[1/21, 9:44 PM] BintaUmarAbbale: _MASHAHURI!_ *************************⬇********************** ************* Ai Hausa Novels **************** *************************⬆ ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ⬇ ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ⬆ ************************** *_Mallakar: Binta Umar_* *_Don Allah kar ku futar min da book ku kasance masu amana!!!!!!!🤝🏻_* *31* Hanifa sam bata yi wani Karin kummalo me dad'i ba duk wani Abu da take yi tana yi a tsorace! Ganin yanda Nasir ya tsira mata idonsa yana tuhumatar dasu yasa gabanta ya tsananta fad'uwa simi-simi ta mi'ke ta futa, duk babu Wanda ya damu da futar ta sai da Ammi taji motsi kamar ana wanki yasa tayi magana kamar haka. "Hanifa wanki me kike yi da safiyarn nan madadin kizo kiyi shirin makaranta sai ki kama wanki." Muryarta na rawa tace"Ammi hijab dina nake wankewa duk ya 'baci da fallatsin kwata." Ammi tace"Yau babu zuwa makaranta kenan."!? Shiru tayi tana cigaba da durzar hijab din. Abbu yace." Dole yanzu idan na futa in tsaya shagon malam Saleh na yanko mata yadin hijabai naga duk sunyi 'karanci." Nasir yace." Abbu ka bari zan siyo mata a kasuwa sunfi sauki." Abbu yace." To masha Allah Nasir Allah yayi maka albarka." Duk suke fad'i "Ameeen." Suka cigaba da hirarasu Hanifa na jinsu, sai da ta tabbatar da ta wanke hijab din sosai sannan ta hak'ura ta koma cikin dakin ta sanja kaya ta futo ta zauna a rumfar ji takeyi duk a takure, Nasir ne ya mike ya futa Hafiz ya bi bayanshi mintuna goma tsakani Ammi ta mike taje ta hadawa Abbu ruwan wanka kafin ya mike ya futa daga rumfar Hanifa suka bari ita kadai tana ta tunanin abunda ya faru ita da Khalid jiya ji tayi tsigar jikinta duk ta mike wani irin sanyi ya soma shigar ta tunda uwarta ta haifeta bata ta'bajin sha'awar d'a namiji ba sai akan Khalid sunkuyar da kanta tayi tana jin ruwan hawaye na kokarin zubo mata. Kamar daga sama taji muryar Nasir tsaye a kanta. Da sauri ta d'ago kanta tana kallonsa ganin idonta yayi yai ja yasa ya sassauta muryar shi yace." Zo muje ina son magana dake." Hanifa ta mike ta shiga daki domin dauko hijab shi kuma ya futa ya koma d'akin su. Cikin hijab ta futo suka ci karo da Abbu zai shiga band'aki ganinta cikin hijab yasa ya tambaye ta ina zataje muryar na rawa tace"Ya Nasir ne yake kirana." Abbu ya saki wani murmushi na jin dad'i yace." Kije gurin shi kinji ko Allah yayi muku albarka." A hankali tace"Ameen sannan ta wuce. Abbu kuwa cikin zuciyar shi yake tunanin yaran sun soma kulawa da junansu dama abunda yake so kenan. Hamdala yayi cikin zuciyar ya shiga bandakin bakinsa dauke da addu'ar da Annabi Muhammad Slw ya koyar. Nasir na zaune shi kadai a dakin Hanifa ta shiga da sallama, ya nuna mata gurin zama yana kallonta cikin nazari yace. " Hanifa jiya ina kike je cikin dare k'arfe goma sha d'aya na dare."!? Sunkuyar da kanta tayi ba tare da tace komai ba. Muryarsa ya kwantar sosai yace." Kinyi shiru bayan kuma kece kikace idan na rufa miki asiri zaki fad'a min inda kikaje ki yarda dani babu Wanda zan fad'awa." A hankali ta d'ago kanta ta kalleshi na minti biyu tayi 'kasa da kanta tace"Gidansu Asalamiyya naje."! Murmushi me ciwo Yayi kafin yace." Gaskiya ban yarda da wannan maganar taki ba, jiya fa naji jikin ki yana 'kamshin turare irin na maza ki fad'a mun Gaskiya kawai." Ranta ya d'an 'baci da maganar sa tace" Ya Nasir me kake nufi ne."!? Sassauta muryarsa yayi yace." Bana nufin komai dake sai alkairi." Tace" to ka yarda da maganar da na fad'a maka cewar daga gidansu Hanifa nake. " kai tsaye yace."To waye ya fesa miki wannan turaran na jikin ki me mugun 'kamshi."! Hanifa taji gabanta ya fad'i! shiru tayi domin bata da abuncewa Nasir ya cigaba da cewa"Idan baki fada min gaskiya ba to babu shakka Yanzu nan zan Sanar da Abbu abunda yake faruwa." Kuka ta fara yi masa ta kalleshi tana jin kamar ta gaggura masa mari tace"To ni na fad'a maka Gaskiya ta duk ka takura min me kake so nace maka ne."!! Murmushi yayi Wanda kana ganinsa kasan na takaici ne yace." Gaskiyar ki Sam bata samu muhalli a gurina ba shiyasa nake so ki fada min." Shiru tayi masa tana zumb'ura baki, mik'ewa yayi da sauri! Yana fadin"To tunda kin'ki bari kawai in je in fad'aw....... Kafin ya karasa ta mike da sauri! Ta tari gabansa tana share hawayen fuskarta tace" Wai Ya Nasir kana so ka had'ani da iyayena ne kome."! Girgiza kansa tayi yana jin tsananin 'kaunarta cikin zuciyarsa tace" To shine zaka fadawa Abbu." Yace." Ai kin ki fada min Gaskiya ne." Cikin ina ina tace"Ka koma ka zauna zan fad'a maka." Komawa yayi ya zauna itama ta zauna minti uku tsakani tace"Nifa ba gurin Wanda naje kamar yanda kake tunani kawai Ya Abbakar ne ya aiko kanwarahi Asalamiyya jiya wai inzo inji Mas........ Shiru tayi ta kasa karasawa Nasir yace."Kinyi shuru kuma." ? "Wai inzo inji wannan Mawa'kin nan MASHAHURI wai yana sona."! Nasir yaji wani irin fad'uwar gaba ta rikito masa jin abunda Hanifar take fad'a a take ya nemi nutuwarsa ya rasa gumi ya fara zubo masa kamar ba Safiya kallonta yayi idonsa duk sun sauya saboda tashin hankali yace." Da kike je me yayi miki ? Abunda nake so kawai ki fada min kenan." Gabanta na fad'uwa tace"Ni babu abunda yayi min." Bata ji zata iya fad'ar abunda Khalid din yayi mata. Cikin b'acin rai Nasir yace." Amma kike yi k'amshin turaransa ni zaki rai nawa hankali Hanifaa."! Jin yanda yake d'aga murya sama yasa ta d'ago kanta da sauri tana kallonsa domin kwata_kwata bata so su Abbu suji komai ta lura Nasir din kamar baya Cikin nutsuwar shi._Ni ko nace dole ne ya hau ka ce saboda yana kishin ki. Cikin wani sabuwar tsawar!Nasir yace." Zaki fada min abunda kukayi dashi ko sai na Zane ki a gurin nan."!? Kuka tasa zata futa daga d'akin yayi saurin tare hanya yana zare mata jajeyen idonsa cikin kuka tace." Ni ka matsa ka bani hanya na wuce kawai ka nayi min kallon 'yar iska da kake tuhumata kan wani abu daban." Marairaice fuskarsa Yayi kamar zaiyi kuka yace."Hanifa ki rufa mun asiri don girman Allah ki rike mun amanar kanki wallahi Hanifa tun kina zanin goyo Allah ya jarrabe ni da tsananin so da kaunar ki don Allah kar ki kware min baya Hanifa kar wani banza a waje ya yaudare ki, Hanifa kiji tausayin Abbu da Ammi da suke tsaye a kanki suka baki tarbiya don Allah kar ki zubar musu da mutumcin kar ki kunya ta su a idon duniya." Wani irin kallo ta watsa masa tana jin wani irin haushin sa da yace yana sonta danne 'b'acin ran dake taso mata tayi tace." Ya Nasir daga kawai ka ganni a waje cikin dare shine har ka fara zargina."!? Girgiza kansa yayi yana rike hannunta guda tayi saurin fuzge wa ta futa daga d'akin a fusace. "! Karo suka ci da Abbu ya futo daga wanka yaga fuskarta a murtuke kamar ma tayi kuka jikinsa ne yayi sanyi ya kira sunanta tsayuwa tayi tana sunkuyar da kanta. Abbu yace." Ke da d'an uwan naki kun fahimci juna ko."? Hanifa gabanta ya cigaba da fad'uwa shiru tayi Abbu yace." Kije idan na dawo anjima da yamma zamuyi magana dake." Da sauri ta shige daki lokacin Ammi na kicin fad'awa tayi kan gado ta fashe da wani irin kuka me cin rai itafa duk yanda za'ayi sai dai ayi amma baza ta yarda ta auri Nasir ba Sam baiyi mata ba wani 'k'ato dashi gashi gajere baki da ha'kora a bakinsa, kuka tayi tayi kafin taji motsin Ammi a dakin tayi lif! Ammi ta ji tana cewa"Hanifa futo ki tayani tsintar shinkafar nan ta yau ma bata da tsinta sosai Allah dai ya shiyasa yaron nan albarka."! Hanifa tasan kowa Ammi take nufi Nasir domin shine yake musu awo a gida shi kuma Hafiz tayi cefa ne watarana kuma Abbu yayi. Shuru tayiwa Ammi dake magana ita kuma sai tayi tunanin ko tayi bacci ne sai kawai ta k'yaleta ta cigaba da aikin ta. ***** Nasir kuwa sai da yayi d'an karamin hauka a d'akinshi Kafin ya samu ya dawo normal wannan karon ma duk ya fashe glass din wayarsa gurin kallon pictures din hanifa da yanda yake matse wayar a jikinsa, wanka yayi yana jin wani irin daci a cikin zuciyarsa babu shakka yarinyar shaik ta shammace shi bai ta'ba tunanin zai tsinci kansa a cikin wannan yanayin ba, dole ya sanja shawara baya tunanin aure ko kadan a rayuwar sa amma tsananin sha'awar yin sex da yarinyar shaik ta hadda sa masa yake jin zai ita yin aure domin bukatar sa idan ta taso amma Sam bai yarda da haihuwa ba. Yana d'acin rai ya shirya jikinsa tsaf cikin wasu had'addun k'ananun kaya da suka futo masa da sufar sa ta namiji ya dauki wayarsa me bala'in tsada wacce tayi ratsa-ratsa sim card din ya cire ya jefar da wayar a gurun domin shi kam wayar ta tashi daga aiki a gurin shi dole yanzu idan ya futa ya siyi wata. Kai tsaye part din Mamy ya nufa shiru parlor babu hayaniyar komai sama ya nufa Kafin ya shiga dakin Mamy din yaji hayaniya na tashi tsakanin iyayen nasa biyu Tsayawa yayi bakin 'kofar yana sauraron tashin maganar su Mamynshi yaji tana kuka tana fad'in"Har kullum ina 'kara fad'a maka cewa Wannan rayuwar da kake d'ora yaron nan akai ba mai kyau bace ka kasa ganewa abunda nake so in fahimtar da kai anan shine duk irin tarbiyar da ka bashi to ita zai bawa yaranshi, ni na zama 'yar kallo a cikin gidanan kome na fad'a ba'ayi kullum abunda kasa shi kakeyi Yanzu gashi ka bashi lasisin da zai futa yayi zina har fad'a kake yi cewar yaje ya aikata tunda kana da KUDI duk wannan abun ba yanzu nake jiye muku ba sai nan gaba."! Mamy ta k'arashe maganar ta tana kuka gami da cigaba da had'a kayanta Alhaji Tijjani dake tsaye kanta yana sakin murmushi cikin isa da 'k'asaita gami da izza da giyar kudi yace." Duk wani Abu da kike fadarshi a banza yake a gurina abunda NASA kaina shi zanyi ke baki isa ki hanani inji dadina ba kuma yarona baki isa ki hanashi yayi abunda yake so ba don haka kiyi abunda zakiyi."! Mamy ta cigaba da kuka tana hada kanta tace" Zanyi kuwa abunda nayi niyya domin bazan iya cigaba da zama wani ciwo ya kamani ba saboda wannan bakin cikin da kake kunsa min." Alhji Tijjani ya buge babbar rigarsa ya mike da niyar tafiya yana fadin "Kifi ruwa gudu da kafarki zaki dawo domin kin San aurana dake babu saki." Yana gama fadin maganar shi ya bude dakin karo suka ci da Khalid dake tsaye hannunsa duk biyun cikin aljuhu kanshi a 'kasa yana tunani tunda ya taso bai taba jin iyayen NASA sunyi fada da tashin hankali ba sai Yau babu shakka yasan ba tun yau ba Mamynshi Tana mutukar hakuri da halin dad dinshi domin shi mutum ne me mugun son kanshi da yawa gashi da baud'addan ra'ayi. Nasir ya d'aga kanshi ya kalli dad din nashi babu yabo babu fallasa ya bashi hannu suka gaisa yace."Dad me yasa Mamy ke kuka. "? Alhji Tijjani ns murmushi yace." Wai dole sai anyi maka Dole kayi aure kan nace a kyaleka shine take kuka har tana 'kokarin hada kaya zatayi yaji." Ya mutsa fuskarsa yayi yace." Dad muje dakin muyi magana kaji." Dad din ya kalli agogon hannunsa yace." Muje a gurguje banaso na makara domin zanyi wasu baki."Dakin suka koma Lokacin Mamy har ta gama had'a kayanta ta ta yafa mayafi suka shiga Khalid Yayi saurin rungume ta yana rarrashin ta tare da fad'in "Mamy plaesa stop crying ! Ki zauna zamuyi magana don Allah nima yanzu na janye 'kudirina na baya auran nake so." Mamy taji zuciyarta tayi sanyi don haka sai ta koma ta zauna gefan gado tana sauke ajiyar zuciya!.... *29/12/2019* _BintuUm@rAbb@le_ [1/21, 9:44 PM] BintaUmarAbbale: _MASHAHURI!_ *_Mallakar: Binta Umar_* *_Ki biya ki karanta cikin kwanciyar hankali, ke kuma da kika futar da book d'in kinci Amana!_* *08089965176* *07084653262* *0542382124.... Binta Umar gt bank* *32* Alhaji Tijjani ya kalli Mamy dake sauke ajiyar zuciya, murmushi yayi ya kauda kansa daga kanta yace." Tsofai-tsofai dake zakiyi yaji abunda bakiyi shi da 'k'uruciya ba yanzu zaki aikata shi kece baki sani ba aurana dake mutuwa ce zata raba." Idan da sabo Mamy ta saba jin ire-iren wad'annan kalaman daga bakinsa shiyasa Sam! Basuyi wani tasiri a zuciyarta ba. Khalid ya kalleshi tare da fadin"Dad kayi shuru ka bar maganar don Allah." Alhaji Tijjani yace."magana an barta my son Yanzu kai muke saurara a INA ka samo matar aure kuma 'yar wacece."!? Ajiyar zuciya ya sauke tare da fad'in"Dad ubanta ba wani bane a garin nan kawai ni ita tayi min." Alhaji Tijjani yace." Za'bin ka shine nawa insha Allah zan sanya ayi mun bunkice sosai kan yarinyar da iyayenta Kafin muje Neman maka auran ta." Ya mutsa fuska Yayi yace." Dad nifa bana so aja lokaci me tsayi ." Alhaji Tijjani yace." Daga nan zuwa gobe insha Allah zan gama duk wani bunkice na ka kwantar da hankalin ka." Khalid yace."Nagode Dad." Alhji Tijjani ya futa daga dakin da sauri domin har ya wuce lokacin futar sa. Mamy ta kalli d'anta tace"Myson da ni kuma nake cewa ko zaka auri 'yar gidan Momyn ka Mariya gobe insga Allah zata zo ma sai ku fahimci juna." "Mamy pls don Allah kiyi hakuri ki bar maganar yarinyar nan domin ni Sam bata yi mun ba wannan da zuciya take so din ita nake son aura." Mamy tace"Shikkenan Allah ya sanya alkairi yaushe zaka kawo mun ita mu gaisa."? Ji yayi gabansa ya fad'i da jin maganar Mamy din sai ya fara tunanin yaushe ma har sukayi sabo da yarinyar da har zai kawo ta gurin Mamy, take ya fara tunanin yanda zai bullowa al'amarin zuciyarsa tace" kana da kudi kawai abunda zakayi kaje gidan ka fara yi musu yayyafin KUDI komai ustazancin sa idan yaga naira sai ya watsar kudi sune 'kare magana.! ****** Kamar ko da yaushe ta futo cikin shirin zuwa makaranta Ammi tayi mata fatan dawowa lafiya, a nutse take tafiya Cikin sababbin uniporm dinta wanda Nasir ya kawo mata hatta da ni'kaf dinta sabo ne gidansu Asalamiyya ta shiga a gurguje suka gaisa da babarsu ko zama batayi ba Asalamiyya ta futo suka tafi. A hanyar su ne ta tafiya Asalamiyya tace"Wai Hanifa ya kukayi da MASHAHURI kuwa nagano yana tsananin sonki a 'kwayar idonsa." Hanifa ta ta'be bakinta tare da fad'in"Asalamiyya ki rabu dani da zancan wannan d'an iskan don Allah ni Yanzu addu'a nakeyi Allah ya cire min sonshi jiya da wani abun ya faru dani dake da Ya Abbakar kune sila domin da kyar na kwaci kaina daga hannunsa Ashe Dan iska ne." Asalamiyya tace"Kiyi hakuri don Allah wallahi ban San abunda za faru ba kenan nima Ya Abbakar ne ya takura min Dole sai naje na kiraki." Hanifa tace"Asalamiyya ke kawata ce tun ta 'kuruciya babu abunda zan 'boye miki wallahi inayi masa so Wanda bansan iya adadinsa ba amma yanzu bana jin zan iya auransa tunda hannunsa ya ta'bani naji na tsaneshi yanzu ina gani idan ya kama wata macan ma haka zaiyi mata." Asalamiyya tace"Dama tuntuni nake so ki fahimci cewar shi d'in ba tsararan ki bane Kiyi addu'a Allah ya za'ba miki miji mafi alkairi." Ajiyar zuciya ta sauke tare da fad'in"Insha Allah 'kawata ki tayani da addu'a.'' Suna wannan hirar suka isa makarantar. Tsaf! Ya shirya da niyyar shiga studio kasala da sha'awa suka hanashi kwanciya yayi parlor yana tunani har Mamy ta sauko daga sama ta ganshi cikin wani yanayi tace"Myson ya ka kwanta ne ka shirya tsaf kuma ka kwanta. "? " Mamy kasala nake ji wallahi ko na shiga studio din babu abunda zan iya yi ni bacci ma nake ji." Mamy tace"To Allah ya sawake myson amma kar kayi bacci da yamma." Gyada kansa kurrum yayi yana lumshe ido Mamy ta wuce kicin taso ta fahimci abunda yake damun Dan nata. K'arfe shida dai-dai suka futo daga makarantar a nutse suke tafiya ba kamar Hanifa da take tafiya kamar wata sarauniya ko me nata a nutse. Dai-dai inda yake parking din motar sa nan suka ga wata had'addaiyar mota sabuwa dal! Hanifa ta kauda kanta da sauri ta wuce tana d'agawa Asalamiyya hannu da ta shige gida, Khalid kuwa yana cikin motar duk yaga wuce warsu shima bai Dade da zuwa unguwar ba yana jiran futowar Abbakar........ Ta mirror din motar ya dinga kallon Hanifa yana sauke zazzafar ajiyar zuciya har ya daina ganinta a lokacin ne kuma ya koma ya kwanta kamar Mara lafiya Abbakar ya 'kwankwasa glass din motar ya bude masa tare da koma wa ya kwanta kallonsa Abbakar din yayi tare da fadin"Guy zamu je studio nan kuwa naga kamar kayi laushi wallahi. Idonsa a lumshe yace." Abbakar yarinyar shaik ta Shammace ni ta rusa min duk wani tsarina ada Sam bana ra'ayin aure amma a halin yanzu saboda yanda sha'awar ta take so ta kashe ni nake ji zan iya aure yanzu ita kad'ai nake muradi Abbakar kaina duk ya 'kulle bansan ya za'ayi na 'bullowa al'amarin ba." Abbakar ya kalleshi a nutse yace." Guy kana gani wannan abu zai yi kuwa? Nasan tuntuni akwai dabi! A tsakaninka da Ya shaik ina ganin ka tarowa kanka wata rigimar ne kawai." Lumsassun idonsa ya bude yana kallon Abbakar d'in yace." Na sani wallahi ni duk wannan baya damuna tunda ina da abunda zan toshe masa baki dasu so kawai ita yarinyar itace abunji ni kuma kasan zina ba halina bane da tuni an wuce gurin." Dariya Abbakar yayi yace." Baka da matsa da Hany domin ina da tabbacin cewar baza ta bujerewa soyayyar ka ba kawai dama shaik din ne abun dubawa amma kuma tunda kayi maganar kudi nasan kome zai zo da sauk'i. Key din motar ya mi'ka masa ya karba yana 'yar dariya yace." Gaskiya nima nayi mamakin Hanya tun ba"aje koina ba taci galaba akan ka." Khalid ya Dan ya mutsa fuskar sa yana sakin siririn tsaki yace." Nifa ba wai sonta nakeyi ba kawai dai inaso in kawar da sha'awarta da ta dameni shikkenan abunda yasa kaga na matsu in aureta ita kuma bata isa ta sani na aikata zina ba." Gyda kai abbakar yayi yana kokarin kunna motar yace." Gaskiya ne guy ai Hany ta tsinci dami akala Allah yasa kar tayi wasa da damarta." Motar ya ja suka bar unguwar. **** Hanifa kuwa sakewa tayi a cikin gida tana taya Ammi aikace-aikace har lokacin sallahr magariba a lokacin Abbu ya shigo gidan da sauri ta mike taje ta karb'i ledar da take hannunsa tana masa sannu da zuwa dafa kanta yayi yana murmushi yace." Hanifa Allah yayi miki albarka." Ammi ta futo daga kicin tana yi masa barka da zuwa buta ta mik'a masa domin tasan alwala zai d'aura Kafin yayi komai tunda lokacin sallah ne. Ko da suka shiga studio an had'a komai Khalid ya tsaya da niyyar fara wa'karshi yaji muryar shi na rawa ya gagara nutsuwa dole tasa ya matsa daga gurin hade da cire abun dake mak'ale a kunnanshi ya jefar a gurin cikin wata katowar kujera ya zauna ya dafe kansa Cikin damuwa yake mamakin kansa wato yanzu yarinyar Shaik baza ta bari yayi komai na rayuwa ba Kenan. "? Why! Abbakar ne yazo ya dafa kad'arshi tare da fad'in" Yans Guy ka fara Abu kuma ka zauna please kasa dauriya cikin zuciyarka mana."! Shiru yayi masa kawai Abbakar din yq zauna kusa dashi yana rarrashin sa tsawon mintina goma kafin ya d'ago kansa a hankali yace." Muje gidansu yarinyar Abbakar ita kawai nake da muradi na gani a halin yanzu." Abbakar ya kalleshi cike da mamaki! Lallai yanzu ya tabbatar Khalid din ya fada komar son Hany dama shi yasan babu da NAMIJIN Da zai ga siffofin yarinyar ya iya daurewa zuciyarsa duk abunda Khalid din a halin yanzu bai ga laifinsa ba A kasalance ya mi'ke Abbakar din ma ya mike yana d'an satar kallonsa ganin duk yayi wani laushi kamar ba Khalid din da ya sani ba namijin duniya muskili mai jan'aji amma ta farar d'aya soyayya na kokarin ta komar dashi malalaci! Gashi dai kiri-kiri ya shiga studio Amma ya kasa tsinana komai, ko a cikin mota ma ba wata hirar arziki suke ba,Abbakar din ne me jansa sa magana yana amsawa sama-sama, k'arfe Tara da kwata na dare sun shigo unguwar tasu, bayan sun futo daga motar Khalid yace." Kira Mobson yazo muje dashi ." abbakar ya futo da wayarsa ya kira Mobson din Wanda yake shirin tafiya club yana sanya da wasu 'yan iskan kaya, wando ne iya gwiwa sai k'aramar Riga da ta d'ame shi ya d'aura bandana a kansa gaban rigar dake jikinsa kuwa hoton mawa'kin nan ne wato macal jocson yace." Ni gani zan tafi club ne yanzu." Abbakar yace." Ka futo kawai gamu nan karasowa Mobson ya futo daga shagon sa ya kulle can ya hango su suna zuwa gurin shi ko. Suna karasowa ya basu hannu suka gaisa Abbakar yace." Gidan ya shaik zamu je." Dariya yasa yana nuna Khalid yace." Guy ka shirya wani wulakancin kenan!? Hahahahaha yau kuma akan me zamu je masa." Abbakar yace."Dallah ka nutsu malama neman aure zamuje." A zabure! Mobson yake kallonsu yace." Ban gane Neman aure ba? Hahahahaha. "! Ya kara sakin wata mahaukaciyar dariya wani kallo Khalid din ya watsa masa yace." Kaifa tsiyata da Kai rashin kamun kai dubi wata dariya da kake yi dallah malam muje mu." Mobson ya kunshe dariyar sa yana fadin "Muje to lallai yau zan sha kallo da dariya." Abbakar ya kalleshi a nutse yace." Na lura har yanzu baka fahimci inda abun yake ba, yau fa da wani sabon salo zamuje gidan ya shaik din don Allah ka nutsu kar kayi mana shirme domin yau bashi ne zai kaimu ba." Mobson yace." Wai don Allah da gaske ne Wannan maganar."!? Khalid yace." Eh ko akwai wani aibu ne."!? Girgiza kai Mobson yayi yace." No! Kawai dai naga abun ne akwai matsala kai ko Abbakar din kunsan ko a mafarki Shaik bazai tsaya yw saurare ku da wannan maganar ba amma dai tunda kunce zakuje muje in raka Ku."! Tare suka rankaya suka nufi gdan kamar zuwan su na farko lokacin da suka je Abbu ya koya musu ilimin jima'i. *30/12/2019* _BintuUm@rAbb@le_ [1/21, 9:45 PM] BintaUmarAbbale: _MASHAHURI_ *_Mallakar: Binta Umar_* *_Ki biya ki karanta cikin kwanciyar hankali ke kuma da kika futar da book d'in na barki da Allah!_* *08089965176* *07084653262* *0542382124....Binta Umar Gt bank* *36* Khalid ne ya d'auki Abbakar a motar dady d'insa suka wuce gida shi kuma Alhaji Tijjani da abokinsa sai bayan sunyi sallahar Insha a cikin kasuwar sannan suka nufi gidan Abbu cikin motar Alhaji Lawan din. Abbu na zaune a 'kofar gida kamar yanda ya saba hannunshi rike da alk'urani mai girma yana haskawa da torchlight 'karama karatu yake yi cikin nutsuwa da dadin sauraro can gefe suka yi parking din motar duk suka futo suna baza babbar Riga tuni k'amshin turaran su ya dume gurin kana ganinsu kasan Alhazawa ne, Abbu kansa a kasa yake sha'ko k'amshin turaran da yaji jikin Alhaji Tijjani d'azu a hankali ya d'ago kansa Wanda yayi dai-dai da karasowar su gurin. Sallama suka yi Abbu ya kai karshen ayar da yake kai ya amsa musu yana me rufe alk'uranin dake hannunsa gurin zama ya nuna musu dake irin k'atuwar daddumar nan ce Alhaji Lawan ya tube takalmin sa a nutse ya zauna shi kuwa Alhji Tijjani kamar ba zai zauna ba domin bai so Abokin nasa ya zauna ba a cewar sa daddumar bata kyau zasu iya daukar Datti da kyar dai ya zauna yana dauke kansa domin har yanzu yana jin zafin Abunda Abbu yayi masa. Cikin kamala da dattako Alhaji Lawan ya mik'awa Abbu hannu suka yi musabaha yana tambayar sa mutanan gida abbu yace." Kowa lafiya lau Alhmdullahi." Hannu ya mikawa Alhaji Tijjani tare da fad'in"Barka da dare Alhaji. " Alhaji Tijjani ya mik'a masa hannu yana fadin "Barka dai Arrama kaga mai bakin naci ya kara dawowa ko."!? Murmushi Abbu yayi kawai ya maida hankalinsa kan Alhaji Lawan da yake masa magana. " malam mun sake dawowa a karo na uku gurinka muna kara Neman alfarma a gurin ka ba don halinmu ba Malam idan har ka bamu yarka zamu rike maka ita da amana kamar yanda addini ya tanada Gaskiya banji dad'i Abunda ya faru d'azu ba ka dauke she abusa kuskure Alhaji duk yayi min bayanin komai kuma na fahimta shima na fahimtar dashi, Hak'ika Allah ya jarrabi yaron nan da soyayyar yarinyar ka don girman Allah ka duba al'amarin nan Arrama."! Alhji Lawan ya k'arashe maganar sa cikin kwantar da murya. Abbu yaji wani irin nauyin mutumin sosai yake jin nauyin ya d'ago kansa ya kalleshi har ya samu damar fadamasa abunda yake bakinsa shiru yayi yana tunani kansa har yanzu a kasa, Alhji Lawan yace."Aramma kar kayi kokwanto akan al'amarin insha Allah akwai alkairi a ciki muna sauraran amincewar ka." Abbu ya dago kansa a nutse yace."Alhaji wallahi kafi k'arfin kazo Neman Alfarma a gurina na kasa yi maka ita mutukar ina da iko da ita wallahi idan da babu maganar Nasir a kasa to babu shakka zan bawa yaron nan Hanifa ya aura duk da cewa tarbiyarsa bata yi min ba, to amma babu yanda Allah baya shirya bawansa watak'ila ta dalilin auran ma sai ya shiryu ya gyara halayen sa."! Alhaji Tijjani yaji kamar ya shake Abbu wato saboda samun dama a gabansa yake kokarin aibata d'ansa kawai saboda sunzo Neman alfarma a gurin shi babu shakka da badon wanann al'amarin ya ratsa ba da babu abunda zai hanashi ya daure shi saboda yana kokarin shiga hurumin da bana shi ba, a ganinshi kamar Abbu yana so yayi danshi baki. Abbu ya cika da cewa"Alhaji ka dubi girma irin na al'kawari kayiwa magana ta kyakyawar fahimta akwai yaron yaya ta Dana rik'e ya girma a hannuna ya nuna min yana son Hanifa tun tana k'arama yake dawainiya da ita Nasir babu abunda zai nema a gurina na hanashi nine uwarshi nine ubanshi tunda na fahimci haka nayi masa alk'awarin aura masa Hanifa saboda na yarda da tarbiyar da na bashi, shi yasan da wannan alk'awarin ni nasa ni mahaifiyar sa ta sani hakanan mahaifiyar hanifa ta sani garin mu da duk wasu dangina sun San da wannan alk'awarin ita kanta Hanifar na kira ta na shaida mata kudirina akanta ta sani kaga yana da kyau in cika wannan alk'awarin da na daukar wa yaron nan domin kubuta daga fushin ubangiji ina yi wa wannan yaron fatan alkairi a rayuwar sa Allah ya mu sanya masa da wata wacce tafi Hanifa komai na rayuwa." Shuru gurin yayi bayan Abbu ya gama maganar shi tabbas maganar da yayi abun dubawa ce, Alhaji Lawan yake maganar cikin zuciyarsa kafin ya d'ago kansa ya kalli abbu zuciyar sa duk babu dad'i yace." Arrama abunda nake so ka fahimta anan shine ita rayuwar nan da kake gani tana tafiya ne da ZAMANI tabbas Annabi Muhammad (Slw) ya hore mu da zabawa yayan mu miji suna 'yan mata wato idan zamuyi musu auran fari, a shekarun baya iyayanmu da kakaninmu duk irin wannan auran akayi musu har muka zo wannan duniyar, mai cike da rud'u Abunda nake so ka fahimta anan shine baza ka hada wancan lokacin da wannan ba domin Zamani ya sauya irin wannan auran da kake kokarin hadawa yana iya lalata zumunci tunda abunda na fahimta a maganar cewar ita yarinyar taka baka bata za'bi ba baka tambayeta shin tana son zabin da kayi mata ko kuwa bata so domin samun nutsuwar ta, yaran yanzu da nada ba daya bane idan shi yana so ita kuma bata so kaga akwai matsala babba kofa anyi auran za'ayi ta samun matsala kamar yanda kasani nima na sani cewar babu abunda yake damun Al'umma a halin yanzu irin yanda zamantakewa ta aure ta lalace kuma al'amarin duk ya samo Asali ne daga faruwar irin wannan Abu damu iyaye muke yi, arrama yana da kyau ka zauna da Yarinyar nan ka tambaye ta ra'ayin ta kan zabin da kayi mata saboda gudun afkuwar wata matsalar wacce ba'a fata. Abbu yayi shuru yana tunanin maganar Alhaji Lawan baya shakka da irin tarbiyar da yayi wa Hanifa kuma yasan baza ta bashi kunya ba kamar yanda ta fada masa zata yi masa biyayya shi yasan nan gaba zata fi kowa murna da jin dad'i bayan ta mallakin hankalin kanta zata San baza zaben tumun dare yayi mata ba. Yace."Alhaji duk naji maganar insha Allah zan zauna da yarinyar muyi maganar da ita idan ta nuna bata son Nasir zan bukaci ta kawo min zabin ta idan ya kasance shi wannan yaron naku ne to insha Allah zaku ji daga gare ni." "Alhamdullahi."! Alhaji Lawan ya fada da murmushi ya fuskar sa yace." Mungode K'warai arrama kuma muna sauraran ka daga nan zuwa wane lokaci."!? Abbu yace." Daga nan zuwa gobe insha Allah." Alhaji Tijjani ya sauke ajiyar zuciya tunda suke maganar sai yanzu ya samu sassaucin a zuciyar sa ya kalli Abbu a nutse yace." Muna saurare domin yaro yace baya bukatar aja lokaci in yaso sai ka yanke sadakin yarinyar ka." Takaici bai bari Abbu ya bashi amsa ba kawai hannu ya mik'awa Alhaji Lawan suka na sallama cike da mutumuta juna." [1/3, 10:30 AM] .: Bayan tafiyar su Abbu ya jima a gurin yana tunanin maganganun alhaji Lawan sosai suka shiga jikinsa kamar yanda ya dauki alk'awarin zai zauna da Hanifa to babu shakka zai zauna da ita gobe da safe domin yaji meye ra'ayin ta a game da auran Nasiru. Yana kokarin shiga gida lokacin su Nasir din suka dawo tare suka shiga cikin gida Nasir hannunsa rike da daddumar Abbu. Ammi tayi bacci hakama Hanifa tayi bacci bayan ta gama koke-koken ta. Alhaji Tijjani na Sanar da Khalid abunda abbu yace take yaji wani irin sanyi ya dura a zuciyarsa da yana zaune yana d'acin rai Mamy sai lallabashi takeyi yaci abunci yana kaucewa murna tasa shi ya zage ya cika cikinsa da abinci yana hira da iyayen NASA har da dariya Mamy ta dinga mamakin sa sai dai tayi shuru kawai tana addu'ar Allah yasa yarinyar rabonshi ce don ta lura yaron nata bai iya so ba, Alhaji Tijjani kuwa yaji dad'i sosai da yaga Khalid din ya saki jikinsa har sa dariya, dama shi babban jin dadin sa a duniya walwalar danshi don bai fiye damuwa da damuwar yayan shi mata ba sai da ita Mamy itace me nuna kulawa a kansu. Anan parlor suka barshi yana kallo Sam ya'ki komawa part dinshi, kallon wa'kokin turawa yake wata mawa'kiya Nicky minaj tana wa'aka sosai yake son yarinyar da muryar ta mik'ewa yayi zaune yana kallon siffar jikinta gaban shi ya fad'i Cikin rawar Hannu ya dauki wayarsa ya fara duba pictures din Hanifa tsarin jiki da yanayin fadin 'kugu gami da cikar nonowa duk irin nata ne sai da Hanifa tafi ta fari gami da girman idano wata lafiyayyar ajiyar zuciya ya sauke a take muguwar sha'awar sa ta motsa masa pictures din yake kallo jikinsa na tsuma jijiyarsa ta mike da 'karfin ta sai motsi take masa, kwanciya yayi kan doguwar kujera yana rintse idonsa tare da hade kafafunsa guri daya nishi yake saki yana kara matse wayar a k'irjinsa, wasu zafafan hawaye ne suka fara zubo masa ta gefen ido, cikin futar hayyaci ya mi'ke zaune hade da jefar da wayar kan kujera kanshi ya dafe duka sa hannunwan sa biyu har yanzu idonsa a rintse yake yafi minti talatin Cikin wannan halin kafin ya fara dawowa dai-dai ya mike da sauri ya futa tsit!!! Harabar gidan sai haske ko ina part dinshi ya bude ya shige kai tsaye toilet ya nufa ruwan sanyi ya dunga kwarawa a jikinsa yana makyarkyata gashi dai lokacin anyi ruwa an dauke gari ya dauki sanyi haka Khalid ya dinga zubawa jikinsa ruwa ya futo daure da towol zubewa yayi kan bed yana numfarfashi blanket ya jawo ya rufe jikinsa gabadaya har fuskarsa Kafin kice kwabo jikinsa ya rikice zazzafan zazzab'i ya rufe shi! **** Jiki a sanyaye take yi komai tunda ta tashi taki sakewa da kowa gabanta sai fad'uwa yake yi Karin kummalo ma kamar bata so haka tayi kamar yanda ta saba bayan taga ma karyawa ta mike zata shiga daki Abbu ya dakatar da ita, komawa tayi ta zauna tana jin sabuwar fargaba... Mik'ewa yayi yace." Hanifa kizo d'akina yanzu zamuyi magana." A hankali tace."To Abbu." Wucewa yayi Ammi tace"Zaman me kike yi munafuka ki tashi ki bishi kuma kiyi masa biyayya Hanifa ni yanzu lamarin ki ya soma bani tsoro." Jiki a sanyaye ta mike tabi bayan Abbu tana mamakin Ammi wai yau ita take kira da munafuka." Sosai taji ciwon abun har sai da hawaye suka zubo mata saurin gogewa tayi ta shiga dakin Abbu bakinta dauke da sallama. Yana zaune gefan katifa ya amsa tsuguna wa tayi bakin kofa yace." Karaso ciki sosai ai sirri zamuyi." Hanifa ta matsa ciki sosai tana sinne kanta gabanta sai dukan uku-uku yake. Shiru na minti biyu Abbu yayi gyaran murya tare da fad'in"Hanifa ina so ki fad'amin gaskiyar abunda zan tambaye ki kar ki munadurce ni kar ki kuma munafurci kanki ni mahaifin kine me kaunar farin ciki, ina so duk wani abunda yake ranki ki fadamin shi kinji ko."!? Daga kanta tayi tare da fadin"Insha Allah Abbu zan fada maka." Abbu yace." Alhamdullahi haka nake son ji daga gare ki, shin Hanifa meye ra'ayin ki a game da auran ki da Nasir ma'ana kina sonsa ko bakya sonsa bana so daga baya kizo kina kuka dani duk ni nasan bazan zab'a miki abunda zai cuce ki a rayuwa ba duk inda nagartacan namiji yake Nasir ya kai shiyasa nake miki sha'awar auran sa INA so ki fadamin gaskiyar abunda take zuciyar ki." Shuru tayi batace komai ba yace." Ke nake saurare." Tayi shiru nan Abbu yace." Kar kiji nauyin komai ki fada min gaskiya." Muryarta na rawa tace"Abbu ni bani da zab'i kuma bani da ra'ayi sai naka nasan hazak'a zab'a min abunda zai cutar dani ba duk abunda ka yanke a kaina dai-dai ne." Abbu ya sauke ajiyar zuciya a fili yace." Alhmdullahi nagode Allah Hanifa Allah ya shi miki albarka nagode irin biyayar da kike min insha Allah kema yayanki zasu biki kuma insha Allah zakiyi alfahari dani a ko ina kike kuma zakiyi alfahari da zabin da nayi miki, dama maganar kenan ki tashi ki tafi." Hanifa ta mike da jiki a sanyaye ta futa daga d'akin...... Ammi ta kalleta lokacin da take shigowa dakin ganin yanayin fuskarta yasa ta aje tsintsiyar da take hannunta ta nufi dakin Abbu. Hanifa na ganin futar ta ta fashe da kuka tana damk'e bakinta da hannuta domin kar sautin kukan ya futo tunani takeyi yaya ma za'ace tace da Abbu bata son zabinsa mutumin da ya sadaukar da rayuwasa duk a Kansu ta gwammace son Khalid ya kashe ta kan ta fadawa Abbu cewar bata son Nasir su idan sun fahimci haka daga gurina sai su aura mata Wanda take so. _Hanifa kinyi ganganci_ ****** Ganin har k'arfe Tara da rabi Khalid bai futo ba yasa Mamy ta nufi part d'insa hannuta rike da wayarta tana kara gwada kira domin tun d'azu take kiran wayoyinsa duk a kashe dake a bude ya bar kofar dakin yasa tana turawa ta bude kai tsaye bedroom d'insa ta nufa nan ma tana tura kofar ta bud'e can ta hango shi kudundune kan bed da sauri ta karasa gurin tana fadin"Myson yaya ne blanket din take kokarin cirewa ya bude jajayen idonsa yana kallonta ganin yanda jijiyar kansa ta mike tayi rada-rada tasa hankalinta ya kara tashi ta cire blakent din tana ta'ba jikinsa taji zafi kau! "Innalillahi wa'ina ilahi raji'un! Myson me yake damun ka."!? Kansa ya nuna mata da hannunsa. Hannu na rawa ta fara laluben numbar family dactor masu wayar is switch up. Cikin damuwa tace" Myson tashi ka sanya kaya mu wuce hospital zafin jikin nan ka tayi yawa." A hankali yace." Mamy ki barshi kawai zazzab'i ne kuma Masha magani zai sauka." Girgiza kanta tayi tace"ban yarda ba kawai ka tashi muje asibiti a duba ka." Mik'ewa yayi yana ya mutsa fuska yace." Mamy Bari inyi wanka tukkuna." Cikin damuwa "Tace ka sanya rigarka kurrum muje idan ka dawo kayi wankan." "Mamy k..... Ka tseshi tayi ta hanyar daga masa hannu, yasan halin mamyn sa da damuwa shi kuma abunda yasa baya son ya mike a gabanta saboda babu kaya a jikinsa sai k'aramin towol kuma har yanzu joystick d'insa a tsaye take sai dai ba kamar jiya ba shi kanshi yasan wannan zazzab'in da yake yi ba na komai bane sai na tsantsar sha'awar da ta dame shi, Cikin sa'a kuwa ta mike da sauri wardrobe d'insa ta bude tana Ciro masa kaya shi kuma yayi wuf ya dira daga gadon toilet ya bude ya shige da sauri. Mamy ta juyo da sauri tana kallon kofar toilet din girgiza kanta tayi ta rufe wardrobe din bayan ta dauko masa Riga da wando Pakistan irin na maza zama tayi gefen bed din tana jiran futowar sa. *3/1/2020* _BintuUm@rAbb@le_ [1/21, 9:45 PM] BintaUmarAbbale: _MASHAHURI_ *_Mallakar: Binta Umar_* *_Ki biya ki karanta cikin kwanciyar hankali ke kuma da kika futar da book d'in na barki da Allah!_* *08089965176* *07084653262* *0542382124....Binta Umar Gt bank* *40* Khalid kuwa 'kin sakin jikinsa yayi a motar Hafiza sai jansa take da magana Yayi mata banza haushin abunda Mamy tayi ma yarinyar Shaik yake ji har yanzu don haka Mamy nayi parking ya bude motar ya futa kai tsaye part d'insa ya nufa Mamy da Hafiza suka bishi da kallo girgiza kai Mamy tayi ta bude mota ta futo Yana shiga dakinshi ya fara neman wayar dady nashi cikin sa'a ya samu wayar ta shiga ajiyar zuciya ya sauke a hankali yace." Dad ya kasuwar ? Tun d'azu ake Neman ka a waya ba'a samu ba."Yace." Ina tare da baki ne Myson amma yanzu sunyi sau'ki yanzu zan dawo gida Insha Allah. " "Dady ina fatan jin alkairi daga bakinka game da maganar Hanifa." Alhji Tijjani ya dawo nutsuwar sa sai yanzu ya tuna da maganar wallahi jama'a sun sanya ya manta yace." Myson ka kwantar da hankalin ka insha Allah zamu koma Yanzu ni da Alhaji Lawan insha Allah. " ajiyar zuciya ya sauke yana jin wata irin fargaba domin zuciyarsa bata bashi cewar za'a samu nasara Yace. " Shikkenan dady ina sauraran Ku." Kashe wayar yayi ya kwanta rigingine ya kurawa calling ido yana tunani abunda ya faru tsakaninsa da ita a d'azu Alhji Tijjani kuwa bayan sunyi sallahr Isha'i kamar jiya suka nufi gurin Abbu yau yana cikin gida sai da suka aika yaro akayi musu sallama dashi abbu bai bata lokaci ba ya futo dama ya tsammace su suka gaisa cikin mutumci Alhji Lawan yace." Arrama mun dawo domin karb'ar sakamako. " Shiru abbu yayi na minti biyu yace." Alhji kuyi hakuri don Allah kamar yanda na fada cewar zan zauna da yarinyar jiya to na zauna da ita kuma ta tabbatar min da cewar tayi na' am da zab'i na saboda haka ina yiwa Wannan yaron fatan alkairi." Alhji Tijjani yaji wani irin gumi na zubo masa yana mamakin Ashe a duniya akwai Abunda zaice yana so ya kasa samunshi. Alhji Lawan yace."To arrama babu komai Allah ya sanya alkairi a ciki mungode." Yanda ya fadi maganar zaka San ransa a bace yake. Alhji Tijjani kuwa bakinsa mutuwa yayi wani irin kallon tsana yake watsawa Abbu din ya buge babbar rigarsa ya bar gurin Alhji Lawan kuwa ya tsaya suna sallama da Abbu kafin ya biyo bayansa. Dady jikinsa babu kwari ya shiga gida duk da cewa kasuwa tayu kyau an samu kudi sosai amma yana fargabar tunkarar Khalid din da wannan maganar Mara dadin ji. Tun kafin ya shiga parlor ya fara jiyo hayaniya Maganar ta ya tsinta inda take fadin"Khalid indai nice na haife ka to ban amunce ka auri wannan yarinyar ba Ka auri NASIRIN idan baka sonta to kaje ka nemo wata yarinyar domin wannan yarinyar da kake so bana Allah da Annabi bane ko kunyi aure bazaiyi karko ba saboda kun gama ta'ba junan ku a waje idona yq nuna min na gani dama so nake mu dawo gida ayi wacce za'ayi domin wannan Koron ina ji ina gani baza'a yi Abunda bai dace ba. Cikin 'bacin rai Alhji Tijjani ya shiga ciki yana kallon yanda Mamy din tayi tsaye kan Khalid tana zuba masa masifa Yace." Wai ke Mamy me yake damun ki ne."!? Duka suka juyo suna kallonsa domin basu yi tsammanin shi ba Khalid ya dago idonsa Wanda ya kada yayi jazur yana kallon Mahaifin nasa, Dad din ya cigaba da cewa"Wannan yarinyar da kike ta magana akanta idan matarshi ce sai ya aurta idan kuma ba matarshi bace bazai aureta ba gwarama ki kwantar da hankalin ki akan lamarin ko da zina ya aikata da ita yana da damar da zai aureta kuma ke baki isa ki hana auransu yayi albarka ba ki tasa yaro a gaba kina zuba masa fad'a kamar me? To ki shiga hankalin ki."!!!! Mamy ta fashe da kuka tana fadin"Dady Abunda zakace kenan! Duk abunda na fada banyi karya ba kuma ga Hafiza nan shaida mungansu da Idan mu yayi k'aryar bashi da lafiya yarinyar tazo har asibiti sun kule kofa da kyar na samu ya bude kofar shine ya 'boye yarinyar a band'aki ."! Ko ba haka bane."!? Ta fada tana kallon Khalid din da kanshi yake sunkuye a kasa wani irin kyarma jikinsa yakeyi na tsananin b'acin rai ya rasa yaushe Mamynsa ta zama burkitacciya. Alhji Tijjani ya zauna kusa da Khalid din ya dafa kafadansa tare ra fadin"Abunda mahaifiyar ka ta fada gaskiya ko ba gaskiya bane." ? Kukan Mamy ya tsananta wato bai yarda ma sai ya tambayeshi Khalid ya dago kanshi sake Sara masa yace." Dad duk abunda mamy ta FAda haka ne." Gyada kai dady yayi yace. " mai ya kai ka hospital. " A hankali yace." Dad Mamy CE wallahi jiya na Dan kwana da zazzab'i amma kafin safiya ya sauka shine mamy ta matsa dole sai munje asibiti na samu Dr ya sa min ruwa naji kwari a jikina yanza." Gyada kai dad din yayi yace." Ya akayi kuka kulle kofa da yarinyar mutane duk dai nasan ka baka sha'awar aikita zina amma shaidan zai iya rijayar ka." Cikin damuwa Yace. " Dad yarinyar ce tazi duba jikina a lokacin to jin muryar Mamy din yasa na kulle kofa na b'oye ta a toilet saboda sanin halin Mamy din ba ta kaunar t....... Ya katse shi ta hanyar fad'in"Myson da gaske yarinyar na sonka shine mahaifinta yace ya zauna da ita tace ya zab'a mata miji a taikace dai mahaifinta Yace kayi hakuri ka nemi wata domin yayi mata miji Dan uwanta kuma itama yarinyar ta amunce da zabinsa ." A zabure! Yace. " Wallahi 'karya yake dad yarinyar shi bata da miji sai ni duk abunda ya fad'a muku yayi karya dady yarinyar itace ta fara nuna min so tun bana sonta na zo INA sonta kuma ko d'azu ta kara tabbatar min da haka tana kuka tana komai muka rabu da juna."! Alhji Tijjani yayi kasake yana tunanin wannan lamari Yace."Yanzu ja fahimci cewar wancan mutsiyacin mutumin me gemun banza shine bayaso ya baka yarshi yarinya na sonka shi kuma yana so ya rusa muku farin ciki saboda mugunta Wallahi da ina da hali sai na daure shi."! Ya k'arashe maganar a zafafe! Mamy kuwa komawa tayi ya zauna tana hamdala cikin zuciyata a ganinta tunda uban yarinyar bayaso to suma dole su hak'ura. Cikin wani irin yanayi na tashin hankali ya mi'ke tsaye kokarin futa yake duk suka bishi da kallo sai da ya kusa zuwa bakin kofa ya fad'i a gurin, cikin tashin hankali Alhji Tijjani yayi kansa yana salati. Mamy da Hafiza suka karasa gurin cikin tashin hankali Waje ya futa da sauri ya kira daya daga cikin securitys daukar shi sukayi suka futa, dravar ne ya bude motar suka saka shi ciki Alhji Tijjani ya shiga ciki da damuwa suka futa daga gidan Mamy da Hafiza suka shiga mota cikin damuwa suka bi bayansu. Hafiza hawaye take sharewa tana fadin"Mamy kinga irin abunda nake ka fada miki ko wannan fad'uwar da bro yayi tana nufin abubuwa da dama don Allah ki dinga hakuri Abu komai a sannu a hankali." Mamy shiru tayi kawai zuciyarta duk babu dad'i motar Dady din take bi wacce take wani irin gudu kan titi. Kai tsaye pravite hospital suka nufa emagancy aka nufa dashi Alhji Tijjani sai kaiwa yake yana kawowa a gurin yana ganin kamar Matar tashi ce silar faruwan komai wata zuciyar tace masa babu mutumin da ya jefa rayuwar danka cikin bala'i da damuwa sai wancan me gemun banza Wanda ya kasa fahimtar Abunda yake faruwa a take yaji wata irin tsanar Abbu ta kamashi cikin zuciyarsa yake fadin har in dai wani ciwon ya kama danshi ta sanadiyar wannan Abu to babu shakka sai yayi shari'a dashi. Ko dasu Mamy suka iso asibitin Alhaji Tijjani wuta ya bude mata sosai yake zazzaga mata bala'i yana "Fad'in" Idan kuka kasa zuciyarsa tayi buga dake da wannan mutsiyacin mutumin wallahi sai na daure Ku."! Mamy dai shiru tayi jikinta duk yayi sanyi yanzu kuma ta fara nadamar abunda ta aikata wa Dan nata hawaye ta share lokacin da ta tuno maganar da ya fada mata a asibiti d'azu da yake cewa"Mamy idan kina bukatar kwamciyar hankalina ki so abunda nake so shine zaki ga walwala ta da farin ciki." Hawaye ta share cikin sarewa da al'amarin, ya kalleta da fuska a turbune yace." Baki fara kuka ba tukkuna Wallahi wani ciwon ya kamashi sai na bata miki rai."! Hafiza da taga dady nasu yana daga murya tayi saurin karasawa kusa dashi tana rarrashin sa da kalamai masu dad'i da kwantar da hankali. Tana kuka tace" Dady me Dr yace game da Khalid din." Ajiyar zuciya ya sauke yana kallon yar tasa da damuwa a fuskarsa Yace. " an shiga ciki Dr bai futo ba tukkuna amma numfashin sa ya dauke gaba d'aya." Hankalin su ya kara tashi Mamy sai ta fara addu'a Cikin zuciyarta......Hafiza kuwa hawaye ta fara sharewa cike da tausayin Dan uwanta. Dr ya futo ya kira Alhji Tijjani wani ofis suka shifa Dr ya cire glass din dake idonsa Cikin damuwa ya kalle shi yace." Alhaji gaskiya an auna arziki sosai domin Yaron ka jininsa yayi sama irin Wanda ba'a so tsananin damuwa da fargaba gami da rud'u sune suka haddasa masa shiga wannan halin gashi dama babu cikakkyar lafiya a tare dashi shiyasa ya da ya mike jiri ya yar dashi yana da kyau a kiyaye duk wani Abu da zai bata masa rai ko kuma ya sanya shi damuwa don gaskiya banyi tunanin zai farfad'o ba tare da wani shashen na jikinsa ya samu matsala ba amma cikin ikon Allah ya farfad'o komai nashi yana aiki sai dai matsanancin ciwon kan da yake damunsa insha Allah shima zai daina in har za'abi kaidojin komai." Alhji Tijjani yace." Insha Allah Dr Yanzu ya jikin nasa."!? Dr yace." Alhmdullahi ya samu bacci yanzu ka kwantar da hankalin ka." Ajiyar zuciya Ya sauke yayi wa Dr godiya ya futa.... Kan Mamy din ya tsaya muryarsa babu sauki a cikinta yace." Maza Ku koma gida domin zaman Ku a gurin nan bashi da amfani. " Mamy ta d'ago jajayen idonta tana kallonsa cikin rawar baki tace." Ya jikin My..... Kafin ta karasa ya daka mata wata irin tsawa a harzuke Yace." Ba'a sani ba! Duk bake ce kika zama silar faruwar komai ba, zaki tambayi jikinsa yanzu da kin damu dashi ai baza kiyi masa abunda zai jawo masa hawan jini ba."! Hankali a tashe take kallon mijin nata yanzu yaron nata ne yake da hawan jini ko su da suke manya Allah bai Dora musu ba sai shi tasan hawan jini mugun ciwo ne dole tayi taka tsan-tsan..... Bala'i yake zuba mata sosai hade da cin mutumci Mamy tayi da ta sanin abunda tayi ita kuwa Hafiza Mamy ta kama suka futa da gurin tana share hawaye da tasan wannan tashin hankali zata zo ta tarar da bata zo gidan ba, Abunda take fada kenan cikin ranta, haka suka koma gida zuciyonsu duk babu dad'i lokacin Mus'ab ya Dade da yin bacci gurin me aikin Mamy Habiba. A furgice ta tashi tana zare ido cikin dakin! Duhu d'umdum kasancewar basa kwana da hasken wutar lantarki duk sun kashe kwaya kwayan gidan... Hannunta na kyarma ta lalubo k'aramar torchlight din da suke haskawa ta kuna tana kallon dakin jikinta sai rawa yake yi ga wata irin fad'uwar gaba da take ji, takure wa tayi guri guda wasu irin hawaye suka fara biyo kuncinta Munmunan mafarki tayi Wanda yayi mutukar gigita ta da bata tsoro wai Khalid ya mutu gashi kwance a makara mutane sun dauke shi zasu kaishi makabarta lokacin ne ita kuma ta futo daga gida tana kuka tana rirrike makarar tana fadin"Kar ku rabani dashi bamuyi aure ba bai mutu ba!! Don Allah Ku sauke shi Wallahi be mutu baaa."!!! Kuka take sosai tana rirrike makarar kawai sai taga Abbu ya ratso cikin jama'a yazo yana Jan hannunta ita kuma tana turjewa tare da rike makarar Abbu ya'ki cewa komai sai janta yake a lokacin ne tace"Abbu ka sake ni kar ka rabani da mijina."!!!!!! Muryar Abbu din taji yana fadin"Hanifa kinga mijin ki nan."! Tana juyowa taga Nasir yana yi mata murmushi Abbu ya kama hannunta ya hada da na Nasiru din yana fadin"Hanifa wannan ne mijin ki!!!! Lokacin ta farka a furgice!! Kanta ta sanya tsakanin k'afafunta gabanta na wani irin bugawa Yanzu idan Khalid ya mutu da gaske ya zata yi da rayuwar ta, zuciyarta tace sai ki hak'ura kiyi masa addu'a kawai girigaza kanta tayi kamar wata mahaukaya ta diro daga kan gadon waje ta futa ta tsaya tsakar gida tana zare ido k'arfe 3 na dare gari yayi tsitt! Hanyar futa ta nufa, tana tangadi! Nasir yaji motsi a soro da sauri ya kunna torchlight d'insa ya mike zaune yana fadin "Waye anan."!? Hanifa ta dawo hayyacin ta soron take bi da kallo tana tunanin ya a kayi tazo cikin gidan tayi nufin komawa da sauri.lokacin ne shi kuma Nasir ya futo yana hasketa da torchlight dinsa. Kallon juna sukayi gabansa ya fad'i ganin yanda idonta sukayi jazur duk sun wani juye bakinsa na rawa yace." Hanifa ina zakiji ne ? Me ya futo dake yanzu? Kafin tayi magana suka ji muryar Abbu yana fad'in "Nasiru menene ya faru." ? Hanifa ya gani tsaye a jikin kofar futa. Cike da mamaki yake kallonta. Nasir yace." Abbu babu komai kawai ina kwance naji motsi ina futowa naga tana kokarin bude kofa ta futa." Abbu ya kalle ta cikin nutsuwa baice komai ba yaja hannunta suka nufi cikin gidan ya juyo yana kallon Nasir da yayi kasake a tsaye yace"Kaje ka kwanta Nasiru da safe zamuyi magana." Nasiru ya shiga dakinsu yana mamaki abun. Ammi na tsaye a tsakar gida Abbu ya shigo da Hanifa kai tsaye dakin sa ya nufa da ita ita kuma sai zazzare ido takeyi kamar ma bata cikin hayyacinta. Abbu ya zauna da ita gefen kati Ammi ta zauna jikinta duk a sanyaye Kallonsa tayi tace"Abbu wai menene? Naji maganganu sama-sama."! Abbu ya kalli Hanifa ba tare da ya bawa Ammi amsarta ba yace. " Hanifa ina kike kokarin zuwa da daran nan."!? Kallonsa tayi wasu irin hawaye masu zafi suka zubo mata a fuska.Ammi ta daka mata wata irin tsawa tana fadin"Ba tambayar ki akayi ba ne."!? Abbu da jikinsa ya gama yin sanyi yace." Halima yi mata a hankali kar ki manta kuma dare ne Yanzu. " Shiru Ammi tayi gabanta na fad'uwa wato Hanifa futa zata yi to ina zata je? Dukan su basu da amsar sai a gurin ita Hanifa r Abbu yace."Hanifa ina zakije da dare."! Wannan karon muryarsa a kaurare take. Kuka ta fashe dashi tana fadin",Abbu mafarki nayi ya mutu!!!! Ammi da Abbu suka kalli juna cike da mamaki suka ce waye ya mutu? Kuka ta fashe dashi ta fad'a jikin Ammi tana wani irin kuka take fadin"Ammi nayi mafarki ya mutu za'aje a bunne shi!!! Ammi jikinta ya soma rawa ganin yarinyar ta tana wani Abu kamar zauntacciya tace"Wai wa kika gani ya mutu an fada miki mafarki gaskiya ne."!? Tana kuka tace"Ammi wannan da gaske ne wallahi ance min ya mutu.!" Abbu yace." Wanene ya mutu."? Cikin futar hayyaci tace"Abbu Khalid ne na ganshi cikin makara mutane sun dauke shi zasu kaishi su bin......... Bata 'karasa ba Ammi ta yarfa mata wani irin mari!! Wanda yasa ta kwallara 'kara! Da tasa gidan ya amsa su Nasiru suka futo a gigice! Bakin kofar dakin suka tsaya cikin tashin hankali.! *7/1/2020* _BintuUm@rAbb@le_ [1/21, 9:45 PM] BintaUmarAbbale: _MASHAHURI_ *_Mallakar: Binta Umar_* *_Ki biya ki karanta cikin kwanciyar hankali ke kuma da kika futar da book d'in na barki da Allah!_* *08089965176* *07084653262* *0542382124....Binta Umar Gt bank* *41* Ganin irin kukan da take ne yasa Nasir shiga cikin dadin yana kokarin d'ago ta Hanifa ganin yana kokarin ta'bata ne ta fuzge jikinta ta koma gefe guda tana kuka had'e da sharbe majina! Ammi ta cigaba da fad'a tana cewa"Wallahi duk wata futana taki zakiyi ta ki gama Hanifa baki da miji sai Nasiru shi wancan din da kika kwallafa rai akanshi dole ki hak'ura domin zuciya ta batayi na'am da ki aure shi ba idan da ma mutuwa yayi to da mun huta da wannan bakin ciki da kike so kin kunsa mana." Shuru dakin yayi sai sautin kukanta ne kurrum yake tashi Abbu yayi gyaran murya tare da fad'in "Halima duk Wannan maganar bata taso ba idan zakiyi magana ki dunga taunawa kafin ki fade ta, Nasan k'uruciya CE take damun ita Hanifar kuma ni magana a tsakani na da ita ta kare dole babu gudu babu ja da baya aure tsakanin ta da Nasiru indai ina raye a duniya sai anyi shi tunda na bata hakkinta a matsayin ta tace ta bani wuka da nama magana kuma ta wuce a gurina." Jin abunda Abbu din yake cewa ne yasa Hanifa ta kara fashewa da kuka tana burgima a kasa Hafiz ne ya shigo dakin a zuciya ya dagota tare da daga hannu zai mare ta Abbu ya rike hannun nasa yana girgiza masa kai, yana numfarfashi yace." Abbu baka ganin iskanci. Da take yi kamar hanifa ana gaya mata magana tana wani Abu kawai ka rabu dani na Zane mata jikinta tunda kokari take ta tona mana asiri a gari." Abbu yace." Hafiz k'yaleta duk wannan abunda take yi me wucewa ne watarana sai labari yawan dukan bashi da amfani. " Hafiz ya futa daga dakin ransa a b'ace, Nasiru kuwa duk jikinsa yayi sanyi sai yake jin kamar yace da abbu din shi ya hak'ura kawai saboda baya son tashin hankali da abunda zai taba zumuncin iyayansa. Haka suka yi ta Abu daya har asubah Hanifa bata daina iface-iface ba dayawa daga cikin makotansu sunji abunda yake faruwa gidan shaik din sai suke tunani. Ko wani abune ya faru to da yake babu wani zaman lafiya sosai a tsakaninsu yasa babu Wanda ya tambayi ba'asi.......sai k'arfe shida da rabi sannan Hanifa tayi sallah idanunta duk sun kumbura sunyi jazur ita burunta kawai taje gidansu Abbakar ta tambayeshi lafiyar Khalid gashi Abbu yace kar a kara barinta ta futa makaranta ma ya soke ta daga yau ta zauna a gida har lokacin d'aurin auran su da Nasiru Ammi taji dadin wannan hukunci da ya yanke. **** Garau ya tashi Dr na tsaye a kanshi yana duba jikinsa tare da tambayar yaya yake jin yanayin jikin nasa, Khalid yace. "Baya jin wani Abu sai dai rashin k'arfin jiki." Dr ya cigaba da bashi shawarwari da yanda zai inganta lafiyar sa kana yace." Duk wani Abu da ranshi da gangar jikinsa yake so to yayi kokarin biya wa kanshi bukata wannan shine zai sa ya samu ingantacciya lafiya kuma ya rage saka damuwa cikin zuciyarsa. Khalid duk ya dauki shawarar Dr domin ya Riga ya gama yankewa kansa hukunci mutukar Shaik bai bashi auran Hanifa ba sai ya haddasa masa b'acin rai kamar yanda ya haddasa masa zaiyi amfani da irin son da Hanifar take masa ya rama abunda yayi masa, tunda dai shi baya jin rarrashi da ban baki. Wannan shine abunda ya kudurta cikin zuciyarsa,ko da Dady nashi ya shigo yaga jikin NASA yayi sauki sai ya kwantar da hankalinsa ya zauna kusa dashi yana rarrashin sa da "Ya kamata ka rabu da yarinyar nan tunda ubanta baya do duk ga 'yan mata nan yayan manyan masu kudi da yayan sarauta duk wacce ka nuna kana so da gudu ubanta zai amunce Myson kana wahalar da kanka gurin yar gidan mutsiyacin mutumin da bai gaji arziki ba inda ya gaji arziki bazai yi wannan jahilcin ba arziki na binshi yana gudu saboda bashi da rabo." Ya karasa maganar cikin tsananin jin haushin Abbu. Khalid ya sauke ajiyar zuciya cikin yanayin maganar sa yace." Dad ka Bari kawai magana ta wuce a gurina tunda dai mutumin bayajin Allah da Annabi ni na San abunda zanyi akan al'amarin amma maganar cewa in rabu da yarinyar shi Sam bata taso ba Dad kamar yanda suka bani wahala nima sai na basu ita tunda dai ya'ki yarda ayi abun cikin dad'i da kwamciyar hankali to zai fuskanci b'acin rai."! Alhaji Tijjani ya daga kafad'a sama alamun maganganun da Khalid din yayi basu dame shi ba yace." Duk abunda kake ganin shine mafuta a gareka ka aiwatar dashi ina goyon banyanka." Khalid sakin jiki yayi sukayi hira da dad din NASA kafin dr ya shigo ya sallemsu, suka nufi gida. Ammi kuwa futa tayi daga sabgar Hanifa ta cigaba da aikace-aikacen ta babu abunda ya dameta da Hanifar da take jin kamar ta hadiyi zuciya ta mutu ta huta gashi har yanzu gabanta bai daina fad'uwa ba, k'arfe goma shabiyu Abbu ya futo tsaf dashi ya tsaya kusa da Ammi dake zaune kan k'aramar kujera tana gyara alaiyahu yace."Halima zanje dorayi gurin Malam labaran domin ina so cikin satin nan mu tafi gombe jikina Yayi sanyi da wannan al'amari ina ganin gwara kawai muje yan uwa su shaida a d'aura auran yaran nan duk tsiya nasan idan taga ta zama matar wani zata hak'ura da Wannan yaron." Ammi tace"Abbu haka yayi nima hankalina yafi kwanciya da hakan muyi nesa da garin gaba daya idan ankwana biyu sai mu dawo." Gyada kai Abbu yayi yace." Halima mawuyacin abune zai dawo damu garin kano idan muka koma mahaifarmu shikkenan kuma." Ammi tayi hamdala cikin zuciyarta dama Kwata-kwata bata kaunar zaman garin kano saboda yanda aka takura musu ko ina babu sakewa. Abbu yayi mata sallama ya futa ta rakashi da addi'ar dawowa lafiya Duk Wannan maganar da suke yi a kunnen Hanifa gwiwar ta tayo sanyi k'alau Jin abunda Abbu ya fada, ta fara share hawaye tana tunanin mafuta ta koma daki ta rakube jikin gado Motsin Ammi taji tana jawo ruwa a rijiya da sauri ta mike tana le'kawa taga ta shiga band'aki hijab dinta ta jawo dake jikin kyaure a rataye ta fuce daga gidan da sauri! Kai tsaye gidansu Asalamiyya ta nufa gabanta na cigaba da fad'uwa addu'a take Allah yasa ta tadda Abbakar a gidan aikuwa a kofar gida ta ganshi a zaune shin kadai yana latsa waya. Mik'ewa yayi suka shiga soron gidan yana mamakin ganinta a hargitse yace." Hany meye naga duk kin hargitse idanunki sunyi jawur." Cikin kuka ta fada masa irin mafarkin da tayi sannan ta fada masa maganar da taji Abbu na fadawa Ammi yanzu. Da sauri ya Ciro wayarsa ya fara kiran Khalid din bugu daya tayi ya dauka Hanifa taji muryarsa radau ajiyar zuciya ta sauke ! Abbakar yace." Guy gani ga hany fa tana kuka wai tayi mafarki ka mutu." Mik'ewa yayi zaune sosai da wayar a hannunsa yace." Pls bani ita." Abbakar ya mik'a mata wayar batasan sanda ta karba ba da sauri ta kara a kunnen ta cikin kyarmar baki tace." Ashe baka mutu ba."!? Wani killer smile yayi ya shafa sumar kansa cikin wani irin murya yace." Na kusa mutuwa baby sonki ya sanya ni a gaba wai ya za'ayi ne uhum."!!!! Muryarsa tayi bala'in kashe mata jiki taji k'afafunta sun kasa daukarta jingina tayi jikin bango tana lumshe ido tace"Wallahi nima bansan ya za'ayi ba gashi Abbu ya matsa min sosai yace ma zamu koma gombe ne gaba daya kuma ma yace aurena da Ya Nasiru dole sai anyi." Wayar ya rike sosai a hannunsa ya gyara zama yana mamakin Ya Shaik wato guduwa zaiyi daga garin ma saboda shi lallai shima ashirye yake." Ma'ke muryarsa yayi dama gata da sanyi kamar ta mata yace." Ok idan Abbu ya gudu dake ni kuma zaki gudu da zuciya ta nasan lokacina yazo karshen rayuwata yazo baby zuciyata had'e take da taki kar ki bari a rabamu nasan kema kina sona kinji." Cikin shagwaba ya karasa maganar. Wannan salon da yayi amfani dashi yayi mutukar tasiri a zuciyarta ta inda ta manta ma ita da wanene a gurin ta lumshe idonta tana k'ara kankame wayar a hannunta ido a rufe tace"to me kake so inyi nima nasan Kai nake so amma Abbu ya hana ni kai wai dole sai na auri zabin sa."! Fuska ya bata kamar tana kallonshi ya canja murya tayi kalar tausayi yace." Abunda zakiyi kawai kije kije masa ni kike so hakan zakiyi na gane kina sona da gaske." Girgiza kanta tayi a hankali tace"Bazan iya ba ni dai.'"! Khalid ya sha kunu tare da mik'ewa tsaye ya Dan daga muryarsa da b'acin rai yace." To tunda baza kiyi min yanda nake so ba ki bawa Abbakar wayar ki gwamace sonki ya kashe ni ko gwara ma na mutu akan in zauna in ganki tare da wani."!!!! Shiru tayi gabanta na fad'uwa.! A Dan fusace yace." Ki bawa Abbakar wayar zamu yi magana."! Mik'awa Abbakar wayar tayi jikinta duk yayi sanyi. Abbakar ya futa waje suna magana dashi kusan minti biyar ya dawo yana kallonta a hankali yace." Khalid yace wai kizo muje gurinshi yana so ya ganki ." girgiza kanta tayi yace." Saboda me."? A hankali tace"Abbakar ina jin tsoro ne wallahi." Tsaki Abbakar yaja yace." Kiyi ta tsoro ki cuci kanki guy nan yana bala'in sonki ke kin samu kina wasa shin kin San iya adadin yan matan da suke sonshi kuwa? Kin San kud'in da mahaifinsa yake dashi a garin nan? Wallahi Hany kiyi wa kanki fada kar ki bari Abbu ya cuce ki kisan yanda zakiyi ki kubutar da kanki." Wad'annan hudubobin na Abbakar sunyi bala'in tasiri a zuciyar Hanifa take tayi na'am dasu taji zuciyarta ta kekashe kallonsa tayi Tare da fad'in"Abbakar muje in ganshi ko naji dad'i cikin zuciyata." Abbakar ya nufi kofar futa tabi bayansa. Titi suka futa suna tsaye suna jiran abun hawa Abbu ya sauka daga a dai-dai ta can ya hango Hanifa suna kokarin shiga a dai-dai ta sahu ita da Abbakar sosai Abu ya bashi mamaki ganinta babu ni'kab hijab din jikinta ma babu girma sosai yake tunanin ya akayi ta futo daga gida kuma INA zasu je ita da Abbakar din.!? Bashi da Wanda zai bashi amsa haka yana ji yana gani a dai-dai tahu ta wuce dasu da gudu ko da wasa Hanifa bata ganshi ba saboda yana can daya tsallaken dama kuma duk hankalinta da nutsuwarta ba a jikinta suke ba. Hanifa taga sun tsaya a kofar wani tankamamen gida Abbakar ya futo da kudi ya bawa me Babur din yayi tafiyarsa ita kuwa Hanifa unguwar take bi da kallo gidajen manya manya amma duk girman gadajan basu kai Wanda taga Abbakar ya nufa ba, jiki a sanyaye take bin bayansa Hankalinta bai kara tashi ba sai suka shiga ciki taga yanda securities suke binsu da kallo sai ta tsorace! Sosai ta kankame hannunta cikin hijab dinta kamar munafuka haka tayi kasa da kanta, Abbakar ya gaisa dasu sama-sama suka wuce ciki....... Kai tsaye part din Khalid suka nufa Yana tsaye bakin window din dakinshi ya hango zuwansu kallonta yake yi kamar tsowon maye yayin da sha'awarta take kara ninkuwa cikin zuciyarsa, baya so ya aikata wani Abu na batanci a kanta kuma baya so ya aikata abunda Allah ya haramanta amma Yana ganin kome yayi mata a halin yanzu ubanta me ya jawo tunda dai ya'ki yarda ya bashi auranta....... Dake akwai 'yar tazara daga gurin da ya hango su sai ya bude kofa ya futo ya tsaya hade da soka hannunsa cikin aljuhu yana jiran 'karasowar su, Har yanzu idonsa ns tsaye a kanta, jikinta ya bata ana kallonta a tsarge ta dago kanta aikuwa suka hada ido dashi yana wani marairaice fuska, Hanifa cigaba da tafiya tayi kuma bata dauke idonta daga kansa ba tana jin wani irin fleengs a tartare da ita gaskiya Allah ya sanya mata son guy kamar ta mutu haka take ji tsigar jikinta har ta fara mik'ewa, suna karasawa Abbakar ya bashi hannu suka tafa kamar yanda suka saba ya kalli Hanifa da ta jingina da bango kanta a 'kasa yace."beb kinzo."? A langwabe ta daga masa kai! Yace."Good yanzu na kara tabbatar da cewar kina so ki shigo mu tsara yanda zamu yi ko."!? A kasalance yake maganar, Hanifa ta Dan kalleshi tana so tayi magana amma yanayin da ta ganshi ya sanya taji tana Neman ta rasa nutsuwarta yana sanye ne da karimin wando short nickar da wata d'amammiyar vest abunda da Wanda yake da jiki a murd'e ko ina na jikinsa a cike yake babu wata rama lafiyayyar fatarshi sai shek'i takeyi alamun ana gyara ta sa sabulai gami da mayamayai masu tsada,, k'irjinsa ta Dan kalla taji wani irin Abu a jikinta da sauri tayi kasa da kanta, shi kuma ya matso jikinta sosai masifaffan k'amshin sa yayi mata sallama, hannunta ya rike cikinsa yana Dan murzawa kadan ya kalli Abbakar yana Dan ya mutsa fuska domin har ya fara kwancewa domin dumin hannunta ya soma gigita shi yace."Guy kaje kawai ni zan maido da Queen gida Ok."! Abbakar ya bude bakinsa cike da mamaki yake son yin magana Khalidn ya harare shi kadan yaja hannunta suka shige ciki Abbakar ya bishi da kallo yana sakin dariya ya San halin Guy tunda yaga ya rikice yasan bazai bari yarinyar ba sai yadan 'Dana gyda kansa yayi kawai ya bar gurin. Suna shiga cikin parlor sosai Hanifa taji wani kamshi da sanyi dad'i sun ziyarci hancin ta wata irin ajiyar zuciya ta sauke tana kokarin ta kwace hannunta daga nashi ya rike tamau! Kokarin juyo fuskarta yake su kalli juna tana kauda kanta, a hankali yace." Beb ki juyo ki kalli maraya ki kalleni da wad'annan kyawawan idon naki ko na samu zuciyata ta daina zafin da take yi kinji ko."! A kasalance ta kalleshi tana marmar da gashin idonta hakan da tayi ya burge shi sosai ya sanya hannunsa a saman idonta yana wasa da gurin, lumshe idonta tayi tana jin wani irin shauki gami da kaunar sa na kara nunkuwa a zuciyarta jikinta ya hau bi da kallo duk da cikin hijan take bai hana bayyanuwar manya-manyan Brest dinta ba Wanda suke mutukar razana shi da bashi tsoro yau dai yayi alk'awarin sai ya gansu a fili.... Hanifa na can da ido a rufe taji ya kamo 'kungunya ya Dora hannunsa kan bom-bom dinta ya dDan dukesa kad'an, tayi saurin bude idonta tana kallonsa, girarsa guda ya daga mata yana Dan sakin murmushi Wanda ya tafi da imaninta...... Ta bishi da kallo har suka isa doguwar kujera 3sitar ya zaunar da ita cinyarsa bayan ya bude kafafunsa ta zauna sosai a jikinsa kallon juna suke yi kamar babu gobe Hanifa duk ta wani susuce sai faman motsa idonda take tana tutturo baki gaba tasan abunda sukeyi bai dace ba amma sonshi da take da kuma yanda gangar jikinta take amsar sakonshi yasa ta kasa hanashi Abunda yake mata....... Cikin wani salo ya dora hannunsa kan le'bunanta da yake mutukar so ya Dan lumshe idonsa a hankali yace." beb ina son wannan ya za'ayi uhum."!! Hannunta me dumi tasa tana kokarin cire hannunsa gefe guda tana jin wani irin Abu na zungurinta yana kuma motsi tsil-tsil!!!! Ganin tana son sauka ne yasa cikin dabara ya zura hannunsa cikin hijab din yana kokarin zare shi hannunsa ta rike tana girgiza masa kanta, shima kansa yake girgizawa cikin langwabe Kai yace." beb pls ki bari in gani ko yaya ne kinji ko."! Kauda kanta tayi gabanta na fad'uwa, Khalid ya saki murmushi cikin zuciyarsa ya lura yarinyar ta kamu sosai hijab din ya zare ya jefar dashi kasa ido ya tsurawa k'irjina yana lumshe ido jikinsa har ya soma rawa duk da cikin rigar atamfa suke bai hanashi ganin yanda shatin niples dinta futo ba abunda ya k'ara gigita shi shi kenan! Ya rike kunguta da kyau! Yana me Dora kansa kan k'irjinta cikin dabura ya zura hannunsa yana kokarin zuge zif din rigarta kuma bai fasa gogo mata fuskarsa ba a gurin...... Idonta a lumshe take kokarin cire kansa tana kokarin sauka ya rike ta tamau! Har sai da yayi nasarar zuge mata zif din da sauri ya cire rigar yayi jifa da ita, Hanifa ta sanya hannu biyu ta rufe k'irjinta Wanda ko rabinsu bata rufe ba saboda girimansa hakan da tayi ya tayar masa da hankali yaji kamar hannuwansa ne a kai jiki na kyarma ya fuzge hannunta ya Dora nasa a kai, kan nono ya kama duka hannun NASA yana murzasu yana sakin nishi duk ya rikitata da salonsa, kuka take tana kokarin cire kansa da manna a gurin yana lashewa!! Ganin ya'ki ya daina ne yasa ta fara du kansa tana kuka take fadin"Ka Bari nace nifa banzo gurin ka don mu sa'bi Allah ba, babu kyau abunda kake min haramun ne." Sam bai san tana yi ba domin burkicewa yayo sosai ya kwantar da ita kan doguwar kujerar ya haye kanta sai lasar jikinta yake sai kace maye! *10/1/2020* _BintuUm@rAbb@le_ [1/21, 9:45 PM] BintaUmarAbbale: _MASHAHURI_ *_Mallakar: Binta Umar_* *_Ki biya ki karanta cikin kwanciyar hankali ke kuma da kika futar da book d'in na barki da Allah!_* *08089965176* *07084653262* *0542382124....Binta Umar Gt bank* *34* Yace." Myson ka kwantar da hankalinka yarinya ko yar waye ni zan shige maka gaba ka aureta raina ya 'baci da jin abunda ka fada min yanzu cewar yarinyar ma d'iyar talaka ce har za'a zauna ana wasu surutai a kanta yanzu don dare yayi amma insha Allah gobe da kaina zanje har gidansu yarinyar kai zauna cikin shiri zamuje tare da kai har gidan ka kwantar da hankalin ka." Khalid yace." Allah ya kaimu dad nifa a matse nake sosai Wallahi banaso abun ya dauki dogon lokaci." Mamy ta kalleshi cikin nutsuwa tace"Myson idan mutuminan ya'ki amin cewa ka hak'ura kawai kazo gurin Nasrin yarinyar tana da hankali da nutsuwa nasan kuma duk zata dauke maka laluran ka." Khalid shiru yayi mata saboda yasan zai iya fada mata abunda ranta zai b'aci shine yasa yayi mata shuru kawai shi kuwa Alhaji Tijjani sai fada yake yi ranar Khalid Hanifa Abbu Ammi babu Wanda yayi bacci me dad'i Khalid kasa tafiya yayi part d'insa nan parlor yayi kwanciyar sa har garin Allah ya waye ya tashi ya koma part d'insa domin shiryawa kwana yayi yana mafarkin Hanifa sai da yayi wankan tsarki saboda bai yadda da kanshi ba ya futo ya kimtsa jikinsa cikin wata lafiyayyar shadda geznar irin ta maza anyi masa dinki irin na zamani dama shi ba ma'abocin sanya hula bane sumar shi ya gyara sosai ya gyara sajanshi ya kara kwanciya lif a kyakyawar fuskarshi turaran shi ya dauka ya fesa a jikinsa a take dakin ya dumame da masifaffan kamshi mai dad'i takalmi me gidan yatsa ya sanya a nutse ya futa namiji tsayyaye ingarma jarumi ta ko wane fanni so yana nema ya sanya ya zama malalaci yanzu yanayin tafiyar shi ma ta sauya komai na duniya yayi masa zafi Kwata-kwata baya son damuwa yanzu tunanin yanda zai samu ya mallaki Hanifa kawai yakeyi. Cikin rashin k'warin jiki ya isa part din iyayen sa Alhaji Tijjani da Mamy suna zaune gurin cin abunci ya shiga da sallama a bakinsa kai tsaye daining din ya nufa yaja kujera ya zauna yana ya mutsa fuska Hannu ya mik'awa dad din NASA sukayi musabaha sannan ya shagwabe fuska yana kallon Mamyn sa yace." Mamy jiya da kyar nayi bacci duk kuka barni a parlor ni kad'ai. " mamy ta bude bakinta cike da mamaki tace"Myson kana nufin a parlor ka kwana."!? Gyda kansa yayi kamar wani maraya yace." E Mamy bana so inje part dina ni kadai abun zai 'kara tsanani." Mamy tace"Wannan yarinya ko wacece bata kyauta min ba duk tana nema ta mayar min da yaro lusari myson nifa kwata-kwata jikina na baki kamar babu alkairi a tarayyar ku da ita shiyasa nakeyi maka maganar Nasrin itace dai-dai da kai." 'Bata fuskarsa yayi yace."Mamy jiya ma fa haka kikayi min nayi miki shiru Mamy kika 'karayi min maganar 'yar lukutar yarinyar nan kuka zanyi miki yasin." Cikin shagwaba yake maganar mamy da Alhji Tijjani suka saka dariya yace." Allah dad ita Mamy ta kasa ganewa har yanzu." Mamy na dariya tace." Ta ina zan gane yarinya na nema ta mai dakai sususu zanso ingata da idona." Murmushi yayi yace." Zan kawo miki ita gida insha Allah. Ta'be bakinta tayi tace"To Allah ya kaimu lokacin ina fatan kar a samu wata matsala idan kunje gidan nasu. " Mamy babu matsalar da za'a samu insha Allah zan amunce mamy nifa yarinyar tana sona mahaifinta ne matsala kuma dama mun ta'ba samun sa'bani dashi shekaru biyar da suka wuce." Mamy tace"Ai kaji ko lokacin kana kan k'uruciya duk da ban San abunda ya hadaku ba nasan Kaine baka da gaskiya Yanzu tunda kana son abun shi sai ka durkusa masa." Dad ya kalleta a yatsune yace." Yarona ne zaije gurin talaka yana durkusa masa lallai baki da hankali indai ina raye yarona sai ya auri yarinyar komai kika ga anyi shi da kai to kana da kudi." Girgiza kai Mamy tayi tace"Allah ya bada nasara ai babu abunda nace me zafi anan ina fatan alkairi." Dad din ya tashi daga gurin yana mita hade da fadin "Indai kudi suna magani a duniya to zamu siyi komai su yanke kud'in sa dakin yar tasu zan biya ko nawane."! Mamy ta bishi da kallo yana kokarin hawa sama sai masifa take yi, Sam bata kaunar d'abi'ar mijinta na girman kai gami da homa mutum ne shi mai nuna shi wanine a duniya gashi bashi da kyauta ko kadan duk uban dukiyarsa baya sadaka baya bada zakka baya hubusi duk abunda Allah yace da me dukiya yayi Sam Alhji Tijjani bayayi Cikin ikon Allah kullum dukiyar tasa kara habaka takeyi Allah kenan. _Ni kuma cewa nayi akwai ranar da Allah zai futar da zakkar shi a cikin dukiyar tasa, ubangji ya zuba masa idone kawai yana kallonsa_ Cikin wata lafiyayyar shadda wagambari Riga da malin-malin anyi masa wani irin aiki gaban babbar rigar da bayanta kana ganin shi kasan Alhji ne kudi kuma sun zauna ko ta ina ya murza hula damga 'yar asali ya futo yana baza 'kamshin turaransa Khalid ya mike tare da bin bayansa Mamy kan iya kacinta kofar parlor sai da taga sun shiga mota, sannan ta koma ciki tana addu'ar Allah yasa akwai alkairi a cikin wannan al'amarin *GIDAN ABBU* Bayan sunyi Karin kumallo kamar yanda suka saba Hanifa ta mi'ke zata shige daki dama babu makaranta tunda Alhamis ce Abbu yace." Hanifa dawo ki zauna ina so nayi magana dake." Ji tayi gabanta ya fad'i ta juyo a hankali ta dawo ta zauna inda ta tashi. Abbu yayi gyaran murya a nutse yace." Hanifa tunda Allah yasa na haife ki nake da buri a kanki Ku biyu kacal Allah ya mallaka min ina alfahari da haka kuma kullum cikin godewa ubangji nake bisa baiwar da yayi min Hanifa INA so ki rike mutumcin ki Wanda Allah yayi miki a matsayin ki na ya mace mai daraja ki kama kanki daga nan har zuwa lokacin da zan auran dake ina fatan kin fahimci kudurina a kanki da Yayanki Nasiru ki? Ina so in hadaku aure dashi idan Allah ya nufa, jiya da daddare wani yaro yazo min da magana a kanki yana cewar yana sonki da aure to tun wuri na sallameshi na fada masa cewar nayi miki miji yayi hakuri, nasan yaron sosai yana da rawar kai ko da wasa ban amunce ki shiga huruminsa ba dole watarana zaku had'u a hanya babu ke babu shi idan yayi miki wata magana kice babanki yayi miki miji kinji ko." Hanifa da tunda Abbu yake maganar take jin wani irin a jikinta tace."To Abbu insha Allah zanyi maka biyyaya kamar yanda kake so." Muryarta na rawa ta 'karashe maganar Ammi dai kallonta takeyi tana tausaya mata tunda ba tun yau ba tasan bata son Nasiru tunda tana fada da bakinta..... Yace." jeki dauko a'kurani muyi karatu." Mik'ewa tayi tana jin wani irin jiri na kwasarta dakin Ammi ta shiga ta dauko alk'urani ta futo kenan suka ji sallama ana sauke kaya a cikin gidan, Abbu ya mike a nutse yana amsa sallamar ya futa kawai sai yaga ana shigowa da buhuhunan abunci da k'aton k'aton din taliya da macaroni gami da sauran kayan masarufi.! Cike da mamaki! Abbu yace." Wannan kayan fa daga ina ? Ku daina saukewa ba gidan nan bane." Wani matashi yace." Ya shaik kayi shiru kawai kwananan zaka daina sanya yadikan toyobo domin 'yar ka ta jawo maka arziki har gida hahahahaha dama wannan yarinyar taka dakake 'boyewa Ashe kasan kadara ce shiyasa kake kaf-kaf da ita. "! Suna shakiyanci suna sauke kaya har sai da tsakar gidan ya kusa ciki sannan daya daga cikinsu yace." Ya shaik *Alhji Tijjani Canji* yana jiran ka a waje."! Yana gama maganar shi ya futa daga gidan da sauri! Kafin Abbu yace wani Abu Nasir da Hafiz sun shigo cikin gidan suka dinga bin kayan abincin dake jibge da kallo Nasir jikinsa yayi sanyi domin ya Riga ya fahimci komai tunda yaga Alhaji Tijjani da yaron sa a tsaye a waje, Hafiz yace." Abbu wannan kayan fa? Kuma me ya kawo wancan mutumin kofar gidanan."? Daga masa hannu Yayi kawai ba tare da yace komai ba ya futa daga gidan, shi kuwa Nasir jikinsa a sanyaye ya bude dakinsu ya shiga zubewa yayi cikin kujera yana jin wani irin zafi a zuciyarsa addu'a yakeyi Allah yasa kada kudi su rinjayi zuciyar Abbu. Alhaji Tijjani sai bin unguwar da wani irin kallo yake yana ya mutsa fuskarsa idan banda dalili babu abunda zaisa ya shigo cikin unguwar domin duk mutanan cikinta ba tsaransa bane don dai babu yadda za'ayi ya hana danshi abunda yake so shiyasa kawai yake biye masa amma shi a ra'ayinsa yafi so Khalid ya auri 'yar gidan shuwagabanin kasa amma ta 'bige da 'yar talaka. Abbu ya futo cikin kamala ya mik'a masa hannu sukayi musabaha da Juna ya mik'awa Khalid ma suka gaisa, Alhaji Tijjani na ya mutsa fuska yace." Ina fatan Arrama yaga sa'kona."? Abbu yace." Wane irin sa'ko Alhaji."? Gyaran murya Alhaji Tijjani yayi yace."Wannan iyayen kayan abunci da masarufi da na jibge maka a cikin gidan ka sun isa ka gane komai." Abbu yayi murmushi tare da gyara tsayuwarsa yace." Maddalah nagode Alhji Allah y kara suttura da rufin asiri ni bazan ce maka ba mubakaci bane Hak'ika ina bukata to amma kullum Allah ne da ita Ubangiji baya hanani abunda zan kawo gida mu sanya a bakin mu, wannan kayan abunci da kasa aka jibge min sunyi min yawa Abunda yafi kamata kayi shine ka kaisu gidajan marayu sannan ka nemi mabukata sosai sai ka sadakar musu ni Allah yayi mun rufin asiri nafi k'arfin cikina." Wani irin murmushi Alhji Tijjani yayi yace." Arrama wannan kauli da ba'adin duk kai kasan su ni dai kayan abunci kai nabawa saboda ina Neman biyan bukata a gurinka kana iya zuwa kaje ka SADAUKAR dasu babu damuwa, babban abunda ya kawo ni gurina shine yarona." Yafad'a yana nuna Khalid dake tsaye kanshi a kasa ya zura hannunsa cikin aljuhu Dad ya cigaba da cewa"Yarona yaga yarinyar ka yana sonta da aure jiya ya fadamin yazo gurin ka kan maganar kace wai kayi wa 'yarka miji Hak'ika banji dadin wannan maganar ba Arrama kai abun alfarinka ne yarka ta auri yarona kuma ta bangaranka abun alfahari ka ne ka hada zuria dani, to shine nace ni Bari in taso 'kafa da 'kafa in same ka kan maganar ina so idan da hali maganar da ka fada kan yarka ka warware ta inaso ka mallakawa yarona 'yarka ko nawa kake bukata ni zan baka kafadi nawane sadakin yarka tunda daga kan million daya zuwa millions goma zamu biya."!! Maganganun Alhaji Tijjani sunyi mutukar yiwa Abbu zafi a zuciyarsa shi mutum ne mai kawaici da danne b'acin rai akan Dade anayi masa Abu a rayuwa yana kauda kansa amma yau yanda yake jin ciwo game da maganar banza da Alhaji Tijjani yazo masa da ita yasa ya bude bakinsa ya fara magana a kausashe! "Alhaji duk naji maganar ka, kamar yanda na masa cewar nayiwa Hanifa miji hakane babu fashi kudi ko mulki ko sarauta basu isa su kani na kwance alk'awarin da na dauka ba, bana bukatar kudi nafi bukatar kwamciyar hankali yarinya ta Hanifa ba siyar da ita zanyi ba idan ma zan siyar da ita kai baka da kud'in da zaka iya siyan ta, naira dubu biyar kacal nake bu'kata a matsayin sadakin ta kuma bada b'angaran ku ba, saboda haka bana bukatar komai naka Alhaji wannan kayan abunci dake zube min bana bukatar su ni Riga nayiwa Hanifa miji Yayi hakuri ya nemi wata yarinyar." A hasale! Alhji yace." Karya kake kace baka bukatar wani Abu a gurina dube ka fa? Dubi gidan ka dubi sutturar dake jikinka."? Yafad'a yana ta'ba yadin toyobo din da yake jikin Abbu cikin izgili ya cigaba da cewa "Dama Ku 'yan Izalah baku da mutumci bakwa kaunar duk wani mai arziki a cikin duniyar nan daga zarar anyi magana sai ku fara fadin" Allah da Annabi har ni zaka fadawa magana idan banda yarona ya nace kan yarka mai gadin gidana baka isa na dauke k....."Dad."! Khalid ya katse mahaifin nasa daga hayaniyar da yake. Abbu kuwa shuru yayi yana mamakin k'arfin hali irin na mutumin yazo kofar gidan shi ya dinga kokarin wulakanta shi gashi har an fara taruwa a gurin....... Muryarsa na d'an rawa yace." Dad nayi nufin raya sunna da 'yarshi yace bai yarda ba a rayuwata ban ta'ba tunanin zan zo gurin wannan mutumin Neman alfarma amma saboda yanda Allah ya jarrabe ni da tsananin kaunar yarshi Nazo na kaskantar da kaina gurin shi duk da haka ya'ki ya karb'i maganar da muhimanci yarinyar ka ita ta koya min yanda zan sota.' Yafad'a yana kallon abbu ya cigaba da cewa"Ya shaik Yarka Hanifa ni take so duk wani Wanda zaka aurata mata a yanzu zata zauna dashi ne kawai domin tayi maka biyayya ina me baka sha'awa ka aura min ita domin samun nutsuwar ka da kwamciyar hankalin yarka. "! Alhaji Tijjani ya buge babbar rigarsa ya bi bayan Khalid da tunda ya kare maganar shi ya bar gurin cikin tsananin b'acin rai da damuwa.! Jama'ar da suka taru a gurin suka yi wa Abbu caaaaaa! Aka masu zagin sa nayi masu fadin yw cuci kansa nayi wasu tsantsar wautarsa suke gani cewar arziki yazo masa yana guduwa dayawa daga cikinsu suna fadin inama yarsu ce da tuni sun bada kai bori ya hau, hayaniyar da tayi yawa yace yasa Nasir da Hafiz suka futo daga cikin gida suka shigar da Abbu suna tambayar sa abunda ya faru." *1/1/2020* _BintuUm@rAbb@le_ [1/21, 9:45 PM] BintaUmarAbbale: _MASHAHURI_ *_Mallakar: Binta Umar_* *_Ki biya ki karanta cikin kwanciyar hankali ke kuma da kika futar da book d'in na barki da Allah!_* *08089965176* *07084653262* *0542382124....Binta Umar Gt bank* *43* Sai da ta tabbatar sun futa daga cikin gidan sannan ta mike zaune tana gyara hijab dinta suka hada ido dashi ya mirror girarsa guda ya daga mata da murmushi a fuskarsa yace." Matsoraciya kawai." Turo baki tayi tana dan hararasa yana kallonta ta mirror din yace." Me nayi miki kike hararata."!? Shiru tayi masa tana kauda kanta, ya saki yar dariya tare da fadin"Idan baki fadamin ba zan tsayar da motar ne in hukunta ki yanzu." A hankali tace" me kake so nace maka to."Ajiyar zuciya ya sauke yana. Lumshe idonsa yana bala'in son muryarta kamar yanda take son tashi...... Wani k'aton supar market ya shiga da motar ta kalleshi a tsorace tace"Me zamu yi anan gurin kum."!? A hankali yace." Ki futo mu shiga ki duba abunda kike so." Kafadarta ta make tana fadin" babu wani Abu da nake so ni dai don Allah mu wuce gida." Bude motar yayi yana fadin"Baki isa ba tunda muka shigo to sai kinfuto Wallahi " kallonsa take yans rufe mota ya runkufo da kansa tare da fadin"Ki futo Yanzu ko in ciccibe ki." Jikinta babu kwari ta futo a hankali tana kalle- kalle a gurin, yayi gaba tana binshi a baya hadaddun yan mata da samari ne gurin suna duba kaya yana shigowa kallo ya koma kansa 'yan mata sukayi caaaa a kansa Wai don Allah ya bari suyi hoto babu yanda ya iya haka ya tsaya suna ta salpie tare Hanifa na gefe guda tana kallonsu zuciyarta sai zafi take mata ganin wani irin yahudanci da yake sai rungume yan matan yake da sunan hoto su kuma sai gantsaro k'irji suke suna gogo masa a jiki sai taga babu wani damuwa da yayi murmushi yake yana biye musu kishi kamar ya kashe ta haka sukayi tayi samarin ma suka dunga dakaur shi a hoto da wayoyinsu gajiya tayi ta kama hanya zata futa, yayi saurin futowa daga tsakiyar su hannunta ya kamo suka koma ciki, duka suka bisu da kallo domin Sam basu tsammanin tare yake da yarinyar ba tunda shi kadai ya shigo gurin sai dai yana shigowa itama ta shigo mamaki suke shi kuma me ya hadashi da Wannan mai hijab din yana wayayyen mutum kuma sananne a duniya. Hannunta na cikin nashi suke zaga cikin kantin ta kasa daukar komai sai shine yake jidar mata kaya musamman rurarika da kayan kwalliya na mata sosai yake hada mata kaya ta kalleshi a fakaice tana mamakin yanda ya cika kwando da kaya ita ba mahaukaci ya bace da zata shiga da kayan nan cikin gidansu to tace dasu Ammi waye ya siya mata? Ita kadai take Wannan zantukan cikin zuciyarta har suka karasa gurin biyan kudi aka juye kayan cikin manya-manyan ledoji uku Khalid ya biya kud'in suka futa daga gurin.Hanifa kan ganin gari ya soma duhu yasa hankalinta ya tashi ta fara tunanin abunda zata fada a gida suna shiga mota ya lura da yanda take marmar da ido duk damuwa a tare da ita, Abu biyu ne ya hade mata kishi da damuwa domin idan ta tuno da yanda ya dinga rungumar yan mata da sunan hoto sai taji ta tsane shi ko kallon sa bata so tayi, yana driving yace." Beb naga duk kin wani koma shiru meye wai."! A marairaice tace"Gida nake Jin tsoro Wallahi." Tab'e bakinsa yayi yace." Budurwa kamar ki a dinga sanya miki ido ya kamata fa ki kwaci yan cinki domin ni bantaba ganin inda akayi wannan takurar ba sai a gurin Shaik kullum cikin takura da tsanani." Ya k'arashe maganar yana Jan tsaki k'asa-k'asa, taji ciwon tsakin da yayi dannewa tayi tace"Laifin kane duka ai daga yau bazan Kara zuwa inda kake ba." Murmushi yayi yana shafa sumar sa yace." Ranar da zakizo Ba zakiyi shawara da kowa ba 'yan mata." Hararsa tayi ta dauke kanta tana kallo ya karya kwana ya shiga da motar layinsu yara da matasa suka tasu yuuuuuuu! Suna bin motar da gudu kasamcewar sun San mai ita, a lokacin ne kuma gabanta ya tsananta fad'uwa tana fargabar ta futo daga cikin motar a idanun jama'a......Haka dai tayi shahada ta futo tana sinke kanta kamar munafuka ta kasa dago kanta kokarin wuce take ya rik'o hannunta ta baya dago kanta tayi tana kallonsa shima yana kallonta a lokacin ne kuma Abbu da Nasir Hafiz suka doso gurin dukanin su zasu nufi massalaci idanunsu ya sauka akan Hanifa dake daf da Khalid hannunwan su a hade suna gashi tsakaninsu babu wata tazarar kirki su Kansu suna jin bugun numfashin junanansu Khalid ya saki wani killer smile lokacin da suka hada ido da Abbu ya dauke kansa kamar bai ganshi ba cigaba yayi da yi mata magana kasa kasa ita kuma sai kallonsa take tana marairaice fuska kwata-kwata bata lura dasu Abbu ba domin baya ta basu sai da suka wuce ne taga giftawarsu gabanta yayi wata irin mummunar fad'uwa da hannu ta nuna masa su. Daga kafad'a yayi alamun bai damu ba yana wani tabe baki.... Kamar zata kifa kasa haka ta bar gurin gabanta na wani irin bugawa kallo ya bita dashi hakanan jama'ar da suke gurin suka dunga kallonta suna mamakin meye alakarta da Mashahuri da har ta kaita shiga motsarsa. Khalid kuwa motar ya shiga yana jin wani irin farin ciki a zuciyarsa Yanzu duk wata damuwa da take damunsa ya samu saukinta saboda yasan ya dasawa yarinyar tambarin da bazata taba mañcewa dashi ba kuma ya lura sonsa yayi mugun k'arfi a cikin zuciyarta bayan Wannan kuma yaji dad'i da yaga Ya Shaik kuma shima ya ganshi ko babu komai shima ya dasa masa damuwa da b'acin rai kamar yanda ya dasa masa a zuciyarsa. Wayarsa ya dauka ya kira Abbakar..... Sai murmushi yake saki yana shafa kanshi idan ya tuno abunda ya faru dashi da ita sai ya kara jin wata sha'awarta na kara nunkuwa a cikin zuciyarsa,,, Abbakar na zuwa ya ganshi Cikin walwala da farin ciki ya bashi hannu suka tafa yana fadin"Guy da'alama dai ta waru naga sai nishadi kake. " da murmushi a fuskarsa yace." Abbakar yau na kara tabbatar da cewar yarinyar nan tana sona wallahi kawai don karan kaina na k'yaleta babban abunda yayi min dad'i a zuciyata shine yanda Shaik ya gammu tare da ita nasan dole zan saka zuciyarsa a damuwa." Abbakar ya kyalkyale da dariya yana bashi hannu manya-manyan ledojin dake gabansa ya mik'awa Abbakar din yace." Gashi a samu yaro ya kai mata yanzu_yanzu."Abbakar yace." Insha Allah Yanzu zan sanya Asalamiyya ta kaimata." Sallama sukayi da juna Khalid yaja motar ya bar unguwar........ Abbakar kuwa Asalamiyya yaje ya azalzala dole ta bar abunda takeyi ta tafi gidansu Hanifa babarsu sai kallon Abbakar din take tana so ta tambayeahi komeye domin sai take zargin ko shine yayi mata siyayya su sunanan dede da man shafawa baya sai musu ganin Abbakar din ya futa yasa tayi shiru amma taci alwashin sai ta tambaye shi idan ya kara shigowa. Tsayuwa tayi a soron gidan gabanta na fad'uwa takasa shiga ciki tans tuno tun lokacin da ta futa daga gidan k'arfe daya saura na rana Yanzu gashi ana kokarin kiran sallahar magariba motsin ammi take ji a kicin tana aiki kawai tayo shahada ta shiga gidan suka hada ido da Ammi da ta futo daga kicin fuskarta kawai ta kalla ta gane tana cikin damuwa kasa tayi da idonta Ammi ta shige ba tare da tace mata komai ba, tsaye tayi a gurin cikin damuwa ita kuma Ammi na sabgar gabanta 'kala bata mata ba har ta Dora alwala tana kokarin shiga ciki Asalamiyya tayi sallama . Ammi ta dakata tana amsa sallamar Asalamiyya ta karaso hannunta niki-niki da ledoji Hanifa tunda taga ledojin taji tsayuwa na Neman gagarata sai ta tsuguna a gurin tana jin wata irin fargaba da damuwa tana jin suka gaisa Asalamiyya tace"Gashi inji ya Abbakar wai na Hanifa ne." Ammi tayi shiru tana kallon ledojin daga bisani tace"To maddalah Asalamiyya a jesu anan gurin kinji ko." Asalamiyya tayi yanda akace mata tayi mata sallama Ammi tace "ki gashe min Ummanki." Tace "Zataji Ammi." Sai da tazo futa ne ta tsaya kan Hanifa tana yi mata magana taga taki dago kai tw kalleta kawai sai ta wuce abunta tana mamakin meye dalili. Ammi ta shige ciki dadduma ta shimfid'a ta tada sallah kana ganinta kasan tans cikin damuwa . Jikinta babu kwari ta mike a hankali taje ta dauki buta band'aki ta shiga ta kama ruwa ta futo ta d'aura alwala a hankali ta shiga can kuryan dakin ta shige kamar yanda ta saba, kayan jikinta ta cire da sauri ta zura doguwar Riga da babban hijabi ta tada sallah. Abbu Nasir Hafiz dukaninsu Cikin damuwa da takaici suka shigo gida sai sukayi karo da abun mamaki ledojin da suka gani ya basu mamaki sosai cikin rumfar suka shiga Hanifa naji muryar Abbu gabanta ya hau fad'uwa amma duk da haka dai tayi alk'awarin fada masa abunda yake Cikin zuciyarta domin tana ji tana gani bazata yarda da auran Nasiru ba alhalin ga Wanda take so, Ammi ya kalla dake share hawaye tana addu'a sai bayan ta shafa addu'ar ne yace." Ta shigo ko." Ammi tace"Tana cikin daki Yanzu." Gyada kansa yayi ya cigaba da cewa"Ba sai an tamnayeta komai ba mun gani Yanzu daga gurin Wanda take Halima bantaba tsammanin yarinyar zata yi min haka ba kiri-kiri tana nema ta zubar min da mutumuci ta maida ni k'aramin mutum a gurin jama'a." Yanda ya fad'i maganar zaka San yana cikin damuwa da b'acin rai.Nasir da Hafiz suna tsaye duk ransu babu dad'i Nasir ji yake kamar yaje gurin Khalid din ayi wacce za'ayi domin wata irin tsana yake masa Mara misali...... A zuciyacr Hafiz yace." Abbu mutukar wannan yarinya ta sanya hawayen ka suka zuba to Wallahi sai na karyata sai nayi mata dukan mutuwa a gidanan domin ba kai kadai take kokarin zubarwa da mutumci ba har damu kanku yaron da duniya ta shaida bashi da d'a'a da d'abiu masu kyau saboda tsabar ita din jakace cikin jakuna take binsa suna yawo a mota Abbu ka k'yaleni na karya ta na zubar da shegiya kowa ma ya huta....... Rai abace Abbu yace." Hafiz aiki da lura mana."! Shiru Hafiz yayi yana sauke ajiyar zuciya Ya cigaba da cewa"Kar in kara ji ka kirata da wannana kalmar ta jaka kaji ko."!? Hafiz yayi kasa da kansa cikin damuwa da b'acin tai...... Ammi tace"Abbu nifa wannan yarinya na soma ma zarginta domin ba yau na fara jin k'amshin turare a jikinta na tabbata suk Dade suna tare da yaronan wallahi zuciyata ta shiga rud'u a kanta." Abbu yayi shiru na minti biyu kafin ya bude murya ya kira Hanifa da duk abunda akeyi tana ji tayi shiru... Amsawa tayi da sanyin murya ta futo duk suka bita da kallo abbu ya nuna mata kusa dashi ta zauna Hafiz kuwa ji yake kamar yaje yayi ta dukanta ko ya samu sassauci ita kuwa Ammi Sam taki kallon inda take. Abbu ya kalleta cikin nutsuwa yace." Hanifa wannan abunda kikayi shine dai-dai."!? Shiru tayi tana zumb'ura baki yace." Kiyiwa Allah da manzon sa ki dawo cikin nutuwar ki ni Mahaifin ki ne bazan taba yi miki abunda zai cuce ki ba kiyi min biyayya kamar yanda na umarce ki kika amunce min zakiyi idan kikayi min biyayya zaki samu riba a duniya da lahira Hanifa tarayyarki da wannan yaron bana sonta domin ni banyarda da d'abi'unsa b..... Kuka ta fashe musu dashi tana fadin"Abbu ka daina fadin haka wallahi yana da d'abi masu kyau don dai kai dashi bakwai jituwa ne amma Khalid yana da hankali kuma yana mutukar sona da gaskiya."! Duk suka yi shiru suna mamakin maganganun ta, Nasir yaji kamar ya cakawa kansa wuka ya huta da wannan bakin ciki..... Abbu ya sauke ajiyar zuciya tare da fadin"Duk abunda kika fada bakiyi karya ba Hak'ika ko wane Dan Adam yana da nasa baiwar da Allah yayi masa amma kuma ko a gurin Allah wani yafi wani hakanan kuma cikin jinsin mutane dole a samu Wanda yafi nagarta har kullum ni burina a duniya in samar miki farin ciki Wanda ko bayan raina ne zakiyi farin ciki da abunda nayi miki."! Cikin kuka tace"A'a Abbu babban farin cikina a yanzu shine kawai ka yarda na auri Khalid alk'awarin da kayiwa Ya Nasir ka rusa shi ni dama fa bana sonsa kawai dai nayi kokarin nayi maka biyayya ne kuma zuciyata ta kasa yin juriyar hak....... Bata karasa ba Ammi ta mike tsaye a kanta ta dinga dukanta da hannunwan ta cikin b'acin rai murya na rawa take fadin"Hanifa idan kikayi mana haka Kin cuce mu kuma kin zama yarinya mara tarbiyya Allah sai ya saka man.......abbu ya rike hannunta yana kokarin zaunar da ita ransa duk a bace yake fadin"Halima mutukar na kara ganin hannun ki ya taba jikin yarinyar nan da sunan duka ranki sai ya b'aci. "!! Cike da b'acin rai yayi maganar Ammi ta shige kuryan daki tare da zama gefen gado tana share hawayen bakin ciki. Shi kuwa Abbu Hanifa yake kallo dake ta faman gursheken kuka.! *12/1/2020* _BintuUm@rAbb@le_ [1/21, 9:45 PM] BintaUmarAbbale: _MASHAHURI!_ *_Mallakar: Binta Umar_* *_Ki biya ki karanta cikin kwanciyar hankali ke kuma da kika futar da book d'in na barki da Allah!_* *08089965176* *07084653262* *0542382124....Binta Umar Gt bank* *37* Jikinsa daure da towol me Dan girma ya futo hada ido suka yi da Mamy din sai yayi sauri kauda kansa yana nufi dressing mirror dinshi Mamy tace"Myson kai da kake zazzab'i ina kai ina Wanka zazzab'in sai ya kara k'arfi naga kuma sai wani kauda kanka kake kamar wani Mara Gaskiya." A hankali yake mutsika mai a jikinsa yace." Mamy nace miki fa ba wani sosai nake jin zazzab'in ba kawai dai don kince dole muje hospital ne." Mik'ewa tayi tana kokarin futa tace"ni dai ka sanya kayanka ka futo ina jiran ka." Shikkenan Mamyna yanzu zan futo. " abunda ya fada kenan ya cigaba da abunda yake yi, Mamy ta futa tana wasiwasi cikin zuciyarta yanzu ta soma fahimtar abunda yake damun Dan nata, Khalid na sanya kayansa yana tunanin abunda zasuji daga gurin Abbu tunda yace a saurare shi daga yau zuwa gobe,turaranshi me masifar kamshi ya fesa ya dauki wayarshi ya futa daga d'akin. Mamy na zaune a parlor ta shirya tsaf! Don har ta sanya hijab ya shigo Cikin sanyi jiki kallo ta bishi dashi cike da kulawa tace"Myson idan na kira wannan yarinyar shaid'aniya har sanja fuska kake yi nifa na gane duk itace sanadiyar fad'awar ka cikin wannan halin tun ranar da naga kana kallon pictures dinta Shikkenan ka susuce kazama komai naka salau-salau Wannan Yarinyar ko shad'ain ma dole yaji tsoront..... Ka tsaye ta Yayi ta hanyar fadin "Mamy stop."! Cikin yanayin damuwa ya fad'i maganar yana kokarin zama kujerar cin abinci. Ya mutsa fuskarsa ya fara yi yace." Mamy wannan yarinyar da kike magana a kanta ba itace zata sanya ni shiga damuwa ba kawai dai daga Allah ne kuma Mamy kamar kinayi mata daukar Mara tarbiya Mamy itace f.... Kafin ya karasa itama ta katse shi ta hanyar fadin"Itace yarinyar da kake so ko."!? 'Daga kansa yayi kamar wani yaro Karami, jinjina kai tayi tace"lallai biri yayi kama da mutum wato myson ka rasa wa zaka so sai wannan Mara kunyar yarinyar me nuna tsaraicinta a waje shin kasan iya adadin maza nawa ne suka ga jikinta shine zakaje ka kwaso min kara da kiyashi myson ga yarinyar kirki nace maka ka aura kaki daukowa kanka masifa."! Cikin damuwa takw maganar. Khalid yaji wani irin daci-daci a bakinsa jikinsa ya fara daukar zafi zazzab'i na so ya sake hawansa Mamy tayiwa Hanifa mummunar fahimta ya za'ayi ya ganar da ita cewar ba mara tarbiyya bace. Yace." Mamy mu bar maganar don Allah kin San bana son damuwa ko? Kaina zai fara ciwo Yanzu. "! A hasale tace"Kanka ya Dade baiyi ciwo ba Myson ai me daure maka gindin ya futa dole inyi magana nace maka idan kasan wannan yarinyar ce wacce ake ta d'auki babu dad'i akanta to tun wuri ka janye maganar auranta kazo ka nemi Nasrin yarinyar arziki kuma cikkakiyar macace."! Shiru yayi yana kurbar ruwan tea d'insa yasan da Dad dinshi na gurin Mamy baza tayi masa wannan Shouting din ba tuni zai hana shi kuma Allahn da ya hallice Sam baya kaunar hayaniya don dai babu yanda zaiyi da ita ne. Hafiza ce ta shigo parlor da sallama a bakinta, da gudu yaron ta Mus'ab ya nufi gurin su Mamy yana fadin " ancle Oyoyo."! Khalid ya d'ago kanshi da sauri yake kokarin dakatar da yaron ganin Chocolate a hannunsa duk ya 'b'aci yasa ya fara ya mutse fuska Mus'ab kuwa kokarin tab'a jikinsa yake yana murna wata irin tsawa ya buga masa wacce tasa yaron ya Ruga gurin Mamy da gudu ya fara kuka Hafiza ta 'bata fuskarta tana Harar sa tace"Wallahi kai mugun d'an wulakanci ne yaron nan tun a mota yake fad'in ancle Khalid Oyoyo shine saboda tsabar wulakanci zaka buga masa tsawa saboda baka San zafin haihuwa ba."! Hararata yayi kawai bai ce komai ya cigaba da kurbar tea d'in sa yana jin haushin zagin da Mamy tayi wa Yarinyar Shaik. Mamy tace"Ke kuma daga ina da sassafe haka."!? Zama tayi daya daga cikin kujerun gurin tace"Mamy naje hospital ne na kai Mus'ab jiya ya ha namu bacci wai Ashe kunnen sa ne yake ciwo." Mamy ta jawo Mus'ab din tana dubawa tace"babu shakka kuwa gashinan har ya soma ruwa." Hafiza tace"Wallahi jiya yasha kuka har ya bani tausayi. " Mamy tace"Ciwon kunne ai masifa ne wallahi sai ki kiyaye bashi magani kan 'ka'ida kuma ki dinga sanya masa hula idan iska ta kad'a." Tace"Insha Allah Mamy Dady ya futa ne." ? Ya futa tun sassafe yau yana da ba'ki ne." Cikin shagwaba tace"wallahi wasu kudi nake so masu kauri a gurinsa." Wani irin kallo Khalid ya watsa mata yana ta'be bakinsa, 'bata fuska tayi tace"Dan rainin hankali kawai baka gaishe ni ba ina matsayin yayar ka kana tab'e min baki." Bata fuskarsa yayi kicin-kicin da ita ya tsani suce sun girme shi a ganinsa tunda shine namiji a cikinsu dole su bashi girma yace." Wannan kud'in masu kauri da kike magana akansu to ba samu zakiyi ba indai nine zan futar dasu zaki daskare anan gurin." Mamy ta kalleshi tare da fadin"Kudinka ne da zaka fad'i haka? Kuma ai ba Kai ta tambaya ba ko." ? Shiru yayi kawai yana latsa wayarsa Haushi ya turnuke Hafiza Tace " Wallahi komai dare ina gidanan idan ta kama ma in kwana sai na kwana dady ya dawo ya bani kudi domin ba kai kadai ya Haifa da zaka dinga gwadawa mutane iko."! Ganin yanda take masifa ne ya bashi dariya ya gimtse fuskarsa tare da fadin"Ki Bini a hankali kawai ki samu idan kuma ki kece hayaniya zakayi Wallahi baza a bayar ba." Shiru tayi masa tana hada tea domin haka ta futo daga gidanta bata karya ba. Mik'ewa yake kokarin yi Mamy tace"Ina zakaje ne."!? Tsayuwa yayi ba tare da yace." Komai ba Mik'ewa tayi tana kallon Hafiza dake bawa yaronta soyayyan kwai tace." Zamuje asibiti mu dawo yanzu." "Mamy waye babu lafiya kuma."!? Mamy tace" Gashinan a gabanki." Yar dariya tayi tace"Mamy godai-godai dashi zaki kaishi asibiti bayan yanzu ya gama rashin mutunci Wallahi ki kyaleshi yayi tafiyar sa shi kadai kar bawa kanki wahala." Mamy tace "Gwara dai na kaishi da kaina a duba shi jiya kwana yayi da zazzab'i wata shegiyar yarinya ce ta sanyo shi a gaba kullum cikin damuwa da tunani haka ta koma." Hafiza tasa ihu ! Tana nuna Khalid da hannunta Wanda yayi wani irin shan kunu shifa Mamy ta takura masa wallahi kamar shi zata ta kai asibiti kawai dai yanayi mata ladabi ne." Hafiza ta cigaba da dariya tana fad'in"Wannan yarinyar yar albarka ce wallahi gwara da ta sanya ka a gaba oh! Ni Hafiza amma Wannan yarinyar ta burge ni wallahi da ta samo lagonka hahahahaha."! Ta k'arashe maganar tana dariya. Kamar ya gaura mata mari haka yake ji ba tare da yace komai ba ya fuce daga parlor yana hira hanci shifa yanzu abunda ya dame shi anan shine yaji daga gurin Abbu gashi dady ya futa Wanda a gurinsa yake sa ran jin maganar , wayarsa ya dauko yana Neman wayar dady nasa akace ma sa line is busy wai ana amfani da ita hak'ura yayi ya bude mota ya zauna dravar dake Jan Mamy yaga ta futo da sauri yaje ya bude mata motar ta shiga sannan ya shiga motar suka futa daga gidan. Wani pravite hospital suka nufa Mamy sai lallabashi takeyi a cikin mota tana bashi shawarar cewar ya rabu da Hanifa domin ba yarinyar arziki bace kuma ita sam yarinyar bata kwanta mata ba ya kwantar da hankalinsa ya duba wata Yarinyar idan ma baya son Nasrin din to ya rabu da Hanifar shine yafi alkairi a gareshi. Lokaci da Mamy take masa wannan maganar ji yayi zuciyarsa tana masa wani irin zafi shifa yanzu duk Wanda zai ce masa ya rabu da yarinyar shaik yana ganin kamar makiyin sa ne idan banda Mamy sa ce da babu abunda zai hana bai fada mata wacce zatayi mata zafi ba, Sam baya kaunar b'acin ranta shiyasa ma da take masa maganar yayi shiru da bakinsa a lokacin kuma zazzab'in ya kara rufe shi ya dinga jin wani irin sanyi tsigar jikinsa na Mik'ewa cikin wannan halin suka isa asibitin. Dake jarumin namiji ne ko alama Mamy ta ba gani ba na cewar yana jin jiki shi dai shi yasan abunda yake ji a jikinsa. Koda Dr ya ga yanayin sa nan ya fahimci zazzab'i me zafi ne yake damunshi Wanda dole ma sai ya kwanta anyi masa Karin ruwa saboda yanayin k'warin jikinsa nan Mamy da taji maganar Karin ruwa ta kara tayar da hankalinta Dr tace "ki kwantar da hankalin ki ba wata matsala bace kawai zan kara masa ruwa ne domin ya samu k'arfi a jikinsa." Mamy futa tayi tana kiran wayar mijinta a hankalinta a tashe Kwata-kwata basa kaunar Abunda zai taba lafiya Khalid din idan bashi da lafiya sun shiga damuwa kenan tasan Yanzu Mijin NATA idan yaji duk abunda yakeyi zai aje ne ya dawo gida. Ko da ta kira wayar itama akace mata line is busy dama kuma ya fada mata yau yana da baki sosai kuma akwai aiki a kasuwa haka ta hak'ura ta dawo jikin dakin da Khalid din yake kwance.lokacin har Dr ya futa bayan ya d'aura masa ruwa, Khalid ya kurawa fuskar wayarsa ido Mamy ta shigo saurin wayance wa yayi ya kashe wayar ya aje yana lumshe idonsa lokacin pictures din Hanifa yake kallo. Zama tayi kusa dashi tana kallon fuskarsa a nutse tace"Myson don Allah ka kwantar da hankalin ka kaji ko."! Bude idonsa yayi a hankali yace." Mamy ki daina tayar da hankali nida bani da wata damuwa a halin yanzu sai guda daya kuma ina so kema ki fuskance idan na samu biyan bukata ta Shikkenan amma nutsuwa da kwamciyar hankali na duk ya tattara ne a gurin yarinyar Shaik ita kadai ce muradi na a halin yanzu." Girman da maganar tayi mata ne yasa kawai tayi shiru da bakinta tana mamakin wannan a'lamari." A hankali yace." Mamy kije gida ki huta please zan kira Abbakar yanzu ya zauna dani zuwa yamma tun d'azu na kira wayar dady ban samu ba." Tace"Nima Yanzu na kira in fada masa baka da lafiya." Kallonta yayi ta kalleshi itama yayi saurin yin kasa da idonsa domin baya son ta fuskanci wani abun yace." Mamy please kar ki fada masa don Allah kin San dai halinsa ko."? Shiru tayi masa kawai Mintuna biyar tsakani Dr ya dawo da magani a hannunshi duk ya mik'awa Khalid ya mike zaune sosai ya karba da ruwan da yake miko masa ya shanye tas Dr yace ." insha Allah zaka samu sauki zuwa anjima ciki harda na bacci domin idanunka sun nuna alamun rashin bacci ka kwanta ka huta zaka tashi da k'arfin jiki." Khalid yace." Tank u dr koma yayi ya kwanta shi kuma Dr ya futa da sauri. Ya kalli Mamyn yace." Kinji abunda Dr yace ko cikin maganin da nasha yanzu akwai na bacci kije gida Da yamma sai ki dawo." Tace"Myson bana son na tafi na barka kai kadai ne." A hankali yace. " mamy yanzu zan kira Abbakar yazo kar ki damu kinga Hafiza na can tana jiran ki." Shiru tayi masa Khalid ya cigaba da lallab'ata da kyar ta tashi ta tafi, ajiyar zuciya ya sauke bayan ta futa wayarsa ya dauka ya fara Neman layin Abbakar bugu daya tayi ya dauka a kasalance yace." Abbakar bana jin dad'i wallahi ina Asibiti yanzu yaya alk'awarin mu. "? Abbakar yace." Guy wane asibiti ne ganin zuwa Yanzu. " a hankali yace." Dr Habib hospital gashinan a wajan ringirod." Abbakar yace. " Nagane hospital din ganin zuw...... Katseshi yayi ta hanyar fadin Abbakar ina alk'awarin mu da kai na jiya. " Yace." Alk'awari yana nan kasan sai k'arfe uku na rana suke shiga makaranta kuma kai yanzu kana kwance a asibiti ya za'ayi kenan. "? Ajiyar zuciya ya sauke yace." Ka bari sai k'arfe uku tayi sai kazo amma ka tabbatar kazo min da ita yanzu bacci zanyi zuwa lokacin." Abbakar yace." Kar kadamu guy zan maka kokari insha Allah Yanzu ya jikin naka."!? A ya mutse yace." Da sauki dai mybe idan na ganta in samu nutsuwa domun ni kaina a halin yanzu na rasa meke damuna wallahi." Yar dariya Abbakar yayi yace."Guy Allah ya Kai damo ga harawa dai." Yana sauke ajiyar zuciya yace." Ameen my friend ina sauraron zuwan Ku." Abbakar yace." Insha Allah." Kashe wayar yayi yana lumshe idonsa da tunanin yarinyar Shaik bacci ya dauke shi mai cike da mafarkinta........ *Yanzu a ka fara labarin* *4/1/2020* _BintuUm@rAbb@le_ [1/21, 9:45 PM] BintaUmarAbbale: _MASHAHURI!_ *_Mallakar: Binta Umar_* *_Ki biya ki karanta cikin kwanciyar hankali ke kuma da kika futar da book d'in na barki da Allah!_* *08089965176* *07084653262* *0542382124....Binta Umar Gt bank* *35* Nasir ne ya zauna da Abbu gefan tabarma ranshi duk babu dad'i sosai yake jin tsananin takaicin zagin da jama'ar unguwa suke masa yanzu idan da zaiyi nufin daukar mataki babu yadda za'ayi Abbu ya barshi shi kam ya rasa wace irin zuciya ce dashi. Cikin wata irin murya Abbu yace." Halimatu kawo mun ruwan sha." Ammi ta bude randa ta ciko Kofi da ruwa ta mik'a masa. Kafa kai Yayi a bakinsa sai da ya shanye tas sannan ya aje kofin yana sauke wata irin ajiyar zuciya shuru Yayi yana kallon guri guda duk sukayi cirko-cirko a kansa mintuna goma ya dawo nutsuwar sa Nasir ya kalla a nutse yace." Kira min Hanifa. " kafin nasir ya yunk'ura Hanifa ta futo daga daki tana matsar hawaye.Abbu ya nuna mata kusa dashi. Zama tayi jikinta duk a sanyaye. Ido ya tsira mata yana kallo Hanifa taji wani sabon hawayen yana zubo mata wani irin tausayin mahaifin NATA ya lullub'e ta. Hannunta ya rike cikin nasa a tausashe yace." Hanifa ki fada min gaskiya kan abunda zan tambaye ki." Kai ta d'aga sama, ya cigaba da cewa"Nasan ke din yarinya ce mai gaskiya bakya karya duk rintsi ni nayi miki wannan shaidar Hanifa ina so ki fadamin shin gaskiya ne kece kika fara fadin cewar kina son wannan yaron da suka zo gidanan Yanzu ." hannu tasa ta toshe bakinta dashi wasu irin zafafan hawaye na kwaranyo mata. Murmushi Abbu yayi yace." Ba kuka nace kiyi min ba gaskiya nace ki fadamin Hanifa." Ammi ta bude baki zatayi magana ya daga mata hannu shiru tayi tana addu'ar Allah yasa hanifa ta fad'i gaskiyar al'amari. Kukan da Hanifa takeyi ya soma bawa Abbu haushi cikin tsawa yace." Idan baki fada min Gaskiya ba yanzu zan sanya yayunki su Zane miki jiki don kinga ina rarrashin ko."!? Hannunta duk biyun tasa ta rufe bakinta dashi muryar ta bata futa sosai tace"Abbu nima ban San lokacin da nace ina sonsa na Wallahi haka kurrum nake jin gabana na fad'uwa Idan na tuna dashi Abbu kayi min addu'a indaina sonshi. " Gurin tsit!! Yayi kowa na mamakin Abunda Hanifa ta fad'a Ammi kuwa mamakinta kadan ne dama tuntuni tasan da maganar Abbu wani irin gumi ne ya tsinke masa a jiki kallon Hanifa kurrum yake cike da mamaki har ta iya budar baki tace tana son namiji. Hafiz ya zaburo! Cikin tsawa yace." Hanifa don baki da mutumci ki rasa wa zakice kina so sai Wannan Dan iskan yaron da ya gagari kowa a gari mawa'kin da bai taba wake ma'aiki ba kullum bashi da aiki sai raye-raye kina so ki zubar mana da mutumci a gari kina nufin ko kin rasa mijin aure a duniya zaki auri wannan Mara tarbiyya to ki rubuta ki aje ko da ran Abbu ko babu ransa bazaki taba auran mawa'ki ba."! Cikin zafi Hafiz ya kare maganar dama shu mutum ne me sanyin hali amma kuma Idan ya dau zafi bai iya fushi ba. Kuka ta saki sosai tana matsawa jikin Abbu domin Hafiz kokarin kai mata duka yake. Abbu yace." Hafiz sassautawa zuciyarka ka saurare ni." Hafiz ya koma ya zauna yana sauke ajiyar zuciya Abbu ya cigaba da cewa "Hanifa batayi laifi ba mune muke ganin kamar ta aikata laifi abunda tayi shi ya samo asali ne daga gurin sayyada Nana khadija matar Annabi Muhammad (slw) babu laifi anan don mace taga namiji ta nuna tana sonta sai dai ita Hanifa zuciyarta batayi mata adalci ba da dauko mata son Wanda ya fi karfinta Idan da wani ne takewa wannan son bazan damu ba wallahi amma jin cewar wai ita da kanta ta furtawa yaron Kalmar so yasa duk jikina yayi sanyi yanzu ma kuma na kara tabbatar da hakan tunda gashi ta fada da bakinta gashi kuma tana koke-koke tabbas Gaskiya ne, Abunda dai bana son yi shi zanyi dole cikin biyu za'ayi d'aya ko mu koma gombe da zama ko kuma in saka gidan nan a kasuwa mu sanja gurin zama duk Dan wannan yaron domin ina ganin idan tayi nesa dashi hankalinta zai kwanta." Duk sukayi na'am da maganar Abbu Nasir yace." Abbu ni narasa wane irin shad'ainin yaro ne Wallahi na tabbata shine ya rinjayi Hanifa har ta furta masa Kalmar so ni a shawarata kawai mu koma gombe shi zafi domin ina jin tsoron sharrin Mahaifin yaron wallahi." Abbu yace." Dole cikin biyu za'ayi d'aya dama." Ammi dai na zaune tana sauraran su dama kuma irin wannan ranar take jin tsoro addu'a takeyi Allah yasa karshen al'amarin ne yazo domin itama bata kaunar Hanifa da Khalid din ko kadan domin tasan Khalid ba sa'an auran yarta bane. Hanifa kuwa jin zagin da Nasir yakewa Khalid yasa taji kamar ta zageshi itama don dai kawai su Abbu na gurin ne hararasa kurrum take yi ta kasan ido tana share hawayen ta, daga k'arshe ma tashi tayi ta shige daki gado ta kwanta ta dura Sabon kuka wai zasu tashi daga unguwar nan akan Khalid ko kuma su koma gombe wato su Abbu har yanzu basu fahimci yanda take ji ba a jikin zuciyar ta, idonta na zubar da hawaye ta zato pastar dinshi da ta soma yagewa ta tsirawa fuskarshi ido lumshe idonta tayi tana kallon k'aramin bakinsa Wanda wani irin kayattacan gashi ya kewaye kasan ha"barshi Wanda ya d'an lotsa kad'an fuskarta ta matsar daf da tashi ta d'ora bakinta kan nasa take ta tuno ranar da yayi kiss dinta hannuta tasa ta ta'bo lebanta tana lumshe ido hawaye suka zubo jikin pastar a hankali tace"I lov my chocolate Khalid Allah ya d'ora min sonka Abbuna baya sonka Zuciya kamar zata stage saboda kaunar kaaaaaa! A carke ta k'arashe maganar tayi ruf da ciki kan pastar tana wani irin kuka me tsuma zuciya. Muryar Ammi taji a kanta tayi saurin goge hawayen ta tana kokarin mik'ewa zaune Ammi tace"Kuka kike yi ko."? Girgiza kanta tayi taki yarda su hada ido da Ammi. Gyada kanta tayi cike da damuwa tace"Na fada miki ba tun yau ba wannan yaron ba tsaran ki bane kika nuna min cewa kin hak'ura dashi Ashe kinyi min lumbu-lumbu ne ko wai Hanifa kamar ke da nasani mace me kunya da kawaici kije ki fadawa namiji cewar kina sonshi Gaskiya nayi mamakin Wannan ab......... Bubbuga k'afafu take yi kan gadon tana kuka take fadin"Ammi wai yaya kuke so inyi ne? Uhumm nace nima bana so nake sonshi a jikina nake ji kuma ai Abbu Yanzu ya gama fada cewa abunda na aikata ba laifi bane Ammi ni dai don Allah ki k'yaleni naji da radadin da zuciya take min kome nake a cikin gidanan daurewa nake yi."!!! Ammi ta sassauta muryar ta saboda bata so Abbu yaji komai cikin sigar rarrashi tace"Shikkenan ai dama ba laifi kikayi ba kawai tarbiyar yaron da kika dauko ce bata yi mana ba shiyasa muke nuna miki illahr hakan." Shiru tayi tana kokari. Kwanciya nan hankalin Ammi ya Kai kan pastar Khalid hannu tasa zata jawo da sauri Hanifa ta rike Ammi naja Hanifa na ja. Cike da mamaki! Tace''Baza ki Bari in ga ki menene ba."!? Zumb'ura baki tayi tace"Ammi ni......... Ammi taja pastar da k'arfi ta fara kokarin yagewa..... Da k'arfi hanifa tace",Wayyo Ammi kar ki yaga min don Alla....Kafin ta 'karasa Ammi ta fuzge pastar daga hannunta ta rabe gida biyu a take Hanifa ta hade kanta da gwiwa tana shashshekar kuka. Ammi kuwa hade pastar takeyi tana kokarin tantance waye a jiki. [1/2, 9:42 AM] .: Cike da mamaki Ammi take kallon Pastar tunani takeyi a cikin zuciyarta yaron duk inada namiji yake ya kai ko ba'a fada mata ba tasan shine Khalid din da ake rigima a kansa sai yanzu ta kara tabbatar da cewar soyayyar Yaron tayi nisa a cikin zuciyar yar tata tunda gashi suna tare da ita tana mak'ale da hotonsa kullum su suna can gefe basu sani ba. Ammi ta mike da pastar a hannunta. Dago kanta tayi tana kallonta har ta futa Ammi kai tsaye kicin ta nufa ta cusa pastar cikin murhu ta kyasta ashana ta kama da wuta, bata koma dakin ba ta cigaba da aikace-aikacenta tana yi Hanifar addu'ar ta Neman zabin Allah tsakar gidan babu komai Wanda ya dangaci kayan masarufin da Alhji Tijjani ya kawo Abbu yasa Duk an futa dasu waje yace duk su Nasir ya rabar dasu kafin kace kwabo kofar gidan ya cika abunka da unguwar yaku bayi dama kowa Cikin bukata yake, bayan sun gama ne suka wuce cikin gari domin fara shirye-shirye. Hanifa kuwa kwanciya tayi ta dinga sharar hawaye Shikkenan Ammi ta kona mata hotonta Wanda shine yake rage mata rad'ad'in soyayyar sa idan ya taso mata. *** Alhaji Tijjani fada kawai yakeyi cikin mota yana ganin kamarshi yaje Neman auran yar talaka tilis har a tsaya ana fada masa magana da kudinsa da komai babu dad'i ko kadan yace." Myson Wannan yarinyar ko itace autar mata ya kamata ka rabu da ita ubanta mutsiyaci ne me k'ashin tsiya Idan akayi auran ma kai da yarinyar zatazo ta gada mana tsiya ne ni idan da zaka bi nawa ra'ayin kaje ka nemi auran yayan sarakai da masu mulkin k'asar nan nasan da gudu zasu amunce maka amma ka tsaya kan yar mutsiyata."! Khalid da yake jin zuciyarsa kamar zata tarwatse yace." Dad ni kaina bayin kaina bane laifin zuciyata ne wacce na kasa sarrafata a halin yanzu kasan aure baya tsarina amma ganin yarinyar yasa naji ina bukatar in aureta in raya sunna Dad meye aibuna da mahaifinta yake gani har zai hanani auranta Dad wallahi nayi rantsuwar ya sake ya aura wa yarinsa wani mijin bani ba to sai na hanasu jin dad'i rayuwa kamar yanda suka hanani jin dadin tawa rayuwar. " Alhaji Tijjani yace." Duk wani kokari da zanyi nayi akai amma zan sanya Alhaji Lawan abokina ya koma da maganar idan ya amunce Shikkenan idan kuma bai amunce ba sai ka hak'ura ko kuma ka dauki ko wane irin mataki akansu." Shuru Khalid yayi yana tunanin mafuta abunda zuciyarsa take tunzurashi ya aikata yana ganin shine kawai zai fi masa don haka ya bari aka zuwa gurin abbu din a karo na uku idan ya'ki amincewa zai zartar da hukunci da ya yanke. Kasuwa suka wuce Khalid wani bene ya hau Cikin kasuwar nan shagunan Alhji Tijjani suke da ofis dinshi nan ya shige ofis din ya kwanta kan kujera yana sake sake yau abunda bai taba sha yaji yana sha'awar sha Mobson ya Dade yana fada masa sigari na gusar da damuwa yau ta dalilin yarinyar Shaik zai fara sha lallai Ya shaik da yarinyar sa sun shammace shi sun shiga rayuwar sa sunyi Kane Kane Wanda yake ganin tilas ne ma ta dauki mataki akan hakan. Mi'kewa yayi ya le'ka ta window yana kallon yanda mutane suke ta harkokinsu na kasuwanci wani yaronsu ya hango shigowar sa kasuwa kenan cikin ikon Allah suka had'a ido dashi Hannu ya daga masa alamun kira ya koma ciki shi koma yaron da sauri ya hau saman ofis din ya nufa sama-sama suka gaisa Khalid ya zaro dubu guda aljihunsa ya mik'a masa tare da fad'in"siyo min sigari kwali daya." Ba tare da bata lokaci ba yaron ya sauka kasa da sauri shi kuma ya koma ya zauna hade da dafe kansa minti biyar tsakani sai ga saurayin ya dawo karba yayi yana mik'a masa canji ya daga masa hannu godiya saurayin yayi ya sauka kasa, Khalid na bude ledar yaga harda leghtar yayi dad'i sosai don haka ya zaro guda ya kunna ya bata wuta Zuka yake yana lumshe ido tare da addu'ar Allah yasa ya daina jin abunda yake ji a zuciyarsa a game da yarinyar shaik. Alhji Tijjani da abokina Alhji lawan suna rattuana maganaer komai Alhaji Tijjani ya fada masa Alhaji Lawan yace." Alhaji kayi gajan hakuri Gaskiya banji dad'i abunda kayi ma bawan Allah nan ba domin wani mutumci yafi kudi a gurunshi kaga mutumin ya nuna maka cewar shi kudunka basu ne a gabansa ba mutumci ne a gabansa Kai da kaje nema Kaine dole zaka kaskantar da kanka kaga yanzu abunda kayi masa zai sa ya kara d'aura damara ko yayi niyyar bawa yaron ka yarinyar ya janye saboda zaice kai ma baka da halin K'warai Gaskiya banji dad'i ba kuma wannan halayyar da ka nuna itace take sakawa ake zagin mu a gari Dole dai yanzu idan mun tashi daga kasuwa muje mu kara Neman alfarma a gurin shi kuma dole mu bashi hakuri kan abunda kayi masa." Alhaji Tijjani sai yanzu ya fahimci kwabar da yayi tayi ruwa domin ya Riga ya gama fahimtar cewar yarinyar itace kwanciyar hankalin danshi Idan Hankalin Khalid din ba akwance yake ba to suma dole zasu kasance cikin tsananin damuwa da b'acin rai. Don haka sai ya amunce da shawarar da abokin nasa ya bashi. Khalid kuwa sai da ya kusa shanye kwalin sigarin nan sannan ya aje lokaci guda yaji wata irin azababbiyar yunwa ta durar masa wayarsa ya dauka hannu na kyarma ya fara kira numbar Abbakar bugu guda tayi ya dauka a sark'e yace." Abbakar ina Cikin kasuwa a halin yanzu don Allah ka shigo ina son ganinka amma kafin kazo din ka tsaya kayi min take away yunwa nake ji wallahi." Abbakar yace." Insha Allah Yanzu zan shigo." Kashe wayar yayi ya zame ya kwanta kan doguwar kujera lamo yayi gwanin tausayi shi kadai yasan Abunda yake damunsa a lokacin. 30mintus Abbakar ya shigo cikin kasuwar kai tsaye 'b'angaran *Alhaji Tijjani Chanji* ya nufa kamar yanda ya sani idan Khalid din na cikin kasuwar baya zama a ko ina sai ofis dinsu kai tsaye can ya nufa hannunsa rike da wata farar leda mai dauke da tambarin *Nagarta restaurant* knocking yayi Khalid yace." Turo kofar." Abbakar ya bude ya shiga ya mai da kofar ya rufe. Khalid mik'ewa yayi ya zauna yana kallon Abbakar din har ya karaso ya zauna kusa dashi kafadarsa ya dafa tare da fad'in "Yane guy naga kamar duk kana cikin damuwa Allah yasa ba hanifa bace." Ledar hannunsa ya karba ya bude abincin ya dauko ya bude bai jira komai ba ya fara ci Abbakar na kallonsa yana masa dariya sai da ya kammala tukkuna ya kalli Abbakar din a nutse yace." Dama haka sigari take sanya yunwa."!? Abbakar yace." No wandar mana da na shigo naji warinta yau ka karya alk'awarin ka kenan." Dariya yake yana nuna shi.'' Bata fuska yayi yace." Abbakar ya shaik naso ya Dora min ciwo d'azu munje gidan dani da dady anyi babu dad'i tsakaninsa da dady wallahi narasa wane irin mutum ne shi me taurin kan tsiya Abbakar idan Shaik ya'ki ya amunce min da auran yarsa to zan aikata Abunda banyi niyyaba akanta." Abbakar ya sauke ajiyar zuciya tare da fadin"Wallahi idan da nasan abunda zai faru kenan da ban turo maka pictures din nan ba tunda ni a ganina sune sila sau nawa kana ganin yarinya baka taba jin kana sonta ba sai da ka ganta a zahiri ni sai nake ganin kamar sha'awar ta ce take damunka da zaka dauki shawara ta kawai shine kayi kokarin kawar da sha'awar ka a kanta ka k'yale 'yar iska shaid'aniya ni shaidaincin ta ma tsoro yake bani tunda ta rikirkita ka to waye ma bazata rikirkita ba."! Khalid ya sauke zazzafar ajiyar zuciya yace." Ka San ni zina ba halina bane kuma banaso yarinyar taci galaba akaina har ta sanya ni na fara aikata wa akanta mutukar sha'awarta da haddasa min bata bar gangar jikina ba to babu shakka zan dauketa ne mu bar gari idan taki amincewa to dole in kauda sha'awarta da take damuna kaga kenan tayi galaba akaina abunda kwata-kwata bana so na aikata a kanta." Abbakar yace." Kaine kake damun kanka a Kansu run wuri ma da haka kayi da yafi domin nake fada maka Wallahi ya shaik Yayi nisa d'azu na samu labarin duk abunda ya faru bayan tafiyar ku duk kayan abunci da Dady ya zube masa futo dasu yayi ya rabar wa da mutane gidan mu an kai shin kafa buhu guda kaga baya bukatar ka da abunda ya shafeka mutumin mugun taurin Kaine dashi kawai ka aikata abunda kayi niyya tunda ya'ki fahimta." Ajiyar zuciya Khalid din ya sauke tace." Dad yace zasu koma tare da Abokinsa mu bari tukkuna muji da abunda zasu zo dashi." Tab'e baki Abbakar yayi yace." To Allah yasa suzo da alkairi amma nifa jikina na bani babu wani cigaba da za'a samu. Shiru sukayi na kusan minti biyar Khalid yace." Yanzu Abbakar ya za'ayi naga yarinyar." Abbakar yayi shiru yana nazari sai kuma yace." Gobe asabar suna da makaranta kuma kullum sai ta shigo gidanmu sun tafi da kanwat..... Khalid yayi saurin katse shi tare da fad'in"ya za'ayi na dauketa a motata." Murmushi Abbakar yayi yace." Duk wannan me sauki ne zanyi maka kokari." Hannu ya bashi suka tafa yace."Abbakar duk cikin abokina nafi alfahari da kai kana damuwa da damuwa ta." abbakar yace"Guy duk an zama daya bazan taba mance alkairin ka a gare ni ba. Hira suka cigaba da yi irin ta abokai har lokacin tashi daga kasuwa yayi.. *2/1/2020* _BintuUm@rAbb@le_ [1/21, 9:45 PM] BintaUmarAbbale: _MASHAHURI_ *_Mallakar: Binta Umar_* *_Ki biya ki karanta cikin kwanciyar hankali ke kuma da kika futar da book d'in na barki da Allah!_* *08089965176* *07084653262* *0542382124....Binta Umar Gt bank* *38* 'Karfe uku shaura kwata ta futo cikin shirin zuwa makaranta baka ganin komai a jikinta sai kwayar idonta muryar ta a dashe tayiwa Ammi sallama ta futa zuciyarta duk babu dad'i. A nutse take tafiya har ta isa gidansu Asalamiyya tana kokarin shiga Abbakar ya dakatar da ita tsayuwa tayi suna gaisawa sannan tayi yunk'urin shiga cikin gidan ya tare hanya cikin wata irin siga yayi magana "Hanifa kin San kuwa Khalid bashi da lafiya."!? Wata irin fad'uwar gaba ce ta rikito mata take taji miyau na bakinta ya tsinke k'afafunta sun soma rawa abbakar din ta tsurawa ido tana kallonsa. Marairaice fuska yayi yace." Wallahi bashi da lafiya sosai d'azu ya kirani a waya yana kwance ma a asibiti anayi masa 'karin ruwa kuma kin San ko meye dalili."!? Girgiza kanta tayi tana son taji abunda zai fada Yace." Wallahi so da kaunar ki ne ya kwantar dashi Hanifa kiyi wani Abu akai mana Abbu yana nema ya tar watsa muku farin cikin Ku ke da Khalid tunda nasan ke din ma shi kike so ya kamata kiyi wani Abu akan al'amarin nan." Da kyar tace" Ya Abbakar me zanyi akan wannan al'amarin? Tabbas bakayi karya ba ina tsananin sonshi da kaunar shi amma bana jin zan iya bujerewa bukatar mahaifina akanshi zan hak'ura dashi kawai watak'ila ma tarayyar mu dashi babu alkairi." Abbakar yace." Ke kanki kika sani Hany shi kuwa da umm!? Ki duba ki gani soyayyar ki tasa shi har ya kwanta a asibiti ya kamata ki tausaya masa."! Ajiyar zuciya ta sauke muryarta na rawa tace"Ya Abbakar yanzu me kake so nayi masa."? Abbakar ya futo da wayarsa Ashe yayi rocouding lokacin da suke waya da Khalid din, muryarsa ta bayyana lokacin da yake cewa "Abbakar jikina da sauki dai amma Ganinta shine samun nutsuwa ta.""""""!! Tsigar jikinta ta dinga Mik'ewa wani irin kauna da sonsa suka bujiro mata hawayen da take kokarin boyewa sune suke kokarin zubowa murya k'asa-k'asa tace " Abbakar ni makaranta zanje gaskiya babu inda zanje."! Abbakar yayi wani Kalar tausayi dashi yace." Kiyiwa Allah da manzon sa kije gurinsa ya ganki ko ya samu sa'ida wallahi na tabbata da kece a kwance cikin halin da yake ciki da tuni yazo minti goma ma tayi yawa zan dawo dake gida." Shiru tayi tana tunani wata zuciyar tace"kije kawai idan aka futo sallah sai ki shiga makarantar zuwan ki Si baya yana nufin kun amunce masa da auran sa ba. A hankali tace"Ya Abbakar muje mu dawo yanzu wane asibiti ne." Ajiyar zuciya ya sauke yana fadin"Asibitin a cikin gari yake muje mu samu a dai-dai ta sahu." Bayansa tabi suka futa daga soran gidan. Bacci yayi sosai sai kusan uku da kwata Allah ya farkar dashi ya tashi da d'an kuzari a jikinsa zazzab'in ya sauka hakanan ciwon kan da yake damunsa ya ragu Mik'ewa yayi ya shiga toilet din dake cikin dakin sabon brush ya cire a ledar shi ya matsa markilin a jiki bakinsa ya wanke sosai ya dauro alwala ya futo kafin ya tada sallah sai da ya kara kallon agogo dake mak'ale jikin bango sannan ya tada sallah cikin nutsuwa. Bayan ya idar yayi addu'a yanda ya sawwaka Mik'ewa yayi yaje ya dauki wayarshi numbar Abbakar ya kira lokacin suna daf da shiga asibitin Abbakar yace." gamu nan shigowa." A za'ke! Yace." Tare da ita ne."!? Abbakar yace." Insha Allah." Hanifa najin lokacin da ya sauke ajiyar zuciya wacce tasa tsigar jikinta ta cigaba da Mik'ewa. Lumshe idonta tayi tana ji zuciyarta kamar zata tsage saboda fargaba cikin wannan yanayin a dai-dai ta ya sauke su cikin harabar a asibitin Abbakar ya sallame shi suka shiga ciki sosai Hanifa a tsarge take tafiya kanta a kasa har suka shiga abbakar na kokarin kiran wayar Khalid din Dr ya futo daga wani room nan abbakar ya tambaye shi Khalid yace." Muje dakin da yake zan shiga yanzu." Abbakar ya kalli Hanifa da tayo lakwas yace." Muje Hany." Bayansa tabi salau-salau. Yana zaune gefan gado da waya a hannunsa kana kallon fuskarsa zaka fahimci yana cikin damuwa bude kofar da akayi yasa ya dago kansa da sauri aikuwa idanunsu ya sark'e da juna saurin kauda kanta tayi tana jin wani yammmm! Sakamakon kallon k'wayar idonsa a hankali take bin bayan Abbakar har suka isa kusa da gadonsa suna magana da Dr da yake fadin"Ashe ka cire ruwan ma." Cikin yanayin maganar sa yace." Sallah zanyi ne yasa na cire dama kuma ya kare." Dr yace." Ya kake jin jikin naka."? Lumshe idonsa yayi ya bude su maimakon ya sauke su kan Dr da yake tambayar sa sai ya sauke su kanta yana yi mata wani irin kallo mai kashe jiki yace." Dr jiki Alhmdullahi Yanzu zai kara warware wa tunda ya samu abunda yake so." Dr yaso ya fahimci wani Abu shine dalilin da yasa ma ya Dan juyo yana kallon Hanifa ganin ita Khalid din yake kallo Murmushi yayi kawai Dr yaso yaga fuskar yarinyar k'wayar idonta kurrum ya gani ta cikin ni'kab yaji gabansa na fad'uwa babu shakka Yarinyar zata yi kyau dama irinsu ne masu b'oye baiwar da Allah yayi musu. Yana wannan tunanin ya gama abunda yake ya futa. Abbakar ya matso kusa dashi ya bashi hannu suka tafa, Khalid ya nuna Hanifa da baki yana wani munafukin murmushi." Dariya Abbakr yasa yace." Guy gata nan ka sallame ta da wuri ta wuce makaranta domun da kyar na rarrashe ta tazo." Kyataccan murmushi ne a kwance a kyakyawar fuskar sa yace." Abbakar kaje waje zamu gaisa da Quin."! Abbakar yace."ko baka fad'a yanzu zan futa." Cikin dariya yake maganar sannan ya kama hanya zai futa, "Ya Abbakar."! Maganar ta ta dakatar dashi juyo wa yayi yana kallonta, marairaice fuska tayi murya ta na rawa tace" Haka mukayi da kai."? Girgiza kansa yayi yace." Hany Ku gama ina waje ina jiran ki." Futa yayi da sauri har da rufe 'Kofar! Hanifa taji gabanta na wata irin fad'uwa Kwata-kwata bata son su 'ke'be guri guda dashi saboda abunda yayi mata kwanaki tana tsaka da wannan tunanin taji muryarahi mai mugun kashe mata jiki yace." Ki cire wannan abun na fuskarki kizo mu gaisa kizo ki duba jikina kiga yanda soyayyar ki ta mai dani."!!! Shiru tayi gabanta na fad'uwa. "Hanifa."! Ta k'ara jin sautin muryar shi ido ta lumshe a hankali ta bude su gami da kallon inda yake zaune ya wani zuba mata ido, a hankali tace" Sannu ya jikin naka."!? Shiru yayi mata tace"Allah ya sawake yasa kaffara ne." Nan ma bai ce komai ba, ganin kallon da yake mata yayi yawa yasa ta kauda kanta kawai ta kama hanyar futa. Mik'ewa yayi da sauri ya tare gabanta rikitattun idanunsa ya zuba mata ya sanya hannusa guda yana kokarin dauke ni'kab din fuskarta. Da sauri ta kwa'be hannunsa tana 'bata fuska tace" Meye hakane."? Hannunta ya rike cikin nashi ya matse tsam! 'Dumin hannunsa ya sanya taji wani irin yanayi a jikinta kafin ta Ankara taji yana Jan hannunta da sauri ta dawo dai-dai tana kokarin fuzgewa tace"Kana aikata haram fa wai so hauka ne ? Shikkenan don nace INA sonka sai ka dunga kokarin wuce gona da iri."! Cikin wani irin voice yace." Nine ma na wuce gona da iri ashe."!? Dauke kanta tayi tace"Ni dai Yanzu Abbakar ne ya tilastani kan inzo in duba jikin ka wai baka da lafiya nifa yanzu bana bukatar Abunda zai d'agawa mahaifana hankali nice nace ina sonka kuma Yanzu na janye Shikkenan kawai Allah yq hada kowa da rabonsa." Maganganun ta sun bata masa rai sosai yace." Abbakar ne ya tilastaki kizo ki dubani wato da bai tilastaki ba baza kizo ba kenan? Ok kar kiyi tunanin kinci bulus kan masifar da kika jaza min kince kina so kin turo min sufar jikin ki kin hanani nutsuwa da kwamciyar hankali in kwana in wuni cikin tsananin begen ki da sha'awar ki saboda ke din Mara imani ne kiyi min wata maganar banza ra wofi anan gurun, kamar yanda kika haddasa min fitina a rayuwata kema sai na haddasa miki duk Wanda zaki aura sai na hanaki jin dadin rayuwa." Hanifa ta fara kokarin b'oye hawayen ta da yake kokarin zubo mata fuzge ni'kaf din yayi ya jefar dashi a gurin....... Suka kurawa juna ido, Khalid ji yayi tsayuwr tana nema ta gagare shi dama jikinsa babu kwari sosai gashi kuma yaga abincin zuciyarsa sai ya fara kokarin janta nufin sa su isa bakin gado. Hanifa kuwa kokarin dauko ni'kaf dinta take tq d'aura ya hanata kuka tasa masa tana fuzge hannuta kawai sai ya rungumeta yana sauke zazzafar ajiyar zuciya. Tudun Brest dinta suka sanya shi ya kusa suma sai ya hau gogo k'irjinsa a gurin yana wani irin nishi hannunsa ya sanya ya runk'unkume kugunta dai-dai kunnen ta taji muryarshi yana mata wa'ka wacce tasa ta fashe da kukun da bata shirya ba. *"Zuciya ta taki ce."!* *"Ruhina na naki ne."!* *"Nutsuwa ta taki CE."!* *"Gangar jikina naki ne.!"* *"Hanifa ta sace zuciyar Khalid ya shiga yanayi na damuwa."!!!!!"* Wannan sune baitocin da suka mugun kashe mata jiki duk wani karsashi da 'k'warin gwiwar da take ji sai ta neme su ta rasa ta zube a gurin tana gursheken kuka. Kanta tsakanin k'afafunta. Gefan gado ya koma ya zauna fuskar dauke da wani irin murmushi Wanda shi kadai yasan meye ma'anarsa, sosai take kuka bai ce mata komai ba sai da tayi shiru don kanta ta dago kanta tana kallonshi da jajen idanunta, yanayin fuskarsa ya sauya! Yana wani marairaice ido da hannu ya nuna mata kusa dashi wai tazo ta zauna. Da kamar baza taje ba sai kuma ta mike ta kara ta zauna zama tayi kusa dashi shi kuma ya sanya hannu sa ya rungumo kugunta kafad'unsu suka had'a da na juna. A hankali yace." Ya kika ji wa'kar."! Shiru tayi tana lumshe idonta, gefan fuskarsa yake gogo mata a NATA fuskar cikin wani irin salo da ya kusa sata ta zauce yace." Ya Shaik yace yayi miki miji hakane."!? Gyada kanta tayi, yace."Kuma kina sonsa."? Girgiza kanta tayi shiru yayi na minti biyu kafin yace." Wace shawara kika yanke mana." Kamar yanda take wa Ammi shagwaba idan tana magana haka tayi masa magana "Ni ban sani ba."! K'aramin bakinta ya tsurawa ido take yaji wani irin fleeng shawa'ar ya tsots le'bunanta ya taso masa idanunsa ya 'kankantar cikin sigar Jan hankali ya juyo da fuskar ta yana mata wani irin kallo. *5/1/2020* _BintuUm@rAbb@le_ [1/21, 9:45 PM] BintaUmarAbbale: _MASHAHURI_ *_Mallakar: Binta Umar_* *_Ki biya ki karanta cikin kwanciyar hankali ke kuma da kika futar da book d'in na barki da Allah!_* *08089965176* *07084653262* *0542382124....Binta Umar Gt bank* *42* Wani irin lasa yake wa fuskanta da kuncinta har ya gangaro saitin bakinta ya sanya hannunsa biyu ya talfo fuskarta yana kallonta da rikitattaun idonsa Wanda suka sanja kala, le'bunanta ya tsurawa ido yana lashe baki. Harshensa ya futo dashi cikin wata iriyar siga ya fara lasar lebenta na lasa yana Dan ciza ahankali,, idonta ta bude tana kallonsa tayi saurin sunkuyar da kanta gashin idonta ya b'oye halin da take ciki gabanta ne yake dukan uku-uku ganin yanda duk kamanin sa suka sauya kafin ta dawo kauda fuska takeyi tana Dan ture shi yana kara sakar mata nauyin sa, sai wani lumshe idonsa yake yana yi abun irin na tausayi muryarsa a sark'e yace." Ki bani na tsotsi wannan sweet moth naki don Allah kar kice a'a."! Cikin shagwaba ya fad'i maganar wannan salon nasa yana mugun kassara mata jikinta shagala tayi da kallon shi yana wani kashe mata ido kafin tayi wani yun'kuri ya zura bakinsa a nata baiyi wata-wata ba ya sarkafo harshenta da nasa tsotsa yake a haukace! Hanifa ta soma raina kanta ganin yanda Khalid din ya gigice kokarin zare mata siket din atamfar yake jikin na kyarma ya dago ta rungume ta yayi kamar wani mahaukaci ya dauketa cak bedroom d'insa ya nufa da ita aje ta yayi kan bed din Allah ya bata sa'a ta mike tsaye da sauri hannunta jikin zif din siket dinta da ya zuge kokari kawai take taja shi sama amma ya Riga ya burge k'irjinta ta kalla murarar gashinan a waje lokacin tsananin tsoro da fargaba suka shige ta, Khalid ya hau bed din ya jawo kafarta ta fada jikinsa jikinsa na kyarma yace." Beb naga duk kin wani furgice pls babu abunda zanyi miki kawai ina so in ragewa kaina damuwa ne sonki na nema ya kashe ni ki Bari inyi remocing dinki ki taimaka wa me sonki kinji ko."! Girgiza kanta takeyi domin bakinta yayi mata nauyi a lokacin ta Gaza furta komai sai zare ido take tana Neman hanyar gudu..... Khalid ya kalli yanda take tsaye kan bed din nonowan ta suna tsaye carrr! Sai motsi suke sakamakon yanda take motsa jikinta a kid'ime ya mike tsaye shima ya rufe ta da jikinsa manneta yayi jikin bango ya rungume ta tsam-tsam! A k'irjinsa yana sauke wata irin zazzafar ajiyar zuciya kuka ta farayi tana ture shi take fadin"Ka bude min kofa na tafi sau uku kenan kana min irin wannan dabi'ar nifa ba irin wannan son nake maka ba don Allah kar ka cuci me sonka."!!!! Jikinsa ne yayi sanyi kadan ya sassauta rik'on da yayi mata fuskarsa ya sanya dai-dai wunyata yana sauke mata numfashin sa da yake sanya wa tsigar jikinta na tashi cikin rikitacciyar murya yace." Ni bazan cuce ki ba sai dai idan ke ki cuci ni ke da Mahaifin ki, na rasa me nayi masa ya tsane ni idan kinga na kyaleki a gurin nan to sai na biyawa kaina bukata ta." Ido ta zaro cike da tsoro take motsa bakinta domin tarasa ma abunda zatace masa, lumshe idonsa yayi yanayin yanda take motsa bakinta yana kara dilmiyar dashi duk ya wani susuce, Hanifa kuwa addu'a ta farayi cikin zuciyarta take taji wata dauriya tazo mata kallonsa tayi tana harhade fuska tace"Yau na tabbatar ba son Allah da Annabi kake min ba jikina kake so Nagode Allah da ban furtawa mahaifina kai nake so ba, dama Abbu yace ya tsani dabi'unka." Jin abunda tace ransa ya b'aci kallonta yake da fuka a hade yace." Wato har wani mugun hali ne dani kenan. " Dauke kanta tayi tana kare jikinta da d'ankwalin kanta." Tsawa ya buga mata ransa a bace yace." Wane irin mugayen dabi'u ne dani da za'a dunga guduna ne."!? Tsorata tayi ganin yanda idonsa ya karayin jazur! Hawaye take sharewa gabanta na cigaba da fad'uwa! Gyda kansa yayi yaje ya zare key din dake jikin kofa da karfafan taku ya karaso kusa da ita muryarsa sama-sama yace." Bana da ra'ayin nayi wata mu'amula dake da ta wuce romancing amma ina tunanin yau zan nunawa mahaifin ki waye Khalid idan na keta abunda ya Dade yana boyewa sai ya tabbatar da cewa ni din me mugwayen dabi'u ne." Hanifa tace"Khalid kar ka zager min mahaifina ina ganin girman sa kuma duk wani Abu dake tsakanin ka dashi na sani kawai ina nunawa ne kamar ban sani ba ina jin ciwon Abunda kuke wa mahaifina." A tsawace! Yace." Ki rufe min baki a gurin nan ko kuma Yanzu in fasa shi wallahi! Shiru tayi gabanta na fad'uwa ya cigaba da cewa"Ke da mahaifin naki duk baku ishe ni kallo ba idan banda jarabta irin ta so ni me zanyi dake."!? Ya fada yana nuna ta da Hannu.... Cikin jin ciwon abunda yace take kallonsa ya mutsa fuska yayi ya cigaba da cewa"Kece babbar shadainiya wacce ta jefa ni a masifa ina zaman zamana kika turo min da pictures Wanda suka sanya ni na kasa nutsuwa a rayuwata koma menene kece sila ke da Abbu naki da kike karewa babu Wanda ya haifar miki da matsala kamar sa saboda haka dashi zakiyi kuka ba da kowa ba."! Yana gama maganar shi ya fuzgo kafarta ta fad'i kan bed din danne ta yayi gaba daya ya zare siket din jikinta ya jefar ransa a mugun bace yake yana ganin idan bai nunawa Shaik wanene shi ba bazai daina aibatashi ba a duniya. Kuka take tana rokonshi Da yayi hakuri ya k'yaleta kar ya wulakanta ta a duniya yana jinta ya shareta yana cigaba da wasa da sassan jikinta cikin futar hayyaci yake kokarin zura Dan yatsansa cikin headquarter nata ta matse cinyarta tana dukansa a haukace! Ko ina duka take a jikinsa tana kuka tana turje-turje gami da bashi hakuri da kyar ya dago kansa ya zuba mata ido duk tayi wani wujiga-wujiga da ita a sark'e yace." Ina so in nunawa Shaik Mugwayen d'abi'una ne da kin daina kuka kina wahalar da kanki a banza da wofi!" Yana gama maganar sa ya maida kansa kan k'irjinta ya cigaba da abunda yake yi........ Ihu! Ta kurma! "Wayo Allah na! Amminaaa."!!!!!! Da sauri ya dago kansa yana kallonta da jajayen idonsa, wani bahagon mari ta taska masa a kuncin sa tana ture fuskarsa dake kusantota da tata. Murmushi yayi yana shafa inda ta mare shi din cikin narkakkiyar murya yace." Ni kika mara ko."!? "An mareka din Dan iska kurum daga yau na daina sonka kuma Allah sai ya saka min abunda kayi min Wallahi kaci amanar so.! Tana shashshekar kuka ta karasa maganar...... Tausayi ta bashi ganin yanda take kuka duk tayi wujiga-wujiga d'agata yayi yana shafa fuskarsa mamaki yakeyi yanda ya kasa aiwatar da abunda yayi NIYYA akan yarinyar. Hannunsa na kuncin sa still da murmushi a fuskarsa yake kallonta wai yau yarinyar Shaik itace ta mareshi lailai yana cikin taskun rayuwa ta tabbata kenan Ya Shaik shine yayi galaba a kansa. Hanifa a jigace ta dirgo daga bed din ta dauki siket dinta ta zura kofar futa ta nufa kamar zararriya rigarta da take yashe a 'kasa ta dauka ta sanya har yanzu kan nonowan ta zugi suke mata saboda yanda suka sha murza a hannunsa tana kuka ta kama hanya zata futa....... Gabanta ya tare yana mata kallon kasa da sama tayi saurin kauda kanta gabanta na fad'uwa muryarsa taji a hankali yace." Wane irin mataki kika dauka Akan maganar da Mahaifin ki yayi? Kin san Wallahi duk inda kika shiga a fadin du niyar nan sai na zame miki kadangaran bakin tulu gwara ma kije ki fada masa ni kike so."! Muryar ta na rawa tace"ka bud'e min kofa na tafi Allah ya saka min abunda kayi min kaci amanar soyayya." Matse ta yayi jikin kofar ya Dora kansa kan kafadar ta cikin wata irin murya ya fara mata wa'ka kamar haka. *Farin ciki na guda ne."!* *A kanki zan zamma wane* *Kinga hallaya Zane ne* *Shi kuma so rayuwa n!* *Me ladabi hankali ne."!* *Kuma d'abi'un ki sune."!* *Ki zama rurin cida ne....... Kunne yana jinki 'yar uwa.!"* Ajiyar zuciya ta fara saukewa hawaye masu d'umi suka shiga gangaro mata a fuska rungume shi tayi kam! Jikinta na karkarwa shima matse ta yayi a jikinsa sosai ya lumshe idonsa yana Jin yanda zuciyarta take bugawa da k'arfi.! Sai ya da tabbatar da cewa ta samu nutsuwa sannan ya sake ta hannunta ya rike suka futa parlor tare suka zauna kujera daya Hanifa sai share hawaye take tana sauke ajiyar zuciya, cikin yanayin maganar shi yace." Akwai shawarar da na yanke akan al'amarin mu kuma ina fatan zaki bani goyon baya." Shiru tayi batace komai ba ya cigaba da cewa"Idan Shaik ya'ki aminincewa da bukatar mu to cikin biyu za'ayi d'aya ko in gudu dake america muyi auranmu ko kuma muje dake koton musulunci a d'aura mana aure wanne kike ka dauka."!? Girgiza kanta takeyi tana jin wata irin fargaba da tashin hankali jin kalaman sa bata jin zata amunce da daya daga ciki, yace." Ke nake sauraro."? "Nifa babu Wanda na yarda zan aikata cikin maganar ka kawai mu barwa Allah al'amarin." A d'an hasale yace." Ashe karya kike yi kenan son da kike min na karya ne."!?. Girgiza kanta tayi tana matse fuskarta da hannunta. Yace."karya ne mana tunda gashi kinki amincewa da bukatata Wannan shine mafuta a garemu baki d'aya." Ganin yanda ya tsare ta da ido kuma fuskarsa a murtuke tsoro taji kar ya kara kaita d'akinsa ta samu Allah ya kubutar da ita tace"To ka bari zanyi sha'awara.' Ya mutsa fuskarsa yayi yana mata wani irin kallo na zallar sha'awa yace." Dawa zakiyi shawara bayan nine abokin shawarar taki.'' Hannunsa ta rike cikin sigar rarrashi tace"Ba da kowa zanyi sha'awara ba da zuciyata zanyi kayi hakuri insha Allah ni dai kai mutu karaba." Lumshe idonsa yayi yana jin dumin hannunta na shiga jikinsa ya bude idon a hankali ya sauke su kanta, lebansa ya motsa kadan yana so yayi magana kuma sai yayi shiru....... Tsira mata jajeyen idonsa yayi kawai. 'Kasa tayi da nata idon tana addu'a neman rinjaye ta lura dole sai da addu'a ganin yanda. Yake mata a lokacin babu abunda bazai iya aikata mata ba..... Tace ." kayi shiru bakace komai ba." Ajiyar zuciya ya sauke yace." Kin tabbata da maganar da kika fad'a."? Kanta ta d'aga masa.... Hannunsa ya zare daga nata ya fara cire zobon azirfar dake 'karamin yatsan sa, d'an ya tsanta na tsakiya ya kamo ya zura mata zoban ya sumbaci gurin kana ya kalleta tare da I'm promise you ina tare dake har abada Ina so inji haka daga bakin ki." Hanifa tayi shiru tana kallon zobon dake hannunta jikinta duk ya shika ta ma rasa wane tunani zatayi kallon zoben kawai take tana mamakin yanda yayi mata bala'in kyau a hannu. Khalid ya rike Dan ya tsan da zoben yake jiki yana kokarin kaishi baki ya tsotsa tayo saurin fuzge wa tana dan hararasa mik'ewa tayi tsaye shima ya mike da sauri ya rungume ta ta baya, Cikin zuciyarta take fadin"Yau naga jaraba gurin mutumin nan dai-dai kunnenta ya sanya bakinsa a hankali yace." beb kiyi min alk'awarin kinji ko." Kokarin gocewa tayi tace"Nayi maka alk'awari insha Allah. " Sakinta yayi yace." Bari inyi wanka in futo sai in kai ki gida ko." Kafin tace wani Abu ya shige bedroom d'insa da sauri. [1/11, 9:21 AM Zama tayi kan kujera tana sauke ajiyar zuciya wannan al'amari ta rasa ta inda zata fasaltashi a yanzu dai babu wani da namiji da take so kamar ta mutu kamar Khalid din ita kanta tasan idan Abbu yayi ganganci aura mata Nasiru to za'a samu k'atuwar matsala watakila ma zumunci ya lalace domin Sam bata yiwa Nasiru kwatankwacin son da take wa Khalid ko kadan tasan dai tana sonshi irin na 'yan uwanta ka kanta duk ya kulle ta rasa wane tunani zatayi a kan al'amarin amma ta yanke shawarar tunkarar Abbu da maganar dake cikin zuciyarta in yaso ko wace-wace dole shi Ya Nasiru ya janye idan yace ya janye shi Abbu din zai hak'ura shima ya janye da Wannan tunanin ya futo ya same ta, kasa dauke idonta tayi daga kanshi yana sanye da lafiyayyar shaddar geznar milk color anyi masa dinki hannu da bakin zare rigar iya Kacin ta gwiwarsa sai dogon hannu inda yayi amfani da links masu shek'i da daukar ido Hannunsa daure da agogo baki na sallahr fata kana ganinshi kasan zai ja kudi lafiyayyar sumar kamshi tasha gyara sai shek'i take, k'amshin turarashi kuwa tuni ya game parlor har ya karaso kusa da ita ya zauna bata dauke idonta ba, sai da yayi kamar zai tsokane mata idone sannan ta dauke idonta tana Dan ya mutsa fuskarta, Kafadar ta ya rungumo dai-dai saitin kunnen ta yace." Nayi kyau ko."!? Gyada kanta tayi tana sauke ajiyar zuciya! Munafukin murmushi ya saki ya Dan sumbace ta a gefan fuskarta kana yace." Nima kiyi min abunda nayi miki zan kara tabbatar da cewar kwaliyata ta burge ki." Mik'ewa tayi ba tare da tace masa komai ba ta kama hanyar futa, cikin shu'umin kallo yabi bayanta dashi yana shafa sajenshi mik'ewa yayi yaje ya bude mata kofa ta futa ya bi bayanta bai yarda sun jera ba gaba yayi da sauri ya nufi inda motocinsu suke Hanifa ta dinga binsa a baya kamar munafuka sai sinkewa take cikin hijab kafin ta karaso ya bude mata motar ta shiga ciki da sauri, Wanda yayi dai-dai da futowar Mamy tare da Hafiza Cikin shirin zuwa unguwa. Khalid ya sauke ajiyar zuciya yana hamdala ga Allah hijab dinta da ya Dan futo ta kasa yayi sauri ya gyara ya rufe motar da sauri lokacin suka karaso gurin 'bata fuska yake yana 'kara cin kuno domin yasan halin Mamy d'insa da takura wa aikuwa suna karasowa tace"Yawwa Myson Muje ka kaimu gidansu NASIRIN mamanta ce babu lafiya wallahi kaga kaima sai ka duba ta ko."? "A'a Mamy kuje kawai ni Yanzu akwai inda zanje ." yafad'a babu wasa a tare dashi...... Hanifa kuwa kwanciya tayi doguwar kujera gabanta na lugudan duka jin muryar matar da ta zage ta a asibiti tasan mahaifinyar sa ce Muryar Hafiza ta jiyo tana fadin"Au! Don zakaje zance shine zaka ki daukar mu a mota naga sai wani ya mutsa fuska kake kamar zaka dauki kashi.""" Ta k'arashe maganar tana tab'e bakinta. Hararata Yayi baice komai ba yace." Mamy pls kuyi amfani da. wata motar don Allah ni ba hanyar Ku zanyi ba." So yake su matsa daga gurin ya bude motar ya shiga don ma Allah yasa motar me duhun gilashi ce. Mamy tace"To aishikenn da ina cewa ko Kai ma zaka je sai ka gashe ta." "A'a Mamy kuje kawai ni idan na samu lokaci zanje." Ya fada yana shafa siririn sajen sa, Mamy tayi gaba Hafiza tabi bayanta suka bar gurin. Ajiyar zuciya ya sauke ya bude motar da sauri ya shiga ya zauna gurin zaman shi ta mirror ya hangota a kwance sosai ta bashi tausayi da dariya kawai ya girgiza kai hade da kunna motar ya futa daga gidan. *Yanzu aka fara!* *11/1/2020* _BintuUm@rAbb@le_ [1/21, 9:45 PM] BintaUmarAbbale: _MASHAHURI_ *_Mallakar: Binta Umar_* *_Ki biya ki karanta cikin kwanciyar hankali ke kuma da kika futar da book d'in na barki da Allah!_* *08089965176* *07084653262* *0542382124....Binta Umar Gt bank* *39* Kallon da yake mata ya rikita ta sosai jikinta ya soma karkarwa tsoro duk ya shige sai ta fara kokarin k'watar fuskarta da ya rike da hannunsa duk biyun..... Cikin zafin nama ya 'kara juyo da ita da sauri ya had'e bakinsa da nata ya hau tsotsar le'bunanta masu mutukar taushi tsotsar su yake yana lumshe idonsa ita kuma ta rinmtse hakoranta taki bude bakin nata hakan ma da tayi shi yayi masa dai-dai dole idan taji wuya ta bude bakin hannunta ya rike Wanda take faman dukan shi dashi shi ya rike tsam! Ya sanya daya hannun nasa cikin hijab dinta. Gantsarewa tayi tana sakin ihu jin yanda ya dam'kar mata Brest da 'k'arfi yana murzawa... Idanunsa ya bud'e yana kallonta tana zubar sa hawaye har yanzu bakinsa na Cikin nata yayi nasarar kamo harshenta a lokacin ya shiga cikin wani irin yanayi mai mutukar wahala lokacin ne kuma bugun da akeyi wa 'kofar dakin ta tsananta...... Kamar a mafarki ya juyo muryar Mamy d'insa da Hafiza suna kiransa, a kasalance ya zare bakinsa daga nata Hanifa ta samu ta mi'ke a guje cikin gigita take kokarin bude kofa ta futa. Ya tari gabanta ita dashi duk sun wani hargitse kowa sai nuffashi yake saukewa. Kuka takeyi sosai tana fad'in"Allah ya isa ban YAfe ba banza Dan iska wallahi Allah sai ya saka min ."! Kokarin rufe bakinta yakeyi domin yana jin tsoron kar su Mamy suji ita kuma tana ture hannunsa tana kokarin futa duk ta d'imauce. 'Daukar ta yayi cak! Ya nufi toilet da ita ajeta yayi kafin tayi wani yun'kuri ya rufo kofar ya futa. Har Yanzu yana jin muryar Mamy tana kiran sunan sa. Muryarsa a sark'e yace."Mamy ganin fa ina toilet ne." Bude kofar yayi Mamy tace"Myson wai me kake ne tum d'azu a ciki ga abokinka yace ya Dade yana jiran ka." Abbakar ya kalla yayi masa alama da idonsa Abbakar ya bar gurun da sauri. Mamy ta kalleshi sosai cikin nazari tace"Meye naga idanunka duk sun sauya ko dai baka samu kayi bacci ba."!? Sumar kansa ya shafa yana kokarin juya ciki yace."Daga bacci ma na tashi shine na shiga toilet a lokacin ne kuma naji maganar ki."! Dakin suke kokarin shigowa tana fad'in"Ai ga alamanan na gan..... Kafin ta 'karasa suka ji wani irin mahaukacin bugu daga kofar toilet Hanifa nayi tana kuka take fadin"Ka bude min kofa munafuki azzalimi Allah sai ya sakamin Abunda kayi min."!!! 'Kasa yayi da kansa yana jin wani irin takaici Hanifa ta tona musu asiri Shikkenan kuma. Mamy tace"Myson muryar wa nake ji tana kuka a band'aki bude ta ka fada min me tayiwa yarinyar mutane."? Jikinsa babu kwari yaje ya bude kofar Hanifa ta futo kamar zararrariya ta nufi kofar futa. Mamy tace" ke yar nan tsaya kar ki futa zo nan ki fad'a min abunda yayi miki kike masa wannan mugun alkaba'in." Hanifa na juyowa Mamy ta mike tsaye da sauri tana nuna ta da hannu ta tace"Myson me ya kawo wannan yarinyar dakin nan." A hankaliYace." Mamy nine na kawo ta ta duba ni.Tsawa ta buga masa tana fad'in"wato kallon pictures dinta da kakeyi bai isheka ba sai da ka gayyato ta nan don shaid'anci shine take kuka don taji muryar mu zata sauya maganar ina ce d'azu a cikin mota sai da na gargade ka ka rabu da ita ko." Hanifa taji zuciyarta ta kara tsinkewa jin irin maganar da take futowa daga bakin matar da take tunanin mahaifiyarsa ce kunya da taikaci suka sa jikinta yayi sanyin da ta kasa bude kofar ta futa. Mamy ta cigaba da fad'a sosai take fad'in"Idan aure kakeso na fad'a maka kaje ka duba wata yarinyar a gari duk ga sunan masu hankali da kyau masu tarbiya na kawo maka yarinya kintsatsiya kace baka so yanzu Myson me zakayi da yarinyar da take bibbiyar ka babu kamun Kai babu komai." Hafiza tace"Mamy ki bar maganar don Allah, bawai Allah zo ki dauki abunki ki tafi."! Hafiza ta fad'a tana kallon inda Hanifa take tsaye tana kukan takaici Yanzu ta bar kukan abunda Yayi mata tana kukan maganganun da mahaifiyar sa ta fada akanta ne kuma yana ji bai ce komai ba. Jikinta a sanyaye taje ta dauki ni'kaf dinta ta juya Mamy tace"Dakata nan."! Tsayawa tayi ba tare da ta juyo ba. Mamy tace"Ki kama kanki kuma ki sani duk inda ya mace take indai ta cika mace tana tattala mutumcin ta ya kamata ki nutsu ki gane rayuwa ko kya samu Wanda zai aure ki da daraja ina so ki k'yale min yaro hakanan ya huta don Allah kar ki kara shiga ray........" Mamy."!!!! Ya katse ta da muryarsa a sha'ke! Shiru tayi tana kallonsa baice komai ba ya mi'ke yana had'a hanya ya 'karasa inda take tsaye ni'kaf din dake hannunta ya 'kar'ba a hankali ya soma d'aura mata, halin bak'in cikin da take ciki ya hanata hanashi abunda yake mata tsaf ya d'aura mata kamar yanda takeyi ta d'ago idanunta masu cike da gashin ido gazar-gazar ta kalleshi k'walla na shatata shima ita yake kallo yana marairaice mata fuska a hankali yace." Kiyi hakuri kinji ko."! Ba tace masa komai ba tayi gaba da sauri ta bud'e kofar dakin ta futa. Bayanta ya bi da kallo har sai da ta fuce ya juya yana fuskantar su Mamy din fuskarsa a had'e yace." Mamy meye kike yi hakane!? Zaki zubar da 'kimar ki a gurinta tuntuni na fad'a miki cewar yanda kika dauketa ba haka take ba Mamy ban sanki da wannan halin ba don Allah ki daina min haka indai kina son kwamciyar hankalina ki so Abunda nake so." Cikin fusata tace"Myson bafa zanso wannan yarinyar ba da jiki kamar na karuwai Wallahi nasan abunda yake rud'ar ka da Ita kenan Kuma nasan sha'awarta kakeyi ni kuma bazan bari ka aure ta ba domin baza ka za'bawa 'yayan ka uwa Mara tarbiyya ba, wallahi tunda naga pictures dinta na tsane ta." Zama yayi gefen gado ya dafe kansa mamy na nema ta d'ora masa hawan jini Hafiza Tace"Mamy don Allah karki tsawalla akan al'amarin nan daga baya Kuma kizo kiji kunya duk da banga yanayin pictures din da turi masa ba amma ni na tsaya nayi wa yarinyar kallon nutsuwa ina ganin kamar da akwai alamun nutsuwa da kunya a tare da ita maganar pictures kuma ki ajeta gefe indai 'yan matan Yanzu mafi akasarin su haka suke turawa samarinsu pictures dinsu don haka karki damu." Mamy tace"Wannan karon fa bazan yarda ba sai dai duk abunda zakuyi kuyi naga Abu da idona ba nuna min akayi ba kuma kice in Bari ya aure ta."! Khalid cikin jin haushi yace." Wai Mamy zina nayi da ita ne? Kofa zina na aikata da ita shari'a ta yarda na aureta ballanta pictures dinta kawai na kalla idan da Wanda a ga laifi ni ni ne ba ita ba."!!! Mamy ta fara share hawaye tana fad'in"Yanzu ni kake fad'awa wannan maganar har da buga min tsawa kamad wata sa'arka."!? Hankalinsa ne ya tashi yasa ya taso daga inda yake da sauri yaje ya rike k'afafunta yana bata hakuri "Mamy please stop crying, wannan kukan da kikayi zan iya jawo min wata masifar don Allah kiyi shuru muyi magana ta fahimta."! Duk a gigice yake maganar domin kwata-kwata baya kaunar 'b'acin mahaifiyar tasa. Mamy matsar hawaye takeyi taki cewa komai Hafiza tace" Mamy wallahi ni banga abun tada hankali ba a nan ki daina wannan kukan don Allah kar wani ya shigo ya zaci wani abun ne." Tace"Hafiza kina jin abunda yake fadamin kan ina nuna masa abunda ya dace dashi har yana min tsawa kinga kenan ko auranta yayi abunda zai dinga yi min kenan. " Girgiza kansa yayi gami da fad'in"Mamy babu wata mace da zan aura tasa tana wulakanta ki wallahi duk son da nake mata sai na rabu da ita mutukar tace baza ta zauna lafiya dake ba, shiyasa nakeso ki kwantar da hankalin ki akan wannan yarinyar ki cigaba da tayani addu'a idan alkairi ce a tare dani Allah ya mallaka min ita idan kuma babu alkairi Allah ya musanya min da mafi alkairi. " "Dole in kasance cikin yi maka addu'a myson amma ni kam wannan yarinya bata kwanta min ba." Hannunta ya rike yana rarrashinta da kalamai masu sanyi har Dr ya shigo ya salleme shi bayan ya hada masa maganin da zai cigaba da amfani dasu. *** Kanta a 'kasa take tafiya har ta futa daga cikin asibitin taji muryar abbakar yana kiranta kin juyawa tayi ta cigaba da tafiya shima Yanzu wani irin haushin sa take ji tana ganin da be tilasta ta zuwa ba da bata fuskanci Wannan b'acin ran ba. Da sauri ya 'karaso gurin da take tsaye yana yi mata magana taki tanka masa yace."Kiyi hakuri na Dan futo waje ne naga mamanshi tazo da ya yarshi DA fatan dai kunyi gaisuwar arziki." Shiru tayi masa wani mai adao-dai ya tsaya gabansu nan Abbakar ya fada masa inda zai kaisu suka shiga, Abbakar ya nace da tambayar ta abunda ya faru take kuka taki fada masa, Khalid ya kira a waya yana tambayar sa "Wai me akai mata ne gatanan tana ta faman kuka." Khalid yaji wani irin a jikinsa Mamy ya kalla da take draving yace." Abbakar bani ita." Hanifar ya mik'awa wayar taki kar'ba Khalid na juyo shashskar kukanta ya 'kara rikice wa Yace." Abbakar ka bata wayar mana bana son wannan kukan ." Abbakar yace." Taki karba Wallahi." Kamar ya kurma ihu haka yaji muryarsa a shake yace."Kara mata wayar a kunnen ta. " Hafiza ta kalleshi cike da mamaki tace." Wannan wane irin takura ne dole ne sai tayi maka magana.Mamy na driving na girgiza kanta duk abunda yake faruwa tana ji a hankali tace"Rabu dashi Hafiza Yayi yanda yake so a cikin motar nan Na lura iyayen yarinyar nan sun gama dashi domin wannan abunda yake ba na me hankali bane." Dariya Hafiza takeyi k'asa-k'asa shi kuma Khalid na aikin tafka mata harara gefe guda kuma yana ta faman rarrashin Hanifa ta cikin wayar Abbakar din sai kalamai yake zubo mata abun Har mamaki yake bashi. Tunda yake soyayya babu wata 'ya mace da ta taba cin sa'a ya furta mata Kalmar so da bakinsa amma Hanifa ta kwance masa kai Wannan aikin na so ne ko kuma na sha'awa? Shiru tayi tana sauraran wa'kar da yake mata wacce ya 'kirkireta a d'azu sosai kalamsa suka kashe mata jiki sai sauke ajiyar zuciya take yi tana sauraran sanya yar muryarshi da take bala'in so Sai da ya tabbatar da ta daina kukan sannan ya kashe wayar yana sauke ajiyar zuciya gaskiya yaji ciwon irin kalaman da Mamynshi ya ya'ba mata duk Wanda aka muzanta irin wannan dole yaji takaici a zuciyarsa lumshe idonsa yayi yana tunano moment dinsu da ita na d'azu. Mamy da Hafiza kuwa abun ya girmama a gurinsu Hafiza har ta fara jin tausayin Dan uwanta ganin yanda soyayya take nema ta zautar dashi gashi ga dukanin alamu zasu sha fama da Mahaifiyar su tunda ta nuna bata son al'amarin. Hanifa kuwa sai kusan biyar shaura ta shiga makaranta aikuwa malam yakub ya tsada ita yana tambayar ta ." a raunane tace"Malam kayi hakuri don Allah wani Dan uwana ne bashi da lafiya naje na duba shi." Malam Yakub yace." Hanifa da kam kin fi kaunar makaranta amma a 'yan kwanakin nan duk kin shiririce duka wancan satin da ya wuce sau biyu kika shigo makaranta ko meye dalili." Cikin rawar murya tace"Malam wancan satin ni'kab dina ne ya bata Wallahi sai da aka dinka wani don Allah kayi hakuri." Malam yakub yace." Ki shige ciki Yanzu kam sai dai ki tadda saura zan shigo yanzu in karb'i haddar jiya." Gabanta ne ya fad'i jin abunda ya fada simi-simi ta wuce cikin aji Asalamiyya na hangota ta window tazo ta zauna kusa da ita jikinta duk a sanyaye." Asalamiyya tace"Hanifa jikin ki kamshi yake me dad'i wallahi wai ina kika je."!? Shiru tayi mata Asalamiyya tace"Ina fatan kinyi haddar ki ko."!? Wallahi Asalamiyya in banda Yanzu malam yayi min magana na manta." Ta fada tana bude al'kuranin dake hannunta, a lokacin ta bude inda akace su haddace ta fara,cikin ikon Allah ayoyin suka zauna akanta, Malam yakub ya shigo ya karba kamar yanda ya fada lokacin tashi yayi aka tashi Tambayar duniya Asalamiyya tayiwa Hanifa kan a ina ta samo turare me kamshi Hanifa taki fada mata dole tasa Asalamiyya ta hak'ura ta k'yaleta amma itama ta fara zargin wani Abu domin k'amshin turaran kamar ta taba jinshi a jikin mutum d'aya, haka dai suka rabu ko wanne zuciyarsa babu dad'i. Ammi ta ganta ta shigo sukuku kallo ta bita dashi har ta shige daki, ammi ta gyada kanta gami da cigaba da aikinta Hanifa kam uniporm din ta hau cirewa jikinta duk babu kwari har yanzu idan ta tuno abunda ya faru ita da Khalid sai taji fad'uwar gaba idan ta tuno da yanda ya damkar mata Brest sai tsigar jikinta ta kara mik'ewa abunda yake kara rikita idan ta tuno yanda ya dinga tsotsar bakinta sai taji wata irin sha'awar namiji ta kama ta, duguwar Riga ta zura tayi kwance a kan gado Cikin damuwa da jin wani irin azababban fleengs lumshe idonta take tana jin yanda kan nonowan ta suke kumborowa bata taba shiga irin wannan yanayin ba sai wannan karon. Cikin wannan yanayi Ammi ta shigo ta same ta. Ammi na shigowa dakin taji k'amshin turaran itama dake a jikin kyauran kofar shigowa Hanifa ta rataye kayan sai ta jawo hijab din tana sansanawa cike da mamaki take kallon Hanifa da gabanta take wata irin fad'uwa tace"Hanifa wannan turaran a ina kika same shi me k'arfin tsiya."!? A Dan furgice tace"Ammi wane turare ne."!? Ammi tace "Gashinan jikin hijab dinki." Cikin ina_ina tace"Ammi na Asalamiyya ne na fesa nima sai da na fesa nazo ina da nasa ni." Ammi ta zuba mata ido tana kallo tace"Wannan turaran na maza ne Hanifa ki fada min gaskiya." Kuka ta fashe dashi tace"Ammi a ina kike tunanin zan samu turaran maza in shafa a jikina ki yarda da magana ta Ammi." Amma tace"Hanifa bana zargin ki da komai kawai da cikin maganar ki da yanda kike inda inda yasa na fahimci alamun rashin gaskiya a tare dake." Hanifa na kuka tana rantse-rantse na cewar turaran Asalamiyya ne sai da Ammi taga tana Neman futa daga hayyacin ta saboda kuka yasa tace to ta yarda amma daga yau kar ta kara fesa wa domin babu kyau. Daga kanta tayi tana fadin"Insha Allah Ammi bazan karaba Ammi ta futa daga d'akin. Goge fuskarta tayi tana hamdala cikin zuciyarta minti goma da futar Ammi din ta mike tabi bayan ta, aiki ta kama mata suna hira kad'an-kad'an haka Abbu ya shigo gidan ya same su sosai yaji dadin yanda yaga Hanifa ta saki jikinta ba kamar yanda ya futa ya barta ba, ledar hannunsa ta karba shi kuma ya dauki buta ya futa waje domin d'aura alwalar sallahr magariba. *6/1/2020* _BintuUm@rAbb@le_ [1/21, 9:45 PM] BintaUmarAbbale: _MASHAHURI_ *_Mallakar: Binta Umar_* *_Ki biya ki karanta cikin kwanciyar hankali ke kuma da kika futar da book d'in na barki da Allah!_* *08089965176* *07084653262* *0542382124....Binta Umar Gt bank* *33* Abbu na zaune kan dadduma a 'kofar gidansa kamar yanda ya saba zama duk daran duniya idan bai yi zaman karatu ba to akwai wani abu da ya hanashi yanzu ma hannunshi na rike da al'kurani mai girma yana karanta a nutse, Khalid tun kafin su karasa yaji gabansa na fad'uwa daurewa kawai yayi har suka 'karasa kusa dashi sunayi masa sallama. Abbu ya d'ago kansa yana kallonsu dake babu haske sosai a gurin yasa fai fahimci ko su waye ba ya nuna masu kusa dashi alamun su zauna, duk suka cire takalman su suka zauna suna saurarar karatun al'kur'an me girma take suka ji wani irin mutuwar jiki sunkuyar da Kansu sukayi domin yau Ya shaik din yayi musu kwarjini sosai. _Ni kuma cewa nayi ai alk'urani ba abun wasa bane duk taurin kan mutum idan yaji wata ayar sai zuciyarsa ta raunanana! Allah kasa muna daga cikin wa'yanda alk'urani mai girma zai ceta._ Abbu sai da ya kammala surarar da yake kai sannan ya rufe alk'urani ya aje kusa dashi ya juyo da hankalinsa Kansu yana mik'a musu hannu alamun suyi musabaha. Abbakar ne ya fara mik'a nashi sai Mobson Khalid ne a 'karshe. Gyaran murya yayi yace." Samari kunzo d'aukar darasi n.'? Abbakar yace." Eh hakane Ya shaik munzo daukar darasi da kuma wata buk'ata ta a gurin ka." Abba sai yanzu ya fahimci ko su wanene a gabanshi ya gane Abbakar sosai tunda akwai ala'kar arziki tsakaninsa da mahaifinsa fuskokin su Khalid yake kallo take ya gane yaran ikon Allah ya fada cikin zuciyarsa babu abunda ya nuna musu a zahiri yace." To Alhmdullahi Masha Allah kace kunzo daukar darasi banga ku da littatafai ba." Shiru sukayi Kansu a sunkuye, shima Abbu kallonsu yake yi cikin nazari, minti biyar tsakani Khalid ya d'ago kansa suka had'a ido da Abbu yace." Ya shaik kamar yanda ka sanni na sanka tsawon shekaru biyar mukayi wa junanmu farin sani a ido yau ina so in sanar maka da cikkaken sunana shine Khalid Tijjani d'an canji a yanzu nake da shekaru ashirin da takwas a duniya naga yarinyar ka Hanifa naji ina sha'awar auranta wannan shine bukatar da muka zo da ita." Abbu ya jima yana mamakin maganar data futo daga bakin Khalid din tsawon mintuna goma babu Wanda yace komai a cikinsu, Abbu ya sauke ajiyar zuciya yana kallon Khalid din cikin nutsuwa yace." Masha Allah Khalid ko da bakayi min bayanin kai wanene ba dama tuntuni nasan kai d'an waye a cikin unguwar nan sai dai abunda zan fada maka anan shine Hanifa tuntuni nayi mata miji kayi hakuri kaji ko Allah ya baka mace mai daraja irinta ko wacce ta fita."! Khalid yaji kamar ya watsa masa ruwan zafi a jikinsa jin abunda ya fad'a yayi wa yarinyar shi miji waye wannan maiganganci lallai abunda bazai ta'ba amunce wa dashi ba kenan yana gani Hanifa tashi ce shi kad'ai. Abbu ya kalla muryar shi babu sauki yace."Shaik daga dubu daya zuwa miliyan zan iya baka kud'in auran yarinyar ka saboda haka ka maida alk'awarin auran Hanifa kaina domin ni nafi cancanta da in aure ta." Wannan magana tayi mugun 'batawa Abbu rai wato yana nufin kudi zai sa ya siyar masa da Hanifa lallai yau ya 'kara tabbatar da cewar yaron bashi da nutsuwa . kamar yanda Khalid din yayi magana babu wasa a maganar shi, yace." Magana ta farko da k'arshe a tsakanina daku itace kar Ku kara zuwar min da wannan maganar kai!." Ya fada yana nuna Khalid ya cigaba da cewa na Riga nayiwa Hanifa Miji tun tana zanin goyo saboda haka babu Wanda ya isa na janye wannan 'kudirin nawa sai ubangijin da ya hallice ni kudi ko mulki ko sarauta basu isa su saka na janye wannan maganar ba, saboda haka ku tashi Ku bani guri na gama magana."! Mobson ya zaburo! Har ya d'aga hannu zai nuna Shaik domin yayi masa rashin mutumci Khalid din ya buge hannunsa Mobson sai gyda kansa yake yana wani irin huci! Khalid yaji maganganun Abbu kamar ana tsiyaya masa dalma a jikinsa sai zufa yake yi murya a Har hade yace." Yanzu ina son ganin yarinyar taka yaya za'ayi."!? Abbu ya bishi da kallo na rashin fahimta yace." Malam Khaludu bakaji abunda nace maka bane." ? Gyada kai yayi yace." Naji."! Abbu ya mi'ke a nutse ya dauki alk'uranisa yace." Ni zan shiga gida Ku tashi lafiya." Babu Wanda yace. Masa komai Abbu ya shiga gida yana mugun mamakin abun. Khalid Abbakar Mobson shuru sukayi suna sun rasa ta cewa,Mobson ya mike yana zura takalminsa yake fad'in "Wallahi da ka barni da wannan mutumin sai na FASA masa baki har sai yayi jini mu zai fadawa Wannan maganar dama ai tun farko sai da na fada muku mugun d'an akuya ne shi ba yarda zaiyi ba arziki na bishi yana gudu aikin banza kawai! Kai kuma Khalid duk ga mata nan a duniya karasa wa zaka mak'ale wa sai yarshi dole ya wulakanta ka."! Khalid ya mike ransa a dagule ya doki kafadar Mobson din yace." Ka rabu dashi Guy nasan dole sai na fuskanci haka daga gurin shi tuntuni mutumin baya kaunata ni kuma yanzu Allah ya jarrabeni da kaunar yarinyar shi, zan cigaba da binshi a sannu a hankali idan ya'ki amincewa tq dad'i to babu shakka zan nuna masa ruwa ba sa'an kwando bane babban kwanciyar hankalinsa shine ya bani auran sa yarshi data dame ni idan ba haka ba dashi da yarshi sai na 'kunsa musu bakin ciki Wallahi."! Abbakar yace." Guy ka rabu da Hanifa don Allah bafa ita kad'ai ce macace mai kyau ba duk ga mata nan burjik zaka zo nan ana maka wulakanci da kud'in ka da komai." Mobson yace." Nima abunda na gani kenan Khalid jinsu kawai yake yi idan suna cewa ya rabu da Hanifa ji yake ranshi na b'aci shifa baiga dalilin da zai sa ya rabu da ita ba, idan bai aure ta ya kawar da sha'awar ta da take damunsa ba yana jin a rayuwar duniya komai nashi zai tsaya. Haka suka karasa inda yayi parking ya bude ya shiga Mobson ya haye maching d'insa sai mita yakeyi yana zagin Abbu! Shi kuwa Abbakar nacan na tausar zuciyar Khalid kan kawai ya hukura da Hanifa Cikin jin haushi da takaici Khalid din yace." Abbakar ka daina min wannan maganar Shaik da yarinyar sa basu isa su sani cikin masiba ba kuma kace in rabu dasu ban dauki fansa ba, nifa yanzu babu Wanda nake jin haushi irinka domin Kaine duk ka zama silar faruwar komai in da baka turo min pictures din yarinyar ba kaga hankalina a kwance amma saboda da kai da ita duk shaid'anune kuka turo min abunda ya tayar min da hankali ya hanani sukuni a rayuwa Abbakar ka kara cewa na rabu da ita sai ranka ya b'aci."!!! Abbakar yace." Itace shaid'aniya dai tunda ina zamana tazo tace tana sonka dole in taimaka mata akanka ni kuma naga Wannan hanyar itace dai-dai." Wani irin tsaki yaja ya kunna motar shi ba tare da yace wa Abbakar din komai ba ya bar gurin cike da bakin ciki da damuwa! *** Abbu da 'bacin rai ya shiga gida kai tsaye dakinshi ya nufa Ammi tayi bacci tun k'arfe Tara ji yayi bazai iya hak'ura da maganar ba yasa ya tashe ta Ammi ta mike ta futa band'aki ta shiga sannan ta dawo dakin. Motsin Ammi shine ya farkar da Hanifa ta fara jiyo maganar sama-sama. Abbu duk ya fad'awa Ammi abunda yake faruwa, Ammi tace"Gaskiya nima ban bada goyon bayan wannan al'amarin ba, Dole idan Allah ya kaimu a kara Jan kunne Hanifa da ta kiyaye babu ita babu Wannan yaro domin ba tsarin auran ta bane ni Sam ban ma yarda cewar tsakani da Allah yake sonta ba kawai dai akwai munufar sa insha Allah kuma Allah ya fishi." Abbu yace." Idan ba makaranta ba kar ki kara bari ta futa ko ina narasa a ina ya ganta har zai zo mun da wannan maganar." Ammi dai shiru tayi domin tana jin tsoron ta fada masa cewar a gidansu Abbakar ne tasan dole zai tambaye ta cewar dama tasan da maganar kenan shiyasa tayi shiru da bakinta. Hanifa kuwa tunda taji maganar da Abbu yake yi ta mike ta zauna dungurgur gabanta na fad'uwa tana mamakin jin cewar wai MASHAHURI yazo gurin Abbu Neman auranta jin abunda Abbu din yace masa ne yasa taji wasu irin hawaye na kokarin zubo mata kwanciya tayi rigingine tana kuka sosai ita kam dama Abbu yayi hakuri ya aura mata shi domin ita bata son Ya Nasir jin zuciyarta na zafi yasa tq zura hannunta inda ta 'boye pastar shi ta dauko touch light ta kunna ta kurawa fuskarshi ido tana jin sonshi na 'kara yin k'arfi a cikin zuciyarta rungume pastar tayi tana sakin ajiyar zuciya haka bacci ya dauketa **** Khalid kuwa duk ransa a 'bace ya koma gida kai tsaye part din iyayen sa ya nufa komai na duniya yana ji yayi masa daci bai ta'ba tunanin zai shiga irin wannan yanayin ba sai gashi lokaci guda rayuwar shi tana zo ta zama abun kallo kwana da yini babu abunda take tunani sai yarinyar wannan wace irin masifa ce take so ta rufto masa. Alhaji Tijjani na zaune a katafaran parlor nashi yana kallon tashoshin Larabawa Mamy na gefen shi taci Uwar kwalliya kamar ba d'azu suka gama fada ba, shi kanshi Khalid din yayi mamaki shiyasa wani lokacin baya shiga sabgarsu sai su shirya su barshi a ciki. Ya shigo bakinsa dauke da sallama yanayin yanda yake tafiya cikin rashin kuzari yasa iyayen NASA mai da hankalinsu kansa har ya 'karaso ya zube kujerar da take kallon dad din nasa, Alhaji Tijjani yace."Myson yanzu nake zancan ka a zuciyata domin d'azu mukayi waya da senotor yace kunyi magana dashi zakayi wa mai girma shugaban 'kasa wa'ka shine nace Wane irin tanadi yayi maka kafin ka shiga studion kasan dole sai ya zube maka ma'kudan kudi ko."? Dad din nasa ya kalla yana jin sabon b'acin rai kullum yana fad'a masa cewar shi fa ba don kudi yake wa'ka ba kawai ra'ayinsa ce ya rasa ina dad din nasa zai kai kudi bashi da magana sai ta kudi idan da kudi suna magana a jikinsa to tabbas zasuyi a jikinsa domin yana da wasu irin mahaukatan kudi Wanda shi kanshi bai San iya adadinsu ba. A ya mutse yace." Dad nifa duk ba Wannan ne yanzu a gabana ba, a halin yanzu babu wata wa'ka da zan iyayi idan ba burina ne ya cika ba kuma kullum ina fada maka bana yin wa'ka domin a bani kudi dad wa'ka ra'ayina ce kawai." Alhaji Tijjani yace." To ni bazan Bari kud'in nan su wuce ni ba mutukar kayi musu wa'ka kamar yanda suke so zasu turo min kud'in ni ina so." Mamy ta kalleshi da mamaki! Tace" sai ka bari mai wa'kar yayi tukkuna ko." Dariya yayi yana kallon Khalid din da yake ya mutsa fuska cikin damuwa yace." Dad yanzu daga gidansu Hanifa nake naje domin in ganta mahaifinta ya hanani ganinta yana kawo min kauli da ba'adi dad kayi wani Abu akai don Allah."! Alhaji Tijjani ya 'bata fuskarsa tare da fad'in"Wannan wane irin Mara rabo ne kamar ka kazo Neman auran 'yarsa ya tsaya yana shirme myson da alama dai Dan 'k'auye ne ko domin sune basu da hankali. " tab'e baki yayi yace." To waye ya sani dad ni dai abunda na sani kawai cewar shi din d'an Izalah ne gudanshi na gaba da gidan su Abbakar Abokin nan nawa." Alhaji Tijjani ranshi ya 'baci in wai yarinyar da Dan nashi yake so d'iyar d'an Izalah ce kuma 'yar talaka ce saboda duk Wanda yake zaune cikin layin talaka ne sai mutum ya futo sosai zai fara karo da manya manya gidaje, amma baiji dad'i ba da Dan nashi yaje Neman auran 'yar talaka kawai Dan dai baya son b'acin ransa yasa zai kyaleshi ya aurta amma da badon haka ba bai ga ta yanda za'ayi ya had'a hanya da talaka ba. *31/12/2019* _BintuUm@rAbb@le_ [1/21, 9:45 PM] BintaUmarAbbale: _MASHAHURI_ *_Mallakar: Binta Umar_* *_Ki biya ki karanta cikin kwanciyar hankali ke kuma da kika futar da book d'in na barki da Allah!_* *08089965176* *07084653262* *0542382124....Binta Umar Gt bank* *51* Ita kadai ya tadda a parlor tayi tsumu da ita, yace." Ina mamy ta barki ke kadai a zaune."!? Shiru tayi masa kawai tana kallonsa tana kokarin b'oye hawayen ta, yana kokarin hawa sama sai ga dady din zai sauko yace." Yawwa dad dama kai nake jira ka dawo Alhaji Tijjani yace." Dama tunda naga wayarka hankalina yayo gida." Kujera guda suka zauna Khalid ya kalli inda take zaune "My wife zo Ku gaisa da dady kinji ko." Alhaji Tijjani yayi saurin kallon inda Hanifa ke zaune yace"Myson ko itace labarin da zaka bani." Khalid yace." Shine Dady yarinyar Shaik na sona K'warai ta biyo ni inda nake dad ina so gobe idan Allah ya kaimu a d'aura mana aure da ita." Alhaji Tijjani ya fata murmushi yana kallon Hanifa dake sunkuyar da kanta kasa yace." Hak'ika so ba karya bane yarinya kin cika yar halak yau na tabbatar da cewa mahaifin ki shine bashi da ra'ayin aura wa yarona ke shine ya fakaice da cewa yayi miki miji Dan uwanki, kada kiji komai don kin rabu dashi kin dawo gare mu ni zan tsaya miki a kome na rayuwa tunda har kika iya SADAUKAR da farin cikin mahaifin ki akan Khalid nayi alk'awari kula dake har karshen rayuwar ki." Wasu zafafan hawaye ne suka zubo mata ta goge da gefen hijab dinta.....Alhji Tijjani yace." Insha Allah gobe zamu shiga kotin musulunci domin su shaida da abunda yake faruwa na auran Dole da iyayen ki zasu yi miki kuma gaban Alkali zamu baki sadakin ki kamar yanda addini ya tanada al'kali da shaidu zasu shaida d'aurin auranku insha Allah." Muryarta na rawa tace"Dady kayi hakuri don Allah ba sai mun shiga koto ba kwai a d'aura mana aure a gida." Alhaji Tijjani yace." Dole mu shiga koto dake domin ki samu wakilai bayan haka kuma alkali zai iya Neman mahaifin ki domin yaji ta bakin shi Idan kuma bai neme shi ba to dama haka muke so mu." Shiru tayi tana tunanin yanzu ko wane irin halin jama'ar gidansu suke ciki tasan dai yanzu sun fahimci bata gidan tana ji Khalid da mahaifin NASA suna hirar su tayi shiru gwanin tausayi.... **** Hannunsa rike da k'atuwar bak'ar Leda ya shigo Ammi na zaune ita kadai a rumfa yayi sallama ya shigo zama yayi suna kara gaisawa yace"Ammi INA Hanifa ne ga dinkunan nata yaya rabi ta kawo.' Ammi tace"Watak'ila tana sashen su Wasila ka duba ta can." Nasiru ya mike ya futo yaro yasa ya shiga ya duba masa ita minti biyu yaron ya dawo yace batanan." Gurin Inno ya nufa tana kashingide da redio a gabanta yayi sallama amsa tayi yace "Inno Hanifa bata shigo gurin ki ba." Girgiza kanta tayi yana fadin",Wace Hanifa kuwa yarinyar da sai taga dama take Magana duba ta sashen su Wasila" yace duk na dubata banganta ba wallahi." Inno ta mike zaune tana fadin "Ka kara dai dubawa Tana cikin gidanan tunda ba wani gurin ta sani ba balle nace ko taje can." Nasir da jikinsa ya soma sanyi ya futa daga dakin inno yana duba ko INA na cikin gidan sako da loko Hankalin sa ya soma tashi ya koma sashen su Hanifa lokacin itama Ammi ta fito tsakar gida sai sukayi kici'bus yace." Ammi yarinyar nan fa bata cikin gidanan don duk na duba ko ina banganta ba." Ammi bats dauki abun da tsanani ba tace"To ko an aikesu tare da Wasila ne."? Yace." Eto ban sani ba amma bari inshiga in duba da kaina." Sashensu su Waslar ya nufa tun kafin ya karasa shiga ya hango ta tana wanke-wanke karasawa yayi yana tambayarta Hanifa sai da ta gaishe shi sannan tace"Ya Nasiru tun safe rabona da ita dama yanzu nake cewa bari in gama abunda nakeyi na shiga gurins." Bai tsaya ya bata amsa ba ya juya da sauri ya bar gurin...... Ammi na tsaye a inda take ya fada mata komai to itama sai jikinta yayi sanyi tana mamakin ina hanifa zataje garin da batasan mutane ba a ciki.....babban tsakar gidan suka futo suna maganar hankalin kowa ya dawo Kansu Inno ta futo tana salati tare da fadin"kadda yarinyar nan guduwa tayi innalillahi wa'ina ilahi raji'un."! Ammi ma sai ta kama mai-mai ta Kalmar innalillahi wa'ina ilahi raji'un cikin zuciyarta gabanta sai fad'uwa yake.....Maman su Wasila ta baza manya da yara su shiga makota ko ta shiga... Suna tsaye suna mamakin abun yaran suka dawo duk babu wani labari....... Halifa ne ya shigo gidan yana fadin"Nifa dazu misalin goma na safe na ganta ta nufi hanyar titi." Salati suka kama Inno Tace"Ashe tun safe bata cikin gidanan." ? Ammi kuwa tunani takeyi wato tun lokacin da tace mata zata je gurinsu Wasila jin rai dangin goro tun lokacin ta gudu Innalillahi wa'ina ilahi raji'un kawai take maimatawa cikin zuciyarta Inno tace"Maza aje a nemo Haruna duk inda yake." Nasiru yace?" Inno ko baki fada ba kuwa zan nemo shi domin ni shi nafi zarga." Kofar futa ya nufa sukayi kicibus da Harunan ya shigo.. Duk sai jikinsu yayi sanyi Haruna ya maze sosai kamar babu komai yace." Yana kunyi jugum jugum Me ya faru."!? Inno tace"Tun safe ake Neman kafurarar yarinyar nan me siffar Aljani ba a ganta ba don ni har na dauka ko Kaine ka dauke ta jin irin furucin da kayi kwanaki akan lamarin auranta da Nasiru." Haruna yace." Nifa inno bana son irin wannan abunda kike min kawai sai in dauki Hanifa to in kaita ina.? Duk abunda ya faru da ita ai kune kuka jawo tunda dai kun ki Ku hak'ura Ku aura mata Wanda take so waya gayamu Ku ana auran dole a wannan zamanin gashinan kun jawo ta gudu." Inno ta hayayya'ko masa cikin masifa tace"Eh baza mu bari ta auri maro'ki ba domin roko ba gadon mu bane duk inda ta shiga ma zata dawo." Haruna wucewarsa yayi cikin gidan yana mita,.... Inno sai zagin Hanifa takeyi gami da surutai a kanta hankalin kowa na gidan ya tashi mussaman Ammi daurewa kawai takeyi tabbas tasan Hanifa zata iya aikata wannan danyan aikin.... Shiyasa ms bata Musa ba, sunan tsaye suna al'ajabin abun Abbu da Kawu Amadu Hafiz suka shigo dama tun a waje sun samo labarin abunda yake faruwa, Inno na ganinsu ta fashe da kuka tans fadin"Kunga abun kunyar da yarinyar ta jawo mana a gari ko? Ace ana ya gobe d'aurin auranta ta gudu yanzu wane irin kallo jama'ar gari zasuyi mana." Abbu ya jingina jikinsa da bango tabbas abunda Allah ya nuna masa a mafarkin sa ya tabbata shiyasa bai shiga rud'u sosai ba saboda sai da ya jera kwana uku yana mafarkin Hanifa ta gudu ya kalli Inno dake ta faman share hawaye tana surutai yace." inno ki kwantar da hankali don Allah ki bar wannan koke koken duk abunda kika ga ya faru to dama daga Allah ne ni dai fatana duk inda yarinyar nan zata shiga to Allah yasa ta fada a hannu nagari kuma Allah yasa ta gane abunda muke taso mu nusashe da ita Hak'ika Hanifa tayi kuskure kuma ta aikata aikin k'uruciya ina so dani da Ku duka muyi hakuri mu barwa Allah lamarin sa domin yafi mu sanin abunda yake lullub'e insha Allah zai warware mana wannan komai." Inno tace"Munzali duk naji maganarka kuma na gamsu ni babban abunda yake damuna shine maganar d'aurin aure yaya za'ayi jama'a sun sani suna jiran lokaci mun raba goro wannan Abu da akwai kunya Wallahi. " Abbu yace." Baza'a FASA d'aura aure ba insha Allah Shi Nasiru ya duba wata cikin yan matan dake cikin gidanan sai a d'aura masa auran da ita." Inno tace"Insha Allah haka za'ayi." Abbu yana gama maganar sa ya shiga ciki ya barsu suna jajanta al'amarin. To ko da Nasiru yaji maganar da Abbu yayi kan ya zab'i waya cikin dangin yasa yayi shawarar zaben Wasila domin yaga suna yanayi da Hanifa a halin yanzu yana jin ko Hanifar ce ta dawo bazai iya auranta ba saboda zarginta da shiga zuciyarsa, daddare ya Sanar Abbu cewar ya amunce a d'aura masa auran da Wasila Abbu ya dunga sanya masa albarka ita kuwa Ammi daki ta shige taci Ku kanta ta koshi tana jin duk duniyar tayi mata zafi Ashe zata haifi yarinyar da zata iya bujerewa bukatar su ta gudu kan da namiji kuka take sosai Abbu na rarrashinta da fadin addu'a ya kamata tayi wa Hanifar ba kuka ba Ammi tana ji a zuciyarta baza ta taba yafewa Hanifar abunda tayi musu ba. **** 'B'angaran su Khalid kuwa shi da dad dinshi sun gama yanke hukuncin komai Mamy na jinsu duk irin maganganun da take uffan batace ba balle dady din yayi mata cin mutumci abunda tasani shine kawai yarinyar ta jefa kanta cikin matsala ta San halin Khalid irin na mahaifinsa ne zata fuskanci takaicin da namiji tunda ta amunce da bukatar su ita dai yar kallo ce kuma kome zasuyi babu saka hannunta tunda sam-sam tarbiyar yarinyar batayi mata ba ballanta ta tagaza wani Abu kan lamarin ta dai zuba musu ido kawai..... Da tagaji ma da zantukansu sai ta mike ta haye sama abunta... Minti goma tsakani dady shima ya mike ya bar Khalid din da Hanifa gurin da take ya koma nanikar ta yake yana fada mata kalamai masu dad'i ita dai jinsa kawai takeyi jikinta duk yayi sanyi idan ta tuno gida sai wasu hawayen su zubo mata haka ya dunga rikita ta da salon soyayyarsa tas yake lashe hawayen da harshen shi ya rungume ta kam yana lallab'ata dole tasa tayi shuru ganin lamarin NASA yana nema ya wuce gona da iri..... Wani bedroom dake cikin parlor ya shiga da ita zauna da ita yayi kan bed din yana shishshiga jikinta sai wani lumshe ido yake. A hankali tace"Don Allah ka bari kaje ka kwanta nima bacci zanyi." A kasalance yace." Um-um! Ni anan gurin ki zan kwana ina son jin dumin jikin ki." Girgiza kanta tayi gwanin tausayi cikin shagwaba tace"Nifa abunda yake hadani da Kai kenan,, yanzu meye yayi saura gani gaka Insha Allah Idan ka kwantar da hankali nu mallakinka CE, jikina yayi sanyi da irin kallon da Mamy ke min shiyasa banaso kake shige min." Dago kanshi yayi taga ya hade fuska kasa tayi da kanta, yace." Kawai dan rabi jikin ki shine wani Abu wai me yasa kike da duhun kai ne auran ki fa zanyi idan da nayi nufin cutar dake da bazan tsaya kai da fata nace dole sai na aure ki ba zaki dinga fada min maganar banza." Idonta ya kawo ruwa jin maganar da yake mata daga ni a hasale yake. Tace" nifa ban fadi maganar don ta bata maka rai ba kawai nace ka daina ta bamin jiki bana so irin kallon da momy ke min." Tsaki yaja ya mike ya futa daga dakin a fusace! Kallo ta bishi dashi cike da mamaki meye abun daukar zafi a wannan maganar kawai daga ta fada masa abunda ya dace. Lallai akwai aiki a gabanta, kwanciya tayi kamar wata marainiya wata irin yunwa na cinta ga tunanin halin da gida yake ciki haka ta dunga share hawaye har bacci ya dauke ta. *** Misalin 'karfe goma sha biyu na dare yaje ya dauro alwala ya dawo cikin dakin lokacin karfafan bacci ya dauke Ammi da taimakon addu'a da yayi mata dadduma ya shimfid'a ya tada sallah raka biyu yayi yayi sallama kana ya koma sujjada ya Dade yana kwararo addu'a wacce duk rabinta ta hanifa ce da nema mata sauki a duk kanin al'amuranta sannan yana rokon Allah yasa ta fada hannu na K'warai ya kuma juyo da hankalinta gida.... Sosai yake rokon Allah bukata kafin ya dago kansa nan ma ya k'ara daga hannun sama ya dunga kwarara addu'a tsawon mintuna ashirin ya shafa, mik'ewa yayi ya nufi gurin kwanciya zuciyarsa tayi sauki sosai daga damuwar da take, cikin ikon Allah yana kwanciya bacci ya dauke shi. Asubah ta gari Abbu.... **** Wani irin bacci tayi Mara dad'i Wanda yasa ta tashi tsakiyar dare tana kuka Mara sauti cikin wani irin yanayi na damuwa taga Ammin ta abun ya daga mata hankali sosai ga damuwar da ta kwanta da ita na b'acin ran khalid din tana zaune har asubah tayi ta mike taje ta dauro alwala tazo ta tada sallah, addu'a take sosai tana kuka ita kam Yanzu duk kanta ya daure ta rasa meye mafuta a rayuwarta..... Kwanciya tayi kan daddumar bacci ya dauke ta Mai nauyin gaske...... K'arfe goma da rabi ya na safe ya bude dakin ya shiga, ganin ta kwance a kasa tana bacci yasa ya karasa gurin, tsuganawa yayi kusa da ita yans jawo kafarta dake lullub'e da hijab firgigit ta mike zaune ganinshi kusa dai ta yasa ta saki a jiyar zuciya kallonta yake babu walwala yace." Kinyi sallah."!? Daga kanta tayi bata son kallonsa saboda yanayin kayan da suke jikinsa singilet ce fara tas sai boxer duk suffar jikinsa a waje gargasa duk ta rufe masa fata..... Ido ya zuba mata yana kallo, ita kuma sai motsi take da bakinta da kyar tace"Ina kwana."? Ajiyar zuciya ya sauke yace." Lafiya lau kefa." Shiru tayi yace." Kwayar idonki ta nuna min da cewar jiya kin kwana kina kuka hakane ko?". Shiru tayi girgiza kanshi yayi yana sakin murmushi yace." Ki futo Ku gaisa da Mamy sai ki shirya zamu wuce koti yanzu domin ina so ayi komai a gama cikin satinan zamu wuce america tare." Jiki a sanyaye tace." Nifa nace baza ni wani koti ba kawai a d'aura auran a haka." Shan kunu yayi yace." Kina da wakili ne anan."? Shiru tayi yaja tsaki tare da fadin"Na lura kina da taurin kai ni kuma bana so in fad'i magana ana musa wa kawai kiyi abunda nace." Yafad'a yana mik'ewa tsaye..... Hanyar futa ya nufa ta bishi da kallo tana kokarin boye hawayen idonta. Juyo wa yayi yace." Ok baki me nace ba nace kizo Ku gaisa da Mamy kiyi break fast, sai ki shirya ko." Mik'ewa tayi jikinta duk babu kuzari ta biyo bayansa. *20/1/2020* _BintuUm@rAbb@le_ [1/21, 9:45 PM] BintaUmarAbbale: _MASHAHURI_ *_Mallakar: Binta Umar_* *_Ki biya ki karanta cikin kwanciyar hankali ke kuma da kika futar da book d'in na barki da Allah!_* *08089965176* *07084653262* *0542382124....Binta Umar Gt bank* *46* Abbu ya zauna kusa da matar tashi yana tambayar abunda yake faruwa ganin ko da ya shigo din Hanifar bata bar kukan da take ba, Ammi tace"Babu komai Abbu Inno ce ta shigo tana fad'a shine nake 'k'ara ja mata kunne ta kiyaye domin bana son abunda zai jawo min abun magana ko kuma ya shiga tsakanina da mutanan gida nace ta kwantar da hankalinta." Abbu ya sauke ajiyar zuciya tare da fad'in"Halima komai yayi tsanani maganinsa Allah amma ni kam lamarin nan yana damuna Wallahi kullum cikin istahara nake ina jin hankalina na kara kwanciya da auranta da Nasir jiya kuma kafin mu tawo nan din nayi wani irin mafarki akan lamarin hakika mafarkin ya bani tsoro to amma nasan shi mafarki ba gaskiya bane Duk da haka na barwa Allah lamarin ya zama mana abunda yafi alkairi." Ammi tace"Ameen suma ameen bari a kawo abinci Yanzu inno ta ta kawo." Abbu yace." Wannan tsohuwa Allah ya kara mata lafiya ubangji Allah ya ja mana da ranta Hak'ika Tana zumunci Allah ne kawai zai biya ta. " Wasila ce tayi sallama ta shigo yarinya 'yar fara bafulatana kyakyawar gaske kana ganinta zaka gane kamaninsu da Hanifa sai dai Hanifa tafita cika da wayewa da fara'a ta shigo jikinta sanye da uniporm tana fadin"Abbu sannu Ku da zuwa ina makaranta sai Addu'a nake a tashi na dawo gida." Ammi ta saki fuska Tana fadin "Wasila kece kika zama haka."? Hannu tasa ta rufe fuskarta cike da kunya, Abbu na murmushi Yace." Ke ko Halima ai ba yau aka haifeta ba tsakaninsu da Hanifa babu yawa." 'Kwarai kuwa Hakane Hanifa na da wata hudu aka haifeta yanzu shekarunsu goma sha bakwai kenan ." abbu yace." Wasila ya makaranta ina babanki."!? Tace." Abbu yana gurin aiki amma nasan dai yana kan hanya." Abbu yace." Munyi waya dashi muna kan hanya yace yana gurin aiki dama.Wasila ta kalli Hanifa dake takure a gefe guda taki kallonta bare sugaisa 'kawarta ce ita idan sukazo garin ma a sashensu take kwana shashen Baba Amadu kenan Wanda ya kasance kanin Abbu uwa daya uba daya...... Wasila ta mike tana fadin"Hanifa zo muje sashenmu muci abinci." Kamar baza ta mike ba kuma sai ta tashi tana gyara hijab din jikinta suka futa daga dakin. Suna shiga b'angaran su Wasila mamansu ta fara yiwa Hanifa wani irin kallo ita kanta Hanifar ta lura da kallon tsarguwa tayi ta nemi guri ta zauna tana sadda kanta 'kasa tana gaisheta sakin fuska tayi tana amsawa take fadin "Ai d'azu Ashe bamu gaisa ba ko."!? Hanifa ta daga kanta Wasila ta futo daga dakinsu ta sanja kaya tana fadin" mama abinci na kicin ko."! Tace"Ki bude Fula's ki debo muku wainar shinkaface." Futa tayi da sauri, Ita kuma mamansu wasila ta cigaba da kallon Hanifa k'asa-k'asa har sai da ta dago idonta suka hada ido sai kuma ta wayance tana mik'a mata wata roba me fad'i gyada ce a ciki marau tace"Hanifa ci gyada kinji ko." Girgiza kai tayi Alamu bata fi ta fara tsarguwa da irin kallon da take mata, Wasila ta shigo dakin da kwanoni biyu a hannunta ta aje gaban Hanifar ruwa taje ta debo cikin jug ta dawo ita kuma Ummansu futa tayi tsakar gida ta cigaba da hidimar yaranta..... Hanifa cin abincin kawai take badan ranta na so ba Ita kuwa Wasila sai hira take mata wani ta amsa wani ta share sai da suka gama cin abinci ne Wasila tace"Nifa na kagu lokacin bukin Ku da Yaya Nasiru yazo domin nayi tanadi me kyau wallahi shagali zamu sha." Wani irin kallo ta watsa mata kasa daurewa tace"Wasila karki kara yimin wannan maganar kinji ko."! Wasila tace"Saboda me."? Kawai bana so."! Tafad'a ranta a Dan bace! Gyada kai Wasila tayi tace"Yar uwa Wai da gaske ne don Allah abunda nake ji kinfi son bare kan Dan uwanki haba Hanifa meye laifin Nasiru. " *************************⬇********************** ************* Ai Hausa Novels **************** *************************⬆ ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ⬇ ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ⬆ ************************** Tana d'an hararata tace"Wasila idan ke kina sonshi don Allah ki aure shi ni kam bana sonshi akwai Wanda nake so." Wasila tayi shiru tana mamakin maganar Hanifa tace"Dan uwanki ne fa."! A hasale tace"To Dan Dan uwanane kawai sai in cuci kaina wallahi ko an aura minshi sai na bashi wahala sai ya sake ni lokacin da bai shirya ba.... Karaf a kunnen mamansu Wasila sai tayi kamar bata ji ba ta shige daki ta dauko abunda zata dauko ta futo.... Wasila kam mamakin maganar Hanifar take ita a ganinta kamar Nasiru had'addan saurayi wace mace zatace bata sonsa..... Cigaba tayi da cin abinci tana tunanin al'amarin Hanifa tace''idan kina so mu shirya dake to Kar ki kara yimin irin wannan maganar ni yanzu mafuta kawai nake nema." Wasila tace "na daina Insha Allah amma zan tayaki da addu'a Allah yq zama miki abunda yafi alkairi." Ameen tace tana jin zuciyarta tayi Dan yi sanyi suka cigaba da hirarar yan uwansu. **** Da kyar ya Kai kanshi gida cikin wani irin hali ya shiga parlor Mamy na zaune tare da Momy Nasrin da ita kanta Nasrin din suna hira Mamy ta mike da sauri ganin yanda ya shigo mata kamar zai fad'i ga bakinsa duk ya bushe idonsa ya kada yayi jazur. Hannunsa ta rike cikin damuwa take fadin"Myson yanzunan nagama kiran wayarka bata shiga ba wai ina kajene nifa bana son abunda zai tayar min da hankali myson wannan wace irin rayuwa ce ka jefa kanka ciki umm!? Yarinyar nan wai ita kadai CE mace a duniya."!? Mamy ta karasa maganar cikin damuwa...... Da kyar ya iya furta maganar "Mamy ba ita kadai bace hasali ma akwai wad'anda suka fita komai na rayuwa narasa abunda yasa zuciyata ta nace mata Mamy wai ko mayya ce ne."!!!! Ya fadin maganar Cikin sarewa da kuma gajiyawa da al'amarin kana ganinshi zaka fuskanci yana cikin damuwa me tsanani." Mamy tace"To waye ya sani myson muje ka zauna." Ta kama hannunsa suka nufi kujera tana fadin "Mutane ne kawai an gansu a unguwa ba'asan daga ina suke ba ni kam Allah yasa yarinyar bata lashe maka kurwa ba."! Ta fada cikin damuwa. Zama yayi yana kallon su Dishi-dishi Nasrin yake kallo da mamanta yace." Mamy wacece wannan."!? Momy Nasrin ta dafe k'irjinta cike da mamaki tace"Ni din ka manta Khalid."!? Nasrin ya kalla wacce ta zuba masa ido tana kallonsa cike da so da kauna yace." Mamy wannan yarinyar ma ban Santa ba."! Hajiya Zainab tayi salati tana Sanar da ubangji tace"Anya kuwa yaron nan na cikin hayyacin sa kuwa."!? Mamy kam hawaye ta fara sharewa tana fadin"To waye ya sani ko yarinyar nan ta kashe masa kurwa innalillahi wa'ina ilahi raji'un.! " Mamy ta fada da wasu hawaye na zubo mata domin abunda Khalid din yake yi kamar wani Mara hankali....... Lokacin da yaga Mamy na kuka ne ya dawo hankalinsa ya tsani yaga Tana kuka tamvayarta yake meye take kuka."!? Hakan ma sai ya kara daga mata hankali jiki na kyarma ta dauki wayarta ta fara Neman numbar mijin nata tana ganin gwara yazo suje a duba kwakwalar Khalid kwr abu yayi nisa bugu guda tayi ya dauka bakinta na rawa ta fada abunda yake faruwa cikin rashin hakuri irin nasa ya rufe ta da masifa kamar yanda ya saba kashe wayar tayi ta zauna tana kallon Khalid din da yake kallonta fuskarsa a Dan hade yace." Mamy wai meye naga kina ta wata magana Don nace bangane Momy Zainab shine kika tayar da hankali, nifa ina cikin hankali itama Nasrin din na ganeta yanzu."! Mamy shiru tayi masa kawai suka cigaba da hira da Kawarta mik'ewa yayi ya futa daga parlor yana jin damuwa cikin ransa shi har ga Allah bai San sanda yayi maganar cewa bai gane su ba amma yaga mamy ta dauki maganar da muhimamci Why!! Soyayyar da yakewa yarinyar Shaik tana nema ta mai dashi zautace yanzu ya fara tunanin wannan abunda yakeyi sone ko kuma sha'awa."? Allah ne ya barwa kansa sani.......... Yana kokarin shiga toilet ne Nasirin ta shigo dakin nasa kayan da suke jikinta suk futo mata da suffarta domin ita tana da wadatar nono amma basu kai girman na Hanifa ba kuma tana da garun jiki irin na hanifa sai dai tsarin jiki me kyau Hanifa tafi ta..... Tsura mata ido yayi tun kafin ta karaso gurinsa kasa tantace wacece yayi domin idanunsa sai suke masa gizo yana ganin kamar Hanifa ce ta dawo wata zuciyar tace itace watak'ila ta gudarwa iyayenta ne, murmushi yake saki har Nasrin ta karasa kusa dashi kafin ta Ankara ya kai mata wawuyar runguma ya matseta tsam! A jikinsa yana sauke ajiyar zuciya lasar fatar wuyanta yake yana kokarin zuge mata zif! Din rigarta.... Nasrin ta gigice tana ture shi daga jikinta a gigice ya kwantar da ita kan bed din ya haye kanta bakinta yake kokarin kamawa yasa ana shi Nasir kuwa yanda tayi laushin fatar jikinsa da yanzu gashin k'irjinsa yake tsikarar jikinta dake yana daure da towol ne iya cinya sai ta fara lanjarewa tana sakar masa jiki da kanta ta kamo bakinsa ta ta fara kiss dinsa Lokacin da ya fara tsotsar bakin nata ne yaji ba irin test din su daya da Wanda ya saba tsotsa ba wancan yayi laushi yafi sugar da Zuma idonsa ya bude Wanda suka kada suka juye suka zama kamar na mashayi ya zubasu kanta, Nasrin ya gani tana ta kokarin mai da bakinsa nata, yayi saurin mik'ewa yana gyara towol dinshi Dan bata fuska yayi yana kallonta ita kuma tana kallon faffadan k'irjinsa me sanya mata haukacewa mik'ewa tayi zaune yace." Ke dama bake bace. "!? NASIRIN ta bata fuska tana fadin" Bangane ba." ? Sosa kansa yayi yace." Owk na dauka fa ita sorry bari inyi wanka in futo kinji ko."! Hanifa taji kamar ta kurma ihu! Lallai ma guy nan wato da bai ganeta ba shiyasa ya rungume ya dauka budurwarsa ce take taji wani irin masifar kishin Hanifa ya dura a zuciyarta. Wanka Yayi ya futo a gurguje tsaye Yayi gaban dressing mirror dinshi yw gama shafe-shafensa NASIRIN na zaune tana kallonsa ko kunya babu sai kallonta yake ta mudibin yana mamakinta bayan ya dauko kayan shi ne ya nufi wani kebantaccan guri ya shirya tsaf ya futo har ya karaso tana kallonsa kusa da ita ya zauna yana lakuce mata hanci yace." 'Yar lukuta taga had'addan guy ta gigice wai yane."!? Bata fuska tayi domin yanzu ba Lokacin wasa bane tace." Khalid naji kanayi min wata magana wai har ka manta da alk'awarin da kayi min ne."!? Dan kallonta yayi ya dauke kansa yana d'aura a gogo a hannunsa Yace. " wane al'akawari nayi miki 'yar lukuta."!? Hummm! Naga kamar kana nema ka manta ne idan kai ka manta ni ban manta ba karfa ka manta Kaine ka koya min yanda zan soka tun ina yarinya kankanuwa zuciya ta makance akan sonka na tafi karatu da soyayyar ka bayan kayi min alk'awarin aure na amma sai na samu labarin gurin Momyna wai ka ma manta dani."!! Ido ya Dan zaro yana kallonta da mamaki yace." Ni ne nayi miki alk'awari kuma yaushe bana son tsari."!! Kuka tasa tace"watarana da kazo gidanmu idan parlor mu na magana zai fada maka wallahi kayi min alk'awari zaka aure ni." Dariya yasa yana nuna ta da hannu yace." Mybe Lokacin kin dame ni da rigima ne kin San fa a lokacin ni kamar tom and jerry nake kallon ki in kina wani shirmen inyi dariya in more gaji yar lukuta ni kam ban miki alk'awarin aure ba ko nayi ma to wasa nake miki." Cikin kuka tace"Kar muyi haka da kai Khalid Wallahi INA sonka kar ka yarda wata ta shiga tsakaninmu." 'Bata fuska Yayi da damuwa yace." Ai maganar wata ma ki aje gefe ta shiga tsakanina da kowace mace ciki kuwa harda ke ni ko ina jin mayya na had'u da ita ban sani ba."! Da damuwa ya fadi maganar." Nasirin tace"Don Allah ka rabu da wannan yar talakwan Wallahi ba ajinka bace." Kafin ya bata amsa wayar shi tayi k'ara yana dubawa yaga no dad dinshi dauka yayi da sallama a bakinsa, Ya mike da sauri yana fadin"Dady ganinan futowa." Nasirin ta mike tabi bayanshi suka futa tare.............. *15/1/2020* _BintuUm@rAbb@le_ [1/21, 9:45 PM] BintaUmarAbbale: _MASHAHURI_ *_Mallakar: Binta Umar_* *_Ki biya ki karanta cikin kwanciyar hankali ke kuma da kika futar da book d'in na barki da Allah!_* *08089965176* *07084653262* *0542382124....Binta Umar Gt bank* *45* Tunda ya tashi yake jin rashin k'arfin jiki haka dai ya daure ya karya Mamy nayi ta masa labarin Nasirin duk a kokarin ta na ta janye hankalinsa kanta shi kuwa yana can tunanin Hanifa ya kwana shida kenan Rabonsa da ita, take yaji yana sha'awar ganinta wayarsa ya dauka dake aje kusa dashi sai a lokacin ma ya tuna bai kunnata ba kunnawa Yayi ya fara neman no Abbakar bugu daya tayi ya dauka Yana fad'in "Guy gamu nan nida Mobson mun shigo unguwar taku." Khalid yace." Meye ne naji muryarka a sama."!? Abbakar yace." Tun d'azu nake kiran wayarka amma aka she babu lafiya Ya shaik ya tattara iyalinsa sun bar gari."! Khalid ya mike tsaye da sauri! Saura kad'an ya fad'i"Hannunsa na kyarma yake fad'in"Da gaske kake Abbakar."!? Abbakar yace." Wallahi a gaban idona suka nufi tasha ni ban San abunda yake faruwa ba kawai sai gani nayi yara da manya sun cika a waje suna kallonsu irin surutun da suke yi ne ma na fahimci abunda yake faruwa." Jiki ka kyarma yake kokarin futa. Mamy tace." Ina zakaje ne Myson wai me akace maka ne naga duk ka gigice. "! Waiwayo wa yayi muryarsa na rawa yace." Mamy wai Shaik ne ya gudu daga gari saboda ni, bai sai duk inda zai shiga a fadin duniyar nan sai na binkito su Wallahi bai isa ba." Mamy ta mi'ke da sauri tana kokarin kamo shi ganin yanda jikinsa yake tsuma sai abun ya bata tsoro ta wani gefen kuma taji dadin hakan amma kuma yanda taga ya tada hankalinsa yasa take jin tsoron kar ya fad'i irin ranan..... Kokarin rike hannunsa take ya fuzge da k'arfi ya futa bayansa ta bi taga ya nufi ma'adanar motocinsu ya shiga da sauri yake kokarin futa tsaye tayi a bakin kofa tana yi masa addu'a tsari. Yana futa mashing dinsu Abbakar na shigowa layin kawai sai ya tsayar da motar sukayi parking din mashing din a gefe guda dake unguwar GRA ne akwai tsaro sosai shiyasa Mobson bai damu ba suka shifa motar Khalid din da gudu yaja suka bar gurin. Sai da suka hau kwalta sosai Khalid din ya kalli Abbakar murya a sanyaye yace." Wane gari ne ma."? Abbakar yace." Gombe ne.'''''' Muryarsa na rawa yace." Muje tasha ko zamu same su." Mobson yace." Guy ka nutsu mana naga sai wani rawar jiki kake yi yanzu idan mukaje tasha kuma muka Tarar basu tashi muce musu me? Bamu fa da hurumin da zamu hanasu tafiya."! Gefen titi ya tsaki da motar ya d'ora hannunsa akansa kusan minti biyar babu Wanda yace komai ya d'ago kansa idanunsa har sun sauya kala yace." Mobson kaina duk ya kulle Wallahi meye mafuta ne."!? Mobson yace." Baka da wata mafuta guy dama da dai mun riskisu ne to zamu iya rusa tafiyar idan muka ja hankalin yarinyar yanzu kuwa ko munje gombe bamu San wace unguwa suke ba kawai zamu wahalar da kanmu ne." Khalid ya daki! Kan mota da 'karfi! Muryarsa a sama! Yace." Mobson bafa Zan k'yale yarinyar nan ba sai na biyawa kaina bukata Wallahi. " Mobson ya d'anyi dariya tare da dukan kafad'unsa yace." Guy Kaine ka tsaya wasa Wallahi wai dole ne sai ka aure ta sannan zaka biya bukatar ka wace irin damace baka samu a kanta ba kawai ka zuba ido kana kallonta ni Wallahi ma haushi ka bani gashinan Yanzu sunyi ciki dai sun Barka da cizon yatsa."! Mobson ya k'arashe maganar cikin jikn ciwon abunda Khalid din yayi......Abbakar yace." Guyz ina ganin abunda yafi kamata muyi kawai mu koma gida mu shirya shawarar me za'ayi zan shiga gida in d'an bubbigi cikin babarmu insha Allah zata 'karamin haske Kansu domin ita mahaifiyar Hanifar suna mutumci watak'ila ma tasan ko a wace unguwa take a garin gombe."! Jin abunda Abbakar din yace." Yasa Khalid din ya sauke ajiyar zuciya babu yanda ya iya ya juya kan motar suka nufi gida sai yanzu yake takaicin rashin bawa Hanifa waya yasan yanda take sonshi zata fad'a masa komai shi kuma ya dauki mataki. Shagon mobson suka yada zango Khalid ya kwanta kan katifa kamar wani maraya lumshe idonsa yayi yana jin wani irin zafi cikin zuciyarsa babu shakka Shaik ya shammace shi, juyi yayi hade da lumshe ido yana tunano suffofin jikin Hanifa da ya tuno lafiyayyar fatar jikinta da k'irjinta ya saki nishi tare da kankame pillo yana cije bakinsa, shi kadai yake wannan budurin a shagon lokacin Mobson ya tafi yi musu take awaye shi kuma Abbakar ya shiga gida gurin babarsu yana bugun cikinta kamar yanda ya fad'a. "Wai kai me yasa ka damu da sanin ko a wace unguwa suke ne."? Babar tasu ta fad'a tana kallonsa cikin tuhuma."! Shafa kansa yayi yana 'yar dariya yace." Umma ai ko babu komai anyi zaman mutumci kuma kinga watarana zamu iya kai musu ziyara." Asalamiyya tace"E wallahi Ya Abbakar in zakaje kaje dani. Yace." Ki bari tukkuna mu San unguwar sai muje Insha Allah. " Babar tasu ta kalleshi a nutse tace"Ni kam ban San unguwar da suke ba a gombe nasan dai 'yan garin ne amma duk zaman da mukayi da Halima ban taba tambayar ta wace unguwa suke ba." Abbakar yaji kamar ya kurma ihu! Shifa ganin tayi shiru tana tunani sai yake ganin kamar zata fad'a masa ne. Futa yayi daga gidan yana Jan tsaki! Shagon mobson ya nufa ya tadda Khalid din yana mur'kususu a kan Katifa, jajaen idanunsa ya dago dasu yana kallonsa Abbakar sai yaji shakkar fad'a masa abunda yake faruwa ya mike zaune da kyar muryarsa a har had'e yace." Meye labari Abbakar ina fatan ta fad'a maka wace unguwa ne yau din nan zamu dauki hanya. " Abbakar yace." Wallahi tace bata sani ba."! Khalid ya sunkuyar da kansa yana jin wani irin takaici duk ya shiga damuwa cikin wannan halin Mobson ya shigo ya same su, zama yayi yana bude abinci yake fadin"Ku bari in gama cin abinci akwai shawarar dana yanke insha Allah. " Shuru sukayi Mobson ya fara cin abincin sa hankali kwance sai gyada kansa yake da'alama yana jin dad'i wa'kar da yake ji ya Cikin eirpiz dinsa Khalid duk haushin sa ya kamashi ganin yanda yake walwala yasa ya buga matsa tsawa "Wai meye Hakane ? Mutane na Cikin bakin ciki kai kana wani gyada kai babu abunda ya dame ka, ka San halin da nake ciki kuwa."!? Mobson yace." To ya kake so nayi? Aini babu Wanda nake jin haushi irinka da ka samu dama kaki ka dama Ya shaik din banza wallahi kana da damar da zaka biyawa kanka bukata da yarinyar ba tare da kowa ya tuhumeka ba tunda ita ke kawo kanta gurinka amma ka tsaya kabawa Gayu kunya mtssssss."! Khalid ya rintse idonsa cikin damuwa Yace. " Guy nima sai yanzu na gane na tafka kuskure da ban nunawa Shaik din ni waye ba har sai da ya samu galaba a kaina amma babu komai zamu sake haduwa ne, kawai kayi ka fad'amin me zanyi Yanzu kaina duk ya kulle wallahi." Abbakar ya dauki leda guda ya futo da take away din ya bude ya fara ci yana kurbar Lemo Khalid ya dunga binsu da kallo Cikin mamaki wato su abinci ma suke ci babu abunda ya dame su Kansa ya dafe yana sauke ajiyar zuciya. Mobson ya goge bakinsa da tissue ya kalli Khalid da kansa yake a sunkuye yace." Guy abunda za'ayi kawai kazo mu shiga studio yanzu ka ragargaji Shaik ka shirya masa wa'ka ta tozarci kan rabaka da yarinyar sa da yayi nasan wa'kar ka babu inda bazata shiga ba INA ganin idan kayi haka jama'ar gari zasuyi tur dashi kuma ko a garin nasu nasan kowa zaiga laifin sa ita kuma Hanifar hankalinta zai tashi nasan a lokacin zata kara rikice musu da koke koke to ina mai tabbatar maka ta dalilin wannan wa'kar da kayi zaka samu mutane masu kiranka a waya dayi maka jaje insha Allah zaka samu Wanda zai ce maka ya sansu yasan a unguwar da suke, ina fatan ka fahimce Ni. " Khalid yayi shiru yana nazarin maganar Abbakar yace."Gaskiya Mobson kwakwalwarka tana ja sosai wannan shawara tayi kyau nasan daga zuwa gobe da jibi wa'kar nan ta futa to zata watsu a gari har taje garin da suke Khalid yana da masoya sosai dole za'a samu wannan zaice yasan asalin Shaik din kaga sai mubi ta kanshi kawai......Ajiyar zuciya ya sauke ya Dan samu sassauci a zuciyarsa yana ganin wannan ma damace yace." Ku tashi muje." Mobson yace." Ka zauna kaci abinci tukkuna." Wani irin kallo ya watsa masa Mobson ya mike da sauri yana dariya suka fuce daga shagon. ***** Kuka 'k'asa-k'asa takeyi cikin motar tabi ta takure kanta gefe guda saboda tsabar kukan da takeyi kanta sai wani irin ciwo yake mata, tana jin yanda suka sake suke ta hira abunsu babu Wanda ya damu da ita Ammi ma Sam bata so su hada ido, sai take ganin kamar rayuwarta tazo karshe tunda kowa ya juya mata baya sun kasa fahimtar halin damuwar da take ciki kuka takeyi zuciyarta nayi mata wani irin zafi lokacin addu'a takeyi kan Allah ya dauki ranta ta huta da wannan masifar da take ji cikin zuciyarta Haka suka isa garin nasu na gado...'yan uwa da abokanan arziki sun tarbe su kowa sai murna yakeyi haka suka nufi family house d'insu Wanda ya kasance babban gida na b'angare-bangare dama tuni an gyara musu shashensu sai suka dunga shiga da kayansi ciki Hanifa kan rakubewa tayi a gefe tana kallon yanda yan uwa suke ta kai kawo wasu daga cikin su fad'i suke sunji dad'i da Abbu din ya dawo gida tare da iyalinsa k'aton daki ne ciki da rumfa sai tsakar gida mai dai-dai ci da kicin da band'aki wadatattu ko ina an shafe shi da sabon fainti cikin dakunan kuma Leda ce sabuwa dal da sabuwar katifa da labulaye sai agogon bango dake mak'ale a bangon daki.... Dakin sai k'amshin turaran wuta yake Ammi ts shisshigar musu da jakar kayansu ciki ta futo tana duba gidan mamaki take sosai ganin yanda yan uwanta suka siya mata komai na bukata kicin din sabbin tukwane ne da saitin Fula's har guda uku kai duk dai abunda zata bukata gurin girki da akwai shi hawaye ta share tana godewa Allah da ya bata yan uwa masu zumunci Inno ce ta shigo ita da wani yaro a bayanta hannunsa da dauke da k'aton faranti Jere da kayan abinci ta Kalli Hanifa dake rakube a gefe tace"Ke kuwa wannan yarinya anyi me bakin hali kowa yana murna ya shigo cikin yan uwa ke kin zauna kina nukufurci." Hanifa ta sunkuyar da kanta kasa tana turo baki Inno ta cigaba da cewa"Kafura me wata irin suffa a fili kamar mutuniyar arziki amma a zuciya sharrin ki yafi na wata babbar macan yarinya k'arama dake kike kokarin zubar mana da mutumci." Ammi ta futo daga kicin tana fadin"Inno sannu."! Kallonta tayi tace"Inanan ni dai wannan 'yar taku me kai kamar na goriba ai wallahi naso Munzali ya karya mata k'afafun da take bi gurin saurayi." Cike da mamaki Ammi take kallonta tana tunanin a'ina taji maganar. Domin taji ribar zancan tace"Allah dai ya kyauta Inno shigo daga ciki mana." Tab'e baki tayi tace"A'a ni dama abinci na shigo na kawo muku in juya b'acin ran wannan yarinya yasa ni na tsaya dama kuma yanzu Nasiru ya futa daga gurina duk ya zayyane min abunda ya faru wato itace ma tayi silar sawowarku cikin dangi Ashe."!? Ammi tace"Sai addu'a al'amarin Inno yanzu dai magana ta wuce mu Baro garin da yaron yake kinga Dole ta hak'ura." Inno tayi k'wafa tare da fadin"Karma ta hak'ura auranta da Nasiru tabbatacce ne da yardar Allah."! Kofar futa tana nufa tana mita.... Inno dai matar Kawu Yahya ce Kawun da ya ragewa Su Abbu kenan macace mai masifar fad'a bak'ar magana hakanan surikanta da suke cikin gidan suke hakuri da haleyenta yanzu ma da shekaru suka kara yi mata yawa abun sai ya kara yin tsayi amma kuma tana da kirki da zumunci, kome ya fari tana tsaye kan lamarin mutum, tana jin Munzali wato Abbu cikin ranta sosai saboda yana mata biyayya kuma yana bukata mata ko da suke kano idan yayo aike ita ke rabawa yan uwa shiyasa take ji kamar itace ta haife shi...... Ammi daki ta shige tana mamakin abunda Nasiru yayi yanzu meye amfanin fad'ar maganar a ganinta idan ya sirrinta asirrin matarsa kansa ya rufawa asiri tunda shine zai aureta bai kamata ya futo da maganar ba ta Dade sosai maganar na damunta kuma ranta ya b'aci yasa ta daga murya ta kira Hanifa dake zaune ita kadai a tsakar gida.... Simi-simi ta shigo cikin dakin kanta a kasa ta zauna gefan ta, Ammi ta jima tana kallonta tausayi ta bata ganin yanda Duk ta furgice tace"Hanifa ki nutsu zamuyi magana ta k'arshe dani da ke." Tace. " INA jinki Ammi." Ajiyar zuciya ta sauke kafin tace "Kin San dai nan da inda muka taso na daya bane ko."!? Hanifa tayi shiru tana sauraronta Ammi ta cigaba da cewa " To ki nutsu ki dawo hankalin ki nan kina cikin 'yan uwa ne gaba da baya kar ki manta nan shine tushe na dani da Mahaifin ki haka kazalika kuma ke shine tushen ki Saboda haka INA so ki watsar da Duk wani Abu da kika tawo dashi garinan maganar wannan yaron da kike so an wuce ta har abada babu ke babe shi, Ubanki ya zama miki miji to kiyi biyayya ki aure shi ki zauna dashi lafiya kar inji Kar ingani mutukar kikayi wani abun batanci a garin nan to mu zaki zubarwa da mutumci saboda haka kiyi kokari ki bamu hakkin mu da Allah ya umarce ki dashi." Tana kuka tace"To Ammi nima ki tayani addu....... Bata karasa ba kuka ya ci karfinta ta kwanta a gurin tana yi zuciyarta kamar ts tsage wato dai ta tabbata an rabata da masoyinta Khalid... Cikin wannan hali Abbu da Hafiz suka shigo suka same ta lokacin shi Nasiru ya tafi gidansu. ***** Wani irin sauti ne yake tashi kad'an-kad'an kana jinsa zaka ji wani irin imani da tausayi ya ziyarce ka sautin yana tafiya ne a slow irin me ratsa zuciyar nan....... A hankali sautin sanyayar muryarsa da ya 'kara sanyayata gurin wa'kar ta fara tashi cikin wa'kar sa me take *Mahaifinta ne.!* *"MAHAIFINTA NE."!* *"Hanifa sanyi na zuciya."!*💔 *"Hanifa Haske na zuciya."!*💔 *"Hanifa Sanyin idaniya."!* *"Wayyo! Hanifa kin* *kama zuciya......💔 Mahaifinki ya shiga rayuwa ta."!* A slow sautin wa'kar ya cigaba da tashi sautin sanyayar muryarsa na 'kara sanyi har wani rawa takeyi saboda tsananin halin damuwa da yake ciki wa'kar ta cigaba da tafiya kamar haka.......... *"Ina sonta."!❤* *"Tana sona."!❤* *"Babanta ya shiga rayuwa."!* *" Ya bar gari saboda Soyayyar gudan jini❤.!"* *"Garin Kano yayi min zafi babu gudan jini."!❤* *"Hanifa tayi 'kaura daga kano........ Ni gombe zani koma gurin gudan jini."!❤* *"Soyayyar babu 'karya tana sona!❤ ina sonta!❤amma babanta ya raba tsaka ni........ Wai ya zanyi ne? Ni garin gombe zana kwana."!!!!!!!!!!!!!"* *"So Mukkuli na zuciya."!💔* *"Hanifa ta kulle zuciya."!💔* *"Ina sonta."!💔* *"Tana so na."!💔* *"Baban ta ya shiga rayuwa!!!!!!!!!🕺🏼🕺🏼🕺🏼* Sai da ya goge wasu gunti hawaye sannan ya cire abunda yake mak'ale a kunnen shi ya jefar kan kujera yaje ya zauna ya dafe kansa yana kukan zuci! Abbakar Mobson zuciyoyinsu duk sunyi sanyi sosai wa'kar ta kashe musu jiki duk Wanda yake cikin halin soyayya yaji wannan wa'kar zaiji kamar dashi ake to ballanta ga Wanda akayi don ita.... A take suka shiga tace wa'kar gami sai da suka tabbatar komai yayi ne sannan suka futo daga studio lokacin Khalid yaji wani irin jiri na d'ibarsa yasan damuwa ce kawai mota suka shiga gabadayan su. *14/1/2020* _BintuUm@rAbb@le_ [1/21, 9:45 PM] BintaUmarAbbale: _MASHAHURI_ *_Mallakar: Binta Umar_* *_Ki biya ki karanta cikin kwanciyar hankali ke kuma da kika futar da book d'in na barki da Allah!_* *08089965176* *07084653262* *0542382124....Binta Umar Gt bank* *49* Kamar yanda ya kwana cikin wasi-wasi da tashin hankali haka itama ta kwana cikin tsananin damuwa da kuma wani irin ciwon kai irin na gefe guda, Safiya nayi ta nufi b'angaran su Wasila duk suna cikin daki basu futo ba taji dadin hakan, dakin Haruna ta tura ta shiga Allah yasa a sakaye yake bacci yake sosai yaji maganar ta a kansa ya Bude idonsa da sauri yana mik'ewa zaune kallonta yake da yanayin bacci a idonsa ya mike tsaye yana fad'in "Hanifa zauna INA zuwa." Zama tayi kan wata k'aramar kujera dake dakin, tana sak'e-sak'e shi kuma Haruna bursh yayi ya dawo dakin ya zauna da mamaki a fuskarsa yake tambayar Lafiya ? Kuka ta sanya masa yace." Kiyi shiru kar wani ya jiki menene? Ko inno CE." Girgiza kanta tayi murya na rawa tace"Ya Haruna har fa Nasiru ya kawo lefe suna b'angaran mu kuma naga sai shirye-shirye suke wai wace irin mafuta ka samo min ne."!? Haruna yace." Yaushe duk akayi wannan bani da labari."! Tace"Ai baza ka sani ba dama tunda baka yini a gida kuma sai dare kake dawowa." Yace." K'warai kuwa hakane."! Shiru sukayi dukan su Haruna ya sauke ajiyar zuciya Yana kallon Hanifar yace." Kin San me."? Girgiza kanta tayi alamun bata sani ba. Yace." Kina da numbar guy ne."!? Shiru tayi tana tunani Sam bata rike numbar sa a kwakwalarta ba kawai dai idan Abbakar ya bata waya bata tsayawa duba numbar girgiza kai tayi tace"ban da ita wallahi." Haruna yace." Yaushe ne sukace d'aurin auran."!? Muryarta na rawa tace"Jibi yau saura kwana uku." Yace."juma'a kenan."? Daga kai tayi ita duk ta 'kagara ya nema mata mafuta sai kallonsa take..... Dakin ne yayi shuru kusan minti biyar sannan yace." Zan kaiki garin kano gobe nasan kin San inda yake da zama in yaso sai mu neme shi ke dashi sai Ku nemawa kanku mafuta duk tsiya dai idan suka ga bakya gari sai su hak'ura da auran ko."! Daga kai tayi cikin jin dadin abunda ya fada tace"Ya Haruna nagode sosai wallahi bazan ta'ba mantawa da kai ba cikin rayuwata." Yace." Haba Hanifa ai duk yiwa Kaine nasan kema watarana kina da ranar da zakiyi min."tace"Yanzu ya za'ayi mu tafi."? Yace." Ke dai kawai ko zauna cikin shiri misalin goma na safe nasan hankalin mutan gidan ya dauke gurin sauraran wannan shirin na rai dangin goro a lokacin zaki San yanda zakiyi ki futo ki same ni bakin layi sai mu tafi tasha Insha Allah. " Tace"Insha Allah zanyi kokarin hakan." Yace." Yanzu kije ki saki jikin ki da kowa kinji ko."? Mik'ewa tayi ta futo daga dakin har yanzu mutanan gidan basu futo ba. Ko da ta koma sashensu sai ta saki jikinta sosai har tana taya Ammi aiki Ammi ta dunga mamakin yanda ta saki jikinta suna hira sai ta fara addu'a Allah yasa Addu'ar tace ta karbu Abbu da Hafiz ma da suka shigo sunga sauyi sosai suma sunyi murna da hakan Abbu ya zaunar da ita yana tambayar ta ko da abunda take bukata ta fada masa ko menene zai siya mata tace"Babu komai Abbu shi kuma Nasir yace." Yayi mata alk'awarin zai siya mata keken dinki sabo fil godiya tayi masa tana jin tausayinsu cikin zuciyarta, kusan k'arfe takwas da rabi na dare bayan sun gama cin abinci dai ga Nasiru ya shigo gidan fuskarsa a sake take yana sanye da wata shadda sabuwa sai k'amshin turarasa yake me saukin kudi ya shigo da sallama ya zauna kusa da Hanifar ko kunya babu saurin matsawa tayi daga kusa dashi tana jin wani irin haushin sa gaisawa sukayi da Abbu da kuma Ammi ya yace." Ammi zamuje da Hanifa gidan babbar yayarmu Rabi zasu gaisa wai tana so ta duba yanayin jikinta ne akwai wasu atampopi da zata dinka mata." Abbu yace." Ai babu wata matsala sai kun dawo." Ammi ta kalli Hanifa da take ji kamar ta Dora hannu aka tayi ta kurma ihu! Tace"Ki tashi kisa hijab dinki kuje." Mik'ewa tayi jikinta duk a sabule ta dauko hijab din Nasiru ya mike Yana fadi sai mun dawo." Bayansa tabi ranta duk babu dad'i Tafiya sukeyi kamar ta kurame taki kulashi shine dai da yaga shurun tayi yawa ya fara janta da magana kanzil bata ce masa sai ma tsabar haushin sa da yake kara nunnukuwa cikin zuciyarta haka suka isa gidan yayar tasa, wacce ta dunga ina a saka ina a aje da Hanifa kayan ciye-ciye ta aje mata gabanta tana ta janta da hira Hanifa gaisuwa ce kawai ta hada su da ita takasa sakewa da ita, haka tace ta mike ta gwada ta, ta dauka Nasir din zai futa sai taga ya zauna ya wani tsura mata ido gashi tana jin nauyin matar ita kuma taki gane abunda ya dace haka dai ta mike gami da cire hijab dinta matar ta fara aunata shi kuma Nasiru ya dunga yi mata wani irin kallo na tsantsar sha'awa babu abunda yafi daukar hankalinsa da shi kamar k'irjinta bai taba dauka cika da kasaitar yarinyar ya Kai haka ba, zuciyarsa ta saka masa wani Abu akanta yana ganin tunda dai jibi ne d'aurin auransu yana da damar da zai rungume ta ko ya samu ya rage zafi da radadin sha'awarta. Kallonta yake idonsa duk yayi ja haka aka gama ta dauki hijab dinta ta zura tana jin haushin matar da rashin kan gado da sai tace masa ya futa a ganinta ai bai dace ba, bata fuska tayi tayi har Nasir din ya fuskanci bata son zaman ya mike yana yiwa yayar tasa sallama mik'ewa tayi ta futa ta barsu minti biyu sai gashi ya biyo bayanta taki kallonsa hannunta ya rike suka futa Rabi tana tayi mata godiya da fadin "Amarya sai munzo ganin daki Hanifa kanzil batace mata suka futa dake soran gidan irin me duhunan ne kawai Nasiru ya kai ta loka ya makure ta da bango k'irjinsa ya danne nata zura hannunsa ta bayanta ya rungume ta kam a jikinsa. Rud'u ta shiga da tashin hankali kamar kunama ce ta harbe ta haka taji lokacin da taji hannunsa a jikinta ta dunga tureshi tana ja masa Allah ya isa kuka take tana ture shi ya'ki sakinta sai kokarin hada bakinsa yake da nata kara ta kurma me k'arfin gaske yayi saurin sakinta yana diri-diri hannunta ya kama ta fuzge da gudu ta futa daga gidan... Jin motsi daga cikin gidan yana jin muryar yayar tasa tana fad'in "Waye nan ne."!? Sai yayi wuf ya futa can ya hango Hanifa ta sauri kamar ta kifa ya dunga bin bayanta da sauri inaaaa ai tayi masa nisa domin har da gudu ma tana hadawa, hawaye kurrum take sharewa tana mamakin halin maza Abbu ya yarda da tarbiyar Nasiru ya zab'a mata shi a matsayin miji Ashe bashi da halin K'warai yabi ya matseta a soro don yana gadara shi zai aureta shine ya fara taba jikinta wata irin tsana da kiyayarsa ta kara nunnukuwa cikin zuciyarta mussaman da ya rungume ta Sam bata ji wani dad'i ba sai zafi da zuciyarta take dole ne ma ta gudu ta bar musu garin gabadaya tunda dai yanzu ta fahimci shima Nasiru din sha'awarta tafi son da yake mata yawa ai ya bari a d'aura aure kome zaiyi sai yayi mata..... Haka ta isa gida tana wannan sake saken Abbu ta tarar dashi da Kawu Amadu suna hira ta gaidashi ta wuce cikin dakin Lokacin Ammi bacci har ya dauke ta, kawai sai ta shige can kuryar dakin ta zube kan katifa har yanzu jikinta rawa yake tunanin abunda Nasir yayi mata take........Ranar bacci rabi da rabi tayi da asubah ta Riga kowa tashi tayi sallah tayi zaune kan dadduma tana gyangyadi sai da ta fara juyo motsin Ammi a tsakar gida ta futo ta fara taya ta aiki suna shira sama-sama har suka kammala abun kari suka zauna suka karya Hanifa dai lokaci kurum take jira ta futa taji dad'i da Abbu da Hafiz sun futa da wuri ita da Ammi ne kurrum sunan zaune Hafiz ya shigo hannunsa dauke da d'aurin goro ya aje k'ara fita yayi ya dauko wani d'aurin guron ya aje ya dinga shigo da dabino da sauran kayan d'aurin aure haka ya tarasu guri guda ya zauna fad'in "Ammi na gaji sosai Wallahi." Ammi ta mike tana fad'in "Bari in kawo maka kayan kari nasan akwai yunwa ma." Hafiz yace." Abbu ma yanzu zai shigo suna tare da Baba Amadu ne." Hanifa jinsu kawai takeyi suna hirarasu gabanta sai fad'uwa yake ta mike gami da zura hijab ta futo kicin din ta tsaya tana fadin"Ammi bari inje gurin su Wasila zanji shirin rai dangin goro. " ammi tace "To sai kin shigo." Hanifa ta bar shashen nasu diri-diri ta fara tana bin babban tsakar gidan da kallo maganganun su Abbu taji a dakin Inno da'alama futowa zasuyi wuf!! Ta futa daga gidan kai tsaye bakin titi ta nufa kamar yanda Haruna yace mata tayi.. Bani da chaji ne kuyi min uziri nagode *18/1/2020* _BintuUm@rAbb@le_ [1/21, 9:45 PM] BintaUmarAbbale: _MASHAHURI_ *_Mallakar: Binta Umar_* *_Ki biya ki karanta cikin kwanciyar hankali ke kuma da kika futar da book d'in na barki da Allah!_* *08089965176* *07084653262* *0542382124....Binta Umar Gt bank* *48* Abbu yana jin sallamar Inno ya futo daga dakin. Inno ta kalleshi tana fadin"Sannu bawan Allah kana ciki yara suna tayi maka hayaniya a gida ita kuma Halima tana jinsu saboda rashin hankali." Abbu ya nuna mata gurin zama yana fad'in "Inno zauna sai muyi maganar." Zama tayi tana kara jadaddada magar Abbu ya kara gaishe ta amsa har yanzu muryarta a sama yace."Inno ki kwantar da hankalin ki kan maganar Insha Allah kome zai wuce nasan itama Hanifar k'uruciya ce take damunta." Tsaki taja tana fadin "K'uruciya ko kuma rashin hankali? Wannan kafurarar yarinyar me shegen bakin hali ai aure ne kawai zai kintsa ta don haka na yanke hukunci cewar rana ita yau za'a d'aura auranta Insha Allah ranar juma'a me zuwa kenan." Abbu yace." Allah ya kaimu Inno nima dama na damu da abun kinga akayi auran hankalin mu sai ya kwanta." Tace"Komai na bukata bazaiyi wahala ba insha Allah daga yau za'a fara shirye-shiryen buki." Abbu yace."Allah ya kaimu Lafiya. " duk Wannan maganar da suke Haruna da Hanifa Nasir Hafiz na jinsu.... Haruna yaja tsaki k'asa-kasa yace." Hanifa wuce muje b'angaran mu na lura idan na barki a gurin nan wad'annan sai sun kusa kasheki duba da yanda suke wani huci a kanki kamar sun kama ki da abun wani." Hanifa ta bi bayansa tana jin wata irin tsanar Nasir dashi kanshi Hafiz din. Shi kuwa Haruna yana sane yace su tafi sashensa yana so ya danyi mata tambayoyi kan lamarin.... Akayi sa'a babarsu batanan taje bukin suna, d'akinsa ya bude yace ta shigo Hanifa ta shiga babu wani jin nauyi a lokacin ita kawai Neman wamda zai taimake ta take akan lamarin,Wasila dake kicin ta bisu da kallo cikin mamaki domin akwai tazara tsakanin sashensu Dana su Hanifar shiyasa bata ji abunda ya faru ba, Haruna yace." Hanifa Wai meye tsakaninku da Mashahuri ne."? Shiru tayi sai da ya kara tambayar ta sannan tace"Ya Haruna shine Wanda nake so yake sona amma kuma Abbu da Ammi sun kasa gane hakan wai dole sai na auri Ya Nasiru."! Haruna yace." Kin tabbatar kina sonsa."!? Daga kanta tayi alamun "Eh." Shiru yayi yana nazarin maganar shi kam yana ganin dole ya taimakawa yarinyar domin ba karamin tausayi ta bashi ba so masifa ne kuma yana ganin iyayen su cutar ta kawai zasuyi domin shi a ganinsa duk uban da ya samu yarsa ta samu mai sonta kamar Mashahurin to zaiyi alfahari da hakan shima zaiso Hanifar ta auri Mashahuri domin ya kara samun shiga a gurinsa bayanan kuma cikin abokansa zai zama abun kallo 'kanwarsa na auran Mashahurin mawa'kin da duniya ta San da zaman sa, wato *Khalid* Yace." Ki kwantar da hankalin ki insha Allah zan shige miki gaba kan lamarin ki zaki cimma bukatarki naji waccan tsohuwar tana fadin"Wai rana ita yau za'a d'aura miki aure ke da nasiru kar wannan ya daga miki hankali insha Allah kafin zuwan ranar na nema miki mafuta." Hanifa ta sauke ajiyar zuciya me sanyi sai yanzu ta Dan samu sassauci cikin zuciyarta tace"Nagode sosai Ya Haruna ubangiji Allah ya kara zumunci. Wallahi ni ba wai ina in Yaya Nasiru bane kawai da bana jin zan iya zaman aure dashi kamar yanda nake son Khalid din ina ganin idan na auri Ya nasiru bazan bashi kulawar da ta kamata ba tunda nasan hankalina yana kan wani daban kaga ni dashi zamu shiga cikin wani hali wannan nake so su Abbu su fahimta amma sun kasa ganewa." Haruna yace."ai baza su gane ba tunda duk cikinsu babu Wanda ya ta'ba fadawa komar so shiyasa suka kasa ganewa ni na tabbatar guy nan na bala'in sonki tunda har kikaga ya zauna ya tsara miki wa'ka irin wannan akwai tsantsar soyayarki a tare dashi." Hanifa ta sauke ajiyar zuciya tana jin dadin kalaman da Haruna yake fada a tsakanin ta da Khalid din.... Koda ta futo daga dakin sai tayi zamanta nan tsakar gidan suna hira da Wasila dake kicin tana yi musu abinci sunanan zaune har Ummansu ta dawo daga gidan suna Lokacin ne kuma aka fara kiran sallah magariba......... Hanifa kin komawa tayi sashen su tayi kwanciyar ta nan har Safiya nan din ma sai kusan goma na safe ta shiga sashensu abun bakin ciki da takaici Inno ta Tarar ita da Abbu da Ammi din suna ta tsara yanda hidimar auranta zai kasance tana tsuguna wa tayi duk ta gaishe su..... Ammi da abbu suka amsa babu yabo babu fallasa Inno kuwa surutu ta kamayi mata, Takaici yasa Hanifa mik'ewa da sauri ta shige dakin tana tsaki k'asa-k'asa tace"Tsohuwa sai shishshigin tsiya kawai katifa ta kwanta ta rungume pillo tana tunanin Khalid a zuciyarta...... Muryar abbu taji yana fadin"Wai yanzu su Nasiru sun tafi gurin masu printing domin a buga katin d'aurin aure gabanta na fad'uwa ta mike zaune tana fad'in "Mutanan da gaske suke ashe ? Innalillahi wa'ina ilahi raji'un." Hawaye ta fara sharewa futowar ta daga sashen su Wasila Haruna ya futa da ta koma ta fada masa halin da ake ciki ita duk kanta ya kulle kuka take tana addu'ar Allah ya kashe Nasiru tana ganin da ta aure shi gwara ta zauna haka babu aure. _Hanifa har kiyayar ta kai haka?_ Motsin shigowar Ammi dakin yasa tayi shiru hade da saurin juya bayanta don kar Ammi din ta fahimci kuka take Ammi ta gama abunda take ta futa daga dakin. *** Khalid wa'kar shi tq samu masifar kar'buwa fiye da yanda kuke tsammani domin ba Najeria kadai ta tsaya ba harda sauran kasashen waje wayoyin jama'a"a kuwa har gajiya yayi da dauka su Mobson suka cigaba da d'agawa suna amsa masa, shi kam duk wannan bai dame shi ba burinsa kawai wa'kar ita isa inda ake so....... Kiran waya ne ya kara shigowa Khalid yace"Mobson ka kashe wayoyin nan haka nifa ba abunda ya dame ni ba kenan." Mobson yace." Bari in daga wannan nagama kamar ta 'k'asar waje ce in yaso daga ita sai a kashe wayar." Gyda kansa yayi Mobson ya daga wayar da tare da sallama Cikin wani irin turanci irin na america mutumin yayi sallama yana tambayar yana magana da Khalid ne."!? Mobson ya bashi amsa da nasa turanci irin namu na Nigeria yace." A'a a bokinsa ne." Mutumin yace." Idan babu damuwa hadani da Khalid din zamuyi magana." Mobson ya mik'awa Khalid wayar dake duk yana jin abunda suke cewa yayi magana da turanci, mutum yace." Sunana Sonop ni d'an america a can aka haifeni amma kuma mahaifiyata bak'ar fatace yar asalin k'asar Ghana ni mutum ne mai son jin wake-wake sosai yanayin muryarka yayi min na saurari wa'kokin ka masu ma'ana muna tare da Abudulbasit Yana jin yaran Hausa ya fassara min Gaskiya ina mutukar jinjina maka K'warai da gaske, dani da abokaina muna so mu ganka ido da ido shine muka shirya domin kawo maka ziyara har Nejeria idan kuma zamu samu muna so kaziyarci k'asar mu muna so Kayi mana wa'ka mai dad'i irin ta gayu ina fatan ka gane."! Khalid ya sauke ajiyar zuciya da murmushi a fuskarsa yace." Sonop nagode K'warai kuma nima ina alfahari daku gaskiya naji dad'i da har wakata taje inda kuke kuma insha Allah kamar yanda ka bukata din zamu shiga studio dani daku zamu yi wa'ka irin wacce kuke so sai kuzo da shiri wannan karon zamu futar da vedio ne insha Allah. " Sonop yaji dad'i sosai yace." Zamu zo najeria cikin satinan." Khalid yace." Babu damuwa ina sauraran zuwan Ku." Sunayin sallama Mobson ya fasa wani irin ihu! Yana buga katifar da suke kai fad'i yake." Guy ka tsallake Wallahi kayi kudi ka gama zaka hada ala'ka da baturan mutum gaskiya kai d'an baiwa ne, Guy kayi bai-bai da talauci don ina me tabbatar maka da cewar mutukar wa'kar ta futa to za'a samu manyan masu kudi ko masu mulki dake America su siya Shikkenan zaman nejeria ya kare sai dai kazo da yawo." Mobson duk a gigice yake wannan maganar yana ihu.!!! Khalid yaja tsaki yana Dan girgiza kansa yace." Mobson naji dadin al'amarin nan nima amma kuma damuwar da nake ciki baza ta barni in samu nutsuwa, kuma kana mantawa da Abu d'aya nafad'a na kara fad'a muku nifa wannan wa'kar da nake yi ba don kudi nake ba kawai ra'ayina ne kai kanka kasan kudi ba matsala ta bane so Ku daina wannan maganar." Mobson ya gyara zamansa sosai yake fuskantar Khalid din yace." Wannan karon baza kayi mana bukulu ba wallahi nake fada maka kafarka kafarmu duk inda zaka shiga a fadin duniyar nan muna biye dakai domin mu muna bukatar kudi kai da kaci ka tada kai sai ka barma na." Khalid yace." Duk abunda na samu ta dalilin wa'ka na bar muku kuci kuyi sadaka kuma Ku bawa Wanda kuke so." Abbakar ne ya shigo ya tsinci maganar da suke ai shi har yafi Mobson din rudewa sai murna suke suna ganin suma lokacin su yazo ta dalilin Khalid Mashahuri Ashe banbadancin da suke masa bazai tashi a banza ba. ***** Lamari fa ya girma ma tsakanin bangarori biyu sai hidima suke gami da shirye-shiryen buki domin har mahaifin Nasiru ya bashi kudi kusan dubu Dari da Hamsin a cewar sa sun isa yayi siyayar aure suturun sawa da kayan kwalliya tundai duk al'amarin na gida ne baza'a tsawwala ba, gurin zama kuwa bashi da matsala domin har an gyara masa wani b'angare dake jikin gidan nasu har fanti anyi sai jiran zuwan amarya..... Nasir akwati biyu ya hadawa Hanifa komai ansaka dai-dai gwargwado Inno da ta gani sai ta dunga fada tana cewa''Yayi barna kudi ai ba irin su Hanifa y akewa gwanin ta ba da ya sani ma turmi uku ya siyo da abunda ba'a rasa ba. Shi dai shuru kawai yayi mata aka shiga da akwatinan gurin su Abbu yayi ta sa'albarka yana fadin "Da ya sani bai wahalar da kansa ba shi kawai burinsa ya rike Hanifa amana. " Nasir yayi masa bayanin komai nan Abbu yayi tawa mahaifin nasa addu'a, Hanifa ranar kwanta tayi kuka bini-bini ta duba hanyar shigowa Haruna kawai take so ya dawo to har k'arfe goma na dare bai shigo ba haka ta hak'ura ta kwanta da kayar bacci ya dauke ta bayan taci kukanta ta koshi.... Wani irin mafarki yakeyi mai dad'i ya dunga rungume pillow yana motsa cinyarsa nishi yake saki yana kara matse pillow da hannunsa...... Duk cikin baccin yake ta motsi da hannunsa burinsa kawai ya damk'i abunda yake tsokane masa ido amma ina sai buge-buge yake a jigace ya bude ido firgigit ya mike zaune wata irin zufa na keto masa. Dakin yake bi da kallo yana Neman inda yarinyar take ya juya da sauri bayan shi da gefansa babu kowa sai tarin k'ananun pillows da suke baje kan bed din, Yanzu ya tabbatar mafarki yake. Sunkuyar da kansa yayi cikin tsananin damuwa da tashin hankalin abunda yake damunsa mafarkin da yakeyi kamar gaske wai gashi ga yarinyar Shaik sunyi aure suna soyayya tana kwance a jikinsa tana masa wasa irin Wanda yake so a rayuwarsa ji yayi joystick dinshi na kara harbawa zuciyarsa ta harba da tsananin damuwa da sha'awa kawai sai yayi 'kasa da kansa wasu 'kananun hawaye na takaici suka fara futa daga idonsa, Wa'kar da yayi domin ita ta tafi can wani guri da ba'a bukatar ta yau kwanaki hudu kenan da tafiyar su amma babu wani labari gamsashe dangane da Wanda yasan su da inda suke zaune a garin gombe kullum cikin bunkice yake yana aikin duba sytem ko zai ci karo da sa'kon Wanda zai ce mishi yasan yarinyar shiru daurewa kawai yake ga wata irin masifa da babu damar ya rufe idonsa suffofinta suyi tayi masa gizo idan ya kwanta bacci ma haka zatazo ta dame shi kullum haka yake fama.... Cike da damuwa ya koma ya kwanta yana tunanin ta inda zai 'bullowa lamarin a duniya yana ji bashi da babban makiyi sama da Shaik shine duk ya jefashi cikin wannan masifar..... Shawarar da ya yanke kawai za suje gombe suyi ta bunkice har Allah yasa a dace, yasan duk umarnin da ya bawa yarinyar zata shi kadai yasan abunda ya shirya domin nemawa kansa mafuta. *17/1/2020* _BintuUm@rAbb@le_ [1/21, 9:45 PM] BintaUmarAbbale: _MASHAHURI_ *_Mallakar: Binta Umar_* *_Ki biya ki karanta cikin kwanciyar hankali ke kuma da kika futar da book d'in na barki da Allah!_* *08089965176* *07084653262* *0542382124....Binta Umar Gt bank* *47* Alhaji Tijjani na tsaye tsakiyar parlor Khalid din ya shigo da sallama a bakinsa suka amsa duka Nasrin ta durkusa har kasa ta gaida shi hankalin sa na kan Khalid din ya amsa mata Khalid ya zauna kan kujera yana fadin"Dady ya kasuwa Mamy ta taso ka ko."? Yace."abunda nake so nace kenan Myson tayi min waya tana kuka wai kana nema ka zauce ka kasa gane mutane duk ta gigita ni na tawo babu shiri kuma gashi nazo na ganka rad'au dama ni na San yaro na jarumi ne." Khalid ya shafa kansa yana Dan murmushi yace." Dady kawai rigimar mamy ce wai kawai don bangane Momy zainab ba shine take cewa na zauce kan soyayyar yarinyar Shaik." Alhaji Tijjani ya zauna kusa dashi da damuwa a fuskarsa yace." Myson yau a kasuwa yini akayi ana sauraron sabuwar wa'kar ka mai taken *Mahaifinta ne!"* wannan mutumin gaskiya bai kyauta mana ba Ko yanzu kafin na futo daga kasuwar sai da nasha tambayoyin mutane kan wa'kar taka in banda Alhaji Lawan babu Wanda yasan abunda yake faruwa,, akwai wani abokin harkata Alhaji Bilyaminu shine ya 'bukaci da kaje ka ga yarinyar sa idan tayi maka sai yayi maka huce haushi da ita."! Nasirin da mahaifiyar ta da ita kan ta Mamyn sukaji wani rugugu a zuciyarsu addu'a suka farayi Allah yasa Khalid din ya bujerewa bukatar mutumin Nasrin har ta soma share hawaye...... Shiru yayi na minti biyu kafin yace." Dad mu bar wannan maganar don Allah inaji a jikina zan auri yarinyar shaik anan kusa kai dai ka cigaba da tayani addu'a."Alhaji Tijjani yayi shiru domin bai so jin haka daga bakin Dan nasa ba yaso ya hada huldar auratayya da Alhaji Bilyaminu domin mutum ne shi shararre a duniya yana da kudi Wanda suka ci Uwar nasa shiyasa yake so ya kara d'aura aminta dashi..... Amma Tunda Khalid din ya nuna baya so ya hak'ura domin samun kwanciyar hankalin sa, mik'ewa yayi ya hau sama yana mita yanda Mamy ta kirashi a waya a cewar sa tasa duk jikinsa babu dad'i domin shi har ga Allah ya dauka wani mummunar Abu ne ya faru da Dan nasa, Mamy dai shiru tayi Saboda sanin halinsa Hajiya Zainab itace me Dan bashi hakuri sai dai ya haye sama sannan tayi shiru.....shima Khalid din daining ya nufa NASIRIN ta mike ts bishi tans so ta zame masa kaska taki ta kama kanta har ya soma jin haushinta domin shi baya son takurawa. Hira take masa yana wani ya amsa wani ya basar haka har ya kammala cin abincin ya mike ya futa daga gidan kai tsaye gidansu Abbakar ya nufa domin yaji me yake tafiya aikuwa tunda yana hawa titi ya fara ganin manya-manyan pastas dinsa a manne daga sama an rubuta sabuwar wa'kar Mashahuri mai taken *MAHAIFINTA NE!* yara ya gani suna ta kallo wasu kuma mannawa jikin shagunan mutane da gefen kwalta ga wani me shagon Chaji ya saki wa'kar cikin mayan sifi'ku gurin dai duk ya hautsine da samari kowa yana fadin albarkacin bakinsa, sai da yayi da ya sanin futowa domin suna ganin motar shi kin barin sa sukayi caaaaa! Suka baibaye shi suna fadin albarkacin bakinsu kan sabuwar wakarsa wasu daga ciki kuwa fad'i suke Shaik yayi a sara kuma ya cuci yarinyar sa.... Haka dai ya dunga daga musu hannu ya samu ya wuce to yana karya kwana da motarsa domin shiga layin su Abbakar ya fara jin sautin tashin wa'kar Mobson ya ware kida layin ya cika da yara da manya ko wane bango ka kalla pastar d'insa manne ya nan ma ganin motarsa ta shigo yasa gurin ya kara hautsine wa da ihu duk suka yanyame motar ya kasa ma futowa daga ciki sai da Abbakar yazo gurin ya futo dashi sannan ya dunga daga musu hannu yana dariya da kyar dai ya samu suka shige shagon mobson duk da haka basu bar gurin ba hayaniya a gurin kamar me! Khalid yaji masifar dad'i da wa'kar ta samu karbuwa tun kafin aje ko INA gashi Dad dinsa ma yaji cikin kasuwa lallai ya godewa Allah kuma yana sa ran wa'kar zataje har garin da yake so. **** A shashen su Wasila Hanifa ta kwana bata shiga b'angaran nasu ba sai kusan 'karfe goma na safe taje suka gaisa da Ammi a lokacin Abbu ya futa..... Aiki ta Dan taya ammi ta dawo ta zauna Ammi ta shigo dakin ta ganta zaune tana zabga tagumi tace"Wato kinan kina tunani ko Hanifa wai baza kiyiwa kanki fada ba ko." ? Kasa tayi da idon ta tana kokarin tsane hawayen da yake kokarin zubo mata. Ammi ta shige daki ta futo hannunta rike da wata roba me fad'i da wake a ciki tace"Ki gyara min waken nan yau ina so inyi mana fate Abbu baya jin dadin jikinsa yanzu ma sun je Chamis ne." Jikinta a sanyaye ta karb'i robar tace"Ammi me ya same shi."!? Zazzab'i ya kwana dashi jiya nasan dai gajiyar hanya CE." Ta fada tana kokarin futa daga dakin Hanifa ts share hawayen tana tausayawa Abbu da rayuwarta..... Waken ta fara gyarawa tana tuno sanyayyar murmushin Khalid da salon soyayyar sa. Haruna ne ya shigo shashen nasu hannunsa rike da wayarsa madaidaciya yana sauraron wa'kar Mahaifinta ne! Bakin kicin ya tsaya suna gaisawa da Ammi, Haruna dai yayan Wasila ne daga shi sai ita yaro ne da yake gan ganiyarsa domin duka sutturunsa babu manya sai kananu ga wani mutsiyacin aski da yake kullum sumar kanshi a taje take da kum a jiki Bini-bini zai cire ya taje mugun Dan gayu ne da son dabi'un nigogi duk gidan sun hak'ura sun kyaleshi Inno ma tayi masifar ta gaji tunda ya fara sauraron wa'kokin Khalid yake da burin yaje har kano gurinsa yana mutukar son wa'kokin sa a cewar sa shima yana da burin ya zama mawa'ki a duniya shiyasa yake so ya zama yaron Khalid wa'kar yake saurara yana gyada kansa cikin shauki dad'i. Ammi tayi kasa'ke! Tana sauraron baitocin wa'kar me taken Mahaifinta ne gashi taji ana ambton sunan Hanifa....... Kafin su Ankara suka ga Hanifa tsaye a Kansu kamar anje fota gurin.... Haruna yace." Ke meye haka sai kace wata aljana zaki fad'o guri." Kallonsa take tana marmar da idonta bakinta sai motsi yake. Ammi ta kalleta yanzu ta fahimci daga inda wa'kar ta futo tunda taga Hanifar ta futo wato yaronan bai rabu dasu ba kenan har ya shirya musu wa'ka wacce take ganin kamar tozarwa ce." Haruna ya kama hanyar futa yana dad'in "To tunda baza kiyi magana ba ni kinga tafiy..... Kafin ya karasa ta bishi da gudu ta rike hannunsa sai ga hawaye sharrrrrrrr!!! Sun biyo kuncinta. Haruna ya tsaya yana kallonta da mamaki a fuskarsa yace." Me akayi miki kike kuka ne? Na lura fa Tunda kuka zo garin nan kin kasa sakewa damu wai meye ne."? Haruna ya kara tunzura zuciyarta ta saki hannunsa gami da zubewa a gurin tana rusa kuka na futar hankali..... Wanda yayi dai-dai da shigowar Abbu da Nasir da Hafiz suka riski abunda yake faruwa Ammi ma futowa tayo daga kicin din duk sukayi tsaye a kanta suna mamaki kukan da takeyi..... Abbu ne yake tambayar abunda ya faru. Haruna yace shi bai sani bs kawai ta futo daga daki ta biyoshi Tana kuka." Ammi tace"Haruna k'ara kunna wa'kar nan suji?" Haruna yasa dariya yana fad'in"Ammi ina ruwan wa'kar Mashahuri da kuma damuwar Hanifa. " jin sunan da Haruna ya ambata yasa duk jikinsu yayi sanyi.... Nasir da jikinsa yake tsuma yace" ka kunna mana Malam." Haruna ya kunna wa'kar yana fadin"Yaro me tashe kenan 'yar wani mutum yake so shine mutumin dake albada ne ya gudu da yarsa harda barin gari donshi mtsssss! Ya karasa maganar yana Jan tsaki! Su dai shiru sukayi masa suna sauraron sautin wa'kar da ya fara tashi a hankali a hankali kafin sautin muryarsa ya fara bayyana ta Cikin wa'kar mai taken. *Mahaifinta ne."!* Abbu yaji jikinsa ya kara rikicewa da zafi jiri ya fara dibarsa bai tsaya ya gama sauraron wa'kar ba ya wuce daki tunda dai ya fuskanci daga inda wa'kar take zuwa yayi ya kwanta kan katifa cikin kuryar daki jikinsa babu dad'i Al'amarin ya soma bashi tsoro addu'a yake cikin zuciyarsa kan duk abunda yafi alkairi Allah ya zab'a. Can tsakar gida kuwa Hafiz yayi kan Hanifa da duka da hauri da kafa dukanta yake yana fad'in "Wannan kukan da kikeyi na uban meye wai ke wace irin mayyace ne don ubanki me zakiyi da wannan Dan iskan da kullum yake kokarin ya to zarta Mahaifin ki, Ammi shigewa tayi kicin ta cigaba da aikinta ranta duk babu dad'i Hafiz bala'i yake ma Hanifa yana dukanta da k'afarsa kamar bai San daga inda take ba Nasir na tsaye duk ya rasa ma me zaiyi yana ganin dukan shine yafi amfani gareta tunda taki hak'ura shi sai yake ganin kamar ma itace tasa Khalid din ya shirya wannan wa'kar...... Haruna ya karaso gurin yana kokarin janye Hanifa dake kwance kasa Hafiz tsaye a kanta yana duka yace." Wai meye ne ni kun sani a duhu na soma fahimtar inda al'amarin ya dosa amma ina bukatar Karin haske a gurinka." Hafiz na cigaba da dukan Hanifa ya kwashe komai ya fadawa Haruna tsaki yaja da k'arfi ya janye Hanifa daga gurin yana fadin"Wallahi sai Allah ya saka mata wannan ai cin zali ne, Hafiz kasan daci da masifar so kuwa? Ko Dan baka son abunda yake damunta a zuciyarta bane,? Haka kawai dame zata ji? Dole sai an aura mata Wanda bata so kan me? Kawai yarinya Allah ya rufa mata asiri zaku cuce ta wannan tsarin baiyi ba wallahi ni bana cikinsa." Haruna ya karasa maganar sa a zafafe! Cikin hayaniya Nasir yace." Kai! Me kake nufi ne? Kana nufin kace abbu din ne yayi ba dai-dai ba kome ko kuma ni kakewa bakin ciki da hassada akan Hanifar da har kake fadin wannan maganar."!? Haruna ya daga kafadarsa alamun babu abunda ya dame shi yace." Kaine ka sani Wallahi Sam baku dace da hanifa kaje ka nemi dai-dai da kai kabarwa Oga matarshi da yardar Allah sai na tsaya mata kan biyan bukatar ta." Tofa fad'ar wannan magana sai ta dugunzuma zuciyar Nasiru yayi kan Haruna kamar zai Doke shi yake zaginsa duk idonsa ya rufe, Abbu na cikin Uwar daki kwance duk yana jinyo hayaniyar da take faruwa Lokacin ne kuma inno ta bayyana a gurin Jama'ar gidan suka fata turawa a gurin da 'daya bayan d'aya..... Inno tace"Wai me yake faruwa ne tun d'azu nake jiyo hayaniyar Ku menene ? Ina Haliman take ne? Tams jinku kuna d'iban albarka irin haka."! Ta k'arashe maganar cikin fad'a da daga murya. Ammi ta futo daga kicin tana fad'in"Inno gani a kicin."! Inno tace"Au! Da kina jinsu suna fada gami da zagin junansu kikayi shiru."? Ammi tace"Inno ayi hakuri don Allah wallahi na rasa ma me zance kan al'amarin.'' Inno ta maida hankalinta kan su Haruna dake rike da Hanifa dake kukan wurjajan!! Tace"Haruna me ya faru ne."? Haruna ya kwashe komai ya fada mata."Inno ta kalli Hanifa ranta a mugun bace tace"Au abun kunyar da zaki jawo mana kenan ? Me zamuyi da mawa'ki Wanda bashi da cikkakiyar sana'a to Bari kiji mu lokacin mu duk saurayin da yake wa'ka ba'a bashi aure domin wa'ka dai ba Sana'a bace don ubanki dame zai rike ki? Duk Wanda yake wa'ka ro'ko yake mu kuma duk fadin zuriarmu bama fatan su auri maro'ki saboda haka idan zaki hak'ura to ki hak'ura Wallahi tallahi bazaki auri mawa'ki ba.'' Haruna yaji kamar ya tsinka ma inno mari jin abunda take fada wai me yasa mutane suke hakane? Wai wa'ka itace inno take kira da ro'ko to shi kuma da yake da burin ya zama mawaki Ashe zasu sallame shi daga cikinsu don babu abunda zai hanashi zuwa kano gurin Mashahuri..... Yace." Inno banji dadin wannan maganar ba a matsayin ki na babba nifa sai dai Idan Ku sallama ni cikin dangi don ina da burin in zama mawa'ki kuma babu laifi anan don Ku bada yarku ga mawa'ki baiwace da Allah yayi masa baiwar da ba kowa yakewa irinta ba." Inno tace." Kul! Haruna kar in kara jin wannan Kalmar daga bakin ka indai ina da mutumci a idonka to ban lamunce maka da wannan sana'ar ta roko kuma kar ka kara maganar ka nemi wata sana'ar zaifi maka.... Ita kuma Hanifa daga yau zuwa rana ita yau za'a d'aura auranta da Nasiru sai inga karshen kiyayyar da takewa Dan uwanta kan bare kuma maroki.... Halima ina Munzali yake."!? Ta fada Tana kallon Ammi dake tsaye taji dadin hukunci da ta yanke tace"Yana cikin daki Wallahi jiya ya kwana da zazzab'i ." Inno ta nufi dakin tana gyara d'aurin zaninta take fadin"Saboda rashin hankali yarinya tana nema ta kai kanta ga halaka waye kuma Khakid to indai ina Raye baza'ayi wannan shashancin ba na Riga na gama yanke hukunci. " ta k'arashe maganar lokacin da ta d'aga labulen dakin............. *16/1/2020* _BintuUm@rAbb@le_ [1/21, 9:45 PM] BintaUmarAbbale: _MASHAHURI_ *_Mallakar: Binta Umar_* *_Ki biya ki karanta cikin kwanciyar hankali ke kuma da kika futar da book d'in na barki da Allah!_* *08089965176* *07084653262* *0542382124....Binta Umar Gt bank* *44* Shiru dakin yayi sai sautin kukan Hanifa ne kawai yake tashi Abbu zuciyarsa zafi kurrum take masa bai taba tsammanin yarinyar zata bujere masa ba sai gashi lokaci guda tana nema ta watsa masa kasa a ido, cikin taaushin harshe yace." Hanifa tun farko sai da na zaunar dake nace ki fadamin gaskiyar game da zabin da nayi miki me zai sanya ki rufe min abunda yake zuciyarki,? Sai bayan kin bari na Sanar da yan uwa da abokanan arziki kuma daga baya ki bullo da wata magana to a gaskiya bazan lamunta ba dole zaki auri Dan uwanki ko kin so ko kinki Nasiru dai shine mijinki kuma zaman Kano kafin nan kafin rana me kama da ta yau mun barshi zamu koma mahaifarmu saboda haka ina me umartarki a karo na biyu cewar ki cire wannan yaro a ranki domin bazan taba yin magana biyu ba da tun farko kin fada min gaskiyar ki zan iya tausar zuciya ta data Nasiru a baki abunda kike so amma yanzu kam lokaci ya kure miki." Yana gama maganar sa ya mike ya futa ransa duk babu dad'i Nasir da Hafiz bayansa suka bi nan suka ci karo da ledojin Shopping Wanda Khalid yayi wa Hanifa Nasir ya dauke su a fusace suka futa da Hafiz din yana fadin"Mu za'ayi wa k'aryar arziki bama so domin mu mutumci yafi komai a gurin bama bukatar kayan mutumin da bai San darajarmu ba."!!! Kuka kurrum takeyi ta hade kanta da gwiwa Ammi ta futo ta bar mata dakin shimfid'a tayi a tsakar gida ta kunna redion ta Sam Yanzu shawarar da ta sanja shine zata daina kula Hanifa har sai ta gane kuranta. Ranar yanda ta fa dare haka taga rana bacci baiga idonta ba Khalid kuwa baccin sa yake harda munshari yana mafarki gashinan yana soyayya da Hanifa haka ya tashi jikinsa kaca-kaca tsaki ya dunga bugawa domin sosai yaji dadin mafarkin Wanda yake ganin kamar gaske sai da ya farka ne ya gane Ashe gaibu ne. Cike da walwala da farin ciki ya shiga sashen iyayen nasa Mamy ta tsaya tana kallonsa cike da mamaki!! Yar dariya yake yana Sosa sumarshi yace." Mamy kin tsaya kina ta kallona ne me nayi kuma.'' Yana kokarin zama kujerar daining yake maganar yake tayi tana fadin"Dole in tsaya in kalleka Myson naga sai wani farin ciki kake da alama dai sun amunce maka ko." Ya fuskanci inda maganar ta ta dosa yace." Insha Allah Mamy Nike da nasara da Mahaifinta tunda dai tana sona magana ta kare idan yana son kwamciyar hankalin yarsa to ya aura mata ni." Girgiza kanta kurrum tayi domin bata da tace wa Mai gidan yana nan tana iya magana cibi ya zama kari shiru shine yafi mata a cikin wannan al'amari cikin shagwaba yace."Mamy hada min break fast yau zanyi irin Wanda na Dade banyi irinshi ba." Tab'e baki tayi tare da fadin"Kamar gaske Yanzu kana fara ci zakace ka koshi." Yace." Mamy ke dai hada mi ki gani ai ina cikin farin ciki ne zanci da yawa." Mamy ta fara hada masa tana fadin "Allah yasa dai." Alhji Tijjani ne ya sauko daga sama yana sanye da shadda yar ubansu anyi mata dinkin hannu kana ganin shaddar da dinki kasan irin na manyan mutane ne sai sabe babbar rigar yake yana ta zabga k'amshin tura ransa ya karaso gurin Hannu ya bawa Khalid din suka gaisa yana fadin"ya kama ta fa yau ka futa kasuwa domin jiya da shekaran jiya aiki ne ya hade min sosai akwai lissafin wasu kudi da zamuyi da Alhaji Ayuba bana so ya cuce ni INA so kaje ka tsaya ayi komai a gabanka inyaso sai a shiga dasu banki." Khalid na kurbar ruwan tea yace." Shikkenan dady zan shigo insha Allah. " A gurguje ya zauna Mamy ta hada masa abun kari yana ci suna hira da Dan NASA Khalid na fada masa abunda ya faru amma bai fada masa cewar Hanifar ce tazo gidan ba yace masa dai sun had'u a hanya ne." Alhji Tijjani ya dunga dariya yana yabawa da jarumtar dan nasa yace." Irin wad'annan mutanan masu taurin kai dama irin Ku ne maganinsu Myson ko auran yar tasa kayi kar ka yarda ya raina ka kowa ya zauna a matsayin sa." Mamy kallonsu kawai takeyi bata da damar da zata tsoma musu baki a maganar su domin idan tayi kuskure ko yayane masifa zata sha gurin mijin nata shiyasa kawai tayi musu shiru amma taki sakar ma dad din fuska dake ta kokarin sakata cikin maganar sai dai kurrum tace "E ko a'a domin ita da zasu bi ta ta ma da sun aje maganar gefe guda don ba k'aramin bata mata rai take ba kwata-kwata bata kaunar yarinyar da Khalid...... Cike da nishadi suka futa daga gidan Khalid na kara samun daurin gindi gurin Dadyn nasa. **** Yau kwanaki hudu da faruwar al'amarin Hanifa duk ta muzanta ta futa daga hayyacin ta kullum cikin b'oye kanta take cikin dakine ko band'aki ko kicin tana kuka babban abunda ya daga mata hankali yanda Ammi ta futa daga sangarta gaisuwa ce kawai take hada su Shikkenan Ammi sai ta dauke mata wuta Abbu kuwa dasu Nasir basa zama kullum cikin shirye-shiryen suke na tafiya gwambe gidan da suke ciki ma tuni Abbu ya sai dashi hade da k'aramin gidanshi dake D'orayi Wanda ya sanya haya can gombe basu da matsalar gurin zama tunda dama yana da gurin shi na gado, Hanifa hankalinta ya tashi sosai mussaman da taga ana ya gobe tafiyar suna ta hada kaya cikin buhunhuna Ammi na ta shiga makota tana sallame gami da Neman afuwar juna dama tuni wani me kafunta yazo ya dauke gado da sif Ammi ta karb'i kud'in kayanta Yanzu kayansu duk suna cikin gana masgo komai Ammi ta kammala hadawa ranar tafiya a ke jira a lokacin ne kuma Abbu ya futo da wannan shopping din na Khalid ya damkasu a hannun Nasiru yace suje har gida su mai yar masa da kayansa dama jira yake lokacin tafiya yayi aikuwa dama Nasiru jira yakeyi take suka nufi gidansu Khalid Nasir yana ji zaiyi futo na futo da Khalid din indai akan Hanifa ne Lokacin da suka isa gidansu Khalid k'arfe shida saura na yamma a lokacin ne kuma motarsa ta kunno kai layin suna tsaye a bakin gate masu gadi sun hanasu shiga sai tambayoyi suke musu Nasir fad'i yake gurin Khalid mukazo ganin motar Khalid din ta shigo layin yasa daya daga cikinsu yace." Gashi nan ma ya dawo." Duka suka juya suna kallon bayansu daya daga cikin masu gadin ne ya bude gate din motar ta shiga ciki da gudu ya bi bayansa har inda ake parking ya bude masa motar yau yana sanye ne da k'ananun kaya dogon wandon jins da shart mai dogon hannu a hannunsa daure da agogo kafarshi tana sanye da rufaffan takalmi yayi kyau sosai amma kuma kallo daya zakayi wa fuskarsa ka gane yana cikin damuwa.... Mai gadi yace."Ranka shi Dade Kayi baki gasu can bakin gate tun d'azu sukace gurinka suka zo...A hankali yace." Ok muje in gansu." Mai gadi yayi gaba da sauri! Khalid din yabi bayansa.... Kallonsu yakeyi daya bayan daya yana so ya tuno a inda yasan fuskarsu... Hafiz ya bashi hannu suka gaisa babu yabo babu fallasa shi kuwa Nasir cogewa yayi yana jin wani irin kishinsa cikin zuciyarsa ga k'amshin turaran da yaji a jikin Hanifa kwanaki yaji shi jikin Khalid din shiyasa yake jin kamar ya kai masa duka yana ganin Khalid ya Riga ya gama tatta'be masa jikin Hanifa yana ji zuciyarsa kamar ta buga saboda kishin sa. A Dan ya mutse yace." Zan shiga gida Yanzu Malam Iliya yake fadamin nayi baki ban gane ku ba."!? Nasir yace."Dama bama so ka gane mu munzo ne kawai mu ja maka kunne kan ka kama kanka kuma ka futa daga sabgar yarinyar nan Hanifa domin dai tuntuni mahaifinta yayi mata miji saboda haka kaje ka nemi wata ga kayan kanan mutumci yafi komai a gurin mu." Khalid ya kalleshi lokacin da yake aje ledojin a gabansa yanzu ya fahimci daga inda suke murmushi yake yana kallon Nasir din da yake sauke nuffashi ya wani murtuke fuskarsa! Cikin yanayin maganar shi yace." Yanzu ni nayi kama da Wanda za'azo har gida ajawa kunne."!? Nasir yace."K'warai kuwa domin kana kokarin shiga hurumin da banaka ba."Girgiza yayi yana Dan ya mutsa fuskarsa yace."Ya shaik din ne ya turo Ku kuzo Ku garfade ni na futa daga hanyar yarinyar shi ko kuma Kaine ka kawo kanka domin naga zakewarka tayi yawa ko Kaine mijin ne."!? Nasir yace." Sanin nine mijin ko bani bane duk bai shafeka ba kawai dai ka futa daga harkar yarinya domin ba sa'ar auranka bace kaje ka nemi dai-dai kai ka k'yaleta tayi zaman auranta Fuskarsa a sake yace." Kake wani wahalar da kanka kana nufin soyayyar da Hanifa take min ta gaibu CE."? Shuru sukayi suna sauransa ya saki dariya yana shafa sajanshi ya cigaba da cewa"So da kaunar da take min bazai taba bari tayi rayuwar aure da kai ba. Domin zuciyarta tana gurina nutsuwa da kwanciyar hankalinta duk ya tattara a hannu abunda kawai nake bukata daku shine kuje ku fadawa Shaik cewa inji ni yayi hakuri ba don halina ba da mugwayen d'abi'una da yake fada cewar ina dasu to yayi hakuri ya aura min yarsa da nake so na raya sunna da ita hakan shine samun kwanciyar hankalin yarsa daku kanku gaba daya." Nasir da Hafiz suka rasa abunda zasuce masa saboda ganin irin maganganu da yake musu na rainin hankali, Khalid kuwa yana gama maganarsa ya wuce cikin gidan Tare da bada umarni a rufe shi aikuwa masu gadi suka bugu gate da k'arfi karar gate dine ya dawo dasu Hayyacin su Nasir ya cizi ya tsa tare da fadin "Gaskiya wannan guy bashi da mutumci." Hafiz yace." Zai aikata abunda yafi haka ma mu dai burinmu ko mun bar gari yasa mu huta wannan shine kawai muje mu mu bar masa tsiyarsa a gurin." Haka suka aje ledojin a gurin suka bar gurin cike da takaici da b'acin rai. ****** Gidansu Asalamiyya ne kurrum Ammi bataje tayi sallama ba ta bari ne sai da daddare tukkuna bayan sun gama cin abinci sai ta tafi gidan, cike da girmamawa suka gaisa da juna Ummansu Asalamiyya na tsokanar ta da fadin"Matar malam sai dare ake ganin Ku.*!? Ammi tace"Wallahi kuwa dama zuwa nayi inyi miki sallama gobe insha Allah zamu tafi gombe kuma Gaskiya babu ranar dawowa watakila ma mun tafi kenan." Ummansu Asalamiyya ta rike baki ciki da mamaki tace"Bangane me kike so kice min ba Halima."!? Ammi tayi mata bayanin abunda yake faruwa Shiru tayi tana nazarin maganar daga bisani tace"Halima ni kam wannan tafiya taku batayi min dad'i ba wallahi Hanifa kuma ta bata wayonta tunda akan bare take nema ta tozarta Dan uwanta gaskiya bata kyauta ba Allah yasa haka shi yafi alkairi. " Asalamiyya ta futo ta tsaya jikinta duk yayi sanyi tace"Ammi don Allah kar Ku tafi kinji." Murya na rawa tayi maganar Ammi tace"Asalamiyya kawarki na nema ta jawo mans abun magana a gari game da wannan yaron taki ta rabu dashi." Asalamiyya tace"Ammi kuyi hakuri don Allah Wallahi ni banga aibun sa ba mutumin da yake da farin jini kuma yana da kirki kawai dai baku fahimce shi ba." Ummansu tace "rufe min baki shashasha dama ai baza Ku gane abunda ake nuna muku ba sai Abu ya faru kizo kuna da kun sani duk iyaye na K'warai baza su so yarsu ta auri irin wannan yaron ba da ya maida mutane ba a bakin komai ha nutsatstsiyar yarinya kamar Hanifa bata dace dashi ba." Asalamiyya tayi shiru tana mamakin lamarin itafa duk aibata shi da suke da fad'ar munanan halayensa bata taba gani ko taji ance gashi ya zagi wani ba ko tayiwa wata Cikin shege tun dai abunda ya faru tsakanssa da Abbu bata taba jin ance yayi wani Abu na rashin kyauta wa a gari ba amma duka sunyi masa mummunar fahimta. ta mike tana karayi wa Ummansu Asalamiyya sallama, har soro ta rakata ta dawo gidan jikinta duk a sanyaye sun Riga sun saba sosai gaskiya bataji dadin wannan Abu ba amma tana fatan haka shine alkairi.....Asalamiyya kuwa daki ta shige tana kuka sosai taji rashin dadin al'amarin sun shaku da Hanifa gashi zasu rabu da juna....... Yanda taga rana haka taga dare asubar fari suka tashi kowa Yayi wanka ya shirya tsaf Ammi ta bar mata ruwan wankanta cikin tukunya jikinta a sanyaye ta futo ta juye ruwan band'aki ta shiga ta dunga kuka na bakin ciki tana tunani an rabata da Khalid Shikkenan ita ba waya ba balle ta fada masa halin da ake ciki haka tayi wanka ta futo Ammi ta kalleta taga idonta yayi fulu-fulu gyada kanta kurrum tayi ta cigaba da hada abun Karin kummalo tana addu'ar Allah ya sa karshen abun akazo..... A gurguje suka karya Nasir da Hafiz suka dunga dibar kaya suna futa dasu bakin titi nan 'yan unguwa suka San abunda yake faruwa yara da manya duk suka tsatsya suna kallon ikon Allah surutu da kananun maganganu har cikin gidajen matan aure cewa ya shaik zai bar gari zai koma garinsu gombe saboda Khalid Mashahuri, lokacin Abbakar da Mobson suna tsaye kofar shago nan Abbakar ya fahimci a abunda yake faruwa hankali a tashe ya shifa gidansu d'akinsa ya shiga da cire wayarsa da ya jona a charge Khalid ya soma kira hannunsa sai rawa yake,,,,,, Sai biyu yana kiran wayar ana masa switch up, da sauri ya futo ya tadda Mobson zai tafi yawonsa kan mashing d'insa yace." Muje maza gidansu Khalid wayarsa a kashe take." Mobson yaja mashing da gudu suka bar gurin...... *13/1/2020* _BintuUm@rAbb@le_ [1/21, 9:45 PM] BintaUmarAbbale: _MASHAHURI_ *_Mallakar: Binta Umar_* *_Ki biya ki karanta cikin kwanciyar hankali ke kuma da kika futar da book d'in na barki da Allah!_* *08089965176* *07084653262* *0542382124....Binta Umar Gt bank* *50* Haruna na tsaye a gefan titi ya hangi tawowar Hanifa da sauri ya fara Tarar me abun hawa tana karasowa ta shiga shima ya shiga suka bar gurin.... Sai da sukayi nisa sosai diraban yace." Ina zan kai Ku."? Kai tsaye Haruna yace."kai mu tasha da sauri." Mai a dai-dai ta ya kara gudu minti goma KACAL ta kaisu tashar garin.... Suka futo Haruna ya futo da kudi ya bashi hakkinsa sannan suka shiga cikin tashar sosai gurin da ake lodin motar kano suka nufa cikin sa'a saura mutum uku ta cika suna zama da minti biyar wani ya shigo mota ta shi. Sai da sukayi nisa da tafiya ne ta dunga jin gabanta na fad'uwa Abbu da Ammi ta tuno tana tunanin Idan suka gane guduwa tayi ya zasu ji a ransu? Wasu siraran hawaye ta goge tayi kasa da kanta don kar mutanan dake cikin motar su fuskanci wani abun, Haruna na gaban mota kusa da direba shiyasa bai san wainar da take toya ba, haka sukayi ta tafiya kan titi kowa na abunda ya dame shi Hanifa kam gabanta ne yake wata irin fad'uwa haka dai har suka isa kano ta dabo tumbin gwiwa kano ko da me kazo an fika. Suna sauka a mota Haruna yace.'' Yanzu Kai tsaye inda yake zamu nema ina fatan kin San gidansu ko."!? Daga kai tayi jikinta duk yayi sanyi yace." Naga kinyi sanyi ki kwantar da hankali ki duk abunda kike tsammanin zai faru a gida Dole ya faru amma da anyi kwanaki zai wuce sai ki zo ki basu hakuri kawai amma hakan da kikayi shine mafuta a rayuwar ki suma baza su gane ba sai nan gaba." Ita dai shiru tayi tana addu'a cikin zuciyarta Dan sahu ya tsare ya kalleta tare da fadin"Wace unguwa ce.? A hankali tace"Shagari quetars ne ." Haruna yace." Shiga muje." Shiga tayi ta zauna jikinta a sanyaye.... Suka tafi. Tunda suka doshi layin gidansu Khalid din gabanta yake wata irin fad'uwa aikuwa gate din taga an bude wata 'bakar mota ta futo a guje motar irin tintc din na ce yasa bata gane ko wane a ciki ba, shima Khalid dake hankalinsa ba a jikinsa yake ba yasa bai gane komai ba, motar tabi da kallo nan ta gane tashi ce domin wataran yana zuwa unguwar su da ita, da sauri tace." Ya Haruna gashi can cikin mota da alama futa zaiyi." Haruna ya futo da sauri kamar zai bi motar da gudu ta Riga tayi musu nisa.... Gurin me gadin ya nufa yace"Yallab'ai don Allah bani numbar Mashahuri zamuyi magana dashi." Kallon banza ya watsa masa ya rufe gate din... Haruna ya saki baki cike da mamaki.... Komawa yayi ya sallami mai Dan sahun yana fad'in "Ai tunda munzo munyi mai wuyar insha Allah zamu samu Wanda zai bamu numbar shi, tsayawa sukayi jikin gate din suna raba ido. Khalid kuwa da shiri ya futa kai tsaye gidansu Abbakar ya nufa lokacin suma sun shirya suna jiran zuwanshi..... Yana parking ne ya shafa jikinshi yaji babu waya takaici ya ishe shi dole tasa ya juyar da mota domin ya koma ya dauko bazai iya tafiya ya bar wayar ba saboda pictures din da yayiwa Hanifa lokacin da taje gidansu tana dashi yake so yayi amfani gurin bunkicen inda suke...... Tun daga nesa yaga kamar idonsa ne yake masa gizo hannunsa da yake draving ya kama rawa da sauri ya figi motar ya ci wani irin burki a gaban su so yake kurrum ya tabbatar IRA dince ko kuma dai ta soma yi masa gizo Haruna na ganinshi ya futo daga cikin mota ya sauke a jiyar zuciya da har ya fara tunanin mafuta domin so yake ya koma da wuri don kar mutanan gidan su farga kuma suga bayanan zasu zarge shi..... Hanifa ganin ya nufo ta gadan-gadan yasa tayi saurin tsuguwa tana dukunkune jikinta da hijab yana zuwa ya d'aga da duka hannuwansa biyu ya hau tatta'ba fuskarta yana fadin"Beb kece ko kuma idona ne yake min gizo."!? Haruna ya karaso gurin fuskarsa a sake yace."itace ranka shi Dade." Haruna ya kalla da mamaki a fuskarsa yace." Ina ka samo min ita."!? Dariya Haruna yayi yana jin wani irin nishadi yau gashi suna magana da Mashahuri yace." Ni din ai yayan ta tana a matsayin kanwata ne."! Khalid ya saki kafad'un Hanifa ya rungume Haruna yana fad'in "Gaskiya bazan taba mancewa da Kai ba a rayuwata me kake so nayi maka ka fade shi kome nene kar Kayi shakka." Haruna yace." Ranka ya Dade bana bukatar komai a gareka ganin da nayi maka ta sanadiyar Hanifa ya gamshe ni Hak'ika naji dadin Wannan alakar taku kai dai ita shiyasa nayi ruwa nayi tsaki gurin ganin burunku ya cika gobe ne suke shirin d'aura mata aure shine na kawota Ku samawa kanku mafuta. " Khalid yaji wani irin cikin ransa wato da sai da suje suji mummunan labari Shaik ya daura mata aure da wani.... Kansa kawai yake gyadawa yana godewa Allah cikin zuciyarsa hannunta ya rike ana shi yana murzawa ya kalli Haruna tare da fadin "Mu shiga ciki kaci abunci ka huta ko kayi kokari kuma kayi jihadi." Haruna yayi dariya tare da fadin "Ai kar ka damu kawai na hango cancantar ka da ita ne shiyasa nayi Wannan abun." Shiru Khalid din yayi duk hankalinsa na kan Hanifar yana kallon yanda duk idonta ya zurma duk tayi wani firi-firi da ita sosai ta bashi tausayi yana ji kamar ya dauketa haka suka shiga cikin gidan kafadarta na gogar tashi kai tsaye part din Mamy ya nufa dasu kana kallonsa kasan yana cikin farin ciki yaga muradi na zuciyarsa Hanifa. Daf da zasu shiga ciki ne Hanifa taja tunga ta tsaya tana matse ido kallonta yayi yana marairaice fuska yace." Menene. "!? A hankali tace" Ina jin tsoron shigane."! Yace." Kar ki damu babu abunda zai faru Insha Allah Mamy zata karb'e ki hannu biyu." D'ago kanta tayi tana kallon Haruna da ya zuba musu ido yana mamakin yanda suke kaunar juna yace." Ki shiga mana babu abunda zai faru kamar yanda oga ya fada." Hannunta dake cikin NASA ta cire ta kudunfune su cikin hijab tana jin tsoron haduwarta da mahaifiyar sa tasan bata kaunarta duk da batayi wannan tunanin ba sai yanzu.... A langabe yace." Beb ki nutsu babu fa wani damuwa insha Allah kin shigo cikin family me kyau." Tana kokarin b'oye hawayen ta tace" muje to." Hannunta dai yake so ya rike ta hana haka suka shiga yana ta faman kallonta kamar zai cinye ta sai magana yake mata k'asa-kasa. Mamy na sama lokacin da suka, zama ma bai bari tayi da kanta na shi ya zaunar da ita kan kujera, ita kam kunyar abunda yake mata take ji ga Haruna yana kallo, batasan Haruna yana daukar darasi bane..... Yace." Mamy na sama bari in kirata ko."? Kai ta daga masa da sauri ya tafi yana waiwayen ta ita kanta sai mamakin rawar jikin da yake mata take. Mamy na shirin saukowa ya shiga dakin tace"Myson meye na ganka duk a furgice." Muryarsa na Dan rawa yace." Mamy gashi can na kawo miki Hanifa please Mamy don Allah kar ki nuna mata wani Abu Mamy in dai kina son walwata da farin cikina to ki kula min Hanifa kafin in samu mafuta." Kallonsa tayi da mamaki tace"Myson bangane ba kana nufin gombe din kaje ka dauko ta ko kuwa."? Girgiza kansa yayi yace." Mamy yarinyar ce ta kawo kanta da kanta tare da yayanta wai gobe za'a d'aura mata aure da wani shine tazo gurina muyi aure." Mamy taji kanta ya kulle tana mamakin anya yarinyar nan kuwa na da hankali! Namiji tabi ta gudarwa iyayenta kawai saboda soyayya lallai akwai alamun tambaya kan yayan NATA domin idan uwarsu daya ubansu daya da ita bazai goyi da bayan abunda zatayi ba.... Saboda samun nutsuwar yaron NATA tace"Muje kasa gurin su amma Myson nayi mamakin wannan al'amari" yace." Mamy yarinyar tana na ina sonta ubanta ya shiga tsakani." Takaici bai bar Mamy tace komai ba suka sauka 'kasa. Hanifa na hango isowar momy gurin ta sunkuyar da kanta kasa gabanta sai fad'uwa yake, Mamy ta zauna kan kujerar da take fuskantar su fuskarta a Dan sake take amsa gaisuwar Haruna tana tambayar sa mutan gida Haruna yace." Kowa lafiya lau. Sakkowa tayi kasa ta durkusa murya a sanyaye tace"Mamy ina yini."!? Mamy tace"lafiya Lou ya kika bar mutanan gida."!? Murya na rawa tace"Sunan lafiya Lou." Shiru parlor yayi mamy duk ta rasa me zatayi babu abunda take mamaki sai irin gangancin da yarinyar tayi gaskiya ba matar aure bace tunda zata bujere ma iyayaenta saboda son zuciyarta. Khalid kuwa no din dady dinshi yake kira so yake kawai ayi wacce za'ayi tun kafin su Shaik su Ankara da abunda yake faruwa an d'aura masa aure da ita. Mai aiki ce ta shigo parlor ganin baki yasa ta koma kicin din ta hado musu abinci da abun sha , ta jera kam centar table din dake gabansu Mamy ta mike ta haye sama zuciyarta na zafi ganin yanda Khalid din yake ta rawar jiki akan yarinyar.... Haruna ya had'a abinci Yana ci a gurguje ya kammala ya goge bakinsa yana kallon Khalid din dake jikin Hanifa a ma'ke duk ya dagula mata lissafi sai matsawa take yana kara nanikar ta yace." Oga ni zan tafi bana so iyayen mu su farga da al'amari suga bananan nasan zasu zargi wani Abu." Khalid ya gyara zaman sa sosai yace." Ka bari dad ya dawo mana Yana kan hanya Insha Allah. " Haruna yace." Ka mik'a min gaisuwa ta gurinsa insha Allah zan kawo muku ziyara kuma ina muku fatan samun albarka cikin auran Ku." Khalid ya mike daga inda yake yana fadin"muje in kai ka shiga mota insha Allah zan neme ka idan kura ta lafa ka bani numbar wayark." Nan sukayi musayen numbar Hanifa na kallonsu hawaye na zuba a idonta murya na rawa tace"Ya Haruna idan kaje ka bawa Abbu da Ammi hakuri don Allah kace kar su kullace ni." Haruna yace." Na fada miki ki daina wannan koke koken da kikeyi komai yayi farko yana da k'arshe Insha Allah kome zaizo da sauk'i." Haka dai ya lallab'ata suka kama hanyar futa da sauri ta mike ta biyo bayansu... Khalid ya juyo yana mata wani irin kallo yace." Ki koma ki zauna Zan dawo yanzu." Tace"Muje in raka ko." Tunani yayi cikin ransa kar ta bujire idan sun je gurin shiga mota tace sai ta koma yasa ya jawo ta jikinsa da sauri ya rungume ta tsam-tsam a jikinsa yana rarrashinta Haruna yayi saurin futa ganin abunda yafi k'arfin idonsa, Mamy na kokarin saukowa ta hango abunda yake faruwa da sauri ta koma cikin d'akinta tana mamakin halin Khalid din bashi da kunya ko kadan da kuma ita yarinyar da bata da kamun kai a gidansu saurayi take bari yana taba mata jikinta ita kam da tana da yanda zatayi da ta hana auran nan jira zuwan Dady take taji wane irin hukunci zai yanks tasan dai zai bi son zuciyarsa ne da kuma ra'ayin dansa. [1/19, 10:02 AM] .: Da kyar ya samu ta hak'ura ya zaunar da ita kan kujera ya futa da sauri. Part dinsa ya nufa minti biyar ya futo Haruna na tsaye na jiransa yace." Haruna muje kasan motar ma a waje na barta saboda farin ciki." Tare suka jera Haruna sai murmushi yake. Kudin mota guda Khalid ya biya domin baya son a tsaya Lodi ya futo da kudi ta bawa diraba Wanda suka fi kudinsa, Haruna ya mik'awa wata fararar ta karda kana ganinta kasan kudi ne a ciki tunda ga alamarsu nan Haruna ya karba yana godiya Khalid bai bar gurin ba sai da yaga motar ta tashi sannan ya nufi inda yayi parking din tashi ya nufi gidan..... Daf da zai shiga gidane wayar shi ta fara kara yana dubawa yaga Mobson dariya yayi ya daga wayar. Mobson yace." Guy ka barmu muna jira tun dazu Allah yasa lafiya dai." Khalid ya sauke ajiyar zuciya yana shafa sumar kansa yace." Mobson Allah ya gajarta mana wahala Yanzu haka yarinyar nan na hannuna ta kawo kanta." Mobson ya kalli Abbakar dake zaune kusa da cikin mamaki.! **** Tsumu tayi a parlor sai kalle kale take tana kallon yanda me aiki take shige da fuce tana aikace aikacen ta bata ce mata komai ba ita ma haka, motsin taji daga sama taga mamy na kokarin saukowa gabanta ya fadi da sauri tayi kasa da kanta.... Mamy ta karaso tsakiyar parlor tana kwala wa mai aiki kira ta futo da sauri tana fadin"Hajiya gani." Mamy tace"Ki kwashe Wannan kayan abinci ki gyara gurin dady na kan hanya."! Dayyiba me aiki tace"Hajiya naga bakuwar bataci abinci bane."! Momy ta nemi guri ta zauna tana fad'in "Kiyi abunda nace miki kawai." Dayyiba ta fara dibar kayan abincin tana shiga kicin dasu, Mamy ko kallon inda Hanifa take zaune bata yi ba ta kunna TV tana kalle-kallenta...... Minti goma tsakani Alhaji Tijjani ya shigo parlor k'amshin turarasa ya cika gurin Hanifa kanta a kasa take masa sannu da zuwa ya tsaya yana amsawa gami da nazarinta wucewa yayi ciki sosai mamy ta karb'i jakar hannunsa tana masa barka da zuwa ya amsa sama-sama yana tambayar ta Hanifa. ? A cunkushe tace"Myson ne ya kawota ya aje ni baiyi min bayanin komai ba amma dai yanzu zai shigo gidan." Kallon gefen da Hanifa take zaune yayi na minti biyu kafin ya dauke kansa ya nufi sama Mamy ta bishi a baya..... Suka bar Hanifa ita daya a parlor jikinta duk yayi sanyi amma har yanzu batayi na damar abunda tayi ba kamar yanda Haruna ya fada cewa komai zai wuce Insha Allah tana fatan komai din ya wuce tasan dama dole zata fuskanci matsala daga gurin mahaifiyar sa ita a ganinta Wannan ba damuwa bace tunda Khalid din yana sonta.. *19/1/2020* _BintuUm@rAbb@le_ [1/21, 9:46 PM] BintaUmarAbbale: _MASHAHURI!!_ _*Ki biya ki karanta cikin kwanciyar hankali, ke kuma da kika futar min da book na barki da Allah!.*_ *08089965176* *07084653262* *0542382124....... Binta Umar Gt bank* *52* Sama-sama Mamy ta amsa gaisuwarta ta cigaba da abunda takeyi Alhji Tijjani ya sakko cikin shiri yaci wata Uwar shadda me mugun tsada dinki babbar Riga da yar ciki sai kamshi ne yake tashi a gurin. Kana kallonsa kasan alhaji ne Wanda yaci ya tada Kai da kudi, bakin daining din ya tsaya yana gyara agogonsa har kasa ta durkusa tana gaishe shi ya saki fuskarsa sosai yana amsawa Mamy ya kalla da tayi kicin_kicin da fuska yace." Ki kawo min abinci parlor." Wucewa yayi Mamy ta hada masa break fast din ta dauka duk zuciyarta babu dad'i jiya kwana sukayi ita dashi suna rigima kan auran tace ita bata so shi kuma yace tunda yaro yana so sai anyi shine zai shige masa gaba kan komai kuma idan tayi wani abun da ya tada hankalin Khalid din to ranta sai ya 'baci..... Tun safe ta kira aminyarta Hajiya Zainab mahaifiyar Nasrin kenan tana so tazo suyi shawarar meye mafuta.... Hanifa cin abincin take sama-sama ta tsame hannunta tana kokarin tashi daga gurin ne ya shigo parlor saurin sunkuyar da kanta tayi gabanta na fad'uwa ganin wani irin kyau da yayi ya futo ango sak yana sanye da irin shaddar dake jikin dady nashi babbar Riga da yar ciki har dinki ma iri daya ne sai zuba kamshi yake ya Dora hula saman lafiyayyar sumar sa sai shek'i take. Ka tsaye inda take ya nufa... Cikin yanayin muryarsa yace." Ga naki kayan kije kiyi wanka ke kadai muke jira." Dago kanta tayi ta fara kwal-kwal hawaye na so ya zubo yayi sauri kauda kansa daga gareta a hankali tace"Nifa nace bazani koto ba." Cikin wani irin yanayi yake kallonta yace." OK ya kike so ayi Yanzu nifa yau din nan nake so a d'aura mana aure na shirya tafiya ta Monday komai nayi miki na tafiyar baza ki rusa min tsari ba." Tana share hawaye tace." Kawai a d'aura a gida.. Kallonta yayi na minti biyu kafin ya bar gurin. Can parlor ya nufa ya zauna kusa da dady nashi yana dafe kansa. Alhji Tijjani yace." Ya akayi ne ango. " bata fuska yayi yace"Dady yarinyar naso ta bamu matsala wai bata so aje koto." Murmushi Alhaji Tijjani yayi yana kurbar tea a hankali yace." Son yarinyar nan na lura tana kaunar mahaifinta gashi shi kuma baya kaunar ta don da yana kaunarta zai so abunda take so kamar yanda nake son abunda kake so, kasan abunda yasa bata so aje koto."!? Girgiza kai yayi cikin damuwa. Yace." Tana jin tsoro ne alkali ya bukaci ganin mahaifinta ni na gane." Khalid ya sauke ajiyar zuciya da damuwa a fuskarsa yace." Dady meye abunyi yanzu."? Kar ka damu insha Allah da an sako daga sallahr jama'a za'a d'aura auran Ku a massalaci tunda bata so aje koto Alhaji Lawan zai zama waliyinta insha Allah, duk dai bai San abunda yake faruwa ba zan masa bayanin. Komai insha Alla." Ajiyar zuciya ya sauke hade da kwanciya kan kujerar so kawai yake yaga an d'aura auran yasan dai ko menene zai biyo baya mai sauki ne idonsa ya bude a hankali yake bin Mamynshi da kallo wacce take kokarin barin gurin ya lura tunda ya kawo hanifa gidan take sha masa kamshi to koma dai menene zai lallab'ata har ta huce fushinta. *** B'angaran su Abbu komai ya tafi dai-dai an d'aura auran Nasiru da Wasila cikin amunce kome Abbu yake yanayin sa ne cikin tawakalli da mik'awa Allah lamuransa haka ya dunga hidima da jama'a har taro ya watse mutane yan Gaza gani suyi shiru suka dunga yi kasa jaje da abunda ya faru tunda gari ya dauka cewar yarinyar shi ta gudu haka dai yake kokarin danne damuwar sa har taro ya watse Nasiru kam sabgar gabansa yake don sai ka rantse da Allah bai taba cewa yana son Hanifa yaji zugar jama'ar gari da suke fadin "Kawai ya watsar da yarinyar tunda bata da tarbiyya watak'ila ma za'a iya yin auran ta kasheshi tunda bata sonsa wannan kallma ta bashi tsoro sosai don haka sai ya watsar da lamarin hanifa ya shiga hada hada da jama'a wato dai Wanda Abu ya shafa shi ya shafa, haka cikin gidan ma ko ina ka zauna zancan kenan mata da cancana magana masu zagin Hanifa nayi da fadin" Taje duniya ce zata koya mata hankali masu hankalin cikinsu kuwa fadi suke rayuwace ita haka kaddararta take amma gaskiya masu zaginta sun fi yawa, da gayya suka dunga shiga shashen Ammi suna yi mata jaje sai su fake da cewar Allah sanya alkairi suka shigo yi mata, ita dai haka ta daure tana Amsar baki tare da 'yan uwanta amma fa da zaka tona zuciyarta a lokacin ganin b'acin ran da take ciki sai ka tausaya mata. **** Alhji Tijjani yayi jiran zuwan Abokinsa Alhji Lawan Wanda yake so ya karb'i waliccin Hanifa to har aka idar da sallahr juma'a bai samu isowa ba,,, haka ya hak'ura Alhji Bilya ya karb'i wallicin Khalid maimartaba da bai San abunda yake faruwa ba ya karb'i wallicin Hanifa aka d'aura aure kan sadaki dubu Dari biyu nan sarki yayi addu'a kowa ya shaida d'aurin aure aka shiga raba goro da alawa, Maimartaba ya damk'a kudin sadaki hannun Khalid tare da umartarsa ya baiwa matarsa hannu da hannu Khalid na karba suka bar gurin shi da abokansa da suka zame masa garkuwa.... Mota suka shiga cikin farin ciki suka nufi studio yau wa'kar da zai saki ta mussamance. _Khalid kenan kanwa takar tsami kwarnafi ya kwana_ *** Alhaji Tijjani shi da Alhji bilya a gefe guda suna tattaunawa game da yanda Al'amarin ya kasance Alh bilya yace." Abunda Kayi shine dai-dai tunda dai yarinyar ita ta kawo kanta in banda abun Khalid ma nace yaje gurina ya duba mata ya'ki babu laifi hakan ko yau yayi niyyar kara ta biyu zai iya zuwa ya duba cikin yarana insha Allah. " Alhji Tijjani yayi godiya da jin abunda yace to suna kokarin rabuwa ne Alhaji Lawan ya iso gurin gaisawa sukayi cikin mutumci Alhji Lawan yace." Tum kafin in iso nan ake tayi min murna Khalid ya daura aure hakane." Alhji Tijjani yace." K'warai kuwa tun safe nake Neman wayarka a kashe nace ko madam ce ta hana daukar wayane."? Dariya Alhji Lawan yayi yace. " ko daya yau ns yini ina bacci ne a gida gashi ban samu sallah ba." Alhji Tijjani ya shiga warware masa duk abunda ya faru.... Ransa a Dan bace yace." Alhji wannan abunda da kukayi gaskiya bai dace ba, kuma ni banji dadin sa ba tun farko idan nasan abunda yake faruwa bazan bari a d'aura auran nan bata da sanin mahaifin yarinyar nan ba, dole zan dauketa in kaita har gabansa in nuna masa illahar abunda ya aikata itama in nuna mata kuskuranta na aikata haka nasan zaiji kunya kuma zai amunce da bukatar mu saboda abunda yarinyar tayi amma a d'aura aure kai tsaye ba tare da ya sani ba akwai ciwo a ciki." Alhji Tijjani yace." Kasan fa taurin kan mutumin nan Alhaji wallahi zamu iya zuwa har garin ya nuna bai yarda ba ni a ganina d'aura musu auran shi yafi cancanta gudun haihuwar d'a Mara ido saboda haka ka rabu dashi kawai ina ganin duk abunda ya faru shine jawa kanshi. " Alhji Lawan yace." Dole gobe mu shirya zuwa garin tare da yarinyar domin ta nemi gafarar iyayenta abunda tayi aure dai an Riga an d'aura shi Allah ya basu zaman lafiya amma banji dadin yanda ya kasance ba." Alhji Tijjani yace." Wannan karon sai dai Kai kaje domin ni!! Bazanje gurin talaka kamar wannan mutumin ba ina rokonsa Abu yana nuna min iko aure da yarshi an d'aura sai ya barwa Allah kawai." Alhji bilya Wanda tunda suka fara maganar baice komai ba yace." K'warai kuwa wannan magana itace dai-dai Alhji su talakawan nan ka sake ka basu fuska sai su raina ka, kawai ka kyaleshi da an kwana biyu magana zata wuce." Kallonsu yayi yana mamakin maganar su kullum maganar su kan talaka take sun ki su gane cewar mai kudi da talaka duka Allah ne ya hallice su ba da wata manufa ba, duk sun da yaso zai iya kwace kudin ya mai dakai talaka ya damka kudin hannun talaka da kake rainawa su har yanzu sun kasa gane haka sai suke ganin kamar iyawarsu ce.... Ranshi a bace yayi musu sallama ya barsu gurin *** Hanifa zaune a cikin bedroom din da ta kwanta jiya taci kukanta ta koshi tunda taga k'arfe biyu ha wuce ta sannan an Riga an gama d'aurin aure kafin ya futa ya fada mata cewar bayan sallahr juma'a za'a d'aura auran kuka take yi tana sharbe majina zuciyarta Sam ta kasa nutsuwa guri daya sai wasi wasi take mata tana tunanin anya abunda tayiwa iyayenta ya dace shin ko yanzu wane irin hali suke ciki tasan dai duka zuciyoyin su babu dad'i tana nan zaune tana sake-sake taji hayani daga parlor shiru tayi gabanta ns fad'uwa jin kamar ana kokarin bude kofar dakin da take ne yasa tayi saurin rufe jikinta da hijab har fuskarta tana ji aka bude dakin aka shigo tare da sallama.... *21/12020* _BintuUm@rAbb@le_ [1/22, 10:59 AM] BintaUmarAbbale: _MASHAHURI!!_ _*Ki biya ki karanta cikin kwanciyar hankali, ke kuma da kika futar min da book na barki da Allah!.*_ *08089965176* *07084653262* *0542382124....... Binta Umar Gt bank* *53* Hafiza da Kalisat suka shiga dakin kai tsaye inda take zaune suka nufa, Hafiza tace "Amrya gamu munzo siyan baki ki bude idonki mu gani mune mazajen ai." Jin muryar me magana yasa ta gane ko wacece sistar dinsa ce ajiyar zuciya ta sauke ta bude fuskarta a hankali suka hada ido da juna.... Kalisat tayi murmushi a hankali tace"Sannu kinji taso muje parlor ga me lallai na dauko miki ta gyara ki." Hanifa taji wani irin sonta cikin zuciyarta ta lura sistars dinsa suna da saukin kai... A hankali tace"Ina wununku." Suka amsa mata fuska a sake, Hafiza tace"Muje parlor kin zama yar gida ki daina takure kanki a daki mu muna da saukin kai karki damu abunda brother dinmu ke so muma shi muke so." Tace"Nagode Allah ya saka da alkairi. Hafiza ta rike hannunta suka futa parlor Mamy da Hjy Zainab suna zaune parlor suna shira Mamy tayi saurin kauda kanta tana Dan Jan tsaki cigaba da magarta tayi ita kuwa Hjy Zainab na can tana kallon Hanifa tana mamaki kyawun yarinyar lallai dole yaron ya gigice. Har inda suke hanifa taje ta tsuguna tana gaishe su.... Hjy Zainab ta amsa babu yabo babu fallasa ita kuwa mamy kam dauke kanta tayi tana magana da Khalisat, jiki a sanyaye ta mike ta bar gurin.... Mai lallai ta hada komai Hanifa ta zauna ta fara zana mata k'afafu da hannu abunda da lafiyayyar farar fata take kunshin ya futo yayi kyau sosai. Mamy kuwa da kawarta bar parlor sukayi sama suka nufa suka cigaba da zancan su suna ta aibata Hanifa mamy taki gane cewa komai Allah ya kaddara sai ya faru to sai ya faru ita kuma Hjy Zainab dole ta biye mata tunda tana so ya auri yarta. **** Muryarahi take tashi cikin wa'kar shi me taken *Alk'awarin ya cika* *"Alk'awari ya cika yau na zama ango ga Hanifa."💗* *Alk'awari ya cika yau na zama jigo ga Hanifa."💓* *"Alk'awari ya cika Hanifa ta zama Mallaki na!"💜* *"Yau ango nake ni Khalid na tsinci dami a kala Hanifa ta zama mallaki na🖤* *"Alk'awarin Allah ya cika Hanifa da Khalid sun mallaki juna soyayya ruwan Zuma mai harbin Wanda ke adawa da hakan shine dan asara!* *"Alk'awari ya cika! Yau na auri Hanifa babu ni babu asara!* *"Hanifa da Khalid alk'awarin Allah ne....!* Yanda yake sakin baitukan zaka San da biyu yake kuma muryarsa a sama yana cikin farin ciki ya Kai karshen wa'kar tashi ta *Alk'awarin Allah* take su Mobson suka shiga tace komai suka sake ta a gari. *** A gajiye ya isa gida kai tsaye part din iyayen nasa ya nufa tun kafin ya shiga ya jiyo hayaniyar su Hafiza tsaki yaja ya bude kofar da sallama a bakinsa, Khalisat ce ta amsa, babbar rigar sa dake hannunsa ita ya jefar kan kujera ya cire hular ma ya aje, zama yayi cikin kujera cikin gajiya... Hafiza tace"Ango manya." Bude idonsa yayi ya kalleta dauke idonsa yayi ya mayar kan Hanifa dake takure guri guda, k'afafunta yake bi da kallo... Hafiza ya kalla fuskarsa a hade yace." Waye yasa kukayi mata wannan abun. "!? Hafiza ta harare shi ranta a dan bace tace"Wato nice marainyar wayon ko.? Zaka tsare ni da ido kana tambaya." Bata fuska yayi yace." Nifa bana son shouting kawai na tambaye ki ne." Khalisat tace"Nice na dauko me lalle tayi mata Kai ma kafi jin dadin kallon amaryarta ka.". No Aunty bana son wannan abun wallahi." Ya fada tsakaninsa da Allah. Tace"Aikuwa kwalliya ce gashi kuma amaryar taka tana da kyawun fata dubi yanda lallan yayi mata kyau... Yace." Aunt Dan dai kece fa da wancan ne da sai munyi fada da ita ni nafi son ganin skin dinta haka yafi min kyau." Khalisat tace"E lallai yau naji dad'i har aunt ake kirana nagode kanina." Dariya yayi ya saci kallon Hanifa had'iye yau yayi ya lumshe idonsa cikin zuciyarsa yake fadin yau dai zan kewar da wannan masifar na huta.... Mamy ce ta sakko ita da kawarta Hjy Zainab ta tsaya tana tsokanar sa shi dai murmushi yake mamy ta bar gurin can bakin kofar futa ta nufa tana jiran kawarta ta, duka sun fuskanci yanayin mahaifiyar tasu sai jikinsu yayi sanyi mussaman uban gayyar yana son mahaifiyar sa saboda yanda take sonshi cikin yayanta dole ya rarrasheta ya lura taki sakin jiki dashi har yanzu Mamy nayi sallama da kawarta ta wuce sama ba tare da ta kalli inda suke ba. Mik'ewa yayi ya bi bayanta tana zaune gefen bed ya shiga dauke kanta tayi daga kansa ya karaso kusa da ita zubewa yayi gabanta ya kamo hannunta ya rike yana marairaice fuskarsa." Tace"Meye haka zaka zauna min a gaba."! Cikin shagwaba yace" Mamy naga sai shareni kikeyi menene."!? Tsaki taja tace"Myson menene kuwa, ba dai kun hada baki da ubanka kuna yi min abunda kuke so ba babu komai ai." Shiru yayi yana tunani yace." Mamy kiyu hkari don Allah ki barwa Allah lamarinsa ki duba ki gani kafin na samu yarinyar nan sai da na cire tsammani don Allah ki sanyawa abun albarka." Banza tayi masa tana dauke fuskarta, yace." Mamy pls mana."! Kallonsa tayi ya bata tausayi amma tana jin baza ta fasa nata kudirin ba tace"Idan kana so na yafe maka to nima zaka yi min alk'awari daya." Yace." Mamy wane alk'awari ne ki fada kawai kin wuce komai a gurina ni dai ki kaunaci Hanifa shine burina." Tace"Ai nace magana ta wuce nima ina so ka auri Nasrin d'iyar kawata ." Khalid bai taba tsammanin wannan maganar zatayi masa ba yace." Mamy wannan ne alk'awari. " tace"Shine." Shikkenan nayi alk'awari. " kansa ta dafa fuskarta a sake tace"Allah yayi maka albarka ya baka ikon zama dasu cikin aminci yayi maka jagora babu dad'i cikin zuciyarsa yace." Mamy na, tace"Bana so a dauki dogon lokaci don gaskiya ina so in fara ganin yayanka da wuri...." Ta fada da murmushi a fuskarta. Ji yayi kamar ta buga masa guduma akansa shine zai haihu yanzu tabbas Mamy bata San yanda ya'ki jinin haihuwa ba shiyasa take wannan zancan idan Dan ya haihu ne yasa tace ya auri Nasrin to bazai taba haihu da ita ba wallahi shiru kawai yayi mata ita kuma ta cigaba da fadin"Yarinya mai addini kuma me tarbiyya shiyasa nake so zuriarka ta futo ta tsatsonta ni wannan yarinyar daka aura bana son hada jini da ita wallahi." Murmushi kawai yayi cikin zuciyarsa yake fadin"Mamy ki daina wani zabe-zabe dukansu babu wacce nake bukatar haihuwa da ita a yanzu sai dai ko a gaba. Tace"Da so nake zuwa karshen wata a kai kudi da sadaki." Yace." Mamy kin sani zamu tafi america ko, don tun satin da ya wuce naso naje dalilin wannan al'amarin na daga tafiyar ina so mu tafi da hanifa ne." Tace"To ai tafiyar ka baza ta hana komai ba zaka kai sati nawa. " shiru yayi yana tunani Yana so ya huta sosai a can yaci amarcinsa yanda ya kamata domin su Sonop sunyi masa tanadin komai jiran zuwansa suke kuma sun San tare da wife dinsa zaizo. Yace." Mamy ban tsaida ranar dawowa ba amma kome ake bukata na Neman aure ayi kawai ni lamunce insha Allah in na dawo sai ayi komai." Tace." To shikkenan myson ina jin tsoron fad'an dady Ku wallahi." Mamy ki dashi zanyi masa bayanin komai. " tace." To shikkenan. " Sakin jiki tayi suka dunga hira har lokacin sallahr magariba Khalisat da Hafiza suka hau saman domin yin sallah da kuma shirin tafiya... Ganinsu su kadai yace." Ina Hany din." Hafiza tace"babu yanda bamu yi da ita ba taki jawowa na lura tana da kunya gaskiya." Mamy ta tab'e bakinta, shi kuma ya mike ya sauka 'kasa, bata parlor Kai tsaye bedroom din da ya fahimci tana ciki ya nufa, yana shiga ita kuma tana kokarin shiga toilet. Sai ta tsaya tare da sunkuyar da kanta Cikin yanayin tafiyar shi ya karasa kusa da ita yayi mata rumfa da k'irjinsa me fadin gaske jingina tayi jikin bango (garo) tana kifta ido tsura mata idonsa yayi yana kallon yanda gashin idonta yake motsi fuskarta ya kamo da hannunsa ya tsurawa le'bunanta ido lips dinshi ya tura a bakinsa ya Dan ciza a hankali ya fara sakin wa'kar shi ta *Alk'awarin Allah ya cika* hanifa ta tsira masa idonta tana kallon yanda bakinsa yake fidda sautin wa'kar tanayi mata dad'i sosai sai lumshe ido take, sai da ya kai geji sannan ya sauke ajiyar zuciya da muryarsa mai mutukar kashe mata jiki yace." Ya kikaji wa'kar."! Tayi dad'i " ta fada a hankali murmushi ya saki ya fara matso da fuskarsa kusa da tata, cigaba tayi da kifta ido tana kauda fuskarta da take rike a hannunsa hade k'irjinsa yayi da nata ya danne jikin bango taushin Brest dinta suka sanya ya sauke ajiyar zuciya bakinta yake kokarin kamawa da nasa ita kuma tana kauda kanta a hankali yace." Ki bani na tsotsa kinji ko." Girgiza kanta tayi yace." Me yasa ? A hankali tace " lokacin sallah ne kaje Kayi sallah." A kasalance yace." Bazan iya kome ba idan ban sha ba." Salon yanda yake maganar ya kashe mata jiki sosai ga masifaffan k'amshin tura ransa na kassarata, kasa tayi da idonta itama tana bukatar hakan to tasan halinsa bataso abun yayi nisa kuma bata so yayi mata fushi irin na jiya kawai ta k'yale shi ya fara bin fuskarta yana lashewa da harshen shi har yazo bakinta ya duna yi masa wata irin tsotsa ta futar hankali yanayi yana ya mutsa mata jiki gami da murza mata Brest duk ya futa daga hayyacin sa, daukarta yayi ya dure ta kan bed a d'imauce ya haye kanta yana sakin nishi bakin NATA yake kokarin cafkowa a karo na biyu sai ta fashe masa da kuka tana ture shi daga jikinsa take fadin"Ka bari haka le'bena zafi wallahi gashi kuma lokacin sallah zai wuce." A hargitse yace." Bai ishe ni ba ki bari nasha na gamsu pls beb."!!! Murya a sark'e ya fad'i maganar da k'arfi ta ture shi ya fad'i kan bed abunka da dama jiki ya saki... Ta sauka 'kasa taja gyara rigarta da ya d'age mata sama toilet ta nufa da sauri. Shi kuwa rike mararshi yayi yana rintse idonsa jin wani irin murdawa Da tayi da kyar ya mi'ke ya bita toilet din.. *22/1/2020* _BintuUm@rAbb@le_ [1/23, 11:38 AM] BintaUmarAbbale: _MASHAHURI!!_ _*Ki biya ki karanta cikin kwanciyar hankali, ke kuma da kika futar min da book na barki da Allah!.*_ *08089965176* *07084653262* *0542382124....... Binta Umar Gt bank* *54* Kallonshi take s tsorace har ya karaso inda take tsaye sai taga ya bude famfo ya fara d'aura alwala ajiyar zuciya ta sauke don har ga Allah ta dauka wani abun zai sake yi mata juyawa tayi ta fara alwala ya rigata gamawa ya futa Yana cije lips dinshi yaci sa'a babu kowa a parlor Kai tsaye massalaci ya nufa. Tana idar da sallah ta zauna tayi shiru tunanin halin da iyayenta suke ciki take hannu ta daga sama ta fara addu'a " Ya Allah kafini sanin halin da nake ciki, ya ubangji Allah ka kawo min sauki cikin lamaruna, Allah kasa aurena da wannan bawa naka ya zama alkairi a rayuwata Allah ka sanya sanyi da kwanciyar hankali a zuciyar mahaifana Allah ka dubi zuciyata....."! Tana kuka ta 'karashe addu'ar. Kwanciya tayi hawaye na tsiyayo mata babu laifi taji saukin zuciyarta sakamakon addu'ar da tayi....... Ammi zaune a kusa da Abbu dake kwance a katifa hannunta rike da mafici tana masa fiffita Hafiz ya shigo hannunsa rike da wata Lede Haruna ya shigo tare da Musa me chamis Ammi ta mike ta shiga daki jikinta duk a sanyaye, Haruna ne ya karasa kusa da Abbu ya dago kafad'unshi yana kokarin tayar dashi zaune Musa yace." Kyaleshi a haka." Haruna ya matsa Daga gurin Musa ya fara aikinsa, hannun Abbu ya kama ya fara lalubar jijiya da kyar ya samu sai ya fara sanya masa ruwa bayan ya kammala ya kalli Hafiz a nutse yace." Yanzu zai samu baccin da ake bukata insha Allah abunda ya haddasa masa mugun ciwon kai damuwa ce da rashin bacci saboda haka Idan ya tashi Ku bashi shawarwarin kan ya cire damuwar dake ranshi saboda jininsa yana barazanar hawa a kiyaye da bata masa rai. "! Haruna yace." Insha Allah. " Musa mai Chamis ya had'a kayansa yana shirin futa Haruna ya biyashi hakkinsa suka futa tare. Inno ce ta shigo cikin dakin ta zauna gefan Abbu ganin yanda ya rame lokaci guda sai ta fashe da kuka mai sauti tana fadin"Wannan yarinya! Wannan yarinya! Anyi kafura mara tausayi nasan duk damuwar ta ce ta jawowa Munzali shiga Wannan hali ni me zanyi da Hanifa wallahi babu mu babu ita kamar yanda ta zab'i maroki to taje iyayensa su zama iyayenta amma su sun yafe ta. Ammi ma dake cikin daki hawaye take sharewa tana jin a zuciyarta babu wanda zai sanya ta ta yafewa Hanifa abunda tayi.... Hafiz yace." Ni wallahi bana so ma kuke zancanta Ku k'yaleta duniyace wallahi sai ta koya mata hankali kuma duk ranar da ta dawo tace mu yan uwanta ne sai na kusa kashe ta a gidanan taje mun barwa duniya ita." Abbu duk yana jin irin maganar da suke yaji zuciyarsa tayi rashin dad'i duka sun tsaurara kan lamarin da wannan alwashin da suke dauka kamata yayi suyi mata addu'a a duk inda take Allah ya tsareta a hankali yace." Hafiz kar nakara jin irin wannan maganar ta futo daga bakin ka, yanzu kai sai ka kashe mutum."!? Hafiz yayi shiru Abbu ya cigaba da cewa "Wannan Kalmar Sam bata dace da muminin mutum ba, sannan wannan rashin lafiyar da nakeyi ni a ganina bata da nasaba da Abunda Hanifa tayi daga Allah ne kawai har kullum inayi mata addu'a kan Allah ya tsare ta kuma ya karkato da hankalinta gida abunda ya kamata kuma kuyi kenan bana son irin wannan maganar da kuke yi a kanta." Inno tace"Wai me yasa Baka San laifin yarinyar nan ka duba fa kaga Abunda tayi maka." Murmushi yayi a hankali yace." Inno nasan Hanifa bata kyauta min ba, nayi mata uziri saboda nasan ajizanci irin na d'an Adam kuma akwai k'uruciya a tattare da ita shiyasa na YAFE mata kuma INA yi mata addu'a Allah ya shirye ta yasa tans hannu nagari." Inno tace"To kai tunda ka YAFE mu bamu yafe mata ba kuma bata da gurin zama a cikinmu taje duniya ce." Girgiza kansa yayi yana jin ciwo sosai cikin k'ashin jikinsa ga kansa dake mugun sara masa yace." Inno Hannunka fa baya rubewa ka yanke ka yar bana jin dad'i idan kika fad'i Wannan maganar wallahi. " inno ta mike a fusace take cewa"Mu kuwa wannan hannun namu mun yanke mun jefar dashi har abada." Futa tayi tana mita gami da tsinewa Hanifa kan abunda tayi. Abbu kam juyawa yayi a hankali ya lumshe idonsa yana tunanin halin rayuwar da Hanifa ta jefa kanta a ciki. *** Bacci tayi ta farka a furgice!! Shiru gidan motsin da takeji a parlor ta daina ji cikin tsoro take bin dakin da kallo ta kalli agogon dake manne a bango k'arfe 12:30 na dare a tsorace ta mike kan bed din ta haye taja bargo ta rufe jikinta gabadaya tsoro take ji ga wata irin masifaffiyar yunwa na kokarin cinye mata 'yayan hanji cikinta ta rike tana mutsikawa yau sha rabonta da cin abinci ta koshi yanzu yunwar ce ta taso mata sosai. Motsin bude kofa taji tayi shiru hade da takure wa cikin bargon..... Bude kofar yayi ya shigo dake akwai haske a dakin ya hangota cikin bargo kudundune karasa wa yayi ya zauna yana kokarin janye bargon hade da kiran sunanta, jin muryarsa yasa ta bude fuskarta Tana kallonsa,ya kalleta da rikitattun idanunsa a hankali yace." Tashi ki tayani hira." Mik'ewa zaune tayi tana dan zumb'ura bakinta yunwa takeji amma ta kasa fada masa bed din ya hau sosai yana kokarin jawota jikinsa taki yace."Meye hakane ki saki jikin ki babu abunda zanyi miki." Shuru tayi masa ya sanya ha'barsa kan kafad'arta hannunsa ya zura ya rungumo kugunta yana wasa da k'irjinta tsigar jikinta ta fara mik'ewa ta fara mutso mutso tana kokarin tureshi ya kwantar Da ita.... Kuka tasa tana tureshi 'bata fuska yayi yace." Bafa nason Wannan abunda kike min hakkina nane na baki sadaki kuma sai ki hanani tabawa." Hawaye ta goge tana kauda fuska tace"Bai dace ba fa kar ka manta a cikin gidan Ku muke." A yatsine yace"To saime? Don a cikin gidan mu nake sai in fasa ta'baki." Shuru tayi ganin ya hasale girgiza kansa yayi ya cigaba da wasa da sassan jikinta Yana kokarin cire mata rigar jikinta duk ta rasa yanda zatayi dashi ta lura kukan da takeyi kamar yana kara masa k'arfi ne..... Turo baki tayi cikin shagwaba tace"Nifa yunwa nake ji don Allah ka k'yaleni wallahi INA inajin kunyar Mamy." Fuskarsa daf da tata yace." Ki cinye ni ki huta kinji ko." Kasa gane inda maganar sa ta dosa tayi shiru ya cigaba da ya mutsa mata jiki tun tana daurewa ta sare ganin ya cire mata komai na jikinta zindur ta barta ya wani gigice mata bargon ya jawo ya rufe su gabadaya ya kafa fuskarshi a k'irjinta yana tsotsar Brest dinta duk biyun idan ya tsotsi wannan sai ya saki ya tsotsi wannan a haukace yake mata salon soyayyar sa data masifar rikirkita mata lissafi ta rungumeshi kam! A jikinta tana sauke numfashi jijiyoyin jikinta duk sun saki sosai take karb'ar sakon da yake aikata mata hannunsa ya zura kasanta yana shafawa jin damshin ruwa ya kara tayar masa da hankali ya fara kokarin zura yatsansa cikin headquarter d'in yaji a matse ga wani irin taushin tsokoki gami da wani irin ruwa me dumi yana zubowa, ya sauke zazzafar ajiyar zuciya kansa ya kafa a gurin ya lasa yana tande ruwan da yake zuba yana zuwa cibiyarta yana tsotsa yana komawa headquarte yana zura harshe yana tsotsa! A gigice ta damk'i sumar kansa tana wata irin mik'a tare da wani irin nishi wani irin hawaye na zubo mata, wani irin masifaffan dad'i take ji Wanda bata taba jin irinsa ba tana jin a duniya bata da babban masoyi sama dashi ji take babu abunda zai sa ta rabu dashi, nishi take saki tana kara damke wuyanshi hade da sake ware masa cinyarta"Ahhhh! Ahhhh! Abunda kawai take yi kenan, Khalid kuwa yafita shiga rud'u kawai dai yana so ya kaita geji ne domin ya sameta yanda yake so, sai da ya tabbatar ya gama samun ta a hannunsa sannan ya fara kokarin shigar da joystick dinshi da tayi wani irin bala'in mik'ewa ta wani kara girma a hankali ya dunga wasa da ita a gurin har ya samu kanta ya shiga Hanifa nacan duniya dad'i duk ta dauka bakinsa ne a gurin sai da take wani Abu a shigeta da k'arfi taji wani kettt! A jikinta ta kwala wata irin kara wacce ta tayar da Mamy daga bacci ta mike zaune tana raba ido......... Khalid da ya samu ya shiga sosai sai ya safara kai kawai da wani irin kuzari yake sasakar Hanifa yana buga sambatu gami da iface-iface na dad'i Hanifa kuwa duk ta manta dad'i da ta kwasa tana karb'ar gashi gurin gwarzon maza MASHAHURI. Ta tabbata dai Khalid ba a fagen wake yake MASHAHURI ba a kowane fage shi jajurtacce ne kuma MASHAHURI ne. Dadin da yake kwasa ya kasa saurarawa yarinyar mutane duk wani sprm da ya tare masa a Mara sai da zubar dashi a jikin Hanifa Khalid yafi k'arfin awa shida kan Hanifa yana aikin Abu daya tun tana kuka da dukansa har ta daina ta kyaleshi shi kanshi bai San iya adadin realizing din yayi ba idan ya zubar bayaji kamar sake kara masa k'arfin sha'awa ake sai da ya kai geji da don kansa sannan ya sauka daga kanta plate yayi kan bed din yana sauke nuffashi abun mamaki joystick dinshi tanan a mike taki kwanciya Hanifa tayi sauri kanta gabanta na wata irin fad'uwa ganin girman abar tashi ya tsorata, kuka sosai tana mamakin rashin imaninsa, kafin ta Ankara taga ya kara hayewa jikinta yana kokarin sake mayar da kayan aikin ai bata San sanda ta kurma ihu ba ta dunga dukan shi ko ta ina tana fadin "Ka daina kar ka kashe ni yunwa nakeji wayyo Ammina."!!!!!! Mamy da ihun Hanifa na biyu ya gigita ta sauko kasa tana kasa kunne sosai na ta juyo maganar ta tana kuka tsaki taja ta koma ta kwanta tasan halin rashin hakurin yaron nata ba tare da wata damuwa ba ta shige cikin bargo tana jiran a kira sallahr asubah..... Khalid kuwa haikewa Hanifa ya karayi sosai yake sasakar ta kamar ya samu cikkakiyar mace bai sauka daga kanta ba sai da gari yayi haske ya mike a jigaje ya shiga toilet tsayuwa yayi gaban mirror yana kallon fuskarsa bushashen hawayen dake fuskarsa ya shafa yana mamaki kuka yarinyar shaik ta sashi lallai lamarin babbane Ashe haka mata suke da dad'i ko kuma yarinyar shaik din ce me wannan dadin? Shi kadai yake tambayar kansa wanka yayi ya futo ya tadda ita tana ta kuka cikin tsananin azabar wahala! *23/1/2020* _BintuUm@rAbb@le_ [1/24, 11:35 AM] BintaUmarAbbale: _MASHAHURI!!_ _*Ki biya ki karanta cikin kwanciyar hankali, ke kuma da kika futar min da book na barki da Allah!.*_ *08089965176* *07084653262* *0542382124....... Binta Umar Gt bank* *55* Zama yayi kusa da ita yana wani lumshe mata ido tuno dadin da ya kwasa a tare da ragowar ruwan da yake hannunsa ya yarfa mata a fuska ya lumshe mata ido yana watsa mata wani shumin kallo.... Hanifa kan tsoronsa takeji jikinta sai rawa yakeyi taki kallonsa gashi data motsa cinyarta zataji wani irin zugi mai ratsa kwakwalwa..... Muryarsa a sanyaye yace." My Sugar na ki tashi kiyi wanka ko." Hawaye ya kara zubo mata da kyar tace"Bazan iya tashi ba." Kallonta yayi yace." Da zafi ne."? Daga masa kai tayi.... Mik'ewa yayi ya maida kayansa na jiya ya janye bargon dake lullub'e a jikinta ganin yanda bedshirt din yayi kaca-kaca da jini ya daga masa hankali kallon fuskarta yayi sai a lokacin ma yaga yanda ta rame tausayi ta bashi ya shiga d'age mata 'k'afafu ihu! Ta sanya ta tureshi tana fadin"Wayyo na shiga ukuna ka daina ta'bani ko ina na jikina zafi yake min." Ransa babu dad'i ya futa daga dakin. Mamy ya samu bakin daining ya karasa kusa da ita kauda kanta tayi tana amsa gaisuwar da yake mata, yace." Mamy... Kallonsa tayi tace." Ka kira sunana kuma kayi shuru." Yace." Mamy yarinyar nan ce ta kasa tashi. " mamy ta gane abunda yake nufi ta cigaba da abunda take yace." Mamy kiyi wani Abu akai mana." Hararasa tayi tana bata fuska tace"Ka kiyaye ni wallahi me zanyi mata ni." Yaji babu dad'i a zuciyarsa yace." Tana jin ciwo a gurin fa." Tace"Ka kira daya daga cikin yan uwanka idan da halin taga Dr sai a dubata." Fuskarsa ya bata yace."Mamy ni kece zaki duba min ita kinji." Tsaki taja ta haye sama abunta don tans mutukar jin haushin mu'amular aure data shiga tsakakinsu kwata-kwata bata so yaron nata ya haihu da yarinya.... 'Kasa yayi da kansa yana nazari Sam baya son terere shiyasa baiyi tunanin kiran daya daga cikinsu amma yanzu dole ya kira Khalisar ita babbar su kuma tafi Hafiza iya rike girma bedroom din ya koma ya tadda ita tans kuka ta bud'e cinyoyinta gurin yana shan iska, yana ganin haka yaji gabansa yayi wani irin han'koro yana motsi sha'awarta ta kamashi lumshe idonsa yayi ya kasara bed din zama yayi yana Dan cizar lips dinshi gurin ya kurawa ido ganin yanda yayi jazur kamar danyan nama ga Abu jini jini sperm duk ya bushe gurin hade da cinyoyinta, kokarin kai hannu yake ya ta'ba tayi sauri rufewa da bargo tana rintse ido cikin tsananin azabah...... Kallonta yayi na minti biyu ya dauke kansa wayarsa ya Ciro ya fara Neman numbar aunt tashi Khalisat. Bugu daya tayi ta dauka sama-sama ya gaishe ta tace"Tunda naga wayarka nasan babu lafiya Kai da baka damu da kiran mutane a waya ba." Ajiyar zuciya ya sauke yace." Aunt pls kizo kiyi aikin Allah." Tace "Akwai aikin da yafi na gidan mijina ne."!? No! Wannan ma da zakiyi zaki samu lada." Yafad'a tana Sosa sumar sa tace"Menene."? Yarinyar nan zaki zo ki duba." Tsaki tayi tace"Wai meye kake kwane-kwane wace yarinya ce."!? Da kyar Yace." Hanifa mana."? Me ya sameta."!? Don ita har ga Allah batayi tsammanin zaiyi wa yarinyar wani Abu ba... Yace."wai sai nayi miki filla-filla ne kawai kizo ki gani mana." Yanda ya fad'i maganar ta gane ransa ya b'aci tace"Zanzo amma gaskiya sai Abban Mufida ya futa kasan yau lahadi ko." A dab hasale yace." Shikkenan tunda baza kizo ba ni yanzu nake so zan nemi wata." Kashe wayar yayi a fusace. Kiransa tayi ya'ki dauka sai da ta kira sau uku sannan ya dauka tare da fadin"to me zakice kuma." Tace"Sarkin 'yan zuciya ganin zanzo naga komeye duk da dai INA zargin wani Abu amma komeye zanzo na gani." Kashe wayarsa yayi ba tare da yace mata kome ba...... Kallonta yayi a Dan ya mutse yace." Please beb ki daina Wannan kukan ya isa haka ko wace mace da haka ta saba." Ko kallonsa batayi ba ita kadai tasan abunda yake damunta.... Yana zaune yana latsa wayarsa yaji motsin bude kofa saurin mik'ewa yayi ya jawo bargo sosai ya rufe mata jikinta Khalisat ta shigo da sallama 'bata fuska yayi yace." Sai yanzu kikaga damar zuwa. " ko kallonsa batayi ba ta nufi gurin Hanifa domin tun kafin ta shigo mamy tw fada mata abunda ya faru..... Kokarin janye bargon take Hanifa ta rike tana kuka Khalisat ta dago kanta tana Dan hararsa tace"Kai kam baka da imani wallahi ka futa waje zamuyi magana da ita." Ta'be bakinsa yayi ya Sakai ya futa daga dakin. Khalisat ta kalli Hanifa dake faman rintse ido cikin zugin zafi da kuma kunya tace"Sannu kinji ko ki bari in duba miki gurin in gani." Hanifa tace"Aunt ki barshi babu kome so nake na tashi na kasa mik'ewa " Khalisat tace dolene dama ki bari in duba ko kina so wani yaga jikinki kinga ni yar Uwar mijinki ne babu matsala ai." Hanifa ta rike bargon tamau taki saki kunyar ta take ji. Khalisat ta mike ta shiga tolirt ruwa me zafi ta hada ta zuba detol kadan ta futo tana fadin"To tashi Muje ki shiga ruwan zafi sai muje asibiti.. Hanifa tayi tayi ta tashi ta kasa duk motsin da zatayi cikin ciwo ne wasu irin hawaye na zuraro mata, tausayin ta ya rufe Khalisat tabbas Dan uwan nata ba k'aramin aika-aika yayi ba.. Futa tayi parlor cike da tausayin yarinyar Yana tsaye suna magana da dady shi babu abunda ya dameshi ta karaso gurin jikinta a sanyaye Alhaji Tijjani yace." Ya akayi ne babbar yaya kema kinzo karb'ar kudin ne." Girgiza kanta tayi tace"ko daya dady kaga Wanda ta ta soni nan. " dariya yayi yana kallon Khalid din da ya kurawa yayar tashi ido ganin yanda ta futo fuskarta da alamun tausayi yace." Menene. "!? Tace." Ka shige muje ka dauketa ka shigar da ita toilet Wallahi ta kasa tashi Khalid baka da imani. " Mamy dake tsaye da jakar dady a hannunta tana kallon Khalisat din tace"Kamar yaya ta kasa tashi nifa bana son haka yarinya da shekarunta da kome zata dunga langwabe wa. " khalisat tace"Mamy kenan don bakiga Abunda yayi bane wallahi ta bani tausayi." Tab'e bakinta tayi tace "Allah ya kyauta musu..... Khalid dakin ya nufa Khalisat tabi bayansa Alhaji Tijjani yace." Ni duk kun sani a duhu meye ya samu yarinyar ne." Mamy tace"Babu kome rayuwar aure sukayi shine wai takasa tashi." Bai dauki maganar da muhimanci ba yace." Ok Myson babu sauki an samu abunda akeso." Tsabar takaici bai bari tace masa komai ba jakarsa ta mik'a masa ya futa ita kuma ta koma sama. Yana shiga dakin ya ciccbeta kai tsaye toilet din ya nufa da ita ta rukunkume shi tana cije baki shi kuma tsigar jikinsa sai mik'ewa take jin yanda take Goga masa Brest din ajiyar zuciya ya dunga saukewa kokarin ajeta kasa yake taki sakin shi sai hawaye take, haka Khalisat ta shigo ta samesu tace"Ga ruwa nan na had'a mata sakata a ciki sai ka futa." Kokarin saka yake tana mak'ale shi a hankali yace." Pls beb ki sauka mana ki shiga ruwan dumi kuma ki zama jaruma bana son Wannan kukan kinji ko." A hankali tace"Zafi kasana kamar an tsaga da reza." Kallon fuskarta yayi a lokacin yaji mugun tausayin ta ya tsigar masa ganin yanda tayi wujiga-wujiga lebanta duk ya bushe rarrashinta yake ya samu ya dannata cikin ruwa ta saki kara tana rike hannunsa... Ajiyar zuciya ya sauke ya tsira mata ido minti biyu yaga tana kara ware cinyarta cikin ruwan tana lumshe idonta mik'ewa yayi yana kallon Khalisat dake kallonsu tana mamakin son da saukewa junansu tace"Kaje ka nemo dr ina tunanin kajiwa yarinyar ciwo domin abunda take yayi tsanani an sani ko wace mace ranar daran farkonta tana shiga irin wannan yanayin amma nata yayi tsanani." Yace." Nifa babu wani namiji da zai gane min gaban matata haka kawai." Tace"Ka kira Dr Abdullah sai kace ya turo maka abokiyar aikinshi tazo ta dubata sosai." Yace."Yanzu kikayi magana." Futa yayi ya nufi part dinsa domin shirya wa...... Hanifa manta da Khalisat a gurin ta dunga bude k'afafunta ruwan zafin na ratsata lumshe ido kawai takeyi bude idon tayi suka hada ido da Khalisat din wata irin kunya ta. Lullub'e murmushi Khalisat tayi tace"Idan kinga ki kirani nazo na taimaka miki." Tana gama maganar ta ta futa..... Hanifa ta. Sake sosai ta dunga watsa ruwa a gurin Tana jin dad'i. Khalisat kuwa bedshirt din ta cire tana mamakin yanda ya b'aci nannde shi tayi ta futa dashi domin bawa me wanki ta dawo dakin shimfid'a musu bedshirt din tayi ta zauna tana jiran futowarta Sai da taji ruwan yayi sanyi sannan ts bude lumsassun idonta bacci ne me dad'i ya dauketa ts mike tsaye a hankali ta daddafa bango wani ruwan ta sake hadawa ta koma ciki kusan minti ashirin tayi ta futo ta samu sauki abun kadan amma duk da haka tana jin yanza gurin yake zugi wankan tsarki tayi ta daura towol ta lullub'e jikinta sosai bango take bi har ta isa bakin kofa Tana kokarin budewa Khalisat ta bude riketa tayi suka futa tare ta zauna Da ita gefan bed kayan sawa take nema babu tace." Duk ina kayan sawarki suke." ? Hanifa taji wani irin tausayin kanta tace"aunt babu sai wannan da na cire su." Can gefen bed din ta tsinto kayan a watse dake shaddace duk ta ya mutse Ta mik'a mata tare da fadin ki sanya bari in kawo miki Break fast kiyi Insha Allah yau za'ayi miki suyayyar kayan sawa dana kwalliya." Idonta na tara k'walla ta karba duguwar Riga.... Khalisat ta futa jikinta duk a sanyaye sosai take tausayawa yarinyar..... Mamy na zaune a daining tana karywa khalisat ta karasa gurin tace"Mamy dama babu abunda Khalid ya siyarwa yarinyar na aure." Mamy na Dan gwalar biredi da farfesun kifi tace." Bakya ganin a yanda akayi auran nasu." Ajiyar zuciya ya sauke tace"Mamy yarinyar na bani tausayi sosai ke kuma na lura kamar bakya sonta." Hankali kwance tace"Gaskiya ne bana sonta don dai anfi karfina ne." Khalisat tace",Sorry mamy kiyi hakuri ki karb'i lamarin don Allah ki samu musu albarka." Mamy tace"ke bana son shirme kinji na fadi wata mummunar magana a game da auran ne." ? Khalisat ta girgiza kanta tace"To kar ki kara yi min irin wanna maganar." To mamy bazan kara ba amma ki dunga sakar mata fuska na lura fa tun jiya kike share lamarinta."! Ke! Zanci Ubanki Wallahi." A fusace tayi maganar ta cigaba da cewa"Haka kawai zaki San sheni da surutu idan kingama abunda ya kawo ki ki tafi dakinki bana son wata magana, cikin takaici Khalisat ta fara hada break fast tsaf ta hada ta nufi dakin ranta duk a bace. Da kyar Hanifa ta zauna kasan kafet Khalisat ta hada mata tea me kauri ta zuba mata farfesun kifi hade da soyayyan dankali da kwai bredin ta shafe shi da bota girgiza Kai tayi tace",aunt ruwan tae kawai zansha wani iri bakina. "Khalisat tace" Ki daure kici dankali kinji Dr zata zo ta duba ki kinga zaki sha magani." Hanifa tana jin nauyin khalisat din sosai yasa ta kasa yi mata musu ta fara kurbar tea din tana hadawa da dankali dake akwai yunwa a tattara da ita taci sosai da sosai aunt taji dadin haka tace"Ko zasha farfesun." Girgiza kanta tayi tana jin zuciyarta na tashi tea da da dankalin da tasha sao taso mata yake tace"aunt bazan iya ci ba cikana yana murda min." Ta fada tana rike cikin. Shigowar su dakin yayi dai-dai da lokacin da amai ya tsinke mata ta dunga kwarara shi a gurin.... Hankali a tashe khalisat ta riketa ita kuma sai yunkoro take sai da ta amayar da duk abunda taci. Yana tsaye Kansu hannuwansa zube cikin aljuhu ya mutsa fuska yake yana jin haushin abunda takeyi shifa ya tsani ganin kazanta kuma ayita rarrashin mutum ya'ki hak'ura shi baya son irin haka baya son abunda zai daga masa hankali kuma tazo tana tayiwa mutane amai babu kyawun gani..... Tsaki yaja ya juya futa.... Dr da Khalisat suka gyara gurin hausawa na cewa ciwon ya mace na mace ne sai da suka gyara gurin tsaf sannan Dr ta shiga dubata, hanifa daurewa kawai take amma duk da haka hawaye na bin fuskarta tana tuno irin kallon da yayi mata kafin ya futa.... Dr ta kalli khalisat da damuwa a fuskarta tace"Yarinyar nan fa ta 'karu Wallahi sai andinke gurin." Jin abunda Dr tace yasa gabanta yayi mugun fad'uwa. Tuni hawayen dake zuba a idonta yaka yawa.... Khalisat tace"Dama nima na zargi haka saboda yanayin yanda take tafiya da kuma yanda take kuka da gurin....Dr tace"dama irin wannan emergency ne na tawo da kayan aikina, yanzu zanyi mata insha Allah idan ana kula da gurin kwana bakwai ya hade." Khalisat tace"Insha Allah." Hanifa tana ji Tana gani Dr ta dinke ta kamar wata 'kwarya kuka kawai take tana jin damuwar da take ciki ta kara nunnkuwa Dr ta had'a mata magani sosai Wanda zaiyi saurin dausashe gurin tayi musu sallama ta futa. Ganin kuka da damuwar da Hanifar ta shigane yasa Khalisat din ta zauna tana rarrashinta har sai da taga ta saki fuska sannan ta futa ta barta..... Lokacin Khalid na kokarin barin gidan suna magana da Mamy tace." Khalid zauna zamuyi magana." Jin haka yasa mamy basu guri... Yace." Menene."!? Babu wasa a fuskarta tace." Nace ka zauna dai." Zama yayi yana duba tsadaddan agogon dake hannunsa ta fara magana kamar haka.... *24/1/2020* _BintuUm@rAbb@le_ [1/25, 11:01 AM] BintaUmarAbbale: _MASHAHURI!!_ _*Ki biya ki karanta cikin kwanciyar hankali, ke kuma da kika futar min da book na barki da Allah!.*_ *08089965176* *07084653262* *0542382124....... Binta Umar Gt bank* *56* Zama yayi kusa da ita yana fadin"Ina sauraron ki." Khalisat ta gyara zamanta babu wasa a fuskarta tace"Khalid yarinyar fa ta 'karu yanzu sai da dr ta dinke gurin don haka nake gargadinka da ka kula don Allah kar kasake takar ta sai bayan sati biyu saboda gurin ya had'e yanda akeso." Da mamaki a fuskarsa yace." Kamar yaya? Ban fahimci maganar ki ba." Hararsa tayi tace"So kake nayi maka filla-filla kome."? Shafa kwantaccan sajensa yayi yace." Nifa ban gane kome ba kince kar in kara takarta sai gurin ya warke meye taka kuma wane gurine zai warke."? Cike da jin takaicinsa tace"Ina nufin ita matar taka daka gwadawa k'arfi jiya da daddare kaji mata ciwo a gabanta Wanda hakan ya jawo mata matsala gurin ya bude sai da aka gyara." Dariya yasa sosai yana kallon Khalisat din yace." Owk yanzu na fahimci me kike nufi." Mik'ewa yayi zai tafi tace"Bafa wasa nake da kai ba na fahimci baka da imani don girman Allah kar kaje ka bude dinki nan"! Tsayawa yayi yana kallonta tare da fadin"Wai me aka dinke ne."!? Ganin yana Neman raina mata hankali yasa ta dauki romot dake Ajiye kusa da ita jefa masa yana dariya ya futa daga parlor yana mamakin wai an d'inke gurin kuma kar ya 'kara takarta sai nan da sati biyu lallai suna wasa da irin dadin da ya kwasa a tare da yarinyar yanzu ma Allah-Allah yake dare yayi ya samu su ke'be yana ganin babu abunda zai hana bai biyawa kanshi buk'ata ba, motarsa ya shiga ya futa daga gidan.. Kai tsaye Gidansu Abbakar ya nufa domin su kammala shirye-shiryen tafiya gobe insha Allah zasu d'aga zuwa america............... *** Washe gari Abbu ya tashi jikinsa da kwari kuma ya samu bacci kamar yanda akeso Ammi na kula dashi sosai yanzu ma suna zaune ita dashi suna hira Nasiru ya shigo da sallama a bakinsa fuska a sake Abbu ya amsa ya nuna masa gurin zama Nasiru ya zauna yana kamshi irin na amare suka gaisa a mutumci Ammi tace"Ina Wasila." Nasiru yayi murmushi cike da nishadi yace." Tananan lafiya lau Ammi yaushe zakuje?" Ammi tace"Zamuzo insha Allah." Abbu kuwa sai murmushi yake yi ya cigaba da yi masa Nasiha kan ya kula da hakkin matarshi da yake rataye a wuyansa ya sauke duk wani Abu da aka halasta masa Nasiru yaji dadin nasihar Abbu ya mike yana yi musu sallama kasuwa zai tafi domin shi da Hafiz sun hana Abbu zuwa ganin kwana biyu baya cikin koshin lafiya dubu uku ya zaro cikin aljihu ya mik'awa Ammi yana fadin"Gashi ayi cefane Ammi tace"Nasiru kudinan yayi yawa kaima kaima Yanzu nauyi ya hau kanka. " yace." Babu komai Ammi a cigaba da yi mana addu'a." Abbu yace." Insha Allah kullum cikin yi muku addu'a muke." Nasir yayi musu sallama ya tafi dukaninsu sukaji rashin dad'i a zuciyarsu na rashin da Hanifa tayi da tayi da tuni tana d'akinta yanzu ko wane irin halin take ciki.? **** Haka ta yini cikin daki cikin tsananin azabah da yunwa don tun bayan sallah azahar Khalisat ta tafi saboda wayar da mijinta yake mata bayaso tayi nesa dashi mussaman ranar weakened kafin ta tafi sai ta tabbatar da Hanifar ta kara shiga ruwan zafi sannan tace daddare kafin ta kwanta ta kara shiga abunda batayi tunanin bata ba shine abinci lokacin kuma mai aiki ta gama tana jerawa a daining har Mamy na fadin ta tsaya taci abinci tace in taje gida taci...... Tun ruwan tea din da tasha kuma ta amayar dashi babu kome a cikinta sai daki yunwa na nema ta cinye mata yayan hanji ne yasa ta dauko bired din dazu ta fara dangwala da miyar kifin da tayi sanyi haka ta dunga cusawa tana share hawaye Sam ita kifi bai dameta ba saboda k'arninsa amma da yake babu yanda ta iya haka take ci domin ta kori yunwar dake damunta. Mamy na zaune a parlor ya shigo da sallama a bakinsa da mamaki yake kallonta yace." Mamy baki kwanta ba duba time fa." Mamy tace"kai nake jira ka shigo." Yace?" Mamy ko wace irin magana ce bakya bari sai da safe." Tace"Zauna ni bana son dogon zance." Zama yayi yana kallon fuskarta ganin yanda ta sha kunu yasa ya gane akwai matsala yace." Mamy ina jinki." Fuska a hade tace." Maza ka dauketa Ku tafi part dinka domin yau baza Ku hanani bacci DW shashanci ba abunda ya zaunar dani kenan. " Sunkuyar da kansa yayi cike da kunya yace."Mamy da kinyi hakuri ma daga yau fa Shikkenan gobe 12:00 Pm zamu tashi." Tace" Eh duk da haka dai dauketa Ku barmin daki" yana dariya ya mike yana fadin "bari to in futo." Tace"Inan zaune sai naga futowarku zan bar gurin nan." Dakin ya bude ya shiga yana mamakin halin Mamyn nashi.... Lokacin da ya shiga tana toliet cikin ruwan dumi yini tayi tana shiga bacci ne yake fuzgarta taji motsi a dakin a daddafe ta futa daga ruwan tana cije lips dinta ta maida siket dinta kokarin futowa take ta shigo kallo ya bita dashi a nutse yace." Me kikeyi a toilet. " ba tare da ta kalleshi ba tace." Babu komai." Wucewa tayi zata zauna kan bed yace." Beb yau ba'anan zamu kwana ba muje part dina." Gabanta ya fadi tace. " Bangane ba ni nafi son nan." Harga Allah tafi son nan tana ganim kamar Mamy din zata zame mata garkuwa 'bata fuska yayi yace." Ni kuma nace bana so yaya kenan. " shiru tayi masa kanta a kasa, ya karaso gurin hannunta ya ruke suka futa daga dakin.Mamy na ganin futowar su ta dauke kanta Yace." Mamy sai da safe." Allah ya tashemu lafiya." Hanifa nauyi da kunya ya hanata cewa komai simi-simi tabi bayansa suka futa daga parlor mamy taje ta kulle kofar sama ta haye abunta. Rungume take a jikinsa haka suka shiga bedroom dinshi ya zaunar da ita kan bed kallonsa take gabanta na fad'uwa ganin yanda yake jifanta da wani shu'umin kallo yace." Bari inyi wanka na futo ko." Shiru tayi masa ya shiga toilet minti goma ya futo jikinsa daure da towol me fadi kai tsaye bed ya nufo tayi saurin kauda kanta ya zauna kusa da ita a hankali yace."ko zakiyi wanka ne." ? Girgiza Kai tayi tana so tace masa yunwa takeji amma kunya ta hanata mik'ewa taga yayi ya bude sif dinshi wata akwatu taga ya dauko ya tsuguna yans budewa wata mutsiyaciyar Riga ya dauko jikinta duk igiyoyi ko da wasa ka kalli rigar baza ka taba tsammanin zata sawo jikin mutum ba ya rufe akwatin tare da mik'ewa zama yayi kusa da hade da mik'a mata rigar yace.ki cire Wannan kayan ki sanya wannan nafi son irin wannan dressing din shiyasa ma nayi miki tanadinsu su nakeso ki dunga sanya minsu idan muje can ma zan siya miki wasu." Karba tayi tana dubawa shi kuma ya kwanta rigingine yana kallonta tunani take ta yaya zata fara sanya rigar ta ganta duk a hargitse tace"Ya zanyi insa wannan rigar duba fa ka gani kamar ba Riga ba ni sanyi nake ji bazan iya sanyata in kwana da ita a jikina ba." Fuskarsa ya bata yace." Wai ke meyasa yar 'kauye ce ne? Ki cire wannan banzayen kayan na jikin ki nace ko."! Kallonsa tayi taga yana watsa mata wani kallo.... Zumb'ura baki tayi taki cirewa." Wai ba magana nake miki bane."! A kufule ya fadi maganar." Shareshi tayi sai ya fara kici-kicin tab'e mata rigar jikinta yana kokarin danneta ta sanya ihu tana tureshi take fadin"ka d'agani karka famamin ciwona." Jin abunda tace sai ya 'kara masa kuzari yayin da sha'warta ta kara kunno masa, cire mata rigar yayi ya cire birixiyar ya jefar da ita sikit din ya cire ya barta daga ita sai pant kuka take tana tureshi shi kuma yana kokarin sanya mata rigar hannunsa sai karkarwa yakeyi saboda yana yake shafar Brest din a gigice ya jefar da rigar ya kwanta a kanta yana sauke ajiyar zuciya ya kama bakinta ya fara sha yana wasa sa Brest dinta sauke nuffashi take tana tuttureshi bata so ta sakar masa jikinta duk da tana jin dadin abunda yake mata to bata so ya samu kafar da zai kara gana mats azabah irin ta jiya...... Sosai yake ya mutsa mata jiki da salon soyayyarsa yake kokarin zare mata pant din ta rike hannunsa Tana ture kanshi dake nane da k'irjinta in banda zafi babu abunda kan nonota yake mata, da kyar tace." Ka k'yaleni ni." Ki yayi ya cire wando ya jefar yatsansa yake kokarin zurawa ciki ta matse cinyarta tana dukan bayan shi take fadin"Kar 'bata min ciwo na."!!! Baya cikin nutsuwar kokarin yake ya talle mata cinya ta gartsa masa cizo a bayanshi d'ago jajayen idanunsa yayi yana kallonta yace." Ranki zaiyi mummuman b'aci wallahi." Tana kuka tace." To na fad'a maka abunda yake da akwai Dr tace kar a'kara ta'ba gurun har sai ya warke." A fusace yace." Dr din taci uwarta ta isa ta hanani ta'ba abunane da zata kafamin shad'ai fockyou!!! Kuka take tana dukanshi had'e da zabga masa magiya amma ko ya saurare ta baiyi ba ya zura d'an ya tsansa a gurin yana wasa dashi yanajin kaushin zaran da akayi mata dinki dashi bai dame shi ba, sai da ya tabbatar ya bud'e gurin yanda yake bu'kata ya fara kokarin shigar da gabanshi gurin wata irin 'kara ta 'kwallara ko a jikinsa ya fara safa da marwa a gurin yanayi yana marmatsa mata Brest Cikin tsananin dad'i yake lumshe idonsa yana cije bakinsa yana kara kuzari da k'arfi har ya samu yayi realising kin sauka yayi sai da ya gama zubarwa ya 'kara tashi da wani sabon kuzarin ya cigaba da aiki babu kakkautawa.! *25/1/2020* _BintuUm@rAbb@le_ [1/26, 11:31 AM] BintaUmarAbbale: _MASHAHURI!!_ _*Ki biya ki karanta cikin kwanciyar hankali, ke kuma da kika futar min da book na barki da Allah!.*_ *08089965176* *07084653262* *0542382124....... Binta Umar Gt bank* *57* Tsananin azabar da Hanifa take sha ya hanata kuka tana jin yanda Khalid yake ta faman sukuwa a kanta yana buga sambatu lumshe idonta tayi wasu irin hawaye na zuraro mata na tsananin azabah haka Khalid ya dinga aikin Abu daya tun tana gane me yakeyi har ta daina fahimtar komai jikinta ya shika amma duk da haka gogonku bai sauka ba sai da ya kawo sauku hudu sannan ya samu nutsuwar da yake bukata ganin idonta a rufe yasa yayi tunanin ko bacci take kawai sai ya shige toilet yayo wanka kana kallonsa kasan yana cikin farin ciki yana futowa ya sanya short nickar da wata matsatstsiyar riga firji ya bude ya dauko madarar holandia wata irin yunwa yake ji futa yayi daga dakin minti biyar ya dawo hannunsa rike da wani irin had'addan biscuit mai mugun tsada Zama yayi kan sofa yana ci yana had'awa da madarar bayan ya kammala ya fara duba sakkonin dake wayarshe ya manta da Hanifa a tunaninshi bacci takeyi sai kusan k'arfe daya saura yaje ya kwanta fuskarta ya tsurawa ido yana kallo..... Gabansa ya fad'i ganin bata numfashi mik'ewa yayi ya janye bargon da ya rufe ta dashi yana kallon k'irjinta babu alamun harbawar numfashi ya daga hannunta yaga ya fad'i yaraf!!! Jiki na kyarma ya sauka daga bed din furji ya bude ya dauko ruwa me sanyi fuskarta ya tuttule mata ko motsi batayi ba ya dunga jin fad'uwar gaba yana jin tsoron kar ta mutu ya cutu yanzu yana ganin ta zame masa garkuwa kuma bayan haka tsananin dad'i da yake kwasa a tare da ita yakewa dagota yayi ya rumgume a jikinsa yana tunain mafuta........Yafi minti goma tana rungume a jikinsa ya rasa ya zaiyi ya hada bakinsa da nata amma duk da haka taki dawowa kwantar da ita yayi jikinsa duk yayi sanyi ya kara dauko wani Ruwan mai mugun sanyi ya tuttula mata a fuska. Ajiyar zuciya ta sauke! Numfashin ta ya dawo amma bai dai-dai ta ba kuma idonta na rufe ganin harbawar numfashin ta yasa ya sauke ajiyar zuciya rungume ta yayi kam! Kam a jikinsa yana sauke ajiyar zuciya....sunanta yake kira 'k'asa-k'asa shiru batayi magana ba"Beb pls ki bude idonki kinji ko nine ko? Bazan 'karaba kiyi min hakuri ki bude min wannan kyawawan idanunki kinji My Sugar ilovyou beb ina mutukar sonki ne shiyasa na kasa sarrafa kaina ki bude idanunki ki kalleni." Sama-sama take jin maganar shi ta bude idonta a hankali tana kallon fuskarsa wata irin tsanar sa take ji a zuciyarta ta tabbatar da cewa ba ita yake so ba jikinta yake so ta fad'a masa cewa gurin akwai matsala ya haye ta sai da ya 'bata mata guri babu abunda zatace masa, kwace jikinta tayi ta kwanta tana wani irin kuka me cin rai." Ya kara yun'kuri kamota ta goce a hankali yace?" Menene yake miki ciwo yanzu."? A fusace tace"Ni ka k'yaleni ka cuceni ka cuceni ka cucen.... Wani irin kuka yaci karfinta ta dungayi tana dukan katifar gadon.... Baiji dad'i Abunda tace ba yace?" Kawai saboda na karb'i HAKKINA shine kike cewa na cuce ki."! Ka rufe min baki ni bana son jin wad'annan mayaudaran kalaman naka."!! Da kuka ta fadi maganar. Ranshi a bace yace.'' Ni kike fadawa wannan maganar don kinga ina rarrashin ki." Shiru tayi masa tsaki yaja ya mike ya bar gurin kan Sofa ya kwanta yana latse-latse a waya ransa duk a bace yaga alamar yarinyar nan na nema ta raina shi zai dauke mata wuta shi baya son raini ko kadan.. Yana kallonta tana kici-kicin tashi har Allah ya bata sa'a ta mike tsaye da dafa bango ta shiga toilet ta samu ta hada ruwa me dumi ta shiga ciki tana jin wani irin sanyi na ratsa mata jiki haka dai ta daure ta zauna cikin ruwan sosai tana Dan ta'ba gurin da hannunta addu'a take Allah yasa dinki bai warware ba haka dai tana ji kamar bai warware ba addu'a takeyi cikin zuciyarta tana goge hawaye da kyar ta futo daga cikin ruwan tayi wanka sanyi na ratsa ta jikinta nannade da towol ta futo tana kyarma ta zube kan bed da sauri ta jawo bargo ta rufe jikinta dashi sanyi ya isheta jikinta ya dunga kaf-kaf tana datse hakora ko kallonta baiyi haushinta yake ji ya kashe wayarsa tare da juya mata baya, zazzafan zazzab'i ne ya rufeta haka wani irin bacci ya dauketa mai cike sa mafarkai barkatai. Takwas saura ta farka da wani irin ciwon kai dakin take bi da kallo tana nemansa bayanan hawaye ta goge ta mike zaune tana laluben kayanta ace mutum yayi ta fama da Riga daya kwana biyu taga duk ta b'aci dad'i akanta kayan suka kwanta gashinan harda gajeran wandon sa mik'ewa tayi da kyar ta shiga toilet alwala ta dauro ta futo jikinta babu kwari ta bude sif dinshi rigarshi jallabiya ta dauko ta zura a jikinta ta dauki hijab dinta dake yashe a kasan dakin sallah ta tayar bayan ta idar ta fara addu'a tana kuka cikin wannan halin ya shigo ya sameta ganin halin da take ciki ya Dan ta'ba masa zuciya daukar abunda ya shigo dashi yayi ya futa mintina GOMA ya dawo dakin lokacin ta gama addu'ar tana zaune ta hada Kai da gwiwa tana kuka Mara sauti tsayuwa yayi kanta taki dago kanta ta kalleshi wani irin haushin sa take ji.... Yace." Kije Ku gaisa da Mamy kiyi break fast 12:00 dai-dai zamu tashi." Shiru tayi masa tana kara matse jikinta jikin hijab yace." Beb kina jina ko."! Dago kanta tayi tana kallonshi da jajeyen idonta yayi saurin kauda kansa yana ya mutsa fuska yace." Bana son kuka a rayuwata ke kuma na lura baki da aiki sai kuka kome kuka kome kuka mtsss! Murya a sark'e tace"Ka kira min Ya Haruna ina son nayi magana dashi." Wani irin kallo ya watsa mata a cunkushe yace." Wace irin magana kike so kiyi dashi yanzu."? Ni dai kawai ka kira min shi." Ta fada tana dauke kanta. Yace." To bazan kirashi ba kiyi abunda nace ko." Hawaye ta share tace. Don Allah ka kira minshi kaji. " Zama yayi kusa da ita yace." Ki fada min komai yake damun ki tunda nine nake kusa dake Haruna babu abunda zai iya yi miki." Tace"Ni dai ka kira min shi kawai." Rai a bace yace." Nace bazan kira ba na gadama sai in goge numbarshi Wallahi me zakiyi musu bayan kin rabu dasu ki dauke hankalinki daga Kansu shine yafi amfani dake." Kallonsa take cike da mamaki ya daga mata girarashi guda yana sakar mata wani shu'umin murmushi dauke kanta take tana mamakin jin kalaman sa wai ta rabu dasu ita ta dauka zai taimake ta ne ta sasanta dasu dauke kanta tayi tana bata fuskarta ya mike yana fad'in"Ki futo kar in kara yi miki magana. " Tana kallonshi ya futa minti biyar ta mike da kyar ta nufi part din Mamy. Mamy na ganin shigowar ra ta dauke kanta hanifa ta karaso ta zauna jikinta babu kwari har yanzu tana Jin zazzab'i da ciwon kai daurewa kawai take ta gaida mamy cikin ladabi mamy ta amsa babu yabo babu fallasa zama tayi shiru mamy ta mike ta bar mata gurin. Can daining ta hango Khalid yana karyawa hannunsa rike da waya yana dubawa, mik'ewa tayi ta futa, ya bita da kallo yana gyada kansa ya kasa gane wane irin hali ne da yarinyar a nutse ya gama break fast dinshi ya bar gurin part din nashi ya koma ya tadda Ita tana kuka tsaki yaja yana dafe kanshi a hasale yace." Why! Beb meke damun rayuwar ki ne kuka kuka nifa na tsani wannan dab'iar wallahi." Tana kuka tace"Ba Dole inyi kuka ba dole inyi kuka ko ina babu sauki kai da na amunce da Kai kana ta azabatar dani wallahi na soma nadamar amunce maka ka cucen...... Kafin ya karasa ya rufe mata baki da tafin hannunsa jawota yayi ya rungume tsam a k'irjinsa yana jin yanda k'irjinta yake bugawa kuka take tana fuzge jikinta take fadin"Ni babu inda zan bika wani gari kaje ka dunga bani wahala I hit you."!! Lumshe idonsa yayi cike da tsabar takaici da damuwar Abunda yarinyar take masa ya cije lips dinsa yana jin kukanta na taba masa zuciya yace."Beb kiyi hakuri nace bazan karaba don Allah ki daina wannan kukan yana damuna pls. "!!! Fuzgewa tayi tana fadin" Ni dai nace ka kira min Haruna kuma babu inda zan bika gida Zan koma."!gaban shi ya fadi jin abunda take cewa lallai bata da hankali a halin yanzu yana ganin babu Wanda ya isa ya ra bashi da ita babu abunda yake hange a tartare da ita sai dadin ta a gogon bango ya kalla yaga Tara da rabi cikin wata irin murya ya sanya bakinsa dai-dai kunnenta ya fara rera mata wa'ka kamar haka. *"Ashe da rai nake sonki gimbiya bada zuciyata!ba💗💗💗💗💗💗💗💗* *"komai ruwa da iska akanki baza na daina kewa ba."!* 💗💗💗💗💗💗💗💗 *"Zuma a baki dad'i gare ta kin bani taki lasa indai a kanki ne nayi nisa ba kiran da zan amsa."!* 💗💗💗💗💗💗💗💗 *"Tilas! Ganin mu tilas! Barinmu kaunar ki tunda nai nisa Sam ba batun na fasa tunda nai nisa."* 💗💗💗💗💗💗💗💗 *"MASOYI YANA DA RANA."* *"MASOYI YANA DA RANA!"* *MASOYI YANA DA RANE NE.!!!!!!!!!!!!!!"* Wa'kar tayi mata dadi sosai amma bata nuna masa a fuska ba sai ma kokarin kwace jikinta da takeyi yana kara rungume ta hade da marairaice mata fuska yana rarrashinta da kalamai masu sanyi Wanda suka kashe mata jiki sosai ta fara share k'ananun hawaye... Sai da ya tabbatar ya kashe mata jiki sannan ya sake ta futa yayi daga dakin minti goma ya dawo da kayan Break fast zama yayi ya hada mata yana lallab'ata da kyar ta shanye tea cup daya doya da kwai take ci sosai ha mike a nutse yace ." Bari in kawo miki kaya ki sanya amma kafin inzo kiyi wanka kinji ko." Daga kanta tayi ya futa daga dakin yana sauke ajiyar zuciya a waya ya kira Abbakar yace." Idan zaku shigo ka tsaya Sahad sto ka siyowa Hanifa dinkakkun kaya kala biyu yace." Insha Allah yana nan tsaye harabar gidan Abbakar da Mobson suka shigo kan macing tare suka shiga part din Nasa ya karb'i ledar bedroom din ya shiga lokacin tana toliet tana wanka shima wankan yakeso yayi sai ya afka ciki Cikin damuwa take kallonsa ganinta babu kaya ya tayar masa da masi faffiyar sha'awar sa tsira mata ido yayi yana cizar lps dinsa a tsorace ta rufe jikinta da towol ta futa daga toilet din tana zumb'ura bakinta. Kallo ya bita dashi yana sauke ajiyar zuwa a gurguje yayi wanka ya futo daure da towol tana zaune gefen bed a sark'e yace." Ki bude ledar nan." Ledar ta bude taga doguwar Riga da wani les me tsadar gaske dinkin Riga da sikit ne les din ta sanya ko brizayya babu amma dake nonowanta a tsaye suke dinki ya zauna a jikinta sosai ya dunga binta da wani mayen kallo haka ya shirya cikin wasu uban suit masu mugun kyau farar safa ya sanya kafafunshi ya sanya takalmi sahu ciki sumarshi ya taje sosai sai shek'i take hannunsa rike da kwalbar turaranshi ya karaso inda take zaune mikar da ita yayi ya rungume turaran ya bude ya dunga fesa mata a jiki yana sansana jikinta kamar wani tsohon maye! *26/1/2020* _BintuUm@rAbb@le_ [1/26, 6:50 PM] BintaUmarAbbale: _MASHAHURI!!_ _*Ki biya ki karanta cikin kwanciyar hankali, ke kuma da kika futar min da book na barki da Allah!.*_ *08089965176* *07084653262* *0542382124....... Binta Umar Gt bank* *58* Kauda fuskarta take yana 'kara kusanto da tashi fuskar bakinta yake so ya kama data fuskanci haka tayi sauriin sunkuyar da kanta tana goce-goce ya riketa tsam ya matseta a jikinsa ya had'a bakinsa da nata ya dunga tsotsa yana lumshe idonsa Wani irin zugi lebanta yake ta lura kamar maye yake duk sanda ya kama harshenta sai ya dunga zu'kushi kamar zai tsinke mata yanayi yana had'awa da le'bunanta azaba da ta isheta sai ta fashe masa da kukan da ya sanya ya dawo nutsuwar sa s'akinta ya yana binta da rikitattun idanunsa da suka kankance da sauri ta goge fuskarta ta futa daga dakin.... Hada ido sukayi da Abbakar da suke dakon futowar su saurin kauda kanta tayi taje ta zauna kan kujera tana gaishe su cikin sakin fuska suka amsa ta dauke kanta daga Kansu ganin irin kallon da Mobson yake mata tsaki take ja cikin ranta ta manta bata sanya hijab dinta ba kuma batayi tsammanin ganinsu a gurin ba mik'ewa tayi ta nufi dakin suka buga karo kansa ya dafe yana kallonta da shu'uman idonsa yace." Kika buge ni ko." Zumb'ura baki tayi zata shige ya rike hannunta cikin kasalalliyar murya yace." Me zaki koma ciki kiyi kuma."? Hijab dina zan dauko."Owk ." abunda yace kenan ya saketa ta shige dakin shi kuma ya karasa gurinsu Abbakar Mobson ya bashi hannu suka tafa yana fad'in"Guy kana wuta fa."! Sajanshi ya shafa yana sakin wani killer smile yace." To ya San ranka." Mobson ya d'aga kafad'a irin na gayu yace." Kayi babu komai lokacinka ne."! Hannu ya bashi suka tafa kana suka mike Wanda yayi dai-dai da futowar hanifa daga daki wucesu tayi Khalid ya kalli Abbakar yana nuna masa ita da baki dariya suka sanya cikin hakiyanci Abbakar ya bashi hannu suka tafa cike da nishadi suka futa. Abbakar da Mobson suka tsaya harbar gidan shi da ita suka shiga part din Mamy. Khalisat Hafiza da Mamy din suna zaune suka shiga hannunsa rike da nata. Mamy na ganinsu ta dauke kanta zama yayi kujera ita kuma Hanifar ta zube kasan kafet kanta a kasa take gaishe da yayyun nasa Cike da tausayi Kalisat take amsawa ita dai haka kawai yarinyar take bata tausayi Hafiza yar jam'iyar Mamy ce babu yabo babu fallasa ta amsa mata Khalid yace." Mamy zamu tafi kiyi mana addu'a. " Tace"Allah ya dawo daku lafiya amma kafin nan ina so in San cewar ka fad'awa Dady Ku maganrmu ko? Saboda ina son kafin Ku dawo ayi komai a gama." Yace." Mamy babu matsala munyi maganar dashi kiyi komai kamar yanda kike so." Sosai ta saki fuskarta tace"Allah yayi maka albarka." Amsawa yayi da "ameen kafin ya mike tsaye da niyar tafiya jikinta a sanyaye ta mike Khalisat ta dunga kallonta tana kallon yanayin tafiyar ta a zuciyarta tace." Allah dai ya daukewa yaron nan hankali kan yarinyar nan ya barta ta warke." Haka dai suka futa Mamy taja tsaki tana fad'in"Yarinya da ido a tsatstsaye amma saboda kinibibi sai wani salo-salo take ni kam Sam bana kaunarta wallahi." Hafiza tasa dariya tana fadin"Momy kenan nima gaskiya bata Wani kwanta min ba kin San duk Wanda yafiye sinke-sinke to bashi da dadin sha'ani na lura da yarinyar ko ido bata iya hadawa da mutane." Mamy tace"Ai dole ta kasa hada ido da mutane tunda tasan Abunda ta aikata wai mace ta gari CE zata gujewa iyayenta ubangiji Allah ka tsaremu da masu irin wannan halin. " rai a Dan bace Khalisat tace." Mamy bana jin dadin yanda kike wannan maganar wallahi don Allah ki daina shifa bawa bai ta'ba tsarawa kanshi rayuwa ba face sai wacce Allah ya tsara masa Wallahi mamy kaddarace wacce bata wuce kan kowa ba ni kuma hakan da sukayi ya burgeni saboda basu aikata haramun ba shi ya kafe sai ita zai aura ita kuma ta gudo saboda shi har sai da sukayi auri junansu kinga ko tanan Allah ya tseratar dasu ga aikata zina tunda ke da kanki kike fad'a cewa kinsha kamashi da yarinyar amma saboda k'arfin addu'ar ki a kanshi bai aikata wani abun akanta ba shiyasa yanzu ma nakeso ki cigaba da yi musu addu'a Allah yasa haka shi yafi alkairi a rayuwar su." Mamy jikinta yayi sanyi jin maganar da Khalisat tayi tace"Duk naji maganar ki kuma Insha Allah zanyi kokarin daurewa zuciyata kan lamarin ammafa Dole sai ya kara aure anan kurkusa." Khalisat tace"Duk wannan babu matsala tunda dai ya amunce Shikkenan Allah ya sanya alkairi." Tace"Ameen cikin wannan satin ma nake so ku shiga kasuwa har ita Nasrin duk wani abunda take bukata taje ta had'a kayan lefanta da kanta ina ganin haka zai fi." Hafiza tace"Hakan yayi kyau."! Cikin kwantar da murya khalisat din tace." Mamy amma tare za'a had'o da ita Hanifar ko." Tace"Eh tunda kina son haka sai ayi." Khalisat tasa dariya mamy din tace"Na lura yarinyar ta gama dake ai?" Khalisat tace"A'a mamy tausayin ta nake ji." Dariya sukayi dukaninsu suka cigaba da hira Cikin nishadi. Kai tsaye Airport suka nufa lokacin tashin jirgi yayi suka d'aga Hanifa ta 'kankame shi tana rintse idonta jin yanda jirgi yake wani irin 'kugi jikinta ya dunga kyarma hawaye duk ya wanke mata fuskarta..... Shiru yayi mata yana Dan hararata ganin yanda mutanan fake jirin suke kallonsu shifa bayason k'auyanci duk yawanci mutanan dake jirgi turawa ne sai 'kwarori Hausa kad'an sai yaga kamar k'auyanci ne a ganshi da ida da wani kurmeman hijab yana Jan kasa, kokarin cire mata shi yake ta dago jajayen idonta tana kallonsa..... Fuska ya 'bata yana fadin"Bana son shirme da k'auyanci cire wannan banzan abun duk kin sanya ana kallon mutane?"!! A tsorace take kallonsa tabi ya cikwikwoye hijab din a hannunta bakinta na rawa ta ma rasa me zata ce masa........ Juyawa tayi bayanta can ta hango Abbakar da Mobson gurin zamansu sai faman duba waya suke ta kalleshi kamar zatayi kuka tace"Kayi hakuri ka duba fa duka nan babu muharramai na duk ma arna ne a gurin gaka hakan bai dace ba tunda ina da aure." Yana watsa mata wani irin kallo yace."Waye ya damu dake anan? Kowa harkar gaban shi yake ke kike ganin kamar wani ya damu dake ga mata nan da suka fiki cika da komai sunyi kwaliyya ta burgewa ke kin lullub'e jiki sai kace wata matar Liman shin kin San cikin mutanan da zamuje kuwa." ? Girgiza kanta tayi tace"Na gane Abunda kake nufi ina so in ganar da kai cewar hakan bai kyautu ba kuma haramun ne wani namiji ya kalleni a haka zunubi zai hau kaina. " Wannan Kalmar da ta fad'a ta ina so in ganar da kai tayi mugun bata masa rai yace." Ke! Ni zaki ganar."! Shiru tayi ta sunkuyar da kanta ganin yanda ya fadi maganar a hasale! Ya cigaba da cewa"Kamar ni zaki zaunar kina fad'awa zaki ganar Useless! Dake duk wani Abu da zaki ganar dani na sanshi, bana ra'ayin shi tsarina na fad'a miki bana son gaddama da musu ke kuma na lura d'abi'ar kice bari in fada miki wani ni nan da kika ganni bana fad'ar magana a musa min kije ki tambaya wanene Khalid ko yayyuna abunda na umarta shi suke bare ke Villager dake! Ki kiyaye ni wallahi kar in 'kara umartaki da yin wani Abu kice zaki kawo min 'kauli da ba'adi ni zaki ganar!."!? Ya kara maimata maganar a karo na biyu ya tsura mata ido cikin fushi!!!! Hawaye ya dunga zuba a fuskarta tace"Kayi hakuri kaji." Ture ta yayi daga jikinsa yana Jan tsaki yace." Wato ni zaki nunawa ke 'yar arrama ce kome."!? Tayi shuru yace."To yanzu ko shine yazo nan bai isa ya hanani in baki umarni ba tunda a halin yanzu bashi da hurumi dake! Becafull!! Masifa ya dunga yi mata yana had'awa da cin mutumci a fakaice sai da yayi mai isararsa sannan ya k'yaleta ta dunga share hawaye babu yanda ta iya ta cire hijab din ta kudundune shi a hannunta tana jin wata irin kunya gani take kamar tsirara take ko kallonta bai yi ba yana ta aikin latsa wayarsa fuskarsa a mutukar murtuke! *26/1/2020* _BintuUm@rAbb@le_ [1/27, 11:31 AM] BintaUmarAbbale: _MASHAHURI!!_ _*Ki biya ki karanta cikin kwanciyar hankali, ke kuma da kika futar min da book na barki da Allah!.*_ *08089965176* *07084653262* *0542382124....... Binta Umar Gt bank* *59* Kamar yanda ya fad'a din cewar babu kowa da ita hakane ya kasance taga kowa harkan gaban shi yake sai ta samu sakewa ta sauke ajiyar zuciya tana satar kallonshi Har yanzu fuskarsa a had'e take tam!! Sai latsa wayarsa yake damuwa ta shiga sosai ta tsani taga yanayi mata wannan shariyar kanta ta d'ora kafad'arshi ta lumshe idonta da gefen idonsa yake kallonta sai ta bashi tausayi sosai hannunsa ya zura ya rugumo kugunta yana kiss din goshinta idanunta a lumshe yaks taji dadin abunda yayi mata hakan yana nuna mata cewar ya sauka daga fushinsa, sai ta kara lafewa a jikinsa jirgi ya cigaba da tafiya dasu sararin samaniya cikin hukuncin Allah......... Sonop dai maihaifinsa mai kudin gaske ne a k'asar ta america yana d'aya daga cikin masu fad'a aji a 'k'asar kuma ma'kiyin Allah da Annabi ne mugun bayahude ne duk Wanda yazo mishi da maganar Annabi Muhammad (Slw) sai ya sa an kashe shi da sannunsa auran jinsi tsakanin mata da maza kuma yana taimakawa k'ungiyar ta ko wace siga idan suna bukaci Wani Abu da gudu yake musu gwamantin k'asar ma bata zartar da wani Abu sai da sa hannunsa domin yana mutukar kawo musu cigaba babu irin makaman Ya'kin da bashi dasu kwantena kwantena haka suke dasu na ya'kar musulmai Mugun mutum ne mai mutukar kishin kansa da k'asar sa ya tsani musulunci da musulamai d'anshi d'aya Sonop sai matarshi Linda Tony mutum ne mai kudi Wanda bai San iya adadinsu ba Sonop na yin abunda ya ga dama a k'asar tasu ko wace mace ya kyalla ido ya gani yana so sai ya biyawa kansa bukatar sa hankalinsa yake kwanciya dangane da zuwansu Khalid k'asar Sonop ya Sanar wa mahaifin nasa yaji dadin hakan domin shi yana mutukar son Abunda danshi yake so wani k'aton gida Sonop ya sanya aka shirya wa Khalid din aka zuba mishi komai na rayuwa da jin dadi.... Wasu zungura zunguran motaci ne suka zo daukar Khalid daga airport a cikin madu Tarar tashi har da uban tafiyar Tony wato mahaifin Sonop kenan yana sanye da wasu irin cort masu shegen tsada idanunsa sakaye da farin glass kanshi kwal babu d'igon gashi ko kad'an..... Hanifa na ganin jirgi ya sauke ta kara tukure kanta take mutane suka mike suna sauka a nutse Khalid ya rungume ta a jikinsa suka fara sakkowa daga jirgin su Abbakar na binsu a baya........ Sonop da abokanshi suna hango Khalid suka nufe shi cike da farin ciki ya saketa ya fara rungume su sunayin wata irin gaisuwa irin tasu... Da ido Sonop yake tambayar shi Hanifa ya gyada mishi kai.... Lumshe idonsa yayi ya bude kan Hanifa a hankali yace." She is beutufful "! Khalid yayi murmushi yana nuna masa su Abbakar Ya nufi gurinsu rungume su yayi yana musu magana da turanci to turancin nasa ba irin nasu bane abunda suka gane ciki shi suka amsa kafin su bi bayan shi zuwa zungureriyar motar da Tony yake ciki a hakince! Abbakar da Mobson sai da suka tsorata ganin hamshakin mutumin da ya futo daga motar suka matsa gefe guda suna gaishe shi cikin turanci ya amsa ya karasa gurin Khalid rungume shi yayi yana Dan dukan bayanshi cikin turanci Khalid din ya gaidashi Tony ya amsa yana tambayar shi iyayen shi Khalid yace "Duk sunan lafiya Lou." Hannunsa ya rike suka shiga motar tare Sonop ya shiga take sucuritis dinshi dake tsaye a gurin suka shiga motar dravar yaja suka bar gurin........ Hanifa taji kamar ta d'ora hannu aka ta kurma ihu! Mai hakan yake nufi khalid ya manta da ita a gurin kome ya shiga mota ya barta Cikin kattin maza a garin da bata San kowa ba kuka ta farayi sosai tana bin hanyar da suka bi da kallo Joy da Johnson abokan Sonop suka kalli Su Abbakar da turanci sukayi musu magana cewar su shigo mota zasu bisu a baya.... Ganin irin kukan da Hanifa takeyi ne ya sanya Abbakar yaji tausayin ta yace." Sorry Hany ki daina wannan kukan mana ki zama big girl kin San wannan garin fa na wayayyone kina kuka baki kyau ba." Hawaye ta share yace." Muje mota yanzu za muje inda yake." Murfin mota ya bude mata ta shiga Mobson yayi saurin shiga ya zauna kusa da ita yana naninkarta tayi saurin matsawa gabanta na fad'uwa Abbakar ya shiga Sai joy ya zauna kusa dashi shi kuma Johnson ya zauna mazaunin dravar yaja motar suka bar gurin... Gudu kawai motar takeyi kan titi Hanifa ta takure jikinta tana kauda kanta duk dago kan da zatayi ta tsinci Mobson na kallon k'irjinta ta mirror din motar shima Johnson abunda yake kallo kenan yana Sosa kansa rigar les din jikinta ta matseta sosai kar Ku manta da cewar Hanifa tana da manya manyan nonowa duk sun futo saman rigarta gashi babu hijab, kamar zatayi kuka haka take ji Cikin wannan yanayi suka isa masaukin nasu tunga gate suka tsure da al'amarin wani irin gida ne mai mugun daukar hankali da kayatuwa Mobson yaji dadin zuwansa garin yana ganin babu abunda zai sanya ya koma najeria yayi bai-bai da ita tunda ya samu ya shigo kasa mai 'yanci zaiyi Abunda yake so." Khalid da Sonop na tsaye harabar gidan suna magana motar tayi parking Khalid ya karasa gurin Joy ya bude motar ya futo Abbakar ya futo sannan Mobson Hanifa ce ta k'arshe yana kallon fuskarta ya fahimci tayi kuka hannunta ya rike baice komai ba ya jata suka shiga cikin gidan..... Suna shiga taji wani irin sanyi na ratsa ta hannunsa ta kara rikewa kam tana bin had'addan parlor da kallo ko ina fitilone dal-dal da wasu irin show glass duk kusurwa ababen shanye+shaye a ciki sai wasu irin lafiyayyayun kujeru milk color hakanan labulayen parlor duma milk calor ne masu wata irin baza.!! Wasu irin shirga shirgan sifi'ko ne a kusuwar parlor sai wata makekiyar TV plasma LCD ash color manne a bango samanta wani tafkeken agogon bango ne da hoton Tony da Sonop jiki suna sanye da wasu irin suit masu kyau da tsada dukansu wuyansu da wata siririyar sar'ka mai dauke da tambarin addininsu sosai jikinta yayi bala'in sanyi tayi saurin dauke kanta daga hoton, zaunar da ita yayi kan kujera yace." Ki zauna nan ina zuwa yanzu." Kafin tace komai ya futa daga parlor tayi saurin rintse idonta Sam bata so ta kalli fuskar mutumin ganin shi kamar wani mala'ika fuskarsa babu annuri ko kadan, Sunkuyar da kanta tayi tana jin wata irin fad'uwar gaba a tare da ita. Part din dake kusa dashi ya sanya su Abbakar suka shiga nan ne masaukinsu babu abunda babu na rayuwa Sonop yace suyi wanka su huta idan suka ci abunci zasu shiga kasuwa, Khalid a maimakon ya koma part dinshi sai yayi zaman shi nan kuka ya kawo musu abinci mai rai da lafiya suka ci sukayi wanka suka shirya tsaf! Suka shiga gari..... Abunda ya sanya ya share lamarin ta yana so ya koya mata hankalina domin har yanzu Idan ya tuna maganar ta ta d'azu sai ranshi ya b'aci wai kamarshi zata ganar lallai yarinyar shaik ta rainashi..... Basu dawo gidan ba sai misalin k'arfe goma sha biyu da rabi suka shigo cikin wata irin mota mara murfi sautin kid'ane kawai yake tashi Mobson ya samu Abunda yake so Khalid na futowa ya nufi part dinshi su kuma har Sonop din suka nufi daya part din Sonop yaso yabi Khalid din ganin bai bashi fuska ba yasa ya maze amma yana so ya sake ganin kyakyawar matarshi da yake mamakin Ashe dama Cikin hausawa 'yan najeria akwai kyawawa irin wannam shi dai beb din tayi masa sosai. Yana shiga parlor ya fara binshi da kallo babu ita a gurin sunanta ya fara kira a hankali "Beb! Beby kina ina ne."! Hanifa dake bayan kujera a takure tana bacci taji kamar a mafarki yana kiran sunanta bude idonta tayi taji motsi a kusa da inda take yana fad'in" Hany beby kina ina."!! Futowa tayi da gudu taje ta rungume shi tana wani irin kuka mai tsuma zuciya ajiyar zuciya ya sauke ya zauna da ita cikin kujera yana shafa kanta yake tambayar ta menene. "! Jikinta sai kyarma yake ta kasa cewa komai tana faman kuka! Tsaki yaja yace." Bana son wannan kukan idan bazaki fada menene ba zan k'yaleni." Majina taja muryar ta na rawa tace"Me yasa ka tafi ka barni cikin wannan gidan tsoro nake ji Wallahi don Allah kar ka kara tafiya ka barni." Kanta ya shafa yana lumshe idonsa dumin jikinta ya soma rikita shi yace." Sorry My Sugar!! Muje kasuwa ne kinsan baki da kayan sawa da kome na rayuwa so nayi miki siyayya irin kayan da nake so ki dunga yi min kwalliya dasu ina so kafin mu koma najeria ki dawo big girl kin gane ko."! Gyada kanta tayi tana share hawaye lumshe idonsa yake yana jin wani irin azababban fleengs na taso masa a sark'e yace ." INA fatan kinci abinci."! ? _Ni kaina tambayar da yayi mata ta bani mamaki wannan a rainin hankaline a ina zata samu abinci taci._ girgiza masa kanta tayi alamun bataci mik'ewa yayi yana fad'in "Bari nazo yanzu." Tana kallonshi ya futa daga parlor tayi saurin sunkuyar da kanta don bata so ta kalli hoton Tony da Sonop tsoro yake bata. [1/27, 11:28 AM] BintaUmarAbbale: Minti goma tsaki ya shigo hannunsa rike da wata Leda baka abinci ne a ciki da gasasan nama sai yugoht yace." Sakko kici sai kiyi wanka mu kwanta ko." Jikinta a sanyaye ta sakko ya bude ledar yana futo mata da Abincin yana budewa taji wani irin karni na nama ya hau kanta da sauri ta kauda kanta zuciyarta na tashi tace"Banaci wannan ka rufe shi." Shan kunu yayi yana kallonta tana ya mutse fuska yace." Bana son rainin hankali fa kince yunwa kike ji ga abinci nan na samo miki kice bakici." Tana kokarin komawa saman kujerar tace" Bana son irin wannan fa karnin naman babu dad'i. " tsaki yaja ya mike yana fad'in"ke kar kici don Allah cikin ki ko nawa ? Kafad'a ya d'aga ya shige bedroom din domin yin wanka yana kokarin shiga toilet din ta shigo dakin a tsorace take kallonsa tace" INA so inyi sallah tun dazu bani da hijabi yaya zanyi. ? Shiru yayi yana nazarin maganar ta domin tun a jirgi ya wurgar mata da hijab yace." Sai ki aje sallahr sai gobe idan Allah ya kaimu kya rama Yanzu dai babu inda zanje domin nemo miki hijabi." Yana gama maganar shi ya shige toilet. " kallo tabi shi dashi cike sa mamakin jin maganar sa wai ta aje sallahr zama tayi kan bed tana tuninin mafuta Kwata kwata bata so ta kwanta da nauyi a kanta, tana kallonsa ya futo daure da towol ya sanya wata Riga fara matsatstsiya da wando 3qutar dadduma taga ya hau yana Sallah yanda ta lura sai da yayi magariba sannan yayi isha kuma bai Dade kan daddumar ba ya mike bed din ya nufo tayi saurin kauda kanta daga gareshi kwanciya yayi hade da jawota jikinshi tayi saurin fuzgewa tana turo baki. "Meye haka." Ya fada yana bin jikinta da wani shu'umin kallo Hanifa a zuciyarta tace"Wallahi yau komai zakayi sai dai kayi amma bazan zauna ka bani wahala ba." Ya Kai hannu akaro na biyu zai jawota ta bar gurin kan Sofa taje ta zauna tana ya mutsa fuskarta. Ya bita da kallo cike da mamaki! Wai me yarinyar nan take nufi ne."!? Mik'ewa yayi zaune yana kallonta da jajayen idonsa yace." Dawo nan ko kuma yanzu ranki ya b'aci! Shiru tayi masa tana kauda fuska tsawa ya buga mata tare da fad'in"Wai ba magana nake miki ba." ? Murya a cunkushe tace"Ni fa ka k'yaleni." Mik'ewa yayi ya nufo inda take ya tsaya a kanta kamar zai dake ta yace." Ke yar taurin kaice ko."! Kasa tayi da kanta tana jin tsoron kallonsa a haka wani gabjeje dashi ciccibarta yake kokarin yi ta dunga zullewa tana kuka ganin tana so ta bashi wahala ne yasa ya sassauta muryarsa yana mata magana a kunne cewar babu abunda zaiyi mata..... Kin yarda tayi ta dunga bashi wahala tana motso-motso a jikinsa Abunda ya kara rikirkita shi kenan ya gigice mata rigar jikinta ya fuzge ya zare briziyar ya jefar ganin bai kusanci kasanta ba ya sanya hankalinta ya kwanata futular gefen gadi ya kashe yq cire wandon jikinsa samanta ya hau sosai yana kokarin tusa mata joystick dinshi a bakinta hakoranta ta datse gabanta na wata irin fad'uwa wannan wane irin salone! Kuka take masa sosai shi kuma duk ya gigice mata yana fadin"Baby pls stop crying hummm! Idan baki so na shige ki ka sha min abuna Shikkenan idan na samu stysfiend zan kyaleki baby pls ki kamamin kinji."!! Jinsa kawai take amma tana ganin babu abunda zai sanya ta sanya najasa a bakinta tana ganin yin hakan kamar haramun ne ... Ta datse bakinta sosai shi kuma yana ta kara naninka mata joystick dinshi bakinta yana sakin nishi Sam baiyi niyar shigarta ba yau saboda ganin yanayin da take ciki na rashin cin abinci yasan idan ya hauta zai iya kwana akanta yana aikin Abu daya shiyasa yake so tayi masa wasa tanayi masa k'auyanci,,, da yaga tana Neman wahalar dashi kawai ya gangara kasanta k'afafunta ya daga da k'arfi ya cire siket din. Jikinta pant din ya cire ya kafa kansa a gurin yana tsosta Hanifa ta dunga wata irin mik'a tana sauke ajiyar zuciya hade da lumshe idonta wani irin dadi take ji duk yana kallon Abunda takeyi ransa ya b'aci wato shi yace ta tsotse shi taki shi yanayi mata tana jin dadi lallai zai ci ubanta yanzu... Ta shagala cikin jin dadi taji ya danna gabansa jikinta ta kurma ihu tana matse cinyarta bakinta ya rufe da hannunsa daya hannun kuma ya d'aga kafarta sama ya samu ya shigeta sosai a take ya fara aiki babu kakkautawa. *27/1/2020* _BintuUm@rAbb@le_ [1/28, 10:53 AM] BintaUmarAbbale: _MASHAHURI!!_ _*Ki biya ki karanta cikin kwanciyar hankali, ke kuma da kika futar min da book na barki da Allah!.*_ *08089965176* *07084653262* *0542382124....... Binta Umar Gt bank* *60* Wani irin ihu! Take tana dukanshi ta ko ina tana jin wani irin zafi da radadi cikin jikinta kamar an barbada mata barko haka take kuka take sosai tana yi masa magiya kan ya k'yaleta itace take abunta Sam baya Cikin hayyacinsa sasakarta kawai yake yana sakin ihu hade da nishi! Birkitata yayi ruf da ciki ya d'age 'k'afafunta sama gabanshi ya tusa a haka ya cigaba da aiki!! Wasa farin girki Ashe bata ji komai dangane da azabar sai da yayi mata wannan salon ta dunga yunk'urin mik'ewa yana mai da ita da hannunshi da ya lura tana so ta hanashi yaji dadi kawai ya danneta gabadaya ya cigaba da jikinsa Hanifa ta dunga cize bakinta tana dukan pillow din da take kwance akai ta daina kuka sai dai hawaye tana jinsa yana sakin nishi hade wasu irin surutai duk cikin turanci yakeyi tayi lamo tana karb'ar azabah, wani irin han'koro yayi kamar zai kawo taji shiru yunk'urin mik'ewa tayi a karo na ba'adadi ya burkitoto kamar wani mahaukaci ya d'age mata k'afafu ya Dora kafad'arshi ya cigaba dayi Hanifa yau taga bala'i kuka ta cigaba dayi Tana fad'in"Kayi hakuri ka kawo wayyo na shiga ukuna wayyo na shiga ukuna na lalace Allah ya sakamin wannan Abu! Wayyo Amminaaaa!""" Dai-dai lokacin da zaiyi realisn kenan ya Ciro joystick din ya feshe mata fuska da Sprm dinshi,, rintse idonta tayi tana jin wani irin kyankyami ya kamata mussaman da taji karni-karnin abun dai-dai hancinta. Shi kuwa yana sane ya zuba mata a fuska Don ya kuntata mata yaji haushin Abunda tayi masa sauka yayi ya shige toilet abunshi da kyar ta bude idonta ta mike da kyar ta bishi toilet din tana kuka ko kallonta baiyi ba ya cigaba da wankan sa taje ta dauraye fuskarta tanayi kamar bata son tabawa duk yana kallonta mamaki yake wai kyankyamimsa take, shi da yake ba mutum bane yake tsotsar nata shi kuma take jin kyamkyaminsa abun ya bashi haushi gyada kansa kurrum yayi ya daura towol yayi fucewarsa daga toilet din A daddafe tayi wanka ta hada ruwan zafi ta shiga ciki Tana kuka tana taba gurin addu'a take Allah yasa dinki bai wargaje ba _Ni kuwa nace Lallai Hanifa baki da hankali_ Kusan minti ashirin tayi cikin ruwan ta futo d'aura towol tayi ta futo tana tafiya kamar wata yar kaciya dauke kansa yayi yaje yayi kwamciyar sa, cikin kayan da shigo dasu ta duba wasu Sleeping dress ta dauko daya irin mai Riga da wando nan ce amma gajere rigar mai sisirin hannu sanyawa tayi taje ta kwanta tana k'ananun hawaye Khalid kuwa bacci ya daukeshi mai nauyin gaske. Tana kallon fuskarsa da take futar da wani irin annuri haske tana mamakin shin wai shi wane irin mutum ne haka dama haka auran yake ayi tayin Abu daya taji dadi yau da bai Dade ba sosai sau daya yayi amma jiya da shakaran jiya batasan iya adadin da ya Kai b, lumshe idonta tayi bacci na fuzgarta kad'an-kad'an taji wata irin yunwa a haukace ta dura daga bed din niyar futa take sai ta tuno da hoton nan nasu Sonop da gudu ta dawo tana zare ido gaskiya bazata iya futa ba, zama tayi tana Jan kafarshi ya bude idonsa da alamun bacci a tare dashi yace." Menene.''!? S tsorace tace"Yunwa nake ji."!! Bargo yaja yace." Kije parlor ki dauki abincin ki Kar ki kuskura ki kara tashina OK."!!! Baki na rawa tace." Tsoro nake ji." Banza yayi mata ya cigaba da baccin sa..... Yunwa tayi ta zabuarar da ita sai ta sanya kuka ya mike zaune yana dafe kanshi cin yanayi na damuwa yace." Why! Why! Baby kina so ki hanani bacci ne."!? Girgiza kanta tayi yace." Menene. "!? Yunwa nake ji ta k'ara maimata maganar a karo na biyu." Yace." Baki dauko abinci ba kenan. "!? Daga kanta tayi." Mik'ewa yayi ya futa yana Jan tsaki abincin ya dauko mata ya dure a gabanta ransa a bace yace." Gashinan kar ki kuskura ki 'kara tashina."!! Sakkowa tayi ta bude ledar ts Ciro take away din karnin nama na dukanta haka ta dunga cin wata irin jolp din taliya da wasu ganyayyaki taci rabi ta aje robar yoguht ta bude tana sha tana lumshe idonta wani irin azababban amai ya fara taso mata robar yoghurt din ta cire da sauri ta mike ta nufi toilet wani irin amai ta dunga kwarawa sai da ta amayar da duk abunda yake cikinta sannan ta samu lafiya tafi minti goma durkushe a gurin kafin ta yunk'ura ta mike a hankali taje ta wanke bakinta ta tsallake aman ta futa jikinta na kyarma taje ta kwanta kan bed din tsabar zazzab'in da ya rufeta ya sanya ta dunga naninkarshi yana jinta sai ya rungumeta a jikinsa ya cigaba da baccin sa ita kuwa da kyar bacci ya dauketa. *** Misalin shida shaura ya tashi Kai tsaye toilet ya nufa yana sanya 'kafarshi ciki yaji ya taka wani Abu duk da kafarshi da takalmi sai da yaji rashin dadi tsigar jikinsa ta tashi da sauri ya kalli kasan gurin amai ne ca'ba-ca'ba jikin tayas din duk yayi fallatsi jikin bango saurin kauda kansa yayi yana ya mutsa fuskarsa da sauri ya futa daga toilet din muryashi sama yake kiran sunanta. "Hanifa! Hanifa."! Shiru bacci take Mai nauyin gaske ya buga gadon da k'arfi w furgice ta bude idonta tana kallonsa ya watsa mata harara tare da fad'in" Meye wancan a toilet ."!? A kasalance take kokarin tashi zaune tace." Menene. " ? Cikin tsawa yace." Tambaya ta kike."!? Shiru tayi tana tunanin gabanta ya fad'i da ta tuno da aman da tayi jiya baki na rawa ta kalleshi yace. " Dallah tashi kije ki wankewa mutane ni bana son kazanta Wallahi. " kamar zatayi kuka ta tashi ta shiga toilet din jiri na dibarta ta kwance famfo ta fara wanke gurin da kyar ta samu ta gama bata futo ba sai da ta wanke bakinta ta dauro alwala ta fito ko kallonta baiyi ba ya shige toilet din zama tayi gefan gado tana tunanin wai yau itace tayi fashin sallah ta yini guda ba tare da Wani kwakkwaran dalili ba dole ta matsa masa ya kawo mata kayan arziki don Duk kayan da ya shigo mata dasu babu Wanda zata sanya ta iya sallah dasu. Futowa yayi a nutse ya nufi mirror ya fara shafe-shafensa bakinta sai motsi yake Tana so tayi masa magana tana jin tsoron masifar sa. "Sallah nakeso nayi." Tafad'a bakinta nayin rawa. Kallonta yayi ta mirror din ya dauke kansa yace." Ni na hanaki yin sallah ne."!? Tace"Babu kayan arzikin da zan suturce jikina inyi sallah." Tsaki yaja yace."Sai ki bari sai kin samu kayan arzikin sai kiyi sallahr." Wata k'atuwar sif ya nufa k'ananun kayane sa'kale jikin hanga ya cire wasu Riga da wandon jins rigar blue leght ce mai fadi wandon kuma blue ne dark rigar ya tusa cikin wando ya daura blet mai masifar kyau da tsada jikinsa duk tambarin k'asar America sumar shi ya taje ya sanya fencing cap kana ya manna wani bakin glass da yayi masa masifar kyau tana kallonsa ya zauna gefen gado yana d'aura takalmi a kafafunshi ta dunga binsa da kallo kwata kwata babu Wanda zaice cikkaken bahaushe ne dressing din ya mai dashi ruwa biyu kallonta yayi ta cikin glass din ya lumshe idonsa ganin yanda Brest dinta suke shining yace." Zamu futa yanzu Idan kina bukatar wani Abu ki daina Wannan abun da kike ga na danna a parlor masu hidimar gidan zasu shigo sai ki fad'a musu Abunda kike so." Cikin tsoro tace"Don Allah kar ka tafi ka barni." Tsira mata ido yayi yana kallo ya dan shafa sajensa a hankali yace." Idan na zauna din me zakiyi min." Tana goge hawayen dake sauka a fuskarta tace." Kome kake so zanyi maka." Murmushi yayi yace." Jiya me nace kiyi min kika 'ki ai ke din bakauyiyace Sam ba abunda kika iya sai kukan banza. " tace''ni dai kar ka tafi kaji."! Girgiza kansa yayi yace." sorry Bazan Dade ba insha Allah ki kula min da kanki." Hanyar futa ya nufa ta mike da sauri tabi bayanshi rungume shi tayi tana kuka yaji yanda Brest dinta suke sukarshi a baya.... A jiyar zuciya ya sauke yarinyar nan fa tana so ta tsokano shi juyowa yayi ya rike k'afafunta yana kallonta da rikitattun idonsa Wanda suka fara sauya kala harshen sa ya sanya yana lasar fuskarta har ya gangaro bakinta yana so ya kama ta kauda kanta.... Killer smile ya saki ya saketa yana fadin"Ginga illarta ko gashinan daga ganin zanyi kiss dinki kin kauda kanki kuma kina min kuka in zauna a gida in na zauna bazan iya kyakele ki ba." Kofar dakin ya bude yayi fucewarsa ta zube a gurin tana kuka cike da tausayin kanta babu abunda yafi daga mata hankali kamar rashin sallah yanzu yaya zatayi ne." *28/1/2020* _BintuUm@rAbb@le_ [1/29, 11:18 AM] BintaUmarAbbale: _MASHAHURI!!_ _*Ki biya ki karanta cikin kwanciyar hankali, ke kuma da kika futar min da book na barki da Allah!.*_ *08089965176* *07084653262* *0542382124....... Binta Umar Gt bank* *61* Yana futa kai tsaye part din dasu Abbakar suke ya nufa dake a bude yake ya shiga bakin shi da sallama Abbakar ne kawai ya amsa Mobson na toilet na wanka Sonop da Joy suna zaune kan wani makeken kafet suna buga Lodo hannu ya bawa Sonop sukayi gaisuwa irin tasu ta gayu Manson ya futo ciki k'ananun kaya shigar shi duk tafi tasu muni kamar ba bahaushe ba, ko su Sonop basuyi irin shigar shi Khalid dariya yake masa yana nuna shi shi kuma sai wani tsalle yake yana dariya cikin dariya Sonop ya mike yana kallon Khalid ya fara masa magana da turanci wai yana so ya shiga ya gaisa da madam dinshi." Khalid yace." Tana bacci ne sai dai in mun dawo." Lumshe idonsa yayi yana tuno siffofin bab din..... Khalid ya kalli Abbakar dake zaune suna lodo da Joy Cikin harshen Hausa yace." Zamuje mu gaisa da momyn Sonop kana gidane."!? Abbakar ya mike yana fad'in"Mai zai zaunar dani a gida muje nima muga gari." Futa sukayi a tare wata lafiyayyar mota suka nufa Joy ya bude mazaunin dravar ya shiga Mobson ya zauna kusa dashi Khalid da Sonop Abbakar suka zauna a baya, take sautin music ya fara tashi muryar 2pac ta fara tashi cikin wa'kar shi mai taken,Bizzy bone!! Cike da nishadi suka futa daga gidan............. Hanifa da kyar ta duba wata doguwar riga cikin kayan da ya shigo dasu rigar cotton ce amma bata Kai kasa ba ta tsaya mata iya gwiwa duk cikin kayan itace mai dama-dama wata irin hula ta gani cikin kayan kamar ta sanyi ta tattare gashin kanta ta tufke shi hular ta sanya ta zaune gefan gado hade da zabga tagumi yunwa kawai takeji cikinta sai kullewa yake..... A hankali ta mike ta nufi kofar futa sai kuma ta dawo da sauri tana dafe k'irjinta turowa tayi da wannan tafkeken agogon mai dauke da hoton mummunan mutumin nan da danshi gabanta ya dunga fad'uwa yunwa na cigaba da cinta a hankali ta koma ta kwanta kan gadon ta jawo bargo ta rufe har kanta take wasu zafafan hawaye suka fara zubo mata a hankali tace."Wayyo Allah na Ammi na."!! Hawaye ta goge tana shakar majina "Ko wane irin hali Abbu da Ammi suke ciki a yanzu." Cikin zuciyarta take fadin "Wannan maganar. Rungume fulo tayi ta dunga kuka tana fadin" Abbu ka YAFE min ba'a San raina bane abbu nima sonsa ne ya jawo mun." Tana wannan sambatun bacci ya dauketa Cikin baccin nata ta dunga mafarkai Mara dadi ta tashi da wani irin ciwon kai da kyar ta lallab'a ta tashi window dakin ta dake tana kallon harabar gidan gari yayi duhu haske ko ina dab ake da kiran sallahar magariba a ganinta toilet ta nufa kamar wacce kwai ya fashe wa a ciki tayi al'wala tayi rantsuwar sai tayi sallah, tana futowa ta dauki d'ankwalin les din data cire dake yana da girma sai ta Dora skit din kan doguwar rigar jikinta ta hau kan daddumar da taga yayi sallah d'azu sallahr la'asar tayi ta hada da magariba bayan ta idar tayi addu'a ta shafa shiru tayi tana tunane tunane yunwa takeji tana jin tsoron futa parlor dole haka ta hak'ura ta futa dauke kanta tayi Kwata-kwata bata kalli shashen da hoton yake ba a hankali ta latsa abunda ya fada mata aikuwa minti biyu taji ana kokarin bude kofa kafin ta Ankara wani matashin bature ya shigo yana tambayar ta cikin turanci ko akwai abunda take bukata."? Dake ba sosai take jin turancin ba tace." Masa abinci zai kawo mata." Futa yayi ba tare sa yace komai ba, tayi tsaye bakin kofar tana jiranshi minti biyar taga ya futo daga wani guri dake cikin parlor hannunsa dauke da wani tire irin na silver tsorone ya kamata ganin futa yayi amma kuma ya fito daga parlor tayi saurin matsawa tana kallonsa cikin tsoro! Shi kuwa cike da ladabi yake mik'a mata tiran abincin ta karba hannunta na rawa ta shige bedroom din kullewa tayi ta bar key din a jiki zama tayi kasan lallausan kafet din dake kusa da bed ta fara bude abincin saurin rufewa tayi tana ya mutsa fuska Gaza ce guda anyi mata wata irin dahuwa an barbade ta da Wani Abu gasu irin ganyayyaki sai shin kafa da akayi mata dahuwar da faduka da kwai duk ta ca'be babu kyan gani karni ne kawai yake tashi, Hanifa ta tsani karnin ko na menene shiyasa ma bata cin kifi sosai sai dai Jedi jefi da sauri ta bar gurin zuciyarta na wani irin tashi, wai yaya zatayi ne ga yunwa naso ta kasheta tayi a karo na biyu ta futo tana kokarin danna wannan abune taji za'a bude kofa saurin matsawa tayi ta 'buya jikin labule k'amshin turaransa ne ya tabbatar mata da shine da sauri ta futo ta rungume shi ta baya Tana sauke ajiyar zuciya cikin bazata yaji ta ya juyo da ita suna fuskantan juna fuskarsa babu yabo babu fallasa yake kallonta ranshi ya b'aci ganin irin shigar dake jikinta a fusace yace." Wannan wane irin iskancin ne duk ina kayan dana shigo miki dasu jiya zakiyi irin wannan haukan." Kallonsa tayi tana turo baki tunkude ta yayi tayi kamar zata fadi ta tsaya tana kallonshi ya shiga bedroom din bin bayansa tayi jikinta duk a sanyaye ya mik'a wata mutsiyaciyar riga mai madauri a wuya rigar tana da gidan nono kuma duk bayanta a bude yake gashi iyakacinta gwiwa yace." Maza ki sanya yanzu ki futo parlor Sonop naso Ku gaisa duk ya damu dake ke kuma kina so Kiyi wa mutane hauka."!!! Rigar take bi da kallo tana kallonsa tace."Ni bazan sa wannan rigar ba wani ya ganki gaskiya bazanyi Wannan kafurcinba ko bani da aure bai hallataba ballanta da aurena." Fuskarta a hade ta fad'i maganar sakin bakinsa yayi yana kallonta kafin yace." Ke ni kike cewa kina da aure."!? Kasa tayi da kanta tana wasa da hannunta ya jefa mata rigar a fuska ya fuce yana huci! Bayansa tabi da kallo Yanzu ta fara jin haushin wannan dabi'ar tashi idan shi yace tasa masa rigar zata sanya masa amma baza ta ita futar da tsaicinta gasu gardawa ba, dake a bude ya bar kofar tana jiyo hayaninyarsu a parlor sun kunna kad'e-kad'e da ya cika gidan sai ciye-ciye sukeyi mik'ewa tayi ta karasa bakin kofar tana le'kensu tafi minti goma tsaye a gurin tana sakawa da kwance kafin tayi shahada ta futa parlorn bayan ta yafe jikinta da d'ankwalin les din tunda ya hango futowar ta haka yaji ranshi yayi mugun b'aci hula daban Riga daban siket daban wai Wannan yarinyar wace irin yar kyauyece."! Kasa yayi da kansa har ta karaso tsakiyar parlor cikin tsarguwa ta fara gaishe su Sonop ya tsira mata ido yana lashe jajayen lebansa, cikin turanci yake tsokanar ta ita dai batashi take ba hankalinta duk na kan lemon zakin da taga suna sha dasu abarbaba kayan marmari ga sunan nau'i nau'i Khalid take kallo tana marairaice fuska Mobson ya kalleta da murmushi a fuskarsa yace."Ya akayi ne madam ko kinaso kiyi magana dashi ne." Daga kanta tayi cikin tausayin kanta tana jin takaicin irin wulakancin da yake mata, Sonop ne yace." Guy ga madam na magana." Ka tsaye yace." Bani da lokacinta Mtsss! Da tsaki ya karasa maganar. Shiru sukayi Abbakar yaji rashin dadi yana tausayin Hanifa a garin da bata da kowa gashi ya lura da irin rashin kirkin da abokin nasa yake mata. Jikinta babu kwari ta juya da niyar barin gurin tana matse hawayen da yake kokarin zubo mata.... Wani irin kallon sha'awa Sonop ya bita dashi ya kalli Khalid da hankalin shi ke kan wayar dake hannunsa cikin turanci yace." Guy ya kamata kaje ka kula yarinyar mybe akwai abunda take bukata fa." Khalid yace." Rabu da yar'kauye ta bata min rai ne." Sonop ya mike ba tare da Neman izini ba kawai ya shiga bedroom din da Hanifa ke ciki tana kife kan bed tana kuka taji motsin shigowa dakin kin d'agawa tayi tana tunanin shine sai da ya kusantota sannan taji wani irin k'amshin turare na daban ba irin nashi ba dagowa tayi idonta jage-jage da hawaye kawai ta ganshi tsaye a kanta yana mata wani irin kallo.... Da sauri ta zabura ta ma'kure jikin bango tana kallon sa ita fa ta tsani kallon fuskarsa sai kace soyayyan kosai jazur da ita da wani ido kananu ganin jikinta na kyarma yasa ya zaune gefan bed din a hankali yace."Bab take it easy ki nutsu kinji ko." Shiru tayi tana kallonsa yace." Kukan me kikeyi ne? Kome kikeso ki fad'a za'ayi miki Khalid yace kinyi masa laifi ne ki daina kuka banaso. "! Yafad'a yana ya mutsa fuska.!!! Kokarin dura kasa take ya rike hannunta yarrrr taji ta kwala kara Khalid ya shigo dakin ganin Sonop zaune gefen gadon hannunsa rike da nata bai dame shi yace." Guy ka k'yaleta kawai wannan yarinyar yar taurin kaice duk abunda nakeso bashi take so fa tun ranar da aka d'aura mana aure da ita take bani wahala komai nace baza tayi ba kasan bana son takura ina ganin zan maida ita najeria ne kafin in gama abunda ya kawo ni 'k'asar nan." Sonop yace." Guy baza ayi hakaba zata zauna tare dakai damu na lura akwai rashin wayewa a tartare da ita idan babu damuwa zamuje da ita can gurin Momyna akwai Aunty's dina ina nufin 'kannan Momy zasu koya mata zamantakewa." Hanifa tana kuka tana kokarin fuzge hannunta da Sonop ya rike tana jin ciwon abunda yake mata ga Khalid a tsaye ya kasa hanashi dake cikin turanci suke magana yasa bata fahimci komai ba Khalid yace." Good Wannan maganar taka tayi min sosai duba jikinta fa ga gani irin dressing din da tayi babu kyawun gani haka zata sa na saurare ta ne."!! Sonop yace." Na lura akwai yunwa a tartare da ita ya kamata ka tsaya a kanta sosai ka tabbatar da cinta in yaso ko meye sai ya biyo baya. " sakin hannunta yayi mike yana kallonta wata irin gawurtacciyar sha'awarta na yunkoro masa, futa yayi daga dakin yana cije leps dinshi Hanifa ta dunga kuka tana birgima kan bed din tana fadin"Allah ya Isar min Wannan mutumin da ya taba min jiki kana kallonsa Allah ya Isar mun Khalid yau nayi nadamar auranka nayi nadamar za'barka a matsayin miji Allah ya Isar min abunda kayi min ka yaudare n.......... Kafin ta 'karasa maganar dake bakinta ya d'agota a fusace ya kifa mata Wani gigita can mari da sai da taga taurari yana huci! Yace.' Ni kike zagi kina gayawa magana Dan ubanki."!! Hanifa ta rike kuncinta cikin 'barin jiki take kallonsa le'banta sai rawa yake wasu irin zafafafan hawaye sai zarya suke a kuncinta. Cikin yanayi na fushi da b'acin rai! Yace." Wallahi ki shiga hankali ki San irin maganar da zaki na fadamin Dan ubanki ni sa'anki ne ko kuma don kinga na aureki na kwanta dake gado d'aya kike kokarin zagina shin kinsan ni wanene kuwa."!? Hawaye take tana kallonsa ya tattaro miyau na bakinsa ya tofa mata a fuska becafull!!!! Futa yayi daga dakin a mugun fusace!! Suna ganin yanayin da ya futo suka San akwai matsala cikin damuwa Sonop yake Dan dukan bayan shi cikin harshen turanci yake masa magana kan yayu a hankali da komai tunda akwai karancin wayewa a tartare da yarinyar Dole ya fuskanci matsala Khalid sai sauke ajiyar zuciya yake cike da b'acin rai yace." Ku muje muyi abunda ke gabanmu Mobson ya mike yana gyara wandon shi dake sabulewa babu abunda ya dameshi da abunda ya faru da Khalid din da hanifa shi dai burinsa ya za'ayi ya daukaka akasar yana so ya zama big boy so yake ya samu daukakar da tafi ta Khalid din shiyasa yake yiwa Sonop ladabi duk abunda yace ko bai dai-dai bane to a gurinsa dai-dai ne Abbakar kuwa jikinsa duk yayi sanyi da al'amarin bai taba tsammanin khalid zai yiwa yarinyar hakaba duba da irin yanda ya haukace a kanta amma tashi guda har ya sanja hali akanta lallai Adam babu mai iya masa sai Allah amma yana ganin idan haka ta cigaba da faruwa tsakaninsu to zai zauna da Khalid din kome zai faru tsakaninsu ya shirya masa futa sukayi Khalid zuciyarsa duk babu dadi kai tsaye wani had'addan club suka nufa suna so su samu manya-many bebies ne sun shirya zasu shiga studio ne akwai wata wa'ka da Khalid din ya shirya to dole sai da mata da maza ne saboda yanda yanayin ta yake............ Kuka taci iya son ranta ta hak'ura tunda babu mai rarrashinta da kyar ta mike ta futo parlor haske ko ina ga TV na ta faman aiki karar kida duk ya cika parlor suna kallon album na wa'kokin turawa ne gashinan abun babu kyawun gani abunda ya futo da Ita parlor shi ta dauka ta koma d'akinta kofar ta kulle ta bar key din a jiki doguwar ledar ta zazzage kasa taga hijabai biyu da dogwayen riguna biyu hamdala tayi ga Allah ta zauna ta fara shan Lemo da abarba sha take kamar wata mayunwaciya taji dadinsu sosai har ta rage wani guda hudu gatsa tayi ta jingina jikinta jikin bed tana tunanin yanayin rayuwa idan da tasan wannan rayuwar zata fuskanta da auran Khalid da bata aure shi ba abunda take fada cikin zuciyarta ta bude idonta a hankali tana shafa kuncinta wai ita ya Mara har yana zagin ubanta hawaye ya zubo mata majina taja ta mike jikinta duk yayi mata tsani! Toilet ta shiga ta hada ruwa tayi wanka ta shiga wani kimanin minti ashirin tayi a ciki ta futo towol ta d'aura ta futo duguwar rigar ta zura a jikinta ta bud'e ledar pants daya ta dauka ta sanya a jikinta ko brzy batasa ba ta kwanta kan bed ta lullub'e jikinta zuciyarta sai wani irin 'kuna take mata daga zarar ta tuno Ammi da Abbu sai taji hawaye addu'a take tana jin wani irin zafi a zuciyarta har bacci ya dauketa cikin baccinta ta dinga jin bugu Yana kiran sunanunta sama-sama mik'ewa tayi zaune tana kokarin sauka daga bed din wata zuciyar tace "Kar ki bude masa ki koma kiyi kwamciyar ki ." Komawa tayi ta kwanta tana tsaki yanzu ji take bata da makiyi kamarshi. Ranshi a bace ya bar jikin kofar zama yayi kan kujera yana jin yanda mararsa take daurewa ganin lafiyayyun bebis ya tayar masa da hankali yaji yana sha'awar sex shiyasa ya dawo gida yanzu haka Ya bar su Sonop a can ko wanne yana morewa shi ya dawo ta rufe masa kofa ..... Jin kamar zai suma yasa ya mike cikin zama ya futa mota ya nufa ya figeta da gudu kai tsaye club din ya nufa yana ganin bazai zauna ya halaka kansa a banza ba. *************************⬇********************** ************* Ai Hausa Novels **************** *************************⬆ ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ⬇ ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ⬆ ************************** *29/1/2020* _BintuUm@rAbb@le_