. Nawal ta kira ta tambayeta ya su ka yi da Abba. Nawal ta gaya mata cewa Abban ya kira numbarta ba a ɗauka ba shiyasa ya kira Nawal ɗin kuma ta ce ma sa tana bacci. Zai je Minna ne yau, ya na so ta koma gida da wuri tunda Jiji ba ta nan. Sai alokacin ta sauke ajiyar zuciya tana yiwa Nawal ɗin godiya. Tana ma sa kwatance har su ka isa gidan na su. "Thank you Wamako" ta faɗa tana shirin fita daga motar. "Tsaya" Ta juyo tana kallon sa. "Ki zo office ɗina gobe. 10am" "Ni ban san office ɗin ka ba" ta faɗa tana turo ba ki. Ya kai hannu zai ranƙwace ta ta fice daga motar tana dariya. Ya jima zaune cikin motar yana lissafa abubuwa dayawa a ransa kafin daga baya ya tada motar ya bar gidan su... Tana zuwa gida ta samu angry Ameer yana jiranta. Ta san dama shine zai yi ƙorafin rashin dawowarta da wuri. Abdul da Haidar kam hankalin su na ga kallon da su ke yi. Ta ci sa'a Abban ma bai kira ya tambayesu ko ta dawo ba. Tana tunanin ƙila wayarsa ne ba chaji. Tana zuwa ɗakinta wanka ta yi ta sa kayan bacci ta kwanta a gado tana tunanin mi Zaid ya gaya ma ta gobe fatan ta tunaninta da na shi ya zamo ɗaya. Ba ta fi minti goma ba Abba ya kira ta, hasashenta ya tabbata wayarsa ce ta mutu shiyasa bai ƙara kira ba tun ɗazu. Bayan sun gama wayar ta kira numbar Mom. Kira ɗaya ta yi aka ɗauka. Lokacin da Mom ta yi magana wani sabon kuka ne ya tahowa Aaliyah saboda tunowa da rayuwar Mom ɗin ta su ka karanta yau. Its very depressing ace kana fama da matsala amma ka dinga nunawa duniya cewa ba komai tana cikin farin ciki. Who would've thought cewa the famous Aaliyah Badamasi Bulama tayi fama da waɗannan matsalolin. Ko tana gabatar da shiri ba za ka taɓa hasaso matsala a rayuwarta ba. You will just think rayuwarta perfect ne. "Daughter lafiya ki ka yi shiru" muryan Mom ya dawo da ita daga duniyar tunanin da ta tafi. "Lafiya Mom, kawai na missing ɗin ki ne. Yaushe za ki dawo?" "Zai kai wani sati dan Amma ba ta jin daɗi" Aaliyah ta ce Allah ya bata lafiya. Mom ta amsa da Amin. Tana ajiye wayarta sai ga kiran Zaid. Dama ta yi ta kiran layinsa da rana amma a kashe. "Son how are you? Na kira ka da rana switch off" Zaid ya shafa hoton da ke hannunsa wanda hoton Sa'eed ne goye da Mom su na dariya. According to labarin da ya karanta the picture was taken the first day da Mom ɗin ta je Cambridge. "I love you Mom" ya faɗa hawaye na gangaro ma sa. Back then da Dad ya kaishi Switzerland he missed her alot, kullum sai ya yi kuka saboda ba ta taɓa kira ko ta zo wajen sa ba. A hankali ya yarda da maganar Dad cewa Mom ɗin ba ta son sa that's why she abandoned him. Wannan ya sa ya taso da jin haushinta duk da kuwa deep down yana missing ɗin ta. "Zaid" ta faɗa a hankali. "I love you Mom, na missing ɗin ki sosai. Yaushe za ki dawo?" Hawaye ne ya fara zubo ma ta, ba ƙaramin jin daɗin maganganunsa ta yi ba. "Son, Amma ce ba ta jin daɗi amma da ta ɗan ji ƙarfin jikinta zan dawo, nima na yi missing ɗin ka" "Ki ce wa granny kar fa ta mutu akwai biki da ya kamata ta gani" Mom ta yi dariya ta ce "ka amince za ka auri Zahran ne nan kusa. I thought ka ce ka fasa aure wannan shekaran" "Its a surprise Mom, sai kin dawo za ki ji komai" Haka dai su ka cigaba da hira kusan minti goma kafin su ka katse kiran. Baccin daɗi Mom ta yi yau saboda hiran su da Zaid, farin cikin da ta ke ji kamar lokacin da su ka je su ka yi Hajji tare... *** Washe gari yana saukowa sai ga Inna ta fito. "Zaid, Zaidu" ta fara ƙwala ma sa kira Ya tsaya ba tareda ya juyo ba "Mi ya hana ka zo ka gaisheni yau da safe?" Ba tareda ya juyo ba ya ce " ban ga dama ba. Infact na daina gaishe ki daga yau" Inna ta taɓe baki ta ce "Lallai Zaid abinda uwar ka ta saka kenan. Ba ma wannan ba ance jiya ka shiga da yarinya gidan nan kuna tare tun safe har dare. Ba dai ka fasa auren Zahra ba" A fusace ya juyo ya ce "look old woman. Ba ruwanki da harkan rayuwata. Idan ba za ki iya bakin ki a nan gidan ba zan maida ke ƙauyenku" daga haka yai tsaki ya fice. "Allah ya tsine maka, ni ka ke cewa za ka kai ƙauye, ƙauyen uwar ka ko?. Wallahi ka yi hankali da ni Zaid, dan kana jika na ba shi zai hana na maka rashin mutumci ba..." ita ɗaya ta ke ta haukanta shi kan ko waiwayowa bai yi ba... Ƙarfe tara da rabi ta turawa Abba text akan za ta fita ganin gari. Ya kirata ya ce kar ta daɗe dan yau Isma'il da Jiji za su dawo. Driver ne ya kaita kamfanin Zaid ɗin mai suna Wamako Enterprise. Tana shiga receptionist ta mata kwatancen office ɗin Zaid. Tana zuwa ta ja dogon numfashi sannan ta shiga office ɗin bayan sakatariyar sa ta bata izinin shiga saboda Zaid ya sanar da ita zuwan ta. He was on call lokacin da ta shigo dan haka ta samu waje ta zauna tana jira ya gama wayan. " Baby ya ki ke?" Ya faɗa yana ƙarewa fiskarta kallo. "Ni ba Baby ba ce" ta faɗa tana haɗe fiska. " 'yar ƙauye kawai" "Ni ba 'yar ƙauye ba ce" "Zan make bakin ki idan ba ki min shiru ba" Ta churu baki ba tareda ta yi magana ba. Sai da ya ɗan duba wasu takardu kafin ya ce " Aaliyah we have a mission" "Mission kuma?" "Ba na son shirme, you know exactly what I'm talking about" "Zaid Wamako i dont know. Please explain" ta faɗa tana murmushi. "Kin rainani yarinyar nan. Na ga alama sai na fara miki bulala" "Chabɗi". "Oh haka ko?" Ta girgiza kai tana dariya... A hankali ta buɗe ƙofa ta shigo office ɗin cikin takunta mai ɗaukan hankali. Cak ta tsaya lokacin da ta ga fiskar Zaid ɗauke da murmushi. Zaid ɗin da he hardly smile shine ta ke ganin murmushinsa a bajau yau ɗin, hakan ma a gaban mace. Ƙarasawa ta yi wajen sa, ta kissing goshin sa tana faɗin "good morning love" kallon Aaliyah ta ke yi tana hararanta. "Excuse me, ba ki san privacy ba ne" Ta daka wa Aaliyah tsawa. Aaliyah ta tashi da sauri tana faɗin sorry. Sai da Aaliyah ta fita sannan ta ce "who is she?" " Zahra whats the meaning of this?" "Ni zan tambayeka meaning of what i just saw. Ina shigowa garin nan wajen ka na fara zuwa amma shine daga zuwa sai idona ya ci karo da abin takaici. Who is she da za ta zo kusa da kai? 'Yar gidan uban waye ce?" Ya haɗe rai ya ce " none of your business" "Haka za ka ce, shikenan" ta ɗau jakarta ta fice daga office ɗin fuuu. Aaliyah na zaune a office ɗin Secretary ta ga Zahra MCcollins ta fito daga office ɗin Zaid fuuu. Ta ce a zuciyarta Allah ya kyauta. Wayan Secretary ya kira ya ce ta turo ma sa Aaliyah. Tana shigowa ya fara faɗa. "Wajen wa ki ka zo" "Kai ma na" ta amsa cikin rashin fahimta. "Ta ya Zahra za ta ce ki fita ki fita, wajenta ki ka zo ko office ɗin na ta ne?" "She's your girlfriend and..." "Ba na son ƙauyen ci, next time idan ban ce abu ba ki ka yi bulala zan miki" Ok kawai ta ce... *** "Abba please ka rakani shopping yau" "Princess akwai takardun da zan duba and zan je gaida abokina da bashida lafia. Ku je da Isma'il da su Ameer" Ta fara bubbuga ƙafa tana faɗin "Abba ni kan a'a mu biyu za mu je, Daddy Daughter shopping na ke so. Tun da na dawo garin nan ba mu taɓa fita mu biyu ba. "Ok Ok za mu je, amma shopping kawai kuma za mu dawo da wuri dan zan je gaisuwan nan" Ta yi murmushi ta ce "thank you Abba". Haka kawai ya ke jin wani nishaɗi na ratsa shi bai kuma san dalili ba. Shigar ƙananun kaya ya ke son yi saboda weekend ne amma kuma sai ya ji bai gamsu da shigar ba, dan haka ya ciro manyan kaya ya saka... Lokacin da ya fito ya samu Aaliyah da Isma'il su na faɗan su da su ka saba. Isma'il na cewa shigar da ta yi bai mata kyau ba ita kuma tana faɗin ai sai ta cinye gasar kyau a haka. "Hajiya za mu ɗan zaga gari" Abba ya faɗa yana kallon Jiji. Jiji da ke zaune kan kujera ta ce Allah ya dawo da ku lafiya. Abdul da ke cin dambun nama ya ce "Abba mu ma za mu bika" "Auta yau da Antyn ka za mu fita next week sai na fita da ku" Abdul ya ce to a taho ma sa da ice cream... "Jee mun tafi" Aaliyah ta faɗa tana bin bayan Abba da tuni yai gaba. Isma'il ya bi bayan 'yar uwar ta sa da kallo. Yana sauke ido sai a kan Jiji da ta zuba ma sa ido. "Jee wannan kallo haka?" "Ba dole ba, idan da ka cigaba da kallonta haka inaga idanuwanka faɗowa za su yi. Ka fito fili ka gaya ma ta abinda ke cikinka ka ƴi mutum sai shegen zurfin ciki" "Jee Allah kin cika sa'ido" "Shikenan kwanan nan za ka ga ana sallama da ita" Isma'il ya haɗe rai ya bar falon. *** Su na shiga mota ta yiwa Zaid text a kan sun kamo hanya. Zaid ya turo ma ta saƙo akan su ma saura ƙiris su isa shopping mall ɗin. Farin ciki fall a ranta, she's so excited ta ga yadda Abba zai ji idan ya ga Mom yau... Su na shiga ta kira Zaid wanda ya ce mata tun ɗazu su ke cikin mall ɗin. A hankali ta ke tafiya, Zaid ke gefenta yana tura shopping cart ɗin. Ba abinda ta ke buƙata kawai dai dan Zaid ya takura ne shiyasa ta biyoshi shopping ɗin. "Mom ina zuwa, kaman na ga wani abokina ta ɗaya side ɗin barin duba shi" Zaid ya faɗa yana komawa baya da sauri. Wajen da Aaliyah ke jiran sa ya je suna haɗa ido su ka yi murmushi. Su ka cigaba da kallon Mom daga nesa. Cart ɗin da Zaid ya bari ta jawo ta cigaba da turawa, ta zo ƙarshen edge ɗin stack na kayan za ta juyar da cart ɗinta shi ma ya turo cart ɗin sa carts ɗin su ka haɗu. Da sauri ta ɗago ido ta na faɗin sorry. Tana sauke idon ta ta sake ɗagowa da sauri dan ta tabbatarwa idonta ba gizau ɗin sa ta gani ba. Idanuwan su su ka sake haɗuwa a karo na biyu hakanan zuciyoyin su su ka buga a lokaci guda. Taruwan hawaye a idon ta ya sa ta yi saurin ɗauke idon ta daga cikin na shi. Bugawan da zuciyarta ke yi da ƙarfi ya sa ta dafe ƙirjin ta. Shima ɗin tsintar kan sa yai da jin wani zafi a zuciyar sa. A hankali ya daure ya ce "ya haƙuri?" "Alhamdulillah" ta faɗa da sauri tana juyawa saboda kar ya ga hawayen da su ka riga su ka fara zubo ma ta. Tana tafiya tana ƙoƙarin goge hawaye ta jita a ƙirjin wani da sauri ta ɗago ido sai ta ga Zaid. Ganin Zaid ne ya sa ta ƙara kwantowa jikinsa tana ƙoƙarin haɗiye kukan ta. *28-a perfect romantic night* Taimaka ma ta yai ta kwanta kan gado yana ma ta sannu. Ba ƙaramin tausayinta ya ke ji ba, Its not easy for her ya sani, but duk abinda yai ya yi ne dan farin cikinta. All he wants shine ta samu farin cikin da ta rasa shekaru talatin da su ka wuce... Sanda ya fito daga ɗakin ya turawa Aaliyah text kamar haka *activate plan B* Tana ɗaki ta ji shigowar text ta ɗau wayan ta karanta. Tashi ta yi ta sa room slippers ɗin ta ta fito ta wuce ɗakin Jee. A kan sallaya ta sameta tana jan carbi. Ta zauna gefenta tana faɗin "Jee akwai magana da na ke son mun yi, ki rage addu'an na ki mu yi magana" Sai da Jee ta ƙara minti goma kafin ta juyo ta kalli Aaliyah tana faɗin minene?. "Jee, ki yiwa Abba magana ya ƙara aure dan Allah" "Yau kuma?" "Jee, Abba har yanzu da ƙarfin shi he's just 55yrs kuma kin ga ba daɗi baƙi su zo gidan nan su ga ba mata a gidan" "Aaliyah kenan idan baki yana yagewa saboda magana da baki na ya yage. Abban ku da ki ke gani ba auren da zai yi. Lokacin auren marigayiya ma da ya aka yi ya aureta. Ku dai cigaba da yi ma sa addu'a har Allah ya ganar da shi gaskiya" Aaliyah ta kalli Jee ta ce " Abba ba zai iya auren kowacce mace ba amma akwai mace ɗaya da ta dace da shi" Jee ta zuba ma ta ido tana jiran ƙarin bayani. "Aaliyah Badamasi Bulama" "A ina kika san ta?" Jee ta faɗa da sauri "Na san komai Jee, komai. Ta riga ta gama idda, ki yiwa Abba magana dan Allah" Jee ta yi shiru tana tuna baya... *** Da ya san zai ganta har ya sa ta kuka da bai fita yau ba. She's went through alot, the last thing da zai mata shine ya sa ta kuka kuma gashi dalilin sa ta zubda hawaye. Yadda ya ganta she looks better than ranan da aka yi dinner ɗin retirement ɗin ta. "I'm sorry Aaliyah" ya furta a fili... Ƙarfe biyar Zaid ya zo gidan su. Ta tambayi Jee kafin ta fita, har Jee na tsokalarta wai ashe an kusa shan biki. Ganin Abba ba zai dawo ba sai bayan Isha ya sa ta gayyaci Zaid ɗin. "Wamako ya aka yi? ka gaya ma ta?" Ya girgiza kai "Why?" Ranƙwashinta yai ya ce "ba ki ga halin da ta shiga ɗazu da safe ba ne. Ki na so ta sake samun panic attack ne?" "Oh! sorry" "Kin gayawa granny ɗin ki?" With excitement ta ce "Yes, kuma ta ce yau da dare za ta ma sa maganar" "Thats good" Shiru ne ya ratsa cikin motar, ganin shirun yai yawa ya sa ta ce " barin tafi" Ya juyo a hankali ya na kallonta. Ganin kallon ya yi yawa ya sa ta tsargu "Wamako you're making me uncomfortable" "Why?" "Ehm ehm..." wayarta ya shiga ringing ta yi saurin ɗauka. Isma'il ne ya kira yana tambayar ina ta ke. "Ke da waye a motan?" Ya tambaya da ƙarfi bayan ta ce ma sa tana cikin mota. Dama ya shigo gidan ne Jee ke ce ma sa Aaliyah na hira a waje shine hankalin sa ya tashi. "Zaid" ta faɗa a hankali. Isma'il ya haɗiye wani abu da ya tsaya ma sa a maƙoƙoro, da ƙyar ya ce "sai kin shigo". Tana ajiye wayar Zaid ya ce "and who's calling?" "Yaya na" "Yayan ki? Listen girl i'm the only brother you've got. Ba na son shirme. 'Yar yarinya da ke har kin fara tara samari" ya faɗa yana hararanta. "Believe me Wamako, Yaya na ne, jikan Jee ne" "I see" "Allah fah" ta faɗa cikin sakalci... Su na cikin cin abincin dare Abdul ya ce "Abba wai Jee ta ce Princess ta yi saurayi" Abba ya ɗago ido yana kallon Aaliyah da ta yi wuri-wuri da ido Jee ta ce " amma yaron nan Allah ya maka albarka, abinda na ce muku sirri ne" Abdul ya ce "ban gayawa kowa ba fa, Abba kawai na faɗawa" Abba ya ce "Allah ya sanya alkhairi" "Abba he's just a friend" Aaliyah ta faɗa ganin yadda fiskar Abba ya chanja. Haidar ya ce " Abba and he got a very cool car" ya taɓa Ameer yana faɗin "Ameer miye ma sunan motar da ya zo da ita?" Isma'il ya kwaɓi bakin Haidar yana faɗin "gulman ya isa haka"... Tun da aka yi maganar saurayi ya loosing appetite ɗin sa bai fi sokali biyu ya ƙara ba ya tashi. Ba wai Its wrong ba ne Aaliyah ta yi saurayi, maganar ce kawai ta zo a wrong time. Yana shiga ɗakinsa ya fara shirin bacci, with all that happened today bacci kawai ya ke ganin zai sa ya ji sauƙin raɗaɗin da ya ke ji. Yana gama saka pyjamas na shi aka fara ƙwanƙwasa ƙofa. "Come in" Aaliyah ce ta shigo. "Abba i'm sorry, he's just a friend. Jee misunderstood everything" Murmushi yai ya ma ta nuni da ta zo gareshi. Ta ƙaraso ta rungumeshi. "I'm not angry, idan saurayi ne ma my Princess is old enough ai" Murmushi ta yi ta kuma shigewa jikin sa. Bayan fitan Aaliyah ya kwanta amma ko minti biyar bai yi ba aka fara kiran wayan sa ya duba ya ga Hajiya Jiji. Yana ɗauka ta ce ya sameta a ɗaki, cikin ran sa ya ke tunanin ƙila akan abinda ya faru a wajen dinning ɗazu za ta yi ma sa magana akai... "Lamiɗo ina neman alfarma a wajen ka" ta faɗa bayan ya samu waje ya zauna "Hajiya Jiji wani alfarma kenan?" Ya faɗa cike da raha. "Ina so ka yi aure, ka ga yanzu tsufa ta kamani ga shi Aaliyah ma ko ba jima ko ba daɗewa aure za ta yi. Haka za ka ƙare rayuwar ka cikin kaɗaici kenan?" Ya sunkuyar da kai ya rasa abin faɗa, wannan maganar tun suna ƙasar waje ta ke ma sa har su ka dawo Nigeria kuma har yau a wajen sa amsa ɗaya ce. Ba zai iya ƙara aure ba. "Ba ka ce komai ba" "Hajiya a ƙara min lokaci zan yi Insha Allah" "Sai Abdul ya yi aure ya hayayyafa?" "Hajiya kin san samun mace da za ta riƙe min 'ya 'ya na tsakani da Allah a yanzu akwai wahala. Ba na son na kawo wacce za ta watsar da kan 'ya'ya na" "Hujjar ka kenan koyaushe Lamiɗo, sai dai yanzu ba ka da wani fargaba domin wanda na ke so ka aura za ta riƙe ma ka 'ya 'ya tamkar ita ta haifesu" Ya ɗago da sauri yana kallonta da mamaki. "Hajiya idan ba damuwa maganar auren nan dan Allah mu bar shi. Idan da rabo zan yi a gaba amma ba yanzu ba" "Aaliyah na ke so ka aura" Ido ya zaro waje yana jin wani shock a tattare da shi. "Aaliyah ɗin dai da ka sani, 'yar marigayi Alhaji Bulama" "Hajiya!..." "Tunda Allah ya ba ka dama yanzu, sai ka yi amfani da damar ka" "Hajiya mijinta bai daɗe da rasuwa ba, ta ya zan fara irin wannan maganar" "Ka ji min shirme, Lamiɗo ta gama takaba fa, Aaliyah ta ce wata biyu da su ka wuce ta fita daga takaba. Mi ye a ciki idan ka nemi aurenta?".... Chatting ta ke lokacin da Abba ya buɗe ƙofar. Ta yi saurin ta shi zaune dan Its strange, Abba ba ya shigo ma ta ɗaki ba tareda ya ƙwanƙwasa ba. "A ina ki ka san Aaliyah Bulama?, ya aka yi ki ka san ta?, Princess yaushe ki ka fara shiga zancen manya" "Abba..." "Did you check my diary?" Ta taso da sauri ta shige jikin sa tana faɗin "Abba ka yi haƙuri, i saw it by mistake and i read it. Please ka yi haƙuri" Ta san lagon sa, ba ya taɓa iya juran ma ta faɗa. "Have you met her" ya faɗa a hankali "Yes, amma ba ta san ni 'yar ka ba ce" Ajiyar zuciya yai ba tareda ya ce komai ba... *** Zaid na dawowa daga gidan su Aaliyah kai tsaye sashen Mom ya shiga amma ba ta nan. Eliza da ke goge falon ya tambaya ta ce ma sa Mom na wajen Inna. Da sauri ya fita saboda ya san yanzu haka masifa ta ke wa Mom, kuma wallahi ba zai yadda ba, idan ta kai shi maƙura ma koranta zai yi a gidan. A hanya su ka haɗu da Mom ɗin. "Mom mi ta ce miki?" Mom ta yi murmushi tana faɗin "har ka dawo, yau Zahra ta sallameka da wuri kenan?" Hannun Mom ya kama ya ce " Mom dan Allah mi tsohuwar banzan nan ta ce miki?" "Zaid please. She's your grandmother ka daina kiranta haka" "Whatever"... A falon Mom ɗin su ka yada zango. Mom ta zauna a kujera shi kuma ya zauna a ƙasa ya ɗaura kan sa a cinyarta. A hankali ta ke shafa gashin sa ta ce "Son ya maganar ka da Zahra ne. Inna ta fara ƙorafi" "Mom ki ƙyale tsohuwar nan ta yi ta haukar ta ita ɗaya, idan ta gaji da kanta za ta daina. Ba ruwanta da rayuwata" "You're not gettting younger fa, ni ma ina son ganin grand kids ɗina" "Idan ki na so na yi aure nan kusa sai kin min wata alfarma" "Son minene? Ka san ba abinda za ka tambaya da ba zan ma ka ba" Ya ɗago da kan sa ya ce "first of all promise me ba za ki yi kuka ba" "Ok ba zan yi kuka ba" Hannunta biyu ya riƙe ya ce "Mom please ki amince ki auri Professor Sa'eed" "Zaid!" Ta faɗa da ƙarfi "Mom i know everything, you still love him, ki aure shi dan Allah. Your complete happiness is with him" Hawaye ne su ka fara gangaro ma ta yai saurin sa hannu ya fara gogewa. "Mom please stop crying, i just want you to be happy. Nobody will stop you from marrying him now. Nobody" "Zaid ya isa haka, ya isa. Abinda ka ke faɗi ba mai yiwuwa ba ne" Ya ɗaura kan sa a cinyarta ya fara kuka yana roƙonta. "Please Mom, please marry him" Tana kuka yana yi babu mai rarrashin kowa. Ƙarshe Mom ɗin ne ta janye jikinta ta shige ɗaki ta cigaba da kuka. Ina za ta iya auren Sa'eed, ya riga ya ma ta nisa. What will people say mijinta na mutuwa ko shekara bai yi ba ta auri tsohon saurayinta. Kai nooooooooo, ba za ta iya ba, ba ta tunanin ma za ta ƙara aure har ta koma ga mahaliccinta. She'll be 50yrs nan da wata biyu ma su zuwa tana da ɗa what else did she want da ya wuce ta cigaba da bautawa Allah har ta koma gareshi. Ba ta samu yin bacci ba sai chan tsakar dare.... *** Wasa-wasa waɗannan tsofin masoyan kowa yai biris da zancen sake haɗewan su. Ita Mom tana ba da uzurin ba za ta sake aure ba tayi girma a yin wani auren. Shi kuma Abba yana faɗin ko zai nemi auren Mom ba yanzu ba saboda ya yi wuri. Ganin Plan B bai yi tasiri ba ya sa Zaid da Aaliyah su ka activating plan C. Maiduguri Zaid ya je inda ya sanar da Amma halin da ake ciki tareda roƙon ta yiwa Mom magana ko za ta amince. Amma ta ji daɗin zancen nan ta kuma nuna ma sa za ta yiwa Mom ɗin magana. A wajen Abba ma Hajiya Jiji da Aaliyah haka su ka sashi a gaba. Ranan Aaliyah ta zauna a gabansa ta dinga yi ma sa kuka dole sai da ya amince akan zai auri Mom... Amma ta kira Mom akan tana son ganinta dan haka ta shirya ta tafi Maiduguri. Wannan ya sa Zaid yai wa Aaliyah magana saboda this is the perfect time da ya kamata Abba da Mom su samu daman tattaunawa... A kwananta na biyu da zuwa Maiduguri tana zaune a kan sallaya tana azkar sai ga Rabi mai aikin su ta shigo akan ta fito ta yi baƙo. "Baƙo kuma" ta faɗa cike da mamaki. Bayan fitan Rabi daga ɗakin ta cire hijabin sallar ta ta ɗau wani ta saka ta fito. Da sallama ta shigo falon tana kai dubanta ga inda baƙon ke zaune. Lokaci guda ta tsaya chak ganin baƙon da ke neman ta. Ta sunkuyar da kai tana ƙoƙarin daidaita numfashin ta yayinda bugun zuciyarta ya ke ƙaruwa. Ta fi minti uku tsaye kafin ta zo ta zauna tana faɗin sannu da zuwa. "Fatan kin wuni lafiya?" Ya faɗa yana kallonta, gaba ɗaya atakure ta ke, tsoro ta ke ji a chan ƙasan zuciyarta. "Lafiya, ya hanya" "Alhamdulillah" Shiru ya ratsa falon na wasu mintoti kafin ya ce "Hajiya Aaliyah na zo ne da ƙoƙon barata a karo na biyu, ina fata wannan karon Allah ya bani sa'a" Maimakon ta bashi amsa sai ta ce "Hamma ya iyali?" "Alhamdulillah suna lafiya, sun ma ce na gaishe ki" "Na gode" "Hajiya Aaliyah ki bani dama na turo magabata na" Ta zaro ido da sauri tana kallon sa. "Dan Allah ki bani dama" ya faɗa da raunatacciyar murya. Ta fara girgiza kai tana hawaye. "Hamma Sa'eed ka yi haƙuri dan Allah, ba zan iya ba. Mu haƙura da juna dan Allah" ta faɗa murya na rawa. "Ba zan iya haƙura ba, amma zan baki lokaci. Zan jira ki har lokacin da za ki amince da ni" daga haka ya tashi ya fita daga falon. Ta kifa kai ta fara kuka. Tana son shi, ba ta taɓa dena son shi ba, kuma ba za ta taɓa denawa ba. But marrying him is difficult, may be sabon da ta yi da rashin sa ya sa ta ke tsoron kasancewa tareda shi... Da dare Zaid ya kirata yana fushi da ita har da cewa idan ba ta auri Abba ba shima har ya mutu ba zai yi aure ba. "Zaid please, ba za ka gane bane" "Mom i dont give empty threat, idan kin shirya ganina unmarried har ƙarshen rayuwata shikenan kar ki auri Abba. Mom you love him, you always do. Ban san mi zai hanaki auren sa ba" "Son..." ya katse kiran kafin ta ƙarasa maganar. Ba Zaid ne kaɗai yai fushi ba harda Amma. Amma kan cewa ta yi tunda ba za ta yi auren ba ta tattare ta koma chan Abuja. "Amma ki gane..." "Mi ki ke so na gane. Ke fa ba yarinya ba ce da za mu dinga miki faɗa akan abinda kin sani alkhairi ne a gareki. Wannan mutumin kina son shi ba wai bakya son shi ba, amma ki dinga hukunta kan ki saboda tsoron mutane. Mace ba ta taɓa girma a aure balle dukan ku biyu rufawa junan ku asiri za ku yi. Iyalin sa ta rasu ta bar mishi 'ya'ya shin ba za ki aure shi ki kula ma sa da yara ba ki samu lada a wajen Allah" "Shikenan Amma na amince, na amince" ta faɗa tana goge hawaye. *** Ƙarfe shaɗaya na dare har ta kwanta Zaid ya kirata yana faɗin Mom ta amince. Aaliyah ta sa ihu tana rawa, ita ta manta ma dare ne. Sai da ta ji muryan Abba na faɗin "Princess are you Ok?" "Yes Abba i'm just happy" Ita kaɗai a ɗaki ta fara taka rawa, ba dan dare ba ne da ba abinda zai hana ta kunna kiɗa ta tiƙa rawa... Sati ɗaya bayan amincewar ta aka ɗaura auren *Aaliyah Badamasi Bulama* da *Prof Sa'eed Aliyu Modibbo* bisa sadaki dubu hamsin. A cikin Compound ɗin gidan su aka ɗaura auren kuma ba laifi mutane sun zo duk da ma abin ya zo unplanned. Da ya ke bazawara ce ba wani hidima da za ayi. Tarewan ta sai nan da sati biyu dan haka sai lokacin za ayi waliman tarewarta. Kamar wata budurwa ko kuma yarinya haka Amma ta kirayo mai gyara daga Niger aka fara gyarata. Ga mutanen Borno ma ba a barsu a baya ba suma suna na su. Gaba ɗaya kunya ma takeji wai da girmanta ake ta mata wannan gyaran. Tun gyaran da aka mata lokacin haihuwan Zaid ba ta sake yin wani gyara ba. Kullum sai Zaid ya kirata sun yi hira yana tambayar lafiyarta... Yana dawowa daga sallar Isha ya taradda Inna tana ta zuba masifa. Bai kulata ba ya wuce zai haura sama ta ce "zo nan dan Uban ka. Kai ne ka goyawa uwar ka gindi akan ta yi aure. Watan Ahmad nawa a ƙasa har za ta yi aure, wato bayan ta kashe shi shine za ta auri tsohon kwarton ta ...." Saukar mari ya hanata ƙarisa maganar. "Look old woman, yau ne rana ta ƙarshe da za ki disrespecting mahaifiyata na ƙyale ki. Wallahi duk hatsabibancin ki na fiki. Ba abinda zai hana na fasa miki kai da bindiga. Idan auren Mom ya tsole mi ki ido ke ma ki je ki yi mana, na ga kema bazawarar ce" "Zaidu, Zaidu ni ka mara?" " mayya, munafuka, hatsabibiya, annamimiya, killer, inaga ma cin naman mutane ki ke yi ɗanye shiyasa ki ke da taurin rai haka. Dama 'yar maharba kan ai sai haka" ya nuna kan sa ya ce "kin gan ni nan, wallahi na fi ƙarfin ki. Idan ba ki yi hankali ba kwanan nan zan aika ki inda ki ka aika mijin ki da sauran mutanen da kika kashe" Inna ta yi zaman dirshan tana kuka wai jikan ta ke gaya ma ta maganganu haka. Gaskiya ba zai yiwu ba. Ita da ta ke burin ya shiga harkan siyasa, nan da shekaru kaɗan ya nemi kujerar Gwamna. Hajiya Fatima ne ta shiga bawa Inna haƙuri tana ƙoƙarin ɗaga ta. Inna ta ce "bar ni Fatima, bar ni na yi kukan takaici. Wai yau dan ba Ahmad shi ne ɗan sa ke ci min mutunci haka. Wallahi da shi da Uwar sa sai sun ci uban su. Gaba ɗayansu sai na nuna musu ko wacece Hajiya Asma'u Wamako" *** Walima aka yi mai lafiya ranan Alhamis, anci an sha kuma an yi wa'azi. Ranan Jumu'ah Zaid ya taho da Mom Abuja. A airport Abba da tawagar sa su ke jiran su. Gaba ɗaya kunya Mom ta ke ji, wai yau ɗan ta ne ke rakata gidan miji. Ganin Aaliyah kusa da Abba ya sa ta fara kallon Aaliyar tana kuma kallon Zaid da mamaki Aaliyah ta yi dariya ta ce "Yes Mom, i'm his daughter" Abba ke jan motar Mom na gaba yayinda Zaid, Aaliyah da Abdu ke baya. Ɗaya motar kuma Isma'il ne sai Ameer da Haidar aciki... Abba ne ya fito da sauri ya buɗewa Mom ƙofa tana fitowa ya saƙala hannunta cikin na sa ya ce "welcome home my love" ta yi murmushi. Aaliyah da ke gefe ta ce "ohh so Cute" Zaid ya ja kumatunta ya ce "gulma ko"... Jiji aka bari a gida, itama ta sha ado tana jiran ma'auratan. Tana shigowa Jiji ta sa kabbara tana faɗin "Alhamdulillah, Allah na gode da ka sa na ga wannan rana. Marhaba marhaba zuciyar Lamiɗo" Mom tana ƙoƙarin tsugunnawa ta gaida Jiji Jijin ta hanata tana faɗin " a'a Aaliyah Jijin ki ce fa" Sai ga hawaye a idon Mom. "Kul ki ka yi kuka, yau ranan farin ciki ne"... Bayan an zauna Aaliyah ta je ta ɗauko cake ɗin da aka ordering, ɗaya ɗauke da Happy birthday ɗayan kuma Happy married life. Yau Mom ke cika shekara hamsin a duniya. Tare su ka yanka cake ɗin yayinda Isma'il ya ke recording wajen a cameran Aaliyah. Da aka gama aka fara ɗauke-ɗauken hoto. Aaliyah ta je ta kunna kiɗa falon gaba ɗaya ya ɗauka. Mom da ke zaune tana ta zuba murmushi ta je ta kamo hannunta ta ce Mom lets dance, today Its a happy day. Mom day tsayuwa ta yi tana murmushi yayinda Aaliyar ke ƙoƙarin girgiza ta. Kafin ka ce me sauran mutanen ma sun joining barin ma Haidar da ke son rawa kamar me. Jiji kawai aka bari zaune tana kallon su tana dariya. Mom ma ta ɗan fara takawa yayinda Abba ya fito da kuɗi yana mata kari. Ganin yadda Aaliyah da Zaid ke rawa har wani tattaɓata ya ke ya sa Isma'il zare jikinsa ya bar falon, ɗazu da Zaid ke shafawa Aaliyah icing sugar a fiska sai da ya ji kamar zuciyarsa za ta bulluƙo. Dole ya bayyana ma ta abinda ke zuciyar sa kafin maganar Jee ya tabbata. A ƙalla sun kai two hours ana bidiri, anci an sha kuma an girgije. Ganin maghriba ta doso ya sa aka fara tattara wajen. Abba ne yaiwa Mom jagora zuwa ɗakinta. Kissing goshin ta yai ya ce barin je masallaci ko. Ta gyaɗa ma sa kai. Bayan ya fita itama ta shiga banɗaki ta watsa ruwa sannan ta ɗauro alwala... *** Sallama yai ya shigo ɗakin matar na sa kuma masoyiyar ta sa. Tana zaune a sallaya tana jan carbi. Ya ƙaraso ya tsugunna wajenta ya ce "amarya ki zo ki min rakiya mana" yana maganar yana shinshina wuyanta. "Ka bani minti biyar dan Allah" "Take your time my love" ya faɗa yana komawa kan gado. Da ta ƙarisa addu'an ta naɗe sallayar ta ce "na gama" Ya kamo hannunta ya ma ta jagora zuwa ɗakin sa. Sallah su ka gabatar raka'a biyu sannan ya kawo mata kazarta. Tana gani hawaye ya fara zubo ma ta, tunowa ta yi da Ahmad, yadda first night ɗin su ta kasance. "I'm sorry Aaliyah, dan Allah kar ki yi kuka, dan Allah" Ta gyaɗa ma sa kai tana sa hannu za ta goge hawayen ya riƙe hannun matsowa yai sosai ya sa harshen sa ya fara lashe hawayen. Wani yaar ta fara ji ajikinta, haka ya lashe hawayen nan tas. Kaɗan ta ci naman ta ce ya isheta. Ita ta fara shiga banɗaki ta wanke bakinta kafin ta fito shima ya shiga. Yana fitowa ya kashe wuta ya bar dim blue light na ɗakin. Dogon hijabin jikinta ya cire, tana tsaye idon ta a ƙasa, gaba ɗaya kunyan sa ta ke ji. Ƙaramar rigan bacci ta sa ja. Hannunsa da ya kai yana shafa bayanta ya ci karo da tabon ciwuka. Tausayinta ne ya shigeshi. He promised to make her fill happy ta kowanni fanni. "I love you" ya raɗa ma ta a kunne. Wuyanta ya shiga kissing a hankali, yana yi yana shafa bayanta. Tun daya fara taɓata ta ke jin jikinta na amsa saƙonnin sa. A hankali ya fara ƙasa-ƙasa da riganta har ta faɗo ƙasa. Bakin su ya haɗe yayinda hannun sa ɗaya ke wasa da nipple ɗin ta. She missed the taste of his lips, she missed everything about him. Yadda kiss ɗin ke fizgar ta ya sa ta sa hannunta duka biyu ta ƙara jawoshi jikinta sosai. Lokacin da ya raba bakin su hannu ya sa yana shafa fiskarta. "I love you Aaliyah, I love you very much" ta yi saurin kama bakinsa tana tsosan su a hankali. Ji ta ke su dawwama kawai a haka. Ya sa hannu fara ƙoƙarin cire jallabiyar sa ta sa hannu ta ƙarisa cire ma sa. Bakin su sarƙe cikin na juna su ka sauka akan gadon. Sun jima suna yin passionate kiss kafin ya janye bakin sa zuwa nipples ɗin ta, the way he's sucking it ya banbanta da Ahmad. Idan Ahmad na yi daga ta fara jin daɗi kaɗan sai ya koma zafi ko dan dama tun farko ya saba yi mata na mugunta ne oho. Yana tsotsan ɗaya yana shafa ɗaya. Haka ya ringa exchanging ɗin su. Age is just a number when it comes to sex. At 50 tanajin ta a lokacin kamar wata yarinya. Yadda Sa'eed ke tafiyar da komai a hankali ya sa ta sake gigicewa. Bakin su a haɗe ta ji hannusa a ƙasanta, already dama gashi ta riga ta fara jiƙewa. Clitoris ɗin ta ya ke shafawa a hankali kafin daga baya ya sa yatsar sa ɗaya. Ji ta ke kamar ta yi ihu saboda yadda wani daɗi ya ziyarceta. Ba dan bakin su na haɗe ba da ƙila ihun za ta yi. Ƙasa yai da kan sa yana kissing ƙirjinta zuwa cikinta zuwa ƙafanta. Babbar yatsar ƙafanta ya sa a baki yana tsotsa yanayi yana shafa clitoris ɗin ta da yatsar sa ɗaya. Ta rufe ido kawai tana jin daɗin jikinta. She nearly scream lokacin da Sa'eed ya sa harshensa a ƙasanta. It was a different feeling tun tana iya daurewa har ta sa ƙafa ta matse Sa'eed tana ƙoƙarin shafa kansa tana sauke ajiyar zuciya akai akai... Addu'ar saduwa yai sannan ya cusa abunsa cikin abunta. A hankali ya ke turawa yanayi yana shafa nipples ɗin ta....... "Ah Ah Ah" Ya ɗan tsaya ya kalleta ya ce "pain?" Idonta a rufe ta ce "pleasure" Murmushi yai ya ce "i love you Aaliyah" sannan ya haɗe bakin su ya cigaba da swinging abunshi cikin abunta. Wata duniya ta ji ta daban like kamar a iska ta ke tafiya... Its true, duk daɗin sex idan da masoyi ne to daɗin na daban ne. *29-Confused Hearts* Kallon juna su ke cike da so da ƙauna. Nitsuwa ne ya sauka mu su bayan dukkan su sun samu gamsuwa, the beauty of it shi ne bayan gamsuwan da su ka samu akwai tarin lada a abinda su ka yi. Sa'eed ya kissing goshin Aaliyah ya ce "Baby mu je mu yi wanka ko?" Ta gyaɗa ma sa kai fiskarta ɗauke da murmushi. Tana ƙoƙarin tashi ya ɗauketa. "Sweetheart na fa ƙara jiki" "Ina jikin ya ke?. Ban da shekaru ba abinda ki ka ƙara Baby" "I love you" ta faɗa tana manna ma sa light kiss a bakin sa... Bayan sun yi wanka sun fito su ka kwanta rungume da juna, bacci mai daɗi, mai ni'ima ya ɗaukesu.. *** Washe gari bayan sun yi sallar Asuba su ka sake komawa bacci. Abba ne ya fara tashi lokacin ƙarfe takwas ta ɗan gota, bai tasheta ba ya fito. Aaliyah ya samu tana haɗa mu su breakfast, gefenta kuma Isma'il yana ta ma ta tsiya. "Good morning Mr Ango" ta faɗa lokacin da Abban ya ƙaraso gefenta. "Morning Princess, mi ake haɗa mana ne?" "A special breakfast for the best couple of the year" "Cika baki, Abba kar ka kulata ba abinda ta iya. Duk kame-kame ne" Aaliyah ta juyo ta harareshi ta ce "wannan kuma ƙaryan ka Malam" Abba ya ce "da mi zan taimaka mi ki?" "Abba dont worry, i got this. Ka je ka huta breakfast will be ready in a few minutes" Ya ce ma ta Allah ya miki albarka kafin ya fita daga kitchen ɗin. Abba na fita ta ɗeba ruwa a kofi ta watsawa Isma'il. "Wayyo Aaliyah!" "Ni ne ban iya komai ba ko?. Zan ga mai ba ka abinci a gidan nan yau" "Haba cooker, Haba our honorable great Chef. Tuba na ke ranki shi daɗe" Ta murguɗa ma sa baki kafin ta cigaba da abin da ta ke yi. Shi kuwa ya bi bayanta da kallo thinking about how to break his feelings for her... Abba na shiga ɗaki ya samu Mom ta tashi tana gyara gadon na su. Ya ƙaraso ya rungumeta ta baya ya ce "good morning light of my soul" "Morning my heartbeat" Kissing ɗin wuyanta ya farayi yanayi yana shafa ƙirjinta. "Sweetheart zan je na haɗa breakfast fa" "Kar ki damu ga breakfast ɗi na nan" Dariya ta fara tanajin daɗin yadda ya ke murza ma ta nipples ɗin ta. "Zan iya samun breakfast ɗin kuwa?" Ya faɗa bayan ya juyo da ita su na fuskantar juna. Ta girgiza kai. "A taimaka dai" ya faɗa yana langwaɓe kai. Ta sake girgiza ma sa kai. "Shikenan, na haƙura sai lunch" Murmushi ta yi ta ce "idan ya kai lunch ai ya zama ɗumame. Barin serving na ka hot hot" tana gama maganar ta haɗe bakin su. Ita ta ja ragamar breakfast ɗin na su. It was the first time she's on top, and she enjoyed it, Abba ma breakfast ɗin nan ba ƙaramin daɗi ya ma sa ba, especially da ya ke ita ta ke serving na shi... Ƙarfe goma ta ɗan gota Abba ya fito ya ɗauko mu su breakfast. Gaba ɗaya yaran kowa ya karya, da ke weekend ne duk su na gida ba makaranta... *** Washe gari ƙarfe biyar Aaliyah da Mom na girki a kitchen wayar Mom ya fara ringing. Tana ɗauka ta ga Zaid ne dan haka ta sa wayan a handsfree. "Mom ya kwanan amarci?" Aaliyah ta zaro ido a ranta ta ce "lallai Zaid ba shi da kunya" Mom ta ce " lafiya. Ya ka ke?" "Gani nan dai gidan ya min faɗi. I miss you, gaba ɗaya gidan ba daɗi wallahi" "Ya su Inna?" "That witch ta yi tafiya, ko ina ta je oho. Allah ya sa kar ta kuma dawowa ma" "Thats too harsh son" "Yawwa Mom ina guntuwar yarinyar nan?" "ni ba guntuwa ba ce" Aaliyah ta faɗa da ƙarfi. "Ka ji ai, ka dena kiran 'ya ta guntuwa" "Mom 'yar kin nan ta raina ni dayawa. Ko da ya ke na san mi zan ma ta" Mom ta sa dariya. "Zan zo gidan ai, i will surely punish her" "Ba ka isa ba kuwa, ba abinda za ka yiwa 'yata" Kashe kiran yai bayan ya tabbatarwa Mom cewa zai zo yau ɗin... Bayan Sallar Maghrib da su Abba su ka dawo daga masallaci sai gashi tare da su. Aaliyah na saukowa ta hangoshi zaune kusa da Abba yana ta zuba zance. Ta haɗe rai ta zo za ta wuce su Abba ya ce "Princess ba za ki gaida yayin ki ba" "Sannu Yaya" abinda ta faɗa kenan ta wuce dinning, already Mom tana wajen ta fara serving abincin. Aaliyah ta sa ma ta hannu su ka ƙarisa. "Yallaɓai Bismillah" Mom ta faɗa tana murmushi. Abba ya kama hannun Zaid ya ce "Son lets go and eat"... Jee da Isma'il ne ba sa wajen. Jee saboda ba ta cin abincin dare sai ta yi sallan Isha, shi kuma Isma'il dalilin Zaid ne ya sa bai fito ba. Tunda ya ganshi a masallaci hankalin sa ya tashi. Ya sani Zaid wajen mahaifiyar sa ya zo amma kuma zuciyarsa tana gwada ma sa cewa Zaid ya zo ne saboda Aaliyah, shiyasa ya kasa fitowa.... Su na cin abinci amma duk lokacin da su ka haɗa ido sai ya kashe ma ta ido. "Mom kin ga abinda ya ke min ko?" Zaid! Mom ta faɗa da ƙarfi. "Mom ni me na mata? Sharri kawai ta min" Abdul yai saurin cewa "i saw it too. Abba kalla haka ya ke ma ta" ya fara ƙyafƙyafta ido. Abba ya ce " na gani, ka cigaba da cin abincinka" Zaid ya fara sosa kai ita kuwa Aaliyah ta ma sa gwalo. Bayan sun gama cin abinci Abba, Zaid da yaran su ka wuce masallaci dan yin sallar Isha... Bayan ta idar da sallah ta kwanta tana jan carbi ƙwasam sai ta ji ana ƙwanƙwasa ƙofar ɗakin ta. Ta ɗan miƙe zaune ta ce "come in" Zaid ne ya shigo ɗakin yana wani murmushin mugunta. "Shi ne ki ka haɗa ni da Mom ko?" Ta murguɗa ma sa baki. Ya sa hannu ya tallafota yana faɗin "wannan baki mai shegen rashin kunyan nan i have to punish it" kafin ta ce wani abu ya haɗe bakin su, sosai ya shiga kissing ɗin ta abin mamaki maimakon ta tureshi sai ta shiga maida ma sa martani tana kissing ɗin sa tana cusa hannunta cikin gashin kan sa mai santsi.... "Princess, Princess" muryan Abdul ya fargar da ita daga baccin da ta ke. "Wai ki je inji Yaya Zaid" yana gama faɗin haka ya fita da gudu. Ta sa hannu ta shafa lips ɗin ta. Why on earth will she dream about him? And such an absurd dream ma. Ta jima tana tararradin fita kafin daga baya ta samu courage ɗin fitowa. Yaran kawai ta samu a falo lokacin da ta fito inda su ka ce ma ta Zaid ya na waje. Ta ja dogon numfashi kafin ta fita, straight wajen motar sa ta nufa dan ba ta ganshi a compound ba. Sunkuyar da kan ta tayi lokacin da ta shiga motar, tsoron haɗa ido da shi ta ke saboda kunyar mafarkin da ta yi. "Tsabar kin raina ni sai yanzu za ki fito?" "Ka yi haƙuri sallah na ke" ta amsa still kan ta a ƙasa. "Look at me!" Ya daka ma ta tsawa. A hankali ta ɗago ido ta kalleshi yayinda ƙirjinta ya fara bugun uku-uku. "Miya same ki ?" "Babu" ta faɗa a hankali avoiding his eyes. "Kunyi faɗa da saurayin ki ne?" Ta girgiza kai "Oh! Ashe kin ce ba ki da saurayi. Ƙwaila kawai" "Ni ba ƙwaila ba ce" ta faɗa a hankali. "Barin duba to" ya kai hannun sa zai taɓata ta yi saurin haɗe jikinta waje guda tana kare ƙirjinta da kyau. Saukar ranƙwashi ta ji a kan ta sannan ya ce "ni mi zan taɓa a jikin ƙasusuwa" Sai da ta sake jikinta sannan ya fara magana. " ina son shiryawa Abba da Mom surprise honeymoon trip, wani ƙasa da wani ƙasa ki ke ganin ya kamata su je" "I dont know" "Zan kwaɗe kan ki fa. Ina tambayar shawaranki ki na ce min I dont know. To wallahi you must know" Ta yi shiru na ɗan wasu seconds kafin ta ce "tunda an kusa fara azumi why not su je Umara, ka ga sai su yi honeymoon tareda ibadar su a chan". "Baby ashe dai kwanyar ki na ja"... *** Wani lokaci zuciyoyin mutane biyu na haɗuwa ba tareda sun shirya ba. Gangan jikin su zai zama sun banbanta amma zuciyoyinsu sun jima da zama ɗaya. Soyayya mai daɗi, mai tsabta, mai cike da farin ciki Aaliyah da Sa'eed ke shimfiɗawa a gidan na su. Bi sa shawaran Aaliyah, Zaid ya biya wa Abba da Mom Umura. Da farko Abba ya ƙi daga baya da Zaid ɗin ya roƙeshi sannan ya amince. Saura kwana biyu su tafi Mom ta je yiwa su Inna sallama. As usual sai da Inna ta zageta tatas tareda cewa kar ta ƙara zuwa wajenta tunda yanzu alaƙa ta tsinke. With heavy heart haka Mom ta bar gidan... Yau aka ɗau azumi, gaba ɗaya gidan yai wani iri ba daɗi. Ɗan zaman da Mom ta yi kafin su tafi Umara ba ƙaramin chanji su ka gani ba. Dama gida shi ne mace, duk gidan da babu mace sai a hankali cause its not complete. Hatta Abba sun ga chanji tattare da shi saboda yadda kullum ya ke cikin farin ciki... Bayan an sha ruwa an idar da sallar Magarib su na cin abinci sai ga Zaid a gidan. Zuwa yai ya duba su dan tun ranan da su Mom su ka tafi bai ƙara zuwa ba. Daga falo ya zauna bai ƙarisa wajen dining ɗin ba. Jee ta ce ya ƙariso ya ci abinci ya ce ya riga ya ci. "Inaga kunya ya ke ji, Aaliyah maza kai ma sa ko kunu ne ya sha" "Jee tunda ya ce ba ci zai yi ba, Allah ba ci zai yi ba" " ba na son rowa, Yayan kine kai ma sa wani abu ya sa a baki" "Jee ni kan..." ta faɗa tana turo baki... Tunda ta fara takowa ya ke kallonta har ta ƙariso gaban sa ta ajiye plate da mug. Tea ne sai french fries a cikin plate da ketchup a ɗan gefen plate ɗin. Za ta bar wajen ya ce zo nan. Yadda ya ke bin lungu da saƙo na ta da kallo ya sa ta tsargu har ta fara jan rigan ta ƙasa. "Kin san bai dace ba ki ka saka" Short gown ta saka wanda ya tsaya ma ta iya gwiwa. "Acikin Azumi ki ke saka irin waɗannan kayan, so ki ke ki karyawa tuzurai Azumi?" "Tuzurun ai ba a gidan ya ke ba" ta faɗa tana turo baki "Oh really" Ta juya za ta tafi ya ce "na sallameki ne?" "Wamako abinci na ke ci fa" "Je ki chanja kayan nan" "Amma..." "Now!" Cikin zuciyarta ta ja doguwar tsaki kafin ta haura sama. Dogon hijabinta na sallah ta saka ta fito. Kafin ta wuce dinning ɗin sai da ta watsa ma sa harara. Da ta koma Ameer ya ce yau kuma Islamiyya ki ka tuno. "Ina ruwan ka!" Haidar ya ce " ba fa shi ya kar zomon na" Ta harareshi. Su na ƙarisa cin abinci ta tashi da sauri ta haura sama kar ma ace ta yiwa Zaid wani bauta. Zaid bai tafi ba sai ƙarfe tara da rabi bayan sun dawo daga sallar tarawih. Tana ganin kiran sa ta share shi. Haka ya tafi ba tare da sun kuma haɗuwa ba. Bayan mafarkin da ta yi ranan ta rasa gane ma zuciyar ta. Ta kan yi tunanin sa a koyaushe, ba ta san ma'anar hakan ba. And duk ranan da ya zo gidan haka za ta dinga jin bugun zuciyarta na ƙaruwa idan tana kusa da shi. Tun daga ranan har aka gama Azumi sai ya zo gidan, yawanci ya fi zuwa da yamma kafin a sha ruwa hakanan ba koyaushe ya ke tsayawa ya sha ruwa a wajen su ba. *** "Ban gane na baki kuɗi ba. Kuɗin ma this huge amount" "Dan na tambayeka kuɗi sai na gaya ma ka abinda zan yi da su. Zaid ka na da hankali kuwa" "Ofcourse zan tambaya mana. A witch asking for money ai yana nufin za a yi farfesu da kan wani kenan" "Allah ya tsine ma ka Zaidu, ni za kira da mayya. Uwarka ce mayya, na ce Uwarka Aaliyah ce mayya" Zaid ya kwashe da dariya ya ce "kai Asma'u kina da abin dariya wallahi. Yanzu ba ki ji kunya ba calling my Mom Mayya bayan ke ce Mayyar. Look old woman, naira ɗaya ba za ki samu ba balle 5M. Ki na ci ki na sha ki godewa Allah" yana faɗin haka yai gaba. "Zaidu, Zaidu, Zaidu" Ta cize leɓen ta tana tunanin dole ta yi abinda ta yi niyya akan Zaid. Idan ta barshi haka ba ƙaramin walaƙanci zai ma ta ba... Ranan Sallah da ya je gidan aka ce ma sa sun yi tafiya. Takaici ya ishe shi har wuya. Ta ya za su yi tafiya ba tareda sun gaya ma sa ba. Ya buga steering da ƙarfi yana faɗin shit. Ana dawowa daga masallaci su ka wuce Bauchi. Mahaifiyar Isma'il ce ba lafiya har an kwantar da ita a Teaching Hospital. Bayan sun gaisheta aka bar Jee da Isma'il yayinda su suka wuce Durum. Bayan ta shirya za ta kwanta ta kira Zaid dan ta sanar da shi abinda ya faru ta ji numbar sa a kashe, ta kira ɗayan ma a kashe dan haka ta tura ma sa saƙo amma shima bai tafi ba. "What could be happening?" Ta tambayi kanta cike da kewar sa *30-Karma* Iya maƙura Zaid ya kaita. Ba za ta bari ya ɓata ma ta shirinta ba balle ya ma ta katanga da dogon burinta ba. Sunan Hajiya Asma'u Wamako ta ke so a buga a shafin farko na manya-manyan jaridun ƙasar haka nan tana so duk kafafen yaɗa labarai ayi ta maganar ta a wannan rana... Tafiya ce ta kama shi na kwana huɗu dan haka duk da ya san a cikin kwanakin su Mom za su dawo bai fasa tafiyar ba, haka nan ko sallama bai je ya yiwa su Aaliyah ba. Tun ranan sallah rabon sa da gidan su. Ranan da zai wuce airport ya ga ana ta kan shigowa da kaya cikin gidan, ya tambaya aka ce ma sa Inna ce ta yi ordering ɗin su. Bai da lokacin ta dan haka ya wuce ba tareda ya yi magana ba... Wani baƙin jewelry box ta buɗe sai ga wata sarƙan pure diamond aciki yana ɗaukan ido. Ta sa yanƙwanannen hannunta ta fara shafa shi. Ahmad ne ya siya wa Aaliyah, kyautar da ya ajiye kenan zai ba ta ranan 50th birthday ɗin ta, Allah bai yi ba. Da ke duk wani shige da fice na shi ta sani shiyasa ranan da ya kawo sarƙan gidan ma sai da ta gani, da ta tambayeshi sai ya ce na Aaliyah ne. *"Ahmad sarƙan lu'ulu'u za ka bawa Aaliyah. A dalilin me?"* *" saboda ina son ta, saboda ta chanchanchi fiye da haka. Idan akwai abinda ya fi diamond ni Ahmad zan siya ma ta"* *"Ahmad ina raye za ka siyawa matar ka diamond"* *"ki na raye zan ba ta duk wani abu da na mallaka, saboda duk abinda na samu to ta dalilin ta ne"* *"wallahi ba zai yiwu ba. Allah ya kiyaye"* Tun rashin lafiyar Ahmad ta ɗauke sarƙan, tun kafin ma Hajiya Fatima ko ɗaya daga cikin 'ya'yan sa su gani. Ta ɗaura sarƙan akan wuyanta tana kallon kanta a madubi. Ba ƙarya sarƙan ya haskata, tun da ta ke wannan ne karo na farko da ta taɓa saka diamond, duk ƙaryanta ya ƙare a gwalagwalai. Bari a ƙare hidimar nan ta waiwayi Zaid sai ya ƙwammace ƙiɗa da karatu. Maƙudan kuɗi ta saka a wannan hidima, yau ba dan Zahra MCcollins ta taimaketa ba da Zaid ya sa ta ji kunya a idon duniya. Cake kaɗai da za a ma ta 1.2M ne, domin sawa ta yi a designing cake mai kamar statue ɗin ta. Jin kamar ƙaran ƙafar mutum ya sa ta yi saurin maida sarƙan cikin box ɗinsa ta rufe tana leƙen ƙofa... *** Ranan da su Mom su ka dawo, su Aaliyah 'yar ƙaramar walima su ka shirya mu su. Farin ciki a gidan har yai overload. Ganin Zaid bai zo gidan ba har dare ya sa Aaliyah ta tambaya a fakaice. "Mom amma Ya Zaid bai san yau za ku dawo ba?" "Ya sani. Ba ya ƙasar ne, jiya ya wuce Michigan" "Oh" ta faɗa ƙasa-ƙasa tana tunanin ko mi ta yiwa Zaid ya shareta iya waɗannan kwanaki... Gajiya ne a tattare da su. Tare su ka yi wanka su ka kwanta Abba ya ce "ya kamata na yiwa Hajiyata massage" "Alhaji na ka huta na san kai ma akwai gajiyar a tattare da kai" "Kin san indai hidima wa Hajiyata ce ba na gajiya" Juyar da ita yai ta kwanta rub da ciki ya shiga daddanna ma ta kafaɗa zuwa baya. A hankali ta fara jin daɗin jikinta saboda yadda muscles na ta ke warwarewa. Kusan minti biyar yana yi kafin a hankali ya zare rigan baccin da ta sa. Yadda ya ke daddana bare back ɗin ta ya ke ƙara godewa Allah da ya sa daga ƙarshe ya samu Aaliyar sa. Duk lokacin da ya ga tabon jikinta sai ya ji ba daɗi a ransa, yana jin raɗaɗi sosai idan ya tuna cewa tabon jikinta tabon duka ne. Tashi yai ya je wajen dressing mirror ɗin su ya ɗauko kwalban man zaitun. Da ya dawo ya tsiyayi zaitun ɗin a hannunsa ya fara shafa ma ta a bayanta zuwa ƙafafuwanta yana yi yana mammatsawa a hankali. Da ya gama ya juyo da ita tana kallon sa tana murmushi. Nan ɗin ma zuba ma ta zaitun yai a ƙirji zuwa ciki yana shafa mata yana daddanawa a hankali. Maida hankalin sa kan ƙirjinta da yai ya sa ta fara jin abin ya bar massage ya koma wani abu daban. Saukuyo da kan sa yai ya fara tsotsan nipples ɗin ta. "Alhaji na ka sake layi fa" "Hajiyata i'm trying to massage them very well ne" Ta yi murmushi kawai tana cigaba da jin daɗin abin da ya ke yi. Chan ya ɗago ya cire rigan pyjamas na shi yana gamawa ya cire wandon ma. Ya tsiyayi zaitun ya shafa a ƙirjin sa hannunsa da ƙafarsa. Kwantawa yai a kanta yana goga mata jikin sa yayinda hannunsa ke ƙasanta yana yiwa wajen massage. "Alhajina wannan massage ɗin salon sa daban ya ke" "Hajiyata wannan nuru massage kenan" Ta lumshe ido tana murmushi. Bai jima ba itama ta shiga maida ma sa martani ta hanyar massaging ƙirjin sa zuwa abun sa da ke miƙe, daga ƙarshe su ka sealing massage ɗin da passionate love. ........... Idan Shugaba ba zai iya aikin ba miyasa zai ɓa ta ma ta lokaci. Basussukan da ta ci ta ci ne da zimmar tana samun kan Zaid za ta umurceshi da ya biya. Ta ya Shugaba zai ce ma ta abin da ta ke so ba mai yiwuwa ba ne, idan ta iya juya ɗan ta a lokacin baya taya juya ɗan sa zai gagareta. Ko da ya ke ta wani ɓangaren Shugaba ya yi gaskiya domin Aaliyah ce ta ɓata ma ta aiki a ƙarshen rayuwar Ahmad haka nan ita ce dalilin da ya sa ba za ta iya juya Zaid ba. *matuƙar mahaifiyar sa na raye ba za ki taɓa iya komai a kan sa ba. A kowani wayewar rana sai ta roƙa ma sa tsari daga safe har dare. Ni ba na yiwa mutum ƙarya, idan zai yiwu zan faɗa idan ba zai yiwu ba ma zan faɗa. Ki hakura da manufar ki akan jikan ki, gargaɗin da zan miki kenan* Tunda abin ya gagari Shugaba ta nemi Bokayenta na baya ko za a samu wanda zai iya. Idan ta kama a kashe Aaliyar ne ma ai ba komai ba ne amma tabbas sai ta juya Zaid. Yaro sai shegen taurin rai Uban sa bai bata ciwon kai ba sai shi, nawa aka yi shi. Ba dan jinin da ke tsakanin su ba ma da ba abin da zai hana ta sa a hallakashi amma shi kaɗai ne ɗan da zai rinƙa tuna ma ta da Ahmad... Waya kawai ta yi ta samu abinda ta ke so, cewa aka yi gobe ta zo ta karɓi maganin kuma ta shirya wa hakan. Washegari duk da baƙi sun fara isowa haka ta sa dreba ya wuce da ita chan wani ƙauye a Okene. Shi ma dai kusan kashedin Shugaban ya ma ta amma shi ya sama ma ta mafita. Jaddada ma ta yai cewa indai mahaifiyar Zaid na raye to ba za ta taɓa samun galaba akan Zaid ba, sai dai ya bata abinda zai sawwaƙa ma ta wajen kawar da Aaliyar. Ta amshi abin ta nufo Abuja wanda ba su iso ba sai ƙarfe bakwai na safe. Duk ma su tambayar ina ta je sai ta ce duk acikin shiri ne. Ba wanda yai tunanin wani abu sai dai ana ta gulmammakin almabbazarancin da Innar ke shirin yi saboda bikin birthday ɗin cika shekaru saba'in da biyar da za ta yi ranan Asabat. Generators, microwave, fridge, gas cooker, standing fans, electric oven da android phones, abinda Inna ta shirya rabawa a wajen wannan biki kena, shiyasa bikin strictly by invitation ne... Lunch su ke ci lokacin da Inna ta kira Mom. Da mamaki ta ɗau wayar tana tararradin mi Innar za ta ce. Ta sake baki lokacin da Innar ke gaya ma ta batun birthday party da za ta yi ranan Asabat. "Na ce ko za ki zo anjima ki ƙarɓi kayan ashoben da aka fitar na matan gida. Duk da ma ya zo a ƙurarren lokaci ai za ki samu telan da zai ɗinka mi ki kafin jibin ko" Mom ta ce "Insha Allahu zan zo" Har ga Allah ba ta kawo komai a ranta ba, tunaninta ƙila Inna ta fara chanjawa ne. Bayan sun gama cin abinci da ta shiga ɗaki ta ke gayawa Abba yadda su ka yi da Inna. Shi kam hankalinsa bai kwanta da sudden invitation ɗin nan ba amma tunda gimbiya ta nuna tana son zuwa dole ya ba ta dama ta je... ............. Tun daga yadda ta ga an fente gidan an fara decoration ta san abun babba ne. Shekarun baya Inna ta taɓa celebrating birthday lokacin tun Alhaji Wamako na raye amma ko kusa bai kai wannan ba. Kai tsaye sashen Inna ta wuce bayan ta gaisa da wasu baƙi da ta tadda a main parlor. Falon Innar ma da 'yan tsirarun baƙi. Duk wanda ya ganta sai ya sake kallonta, ta ƙara jiki ta yi fresh da ita sai sheƙi ta ke. Jallabiyar da ta sa ta yi rolling da babban mayafi ya sake bayyanata a Hajiyar ta. Gaskiya idan ka samu kwanciyar hankali a gidan aure to ko makaho ya shafa ka sai ya ji. Ba abinda ya kai kwanciyar hankali a gidan aure daɗi. "Hajjaju Makkatun, idon ki kenan" Mom ta duƙa tana gaida Inna. Inna sai murmushin yaƙe ta ke yi. Bayan an gaisa ne Innar ta ce bari ta shiga ta ɗaukowa Mom kaya. Tana shiga ɗaki ta ɗauko abinda aka ba ta wanda ƙaramar gunki ne da aka ɗaurawa jar ƙyalle. Goshin Mom aka ce ta mannawa, shi ke nan kuma Mom za ta kama ciwon kai wanda zai kai ta har lahira. Inna ta ɗauko leshin da aka fitar tana ƙoƙarin cusa gunkin a jikin kayan gunkin ya faɗo a hannunta, har kan gunkin ya ɗan tsage. "Na shiga uku" ta faɗa tana ɗaukan gunkin tana karkaɗe shi. Sai da ta cusawa sannan ta kira Mom akan ta shigo ɗakin. Mom ta shigo cike da sallama. Inna ta ɗau leshin tana faɗin kingan ta za ta mi ki kyau kuwa na ga fari ne. Mom ta ce za ta yi kyau. Inna ta matso tana faɗin "barin ga ni ajikin ki tukunna. Idan bai miki kyau ba akwai wanda su ka yi ja sai a karɓo miki ja" Inna ta manna leshin ajikin Mom a dole wai tana gwadawa. "Ɗan rufe idon ki, ga wani datti a gashin idon ki kar ya shige miki ido" Mom ta rufe ido wanda anan ne Inna ta yi saurin fito da gunkin nan ta mannawa Mom a goshi har sau biyu kafin ta ɓoye gunkin a bayanta tana faɗin Mom ta buɗe ido dattin ya fita... Daga gidan Inna wajen Tailor ɗin ta taje inda ta bada ɗinkin express daga nan kuma ta wuce gida... *** Ranan Jumu'ah ya dawo. Dai-dai Maghrib ya iso gidan na su. Yadda ya ga gidan na su ya cika ne ya sa shi tunanin ko lafiya. Duka ƙannen sa su na gida, abin mamaki ƙannen mahaifin sa ma sun zo idan ka cire Hajiya Safiya da Uncle AbdulWahab, su kaɗai ne ba sa nan. Hajiya Fadila ce ta biyoshi falon sa tana ma sa sannu da zuwa tareda tambayarsa ko da saninshi Inna ke shirin yin wannan almabazzarancin. "Ofcourse not, kin san ba zan taɓa amincewa da wannan shirmen ba infact ba zan bari ayi wanna shirmen ba" ya faɗa da kakkausar murya. "Yi haƙuri shalelen Aaliyah. Ta riga ta kashe kuɗi ta gayyaci manyan mutane kuma zai zamo cin fuska a gidan nan idan aka fasa" "I dont care" "Asma'u Wamako ta yi abin kunya zai shafeka Zaid saboda kai ma jinin Ibrahim Wamako ne" Da ƙyar Hajiya Fadila ta lallasheshi ya haƙura. Ganin hayaniyar gidan ya yi yawa ne ya sa ya fice a gidan ya nufi gidan Mom... Ba ƙaramin yunwa ya ke ji ba, Allah ya taimakeshi ya samesu a dai-dai, dan sun fara cin abinci kenan. Ya zauna aka serving na shi ya faraci sai da ya fara ci sannan ya lura Aaliyah ba ta wajen. Kamar zai tambaya sai kuma ya fasa ya cigaba da cin abincin sa... Da ke ya gayawa Mom a nan zai kwana shiyasa aka shirya ma sa ɗakin baƙi. Bayan ya shiga ɗakin ne Abdul ya shigo ya kawo ma sa sabon brush da toothpaste. "Aaliyah ta yi tafiya ne?" Ya tambayi Abdul. "Ba ta da lafiya ta yi bacci" "Tun yaushe?" "Tun shekaranjiya. Har allura aka ma ta aka sa ma ta ruwa" Zaid ya ce "Allah ya ƙara sauki" Haka kawai ya ji tausayinta ya mamaye haushinta da ya ke ji. Hakanan kuma zuciyar sa na son ganin ta. Ba dan dare ya yi ba da ya sa an kira ma sa ita ya gaishe ta. Haka ya kwana da kewarta a zuciyar sa. *** Gaba ɗaya garin na Abuja ba abinda ake magana a yau Asabat sai birthday party ɗin Hajiya Asma'u Wamako. Make up artist daga India Zahra MCcollins ta ɗauko dan ta yiwa Inna kwalliya a wannan rana. Shiga uku za ta yi wanda dukkannin kayan da za ta saka ba ƙaramin miliyoyin kuɗi aka zuba ba kafin aka siye su. Events uku za ayi a rana ɗaya. Da safe za ayi picnic wanda a gida za ayi shi sai da rana za ayi Luncheon a wani gidan gona sannan da yamma zuwa dare za ayi Hajiya Wamako's night. A duka events ɗin nan uku akwai different cake da za ta yanka, hakanan kowanne da ankon da aka fitar... Da safe ma bai ga Aaliyah ta fito ba wannan ya sa ya ce wa Mom ta gaishe ma sa da mai jiki. Mom ta ce tana ɗaki, ka je ka gaida ta mana, dama kullum sai ta tambayeka. Cike da zumuɗi ya haura sama bayan Mom ta ma sa kwatancen ɗakin. Ya ƙwanƙwasa kofa kafin ya shiga haɗe da sallama. Tana ƙudundune cikin bargo ya shigo yana faɗin "Allah Sarki! ashe wata jinyar mutuwa ta ke. To Allah ya gafarta miki" Ta ɗago ido ta kalleshi ta yi saurin sauke idon ta jin wani shock da ya ziyarceta sakamakon haɗa ido da ta yi da shi. Ganin ba ta tanka ma sa bane ya sa ya sassauta murya ya ce "Baby ya jikin na ki?" Muryanta da baya fitowa sosai ta ce "da sauƙi" a hankali. "Baby ki warke kin ji, ban shirya rashin ƙanwata ba" Aaliyah ta gyaɗa kai tana ƙaƙaro murmushin dole... .............. Anyi taron safe da rana lafiya. Da dare Hajiya Inna za ta yanka cake ta ji an mareta. Ta juyo a firgice amma ba ta ga kowa ba. Kafin ta ankara an sake kai mata wani marin. Wannan karan sai da wuƙan hannunta ya faɗi. "Kin fasa min kan ɗana. Gashi yanzu ya mutu, kina tunanin zan bar ki lafiya ne" wani gigiceccen murya ya doki kunnen ta. Sake marinta aka yi wanda ya sa ta faɗi ƙasa. Ɗagowar da za ta yi ta ga gaba ɗaya wajen ya yi duhu sai wasu irin munanan halittu ta ke gani. "Na shiga uku! ku kunna min wuta, ku kunna min haske" gaba ɗaya mutane aka yo kanta ana tambayar lafiya amma ta wafce ta koma gefe domin mutanen da su ka zo wajen ta ma wani irin halittu taga sun rikiɗa sun koma. A hankali Aljanin nan ya cigaba da tsoratar da Inna yanayi yana sharara ma ta mari. Tuni idon Inna ya makance dan ba ta ganin mutane sai duhu da munanan halittu. "Wayyo ku taimake ni. Ahmad, Ahmad ka ceceni. Na tuba ba zan sake cin zarafin Aaliyah ba. Na yi alkawarin ba zan kasheta ba. Wayyo ku ceceni, Wayyo..." Haka Inna ta haukace a wajen wannan taro na birthday ɗin ta. Mutane aka fara fito da wayoyi ana shooting. Kaf abinda ta aikata sai da ta tona a wajen, yadda ta kashe Jamilah ta kashe Alaja Atinuke ta ke kuma ƙoƙarin kashe Aaliyah da yadda ta yi sanadiyar kashe ɗan ta Ahmad. Duk 'ya'yan ta su ka kama kuka jin abinda uwar su ta aikata. Almost zigidir haka Inna ta fetta da gudu ta bar wajen, ana a tare a tare amma inaa ba wanda ya iya kamata. Under wear skirt ne kawai a jikinta wanda shima ta fara yagashi. Inna na fara hauka 'yan gulma su ka kira Mom su ka faɗa ma ta sannan aka turo ma ta video ɗin abin. Dama da safe kawai ta je hidimar, dan Abba ya hanata zuwa sauran events ɗin ya ce bai yadda da Inna ba, kar ta je ta yiwa Mom walaƙanci acikin taro. Mom ta tsugunna ta fara kuka, she wished Inna ta tuba kafin wannan rana, she wished Inna ba ta ɓata sunan gidan Alhaji Ibrahim Wamako ba... *31-Rich people's problem* Bikin abokin Zaid ake yi, nan ya maida hankalin sa. Bai ma bi ta kan Inna da tawagarta ba, dalilin ƙin attending ɗin events ɗin Inna har faɗa su ka yi da Zahra. Ya san idan ya je za a samu matsala dan haushin Inna ya ke ji kamar ya yankata. Yana wajen Dinner ɗin Mansoor, Zahra ta fara kiran wayar sa, tunanin sa za ta ce ya zo party ɗin ne shiyasa bai ɗauka ba. Ba a jima ba sai ga kiran Hafiz yana ɗauka Hafiz ya ce "Zaid abinda na gani gaskiya ne? Wai Hajiya Inna ta yi hauka?" "What!" "Ka hau online ka gani" Kafin Zaid ya duba wayar wani abokinshi a wajen ya ƙaraso da sauri yana nuna ma sa video ɗin. "Serves her right" ya faɗa yana miƙewa... Tunda ya fita kuwa ake ta kan kiran wayan sa, 'yan uwa, abokai, 'yan jaridu da 'yan gulma. Ganin kiran yai yawa ya sa ya kashe wayar sa. Ba zai iya zuwa gida ba domin ya san dole mutane za su bishi chan. Gidan Mom ne option ɗin sa ko kuma ya wuce hotel. Da farko ya yi niyyar zuwa hotel sai kuma ya fasa ya wuce gidan Mom. Yana tuƙi ransa na ma sa ƙuna. He wanted so badly asirin Inna ya tonu amma ba ta haka ba, but then its for the best... Tun ɗazu ya ke rarrashinta amma ta ƙi yin shiru. " yanzu My Love idan kina kuka haka ya kike son Zaid ya ji kenan? He's greatly affected by this too. Kamata yai mu kirashi mu rarrasheshi kar yai wani abu irrational a wannan lokaci" Sai alokacin ta yi shiru tana faɗin "you're right, ban kira Zaid ba" Tana ƙoƙarin tashi ta nemi wayarta ya riƙeta gam ajikinsa yana faɗin ga waya nan. Ta amshi wayar sa ta fara kiran Zaid amma duka nambobin sa switched off. "Ya Allah! Where's my son" "Ki kwantar da hankalin ki ba abinda zai sameshi". Wasa-wasa duk wanda ta kira sai su ce ba su ga Zaid a wajen ba. Da ta kira Zahra ne ta ke ce ma ta Zaid bai je wajen ba, dinner ɗin abokin sa ya je. Mom ta birkice akan za ta je neman ɗan ta, da ƙyar Abba ya lallacesheta ta haƙura ta zauna, yayinda shi kuma ya ɗau car keys ya fita dan nemo Zaid. Yana shirin tada mota aka buɗe gate ɗin gidan, ya juya sai ya ga motar Zaid ke shigowa gidan dan haka ya kashe tashi motar ya fito. Zaid ya parking motar amma bai fito ba. Kwantar da kansa yai jikin steering yana hawaye. Ya rasa dalilin kukan na shi, tausayin Inna ne ko tausayin kan sa a matsayin sa na jikan Inna. He cant believe despite abubuwan da ta aikata a baya ba ta saduda ba har tana shirin kashe Mom. Wani irin son duniya ta ke da shi haka?. Ƙwanƙwasa window da Abba yai ne ya sa shi ɗagowa yai saurin goge hawayen sa sannan ya buɗe ƙofar. "Alhamdulillah, Son are you Ok?" Zaid ya gyaɗa ma sa kai. "Taho mu shiga ciki, your Mom is worried" Ya kama hannun sa su ka wuce cikin gidan. A falo su ka samu Mom ta yi cirko-cirko tana jiran tsammani. Tana ganin Zaid ta je ta rungumeshi da gudu. "Son are you Ok?" Ganin yadda Mom ta damu ya sa ya yi murmushi ya ce "i'm Ok Mom. Ribar abinda ta aikata ta ke ci" Ta san ɗan na ta, he's good at pretending. Ta sani dole ne abinda ya faru ya dameshi, he might not be closed with Inna but in the end ita ta haifi Uban sa, ita kakar sa ce. Ta sa hannu ta shafa kumatun sa ta ce "we'll get through this Son. Komai zai wuce" "Zan iya kwana a nan?" Jan kumatun sa ta yi da ɗan ƙarfi ta ce "ban hanaka tambayar rashin kunyar nan ba" "Ok Ok, Mom zan kwana agidan mu yau" Ta ce da shi "barin gyara ma ɗaki. Mi za ka ci?" "Nothing Mom, i'm Ok"... Bayan Mom ta tafi ne Abba da Zaid su ka zauna suna tattaunawa, inda Abba ya fara ma sa nasiha akan abinda ya faru yana ma sa tuni da mahimmancin haƙuri. Tareda nuna ma sa abinda ya faru izina ne ga dukkan mutane ma su neman duniya ido a rufe, musamman marasa tsoron Allah irin Inna. ba a jima ba Mom ta zo ta joining na su inda ita ma ta ƙaru sosai da nasihar Abba. Sai ƙarfe shaɗaya Zaid ya ce zai je ya kwanta hakan ya sa su ka yiwa juna sai da safe, su Abba su ka haura sama shi kuma ya shige ɗakin baƙin da ke ƙasa. *** Yana shiga ɗakin ya zauna a bakin gado ya dafe kan sa. Tunani ya ke a ransa yadda abubuwa za su kasance daga gobe. Da ƙarfin tsiya Inna sai da ta yi suna a ƙasar, shige-shige da cusa kai jikin manya ya sa duk wanda ya ji sunan Hajiya Wamako zai ganeta. She's so obsessed with money and fame, ga shi yanzu ta jefa kan ta halaka. Ko kaɗan ba zai sa a nemo ta ba, she should just dissappear forever kawai. Dad ne ya faɗo ma sa rai. Lokacin yana raye he cherished her alot, yadda ya ke binta sau da ƙafa ka ce bawan ta ne ba ɗan ta ba. Ya ma gode wa Allah da ya kasance Dad ba ya raye a yau da Inna ta yi hauka, da ba makawa sai Dad ya samu heart attack. Jin ƙwaƙwalwarsa ta ka sa dena tuno abin ya sa ya fito da kwalin sigari a aljihun sa ya ciro guda ɗaya ya fito da lighter ya kunna ya fara zuƙa. Its being a while da ya sha sigari, wannan ɗin ma ranan sallah ne ya siyeta bayan ya zo ya taradda su Aaliyah sun yi tafiya. A mota ya jefata tun lokacin bai waiwayeta ba sai yau, ya san zai buƙaceta shiyasa ya ɗauko a motar ya shigo da ita... Jikin na ta da sauƙi yau dan ta ma fito ta ci abinci da 'yan gidan. Ta yi hakan ne saboda hankalin Abba ya kwanta dan yana maganar zai kaita asibiti idan ba ta warke ba. Ta ji daɗi da Isma'il bai fito ba, dan yanzu ba ƙaramin kunyar sa ta ke ji ba. Ta ya za ta iya kallon sa bayan abinda ya furta ma ta? And the worse part shine yadda ya ke ji a zuciyar sa gameda ita a wajenta ba haka ba ne. Kallon ɗan uwa kuma Yaya ta ke ma sa. Mafi munin abinma shine yadda zuciyar ta ke shirin sa ta yin abin kunya. Ta ya za ta dinga ganin Zaid a wani matsayi na daban da bai kamata ba? Ta ya tunanin Zaid zai saka ma ta ruɗu ya hanata sukuni?. Kaman yadda Likita ya faɗa ba zazzaɓi kaɗai ke daminta ba har da damuwa. Abin kunya ne ace damuwar na ta bai wuce Zaid ba, yadda ya shareta 'yan kwanakin nan shi ya haddasa ma ta damuwa... Ƙishirwa ne ya tasheta daga bacci, ana gama cin abinci ta dawo ɗakinta ba ta jima ba bacci ya ɗauketa. Ta dubi saman side wardrobe amma ba ta ga water bottle ɗin ta ba, ba mamaki ta barshi a kitchen ne. Ta sa room slippers ta fito. Falon na su ya yi tsit alamun kowa yai bacci. Ta dinga haska torchlight ɗin wayarta har ta kai wajen fridge ta buɗe ta fito da ruwa. Tana cikin shan ruwan ta fara jin warin hayaƙi. Da sauri ta ajiye goran ta wuce kitchen tana tunanin ko an mata gas ne a kunne. Ganin komai normal ya sa ta fito daga kitchen ɗin tana tracing inda warin ke fitowa wanda warin yanzu ya fi ma ta kama da warin sigari... Bismillah ta yi ta tura ƙofar tana haska wayarta tunda ɗakin da duhu ba a kunna wuta ba. Kaman Zaid kaman kuma ba shi ba. Sai da ta matsa kusa ta haska shi sosai sannan ta tabbatar da shi ɗin ne. Sigari ya ke busawa ga ragowar uku a ƙasa da ya riga ya shanye. "Wamako are you Ok?, mi ya faru?" Shiru bai amsa ma ta ba. Ta sa hannu ta cire sigarin daga bakin sa ta jefa a ƙasa ta tattake shi. "Smoking in the night, why? what happenned?" Ya sa hannu ya lalubo kwalin da ke gefen sa yana son sake kunna wata sigarin Aaliyah ta yi saurin ƙwacewa. "Wamako stop this" Sai a lokacin ya ɗago jajayen idon sa ya kalleta. Kallon sa ta ke cike da tsoro da tausayi. "Wamako mi ya ke kamun ka? Ko na kira ma ka M..." Ya jawota da ƙarfi ta faɗa jikin sa wanda hakan ya sa wayar da ke hannun ta ya faɗi. A hankali ya tallafo fiskarta ya fara shafawa a hankali. Bugun ƙirjin ta ya tsananta yayinda jikinta ya ɗau rawa. "Wama..." jin bakin sa cikin na ta ya sa ta kasa ƙarasa kiran sunan sa. Da farko ta ɗauka mafarki ta ke yi but when the reality struck her sannan ta fara ƙoƙarin tureshi tana bubbuga bayan sa. Zaid was just kissing her angrily, passionately and he was so lost enjoying the pleasure ko kaɗan bayajin bugunsa da ta ke yi. A ƙalla ya yi minti ɗaya da rabi yana kissing ɗin ta kafin ya saketa. Kallon ƙwayar idon ta ya ke yi wanda tuni ya fara zubda hawaye ya ce "i'm sorry" Ta yi saurin tureshi daga jikin ta ta bar ɗakin cikin sauri ko wayarta da ke ƙasa ba ta ɗauka ba. Gaba ɗaya jikin sa ya yi weak. Bai san mi ya ke tunani ba ya aikata abin da ya aikata. Ko motsawa bai yi ba a wajen a haka bacci ya saceshi bayan ya shafe kusan minti talatin yana tunanin babban laifin da ya aikata... *** Washegari da sassafe Zaid ya bar gidan ko karyawa bai yi ba duk da kuwa Mom ta buƙaci ya tsaya ya sha ko tea ne. Ganin Aaliyah ba ta fito ba ne ya sa Mom ta ɗau breakfast ta kai ma ta ɗaki. Kwance ta sameta idonta duk a kumbure kamar wadda ba ta yi bacci ba jiya. Mom ta ajiye tray ɗin abincin ta zo ta zauna gefen gado ta ce "Princess jikin ne?" Aaliyah ta girgiza kai "Gaya min mi ya ke damun ki, akwai abinda ki ke so ne? Ko wani ya mi ki laifi ne?" Duk ta girgiza ma ta kai tana faɗin "Mom i'm Ok" Mom ta kamo hannun ta ta ce "ta ya zan ga 'ya ta cikin damuwa kuma hankalina ya kwanta. I'm worried dear, idan ma ba za ki iya gayamin ba ki sanar da Abban ki. Kin gan ki kuwa? Yersterday kin ɗan yi kyan gani amma jiba idon ki. I'm sure kuka kika dinga yi ba ki yi bacci ba" Ta ya za ta gaya ma ta matsalar ta bayan matsalar na ta ka iya ruguza alaƙar da ke tsakanin su. Ta shiga rayuwar Zaid ne only to get Abba and Mom together, amma yanzu zuciyarta ya ci amanarta. What she felt for Zaid is wrong, dole ta yi yaƙi da zuciyarta kafin ta kaita ga dana sani. Gaba ɗaya daren jiya ta wuni ne tana neman dalilin da zai sa Zaid ya kissing ɗin ta. In the end ta concluding Zaid ya yi hakan ne saboda baya cikin hayyacin sa. "Haba takwaras, a hakan za ayi ƙawance ki na ɓoye min matsalar ki" Mom ta faɗa tana jawota jikinta. "I'm sorry Mom, ni ma ban san mi ke damuna ba ne. May be na gaji da ƙasar ne" "Sorry dear, ma za tashi kiyi brush ki ci abinci, kin ga sai mu yi maganar inda za ki je hutu" Aaliyah ta yi murmushi tareda yaye bargon ta tashi ta shige banɗaki. Mom kam abu ɗaya ne ya tsaya ma ta a rai, kuma ta tabbata shine gaskiyar abinda ke damun Aaliyar... Zaid kam lokacin da ya isa gida ko kallo 'yan gidan ba su isheshi ba balle ya mu su magana. Har lokacin gidan na su a cike ya ke da 'yan gulma. Duk wanda ya tambayeshi kuwa kallon banza ke raba su dan ko magana ba ya yi. A chan office ma sai da aka biyoshi ana neman jin ta bakin shi batun haukacewar Inna, tareda neman ƙarin bayani kan abinda ke faruwa ko da gasken ne Hajiya Inna ta aikata abubuwan da ta faɗa. Yadda ya ƙudura aniyar ba zai yi magana da kowa ba hakan ne ta faru dan ƙala bai ce ba. Kusan ƙarfe Uku sai ga Zahra ta zo office ɗin sa. Zaune ta sameshi yana aiki kaman ba abinda ya faru jiya. "My Baby how are you?" Ta faɗa tana manna ma sa kiss a goshi. "Ban san haka Inna ta ke ba, i didnt know she's a devil har na yi asaran kuɗi na akan ta. Baby i'm sorry, ya kamata ace jiya ina kusa da kai but na bar ka na je ina biye evil woman ɗin nan" "Kar ki sake kawo maganar abinda ya faru jiya. As far as im concern nothing happened" "Its Ok if you dont want to talk about it" Ganin bai ba ta fiska ba ya sa ta tafi dan ta san yana buƙatar kaɗaici, is not easy ace mutum mai suna kamar shi dare ɗaya irin wannan abun kunya ya sameshi, ko da ya yi pretending he's Ok ta san deep down abin na damin shi... *** Inna kam ta bar cikin Abuja, da hauka ta fita a garin a ƙafarta abun ba kyan gani dan kusan tsirara ta ke tafiya. Haukan na ta mai baƙin jini ne domin maimakon a dinga tausaya ma ta duk inda ta je sai jifa. Duk abin da ta gani a ƙasa ko bola ta ke ɗauka ta ci. Wasa-wasa sai da ta yi sati uku tana hauka kafin yunwa da ƙishirwa ya kasheta a wani jeji chan ta Kudu. Babu wanda ke kusa balle a busineta haka gawan ya kumbura ya fashe namun daji su ka ci na ci su ka bar na bari. (Mu na da manya-manyan mutane da tsofaffi maza da mata wanda duniyar kawai su ka sa a gaba ba sa tuna makomar su. Ba sa tuna ranan da za tsaya a gaban Rabbil Arshi. Wa su suna ƙara girma su na ƙara zurfafa cikin sheɗanci ne. Dayawa haka su ke mutuwa ba tareda sun tuba ba, wasu tun a duniya su ke fara ganin sakamakon su wasu kuma na su sakamakon an tanada shi a chan. Allah ya kyautata ƙarshen mu ya kuma raba mu da tsufan musiba, Amin)... Wasu daga cikin yaran Inna sun yi ƙoƙarin neman ta amma abun bai yiwuba dan Inna ta mu su nisa. Ƙarshe su ka haƙura su ka yiwa kan su karatun ta nitsu. Washe garin da abun ya faru Mom ta je gidan ta mu su gaisuwa. A nan Hajiya Fatima ta tsugunna tana ba ta haƙuri, ba ta taɓa darajata ba tun da Ahmad ya aurota. Koyaushe tana cikin bin umurnin Inna wanda ta maidata kamar Baiwa. Mom ta ce ta yafe ita ba abinda ta ma ta. Ba ƙaramin daraja da kima Mom ta yi ba cikin 'yan uwan Ahmad wanda a da ba su ɗauketa da daraja ba. Sai gashi yau gaskiya ta fito, dama ance mahaƙurci mawadaci... ................. Cikin wata ɗaya abubuwa sun lafa, an ɗauke ido a gidan Marigayi Alhaji Ahmad Wamako. Batun haukar Inna ya zama tarihi, shekara da shekaru da Inna ta ɗauka tana gina sunan ta a duniya cikin wata ɗaya kacal an manta da ita. First week da abun ya faru media ta ruruta abun kamar me. Ko ina ka shiga labarin Hajiya Wamako ake yi but gradually kowa ya manta da ita. Shiyasa ake so ka yi ayyukan ƙwarai a rayuwar ka saboda idan ba ka nan duniya ta ma ka shaida mai kyau. Babban matsalar da Zaid ya fuskanta shi ne bashi. Ba ƙaramin bashi Inna ta bar ma sa ba. Dan da aka totalling ma sa figures ɗin sai da ya tsorata. Ta ina zai fara biyan bassussukan nan, bashi kamar kuɗin da Nigeria ke bin ƙasar China...LOL. Wannan ya sa ya zama busy ba ya nan ba ya chan, bai gayawa Mom ba sai da ranan ya zo ta ga yadda ya koma hankalinta ya tashi ta ma sa tambayar duniyan nan amma bai sanar da ita komai ba. Bayan tafiyar sa ne ta fara bincike akan abinda ke faruwa har ta gano dalilin da ya sa ya kasa samun sukuni. Ita kan ta da ta ji kuɗin ba ƙaramin mamakin Inna ta yi ba, ko mi Inna ta yi da waɗannan kuɗaɗen Allah ne kaɗai masani. A hankali Mom ta fara haɗa kan kuɗaɗen da za a biya ba tareda ta sanar da Zaid ɗin ba. Ba za ta taɓa bari Zaid ya wahala saboda Inna ba. Lokacin da ta gama settelling kuɗaɗen nan kusan cikin kaso ɗari na ajiyar ta saura bai fi kashi goma ba, a hakan sai da ta siyarda shares ɗin ta na wani kamfani a ƙasar Italy... "Dad you cant do this to me. Ina son Zaid" "Na riga na gama magana Zahra. Ba abinda za mu ƙaru da shi da auren ki da Zaid sai ma rashi. Wamako Enterprise is crashing, believe me kafin shekaran nan ya ƙare Zaid zai sayarda kamfanin nan." "Ba damuwana kuɗin Zaid ba tunda nima ina da shi. I love him Dad" Wannan karan da ƙarfi Alhaji Muhammad MCcollins ya ce "Zahra babu ke babu Zaid. Wai har kin manta abinda ya faru da su ne? He's grandmother run mad few weeks ago. Har yanzu akwai videos ɗin yana yawo a media. Ba zan iya haɗa zuri'a da su ba" "You cant do this to me, ban damu da abinda ya faru da grandmother ɗin sa ba. She's evil, Zaid is not" "Next week zan announcing auren ki da El-Bashir Lawals, kafin nan ku saita kan ku" Yana faɗin haka ya fita. Zahra ta tsugunna a wajen ta fashe da kuka... Alhaji Muhammad na fita ya kira Uncle AbdulWahab ya gaya ma sa officially maganar auren Zahra da Zaid an fasa. Auren da ba dan rashin lafiyan Ahmad ba da tuni an ɗaura. Duk yadda Uncle AbdulWahab ya so ya roƙi Daddyn Zahra bai saurareshi ba kashe wayan kawai yai... Su na gama waya da shi ya kira Mom ya gaya ma ta. Har ga Allah ta ji ba daɗi dan ta san dalilin fasa auren bai wuce saboda Haukacewar Inna ba. Ba za ta ce Zahra na burgeta ba amma tunda Zaid da kan sa ya kawota wajenta tun lokacin su na London ya sa ta ke jin yarinyar a ranta. Domin duk abinda Zaid ke so, to tana so... Zaid ba ya ma ƙasar lokacin da aka yi wannan abun. Sai da Alhaji Muhammad McCollins ya sanar da auren autar sa Zahra da El-Bashir Lawals a twitter handle na shi shine aka yi ta kiran Zaid ana ma sa jaje domin kowa ya san maganar Zaid da Zahra. Ko kaɗan bai nuna damuwa ba infact gaba ta kaishi dan yanzu aure baya gaban shi, he need to save his Company. Abinda ya faru da su ya jawo mu su koma baya dayawa a kamfanin ga bashin da Inna ta bar mu su wanda har yanzu bai san Mom ta biya ba... Tausa ta ke wa Abba a safiyar Asabat bayan ya dawo daga jogging. "Baby kin ga abinda Muhammad MCcollins ya sanar kuwa?" "Na gani. Engagement ɗin 'yar sa da ɗan Alhaji Tijjani Lawals ba" "That's on fair. Kusan two years fa su ke tare da ɗana" Mom ta yi murmushi ta ce "that's rich people's problem. Kullum su na neman mafaka ne wa kan su, suna gudun talauci su na gudun ɓacin suna, su na gudun haɗa zuri'a da tsiya" Hawaye ne ya biyo bayan maganar da ta yi lokacin da ta tuna shekaru talatin da su ka wuce da Baba ya haɗa ta da Ahmad Wamako. Tausayin Zahra ne ya kamata tana kuma yi ma ta addu'ar Allah ya sa auren El-Bash ya zama ma ta alkhairi... *32-I love her* Hankalinta kwance ta ke karanta littafin da ke hannun ta mai suna Me before you na Jojo Moyes. Littafin ba ƙaramin hooking na ta yai ba. Wayarta da ya hau ruri ne ya katse ma ta karatun, ta faɗaɗa murmushinta lokacin da ta ga sunan Mom ajikin screen ɗin. Hira sosai su ka yi kafin daga ƙarshe ta ajiye wayan. Kullum sai sun yi waya da Mom kuma akoyaushe wannan mata ƙara burgeta ta ke yi. Ko kaɗan abubuwan da su ka faru da wanda ke faruwa bai shaking na ta ba she's a strong woman... *One months earlier* "Zaid ko?" Mom ta faɗa tana kallon ta. Cike da kunya da tsoro ta ce "what?" "Kar ki damu 'ya ta, i've been through this also" "Mom I...I" "From day one da na haɗu da ke na san akwai chemistry tsakanin ki da Zaid. And i secretly wish ke da Zaid will be couples one day" Aaliyah ta zaro ido cike da mamakin Mom. "Ba zan iya bugan ƙirji na ce Zaid yana son ki ba, but one thing is certain, ki na da matsayi a zuciyar sa and its a good start" Aaliyah ta shiga ruɗu, why is Mom talking about it so comfortably. Ita da Zaid yanzu sun zama brother and sister. Whatever she felt for Zaid yanzu is wrong. Murya na rawa ta ce "Mom, he's my brother now" "Kar ki damu gimbiyata. Indai Zaid yana son ki to ba wata matsala, the society will gossip at first but who cares, its halaal" Ta zaro ido dan kwata-kwata ta ɗauka musunlunci ya haramta aurenta da Zaid. Mom ta ce " Yes princess, ke da Zaid akwai aure a tsakanin ku" Aaliyah ta sunkuyar da kai tana mai tsananin jin kunyar Mom thinking she was a dummy gaskiya... Kwana uku da maganar su, Mom ta shirya ma ta tafiya zuwa London. Wani course ta ke so ta yi na wata uku a chan, a ƙoƙarin ta na son samawa Aaliyah ɗin nitsuwa. Idan har tana so za ta iya sa Zaid ya auri Aaliyah, but what's the point if the marriage is loveless. The last thing she will ever wish for any girl is to have a loveless marriage. Ta ɗanɗaneshi ta san ɗacin sa. Deep down ta san akwai alamun Zaid zai iya son Aaliyah in the future but she will never force her son to marry a woman he did not love. Gara ta bari zuciyar sa ta kamu da son Aaliyar kuma ya amince da hakan. Haɗa auren Zaid da Aaliyah is her biggest dream now. Kullum addu'an da ta ke kenan, and most times takan ji a ranta cewa rabon Aaliyah da Zaid ne ya sa shekaru talatin da su ka wuce Allah bai ƙaddara aurenta da Sa'eed ba. Jallah Jalaluhu kenan mai yi yadda ya so a lokacin da ya so. And duk abinda ya tsarawa ɗan Adam to ba makawa abin ne ya fi dacewa da shi... *** Bayan Zaid ya dawo Nigeria ne ya gane Mom ta riga ta biya ma sa bashin da kakar sa ta bari. "Mom you dont have to do this, i've being working on a plan kuma..." "Shshshshsh... ba na son jin komai. Kai ka biya bashi ba ni ba, i used your money" "But Mom..." "Kul Zaid, ba na son jin komai. Just take care of yourself, matsalarka matsalata ce" "I love you Mom" ya faɗa yana rungumeta "I love you too Son" Abba da shigowar sa falo kenan ya ce "duk da ban san mi aka yi ba I love you too" Zaid da Mom su ka sa dariya... .......... Da wuya ace komai ya tafi dai-dai. Rayuwa juyi-juyi, a baya rayuwar Aaliyah Badamasi Bulama cike ya ke da ƙunci, ta fitar da tsammanin samun cikakken farin ciki a rayuwar ta, sai gashi kwatsam rayuwar ta juya da ita and this time around farin ciki ne a tattare da ita. Soyayya ba tareda aure ba ya kan zama shirme a mafiya lokuta. Yayinda auren da aka gina shi bisa soyayya ta gaskiya wacce ba ta da algus aciki ya ke kawo farin ciki, nitsuwa da walwala. Sai da Aaliyah ta auri Sa'eed ta gane in the end abinda kowacce mace ta kwarai ke roƙo'o shine bayan sun rayu a duniya to ya kasance ta tashi da mijinta a Aljannah. Kuɗi ba matsalar Mom ba ne tun tana yarinya zuwa budurwa zuwa yanzu da shekaru su ka ja tunda za a iya sakata a sahun dattijuwa. Shekaru hamsin ba wasa ba ne. Ayyukan alkhairi Mom ke ƙoƙarin yi a kowani lokaci kuma Abba ya supporting ɗin ta. Yayinda iya rayuwar ta da Ahmad sallah bai taɓa haɗa su tare ba shi Sa'eed yadda ta san shi tun ƙuruciyar sa haka ya ke sai ma abin da ya ƙaru. Ba ya wasa da yin nafilfilu. Duk dare kafin su kwanta sai ya tabbatar sun yi shafa'i da wutri, haka nan daren Jummu'ah ya zama mu su jazaman wajen raya wannan dare su na ibadah. Ga kuma raka'atanil fajr da ba ta wuce su. When you marry the right person, ba duniyar ku kaɗai zai dinga dubawa ba har da makoman ku bayan mutuwa, domin shine rayuwa ta dindindin, idan akwai abinda ake Forever to rayuwa ce bayan mutuwa. Mafiyawanci lokacin da ka samu zaman lafiya a rayuwar ka, Allah ya buɗa ma ka to lokacin ne kuma girman kai da faɗin rai zai ƙaru ma ka maimakon ya kasance lokaci ne da za ka zaƙe wajen kusanci da Ubangijin ka. Auren Sa'eed ya sa ta ƙara kusan ci da Ubangijin ta. Sosai ya influencing ɗin ta wajen ƙara jajircewa wajen bautan Allah shi kaɗai... Yau Mom tana kitchen aka yi sallama, ta wanke hannu ta goge hannunta da kitchen towel ta fito. Yaran ba sa nan Jiji kuma ta je ƙauye. Ganin Hajiya Fatima da Nusrat ne ya sa ta faɗaɗa murmushin ta. "Maraba Maraba, sannun ku da zuwa" Nusrat ta zo da gudu ta faɗa jikin ta tana faɗin "Mom I miss you" Mom ta ce "i miss you too Auta na" Bayan sun gaisa shiru ne ya biyo baya kafin Mom ta katse shirun da cewa "ku na jin labarin Ummi da mijinta kuwa?" Hajiya Fatima ta ce " su na nan lafiya. Haihuwa ko yai ko gobe" "Mom ta ce Allah ya sauke ta lafiya" Hajiya Fatima ta amsa da Amin. Asma'u ita ce 'yar Hajiya Fatima ta fari kuma ta yi aure tana zaune da mijin ta a Houston, Texas, USA. Mai bi ma ta kuma Maryam ita ma anyi auren ta, wani cousin ɗin ta ma ta aura, su na zaune a Kaduna. Sumayya na karatu a Egypt sai Khadija da ke aji biyar a secondary school sannan Nusrat wanda ke aji huɗu a primary school. "Hajiya zan tare nan da sati biyu fah" Mom ta ce " a'a lafiya? Ina za ki je, mi ya faru?" Hajiya Fatima ta sunkuyar da kai ta ce " aure zan yi sati mai zuwa, kuma chan Gombe zan koma" "Masha Allahu. Allah ya baku zaman lafiya, Auta za ta mana nisa kenan" Hajiya Fatima ta girgiza kai ta ce " tana nan tareda ku. Gara ta zauna kusa da 'yan uwanta, ta fi sabawa da nan chan zai ma ta wuyar sabo" "Amma Hajiya Fatima za ki barta da Khadija kaɗai, ba fa iya kula da ita za ta yi ba. Shi Yayan na su kuma ba samun lokaci ya ke ba" "Shiyasa na kawo miki ita. Na san za ki ba ta tarbiyya fiye da ni" Mom ta ƙara jawo Nusrat jikinta tana yiwa Hajiya Fatima godiya. Haka su ka zauna su na taɗi daga baya kuma Hajiya Fatima ta yi wa Mom sallama ta bar Nusrat wajen ta. Tareda cewa Dreba zai kawo kayanta anjima. Nusrat kam ba ta damu ba dan haka kawai jininta ya haɗu da Mom, duk da ba wai jimawa su ka yi tare ba. Lokacin da Ahmad ke raye sau biyu ya taɓa kaita hutu wajen Mom ɗin a chan London. Mom ta ji daɗin karramawar da Hajiya Fatima ta ma ta. Mutuncin da ba su yi lokacin da Ahmad ke raye ba sai yanzu Allah ya haɗa kan su... Zaid da ya zo da dare ne ya taho da kayan Nusrat, ya zauna yana yiwa Mom tsiya wai ba sabon ba ta yi 'ya. "Mom ina babbar 'yar ta ki ne? Duk zuwa na gidan nan ba na ganin ta" Mom ta harareshi ta ce "ina ruwan ka da ita" "Just asking" ya faɗa yana basar da zancen. Wasa-wasa ya lura duk zuwan sa Aaliyah ba ta gidan. Ya jera sati yana zuwa a jere amma ko wulgawar ta bai gani ba. As first ya ɗauka saboda abinda ya faru daren ranan ne shiyasa ta ke avoiding na sa amma daga baya ya fahimci ba ta gidan ne kwata-kwata. Ranan ya ka sa haƙuri ya tambayi Abdul ina Aaliyah. Abdul ya ce bai sani ba Mom ta ce ta tafi makaranta. Makaranta a ina? Ya tambayi yaron. Amsar da Abdul ya bashi ne ya jaddada ma sa shima kan sa Abdul bai san inda Aaliyah ta ke ba dan da ya sani zai faɗa dan Masha Allah yaron akwai surutu... Lokacin da Hajia Fatima za ta tare ba ƙaramin kuɗi Mom ta kashe ba wajen siya ma ta gifts. Ta so yi ma ta rakiya zuwa Gombe amma Jiji ba ta jin daɗi shiyasa ba ta je ba. Hajiya Fatima wani ɗan uwanta ta aura, Lecturer ne a state university da ke Gombe (GSU) matan sa biyu amma sun rabu da ɗayar yanzu ɗaya kawai gareshi. Yaran sa kuma tara. Shekarun Hajiya Fatima arba'in da ɗaya dan haka har yanzu da sauran shan miyanta indai ba rai ne yai halin sa ba. Happy Married Life Hajiya Fatima Ɗahiru Yunusa. *** A ɓangaren Isma'il rashin samun amsa a wajen Aaliyah ya gamsar da shi ba ta ra'ayin sa. Wani lokaci yana tuhumar kan sa da zurfin ciki da yai tun farko yana cewa ƙila da ya sanar da ita tuntuni da ya samu karɓuwa. He hates to admit it amma gaskiyar magana dai ya sani Aaliyah ta kamu da soyayyar Zaid ne. Kuma ya sani saboda Zaid ɗin ne ta bar gidan... Zaid kam tun yana ɗaukan abun wasa har ya zamo ma sa babban damuwa. Like tunanin Aaliyah ya zame ma sa jiki, ba zai iya cewa ga ya fara jinta haka ba a zuciyar sa amma ya sani abun ya jima may be tun ma kafin ya san ko ita wacece ko kuma bayan ya san ko wacece ita. He's totally confused. Ranan da ya tsaya tunanin ta har ya tuno kissing ɗin ta da yai he was shock da ya shiga banɗaki zai kama ruwa ya ga boxers ɗin sa a jiƙe. Something that ko lokacin da ya ke tareda Zahra hakan bai taɓa faruwa da shi ba... Bai san ya zai categorizing yadda ya ke jin kewar yarinyar nan ba. To him its a very strange feeling bai taɓa jin haka gameda kowacce 'ya ma ce ba. Its a kind of funny to him idan ya tuna ya su ke da ita. Ya san ba komai ba ne but its odd, ta ya dan Mom da Abba su na son junan su sai shima ya dinga jin wani abu gameda Aaliyah... Yau daga office straight gidan Mom ya wuce, jiya bai je ba saboda bai tashi daga office da wuri ba. A gidan ya zauna har bayan Isha. Su na kallon ƙwallo a falo Zaid ya daure ya ce "Abba, Baby ta fara Msc ɗin ta ne?" "No, sai next year" Ganin bai ƙara cewa komai ba ya sa shi ƙara yin wani tambayar "is like zaman ƙauye ya ma ta daɗi tunda ta ƙi dawowa" Abba ya ce "ba ƙauye ta je ba Mom ɗin ta ne ta tura ta hutu" Zaid ya sauke ajiyar zuciya dan bai samu amsar da ke nema ba. Mom ta kawo mu su tray cikeda kankana da aka yanka ƙanana. Abba ya sa hannu ya ɗau fork ya cakkwali kankana ya kai bakin sa ya ce "zo kiyi bayanin inda ki ka kai wa Son ƙanwa, ya fara kewar ta" "Ya tattare shirmen sa chan yai gaba. Tunda ba a nememu ba sai da Zahra ta yi aure, ba ruwan mu da shi" "Mom please nah. Is it wrong Yaya ya tambayi inda ƙanwar sa ta ke ne? Its been almost 3months fa" "Za mu isar ma ka da gaisuwa, shikenan ina?" "Ban yarda ba, ni ki bani contact na ta" "Za ka bushe kenan. Daughter na ta fi ƙarfin ɗaukan kiran ka" Shi kam Abba murmushi kawai ya ke yi ganin yadda Uwa da ɗa ke jayayya tsakanin su... Da dare da za su kwanta Abba ya ce "My love ki bashi numbar Princess ma na" "Ba zan ba shi ba, 'ya ta ba ta son gwanjon zuciya. Sabuwa fill ta ke so" Abba ya zaro ido yana faɗin "yaushe haka ta faru? Ko shine dalilin da ya sa Princess ta chanja kwanakin baya?" Murmushi Mom ta yi tana faɗin " ciwon so ta ke yi" Abba yai kabbara da ƙarfi, bai tsaya anan ba ya sauko daga kan gadon yai sujudush shukri... ................ Wasa-wasa duk zuwan Zaid sai ya yi rigima da Mom akan ta bashi numbar Aaliyah ko kuma ta gaya ma sa inda ta ke amma ta ƙi. Abba kam zuba mu su ido yai dan Mom ta ce idan bai furta son Aaliyah ba, ba za ta sanar da shi inda ta ke ba. Duk yadda Zaid ya so don ya yakice tunanin Aaliyah a ran sa ya ka sa. Kewar ta is draining him. Yau Sunday tun safe ya ke jin sanyi da ƙyar yai sallar asuba ya koma ya kwanta. Stress ne da yawan tunani ya haddasa ma sa zazzaɓi. Ganin abun na damun shi sosai ya sa shi ɗaukan waya ya kira Khadijah. Khadijah na zuwa ɗakin ta ruɗe ganin Zaid haka. Numban Mom ta kira tana sanar da ita halin da Zaid ke ciki. Yayinda Mom ta kira likitan su ta ce ya je ya duba Zaid ɗin itama ta ɗau hijabi ta yi gidan su Zaid ɗin... Abu kamar wasa sai gashi sai da aka ɗaura ma sa ruwa. Likita ya tabbatar ma sa akan dole ya rage tunani. Mom ce ta zauna jinyar sa, sai dare ta koma gida bayan ta ga jikin na sa da ɗan sauƙi. Yana kwance hiran sa da Zahra na faɗo ma sa ranan da ya dawo Nigeria. Office ta je ta sameshi da maganar auren da Baban ta ke shirin yi ma ta. "Zaid, i'm an independent woman, na san 'yan ci na. Ba zai taɓa yiwuwa a min auren dole ba. I'll fight for us" "Ba sai kin yi haka ba, there's no need for that" "Zaid mi ka ke nufi?" Yai shiru na 'yan mintina kafin ya ce " Zahra, Yes we are attracted to each other and i like you but then..." "But then you dont love me?" Ta fashe da dariya. "Zahra i'm sorry, ko da Daddy bai janye maganar mu ba i wanted to quit..." "Enough Zaid. Cin mutuncin ya isa haka, ba fa kai ne autar maza ba. Yes I love you but ba zan juri walaƙanci ba. Ka san maza nawa su ke dying to have me, amma na liƙe ma ka?" "Zahra ple..." Ta ɗau jakarta ta fice daga office ɗin... Wayar sa ta hau ringing ya jawo ta ya sa a kunne bayan ya amsa call ɗin. "Son ya jikin?" "I love her Mom. I dont know what happened to me, i know its crazy but i love her" Mom cike da farin ciki ta ce "who?" *33-Happy married life* Washe gari da sassafe Mom ta isa gidan Zaid. Jikin na shi da sauƙi sai dai rashin kuzari. Jiya bayan sun gama waya da shi kusan kwanan zaune ta yi tana jujjuya maganar tareda tsara yadda bikin 'ya'yan ta zai kasance. Abba da ya ga abun na ta ba na ƙarewa ba ne jan bargo yai ya kwanta abinsa, yayinda ita kuma ta ɗauko jotter ta fara list ɗin abubuwan da za a yi a biki. Amma da ta zo sai ta fara yiwa Zaid tsiya tana cewa ba ta yarda yana son Aaliyah ba. "Mom i'm serious" Zaid ya faɗa lokacin da Mom ke serving na shi breakfast. "Ni ban yarda ba. Ba ka san da 'ya ta ba sai da ka rasa Zahra, 'ya ta ba kwantai ta yi ba balle a kawo ma ta gwanjon zuciya" Bai san mi zai ce da Mom ta yadda da abin da ya ke ji ba. Ta yi soyayya ta san yadda ake ji but why is she refusing to believe him. "Mom please believe me" Mom ta girgiza kai ta ce " 'ya ta ta maka nisa ka yi haƙuri kawai" "Mom ba kya so na samu lafiya ko?" "Allah ya ƙara ma ka lafiya ka ga auren 'ya ta da masoyin ta" "Tunda ba za ki yadda ba shikenan" ya haɗe rai ya ɗau spoon ya fara cin abinci ran sa a ɓace. Perfect timing sai ga kiran Aaliyah ya shigo wayar Mom. Mom ta amsa wayar tana faɗin " ka ji 'yar halak, yanzu fa mu ke zancen ki" Duk hiran da su ke yana ji amma yadda ya haɗe rai ya maida hankalinsa gurin cin abinci ka ɗauka bai jin komai. Da ta gama wayar ta ce "ka ji dai 'ya ta na lafiya kuma na isar da saƙon gaisuwar ka" Yai shiru kamar bai ji ta ba "Son fushi ka yi? Allah ya ba ka haƙuri" Still bai yi magana ba ta dafa kafaɗar sa ta ce "get well Son, ka kusa zama Yayan Amarya"... ............ Kwana biyu jikin sa ya warware har ya fara fita office. Fushi yai da Mom ya dena zuwa gidan ta, tunda ta ƙi yarda da shi shikenan. Har yanzu kewar Aaliyah ya ke yi sosai amma yanzu ya rage tunani ko dan saboda matsalolin kamfanin sa da ya sa shi a gaba... Sati ɗaya bai je gidan Mom ba sai yau. Da ya je ya samu Jiji kaɗai ta ce ma sa sun tafi airport ɗauko Aaliyah. Wani daɗi ya ziyar ce shi amma da ya tuna share shi da ta yi kusan wata uku da sati biyu sai ya haɗe rai yai wa Jiji sallama akan zai tafi. "O'o yaran zamani kenan. Yanzu kai ma ƙorafin bakin za ka yi irin na Isma'il? Ku na son abu amma ku dinga shareshi. Zamanin iyayen ku ba haka su ka yi ba, soyayya ai sai Aaliyah da Sa'eedun ta" Take annurin fiskar sa ya ɗauke jin kalaman Jiji wato wancan guntun saurayin nan da ya ke ma sa girman kai yana ma sa kallon banza son Aaliyah ya ke. No wonder tun day one da su ka fara haɗuwa ya ke haɗe ma sa fuska. Zai tafi Jiji ta ce "yanzu ba za ka jira su dawo ba" "Zan dawo da dare Hajiya" ya faɗa yana ficewa daga falon. Ofcourse zai dawo ko dan yai wa ƙaramar yarinyar nan rashin mutunci for making him suffer. Ba taɓa tunani yarinya kamar Aaliyah ce za ta gigita shi ba. Bai taɓa damuwa da Zahra kamar yadda ya damu da ita ba. Kafin ya bawa Zahra chance a rayuwar sa sai da su ka ɗau kusan wata shida tana fafatawa da shi, and even after that ba wai ta wani samu kan sa ba ne. But this girl, this girl... Yana karyowa da motar sa zai fita Maigadi ya buɗe ƙofa sai ga motar Abba ta cuso kai wanda ya sa dole ya ja tashi motar baya. He wanted to leave amma kuma sai ya tsinci kan sa da kasa hakan, dole shima ya fasa fitan ya gyara tsayuwar motar ya kasheta. Ta window ya hangi fitowar ta daga mota sai murmushi ta ke yi, ta ƙara haske ga 'yar ƙiba da ta yi. Sai da ya gama ƙare ma ta kallo sannan ya fito daga motar yana wani haɗe fiska. Abba ne ya fara mi shi magana bayan sun yi musabaha "Son barka da zuwa, lafiya kwana biyu ba ka zuwa?" Mom ta ce " fishi ya ke da ni ai" Abba ya ce " ki dena sa ɗa na cikin damuwa za mu yi faɗa" Ya dafa Zaid ya ce lets get inside. Mom da Aaliyah su ka bi bayan su da kallo. Aaliyah kam sai ta ga ba ƙaramin ramewa ya ma ta ba. Tunanin ta ko dan Zahra ta yi aure ne... ................. Yana gidan har ƙarfe tara na dare. So ya ke ya samu daman yi ma ta magana su biyu kacal amma hakan bai yiwu ba. Kowa nan nan ya ke da ita. Su na tareda Abba ya ga giftawarta zuwa kitchen, yai saurin miƙewa ya bi bayan ta lokacin Abba na waya su kuma yaran sun shagala da kallon da su ke yi. Ruwa ta tsiyaya a cup ta ke sha lokacin da ya shigo kitchen ɗin. Tsayawa yai yana kallon ta, sai da ta ajiye cup ɗin ta juyo ta gan shi, tsorata ta yi dan ba ta san lokacin da ya shigo ba. Matsowa yai kusa da ita ta ɗan ja baya har ta bugu da kitchen island. "Sannu, sannu da ƙoƙari. Tafiya ba sallama, ba waya ba komai. Why?" Sai ƙyafƙyafta ido ta ke ta kasa magana. Ƙara matsowa yai wanda ya sa kusancin su yai yawa har su na shaƙar numfashin juna. "Why? Saboda kin san zan missing ɗin ki? Saboda kin san zuciyata za ta wahala saboda ke?" Ta girgiza kai a hankali. "Because i kissed you?" Ta haɗiye miyau da ƙyar tana ɗauke idon ta daga na shi. "Ki yi magana ko na miki abinda na yi ranan" Ta yi saurin zaro ido tana kallon sa. Ya tanƙwara kan sa zai kissing ɗin ta ya ji an murɗa kunnen sa. "Naughty boy, daga zuwa za ka dami 'ya ta" "Mom...Mom..." Mom ta sake murɗa kunnen ya saki ƙara "Arrrhhh" Mom ta ja shi su ka bar kitchen ɗin. Aaliyah ta yi murmushi saboda abin ya ba ta dariya yadda Mom ta ke murɗa ma sa kunne. Sai da za ta fito daga kitchen ɗin ne ta ji kunya ya cikata dan ta fara jin hayaniyar Mom da Zaid a falon. Ta dai daure ta fito da sauri ta haura sama... Sati biyu da dawowar Aaliyah, Wakilan Zaid su ka je ƙauyen Durum su ka kai sadakin Aaliyah. Mom ne ta zaɓi ayi bikin ƙarshen shekara wanda ya saura sati biyar kenan. Ƙiri-ƙiri Zaid ya nuna sati biyar ya ma sa nisa, Mom ta ce idan ya isheta za ta sa a maida bikin nan da wata shida sai ya kame bakin sa dan yanzu Mom ba ta ma sa da sauƙi. Soyayya mai tsabta Aaliyah da Zaid ke shimfiɗawa. Tun tana jin kunyar su Abba da Mom idan ya zo har ta sake jiki, domin Mom kam ba ruwan ta nunawa ta ke ba komai. Shirye-shirye ake sosai ba kama hannun yaro. Idan da ta Abba ne ba ya so a yi wani hayaniya amma Mom sam ba ta yarda ba. Bikin Zaid ne fa ɗa ƙwalli ɗaya da Allah ya ba ta, ga Aaliyah ma ita kaɗaice mace cikin 'yan uwanta. Abin mamaki tunda aka saka lokacin biki sai ga 'yan uwan Ahmad kaf ɗin su sun haɗa kuɗin gudumawa sun turawa Mom. Dukkan su sai wani haba-haba su ke da bikin ɗa namiji guda da Ahmad ya haifa. 'Yan uwan Mom ma ba a bar su a baya ba, su ma sun haɗa na su gudummawa... Daga Borno aka kawo mai gyaran jiki aka fara yiwa Aaliyah gyara, cikin ƙanƙanin lokaci jikinta ya amshi gyaran, kallo ɗaya ka ma ta sai ka sake waiwaya ka ma ta na biyu. She looked adorable and stunning... Yau da gobe sai Allah a haka satin biki har ya waiwayo. Tun daga ranan talata aka fara buduri ba a ƙare ba sai saturday da aka ɗaura aure. Biki ne aka yi na zamani wanda aka kashe kuɗi na fitan hankali, bikin ya zama talk of the town kuma ya ranking #1 a jerin bukuwan da aka yi a gaba ɗaya shekarar 2018 wanda ya doke bikin Zahra MCcollins da angon ta El-Bashir Lawals da ke ranking na ɗaya a da. Ita kanta Zahra da ta ga hidiman bukukuwan sai da ta ji kishi ya ɗarsu a ranta. Zaid has always being the best lover she had, har yau tana jinjina ma sa domin shi mutum ne da ba ya neman mata, banda sigari ba ya shan komai. El-Bash is trying his best saboda har yanzu su na cin honeymoon ɗin su but few weeks to their wedding ta rinƙa uncovering past na shi. Akwai tons of ex-girlfriends da ya ke da shi ga kuma 'yan matan da ya nema a baya wanda tana da yaƙinin ba wai ya dena halin sa ba ne kawai dai ya rage ne for marriage sake. Kyau da kuɗi su na da masifar tasiri wajen jefa namiji ga neme -nemen mata ko da bai shirya ba tunda matan ne za su dinga yi ma sa tallen kan su. Its so difficult to deal with an unfaithful husband. Ta haƙura da Zaid ne ba dan komai ba sai dan abu biyu. Na farko yadda duk 'yan uwanta su ka juya ma ta baya gameda shi, na biyu kuma girman kai. Ta riga ta karanci Zaid ya faɗa soyayyar wata daban ba ita ba, soyayyar da ta ɗau tsawon lokaci tana jira ta sameshi a wajen sa. No doubt ta san Aaliyah ce, yarinyar mijin Maman sa. And it hurts her a ce all this while su na tare amma bai ma ta so kamar yadda ya ke yiwa Aaliyah ba. In the end ita ce Zahra MCcollins. And when you are a rich girl, you keep yourself busy building your image, ba ta da lokacin biye ma El-Bash tana arguing da shi akan matan da ke kiran sa. She's a busy woman and a celebrity. Shi ma ba wai yana takura ma ta ba ne with her fancy life tunda shima ba ta takura ma sa ba. Mafiya yawanci mutane ma su kallon Vlogs na ta su kan concluding aurenta da rayuwar ta is perfect, sai dai ita kaɗai ta san how distant she is with her spouse. Zamani ne ya kawo lokacin da za ka dinga potraying perfect life ɗin ka a media while in truth your life is full of shit... 'Yan uwan Zahra ma jikin su ya yi sanyi ganin yadda Zaid yai biki na gani na faɗa. Sun riga sun tsammanci karayar arziƙi za ta samu Zaid but thats not the case, ya setteling bashi da ake bin su sannan kamfanin sa is doing well duk da dai zai ɗau lokaci kafin komai ya dawo normal a kamfanin. Batun ɓata suna kuwa nobody is talking about it. An manta da wata greedy tsohuwa wai Hajiya Inna. Shiyasa ake so mutum ya shuka alkhairi, gashi few months da ɓacewar Inna an manta da ita nobody cares whether she's death or alive. 'Ya'yan ta ma sun amince a ran su ta riga ta mace a wani waje... Mom ne ta ɗauki nauyin gyara gidan Zaid wanda ta riga ta maida takardun gidan zuwa sunan shi, gidan ya fito sosai ka ce sabon gini ne. Abba ma ya yi rawar gani wajen yiwa Aaliyah kaya duk da kuwa auren tuwo na mai na aka yi. Daren ranan Asabat aka kai Aaliyah ɗakin mijin ta, yadda ka san wata duniya za a kaita haka Aaliyah ta yi ta rusa kuka lokacin da za a tafi da ita. Hajiya Jiji na ɗaya daga cikin wanda su ka raka amarya ɗakinta. Tareda Hajiya Sanah da Hajiya Safiya da matar Uncle AbdulWahab wato Hajiya Misturah, sai Hajiya Asabe ƙanwar Abba da su ke uba ɗaya. Sai sauran cousins da Aunties... *** Ƙarfe tara da rabi aka watse aka bar Amarya Aaliyah a ɗakinta. Ta yi kukan har ta gaji, ciwon kai sosai ta ke ji kamar goshinta zai tsage. Ƙarfe goma da rabi Zaid ya shigo ɗakin, he's happy to finally see her as his wife. Akwai daɗi ka auri wanda ka ke so kuma ya ke son ka. Ya gode Allah da bai sa ya auri Zahra ba baya tunanin zai ji farin ciki irin yadda yake ji yanzu ba. Kamar ko wani ango yana so wannan dare ya zama mai tarihi a rayuwar sa amma kuma kash Mr Red ya ma sa tsiya. Shi ɗaya yai sallar nafilah yai wa Allah godiya for giving him the love of his life , he prays rayuwar su ta yi tsayi haka soyayyar su ta jure duk wani trials da za su fiskanta a rayuwar su. He promised to love her more than Sa'eed Modibbo loves Aaliyah Bulama. Bayan ya gama addu'o'i sannan ya kawo mu su kaza da yoghurt su ka ci. Sai da ta yi wanka ta chanja kaya su ka kwanta akan gado manne da juna ba ta da wata fargaba tunda ta san duk ɗokin sa dai yau kam ba hali. Ba ta farka ba sai ƙarfe takwas, lokacin da ta tashi gajiya da ciwon kai ya ragu. Ta fito daga wanka kenan Zaid ya shigo. "Good morning Angel" Ta yi murmushi tana cewa "morning Honey" Ya zo ya rungumeta ya ce "Mom ta aiko mana da abinci ba rin shirya ki sai mu je mu karya " Shi da kan sa ya goge ma ta jiki ya shafa ma ta mai sannan ya sa ma ta doguwar rigan da ta ajiye akan gado, ya kissing goshin ta ya ce "kin yi kyau" Kwana biyu su na gudanar da rayuwan su cike da farinciki. Yau ne dare na uku da kawota gidan Zaid, su na kwance Zaid ya ce " Angel har yanzu baƙon nan bai tafi ba ne?" Ba ta amsa ba ta sa dariya "Kwana nawa ki ke yi ne?" ta ɗaga ma sa yatsu shida "Gaskiya gaskiya gaskiya" ya matseta jikin sa yana shaƙar ƙanshin jikinta ita kuwa sai dariya ta ke yi. Bayan ta yi tsarki sai da ta ƙara kwana ɗaya kafin ya gane ta fara sallah. Tsoron haɗuwar su ta ke yi shiyasa ba ta gaya ma sa ba, cause Zaid bai yi kama da wanda zai ɗaga ƙafa ba. Daren ranan kuwa ta ɗanɗani abinda kowacce cikakken Amarya ke ji ranan farkon ta. Kuka da majina ta dinga yi tana kiran Mom ta taimaketa. He's first time and her first too. Dukkan su bayan abubuwa sun wakana zazzaɓi ne ya rufe su. Da ƙyar ya daure ya haɗa ma su ruwan wanka ya taimaka ma ta tayi wanka sannan shima yai. Ya sani ta ji jiki sosai amma ya zai yi its necessary. Shi kam baƙon yanayi na daɗi da ya sa duk ilahirin jikin sa ya amsa shi ya saukar ma sa da zazzaɓi haɗe da gajiyar biki da zirga-zirgan office. Bacci mai daɗi ya tafi da shi ita kuwa Aaliyah baccin wahala ta yi. Ranan da sassafe Mom ta kira bayan sun gaisa da Zaid ta tambayi 'yar ta. Aaliyah na kwance kan gado ya miƙa ma ta waya ta amsa tana gaisawa da Mom. Jin muryan Aaliyah a dashe ya sa ta tambayi ko lafiya? sai da Aaliyar ta ce mura ke damunta sannan ta fahimci mi ke faruwa, ta mu su fatan alkhairi tareda addu'o'i sannan ta kashe wayar. "Alhamdulillah" ta faɗa a fili. Abba da ke gefen ta ya ce "mi ya faru?" Mom ta ce " wannan sirrin mu ne ni da 'ya ta" Abba da ya ɗago zancen ya ce " ni ma Alhamdulillah ɗana ya zama cikakken namiji" Mom ta fara dariya. Abba ya tashi ya ma ta rumfa ya ce "nima barin maida tsohuwa yarinya" "Sweet love Yara za su je makaranta, ba rin je na haɗa breakf..." ya haɗe bakin su wanda ya hanata ƙarisa ƙorafin cikin ƙanƙanin lokaci su ka lula duniyar ma'aurata... *** Rayuwa kenan asha daɗi asha wuya. Rayuwar masoyan biyu gwanin sha'awa, kamar kowani aure akwai 'yan matsaloli amma Alhamdulillah koyaushe su na ƙoƙarin taƙile matsalolin su a tsakanin su. Yau, gobe, jibi su ke jujjuyawa har ayi sati, wata da shekara. Auren Aaliyah da Zaid na wata tara da kwana shida Aaliyah ta haifi kyakyawan babyn ta. Its as if tun ranan farko ajiyar Zaid ya zauna ajikin ta. Cikin bai ba ta matsala ba, sai da tana wata takwas ne ma ta yi wani kumburi sosai ga baƙi da ta yi. Alhamdulillah kuma haihuwar bai zo da wata matsala ba. Ana saura sati biyu ta haihu Mom ta sa Zaid ya kawota gida inda Mom ɗin ke ba ta kulawa na musamman. Ranan suna ma anyi shagali sosai kuma 'yan uwa dayawa sun halarci wannan suna. Yaro ya ci sunan Ahmad AbulKhair. Tsakanin Aaliyah da Zaid su ka zaɓi sunan ɗan su wanda ko Mom sai ranan suna ta ji sunan yaro, sosai ta ji daɗin takwara da Zaid yai wa Uban sa. Daren ranan sai da ta yi kuka tana ƙara yiwa Ahmad addu'ar Allah ya kyautata makwancin sa... A gida Mom ta ke yiwa Aaliyah wanka. Zaid tun yana sa ran nan da few weeks Mom za ta dawo ma sa da matar sa har yaro yai sati shida. Watarana da ya zo ya ke cewa shi dole zai tafi da matar sa Mom ta ce bai isa ba. Zaid ya tafi gida yana ƙunƙuni Washe gari da ya zo sai ga shi da akwatin kayan sa wai shima ya yi ƙaura ya dawo gidan. Mom ta ma sa tatas akan dole ya koma gida shi kuwa ya ce ba inda zai je, ƙarshe sai da Abba ya sa baki kafin ta amince Aaliyah za ta koma gidan sa ƙarshen sati... Yau gidan yai tsit ba hayaniya. Satin da ya wuce Aaliyah da Baby AbulKhair su ka koma gidan su inda ta haɗata da wata tsohuwa da Jiji ta kawo daga ƙauye da za ta dinga taimaka ma ta da wankan jariri. Jiya kuma yaran gaba ɗaya su ka tafi hutu ƙauye tareda Jiji. Nusrat ma an kaita hutu wajen Maman ta a Gombe da ya ke sun yi jarrabawar first term. Har lokacin da ta je ta haɗa breakfast ta dawo Abba na barci. Jiya daren Jummu'ah ne tun ƙarfe ɗayan dare ba su sake barci ba sai bayan asuba. Ta tsura ma sa ido tana kallon sa, ikon Allah kenan, sai gashi after all the long years of separation sai gashi Allah ya cika mu su burin su na zama miji da mata. Above all ya haɗa zuciyar 'ya'yan su har su ka zo su ka zama ɗaya gashi har da kyautar ɗa. Sa'eed ya yi gaskiya da a duk shekarun nan bai nemi su lalata soyayyar su da zina ba, bai bari shaiɗan ya ci galaba akan su ba. Uwa Uba kuma ya dinga nanata ma ta tasirin addu'a. "Mu dinga Addu'a Aaliyah, ka da mu gaji, Allah mai tausayi ne, zai ji tausayin mu ya sa komai ya zo da sauƙi. Despite everything ina da yaƙinin Allah zai ba ni ke a matsayin mata cikin sauƙi" He's right, he's always right addu'a tana maganin kowacce irin matsala. Za ka iya samun jinkiri amma duk lokacin da addu'ar ka ta ƙarɓu sai ka ga lokacin ne mafi alkhairi gareka. Gashi addu'ar su ta karɓu sun zama mata da miji cikin sauƙi. Da ke ta shagala da tunani ba ta san ma har ya farka ba sai kawai ta ji harshen sa a kumatunta yana lashe hawayen ta. "My love har ka tashi" "Baby kin tashe ni dai, hawayen ki su su ka tasheni. Kin san ba na son ganin hawayen ki" Ganin ya fara kissing ɗin wuyanta ya sa ta ce "hawayen fa bai kai wuya ba Yallaɓai" Murmushi yai ya jawota jikinsa ya ce " 'yan mata na miye matsalar? Miya saki kuka?" Ta ja dogon numfashi ta ce "i'm happy, i'm very happy, Allah ya bani komai. Everything is perfect now. Farin cikina ya cika" "Kin san dai Allah ya ce idan ka gode sai ya ƙara ma ka ko?. To barin nuna miki hanya ɗaya da za ki samu tarin lada" Murmushi kawai ta yi dan ta san inda ya dosa. A hankali ya ɗage rigar ta sama ya fara shafa nonuwanta kafin daga baya ya sa harshe ya fara tsotsan su. Aaliyah Badamasi Bulama ta lumshe ido tana jin daɗi thinking about the days she hated sex and how miraculously komai da ya zama duhu a baya ya koma haske. Gashi yanzu tanajin daɗin duk abinda mijin ta ke ma ta. Lokacin da ya shiga can ciki yana buga mata abunsa ta ji ya kai inda takeso ta fara saka ihu a hankali. This time ba ihun wahala ba ne ba kuma na zafi ba, ba kuma na tsanar mutumin da ke kan ta ba ne, ihu ne na ni'ima,na jin daɗi, na gamsuwa. Ta cigaba da faɗin "Arrhh Arrhh Arrhh" tana rirriƙeshi... *Alhamdulillah* A nan na kawo ƙarshen labarin tsohuwar soyayya. Za ku ga ban tsawaita soyayyar Aaliyah da Zaid ba simply because jigon labarin ba na su ba ne na iyayen su ne. How they loved each other and how their love was tasted with 30yrs of separation. Komai yai farko zai yi ƙarshe haka nan duk abinda Allah ya rubutawa bawa ba makawa sai ta auku gareshi may be not the way you wanted but in the best possible way for you. Tsohuwar soyayya has being a slow project ba kaman Sakatariya ta saboda one thing or the other. Na gode da baku gaji da ni ba sannan ku ka yi haƙuri har ƙarshe. Ina godiya da ihsanin ku gareni wajen biyan kuɗi dan ku karanta labarin nan. Jazakumullahu khairan, Allah ya sa albarka a rayuwar ku, gidajen auren ku, sana'o'in ku, karatun ku, aikin ku, 'ya'yan ku da ma iyayen mu gaba ɗaya, Amin. Allah ya yaye mana dukkan matsalolin mu Amin. Addu'a da tawakkali works hand in hand. Ka da mu taɓa gajiyawa da addu'a dan kawai addu'ar mu ba ta karɓu a lokacin da mu ke so ba. The more you believe in your prayers being answered the more your prayers will be answered fast. Bayan addu'a mu lazimci sadaka. Ba wai sai mun tsawwala ba amma kana ci kana sha kuma ga lafiya sannan kana samun abun hannun ka dai-dai gwargwado. Ai zai kyautu idan ya zamana duk wata kana fitar da wani abu dan ka yi sadaka da shi. Idan kana da hali duk sati. Sadaka ba sai kuɗi ko abinci ba. Ko takalmin ki da ya ɗan kwana biyu kika bawa 'yar maƙotan ku da su ke da ƙaramin ƙarfi compared to ku za ta ji daɗi hakanan za ki samu lada. Yawan sadaka da kyauta da azkar yana saurin sa addu'o'in mu su dinga karɓuwa da wurwuri. ********************** ⬇ ************************** ************* Ai Hausa Novels **************** *************************⬆ ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ⬇ ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ⬆ ************************** Jinjina ga dukkan ku 'yan Tsohuwar soyayya Paid Group musamman Anty Hauwa Jiddah Anty Surayya Lawal Anty @Princess Salma Sisi mi Aisha Modu Alkali Mommy Zainab Jinindabo Malama Najah Hajia Bilkisu Hajiya Hauwa Anty Sameerah Mom Khady... Kai ba za ku irgu ba. Ina godiya sosai.