Compilied By Abubakar Saleh AlQuyraemey Whatsapp Number 08138873799 Visit www.rumbunlabarai.com For More Complete Documents [3/6, 8:45 AM] 💜: *GA IRINTA NAN!!!🙆🏼‍♀️* _(LOVE STORY🌺)_ *NA* _BINTU UMAR ABBALE🍒_ *MANAZARTA WRITES ASSO🖊️📚* _______ *DANDANO🥰* *1* Cikin tsananin gajiya da ishirwa nake tafiya burina kawai na isa gida na samu na watsa ruwa a jikina na kwanta na hutawa rayuwata. gabana ne ya fad'i! lokacin dana tuna d'an iskan yaron nan yana gari nasan da wuya ya barni na sha ruwa a gidan Khalid mugun fitinan nan yaro ne wallahi........Daf da zan shiga layin namu motar Alhaji Nura take kokarin fitowa d'auke kaina nayi na bashi hanya domin ya wuce! girgiza kaina nayi ganin yayi parking din motar ya tsaya cikin raina nace"Ai dama na san sai ya tsaya, galashin motar ya sauke muka had'a ido fuskata na saki nace"Alhaji barka da rana." Cikin kulawa yace."Barka dai Sa'ida ya aiki."? Nace" Aiki Alhamdullihi." kokarin wuce wa nake ya dakatar dani da fad'in "Sa'ida ina al'kawarinmu."? Gefan hijab d'ina nasa na goge gumin fuskata nace" Alhaji al'kawari yana nan inaso na ware ranakun da zan fara gudanar da aikin naka." Yace."Me zai hana ki ware ranaku biyu a cikin sati wato alhamis da juma'a tunda a ranakun yaran basa zuwa isilamiyya in yaso idan sun dawo daga boko misalin biyu ko uku sai ki dinga shiga kina musu lesson d'in." Shuru nai ina nazarin maganarsa nace"Shikkenan Alhaji zan duba maganarka insha Allahu." Yace."To godiya nake gimbiya duk shawarar da kika yanke sai ki kira waya ta ki sanar dani." Nace"To shikkenan babu damuwa." Har nayi yunkurin barin gurin ya dakatar dani! cikin k'osawa na tsaya amma ban nuna masa ba, kudi ya miko min kusan dubu biyar.....murmushi nai nace"Kasan ba zan kar'ba Alhaji nagode." da sauri na bar gurin ina mamakin yawan kyautar da yake min duk had'uwar da zamuyi sai ya dauki kudi ya bani bayan uwar hidimar da yake mana a gida........Tun kafin na karasa na hangoshi dogare a bakin kofar gidan namu yana sanye da k'ananun kaya 3qutar da singlet wacce ta matse shi gabad'aya suffarsa ta mazantaka ta bayyana Gabana ya yanke ya fad'i! duk sanda zan ganshi a haka hankalina yakan tashi ni kaina ina mamakin halin da nake shiga wannan dalilin yasa idan yana gida bana sakewa sosai mutukar zai dinga shige da fice a gidan babu sutturar arziki a jikinsa. Fuska a murtuke na 'karaso...."Malami Bani hanya na wuce." babu wasa nayi maganar. Hanyar ya sake tarewa yana kallona da 'batacciyar fuska yace."Aunty Sa'ida me ya tsayar dake a gurin wancan mutumin."? wani irin kallo na watsa masa nace"Ina ruwanka da shiga sabgar da bata shafeka ba, dan Allah ni bani guri na wuce na gaji." Hanya ya matsa min naja tsaki had'e da kokarin ra'bashi na wuce kawai naji ya matseni a jikin kofar fuskokinmu suka hade numfashin mu na had'uwa. Cikin fad'uwar gaba na tureshi! nayi saurin fad'awa soron ina addua akan Allah yasa wani bai ganmu ba! hannuna ya rike yana marairaice fuska yace."Kina so zuciyata ta buga ko na hanaki kula wancan Alhaji kin raina magana ta ko." Cikin takaici nake kallonsa a fusace! nace"Wallahi Khalid ranka zai 'baci! mutukar baka fita harkata ba shin wai ni sa'arka ce da zaka dinga yi min iskanci." Zuba min idonsa yayi fuskarsa a had'e yace."Ni ina sonki Aunty Sa'ida kuma kin san Allah baki da miji sai ni da kika raina zaki gane baki da wayo." Yana gama maganarsa ya fita, na dinga kallon bakin kofar ina mamakin maganarsa, bani da miji sai shi! Lallai Khalid baida hankali da tunani. tsaki naja na shiga gidan raina duk babu dadi. "Ummatu sannu da aiki." ciki-ciki ta amsa min ban damu da yanda ta amsa maganata ba kawai na shige ciki gidan, Gwaggo kakarmu na samu tana kad'in lagwani! hijab na cire na nemi guri na kwanta ina mayar da numfashi. Kallona tayi tana cigaba da kad'in ta tace" Yau kin dad'e baki dawo ba Sa'ida anya baki fara yawace yawace ba ni wallahi wannan aikin naki ban yardar dashi ba." Cikin mamaki na kalleta, tace"Ai da gaskiyata wane irin aiki ne wannan da za'a fita tun karfe takwas ba za'a dawo ba sai karfe uku ko biyu haba jama'a." Murya na rawa Nace"Gwaggo mai kike nufi dani."? ba tare da wata damuwa ba tace"Abinda nake nufi ai kin san shi." "Kina nufin ina yawon karuwanci kenan."? da sauri tace." Ooh! ni kada ki daura min jakar tsaba ba haka nake nufi ba." hawaye na zuba nace"To meye na cewa baki yarda da aikina ba wato kema kin fara daukar magana aikaina ko." Shuru tayi tana cigaba da kad'in ta, komawa nayi na kwanta hawaye wani nabin wani! nace"Wato saboda 'kasa ta rufe fuskar mahaifina shiyasa kike nema ki d'ora min kazafin na zina kamar bake kika haifi ubana ba." "Kinga Sa'ida kada kisa hawan jinina ya tashi da wannan magana taki ta isheni haka aiki kije kiyi tayi tunda ba zakiyi aure ba sharrin zina da bin maza dole jama'ar gari suyi miki." Da sauri na mike Nace"Gwaggo na gaji zan tattara kayana na koma gurin mahaifiyata tunda keda kika haifi ubana kin kasa yi min uziri a rayuwa ta ni ba ni zan dauki kaina nakai gidan aure ba sai ranar da Allah ya nufa to tunda kun kasa fahimta zan bar muku gidanku." Saukowa nayi na fara hada kayana, Kayan kad'in ta ajiye a gefe tace"Ke Sa'ida bana son shashanci da rashin tunani babu inda zakije kinji na fada miki maganar aure kuma ba zan fasa yi miki ba har sai kin tsayar da miji zanja bakina nai shuru to kaji." Jakar kayana na dauka na kama hanyar fita, sai ta fashe da kuka da fad'in" Au! takani zakiyi ki wuce to bari Babanku Iro ya shigo zan fada masa rashin mutuncin da kike min." Saboda nasan banyi abinda take zargina dashi ba yasa ko sauraranta banyi ba na fita daga dakin da kayana a hannu, haba jamaa na gaji da masifar Gwaggo. Turus! nayi ganin Baba Iro a tsaye suna magana da matarsa! ya kalleni yana kokarin yayi magana! Gwaggo ta fito daga daki tana kuka da fyatar majina da sauri ya karaso gurin yana fadin"Gwaggo lafiya kukan me kike."? Ta 'kara rurucewa da kuka da fadin"Gatanan saboda nai mata maganar aure shine ta hada kayanta wai gurin uwarta zata koma shine har tana sa kafarta tana taka ni ta wuce." Da sauri na kalleta ina mamakin sharrin ta gwaggo tsohuwa mai sharrin tsiya. Baba Iro murmushi yayi inda sabo ya saba raba fad'a tsakanin mahaifiyar tasa da 'Yar d'an uwansa Yace."Haba Sa'ida in da sabo ai yaci ace kin saba da halin Gwaggo me yasa ba zakiyi hakuri ba yanzu da kika had'a kayanki ina kike nufin zuwa." Gwaggo da sauri tace" Zataje can gurin Uwarta ne." Cikin k'unci nace" Baba Iro wai kamar gwaggo itace take min k'azafi to meye amfanin zamana da ita." "Aa ni kada kiyi min sharri Sa'ida daka fada miki gaskiya sai kice nayi miki sharri." Baba Iro yace."Gwaggo maganar ta 'kare haka." Tace."To kace mata kada ta tafi dan taurin kaine da ita." Baba Iro yasa hannu yana kokarin kar'bar jakar hannuna, nace"Baba dan Allah ka kyaleni na tafi wallahi na gaji da rashin hakurin gwaggo ka gafarce ni idan maganata ta 'bata maka rai." Yana 'kokarin magana ya shigo gidan hannunsa ri'ke da leda indomee yaje ya siyo, babu walwala a fuskarsa yace."Me yake faruwa ne naga duk kunyi cirko-cirko a tsaye." Da sauri gwaggo tace"Yawwa d'a nagari ka ganta nan wai barin gida zatayi saboda nai mata maganar aure." wani irin kallo yayi min kafin ya kalli jakar kayana dake hannun mahaifinsa, cikin yanayin takunsa ya karaso inda muke jakar kayan ya kar'ba hannun mahaifin nasa ba tare da yace wani abu ba ya shige dakin Gwaggo da jakar gwaggo bayansa tabi tana surutai! Baba Iro ya kalleni a nutse yace."Sa'ida kiyi hakuri kinji ko gwaggo tun kafin ta tsufa take da rikici ki fahimci halinta sai ki zauna lafiya kada wani sa'bani ya sake shiga tsakaninki da ita kice zaki bar gida nan shine tushenki, sannan kuma inaso ki bawa Alhaji Nura dama ya turo da maganar aure kamar yanda ya nuna alama. Nace"Kawu babu wata maganar aure data ta'ba shiga tsakanina da Alhaji Nura kawai muna gaisawar mutunci dashi ne." Cike da mamaki yace."Sa'ida babu maganar aure data ta'ba shiga tsakanin ki da Alhaji Nura amma yake mana hidima a gida." murmushin takaici nayi nace."Wallahi Kawu babu maganar aure a tsakanina dashi." girgiza kansa ya shigayi yana mamakin maganar, yace."Shikkenan to tunda kince haka dukkaninmu zamu cigaba dayi miki addua akan Allah ya baki miji nagari." a cikin zuciyata na amsa da ameen. gurin ya bari nima a sanyaye na d'aga labulan dakin Gwaggo na shiga, abinda naji suna tattaunawa yasa gabana fad'uwa.... *Masoya ayi min sharing A gruops👏🏻* *IDAN KINA BUKATA KARANTA LITTAFIN NAN #400 NE NORMAL VIP GRUOP #600 ZA'A TURA KUDIN TA WANNAN ACCOUNT DIN.....0542382124....BINTA UMAR GTBANK....IDAN KATIN WAYA ZAKI TURO SAI KIYI MIN MAGANA TA WHATSAPP DA WANNAN NUMBER* *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* [3/6, 8:45 AM] 💜: *GA IRINTA NAN!!!🙆🏼‍♀️* _(LOVE STORY🌺)_ *NA* _BINTU UMAR ABBALE🍒_ *MANAZARTA WRITES ASSO🖊️📚* *2* "Haba 'Da nagari ai idan da gaske kake wallahi ni zan baka goyon baya kaga sai ayi towo na maina dama hausawa na cewa gida bai koshi ba ai ba za'a kaiwa dawa ba insha Allahu Sa'ida matarka c.....Shigowa ta dakin ya hanata k'arasa maganar gabad'aya ita dashi suka bini da kallo, ni kam jiri ne naji yana nema ya kayar dani a gurin dan tsaf na fahimci akan abinda suke tattaunawa Khalid yayi masifar raina ni da har yake iya bud'ar baki ya furta min kalmar so ina a matsayin yayarsa wacce ta girme masa nesa ba kusa ba na rasa wane irin tsaurin ido ne da yaron a matsayina da tsayin shekaruna sai nake ganin bai cancanta ya iya kallon tsabar idona yazo min da wata banzar maganarsa ba, Khalid da wayo na da shekaruna yayi girman jikin da yake tunk'aho dashi kuruciyarsa kaf a gaban idona yayi ta amma yau wai an wayi gari ni yake tare wa hanya yana cewa yana sona. Kwanciya nayi ba tare dana cire hijabin jikina ba kawai na dinga binsu da kallo ina jin tsantsar takaici a cikin zuciyata ni kam ko zan rasa miji a gidan duniya banga abin aure a jikin wannan mara mutuncin yaron ba........Tun sanda na kwanta a gadon yake min wani d'an iskan kallo irin na manufarci a hasale! nace"Wallahi idan baka daina yi min wannan d'an iskan kallon ba sai ranka ya 'baci shashashan yaro mara kunyar banza da wofi." 'Bata fuskarsa yayi dan har sai da fatar saman goshinsa ta tattare haka yake tun yana yaro idan ransa ya 'baci sai goshinsa ya tattare ya watsa min kallon banza had'e da girgiza kansa.......Yana kokarin yin magana ta rigashi da fadin" Ke Sa'ida meye kuma na kiransa shashasha ina laifin wanda zai tallafe ki ni wallahi naji dadin maganar da yazo min da ita duk girmanki da shekarunki ba zaki gagareshi ba dan mace komai girmanta bata fin karfin namiji." Tsaki! naja ba tare da nace komai ba na juya musu baya....'Kawataccen sajan fuskarsa ya shafa idonsa 'kur! a mazaunanta da yake bala'in 'kwa-'kwa! duk da da hijabi a jikinta hakan bai hanashi ganin tudunsu ba, ya dinga jin wata lafiyayyar sha'awa na taso masa, a sanyaye ya kalli Kakar tasu yace."Gwaggo ga indomee na nan ki dafa min zanje na dawo." da sauri tace"To d'a nagari bari na kunna risho ai ina da kalanzir a ciki." Fita yayi daga dakin yana shafa sumar kansa. Sama-sama nake jin surutan ta kafin bacci mai nauyi yayi gaba dani......Can cikin baccin naji maganarsa sama-sama! "Haba gwaggo kefe ba'a abin arziki dake yanzu dan Allah haka ake dafa Indomee duba kin zabga mata ruwa sai iyo take a ciki kawai kinsa nai asarar kudina." Zaune na mike nai saurin cire hijabin jikina jin yanda ya jike da gumi! ina kallonsa yasa hannu yana sosa kansa idonsa kur! a kirjina. girgiza kaina kawai nayi na fara yunk'urin mikewa......Tace."Sa'ida duba dan Allah wai duk wannan gwanintar da nayi masa ban birgeshi ba cewa yake banyi daidai ba." Tukunyar indomee din na kalla da sauri na dauke kaina jin dariya na nema ta sub'ce min indomee guda uku amma ta cika tukunya da ruwa indomeen tayi tsululu duk ta narke a ciki.........Yace." gwaggo bafa zanyi asarar kudina ba ki cinye wannan indomee ki bani dari ukuna ba." da sauri tace ." Wallahi baka isa ba ba zanci kayan atini ba hakan nan zaka daure kaci idan kuma ba hakaba Sa'ida ta baka wata indomee tunda tana da ita in yaso sai ka kaiwa babarka ta dafa maka tunda ni ban iya ba." Ta'be bakinsa yayi yace."Sai dai na kwana da yunwa akan na kar'bi abunta ni ba shashashan namiji bane kamar yanda take kira na nafi karfin ta ciyar dani sai dai ni na ciyar da ita." Gwaggo sakin baki tai tana kallonsa sai kuma tayi dariya da Fadin"Khalid jarumi a gida da wajan ya'ki ka burgeni kwarai da gaske yanzu dai kayi hakuri akan 'barnar da nayi maka." Girgiza kansa yayi yace."Bafa zan hakura ba bari ma ki gani." da sauri ya fara lalaben inda take ajiye Pose d'inta.... Da sauri ta ri'ke gefan rigarsa "Aa Khalid kada ka daukar min kudi wallahi zanyi maka rashin mutunci idan ka daukar kwabo a cikin jakata.....Fita nai daga dakin na barsu suna bugawa dama inda sabo sun saba idan 'yan abin arzikin na kusa suyi ta mutunci idan kuma 'yan tsiyar na kusa suyi ta bugawa, Gwaggo san kudin tsiya ne da ita duk neman da take ba zata ci a cikinta ba sai tai ta tara kudin tana 'boyewa a cewarta sai auran Sa'ida ya tashi sai tayi mata kayan daki da kudin......Pose din ya bude yaga kudi dan'kam 'yan dubu dubu duk sunfi yawa, yace." Lallai tsohuwar nan kudi ne dake duba dan Allah Jakarki kamar ta matar alhaji." Tana kokarin fizge jakar tace"Khalid wannan kudin da kagani ba nawa bane kada ka dauki ko kwabo a ciki." Murmushi yayi yace."Haba gwaggo ina ganin kudi ki hanani kin san Allah sai na dauka." dubu daya ya zara yasa a aljihunsa ya mika mata jakarta, aikuwa ta dinga yi masa mita tana surutai dariya yayi ya kama hanyar fita daga dakin da fadin"Ki cinye indomee da kika dafa ni kuma anjima zanje tevur din mai shayi." Tace."Kaji dai dashi saboda kai zan sanjawa jakata guri haka kawai ba zaka zo kana daukar min kudi ba." Ni dai Ina alwala ina dariya a cikin raina gwaggo san kudi Khalid son kudi koda yake dole Khalid yaso kudi tunda dan makaranta ne yanzu haka yana daf da kammala karatunsa a jami'ar Bayero dake jahar kano yana zuwa gida duk bayan wata guda yayi hutu na kwana biyu ya koma makarana.. 'Dakin na shiga na sameta tana ta surutai uffan bance mata ba dan har yanxu haushinta nake ji akan irin abubuwan da take min, na gyara dadduma a nutse na fara kokarin tayar da sallah, tace"Sa'ida dan Allah ungo wannan jakar tawa ki 'boye min Khalid ya gane inda nake ajiyeta nasan kuma shikkenan kafin ya tafi sai ya tatike ni." Ba tare dana kalleta ba nace"Ki ajiyeta nan na idar da sallah." tace"To 'yar albarka, tukunyar indomeen da sauke daga kan risho tana fad'in "Waye zai ci wannan ai ko almajiri ba zan bawa ba zubar dashi zanyi dan ni banga abinso a wannan abincin ba.....har na idar da sallah gwaggo bata fasa surutai ba nace" Yau me aka girka a gidan.'' Ta'be bakinta tayi 'kasa-'kasa tace"Kin san halin matar gidan da jarabar son d'anwake shi tayi masifaffiyar mata kawai na haifi d'ana amma tafi ni iko dashi dama nasan Rabi tana bin malamai akan Ibrahim." Cikin mamaki na kalleta halin gwaggo sai ita surukar ta ma bata kyale ba kullum cikin zaginta take amma ba tayi a gaban idonta sai a bayan idonta dan itama Ummatu bata daukar raini mara mutuncin kanta ce nace"Gwaggo dan Allah ki daina wannan halin ki zauna lafiya da kowa yanzu meye amfanin zagin Ummatu har kina cewa tana asiri." Baki ta rike tana kallon hanya tace."Ke! Sa'ida maganar ta isa haka kada ki d'aga murya taji amma ni tuntuni Uwale ta tabbatar min da cewa Ummatu ba'a zaune take ba tana yawace-yawacan malamai wai shin bakya ganin ko kara ta ajiye babanku baya iya tsallakawa gashi muma ta daure mana baki dik abinda tayi a gidan shine daidai sannan kice nai mata sharri." Nace"Gwaggo ki rabu da Uwale munafuka ce wallahi tana so ta had'a ki rigima da surukar ki ita kuma ta zauna lafiya da tata idan ba hakaba meye na cewa Ummatu na bin malam......bakina ta rufe tana zazzare ido irin na rashin gaskiya tace."Haba Sa'ida nace dake ki daina kiran sunanta kada taji haba jama'a yarinya ba'a sirri da ita mtssw maganar a barta haka." Murmushi kawai nayi na mike tsaye ina ninke dadduma, ta mika min pose din nata da fad'in "Kar'bi ki adana min kada ya shigo ya sake daukar min kudi." karba nayi na bude gurin da nake ajiye tufafina nasa key na kulle..........Da yake idan mun dauki albashi duk abinda nake bukata naci da sha dana d'aurawa ina siyan abina na ajiye duk ranar da akayi abinda bana ra'ayi sai nayi girkina naci na koshi, fita nayi tsakar gida na dauko doya a kicin na zauna tsakar gidan ina feraye wa. Fitowa tayi daga dakin da buta a hannunta Gwaggo duk rintsi bata bari yara suyi mata wasa da butar alwalarta kullum butar ta cike take da ruwa Macace mai tsafta da kula da ibadah dama dan adam tara yake bai cika goma ba, ganin ina feraye doya yasa ta washe baki da fad'in "A lallai kice yau dadi zamu ci a gidan." Murmushi nai ina kallonta gwaggo akwai kwadayi amma bata yarda ta fitar da kudinta ta siyi abinda take so ba. Nace"Eh lallai doya da kwai zan soya nayi miyar alayyahu saboda haka ke zaki bayar da kudin 'kwai dan banda kudi." shuru tayi tana kallona dariya ta kusa ta su'bce min. Tace." Inji dai guda biyu zai isa." Nace"Haba gwaggo a wannan uwar doyar za'a sa 'kwai biyu guda biyar zaki siya." tace"Haba Sa'ida 'kwai biyar nawa kenan."? kai tsaye nace"Dari uku da hamsin." shuru tayi tana nazari kafin ta girgiza kanta tace"Bari dai nai sallah muyi maganar haba Jama'a yanda rayuwa nan tayi wahala kice 'kwai biyar ina laifi biyu ko uku." Bin ta nayi da kallo ina k'unshe dariya gwaggo kenan mai kwad'ayin tsiya.......Hayaniyarsu naji yo daga waje kafin nayi wani yun'kuri sun shigo gidan su uku, babu walwala na daga kaina ina kallonsu su biyu suna sanye da kayan 'kwallo (ball) mayar da kaina kasa nayi na cigaba da abinda nake naji yace."Salim ku jira ni nasa kayana na fito." Suka ce okey kayi sauri dan Allah." cikin zuciyata nace "Aikin kenan." " Aunty Sa'ida barka da Yamma." a nutse nace" Barka Salim ya kuke." ya d'an sosa kansa yana mirmushi yace "Lafiya aunty muna fatan kina lafiya." " Lafiya Kalau nake." shuru gurin yay na minti biyu na dago kaina kawai sai naga sun zuba min ido! cikin 'bacin rai nace"Salim kaima ka fara zama mara kunya ko."? da sauri yace."Aunty mai ya faru."? girgiza kaina nayi nace"Kuje waje gashinan fitowa daga yau kada ku sake shigowa gidan nan tunda duk kun zama baligai." Wannan magana da tayi a kunnasa ya karaso gurin yana mata kallon daya saba "Akan me zaki hanasu shigowa gida abokaina ne na 'kuruciya kin sansu kin san iyayensu kuma iyakacinsu nan bakin 'kofa ko wani yayi miki abinda bai kamata ba." Nace"Khalid na hanasu shigowa gidan nan saboda bai kamata ba su tsaya a waje ka fito ka samesu." Girgiza kansa yayi yace." Keda Gwaggo babu nauyin auran kowa a kanku meye dan abokaina sun shigo kike fita kina yawo a titi gardawa na kallonki a ofis d'inku na malaman makaranta akwai baligan da suka ci uwar abokaina a kuyanci kike mu'amula dasu baki damu ba sai dan kawai abokaina sun shigo gida kice su daina shigowa ba zai yiwu ba." "Khalid ni kakewa rashin kunya."? ba tare daya kulani ba yace." Salim ku muje dan Allah.'' gaba yayi suka rufa masa baya, girgiza kaina nayi aikuwa zan samu Baba Iro da maganar dole ya tsawatar musu akan su daina shigowa mutane gida kai tsaye............. *Masoya a taimaka ayi min sharing🥰👏🏻* *IDAN KINA BUKATAR KI BIYA KUDIN LITTAFIN GA YANDA ABIN YAKE NORMAL GRUOP#300 VIP GRUOP#600 ACCOUNT.....0542382124....BINTA UMAR GTBANK....IDAN KATI ZAKI TURO #400 NE SAI KIYI MIN MAGANA TA WHATSAPP DA WANNAN NUMBER* *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* [3/6, 8:45 AM] 💜: *GA IRINTA NAN!!!🙆🏼‍♀️* _(LOVE STORY🌺)_ *NA* _BINTU UMAR ABBALE🍒_ *MANAZARTA WRITES ASSO🖊️📚* *3* Motsin fitowarta daga band'aki yasa nai saurin kallon gurin, asuwakin ta dake kan taga (window) ta dauka tana gyarawa tace"Surutun me nake ji ne ina bandaki naji kamar muryar Khalid kuna sa'insa." shuru nayi mata saboda nasan ko na fada mata dalili bai zama lallai ta bani gaskiya ba, zama tayi kan kujera 'yar tsuguno tana kokarin sanya asuwakin a bakinta tace."Sa'ida in dai akace wannan namiji ne to komai 'kan'kantarsa jagora ne idan kina hantarar Khalid wani sa'in haushi kike bani dan duk 'kan'kantarsa da kika raina watarana shine zai jagorance ki." Kallonta nayi ina mamakin maganarta "A'ina Khalid din zai jagorance ni gwaggo dan Allah idan zaki fad'i magana ki dinga tsayawa kina tunani kafin ki fad'a yaro 'kan'kani kina maganar zai jagorance ni Khalid mai ya sani a rayuwa."? Tana goge bakinta da asuwakin tace"Oho! ni dai na fad'a miki gaskiya ki daina raina Khalid da 'kan'kantar shekarunsa komai girmanki ba gagararsa zakiyi ba." Cike da bacin rai nake kallonta, ta d'auraye asuwakin ta ajiyeshi a gefe cikin nutsuwa ta fara d'aura alwala. Kaina na girgiza ina jin tamkar zuciyata ta tsage saboda 'bacin rai gwaggo ta iya kuntukawa mutum abin haushi tayi kamar ba tayi ba, tabbas da wata ko wani ne yayi min wannan banzar magana wallahi sai nayi masa rashin mutumci amma da yake itace babu yanda na iya da ita dole nayi hakuri dan idan nace zanyi magana zata iya yanko wata maganar da zata tarwatsa min zuciya amma idan ba haka ba me zanyi da Khalid bayan manyan mazan dake sona a waje. Sai da na daidaici cewa ta idar da sallahr na shiga dakin, tana zaune kan dadduma cikin hijabi da carbi a hannunta tana ja, ka'ida ne dama idan ta idar da sallar la'asar sai tayi zaman lazimi nace" Zan dauki kudin 'kwan a Pose d'inki." Kanta kawai ta d'aga min na bude sif din na dauko pose din nata na zuge! gudar dari biyar na dauka na mayar da sif din na rufe...... fita nayi domin na samu yaron aike cikin ikon Allah na hango almajirin gidan Alhaji Nura ni'ki-ni'ki da kayan miya a hannunsa, da sauri nace"Sule dan Allah siyo min 'kwai kantin Dauda." da sauri yace."To aunty Sa'ida." kudin ya kar'ba ya tafi na juya da sauri na koma cikin gidan, Ummatu na samu ta fito daga gurinta tana d'auraye kwanuka. sannu nayi mata ta amsa ciki-ciki. wucewa nayi ciki ina girgiza kaina na rasa abinda na tsarewa Matar kwata-kwata bata kaunata duk abinda takeyi min a gidan na ganin ido ne. Har yanzu Lazimin take sai kawai na shiga kwashe kayan wanke-wanken dake dakin na kaisu bakin rijiya na ajiye, Wani irin kallo naga tana bina dashi kafin ta shiga bin kayan wanke-wanken da kallo tace"Sa'ida dan wulakanta abinci shine kika fito da abinci kika zuba masa ruwa idan bakwaci ai sai ku bawa almajirai shima wanda yake kawowa yana shan wahala kafin ya samo ya kawo amma na lura daka ke har Gwaggon bakwa tausaya masa." Jikina a sanyaye nace"Wallahi na manta ban duba ba na zuba ruwa akai kin san ni bana cin d'anwake shiyasa to ban san abinda ya hana Gwaggo cin nata ba." Da sauri tace"To yaya kuwa za'ayi taci bayan taga kina feraye doya ai ba zataci ba ni banta'ba ganin kwad'ayayyiyar mata irin wannan ba." Kallonta nayi ina mamakin maganarta tsaki taja ta cigaba da aikinta, Gwaggo ta bankad'a labulen d'akinta ta fito tana fad'in" Surutan me nakeji ne nifa bana san husuma a gida." Ummatu aikinta ta cigaba dayi bata tanka mata ba nace."Gwaggo babu wata husuma da zata faru ki koma d'aki. Tace."Ummatu naji kamar kina maganar d'anwake ko."? Tace."Eh hakane Gwaggo Sa'ida ta fito dashi naga ko d'aya baku ci ba shine nake mamakin hakan ai da kun san ba zakuci ba sai kuyi min magana na rage garin." Tace."Au!! Sai na fada miki ? Rabi tuntuni fa kin san ni D'anwake bai dame ni ba me zai sanya ki dimanci yi mana shi a gida." Da sauri tace."To gwaggo shi aka bani akace na sarrafa shi Maigidan daya kawo shi zakiyi wa wannan maganar." Gwaggo bakinta ta ri'ke tana jijjiga kanta Ganin al'amarin na nema ya girmama yasa na shiga basu hakuri....Ummatu kwanukan ta ta dauka ta shige gurinta, Gwaggo ta zungura mata bakinta tanai mata yen-yen! da hannu. Dariya ce ta kusa ta su'bce min ta ri'ke hannuna 'kasa-'kasa tace"Rabu da ita Sa'ida 'bakin ciki takeyi ganin kin yanka doya zaki soya tunda ta fito da hassadarta a fili ko d'and'ane kada ki bata mu cinye kayanmu." Tsabar dariyar dake cina ta hanani bude baki nai mata magana da sauri na tsuguna domin wanke kwanukan. ta cigaba da magana 'kasa-'kasa! nace "Dan girman Allah gwaggo ki tafi ki zauna a daki kada taji wata magana ranta ya 'baci matar nan iya 'kokari tanayi dake duk wata rashin kunya da takeyi miki kece kike janyowa kanki." Tsaki! taja tace"Kinga na bar maganar yanzu ina canji na na 'kwai ina lazimi naga kin dauki dari biyar." Ina kokarin bata amsa Sule ya shigo! sai ta hau washe bakinta tana kallon ledojin hannunsa dan ta dauka Alhaji Nura ne yayo aiken daya saba.......Yace."Aunty Sa'ida gashi." Kar'ba nayi nace."Nagode Sule." ya juya ya fita daga gidan bayan ya gaisheta...ta kalleni da fadin" Ganin ledoji a hannunsa Wallahi na dauka aike ne Alhaji yayo mana." shuru nai mata na cigaba da wanke-wanke na sai ta bar gurin tana surutai irin wanda ta saba. Ina daf da kammala soya doyar ya shigo gidan jikinsa bud'u-bud'u! d'auke kaina nayi ciki-ciki na amsa sallamarsa, bece min komai ba ya nufi bakin rijiya ya cika bokiti da ruwa yana wanke jikinsa, kamar wacce akace d'ago kanki ki kalleshi naga jikinsa jagab! yana kokarin cire rigar jessi d'in jikinsa cikin gaggawa na kauda kaina daga kansa gabana ya dinga faduwa ganin yanda gajeran wandon jikinsa ya ji'ke jagab dik ya manne masa a jiki girmansa ya fito sosai...... zama yayi bakin rijiyar ya cigaba da wanke jikinsa sam babu wata damuwa a tare dashi. Har ya gama abinda yake a gurin ban sake kallonsa ba ta gefan idona naga tashinsa daga gurin, ajiyar zuciya na sauke cikin zuciyata nace"Khalid Allah ya shiryar da kai hanya mai kyau. Bayan na gama sai na d'ora ruwan wanka na d'auki fulas din doyar na nufi daki dashi ,karo muka buga da ita tace."Yawwa gwanda da da kikayi kika gama magariba tayi nima yanzu alwala zan d'aura." Ajiyar zuciya kawai na sauke na bata hanya ta wuce na shiga dakin fulas din hannuna na ajiye na fito domin nima na daura alwalar. Sai da nayi wanka tukkuna na samu sukunin zama naci soyayyar doyar. lokacin ita Gwaggo har taci ta koshi ta kishingida tana saurarar redio, zaune ta mike tana gyara daurin dankwalinta tace"Sa'ida badan hali Rabi ba kisa mata biyu a plate a miqa mata ta mayar da yawu." Nace."Aiko baki fad'a ba dama sai an bata hakkinta." komawa tayi ta kwanta tana sake gyara ma daidaicin fulas din dake gabanta. Nace"Wannan fulas din na gabanki meye a ciki."? Tace."Doya ce na ajiyewa Khalid saboda nasan yana san doya da kwai shima." Karamin tsaki naja nace"A maimakon ki ajiyewa Kawu sai ki ajiyewa wani Khalid Baba Iro shi yafi cancanta ki ajiyewa doya ba wannan yaron ba." Tana gyara redion ta tace."Khalid nayi niyyar ajiyewa doya saboda haka sai ki shafa min lafiya." Ta'be bakina nayi a nutse na fara cin doyar dake gabana ina had'awa da lemo. Labulan d'akin ya d'aga yana magana, tayi saurin mi'kewa zaune da fad'in "Yawwa yaro nagari shigo kaci doya da kwai da zafin ta." Baiyi niyyar shiga dakin ba amma ganin mutuniyarsa cikin 'karamar shart irin ta shan iska yasa ya shiga dakin ya zauna suna fuskantar juna....fulas din ta tura gabanshi da fadin" Gashinan da zafin ta dan bata jima da gama soyawa ba." Girgiza kansa yayi yace."Bana bukata." da sauri na kalleshi ina mamaki! nasan halinsa da kwadayi dole shima zaiyi sha'awar doyar amma kai tsaye yace baya so." Gwaggo jikinta ne yayi sanyi tace"Saboda me ba zaka ci ba." Babu walwala a tare dashi yace."Gwaggo daga ranar dana cigaba da cin abincin Aunty Sa'ida zata cigaba da raina ni daga yanzu mutukar abu nata ne a gidan nan to kada ki ajiye min idan ina bukata zan siyo da kudina." Tace."Aa wannan ai doyar ce kawai tata amma 'kwai ni na siya da kudina dan Allah ka daure kaci." Girgixa kansa yayi yana duba wayarsa. Yace."Gwaggo bafa zanci ba wallahi koda zan kwana da yunwa kuwa." Ba tare dana kalleshi ba nace"Kanka ka cuta yaro." Uffan bece min ba ya cigaba da dube-dube a wayarsa. Nace"Gwaggo ai sai ki ajiyewa Kawu dama shi yafi cancanta da ki kyautatawa ganin irin dawainiyar da yake." cikin jin haushi tace."Ke! banyi niyyar bashi ba haba jama'a kin dameni da wani Kawu to bazan bashi ba ga wanda nayi niyyar bawa tunda yace baya bukata gobe da safe naci kayata." Shuru nai mata na cigaba da abinda nake, dakin yayi shuru na tsayin minti uku, kaina na d'ago kawai muka had'a ido dashi gabad'aya hankalinsa na kaina ya zuba min shegun idanunsa na fitina. Nace."Naci maka bashi ne da zaka sani a gaba kana kallona." shuru yayi bai ce komai ba kuma bai daina kallona ba. Girgiza kaina nayi na mi'ke na fita daga dakin na barsu. Kan tabarma na zauna ina duba waya ta ya fito daga dakin yana sanya takalmansa na kauda kaina....."Aunty Sa'ida." naji ya kira sunana cikin sanyi murya. a nutse na kalleshi, ya lumshe idonsa tare da shafa sumarsa yace."Wallahi kin had'u auntyna duk inda ake neman cikakkiyar mace kin kai duk sanda nazo gida hutu da tsananin sha'awarki nake komawa skull." Gabad'aya ji nayi yawun bakina ya bushe! na dinga kallonsa ina mamakin tsagerancin sa Murmushi yayi ya had'e yatsun hannunsa yayi heart 💘 Ilov u auntyna muuuuhhhh!." ya hura min iskar bakinsa. kafin nayi aune har ya fice daga gidan, kaina na sunkuyar 'kasa gabana ya dinga bugawa sosai al'amarin ya firgitani anya kuwa yaron nan bai fara shaye-shaye ba! ? ni kam ina zan kai kaina da wannan abin kunyar dole sai na tasar masa a tsaye zai daina yi min wannan iskancin, jikina a mutukar mace na mike na shiga dakin na kwanta ina tunanin matakin da zan dauka a kansa.. *Masoya ayi min sharing a groups👏🏼* *IDAN KINA BUKATAR KARANTA LITTAFIN GA YANDA ABIN YAKE.....VIP GRUOP#600 NORMAL GRUOP#300 ACCOUNT... 0542382124...BINTA UMAR GTBANK....IDAN KATI ZAKI TURO #400 NE SAI KIYI MIN MAGANA TA WHATSAPP DA WANNAN NUMBER* *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* [3/6, 8:45 AM] 💜: *GA IRINTA NAN!!!🙆🏼‍♀️* _(LOVE STORY🌺)_ *NA* _BINTU UMAR ABBALE🍒_ *MANAZARTA WRITES ASSO🖊️📚* *4* Sa'ida cewa nayi fa ki sawa Rabi doyar nan kada mu wayi gari ta dinga yar mana da habaici kin san dai halinta bata da hakuri." Gwaggo ce ke wannan maganar a lokacin da take kokarin shigowa dakin da buta a hannunta da alama bandaki taje. Zaune na mi'ke ba tare da nace mata komai ba na fara kokarin bud'e fulas din dake kan tabarmar ta. ido ta tsira min a lokacin da nake zuba doyar tace." Bafa cewa nayi ki kwashe mata ba guda biyu kika sa mata ta isa tunda itama idan tayi soye-soyen ta ba bamu take ba." Nace."Gwaggo dan Allah abin duniya ya daina rufe miki ido mecece doya da 'kwai tun d'azu duk kin damu kanki." "Sa'ida kada ki fad'a min magana akan Rabi na lura kema asirin nata ya fara tasiri a kanki ai sai kije ki 'karata ke da ita." shuru kawai nayi mata na fita daga dakin. Ummatu na zaune a gurinta tana saurarar redio na shiga da sallama a bakina, kallon mamaki ta shiga bina dashi, nace."Ummatu doya ce na kawo miki." Babu yabo babu fallasa tace"To nagode." Kar'ba tayi ta ajiye kusa da ita nace"To sai da safe." kamar bata so tace."Allah ya tashe mu lafiya." Koda na koma dakin gwaggo samunta nayi har ta kwanta bacci kan gadonta redion ta a kusa da kanta tana saurara Gwaggo bata kashe redio kullum a kunne take kwana shiyasa kullum cikin siyan batir take da daddare idan ta isheni da shuuuuu! zan tashi na kashe amma idan ta farka sai ta kunna alhalin ko wace tasha sun rufe, al'amarin Gwaggo nada wuyar sha'ani. Da wuri na tashi nayi duk abinda na saba karfe bakwai da rabi na shirya tsaf a gurguje na karya kummalo nayi mata sallama domin tafiya gurin aiki.....Shuru tayi min ba tace komai ba nace."Gwaggo kina ji ina magana ko."? kallona tayi da fadin."Me kika ce."? cike da mamaki nake kallonta nasan sarai taji abinda na fada amma wai tambayata take, ajiyar zuciya na sauke nace."Na tafi sai na dawo." a maimakon tayi min irin adduar data saba sai kawai naji tace."Umm!! juyowa nai ina kallonta nace"Gwaggo ba zakiyi min addua ba."' "Sa'ida kyaleni dan Allah kije kawai ni da wannan aikin naki gwara babu kullum kina yawo a kan titi zagade-zagade babu mijin aure duk wannan kyawun naki da kyawun surar zai tashi a banza a wofi wannan al'amari yana damuna." Jim! nayi ina kallonta kafin nace."Gwaggo Al'amarina ya daina damunki komai da kika gani yana da lokaci ki cigaba dayi min addua." "Umm."! ta sake fada tana ta'be bakinta, kaina na girgiza kawai na kama hanyar fita daga dakin, karo mukaci dashi a lokacin da yake 'kokarin shiga, yana sanye da singlet fara kal da 3qutar fuskarsa ta nuna alamun bai jima da tashi a bacci ba. Cikin kulawa yace." Aunty Sa'ida ki bari yanzu zamu fita cikin a daidaita sahun Salim sai mu kai ki makarantar taku." Ba tare dana kalleshi ba nace."Bana bukata." da sauri na ratse shi na wuce! Ina jin sautin muryar Gwaggo tana surutai wanda suke nuni da jin haushin abinda nai masa. Sai da nayi dana sani akan k'in kar'bar tayin da Khalid yayi min domin nafi karfin minti goma sha biyar a tsaye a bakin titi wani abun hawa na haya bai gilma ta gabana ba motocin gida ne kawai suke wuce wa, dama wani sa'in ina fama da irin wannan matsalar ta rashin abin hawa, wani lokacin kuma ina fitowa titi nake samu yau dai al'amarin sai addua dan tamkar anyi musu gori ko kuma wa'inda suka tafi yajin aiki, agogon dake daure a hannuna na duba takwas saura minti biyar gashi karfe takwas da minti goma nake da Period ajiyar zuciya na sauke ganin adaidaita sahun nasu na kokarin fitowa daga layin duk abuna dole nayi hakuri na shiga mutukar baso nake na makara ba, Motar Alhaji Nura na sake hangowa tana bin bayan babur d'in nasu, saurin dauke kaina nayi ina kallon hanya tabbas nasan sai ya tsaya yayi min magana gashi gabad'aya ban yanke hukunci akan maganarsa ba gabad'aya ma na manta munyi magana dashi jiya. Aikuwa gabana yayi parking ya sauke gilashin motar fuskarsa dauke da k'ayataccen murmushi yace."Ranki ya dad'i an fito kenan."? sakin fuskata nayi nace"Eh wallahi Alhaji barka da asuba ya kwanan iyali." ? cikin kulawa yace."Lafiya kalau sun tafi skull yanzu me zai hana ki shigo na rage miki hanya." Yafada yana kallon kwayar idona, ina kokarin magana adaidaita sahun nasu ta tsaya kusa dani. da sauri nayi 'yar dariya da fad'in"To nagode Alhaji dama na jima a tsaye babu abun hawa." cike da jin dadin kar'bar tayinsa yasa hannu ya bude mota kofar had'e da fad'in ''bisimillah." ba tare da na tsaya na saurari maganar da Khalid yake min ba na shiga motar da murmushi na mussaman a fuskata duk dan na cuzgunawa zuciyar yaron......Motar ya kunna muka bar gurin ko da wasa banyi kuskuran kallonsa ba so nake na 'kuntata masa dan saboda nasan ya tsani ya gan ni tare da mutumin bayan haka kuma inaso na nuna masa bakin rijiya ba gurin wasan makaho bane ni ba matar 'kananun yara bace. Khalid iskar dake gurin ya kaiwa naushi! rai a 'bace ya shiga kai kawo a gurin zuciyarsa kamar zata tsaga kirjinsa ta fito saboda tsananin kishi! Salim yace."Khalid dan Allah shigo mu tafi ka rabu da ita." Yana huci! ya shiga motar, Salim ya mika masa pure water da fadin"Kar'bi kasa zuciyarsa tai sanyi kar'ba yayi kamar gaske sai kawai yayi wurgi dashi kan titi lips d'insa ya ciza da fad'in "Allah Salim wannan Alhajin idan baiyi wasa ba sai nayi masa rashin mutunci babu ruwana da wani kud'insa da shekarunsa wallahi mutukar bai fita daga harkarta ba sai na bashi mamaki."! Salim girgiza kansa yayi yace." Khalid idan da zan baka shawara ka d'auka sai nace maka ka rabu da Aunty Sa'ida saboda nasan kai kanka kasan ba tsaranka bace aunty Sa'ida matar manya ce ganin idonka babu wani gajarabul d'in mutum da yake tunkararta duk masu nemanta manyan mutane ne kana dai kallo da idonka duk kudi da muqami irin na Alhaji Nura idan ya ganta rawar jiki yake mata." Zazzafar ajiyar zuciya ya sauke yana kallon abokin nasa yace."Salim duk abinda ka fad'a akan auntyna gaskiya ne wallahi ni kaina ina mamakin tsaurin idona a kanta Salim na rasa yanda zanyi wallahi aunty Sa'ida ta shiga zuciyata tayi kakagida! a cikinta, Salim bari na fad'a maka wani sirrina da ba kowane yasan dashi ba, tun inada shekara goma sha takwas a duniya na fara mafarki da ita haka zan wayi gari jikina a 'bace! to tun daga sannan na gane cewa na balaga na zama cikakken namiji wallahi Salim babu ranar da zan kwanta bacci banyi mafarkinta ba kuma kai idan kaga irin rayuwar da muke da ita a mafarkin sai kayi mamaki wallahi sosai nake sex da ita ina jiyar da ita dadi tana jiyar dani! na rasa yanda zanyi da wannan masifar Salim ko a skull haka nake fama da wannan jarabar dan dai kawai adduar iyaye na tasiri a kaina amma da badan haka ba da tuni na nemi hanyar da zan biyawa kaina bukata.'' Girgiza kai Salim yayi yace."Gaskiya Abokina na tausaya maka domin ni tuntuni na gane son maso wani kake yi domin jikina na bani aunty Sa'ida bata sonka duba da irin halin ko'in kulan da take nuna maka me zai hana kayi ya'ki da zuciyarka akan abinda kasan ba zaka samu ba." Ranshi a 'bace! yace."Salim idan kaga na daina bibiyar Aunty Sa'ida to aure tayi kai wallahi ko aure tayi ba zan hakura da ita ba saboda bata da wani miji sai ni wannan dalilin ne ma yasa na samu gwaggo na fad'a mata maganar ina ganin ko kowa ya'ki amincewa ita zata goya min baya." Salim yace." Khalid ina jiye maka wahala wallahi na fada maka Aunty Sa'ida tafi karfinka ka hakura kawai." a fusace! yace." Salim wai wannan wace irin magana ce kake? a'ina ka ta'ba ganin mace tafi 'karfin namiji! Auntyna nada 28year ni ina da 23year sai ka fad'a min ina tazarar take kai ni a yanda nake jin jarumta idan an had'a min iri-irin ta goma zan iya dasu ballantana ita da tun a mafarkina na gama da ita na fad'a maka a mafarkina fa tuntuni na gama mata aiki." Salim ya fashe da dariya yana dukan sitiyari yace."Kai Khalid wallahi baka da mutunci wato dai yanzu kana nufin fanko kake kallonta." Murmushi yayi ya d'an sosa tarin sumarsa yace."Aa mafarki daban Zahiri daban yanda nake sarrafa ta a mafarkina to inaso na sarrafata a zahiri wallahi sai na 'kure duk wata fitinar ta." Salim ya dinga dariya yana fad'in Khalid baka da dama wallahi Allah ya baka aunty Sa'ida ka more 'kuruciyarka dan wallahi nima ina son mace mai kyau da tsarin jiki irin nata kullum kamar 'kara mata 'kuruciya ake." Murmushi yayi yace."Nagode da addua abokina." Wasu mata ne suka tsayar dasu, Salim yace."Hajiya ina zakuje."? "Gidan Murtala." matar ta fada tana kallonsa, yace."To ku shigo muje." da sauri suka shiga, shi kuma yaja babur din suka bar gurin. **** Cikin murya mai taushi yace."Ranki ya dad'e har yanzu banji daga gareki ba inaso ki sha'ku da iyalina kafin Allah ya kawo ki cikinsu shine babban dalilin da yasa nace kina shiga gidan a cikin ranaku biyu kinayi musu lesson itama matar gidan tuntuni nayi mata bayani kuma ta amince da manufata.'' Alhaji Nura ne ke wannan maganar a yayin da suke tafiya a motarsa. Ajiyar zuciya na sauke na d'an kalleshi da gefan ido mamaki sosai nake da maganarsa yana sona da aure amma kuma yana kawo wata gurguwar magana mara ma'ana Ta yaya zan dinga shiga gidansa da sunan yiwa yara lesson bayan da maganar aure a tsakaninmu hakan sam bai dace ba, ita kanta matar gidan da ta amince da hakan nayi mamaki amma dai nafi zargin gatse tayi masa tunda mafi akasari maza basu sanshi ba. A nutse nace"Alhaji ni ina ganin ba lallai sai na shiga gidanka nayi wa yara lesson zamu sha'ku dasu ba, hakan kamar bai dace ba tunda har magana aure ta shiga tsakanina da kai a yanzu sai mu bari muga abinda Allah zaiyi idan har Allah ya kaddara aure a tsakanina da kai yara basu da matsala insha Allah zan tsaya na kula da harkar karatunsu amma maganar na dinga zuwa nai musu lesson ka ajiyeta." D'an murmushi yayi yace."Sa'ida kenan ai da amincewar matar gidan nake miki wannan maganar ina ganin hakan duk ba wani abu bane tunda duk an riga an zama d'aya.'' "Alhaji kenan na yarda da amincewar matarka amma ni a ganina hakan ba kamata ba dan Allah kayi hakuri da wannan maganar domin ina ganin hakan shi yafi alkairi." Yace."To shikkenan tunda kince haka yanzu a'ina maganarmu ta kwana? inaso wannan karon ki bani dama na turo da magabata na akan maganar auranki." Jim! nayi ina nazarin maganarsa "Insha Allahu zan kira wayarka idan na koma gida." Cike da farin ciki yace."To masha Allah Nagode 'kwarai Sa'ida sai na jiki.'' Murmushi kawai nayi ban sake magaba ina dai jinshi yana ta bani labarin yaransa sai da dariya yake gaskiya yanda na fuskance shi yana da son yara sosai........cikin wannan halin ya sauke ni bakin gate din makarantar da nake koyarwa a nutse nace"Alhaji nagode kwarai." kokarin bud'e mota nake yace."Idan kun tashi ina iya turo direba ya dauke ki." Da sauri nace"Aa Alhaji bani da matsalar abin hawa idan zan koma gida domin 'kawata Hauwwa tana da mota tana rage min hanya." Yace."To shikkenan ranki ya dade a fito lafiya." Nace."Insha Allah nagode." motar na bude na fita da sauri na daga masa hannu hade da fad'in "A sauka lafiya." cikin sauri na nufi cikin makaranta kafin na shiga sai da muka gaisa da masu gadi cikin mutunci sannan da sauri na shige ciki....... *Masoya ayi min sharing a groups👏🏼🥰* *IDAN KINA BUKATAR BIYAN KUDIN LITTAFIN GA YANDA ABIN YAKE......VIP GRUOP#600 NORMAL GRUOP#300 ACCOUNT.. 0542382124...BINTA UMAR GTBANK.....IDAN KATI ZAKI TURO #400 NE SAI KIYI MIN MAGANA TA WHATSAPP DA WANNAN NUMBER* *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* [3/6, 8:46 AM] 💜: *GA IRINTA NAN!!!🙆🏼‍♀️* _(LOVE STORY🌺)_ *NA* _BINTU UMAR ABBALE🍒_ *MANAZARTA WRITES ASSO🖊️📚* *_Ya Allah kayi mana katangar 'karfe tsakaninmu da ma'kiya! Ya Allah ma'kiyi wanda na sani da wanda ban sani ba Allah ka katange ni dashi👏🏼 Ubangiji Allah ka tsare gabanmu da bayanmu Allah dukkanin mai nufin mu da sharri ko wane iri ne Allah ka mayar masa kansa, Allah a gida da waje ka kare mu damu da zuriarmu Ameen ya hayyu ya 'kayyumu👏🏼_* *6* "A'a Sa'ida bana san sharri! A ina kuka had'u da Khalid d'in da har zakiyi masa wannan gundumeman sharrin yaron da tun d'azu ya fita dan babu yanda banyi dashi ba ma ya zauna yaci abinci yace baya ci sannan kawai kizo kice yana k'okarin lalata dake a soro." Ina 'kokarin magana Ummatu ta bankad'a labule ta shigo dakin da fad'in"Wace magana naji kunayi kuna kuma kiran sunan Khalid." Gwaggo tace."Ke! Rabi abinda ba'a sa da kai ba dad'in kallo gareshi a'ina kikaji mun kira sunan Khalid da har zaki bankad'a labule kishigo a fusace." Murmushi tayi tace."Gwaggo kenan duk fa maganar da kuke a kunne na ke Sa'ida ki shiga hankalinki dani wallahi wato Khalid din zakiyi wa sharri sabida baki da kirki to tun wuri kije ki nemi d'an iskan da yake lalubeki a soro amma ba Khalid ba." Ido na zuba mata har ta 'kare maganarta ban tanka mata ba, Gwaggo tace."To tunda dai kin fad'i abinda ya kawo ki tafi kuma wallahi kada naji maganar nan a bakin kowa mutukar maganar nan ta fita dukkaninku sai ranku ya 'baci."! Ummatu ta'be bakinta tayi ba tare da tace uffan ba ta kad'a kanta ta fita daga d'akin. Duk yanda naso na daure kasawa nayi hawaye na zuba nace."Gwaggo wato nice 'yar iska lalatacciya ko? dukkaninku baku yarda Khalid zai iya aikata abinda na fad'a ba kun goya masa baya ya cigaba da bibiyata ko okey to shikkenan Gwaggo yanzu na gane matsayina a gurinki dan gashinan a zahiri kin nuna min cewa kinfi kaunar Khalid a kaina alhalin duk kece kika haifi iyayenmu to babu komai Gwaggo kinji na rantse da Allah duk ranar da Khalid yayi kuskuran sake ri'ke min hannu sai na d'auki tsatstsauran mataki a kansa.''Cikin zafin zuciya nake maganar. Tace."To me zakiyi masa idan ya ri'ke miki hannu naga dai shine zai aureki to meye abin tayar da hankali kuma." Da sauri nace."Dake dashi zan kai ku gurin alkali sai kiyi masa bayanin da kikayi min yanzu." Ha'barta ta ri'ke tana girgiza kanta tace."Lallai Sa'ida ni zaki kai gurin alkali."? "Kwarai kuwa mutukar baki daina daurewa Khalid gindi ba wallahi sai na dauki wannan matakin." shuru tayi tana kallona, nasan mamakina take, dan na 'kara tsoratata nace" Yanzu ma bari na kira wani abokin aikina wanda d'an uwansa yake aiki a kotun musulunci ta kasuwa na fad'a masa dukkanin abinda yake faruwa." Da sauri ta rike hannuna tana kokarin kar'be wayar tace."Sa'ida ashe baki da hankali kina so ki tona mana asirin gida." Nace." Wane irin zan tona asiri ai gaskiya ce idan munje gaban alkali sai kuyi bayani dake dashi wanda kike daurewa gindin." Hannunta na rawa tace"Yi hakuri dan Allah abar kaza cikin gashinta domin hakan yafi mutunci zan samu Khalid din naja masa kunne ya daina ta'baki tunda dai ba'a d'aura aure ba." Nace."Shin yanzu kin yarda da maganata akan Khalid din ko kuwa baki yarda ba."? Da sauri tace."Haba na yarda mana dama sabida kada maganar tayi tsayi ne yasa kikaji nace ban yarda ba amma nasan Khalid zai aikata kuma zanja masa kunne kiyi hakuri kinji ko." Ajiyar zuciya na sauke nace"To wannan karon dai na hakura idan ya 'kara kwatantawa to zaiga abinda zai biyo baya." Tace."Bama zai 'kara ba insha Allahu.'' Mi'kewa nayi na fita daga dakin ina jin tana fad'in"Kizo ka abincin naki ai tuntuni na shigo miki dashi daki." Nace."Wanka zanyi tukkuna." Da sauri tace."To shikkenan sai kin fito." Bakin rijiya na nufa na cika bokiti da ruwa na dauka na kai bandakin, dakin na koma domin cire kayan jikina. Bayan sallahr isha'i kasancewar ana zafi a gari gashi babu wuta sai mukayi shimfid'a a tsakar gida muna hira, Ya shigo gidan cikin rashin 'kwarin jiki ya zauna kusa da ita da fad'in "Wash Allah Gwaggo na gaji wallahi nayi mutukar galabaita." Zaune ta mi'ke tana gyara daurin dankwalinta tace."Yaron kirki ina kaje ne kuma me kayi ka gaji kana yawo cikin ka babu komai ina fata dai ka samu wani abu kaci."? Ajiyar zuciya ya sauke 'kasa-'kasa ya d'an kalli mutuniyar tasa kafin yace." Wallahi Gwaggo har yanzu banci abinci ba Yau Salim ne ya jani yawo cikin adaidaita sahunsa." Tace."Allah sarki to ina fata ka samo d'an kwabo da d'ari.'' Goshinsa ya murza yace." Na samu me kike bukata."? Baki ta washe tace."Ina bukatar Gashashshiyar kazar Malo mai nama." Dariya yasa yana kallonta yace."Gwaggo kina san dad'i a rayuwarki duba dan Allah kin iya fad'ar Malo mai nama." itama dariya tasa harda tafa hannu tace."To yaron kirki waye baya san dad'i ai mutukar ban takura maka ba to ka siyo min kazar malo mai nama." Khalid ya dinga dariya yana kallonta. Takaicin abinda suke ya isheni sai kawai na dauki wayata ina dubawa, naji yace."Gwaggo ko kudin kenan yau sai kinci kazar Malo." Yun'kurawa yayi ya mi'ke tsaye yana kokarin sa takalmansa yace."Auntyna ke me kike so."? Banza nai masa, Tace."Sa'ida kina ji ya nayi miki magana ko babu dai kyau gaba." Ba tare dana kallesu ba nace."Bana bukatar komai." Tayi sauri tace."Kaji wai bata bukata." Yace."Okey to babu damuwa ai " hanyar fita ya nufa tace"To ina jira dan Allah kada ka fita abokai su ri'ke ka har nayi bacci." Yace."Yanzu zan dawo nima yunwa nakeji ai." tace."To kafin ka dawo bari na fito maka da abincinka." Ba tare da yace wani abuba ya fita daga gidan Mi'kewa tayi ta shiga daki ta dauko masa fulas din abincinsa kana ta dauko kofin silba ta ciko masa da ruwan randarta tazo ta ajiye a kusa da ita. Kallonta nayi rai a 'bace nace"Gwaggo keda zaki sanja masa fuska saboda laifin da yayi shine harda dauko masa abinci ko da yake ai nasan kin manta tunda kinga ya samo kudin siya miki kaza idonki ya rufe to har yanzu ina nan akan bakana." "Aa Sa'ida ban manta ba ina sane inaso yaci abinci ya huta sai nai masa maganar." "Umm! nace naja bakina nai shuru! jin maganarsa shida abokansa a soro yasa na mi'ke na shiga daki, yana shigowa kai tsaye 'kofar Ummatu ya nufa da fad'in " Gwaggo ina zuwa." Da sauri tace."Aa zo ka bani leda ta kafin ka shiga bana so ta za'be abinda ka shigo dashi.''! Dariya nasa ina mamakin 'karfin halin Gwaggo mata ta haifi d'anta amma ta fita iko dashi.....Dawowa yayi da baya ya mi'ka mata leda guda tace."To yawwa yanzu naji magana ka fito ga abincin naka." Yana 'yar dariya yace."To Gwaggo." Gurin mahaifiyar tasa ya nufa domin itama ya bata tata ledar. kwance a d'an tsakar gidanta ya sameta da Mafici a hannu tana firfita shigowarsa yasa ta mike zauna tana kallon ladar hannunsa.....Zama yayi gefan tabarmar da take zaune yace."Ummatu me zai sanya ki takura kanki bakya fita babban tsakar gida kisha iska sosai." Girgixa kanta tayi tace."Khalid 'kyaleni anan yafi min kwanciyar hankali akan na fita Gwaggo ta fad'a min ba'kar magana." Yace."Ummatu idan da sabo yaci ace ki saba da halin Gwaggo wata irin macace mai wani irin hali bayan haka kuma akwai rikicin tsufa a tare da ita." Girgiza kanta tayi tace."Khalid dama ai kai baka ganin laifin Gwaggo duk abinda tayi daidai ne a gurinka." Girgiza kansa yayi yace."Ba haka bane wallahi Ummatu yanzu a matsayin na shekarun Gwaggo dole ayi mata uziri shiyasa kikaga duk abinda tayi nake biye mata saboda samun nutsuwarta ba wai bana san laifinta bane." Tsaki taja tace."Duk da da akwai tsufa to da akwai iskanci wannan tsohuwar guda ce Khalid ni kad'ai nasan irin takaicin da take kuntuka min a gidan nan." Yace."To kiyi hakuri dan Allah komai mai wuce wa ne gashi kema na siyo miki nama." Kar'ba tayi tana duba ledar tace."Sai da ka kai musu suka za'ba tukkuna ni aka kawo min saura ko." Girgiza kansa yayi yace."Aa Ummatu duk d'aya ne wallahi dake da Gwaggon." Tace."Ai kamata yayi ka daina daidaita ni da ita tunda ni na haifeka idan kana neman albarka sai kayi min biyayya." Yace."Ummatu dan Allah ki daina irin wannan maganar wallahi dake da Gwaggo duk daya kuke a gurina ke kika haifeni dole kina da martaba ta mussaman a gurina Gwaggo kuma itace ta raine ni har na girma Gwaggo bata san 'bacin raina komai ta samu nawa ne abinci wannan Gwaggo bata ci sai tare dani sai dana na tafi makaranta tukkuna muka raba kwano da ita Gwaggo takan iya hana cikinta abu ta ajiye min Ummatu kada ki manta Gwaggo itace tayi rabin dawainiyar Karatuna idan tayi sana'arta haka zata tattara kudin ta bani nayi hidimar makaranta dasu duk lokacin da nazo hutu sai ta bani kudi wata bukatar zata taso Gwaggo tayi Baba yayi a haka fa akayi ta tafiya har Allah ya kawo ni wannan lokacin da nake daf da kammala makaranta kinga kuwa dole na kyautata mata domin ta taka muhimiyyar rawa a rayuwata." "Khalid wato ka sani a gaba kanayi min gori ko? to ko banyi maka hidima ba ai ba zaka iya biyana irin dawainiyar cikin ka da haihuwar ka ba, saboda haka kada ka sake sani a gabana kana kawo min wata banzar magana." Shuru yayi yana jinta sai fad'a take masa yace."To Ummatu kiyi hakuri dan Allah insha Allahu ba zan kara ba." Shuru tayi masa ta mike ta nufi kicin plate ta dauko tazo ta zauna tana kokarin sa naman a ciki.....mikewa yayi ya fita daga gurin, nan ya samu Gwaggo a kashingid'e har taci ta gyatse tana gyangyad'i! zamansa a kusa da ita yasa da sauri ta tashi zaune tana fad."Khalid ka fito." "Umm." kawai yace ya zauna ya dafe kansa, cikin kulawa tace."Menene yake damunka."? Shuru yayi yana girgiza kansa, 'kasa-'kasa tace."Kada ka damu da barazanar Sa'ida akan abinda kayi mata d'azu nan ta titsiye ni tanayi min jaraba wai sai ta kaimu kotu ni dakai." Cike da mamaki! yace."Akan wane dalili zata kaimu kotu kuma me nayi mata da har take wannan furucin."? Da sauri tace."Yi magana a hankali Dan bana tsammanin tayi bacci." Tsaki yaja 'kasa-'kasa yace."Me tazo tace anyi mata."? Gwaggo murya a 'kasa tace."Wai cewa tayi kana tare ta a soro kana lalubeta." Yanda Gwaggo ta fadi maganar yasa dariya ta 'kwace masa yace."Ni sharri kawai tayi min abinda ma yau ban yini a gida ba." Gwaggo tace."To nima haka nagani ta shigo fuska a murtuke ta dinga jaraba dan har mahaifiyarka taso ta biye mata na shiga tsakaninsu, jin tana maganar kaimu gaban alkali yasa na bata hakuri nace zan ja maka kunne." Yace."Gwaggo da kin sani ma baki wahalar da kanki gurin bata hakuri ba ni ba d'an iska bane da zatayi min irin wannan sharrin nima zan dauki mataki a kanta dan kafin ta kaini 'kara kotu ni zan kaita tunda tayi min sharri."! Sosai ya fitittuke yake kare kansa Al'amarin ya dinga bani mamaki! dan duk maganar da suke ina jinsu raina kuma ya 'baci sosai da naji Gwaggon na rarrashinsa har tana cewa ai dama tasan Sharrin nai masa ba zai aikata ba, naji tamkar na fita naci masa mutunci sai dai kawai na taushi zuciyata na hakura na kyaleshi ina tunanin irin matakin da zan dauka a duk ranar da ya sake kuskuran ta'ba jikina.. *Masoya a taimaka da sharing a gruops👏🏼* *IDAN KINA BUKATAR KI BIYA KUDIN LITTAFIN GA YANDA ABIN YAKE.....VIP #600 NORMAL#300 ACCOUNT.... 0542382124.....BINTA UMAR GTBANK....IDAN KATI ZAKI TURO #400 NE SAI KIYI MIN MAGANA TA WHATSAPP DA WANNAN NUMBER.* *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* [3/6, 8:46 AM] 💜: *GA IRINTA NAN!!!🙆🏼‍♀️* _(LOVE STORY🌺)_ *NA* _BINTU UMAR ABBALE🍒_ *MANAZARTA WRITES ASSO🖊️📚* *DUNIYAR HAUSA NOVEL* _*Cannal ne na mussaman da zaku samu littafan hausa ko wane iri ne maza ku tafi YouTube kuyi sarcing d'in Cannal din zaku samu 'kyatattun littafai masu dadi! kada ku manta da sunan channal din *DUNIYAR HAUSA NOVELS*_ *5* "Sa'ida tun kafin mu fito daga ofis nake miki wani irin kallo sai nake ganin kamar kina da damuwa a ganina bancanci ki 'boye min abinda ke damunki ba tunda nima duk wani abu da yake damuna bana 'boye miki." Hauwwa ce kenan wannan maganar a lokacin da suke cikin motarta domin komawa gida. Ajiyar zuciya na sauke nace."Wallahi Hauwwa ba 'karya kikayi ba ina damuwa na kuma rasa yanda zanyi na warware ta al'amarin dai sai godiyar Allah. Murmushi tayi tace."Haba 'kawata abokin kuka shi ake fad'awa mutuwa ki fad'a min damuwarki ko akwai shawarar da zan iya baki." Murmushi nayi nace"Dama ina tunanin fad'a miki kikayi magana Hauwwa kin san wannan yaron na gidanmu ko.''? Tace."Khalid ko bashi kike nufi ba."? Nace."Shi nake nufi Hauwwa Khalid ya takura min a gida wallahi wai saboda tsabar rashin mutunci da raini kamar ni zai duba yace yana so." Hauwwa dariya tasa tana kallona da mamaki a tare da ita, tace."So.''? Ta'be bakina nayi nace."Kwarai kuwa Hauwwa Khalid sona yake dan duk wasu alamu ya nuna harda fad'awa Gwaggo wai zai aure ni yaron da a gabana ya girma meye nasa ban sani ba amma da yake yanzu yaga ya fini tsayi da girman jiki shine yake furta min wannan kalma.'' Hauwwa draving take tana girgiza kanta tace."Sa'ida Khalid yayi tsaurin ido amma kuma idan an duba tarihi za'a ga baiyi tsaurin ido ba tunda hakan kamar sinna ce mai zai hana ki aureshi tunda hakan ba haram bane." Wani irin kallo na watsa mata "Hauwwa wannan wace irin magana kikeyi me zan aura a tare da Khalid bana tsammanin zan iya auran 'karamin yaro a yanda nake a haka nafi bukatar cikakken namijin mai kima wanda yasan rayuwa amma auran yaro mai 'karanci shekeru akwai kalubale a ciki." Murmushi tayi tace."Sa'ida wane 'kalubale kike hangowa a tattare da auran Khalid? Yaro kyakykyawa da siffar mazantaka Khalid bai da makusa matsalar kawai kice bashi da kudi sannan kuma bashi da aikinyi in banda haka menene abin'ki a tare dashi."? Girgiza kaina nayi nace."Hauwwa Ra'ayi na ne kawai haka bana sha'awar auran k'ananun yara dan sai nake ganin kamar basu san meye aure ba wannan dalilin yasa gabadaya bana kulasu nafi tsayawa na saurari magidanta masu iyali da suka dad'e a cikin harkar." Hauwwa ta'be bakinta tayi tace"Sa'ida mazan fa suna suka tara kamar yanda matan ma suka tara duk kallon kitse kike musu ni zan fad'a miki wannan kinga dai ni bazawara ce ko to wallahi ba zan auri namiji ba sai na tsaya na duba tukkuna saboda ni kad'ai nasan bala'in dana shiga a gidan aurena kafin na fito." "Hauwwa kenan kin san kowa da tunaninsa amma gaskiya bana yi miki sha'awar auran 'karamin yaro domin kinfi 'karfinsu ki auri namiji daidai dake dan Allah kada kibi son zuciyarki daga baya kizo kina nadama." "Sa'ida kin san Allah ko d'an 20years ne yazo da niyyar aurena na gamsu da shi sai na aureshi domin hakan ai ba haramun bane akan naje na auri babba nazo na sake shiga wata matsalar gwara na auri yaron na cigaba da rainonsa har yayi 'kwari." Cikin wani irin yanayi na mamaki nake kallonta.....tasa dariya da fadin"Kina mamaki ne.''? Girgiza kaina nayi nace."Sosai kuwa idan kin auri dan 20years kin auri d'an cikin ki ko ba haka bane." Still tana dai dariyar tace."Aa Sa'ida bana san sharri a ina na haifi dan shekara ashirin Walid yarona na farko duka shekaransa tara Safna kuma shekararta bakwai." Nace"Kin gani ai tunda kika haifi dan shekara tara kin zama uwa me zai baki sha'awa a gurin auran karamin yaro dan shekara ashirin. Hauwwa baki ta ta'be tace."Ke Sa'ida bari dai na fito miki a mutum! ni Hauwwa ina da tsananin bukata wannan dalilin ne ya janyo mutuwar aurena domin babansu Walid bashi da maida hankali a wannan gurin yafi mayar da hankalinsa gurin neman kudinsa nasha wahala a hannunsa Sa'ida ina fada miki Walid da Safna tsanani rabo ne yasa aka haife su saboda babansu sai ya shafe wata biyu ko uku bai had'a shimfida dani ba, kullum yana yawo a jirgi sai kace tsunsu shi dai ya samu kud'i ni kuma ya barni cikin wahala da bukata wannan dalilin yasa na yankewa kaina shawarar yanke zama dashi dan ba zan iya da halinsa ba." Na jima ina mamakin maganarta kafin nace."To Hauwwa shi 'karamin yaron da kike 'kulafuci a kansa kina da tabbacin zaki samu abinda kike bukata mazan fa duk kusan haka suke tunda dai ba 'kwan'kwasawa zakiyi ki gane daidai dake ba ." Murmushi tayi tace."Sa'ida ana ganewa wallahi shiyasa ai nace miki kafin nayi auran sai na tantance tukkuna kuma ina rokon Allah ya bani daidai dani." Nace."Ta ina zaki gane jarumin namiji Hauwwa." murmushi tayi tace."Sa'ida kenan." draving d'inta ta cigaba dayi ta barni cikin tunani nima irinta ce mai yawan sha'awa da son soyayya shiyasa gabad'aya na shiga tunanin ta inda zan gane jarumin namijin da zai iya daukar lalurata......Alhaji Nura ne ya fad'o min a rai na dinga tunanin siffofinsa dogo ne mai ma daidaicin jiki kwayoyin idanunsa jajaye ba irin na Khalid ba da kullum suke da haske, nace"Hauwwa tunda kin'ki fad'a min ai na gane." Tace."Yawwa ai dama so nake ki gane sai kiyi min bayani." Dariya nayi nace."Kamar dai Alhajina ina nufin Alhaji Nura ya cancanta da wannan sunan. Shuru tayi tana nazari tace."Eh gaskiya kam kwayoyin idanunsa ma sheda ne ina miki sha'awar auransa gashi yana bala'in sonki to amma ai matarsa ce matsala Sa'ida a rayuwata bana san kishiya wallahi." Ajiyar zuciya na sauke nace."Hauwwa ni wallahi kishiya bata firgita ni za'bin Allah kawai nake nema idan Allah ya kaddara Alhaji Nura ne mijina babu ruwana da matarsa tunda ba itake aurena." "Hakane Sa'ida to ina rokon Ubangiji Allah ya za'ba mana abinda yafi alkairi." na amsa da ameeeen ya rabbi......Da wannan hirar ta sauke ni a bakin layin mu ta juya kan motar hannu na daga mata da fadin"Nagode 'Kawata sai gobe idan Allah ya kaimu." ta amsa da "Ameen Allah ya kaimu lafiya." sai da ta bar gurin sannan na nima na bar gurin........ Tunda na hangoshi a zaune a kofar gidan naji gabana ya fadi! hakika Khalid ya zame min 'karfen 'kafa, kici-kici nayi da fuskata, kafin na karasa naga ya mi'ke ya shiga gidan, ajiyar zuciya na sauke naji dad'in hakan saboda na tsani kallon da yake min......Ina shiga soran naji an fizgo hannuna kafin nayi aune naji ya ru'kun'kume ni ta baya! numfashinsa naji yana fita da sauri da sauri ya d'ora kansa a kafad'ata sosai ya ri'ke 'kuguna! gabana ya dinga fad'uwa! murya na rawa nace."Khalid wane irin iskanci ne wannan? zaka sake ni ko sai nai maka rashin mutumci d'an iskan yaro kaw......Kafin na 'karasa naji yayi cikin bayan k'yaure ('kofa) dani, a zabure! na juyo fuskokinmu suka had'u guri guda! Hawaye ne naji suna kokarin kufce min wane irin fitinan nan yaro ne wannan? matseni yayi a kirjinsa yana kiran sunana cikin wani irin sauti "Aunty Sa'ida kina so na mutu ko? ki taimakawa rayuwata kada ta salwance." hawayen takaicin da nake kokarin dannewa sune suka kufce cikin rawar murya nace."Khalid sake ni." "Um!um! Aunty naji dadin rungumeki ki bari na samu nutsuwa ina cikin tsananin damuwa." Yafad'a yana goga gefan fuskarsa a tawa. Shuru nai jikina gabad'aya ya mutu ko yaya nayi motsi da niyyar kwace jikina zai sake matseni sai wani irin nishi yake! "Khalid ni kake wa wannan iskancin ko? ni kake matsewa a soro saboda baka da mutunci Khalid."! murya a sha'ke nake magana. " Aunty Sa'ida har abada babu tozarci a tsakani na dake abinda kikayi min d'azu ya 'bata min rai ko abinci na kasa ci Aunty me yasa zaki za'bi wancan Alhajin ki barni me nai miki ko ni ba namiji bane." Cikin sanyin murya yake maganar yana yawo da hannunsa a jikina. "Khalid ka daina mafarkin abinda ba zai faru ba kasan Allah duk maitarka akaina sai ka hakura dan ni nafi karfin'ka kaje ka nemi daidai da kai." Fuskata ya d'ago yana kallona, naga idonsa yayi jajawur a take tsigar jikina ta tashi! fuskata na fizge! da sauri na daga hannu da niyyar kwad'a masa mari! yayi saurin ri'kewa. Girgixa kansa yake Cikin 'kunar zuciya yace."Ni nafi karfin ki mare ni auntyna! na amince ni maye! ne amma akanki aunty Sa'ida ba zan fita a rayuwarki ba sai na tabbatar da cewa kin zama mallakata mu zuba ni dake."! Tsaki naja na tureshi da fadin"Shashasha mara hankali kawai." gabana ya tare cikin 'bacin ran da banta'ba ganinsa dashi ba yace."Kada ki 'kara kirana da shashasha zan baki mamaki." "Me zakayi min."? nafada ina watsa masa harara......Murza yatsun hannunsa yayi yace." Sai ranar da kika 'kara kirana da kalmar sannan ne zakiga abinda zanyi." "Mtwwws! tsaki naja na ra'ba ta gefansa na shiga gidan.....Ajiyar zuciya ya sauke bayan shigewarta gidan ya shiga shafa kirjinsa yana lumshe ido har yanzu yana jin tudun nonowanta a kirjinsa, cikin mutuwar jiki ya fita daga gidan. " To shikkenan Uwale zan duba maganarki wallahi dama nima sai da nayi wannan tunanin ace yarinya kwata-kwata bata so ayi mata maganar aure bayan tana da mane ma dole ne a nemi taimako." Uwale na kokarin magana na shiga dakin, sai ta washe baki da fadin"Babban mace hakima kin dawo kenan sannu lallai kin dauko rana." Sama-sama na gaisheta na cire hijab din jikina na fita daga dakin na tsani alaqar Gwaggo da Uwale ko kad'an......Bayan fitarta Uwale tace."To shikkenan Gwaggo sai kinzo ina sauraranki." Gwaggo mi'kewa tayi domin yi mata rakiya tana fad'in "Insha Allahu gobe zanzo sai muje Allah dai ya rufa asiri." kallo na bisu dashi ina tunanin inda zasuje....Gwaggo ta dawo gidan tana kallona a fakaice kafin ta shiga dakin, mikewa nai nabi bayanta domin na kafa mata hujjata akan irin iskancin da Khalid keyi min... *Masoya a taimaka da sharing a gruops👏🏼🥰* *IDAN KINA SO KI BIYA KUDIN LITTAFIN GA YANDA ABIN YAKE.....VIP GRUOP...600 NORMAL 300 ACCONT...0542382124.....BINTA UMAR GTBAK IDAN KATI ZAKI TURO #400 NE SAI KIYI MIN MAGANA TA WHATSAPP DA WANNAN NUMBER* *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* [3/6, 8:46 AM] 💜: *GA IRINTA NAN!!!🙆🏼‍♀️* _(LOVE STORY🌺)_ *NA* _BINTU UMAR ABBALE🍒_ *MANAZARTA WRITES ASSO🖊️* *Pegen na yau naki ne* _*Gwanata FATIMA SUNUSI RABI'U Matashiyar marubuciya mai fasaha da amfani da basirar ta a inda ta dace Ina kaunarki Takwara kamar yanda kike 'kaunata💗😊*_ *7* Cikin nutsuwa na kalleta tana ta shiryawa nace."Wai Gwaggo ina zakije ne da sassafe haka."? Tana shafa mai a kafafunta tace."Wallahi ugunwa zamuje da Uwale amma ba zan dad'e ba zan dawo dan ina da aiki a gabana Salisu mai kanti yace nayi masa lagwani zai siya." Nace."Gwaggo wannan wace irin unguwa ce da zakuje da safe karfe bakwai da rabi kifa duba lokaci ki gani ko karyawa bakiyi ba amma kina kokarin fita." "Kinga Sa'ida kada ki takurawa rayuwata ina ruwanki da inda zani zaki dameni da surutai.'' Nace." Babu ruwana amma bari naje na fad'awa Baba Iro cewa Uwale zata jaki yawo." Da sauri nayi yun'kurin fita ta ri'ke gefan rigata da fad'in "Dawo na fada miki inda zamuje." komawa nayi na zauna ina kallonta, tace."Jikar Uwale ce take aljanu shine zamuje mu kar'bo mata magani gurin wani malami." Cike da mamaki nace."Gwaggo Uwale ta fara d'ora ki a turba mara kyau ko yanzu tsofai-tsofai daku ina ku ina zuwa gurin malami." "Sa'ida kada ki fassara mu da wata manufa bakiji abinda na fad'a ba jikar Uwale Nafisa itace take aljanu shine zan rakata ta kar'bo mata magani." Nace."Dole sai kin rakata ita bata san hanya ba."? A tausashe tace."Tasan hanya mana nima ai inso malam d'in ya taimaka min." "Me yake damunki da zakije gurin malami ya taimaka miki ba zakiyi alwala ki roki Allah ba." shuru tayi bata bani amsa ba, nace." Gwaggo ki kiyaye kada Uwale ta jaki gurin bokaye da girma da mutuncin ki me kike nema a duniya wanda ba zaki rok........."Sa'ida wai ni sa'arki ce ne da zaki zauna kina kokarin fad'a min maganar banza waye yace miki gorin bokaye zamuje."? Ganin yanda ta fusata yasa na sassauta murya "Gwaggo kiyi hakuri idan kinji shaushin maganata halin Uwale na sani na rashin tsoron Allah da san duniya." "To naji wuce kiyi tafiyarki nama fasa zuwa tunda zargin da kikeyi min kenan." Murmushi nayi na cigaba da shirye-shiryen tafiya makaranta.......Ummatu ce ta daga labulan dakin ta shigo da sallama a bakinta, dukkaninmu muka amsa mata ta ajiye jug din kunun dake hannunta tace."Gwaggo ina kwana."? Ciki ciki ta amsa tana dauke kanta kamar itace tai mata laifin.....Ummatu ta juya zata fita a nutse nace."Ummatu antashi lafiya." ? ta amsa ba tare data juyo ba....."Rabi yau kuma ina k'osan zaki zo kawai ki ajiye min ruwan kunu a gabana." Kai tsaye Ummatu tace."Nima shi aka bani na kawo miki." a fusace! tace."Magana zaki fad'a min Rabi wallahi ki shiga hankali a gidan nan idan ba hakaba zanyi maganinki .'' Tace."To Gwaggo magana kika fad'a na baki amsa daidai da maganarki Maigidan yau bashi da kud'i sai kowa yaci aljihunsa " Gwaggo tsaki taja ta dauke kanta....Ummatu rai a 'bace ta fita daga dakin. Nace."Gwaggo dan girman Allah ki dinga tauna magana kafin ki fad'a bai kamata ki dinga irin wannan zaman da surukar ki ba." Tsaki taja ta dauke kanta, nace"Na nawa 'kosan zai isheki idan na fita sai na bawa yaro ya siyo miki." "Na hamsin ma ya isheni." tafada tana bud'e jug din kunun........Hijabina nasa nace"Ni zan tafi." tace."Ba zaki tsaya kisha kunun ba."? Girgiza kaina nayi nace"Yau haka na tashi cikina a cunkushe idan naje ofis zan samu ruwan tea nasha da biscuit. " Shuru tayi tana kallona.....Nace."Kada ki damu Gwaggo." tace."To sai kin dawo." Nace."Insha Allah." Ina fita na ganshi a zaune a bakin rijiya yana brush dauke kaina nayi daga kansa nayi sauri na fita daga gidan. Gwaggo na zaune tana sa'ke-sa'ke yaro ya shigo da sallama a bakinsa Labulan dakin ta d'aga tana amsa sallamar y....Yace."Gwaggo wai gashi anty Sa'ida tace na siyo miki kosai.'' Kar'ba tayi ta bude ladar ta bashi guda biyu tace."To jeka nagode." Yaron da sauri ya juya ya fita daga gidan da 'kosan a hannunsa. Gwaggo guda d'aya ta dauka tasa a bakinta ta 'kulle ledar kunun tasha sosai tana jiran shigowar mutumin nata ta bashi......Baba Iro ne yayi sallama a dakin ya shiga ya zauna a nutse ya fara gaisheta ta amsa babu yabo babu fallasa a tare da ita." Yace."Gwaggo sai hakuri da yanayin rayuwa yau na tashi babu kudi a hannuna shiyasa ba'a siyo miki kosai ba." Tace."Aa babu komai Ibarahim yau da gobe ai kayan Allah ne kana kokari damu sosai da sosai Allah ya cigaba da bud'a maka." Yace."Ameeen ya Allah gwaggo ni zan tafi kasuwa." Tace."To ubangiji Allah ya bada sa'a ." ya amsa da ameeen ya rabbi." Bayan fitarsa da kamar minti goma Khalid ya shiga dakin cikin shirin fita, washe bakinta tayi tace"Sarkin ya'ki ina zuwa naga kayi kwalliya haka."? zama yayi kusa da ita da fad'in "Gwaggo yau ake daurin auran wani abokinmu shine zamuje gurin daurin auran ni dasu Salim." Tace."Allah sarki Allah ya sanya alkairi ya nuna mana lokacin naku." babu kunya ya amsa da "ameeen Gwaggo." Tace."Ina fatan dai ka karya ko."? girgiza kansa yayi yana yamutsa fuskarsa.....ta dauko jug din kunun da 'kosan tace."Khalid kada ka fita baka karya kummalo ba maza sha kunu ga kosai nan Sa'ida ce ta siya min." Sai da ta fad'i maganar kuma tazo tana data sani dan tasan da 'kyar idan zaici. Girgiza kansa yayi yace.''Gwaggo ki bari kawai idan na fita zan tsaya gurin mai shayi nasa ya dafa min indomee." 'Bata rai tayi tace."Khalid bana so ka saba da zuwa tevur din mai shayi kada kazo kuna rigima da iyalinka akan haka sabida wasu mazan haka zasu had'a matansu da koko su kuma su tafi tevur din mai shayi ayi musu hadin kauri susha.". Dariya yayi yace."Gwaggo nima ba'a san raina nake zuwa ba lalura ce amma insha Allahu idan nayi aure na daina zuwa da yardar Allah." tace."To haka nake so naji kasan wani abu kuwa."? Girgiza kansa yayi yana kallonta tace."Yanzu nake so na tafi gidan Uwale domin muje gurin wani malami ya taimaka mana akan Sa'ida Alamu sun nuna cewa ba'ka'ken aljanu ne suke damunta." Cike da mamaki yake kallonta kafin Yace."Gwaggo aljanu kuma? A'ina Aunty Sa'idar ta had'u dasu dan Allah ki daina wannan maganar sannan kuma ki rabu da wannan Uwalen bata da kirki.'' Rike bakinta tayi da fadin"Kai jama'a wai shin me Uwale tayi muku ne kuke zaginta Sa'ida ma kafin ta fita sai da ta zageta tatas sannan ta futa haba Khalid Uwale bata cancanci hakaba." Yace."To naji ni dai kada kije gurin malami aunty Sa'ida lafiyarta lau bata da wani aljanu zaki 'bata kud'inki a banza ki wahalar da kanki a wofi." "Khalid da kake wannan maganar kai waye ya fada maka bata da iskokai sune fa suke shiga tsakaninku kuke saurin fad'a da juna ba kaga bakwa jituwa da juna ba nifa saboda kai zanje a taimaka mana a karkato da hankalinta kanka." Dariya yasa ya shiga sosa tarin sumar kanshi da tasha gyara sai kyalli take yace."Ni dai idan saboda ni zakije gurin malami ki bari bana bukata da iskokai da babu aunty Sa'ida tawa ce babu wani aljani ko mutum daya isa ya shiga tsakaninmu soyayyata kuma da kaina zan dasa mata ita a cikin zuciyarta." "Umm!" tace alamun maganar bata gamsheta ba. Wayarsa ya dauko dake famar ringing yasa a kunne da fad'in "Salim ganin fitowa ina sallamar uwargidana ne." Daga d'aya 'bangaran Salim yace."Wace uwargida bayan ban jima da ganinta ta tafi aiki ba." 'Yar dariya yayi yace."Kai wannan ai amarya ce ina nufin uwargidana Gwaggo." Salim yasa dariya da fadin"To yanzu na fahinta amma yana da kyau ka sallameta da wuri ka fito dan kai kadai muke jira mu tafi gurin daurin auran." Yun'kurawa yayi ya mike tsaye da fadin" Gani nan ma fitowa na sallameta." kashe wayar yayi ya kalleta babu cikakkiyar walwala a tare dashi yace."Gwaggo dan Allah kada kije gurin nan." Da sauri tace."Haba ai na fasa zuwa kaga yanzu ma zan fara kad'in lagwani dan Salisu tun shekaran jiya ya kawo min da kudinsa." Yace."Yawwa gwara ki tsaya ki nemi kud'inki shi yafi amfani ki dai cigaba da yi mana addua ." Tace."To shikkenan Sarkin Ya'ki sai ka dawo." Fitowa yayi daga dakin yasa takalmansa masu gidan yatsa ya kama hanya ya fita daga gidan. Sai da taji shuru ta daina jin motsin Ummatu sai ta yafa mayafinta ta futo da kwad'o (key) taja kofar dakin nata ta kulle sad'af-sad'af ta fita daga gidan, Gwaggo sai da ta ganta a gidan Uwale tukkuna hankalinta ya kwanta. Uwale na dakin girki tana d'umame taji sallamar 'kawar tata da sauri ta fito daga kicin din tana fad'in "Gwaggo ashe kina tafe."? Gwaggo ta sauke ajiyar zuciya da fad'in " Wallahi tun safe naso nazo muje yaran nan Sa'ida da Khalid suka sani a gaba kamar munafuka haka na sid'ad'o na fito daga gida Uwale tace."Oh kiji ni da yara sai kace wa'inda suke auranki zasu hanaki fita." Tace."Kema dai kya fad'a Uwale." Dariya tayi tace"To shiga daki ki zauna na kawo mana d'umame muci sai mu tafi." Gwaggo ta shiga dakin ta zauna Uwale ta shigo dakin hannunta dauke langa cike da d'umamen towon shinkafa da miyar kuka harda man shanu! nan suka ci suka koshi suka sha ruwa kana suka gyara lullu'bin mayafansu suka tafi gurin malamin zaure. Kasancewar yau juma'a yasa sha biyu da rabi muka tashi, zaman da nayi da yunwa ya janyo min rawar jiki da zazza'bi a galabaice na shiga gidan na tarar dashi shuru ko'ina a bushe 'Katon mukullin dana gani a kofar dakin Gwaggo yasa gabana ya fad'i wato dai Gwaggo sai da ta fita kenan.....Jakata na fara lalubawa ina addua Allah yasa na samu spire na key din dan dama rabawa mukayi ita ta dauki biyu ni kuma ta bani daya, cikin ikon Allah na lalubo key din dakin na bud'e na shiga Jin yanda ya dauki zafi yasa na d'age labulan na d'ora kan kofar hijabina kawai na cire na nemi guri na kwanta wai na d'an huta kafin na nemi abunda zanci.......Ba tare dana ankara ba bacci mai dadi ya dauke ni. Koda ya shigo gidan kai tsaye dakin Gwaggon ya nufa yana fad'in "Gwaggo ina fata dai kin gamawa Salisu aikinsa dan yanzu ya tare ni a hanya yake min magan.......Kasa 'karasawa yayi ganinta a kwance a dakin tana bacci! ajiyar zuciya ya sauke ya cire takalmansa a nutse ya shiga dakin . Kai tsaye bakin gadon da take kwance ya zauna jikinsa na ta'ba nata, fuskarta ya tsirawa ido yana ayyana abubuwa da yawa a kanta, a hankali ya ra'ba ya kwanta a gadon ya nani'ka da jikinta sosai yasa hannunsa k'asan rigarta ya fara shafa cikinta da 'kasan mararta ajiyar zuciya ya dinga saukewa yana sake nanuwa da jikinta yayin da yake sake cusa hannunsa cikin rigarta yana shashshafa cikinta da mararta sai yayi sama da hannunsa gabansa na fad'uwa ya d'ora kan breast d'inta guda breziyar ya d'an janye ya janyo brest d'in ya fito dashi cikin fitar hayyaci ya fara mulmulashi a hannunsa yana murza nipples d'in yana sakin wani irin nishi tare da cije lips d'insa..... *Masoya a taimaka da sharing a gruops👏🏼* *IDAN KINA BUKATAR BIYAN KUDIN LITTAFIN GA YANDA ABIN YAKE......VIP GRUOP#600 NORMAL GRUOP#300....ACCOUNT.0542382124.....BINTA UMAR GTBANK....IDAN KATI ZAKI TURO #400 NE SAI KIYI MIN MAGANA TA WHASAP DA WANNAN NUMBER* *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* [3/6, 8:46 AM] 💜: *GA IRINTA NAN!!!🙆🏼‍♀️* _(LOVE STORY🌺)_ *NA* _BINTU UMAR ABBALE🍒_ *MANAZARTA WRITES ASSO🖊️📚* *8* Kamar a mafarki nake jin al'amarin. motsi nayi da niyyar na gyara kwanciyata naji an matseni! lokaci guda gabana ya fad'i! da sauri na bud'e idona gabana na cigaba da bugawa ina kuma jin hucin numfashin mutun a wuyana! hannuna na karkarwa na d'ora a saman hannunsa dake matse da breast d'ina yana lugwigwitashi! hannun na ri'ke tamau! yawun bakinta ya bushe! innalillihi wa'ina ilaihi raji'un! waye wannan."? cikin zuciyata nake wannan tambayar sabida rashin kunya hannuna na dam'ke da nasa amma a hakan yake 'kokarin cigaba da ta'ba breast d'in. murya na rawa nace."Khalid."! Zazzafar ajiyar zuciya ya sauke kafin naji muryarsa a shaqe ya amsa da "Na'am auntyna." Dama abinda nake so na tabbatar kenan! a sukwane! na mi'ke zaune juyowa nayi jikina na kyarma! na d'aga hannuna da niyyar kwad'a masa mari! yayi saurin ri'kewa yana girgiza min kai. Yanayin yanda naga 'kwayoyin idonsa sun sanja ne yasa nayi saurin sunkuyar da kaina k'asa wasu lafiyayyun hawaye suka shiga tsere a kan fuskata, Zuf d'in rigata a zuge breiziyata a 'balle duk nonuwa na a waje yaron nan ya samu yana lugudarsu. Jikina ya matso sosai har yanzu hannuna na ri'ke a hannunsa shima sai sai kyarmar jiki yake yace."Auntyna kiyi hakuri kinji Allah kasa daurewa nayi." wani 'katoton abu yazo ya tokare min a makogwaro! a sha'ke nace."Khalid yaushe ka zama d'an iska? yanzu ni kake 'kokarin haikewa wace irin mummunar rayuwa kake so ka jefa kanka a ciki."? Shuru yayi yana kallona nace."Ka zuba min ido kana kallona ko Khalid ina kwance ina bacci kazo ka fito min da nono kana wasa dashi meye amfanin hakan.''? Sumar kansa ya sosa a sanyaye yace."Kiyi hakuri dan Allah na fad'a miki cewa kasa daurewa nayi dama kuma kullum sai nayi wasa dasu a mafarkina." Ajiyar zuciya na sauke nace."Khalid zama na a gidan nan ba zai yiwu ba tunda kana farautata zan tattara na bar muku gidan a yanzu nasan duk wanda zan tunkara da wannan maganar ba zai yarda ba saboda haka zan bar gidan shi yafi alkairi." Jikinsa na rawa yace."Aa Aunty Sa'ida kada ki tafi ko'ina dan Allah ki zauna insha Allah ba zan 'kara ba cikin satin nan ma zan koma skull sai ki zauna lafiya tunda bana nan ." Hannuna na fizge daga nasa na gyara rigata sauka nake 'kokarin yi daga gadon ya ru'kun'kume ni! jikinsa na rawa yace.'' Dan Allah ki tsaya ki fahimce ni wallahi banyi miki hakan da wata manufa mara kyau ba aunt Sa'ida sha'awarki ce tayi min yawa shiyasa dana samu wannan damar na rage." Yana maganar yana tatta'ba min kirji." Tunkud'eshi nayi a fusace! nace"Ba zaka shiga hankalinka ba ko."? kamar wani zautacce ya sake kawo min raruma! da yake abin yazo min a bazata sai kawai muka fad'i a gadon a tare! kafafunsa yasa ya hard'e nawa! ya ri'ke ni tsam! yana shanshana jikina kamar tsohon karan da ya samu nama d'anye. Hankalina ya tashi nace"Khalid sake ni na tashi." "Um!um!." yafad'a cikin sigar shagwa'ba, tsigar jikina ta tashi! "Khalid ba zaka sak......Kasa 'karasawa nayi jin bakinsa a cikin kunnena yana tsosa! Ihu! na kurma! da karfin gaske! na kai masa duka! " Dan ubanka ba zaka sake ni ba."! nafada ina haurinsa da kafafuna! kamar maye ya ri'ke ni tsam! yana tsotsar kunnena da gefan fuskata sai so yake ya kamo bakina ina kaucewa. Kuka na shiga yi ina rokonsa ya sake ni na tashi, da kyar yace."Kin amince da maganata."? Da sauri nace"Wace magana."? A shaqe yace."Ta aure mana." naji kamar ya watsa min wuta a jikina, domin ya sake ni nace na amince." Ajiyar zuciyarsa naji kafin ya sassauta ri'kon da yayi min. nayi saurin fizge jikina na dira daga gadon ina haki da nishi! dakin na shiga bi da kallo! can na hango wayar da gwaggo take chaza redion ta, ita nai saurin daukowa na nannad'e ta a hannuna, a fusace! nayi kansa da duka! dirgowa yayi da sauri yayi hanyar fita yana dariya, hawaye na zubo min na bishi da duka amma ko d'aya ban sameshi ba abinka da d'an ball tsalle ya buga ya tureni ya fita daga dakin yana dariya. Zubewa nayi a gurin na dinga kukan bakin ciki ina nadamar abinda ya faru a tsakanina dashi.....ya zama dole nayi nesa da yaron nan kada watarana ya haike min ya rabani da budurcina. Da kyar na iya wanka nayi sallolina kana na d'ora farar shinkafa tunda inada miya dama haka nake sai nayi miya ta kwana uku ko hudu sai dai kawai na dinga amfanin da ita. Agogo na duba karfe hudu da rabi na yamma babu labarin gwaggo, al'amarin ya dinga bani mamaki yana daure min kai, kasa daurewa nayi naje na samu Ummatu tana hidimar d'ora abincin dare nace"Ummatu dan Allah ko kin san inda Gwaggo taje.''? Ba tare data dauki maganata da muhimmacin ba tace"Ni kam ban sani ba." a sanyaye na fito daga gurin wanda yayi dai-dai da shigowarta. hannunta ri'ke da leda viva. Kallo na shiga bin ta dashi , ta wani sha kunu da fad'in "Meye kike kallona ko kin aike ni ne."? Nace." Gwaggo yanzu dan Allah sai da kika je."? Shareni tayi ta shige daki, bayanta nabi naga tana kokarin d'aga gadon karfenta ina tsaye naga ta tusa ledar ciki ta mayar da zanin gadon ta rufe, nace"Ledar me kike 'boye."? A fusace! tace."Sa'ida ba zaki daina titsiye ni ba ko."? Girgiza kaina nayi na rabu da ita, taja tsaki tare da daukar buta ta fita. 'Daure da alwala ta shigo dakin, na kalli agogo biyar shaura minti biyar nace."Gwaggo a'ina kika tsaya baki sallah ba duba kiga lokaci fa." Ci kanki ba tace dani ba ta gyara dadduma ta tayar da sallah! ajiyar zuciya na sauke na fita daga dakin ina tunanin hanyar da zanbi gurin dauko ledar data 'boye a 'kar'kashin gadonta. "Sa'ida idan kin gama abincin zubo min naci." muryarta naji daga cikin dakin tana magana. nace."Bangama ba tukkuna." Tace ."Salisu mai kanti ya aiko ko."? nace"Ban sani ba dan nima bacci nayi bayan na dawo daga makaranta. Tace."To koma dai ya aiko to sai dai yayi hakuri dan yanda na gaji d'in nan bazan iya tsinana komai ba." Nace."Wai dan Allah gwaggo ina kikaje kada kice min kinbi Uwale gurin malami." Shuru tayi bata tanka ba, sai nima nayi shuru na kyaleta, abincin na 'karasa dahuwa na zuba mata da yawa a plate nasa mata miya da kifi na kai mata. Da sauri tace."Yawwa babbar mace nagode." ruwa na d'ebo mata na ajiye mata a gabanta na fita daga dakin, a nan tsakar gidan na zauna naci nawa abincin na gyara gurin tsaf na koma dakin. Tace."Haba Jama'a yanzu naji dai-dai." shuru nai mata na cigaba da abinda nake, a nutse ta kira sunana, na juyo ina kallonta tace."Naji kina cewa malami me magani zaki ce dan mu ba gurin malamin zaure mukaje ba." Nai shuru ina sauraranta ta cigaba da cewa "Na fad'awa mai magani duk abinda yake damunki kuma ya had'o miki magani Sa'ida inaso ki bani had'in kai dan Allah kiyi amfani da maganin nan domin hankalina ya tashi dana ji yace wai 'bakin aljani ne ya aureki shiyasa bakya so ayi miki maganar aure kuma shine yake shiga tsakaninki da Khalid kuyi ta fad'a kuna samun sa'bani wallahi Sa'ida bakiji yanda hankalina ya tashi ba." Cike da mamaki nake kallonta kafin nace"Gwaggo nice nake da 'bakin aljani."? da sauri tace."Eh mana ko kina kokwanto ne."? nace."Kwarai kuwa Gwaggo ni ban yarda ina da iska ba saboda haka asarar kudin ki kawai kikayi." Marairaice fuska tayi tace"Haba Sa'ida ya zakice baki yarda kina da iskokai ba yanzu shekarunki nawa a duniya kina zaune babu aure duk sa'onin ki sunyi aure sun haihu yaransu sun wayo amma ke kina zaune duk namijin da ya yun'kuro da niyyar auranki sai ya gudu ko kuma a d'aure masa baki a hanashi magana wannan fa duk sharrin iska ne." Murmushi takaici nayi nace."Gwaggo ni abinda na kaddarawa rayuwata shine aure lokaci ne duk yanda naso da nayi aure idan lokacin baiyi ba dole na hakura kuma kina maganar cewa na girma nayi shekaru babu aure ai bani kad'ai bace akwai dubban matan da suke zaune babu aure da yawa daga cikinsu ma sunfi ni girma da shekaru saboda haka ki daina wahalar da kanki akan al'amarina duk ranar da Allah ya kawo lokacin aurena babu mahalukin daya isa ya hana." Tace."Eh duk da haka Sa'ida bakiji bahaushe yana cewa idan kana da kyau ka 'kara da wanka ba ni na yarda da maganar mai maganin nan domin aljani yana da suddabaru iri-iri saboda haka dan Allah kada ki watsa min 'kasa a ido." Murmushi nayi nace."Gwaggo kenan dan Allah ki bar maganar nan kinga lokacin sallah yayi kije kiyi alwala ki sallah ki roki Allah ya za'ba min abinda yafi alkairi." Tace."Sallah ko kince nayi ko baki ce nayi ba dole nayi kuma Ubangiji shima ya fad'a cewa bawa ya tashi ya nema shi kuma sai ya taimakeshi." Nace"Gwaggo ba'a irin wannan al'amari Ubangiji yayi magana ba, Allah yace." Ko ro'keni ni kuma zan amsa muku amma bece wani bawan sa yaje gurin malamin duba ba." A tunzure! tace"Wai Sa'ida waye yace miki gurin malamin duba mukaje."? Nace."Gwaggo dan Allah maganar nan ta mutu haka magani dai idan dan ni kike siyo to kinyi asarar kudin ki dan bazan sha ba." Ina gama maganata na fita daga dakin na barta tana bina da kallo. Bayan mun idar da sallar sai ta mike ta fita daga dakin minti biyar ta dawo hannunta dauke da karamin kaskon wuta da garwashi a ciki.......kallo na bita dashi ganin ta d'aga 'karkashin gadonta tana lalube ledar data shigo da ita ta dauko ta saki zanin gadon ta rufe........ta shiga zazzage magungunan dake cikin ledar.....Wani tsumma ta kwance naga ta d'ebo maganin dake ciki ta zuba a wutar a take dakin ya turni'ke da haya'ki! tari ya sar'ke ni! haya'kin maganin ya dinga shiga bakina da hancina! a gigice na mi'ke na fita daga d'akin ina tari da rirri'ke kirji, ko gama dawowa hayyacina banyi ba itama ta fito daga dakin ido jazur! sai tari take hawaye na zuba daga idonta...... *Masoya a taimaka da sharing👏🏼* *IDAN KINA BUKATAR KI BIYA KUDIN LITTAFIN GA YANDA ABIN YAKE.....VIP #600 NORMAL#300 .....ACCOUNT..... 0542382124....BINTA UMAR GTBANK....IDAN KATI ZAKI TURO #400 NE SAI KIYI MIN MAGANA TA WHATSAPP DA WANNAN NUMBER* *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* [3/6, 8:46 AM] 💜: *GA IRINTA NAN!!!🙆🏼‍♀️* _(LOVE STORY🌺)_ *NA* _BINTU UMAR ABBALE🍒_ *MANAZARTA WRITES ASSO🖊️📚* *9* Haka Baba Iro ya fito ya same mu a tsaye muna tari ga haya'ki na fitowa daga cikin dakin. "Gwaggo lafiya me yake faruwa ne."? Miyau ta had'iya ido jawur tace." Haya'ki na kunna sai tari ya sar'ke muka fito muna shan iska." Yace."Gwaggo wane irin haya'ki ne wannan mai cutarwa.''? Da sauri tace."Na mayu ne kwana biyu kasala tana damuna shine Uwale ta kawo min dama kuma ai sa'i da lokaci ina kunnawa ." Shuru yayi yana kallonta nima na zuba mata ido ina mamakin 'karyar data shirga. Dakin ya shiga da sauri tabi bayansa tana kallonsa tace."Ibarahim me kake nema."? Yace."Garin haya'kin zan duba nagani." Tace."Aa ba sai ka wahalar da kanka ba ai ragowa ne na barbad'a a wuta shine fa ya turnu'ke gidan da haya'ki." Yace."Gwaggo dan Allah ki daina yarda da camfi irin na mutane wane maye ne zai kamaki acikin unguwar nan."? Tace."Aa Ibrahim ai shi maye bashi da kama watakila ma ina hurd'a dasu ban sani ba, to dan nayi haya'ki ai ba laifi bane." Yace."Hakane gaskiya to dan Allah gwaggo kisan irin haya'kin da zaki dinga yi duba dai wannan kinsa gashi gabad'aya ya sar'ke muku numfashi." Da sauri tace."Ai yau ne kawai hakan ta faru amma lafiya lau nake haya'kina to tunda ma dai maganin ya 'kare ai shikkenan." Fita yayi daga d'akin ya kalleni cikin taushin murya yace."Sa'ida ki cigaba da hakuri da halin gwaggo ina nan inayi miki addua akan Allah ya kawo miki miji kiyi auranki." Hawaye naji na kokarin kufce min nace."To Kawu nagode sosai." Yanda na lura dashi shima yana damuwa da halin mahaifiyar tasa dan dai bashi da yanda zaiyi da ita ne.'' Dakin na shiga na sameta tana gyara shimfid'a k'aurin maganin da haya'kinsa ya dinga sanyawa kaina yana juyawa bana tsammanin zan iya kwanciya a dakin domin kuwa zuciyata in banda tashi babu abinda take. Tabarma da bargo na dauka na fita daga dakin....shimfid'awa nayi a wani dan loko a tsakar gidan na koma dakin na dauki fillo da wayata, kallo ta bini dashi har na fita daga dakin. Gwara na kwanta a tsakar gidan yafi min alkairi." Waya ta na bude ina dubawa naga text d'in Alhaji Nura wai yana nan fa yana jiran amsa daga gare ni, murmushi kawai nayi ba tare dana bashi amsa ba na shiga WhatsApp ina dubawa.........Gwaggo da buta hannunta ta fito daga dakin ta nufi bandaki tayi uzirinta ta fito, sai da tazo kusa dani naji tana fad'in " 'Dakina ne babu wanda ya isa ya hanani yin abinda naga dama mutum yayi ta kwana a tsakar gida sauro ma ya ishe shi." Uffan bance mata ba na cigaba da duba wayata, ta ajiye butar a bakin kofar dakin tace."Ai tabbacin mutum na tare da iskokai kenan gashinan ai saboda hayak'in yana da k'arfi sun koro ki daga d'akin ai duk abinda zakayi ba zan fasa turara haya'kin nan ba." Ta gama surutan ta ban tanka mata ba cikin zuciyata ina ta shawarar matakin da ya kamata na dauka Khalid yana barazana ga rayuwata gwaggo tana kuntukawa zuciyata barina gidan shine yafi alkairi....."Sa'ida idan kin koma gidan mahaifiyarki anya kuwa ba zaki takura mata ba."? zuciyata ce take tunasar dani.....Ummana bayan rasuwar mahaifina wanda ta aura babban mutum ne mai iyali itace matarsa ta uku kuma bata dad'e a gidan ba ya cikashe ta hud'un babban gida ne mai d'akuna kowace na rayuwa ita da 'ya'yanta a dakinta sai dai duk ranar girkinta taje dakin maigidan......Alhaji Shamsu babban mutum ne kuma d'an kasuwa yana da shaguna masu yawa a kanti kwari suna harkar atamfofi tun bayan auransa da Ummana yaso na koma hannunsa Gwaggo tayi ta tsula musu rashin mutunci daga shi har Ummana tace babu wanda ya isa yayi iko dani tana raye jininta ba zaiyi agolanci a wani gidan ba. Ganin irin rigimar da takeyi ne yasa duk suka hakura hidima sosai mijin Ummana ya dinga yi min duk sabgar karatuna shine ya dauki nauyi kuma duk ranar da naje gidan ziyara yakan bani kudi masu yawa na tabbata a yanzu idan nace zan koma gidan da zama zaiyi farin ciki sosai kuma zai kar'be ni da hannu biyu, tabbas akwai yiwuwar na koma gaban mahaifiyata da zama dan al'amarin gwaggo da Khalid yana nema ya shallake tunani na. "Sa'ida ya kike kwance a tsakar gida ke kad'ai."? Muryar Baba Iro naji a kaina. Da sauri na mike zaune da fad'in" Wallahi zafi ne ya isheni na fito amma idan gari ya saki zan koma daki." Yace."To shikkenan amma ina fatan sauro baya damun ki."? Nace."Eh da sauki tunda na kunna magani." yace."To babu damuwa." Labulan d'akin Gwaggon ya daga yana dubata. Sunanta ya kira yaji shiru nace."Ai da alama tayi bacci." yace."Eh hakane to sai da safe." Nace."To Kawu Allah ya tashe mu lafiya." Yana barin gurin na koma na kwanta waya ta na kashe na rufe jikina tare da addua a bakina. Yana can gurin kallon ball sai kusan sha biyu shaura ya shigo gidan......shuru ko'ina yayi duhu da sauri ya fito da wayarsa ya kunna torchlight idonsa ne ya sauka kanta tana kudindine a cikin bargo garin ya saki ana iska sosai dalilin da yasa kenan cikin bacci taja bargon ta rufe jikinta har kanta. Tsayawa yayi a kanta yana kallonta tare da haske ta da hasken wayarsa, a hankali ya tsuguna kusa da ita yasa hannu ya bude mata fuska idonsa ne ya sauka kan wayarta da take kusa da ita ya dauka da sauri ya mi'ke daga gurin. Dakinsa dake cikin gurinsu ya bude ya shiga ya zauna bakin katifarsa a nutse ya kunna wayar ya shiga yi mata binkice, babu wasu tarkacen numbobin maza a ciki yaji dadin hakan Number Alhaji Nura ce kawai itama yana ganinta ya gogeta yana tsaki! yana kokarin kashe wayar text ya shigo. Da sauri ya shiga yana dubawa, text ne daga Alhaji Nura ga abunda yake cewa. _Gimbiyar mata kinyi shuru baki bani amsa ba kuma nasan kinga messengers d'ina Sa'ida ko kuma na cire tsammani ne.?_ Ya dinga wani irin huci! kibiyar kishi na sukar sa a ma'kogwaro a duniya nan bashi da babban wanda ya tsana kamar mutumin nan. Hannu na rawa ya fara bashi amsa kamar haka. _Alhaji kayi hakuri fa ban san amsar da zan baka ba shiyasa kaji nayi maka shuru to amma yanzu tunda ka tsananta inso na tabbatar maka da cewa ina da miji zamuyi auran zumunci da 'Dan uwana Khalid saboda haka dan Allah ka daina bibiyar rayuwata haka._ Tura masa text din yayi ya kashe wayar, fulas din abincin sa ya janyo ya bude a nutse ya fara ci bayan ya kammala ya dauki pure water guda yasha ya mike ya fita da wayar a hannunsa Har yanzu tana kwance a tsakar gidan.....a jiye mata wayar yayi a kusa da ita ya juya da niyyar barin gurin shawara ya sanja ya dawo a da baya. A hankali ya tsuguna gabanta 'kasa-'kasa ya shiga kiran sunanta.....mafarkinsa take gashi wai suna kwance a gado d'aya sun lullu'ba da bargo suna wasu abubuwa masu dad'in gaske, kawai ta dinga jin sautin muryarsa a kanta yana kiran sunanta. A firgice ta mike zaune tana zazzare ido a kansa "Khalid me kakeyi anan gurin."? bakinta na fara tayi maganar tana dudduba jikinta addua take Allah yasa mafarkinta ba gaskiya bane. A tausashe yace." Babu abinda nake ban jima da shigowa ba na ganki a kwance ke kad'ai aunty Sa'ida akwai sauro ki tashi ki koma a d'aki." Shuru tayi masa ta mike da sauri ta fara kwashe kayan shimfid'ar sai ya shiga taimaka mata suka kwashe kayan shimfid'ar a tare, duk shige da ficen da suke Gwaggo nacan tana shirgar baccinta. Fitowa tayi da niyyar kama ruwa, kawai sai ta ganshi a tsaye a jikin bango(Garu) gabanta ya fad'i! tai saurin dauke kanta hannunta ri'ke da buta ta nufi bandakin. Koda ta fito yana nan tsaye a inda yake......Sai tasha jinin jikinta cikin sauri tayi nufin shiga dakin ya tare mata hanya...... shuru tai tana kallonsa yasa kirjinsa ya danne nata sai ta jingina jikin bango(garu) bata so tayi magana jama'ar gidan su tashi in banda Kawu Iro babu wanda zai yarda da ita Ummatu da Gwaggo zasu ce sharri tayi masa. Yasa hannunsa ya zagaye 'kugunta dashi sosai ya matseta a kirjinsa yana sakin wani irin nishi kafin yayi magana da wani irin voice "Auntyna dan Allah ki taimaka ki bani bakinki nasha kinji ko." Shuru nayi masa ya dinga wasu irin sambatu yana ya mutse min jikina......"Khalid kafi karfina sharrin ka ya girmi tunani zan had'aka da Allah yayi min maganinka." cikin rawar murya nayi maganar. Jikinsa na kyarma ya tallafo fuskata a hankali yace."Auntyna kada ki had'ani da Allah idan na lalace kema kin lalace aunty Sa'ida bani da laifi kaunarki ta riga ta gama kassara ni mutukar zan gan ki nakan rasa nutsuwata dan Allah da darajar Annabi Muhammad (SAW) ki amince da soyayyata." Girgiza kaina kawai nakeyi hawaye bakin ciki da takaici na kwararo min.....Harshensa yasa ya shiga lashe hawayen yana tsotsar kumatuna kokarinsa ya kamo bakina na fuzge fuskata da sauri nasa 'karfi na tureshi yayi taga-taga zai fad'i! da sauri ya fizgo hannuna a lokacin da nake kokarin shiga dakin kawai na jini a kwance a kirjinsa........Bakinsa yasa a daidai kunnena yana sakin wani irin nishi kafin yasa hak'ori ya d'an ciji fatar kunnena da fad'in "Kina so rayuwata ta salanwace ko aunty Sa'ida mutukar baki amshi soyayyata ba zan iya rungumar transformer ta tashi dani na bar duniya." Ji nayi kamar na shaqe masa wuya saboda takaici na sake yunkurin tureshi ya ri'ke ni gam! gam! yana shanshana jikina tsigar jikina ta dinga tashi............."Kada dai wannan yarinyar bata shigo ba." Muryar Gwaggo ce ta doki kunnuwanmu da sauri muka kalli bakin kofar d'akin hasken torchlight d'inta dalll! da alama fitowa tsakar gidan take kokarin yi da sauri ya sake ni yayi gaggawar shiga gurinsu, ni kuma jikina na rawa na d'auki butar dake ajiye a bakin kofa....ta fito daga dakin tana surutai gani na yasa ta dauke kanta ta nuna kamar bata damu ba nima bance mata komai ba na mika mata butar ta ta kar'ba da sauri na shige dakin ita kuma ta nufi bandaki... *Masoya a takaima da sharing👏🏼* *IDAN KINA BUKATAR BIYAN KUDIN LITTAFIN GA YANDA ABIN YAKE....VIP GROUP #600 NORMAL GROUP.... #300.....ACCOUNT... 0542382124.....BINTA UMAR GTBANK....IDAN KATI ZAKI TURO #400 NE SAI KIYI MIN MAGANA TA WHATSAPP DA WANNAN NUMBER. *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* [3/6, 8:46 AM] 💜: *GA IRINTA NAN!!!🙆🏼‍♀️* _(LOVE STORY🌺)_ *NA* _BINTU UMAR ABBALE🍒_ *MANAZARTA WRITES ASSO🖊️📚* _*Free pege ya kusa 'karewa kuyi maza ku hanzarto domin ku biya kudin karatu🥰🤝🏻 Masu tambayata na turo musu littafin su biya kudinsu sai a sasu a gruop😊 Sannan dan Allah masu plashing su bari! idan kin san ba siyan book d'in nan zakiyi kada ki dauki number ta kiyi min magana dan Allah mu muntuna junanmu🤝🏻 Masoya masu kaunar cigabana ina sauraranku fa💃🏻 Free Pege ya kusa 'karewa ku hanzarto!!!!*_ *10* Na jima kafin bacci ya dauke ni. Da safe kuma na tashi da wata irin kasala da damuwa dan ina idar da sallar asubahi ko hijabin jikina ban cire ba na kwanta kan daddumar. idona kawai na rufe ba don nayi bacci ba sai dan tunanin yanayin rayuwa hakika abunda ya faru tsakanina da Khalid ya tsaya min a raina na rasa yanda zanyi na tunkari gwaggo da maganar gashi ina jin kunyar Baba Iro na ce masa d'ansa yana min me? al'amarin da akwai nauyi da kuma kunya idan ya yarda to na tabbata Gwaggo da mahaifiyarsa Ummatu ba zasu yarda ba zasu ce nai masa sharri ne, amma haki'kanin gaskiya lamarin da akwai ban tsoro da firgici a ciki ina tsoron ranar da zai samu galaba akaina to kuwa tun kafin zuwan ranar gwara na nemawa kaina mafita. Idona a rufe na soma jin 'kaurin maganin jiya a hancina. da sauri na bude idona na mike zaune ina kallonta tana tsaye a kaina da 'karamin kasko a hannunta tana turare ni haya'ki. Da saurin gaske na miqe dan har sai dana bugeta waje na fita na tsaya a tsakar gida ina mayar da numfashi wani irin jiri da ciwon kai ne yake taso min. Fitowa tayi da haya'kin tana fad'in "Sai dai idan waje zaki fita amma duk inda zaki shiga a gidan nan sai na turara miki haya'kin nan dan ba zanyi asarar kudina a banza ba." Ido jawur na kalleta tana sake kusanto inda nake da haya'kin nace."Gwaggo Kina so 'bakin cikin ku ya kasheni ko."? Shuru tayi min ta cigaba da turo kaskon haya'kin inda nake. Takalma na nasa da sauri na kama hanyar fita daga gidan kamar wata zararriya. tace."Au! futar zakiyi kuwa."? ko kallonta banyi ba nasa kai na fita daga gidan. Karo muka buga a lokacin da yake kokarin shigowa hannunsa rike da wata k'aramar bakar leda. Yanda yaga jikinta na rawa yasa yayi saurin rike hannunta a nutse yace."Aunty Sa'ida ina zaki da sassafe haka? yau asabar babu makaranta." Zuciyata ta karye na daure ban bari hawayen sun zuba ba nace."Khalid Sake ni." Girgiza kansa yayi a tausashe yace."Ba zan sake ki ba aunty dan na lura bakya hayyacinki." Ido na tsira masa shima ya tsira min nasa, a haka Baba Iro ya shigo ya same mu....Gyaran muryar da yayi itace tasa muka ankara da shigowarsa yace."Lafiya na ganku a tsaye a soro."? Hannuna dake cikin nasa ya sake ri'kewa yace."Baba da alama babu lafiya dan nima nazo shigowa mukayi karo da ita zata fita a gigice.'' A nutse ya kalleni da fadin"Sa'ida me yake faruwa ne.''? Hawayen da nake kokarin dannewa suka kucfe nace ."Kawu maganar dai guda d'aya ce." Yace."Gwaggo ce ko.''? kaina na d'aga nace"Eh tun jiya ta hanani zaman lafiya a dakinta tace aljanu ne dani kawai yanzu ina kwance na ganta a kaina tana bunka min haya'ki." Baba Iro ya shiga girgiza kansa yana mamakin halin rigima irin na mahaifiyarsa. yace."Sa'ida kiyi hakuri kinji ko mu shiga gidan za'a sasanta." Nace."Kawu nifa idan ba haya'kin nan ta daina bunkawa ba ba zan shiga dakinta ba." Khalid yace."Muje duk inda haya'kin yake zan daukeshi na yar dashi." Jin abinda yace yasa na yarda muka shiga gidan a tare. Suna tsaye ita da Ummatu suna magana......"Wallahi ajanu ne da ita gashinan daga jiya zuwa yau duk ta kasa nutsuwa sakamakon turaran da nake mata kinga yanzu tayi waje a gigice." Ummatu tace."To ai kuwa tunda dai an gano bakin zaren sai a cigaba da nema mata magani.....shigowarmu yasa duk suka kallemu. Khalid kai tsaye dakin ya nufa yana neman maganin Gwaggo kamar ta sani ta dauka ta bawa Ummatu ta 'boye mata....Kawu Iro yace "Gwaggo wannan wace irin rayuwa ce dan Allah ya kike nema ki furgita yarinya kina cewa tana da aljanu a ina suke? Gwaggo na fad'a miki ki daina yarda da surutan mutane akan yarinyar nan shi aure lokaci ne dashi idan lokacinta yayi za tayi aure amma dan Allah ki daina d'ora mata lalura yanzu ina amfanin abinda kikayi Gwaggo da sassafe kin bunka a haya'ki a gida kin firgita yarinya tunda tace bata so ba sai ki k'yaleta ba." "Kai Ibrahim ba fa zanyi asarar kudina ba dole sai nayi haya'kin nan tunda d'akina ne kuma idan ba aljanun ne da ita ba me yasa take guduwa mu da muke shak'ar haya'kin me yayi mana saboda haka ba zan fasa abinda nayi niyya ba idan tana da inda za taje ta tafi." Khalid ya fito daga dakin fuska a murtuke yace."Gwaggo ina haya'kin naga irinsa." Kallonsa tayi lokaci guda ta fahimci abinda yake da akwai tace." Babu sauransa kenan nasa a wuta." Kawu Iro yace."Gwaggo jiya ma fa haka kika ce sai gashi kuma yau da safe kin kuma kunnawa." Kuka ta fashe dashi tace."Yanzu dai kunyi min taron dangi kenan kuna kokarin 'karyata ni ko."? Kawu Iro hankalinsa ya tashi ya dinga rarrashinta tace."Oh!oh! Ibrahim ai 'yar d'an uwanka ta fini a gurinka tunda gashinan a kanta kana nema ka 'kure ni." Yace."Aa Gwaggo wallahi ba haka bane ina ni ina 'kure ki nayi laifi ki yafe mun." Ba tare da tace komai ba ta shiga dakinta ta bar mu a tsaye. Kallonsa nayi naga duk hankalinsa ya tashi nace."Kawu ka kwantar da hankalin ka insha Allahu zan cigaba da hakuri da halinta." Yace."Yawwa Sa'ida dama abinda nake so kenan naji daga gurinki kiyi ta addua kinji ko komai mai wuce wa ne." Cikin dauriya nace."To Kawu nagode." Gurinsu ya nufa ya barmu nida Khalid a tsaye.....Yace."Aunty Sa'ida kada ki damu duk inda ta 'boye haya'kin zan bincika a dakin." Nace."Khalid kyaleta dakinta ne fa tayi duk abinda take so da abunta." "Eh d'akina ne Sa'ida idan kinyi zuciya kada ki sake shigowa." Tana daga cikin dakin take magana. Yace."Gwaggo wace irin magana ce wannan."? "Haba Jarumi ai dole raina ya 'baci akan al'amarin nan ranar da naje 'karbo maganin nan sai da na yini banci ba bansha ba salloli na ma sai had'asu nayi amma saboda wukalancin Sa'ida ta dinga kokarin watsa min 'kasa a ido. Yace." To wai waye ya saki ne? sai fa da nace dake kada kije okey to zanje har gidan ita Uwalen da take janki yawon gurin masu magani na gargad'eta akan hakan ni idan kinyi min baki ba zai kamani ba tunda dai ni ba Baba Iro ba ne." Kuka tasa daga cikin dakin take fad'in "Khalid kada kaje kaci mutuncin Uwale bata cancanci hakaba." Ya d'aga labulan d'akin da fad'in."To idan bakya so naje gidan Uwale dauko min haya'kin." Tace."Shigo ka kar'ba." da sauri ya shiga dakin nima naji wani sanyi a cikin raina.......Wani tsohon magani ta d'auko masa a 'karkashin gadonta a daure a wata tsuhowar leda ta mika masa da fad'in"Gashinan wannan jaraba ta isheni haka." Kar'ba yayi ba tare da ya tanka mata ba ya fito daga dakin. Yana fitowa yace." Ki kwantar da hankalinki ga maganin nan a hannuna zan fita dashi na zubar." Hannunsa na kalla a take na gane ba maganin bane domin wancan a k'ulle yake b'akar leda wannan kuwa ledarsa yaluwa ce.....girgiza kaina kawai nayi na wuce na barshi a gurin, dakin na shiga na sameta tana murd'a redion ta ta dago kanta ta kalleni ta dauke kai tana cigaba da abinda take......gurin dana kwanta na nufa na dauki wayata na nemi gefan gado na zauna wayar na kunna na fara dube dube a ciki.......Ummatu ce ta shigo da jug d'in kunu da mai daidaiciyar silba da 'kosai a ciki. Abin mamaki cikin mutuncin Gwaggo ta kar'ba "Sannu 'yar albarka ai Ibrahim yayi sa'ar mata Rabi wallahi ina jin dadin zama dake sabida kina mutunta ni Allah yayi miki albarka." Compilied By Abubakar Saleh AlQuyraemey Whatsapp Number 08138873799 Visit www.rumbunlabarai.com For More Complete Documents Ita kanta Ummatu sai da tayi mamaki da yake tasan halin Gwaggo sai tayi dariya kawai ta girgiza kanta ta fita daga dakin....Nima dana san dani take ban tanka mata ba na cigaba da duba text d'in da Alhaji Nura ya turo ina mamakin al'amarin.....Kiran wayarsa ne ya katseni da sauri na d'aga nasa a kunnena. Yanda ya amsa gaisuwata yasa naji jikina yayi sanyi nace."Alhaji naga text dinka amma kuma ban fahimci abinda kake nufi ba." A d'an fusace! yace."Sa'ida kada ki mayar dani 'karamin yaro mana, jiya kin turo min text din daya hanani bacci amma yanzu kina wata magana." A nutse nace."Alhaji kayi hakuri kayi min bayanin da zan fahimta na dai ga text d'inka amma ban mayar maka da replay ba." Ajiyar zuciya ya sauke yace."Haba Sa'ida kada kiyi wasa da hankalina mana, nifa ba yaro bane ballanatana kizo min da wasa da gaske nake auranki zanyi amma me yasa kin san akwai al'kawarin aure a tsakaninki da yaron nan Khalid kikayi wasa da hankalina." Jikina yayi sanyi nace."Wace irin magana ce wannan waye kuma Khalid."? Lokacin da nayi maganar tayi daidai da lokacin daya shigo dakin shida Gwaggon suka zuba min ido....na cigaba da cewa."Alhaji ina tambayarka kayi shuru waye Khalid da har kake wata magana akansa yanzu a duniya na rasa mijin aure sai Khalid dan Allah ka daina wannan maganar sannan kuma text d'in daka gani mybe shine ya dauki wayata a bayan idona ya turo maka amma ni da hannuna wallahi ban tura maka wani text ba." Ajiyar zuciya ya sauke yace."Okey to har naji dadi a cikin zuciyata yanzu a'ina maganarmu ta kwana."? nace."Insha Allahu yau ko gobe zan yanke shawara.'' Yace."Haba Sa'ida wace irin shawara ce wannan da har yanzu ba'ai yanke ba."? Nace."Alhaji ka 'kara hakuri dan Allah." Yace."Shikkenan tom ina sauraranki." Sallama mukayi na kashe wayata rai a 'bace na kalleshi yana tsaye idonsa ya kad'a yayi jajazur!! sai wani irin kallo yake min. "Khalid waye ya baka izinin d'aukar min waya."? Kai tsaye yace." Ni ne na bawa kaina izini ko kina da abinda zakiyi ne."? Cike da mamaki! nake kallonsa. Ya zare min manyan idonsa da suka rine da 'bacin rai da 'bakin kishi yace."Ni kike ciwa fuska ko."? Nace."Meye abin cin fuska sarkin tsaurin ido ina kai ina Alhaji Nura da har zaka dauki wayata ka rubuta masa text kasan dai ya kusa haifarka ko."? Yana 'kokarin magana Gwaggo tace."To daya kusa haifarsa mai zai nuna masa? namiji yake shima namiji yake sannan duk abinda yake dashi shima yana dashi sai me kuma."? Kallonta nayi tace."Mara mutunci wacce bata san mai sonta ba, dame Alhaji Nuran yafi Khalid da har zaki dinga ci masa fuska." Nace."Kinga Gwaggo ki cire kanki daga cikin wannan maganarki babu ruwanki ni babu wanda ya isa yayi min dole a gidan nan wanda nake so zan aura bana auran 'karamin yaro a kyaleni." Gwaggo ta fashe da kuka had'e da fad'in "Zagi na Zakiyi ne naga kina zaburowa ko kuma dukana zakiyi butulu kawai." Hawaye suka shararo min nace."Me nayi na butulci kuma? ina zaune a gado na mahaifina ina ciyar da kaina sai me? me nayi na butulci da har kike kirana da kalmar." Jikinta ne kuma yayi sanyi ganin ina kuka.....Girgiza kansa yayi ya fita daga d'akin zuciyarsa kamar ta babbake saboda 'bacin rai. Bayan fitarsa na share hawaye mi'kewa nayi na fara had'a kayan wanki, sai naga tana satar kallona cigaba nayi da abinda nake tace."Sa'ida kinga yau 'kosan yayi kyau gashi da zafinsa ki zuba kunun kisha sai kiyi wanki." Nace."Aa Gwaggo ba zan sha kunu ba kisha kawai.'' Shuru tai tana kallona tsaf na gama had'a wankin na fita dashi can bakin rijiya na zubesu komawa dakin nayi na dauko indomee biyu 'karamin gas d'ina na kunna na d'ora tukunya da ruwa akai na zuba indomee a ciki.....ina zaune a gurin ta dahu na juye a plate kana na kashe gas d'in. Nan tsakar gidan na zauna a nutse naci na fara ci ina Nazarin rayuwa wai ni Gwaggo take kira da Butulu hummm! rayuwa kenan. *Masoya a taimaka da sharing👏🏼* *IDAN KINA BUKATAR BIYAN KUDIN LITTAFIN GA YANDA ABIN YAKE.....VIP GRUOP#600 NORMAL GROUP #300 ACCOUNT... 0542382124.....BINTA UMAR GTBANK....IDAN KATI ZAKI TURO #400 NE SAI KIYI MIN MAGANA TA WHATSAPP DA WANNAN NUMBER* *07084653262* *08089965176* *BINTA UMAR ABBALE* [3/6, 8:46 AM] 💜: *GA IRINTA NAN!!!🙆🏼‍♀️* _(LOVE STORY🌺)_ *NA* _BINTU UMAR ABBALE🍒_ *MANAZARTA WRITES ASSO🖊️📚* *12* Cikin ikon Allah ina tsayuwa a bakin titin wani adaidaita sahu ya tsaya a gabana. "Hajiya ina zakije."? Ya fad'a yana dan le'ko da kansa. Da sauri nace."Hotoro zaka kai ni." Jim yayi kafin yace."Okey to nawa zaki biya."? 'Kugin da naji a bayana yasa nai saurin juyawa Khalid ne da Salim cikin a daidaita sahu suna kokarin shiga layin....Da sauri na dauki jakata na fad'a babur da fad'in "Muje ko nawa ne zan baka." babur din ya buga da sauri muka bar gurin....Sai da naga munyi nisa sosai hankalina ya kwanta a nutse na fito da wayata daga cikin jaka number ta na shiga nema inaso na sanar da ita cewa gani nan a kan hanya. A tsanake muka gaisa nace."Umma gani nan a kan hanyar zuwa." Tace."Da daddare nan Sa'ida ina fata dai lafiya."? Cikin rauni nace."Lafiya Umma." Ta amsa da to "Alhamdulillahi sai kin 'karaso." Kashe wayar nayi nasa a jaka kana nayi saurin sa gefan hijabina na goge hawayen da ya fara zuba a fuskata. Cikin magagin bacci ta tashi tana lalu'ben torchlight d'inta ta kunna tana haske d'akin da fad'in "Sa'ida Ibrahim din be shigo bane."? Shurun da taji yasa tayi saurin kallon inda take kwanciya taga wayam! sai tai zargin ko tana bandaki redion ta ta dauka ta fara kokarin kunnawa wasu tashoshin sun rufe da kyar ta lalubi freedom redio lokacin suma daf suke da rufewa. kimanin minti goma tana zaune ba taji motsinta ba sai ta mike ta fito bakin band'akin ta tsaya tana kiran sunanta. shurun da taji yasa gabanta fad'uwa tana kokarin barin gurin ya shigo gidan ganinta a tsaye a bakin bandaki yasa yace." Gwaggo lafiya me kike anan gurin."? Murya na rawa tace."Khalid Sa'ida bata gidan nan.'' gabansa ya fad'i da sauri yace."Gwaggo bangane bata gidan nan ba." ? Ajiyar zuciya ta sauke tana kokarin barin gurin tace."Jeka kira min babanka idan ma yayi bacci ka taso shi.'' Khalid da sauri ya nufi gurin nasu itama ta nufi dakinta tana haske haske da torchlight nan taga babu jakar kayanta sai ta sake karaya a sanyaye ta zauna kan shimfid'arta tana fad'in "Wannan yarinya bata da hankali ashe." Baba Iro da Khalid suka shiga dakin a tare......Tace."Ibrahim matarka ta tunzura Sa'ida ta had'a kayanta ta gudu." Kawu Iro yace."Gwaggo wace irin magana ce wannan."? Fashewa tayi da kuka tace."Iro d'azu Rabi ta zauna ta 'karewa Sa'ida cin mutunci tana kiranta da Karuwa tsohuwar guzuma saboda kawai ina maganar auransu da Khalid shine fa ta fito tayi mata wannan cin mutuncin a cewarta wai d'anta ba zai auri lalatacciya ba wannan dalilin ya fusata zuciyarta ta had'a kayanta ta gudu." Baba Iro yayi shuru yana jimanta al'amarin! tace."Yanzu ni babban tashin hankalina da damuwa ta inda ta nufa a cikin daran nan." Yace."Gwaggo hakika raina ya 'baci da wannan al'amarin kuma duk irin hukuncin dana dauka akan Rabi kada kice don me ta riga ta gama fusata ni ace wai 'yar d'an uwana na jini take kira da Karuwa." Gwaggo tace."Ibrahim ba zan hana ka ka dauki mataki akan Rabi ba domin ko baka dauka ba ni zan dauka ba zata dinga la'antar zuria ta ba." Yana kokarin fita daga d'akin Khalid ya dafa kafad'arsa a tausashe yace."Baba kada ka yanke hukunci cikin fushi Annabi ya hana." Rai a 'bace! yace."Saboda mahaifiyarka ce ko? yanzu kai a tunaninka abinda ta aikata tayi daidai."? Kansa ya girgiza a sanyaye yace."Nima banji dadin al'amarin ba amma dan Allah kayi hakuri." Ba tare da yace masa komai ba ya bar gurun. Khalid dakin ya shiga jikinsa duk a mace babu shakka yasan wannan hargitsin dake faruwa shine sila da baya shiga sabgar auntyn nasa da mahaifiyartasa ba zata samu hanyar zaginta ba. Number ya nemo a wayarsa ya fara kira, Gwaggo tace."Yawwa dama yanzu zance ka kira ta a waya mu ta fad'a mana inda ta nufa duk da dai nasan watakila tana can gurin uwarta mai hure mata kunne." Jin wayar tana shiga yasa da sauri ya d'aga mata hannu. shuru tayi tana kallonsa, wayar ta 'karaci ringing ta katse bata dauka ba. Hannu na rawa ya sake kira nan ma babu amsa Khalid ya dinga kiran wayar tana katsewa ya kai sai goma, jiki a sanyaye ya kalleta da fad'in "Gwaggo aunty Sa'ida tayi zuciya taki daukar wayar." A sanyaye tace."Khalid dole tayi fushi! bayan fitarka Uwarka sata tayi a gaba taci mutuncinta ta dinga zaginta tana kiranta karuwa." Tana share hawaye take maganar ta cigaba da cewa"Wai yau zuria ta Rabi takewa wannan cin mutuncin." Yace."Gwaggo idan Ummatu tana da laifi kema kina dashi kada fa ki manta irin takura mata da kikeyi Gwaggo keda Ummatu kune kuka kori auntyna Sa'ida daga gidan nan." Shuru tayi tana share hawaye tace."Dan Allah sake kiran wayar ko zata dauka idan kuma bata daga ba ka kira wayar uwartata idan kana da number ta." Yace."Ni bani da Number Ummah Habiba amma bari na sake kira naji ko zata dauka...sake kiran wayar yayi har sau biyu babu amsa, ya sauke nannauyan ajiyar zuciya yana tunanin yanda za'ayi......."Khalid ka fito kaje gidansu abokinka ka kar'bo mukkulin adaidaita sahunsa ka kai ni babban gida.'' Muryar mahaifiyarsa ta katse masa tunani. Da sauri ya mike ya fita sai ya ganta a tsaye da hijabi a jikinta. agogon dake daure a hannunsa ya duba sha d'aya shaura yace."Ummatu me zakije kiyi a babban gida da daddare haka." hawaye ta share tace."Babanka ya kore ni a gidan wai naci mutuncin 'yar d'an uwansa har ta gudu sabida haka nima ba zan kwana a gidan ba.'' Khalid jikinsa yayi bala'in mutuwa da saurin ya jingina jikin bango (garu) Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un ya shiga kira yana jimanta masifar dake kokarin kunno musu....Gwaggo kuwa tana cikin dakinta a zaune tana jin duk abinda ke faruwa ko gezau ba tayi ba tana zaune babu abinda ya dameta. Yace."Ummatu ba zaki je ko'ina ba ina zuwa." da sauri ya nufi gurin nasu hankalinsa duk a tashe.....a kwance ya samu mahaifin nasa a tsakar gidan ya tsuguna gefansa hade da fad'in "Baba dan Allah kayi hakuri matakin daka dauka akan Ummatu bai dace ba." Hannu ya d'aga masa rai a 'bace yace."Khalid tashi ka bani guri bana bukarar jin wata magana daga gareka, Rabi ta kaini karshe kuma dama ba tun yau ba nasan da cewar bata kaunar yarinyar nan Sa'ida alhalin abinda yayi ubanta shi yayi ni mu biyu kacal iyayenmu suka haifa muka haifeku me zai sanya ta d'orawa yarinya karan tsana akan wane dalili? ita ko tausayin maraicinta ba tayi to shikkenan yanda tayi sanadin barinta gidan itama sai ta barshi idan kaga mahaifiyarka ta dawo gidan nan to ka tabbata cewa Sa'ida ce ta dawo." Khalid jikinsa yayi sanyi yace."To Baba dan Allah kayi hakuri dare ne yanzu ka bari da safe kome zai faru sai ya faru." cikin tsawa! yace." Khalid ba zaka tashi ka bani guri ba."? Mikewa yayi ya fita daga gurin ransa a tsananin 'bace...Babu Ummatu a gurin da sauri ya le'ka dakin Gwaggon yana tambayarta tace itama bata san inda take ba, fita yayi da saurin gaske. Can ya hangota tana tafiya yabi bayanta da sauri yana kiranta, tsayawa tayi ya karaso gurin yaga tana share hawaye yace."Ummatu kiyi hakuri dan Allah ki daina kukan nan bari na shiga gidansu Salim d'in na kar'bo key din." Kanta kawai ta d'aga masa zuciyarta na tafarfasa tunda tayi aure tsayin shekara ashirin da biyar wani sa'bani mai muni bai ta'ba shiga tsakaninta da mijinta ba, sai gashi yau akan Sa'ida yarinyar tayi sanadin da mijinta ya koreta daga gidan auranta. Khalid ya karaso gurin cikin adaidaita sahun a sanyaye ta shiga ta zauna yaja babur din suka tafi. Sai da suka hau titi sosai ta sauke ajiyar zuciya da fad'in "Khalid kaga irin tozarcin da mahaifinka yayi min akan Sa'ida ko."? Yace." Ummatu kiyi hakuri amma kema mai yasa kika zageta ki ka kuma yi mata kazafi na zina." Cikin 'bacin rai tace."Ai ba sharri nayi mata ba gaskiya na fad'a me yasa kun san gaskiya amma gabad'ayanku kuke kareta ni nasan Sa'ida mazinaciya ce." Yaji kansa ya sara! gumi na yanko masa yace." Ummatu zuciya takan dauki zafi a duk lokacin da zaki jefi Auntyn Sa'ida da wannan kalmar wallahi ita d'in kamila ce bata bin mazan banza a waje." Tace."To shikkenan tunda kana jin zafi sai ka dauki mataki a kaina kamar yanda ubanka ya dauka wallahi Khalid mutukar ni na haifeka to ba zaka auri Sa'ida ba dan duk na gane take-taken ka." Shuru yayi wani irin gumi! yana tsatstsafo masa . Tace."Idan ka bijirewa umarnina ka auri yarinyar sai nayi maka baki ka lalace gwara tun wuri ka cireta daga cikin zuciyarka." Murya na rawa yace."Ummatu me yasa kike wannan maganar me yasa kika dauki zafi da al'amarin nan kada kiyi min haka dan Allah aunty Sa'ida itace farin cikina." Tace"Humm! dama abinda nake so na gazgata kena gashinan kuma ka furta da bakin ka saboda haka daga yau sai yau na rabaka da yarinyar nan wallahi tallahi ka sakeyi mata magana Allah ya isa."! Ji yayi kansa yana juyowa kan babur din na nema ya kufce daga hannunsa da kyar ya aro dauriya yasa a ransa ya cigaba da driving din yana nanata kalmar innalillahi wa'ina ilaihi raji'un.! "Hakika Sa'ida banji dad'in wannan abubuwan da suke faruwa da rayuwarki ba amma kuma bai kamata ki yanke wannan hukuncin ba dalili kuwa shine kin san halin Gwaggo baud'ad'd'iyar macace zata iya zargina kan cewa ni nake zugaki ki bijire musu." Ajiyar zuciya na sauke a raunane nace"Umma wallahi hakuri na ya 'kare a gidan nan dan saboda bana so watarana su tunzura zuciyata na fad'a musu magana mara dad'i shiyasa kawai na yanke wannan hukuncin." Girgixa kanta tayi tace."To shikkenan ai Allah yasa hakan shi yafi alkairi bari da safe sai na shedawa Alhaji halin da ake ciki idan yaso duk hukuncin da ya yanke miki sai kiyi hakuri dashi." A sanyaye Nace."Tom shikkenan Umma Allah ya kaimu lafiya." kallona tayi cikin tausayawa tace."Naga duk kin rame ko duk fargabar ce."? Murmushin takaici nayi nace."Umma zama da Gwaggo da Ummatu ai sai jarumi mai kuma hakuri sosai suke takurawa rayuwata." Murmushi tayi tace."Ba tun yau ba na san halin Gwaggo macace wata iri wacce baka gane gabanta da bayanta haka nima nai hakurin zama da ita Ummatu kuwa dama can ba muyi wani zaman arziki da ita ba." Nace."Hakane Umma tace." to saboda haka sai kiyi hakuri ki cire damuwa daga cikin ranki ki fuskanci abinda yake gabanki aure idan Allah ya kawo lokacinsa babu wanda ya isa ya hana." Nace."Kwarai kuwa hakane." Ta kalli kwanukan abincin dake gabana a nutse tace."Da alama ba ki bude abincin nan ba."? Nace."Eh ban ci ba tukunna." Tace."To ni zan shige na tafi dakin Alhaji sai ki nutsu kici abincin ki kwanta." nace."Tom shikkenan Umma sai da safe." Ta mike a nutse ta fita daga dakin, cikin nutsuwa na bud'e kwanukan abincin towon farar shinkafa ne da miyar taushe taji gyada sai kamshi take.....dama tsabar fargaba da tashin hankali bata bari naci wani abincin kirki ba saboda haka lokaci guda yunwa ta taso min nasa towon a plate na zuba miya akai a nutse na fara ci ina tunanin halin da Gwaggo zata shiga idan ta farka daga bacci taga bana nan..... *Masoya a taimaka da sharing👏🏼🥰* *IDAN KINA BUKATAR BIYAN KUDIN LITTAFIN GA YANDA ABIN YAKE....VIP GRUOP#600 NORMAL GROUP #300 ACCOUNT... 0542382124.....BINTA UMAR GTBANK...IDAN KATI ZAKI TURO #400 SAI KIYI MIN MAGANA TA WHATSAPP DA WANNAN NUMBER.* *07084653262* *08089965176* *BINTA UMAR ABBALE* [3/6, 8:46 AM] 💜: *GA IRINTA NAN!!!🙆🏼‍♀️* _(LOVE STORY🌺)_ *NA* _BINTU UMAR ABBALE🍒_ *MANAZARTA WRITES ASSO🖊️📚* *11* Ina zaune da plate din indomee a gabana ya shigo gidan, kallo guda nayi masa na kauda kaina, gani nayi ya tsaya yana kallon kayan wanki na dana jibge a bakin rijiya, minti biyu ya wuce daga gurin..... mikewa na share tsakar gidan sannan na shiga dakin na harhad'o kayan wanke-wanke na fito dashi bakin rija. d'akin na koma na sameta ta fara kad'in lagwani nace." Gwaggo zan fara wanki inaso na share miki dakin." Tace."Kije kiyi wankin ki idan na tashi na share." Ba tare da nace mata komai ba na fita daga dakin, samun sa nayi zaune a bakin rijiya daga shi sai gajeran wando yana wanke kayan ball d'insa. Tsigar jikina ta tashi na tsani na ganshi babu suttura a jikinsa nakan ji wani irin yanayi a tare dani, kamar na koma d'aki na zauna idan ya gama abinda yake nazo nayi wankin, sai dai na daure kawai naja bokiti da ruwa a ciki na zuba omo na sunkuya na fara cud'a wankin....Shuru gurin yayi yana ta cud'a kayansa nima ina cud'a nawa. Sunkuyo na d'an gyara karaf! na kama shi yana satar kallon kirjina. cikin dubara na duba sai naga ashe gurin sunkuyo din wuyan rigata ya zame gabad'aya breast dina ana ganinsu. Girgiza kaina kawai nayi na mi'ke. kujera 'yar tsuguno naje na dauko na zauna akai na cigaba da abinda nake........ Hannunsa ya mi'ka ya d'auki briziyata yasa a cikin ruwan omon dake gabansa ya fara cud'awa. Rai a 'bace! na kalleshi da fad'in "Ranka zai 'baci idan baka mi'ko min rigar nan ba." Uffan bai ce min ba ya cigaba da cud'a breziyar yana gyarata, Nace."Khalid ko bakyaji abinda nace ba."? Babu walwala a tare dashi yace."Naji ashe akwai sauran wani abu da zakiyi min bayan wanda kikayi min d'azu." A zafafe! Nace."Nayi maka d'in ai kai ka janyo meye ruwanka da wayata ko kuma Alhaji Nuran sa'anka ne wallahi ka nutsu ka shiga hankalinka idan ba hakaba kana tare da 'bacin rai." Cike da nuna rashin damuwa yace."Mutukar akanki ne a shirye nake da kowane irin 'bacin rai kuma wallahi sai inda karfina ya 'kare zaki gane baki da wayo." Da sauri nace." Ni kake fad'awa wannan maganar."? Shiru yayi ya cigaba da abinda yake a fusace! na kai hannu zan fuzge rigar ya murd'e min hannu har sai da yayi 'kas! cike da mamaki nake kallonsa! Yace."Ki kyaleni na cigaba da wankewa hakan na rage min rad'ad'i! Gabana ya fad'i! wanke breziyya har wani jin dad'i ne lallai Khalid fitinanne ne........Kallona yayi da wani munafikin murmushi a fuskarsa yace."Naga kamar ma tayi miki kad'an idan na tashi had'a miki lefe wacce ta fita girma zan sa miki." Naji wani irin takaici ya rufe ni wai ni ya zanyi da yaron nan ne? shamtarsa nayi na zubar da ruwan oman dake gabansa. Sai yayi murmushi ya cire breziyar a cikin bokitin kawai naga yana marmatsa 'ko'konta kamar yana ta'ba nono sai lumshe ido yake yana cizar lips d'insa....Ruwan Oman dake gabana na d'aga na kwara masa a jikinsa, hakan yayi daidai da fitowar Ummatu daga gurinta, ya mi'ke tsaye da breziyyar a hannunsa.....Ganin mahaifiyarsa yasa yayi saurin mayar da fuskarsa ta salihai "Aunty Sa'ida me nai miki kika watsa min ruwan wanki." Shuru nayi jikina yayi sanyi da irin kallon banzan da mahaifiyarsa keyi min....ta kalleshi rai a 'bace tace."Khalid meye wannan a hannunka."? da sauri ya kalli hannunsa sai kuma ya jefo min breziyyar da fad'in."Ummatu ban san na rike ba mybe a cikin ruwan wanki data watsa min ta had'o da ita." Ta kalleni da rai a 'bace "Sa'ida wane tsabar rashin mutunci ne wannan? me yayi miki dan wulakanci zaki watsa masa ruwan wanki a jiki." Shuru nai mata ba wai dan bani da amsar da zan bata ba sai dan sanin da nayi cewa duk abinda zan fad'a mata yayi min ba yarda za tayi ba. Gwaggo ta fito daga dakin tana fad'in "Me kuma yake faruwa nake jin hayaniya."? Ummatu da sauri tace." Gwaggo duba jikin Khalid ki gani sabida tsabar ita ta cika ishashshiya ta dauki ruwan wankinta ta watsa masa a jikinsa. Gwaggo da sauri ta kalli Khalid jikinsa jagab! da ruwan daud'a! cike da mamaki! tace."Jarumi me ya had'a ku nasan dai ruwa baya tsami banza."? Girgiza kansa yayi yace.''Gwaggo daka kawai zan taimaka mata da wanki shine tayi min wannan wulakancin.'' Tace."Haba Sa'ida me yasa kika aikata haka."? Rai a 'bace na d'ago ina kallonsu nace." Lokacib dana fito da wanki na bance kowa ya taimaka min ba akan me zai zo yasa min hannu sai kace sa'arsa dan wulakaci ya d'auki breziyata yace zai wanke." Gwaggo ta ri'ke bakinta tana yi masa wani irin kallo mai kama da harara.....Ummatu tace"Ke Sa'ida kada kiyi masa sharri yaushe ya dauki rigar nonan naki bayan ke kika watsa masa ruwan daud'a da ita a ciki." Nace."Ummatu kenan ba sharri nai masa ba da idonki fa kin gani amma zaki ce nai masa sharri." Gwaggo tace."To duk dai magana ta wuce kada a 'kara tayar da ita kai kuma Khalid babu ruwanka da ita." Yace."Yanzu ke Gwaggo kin yarda zan aikata hakan? okey idan ma breziyar ta na d'auka domin na wanke mata meye a ciki? ai ba k'irjinta na ta'ba ba ballantana tayi min sharri ." Gwaggo tace."Aikuwa dai babu laifi a ciki tunda tace bata so sai ka kyaleta. Tsaki yaja ya bar gurin yana fad'in "Daga Abin alkairi sharri ya biyo baya wataran ma cewa zakiyi na turmushe ki." Ummatu tayi saurin fad'in "Allah ya kiyaye." Bayansa tabi tana surutai itama Gwaggo dakinta ta koma ta cigaba da abinda take. Tana zaune a d'an tsakar gidanta ya fito daga dakinsa cikin shirin fita yayi gayu cikin 'kananun kaya sai kamshin turare yake, Khalid akwai tsabta da kwalisa kayansa kullum a goge gashi bai yarda da fesa turare me arha ba. "Khalid zo nan ina so nai magana da kai." A nutse yaje ya samu gefanta ya zauna. tace." Kana jina ko."? yace."Eh Umma ina jinki." Tace."Ni ba zan raba ka da 'yar uwarka Sa'ida ba amma inaso kayi nesa da ita dan gabad'aya ni yarinyar bata kwanta min a raina ba ina jin tsoro taje tayi lalata a waje ta laqaba maka sharri ka daina shiga sabgarta." A sanyaye yace."Ummatu me yasa kike mata irin wannan zargin." ? Tace."Kai Khalid yaro ne kai baka san me duniya take ciki ba gabad'aya jama'ar gari kallon lalatacciya suke mata dan ni akwai wacce ta kawo min magana kancewa babu irin lalatar da ba tayi da maza a gurin aikinta wannan dalilin yasa nace kayi nesa da ita bana so taje tayo cikin shege ta d'ora maka." Cike da mamaki! yake kallonta kafin yace."Ummatu amma banji dadin wannan magana ba dan Allah ki daina yarda da surutan mutane bana tsammanin Aunty Sa'ida zata zubar da martabar gidan nan." Tace."Oho! dai Sa'ida tana bin maza bata bin maza ni dai nace ka rabu da ita dan naga kaima tana so taja hankali ka gashinan baka san laifinta.'' Shuru yayi yana girgiza kansa! Tace."Yaushe ne zaku koma makaranta."? Yace."Ai kin san da tuni mun koma wannan yajin aikin da aka tafi ne ya janyo amma naji gwamnati tayi magana cewa kowane dalibi ya koma makaranta ranar mondy." Tace."Jibi kenan zaka tafi."? Yace."Eh insha Allahu." Tace."To shikkenan kafin ka tafi kaje can babban gida ka gaishe su." Yana kokarin mi'kewa yace "To insha Allahu zanje." 'Kamshin turaransa ne yasa nayi saurin juyowa muka had'a ido dashi, saurin dauke kaina nayi ina mamakin a'inda ya samu kudi ya siyi turare mai tsada irin wannan nafi jin 'kamshinsa a jikin Alhaji Nura. Cigaba da shanya kayana nayi har ya fice daga gidan sai kawai na tsinci kaina da bin bayansa da kallo gaskiya dressing din yayi masa kyau sosai. kawar da tunaninsa nayi daga cikin raina na cigaba da abinda yake gabana. Ina tsaka da share inda nayi wanki yaro ya shigo."Wai Salisu mai kanti yace a bashi lagwanin." Nace."Shiga dakin ka fad'a mata. muryarta naji tana fad'in "Bama sai ya shigo ba naji bari na kawo maka ka kai masa." Yaron yace."To gwaggo." ta fito hannunta rike da leda viva ta mika masa da fadin"Kace dan Allah yayi hakuri banyi masa akan lokaci ba." Yace."To Gwaggo zan fada masa." Fita yaron yayi ta kalleni da fadin"Sa'ida yau sha'awar sakwara nake ko zakiyi mana da ragowar doyar can." Nace."Banda kudi da zan sarrafa.'' Tace." 'Dari biyu zata isa ayi miyar."? Kaina na girgiza mata alamun ba zata isa ba, tace."Aikuwa dari biyu zan iya bayarwa ayi cefane." tafada tana kokarin shiga daki sallamar Almajirin gidan Alhaji Nura ta dakatar da ita. Washe bakinta tayi tana kallonsa ya 'karaso inda nake hannunsa ri'ke da ledoji yace."Aunty Sa'ida ina wuni."? na amsa ina kokarin wanke hannuna yace."Daga kasuwa nake Alhaji yace na kawo miki wannan." Hannu nasa na kar'bi ledojin da fadin."To Rabi'u kace masa nagode sosai." Ya amsa da ameen tare da juyawa Gwaggo tace." Rabi'u babu gaisuwa ka shigo kawai ka wuce gurin uwar dakinka."Murmushi yayi yana kallonta yace."Gwaggo Dan Allah kiyi hakuri wallahi hankalina ne yayi gaba ina fatan kin wuni lafiya."? Tace."Lafiya lau Rabi'u ya Alhajin ina fata dai lafiya dan Allah kace masa muna godiya da hidima." Rabi'u yace."Insha Allah zan fad'a masa." Yana fita ta karaso inda nake tana fad'in "Kai amma naji dad'in wannan aiken wallahi nasan harda nama da kayan miya a ciki kinga na huta 'batar da kudina. A nutse nace." Gwaggo wai dan Allah me yasa kike da san abin duniya ne inace d'azu kika gama zagin mutumin nan amma yanzu kinga kayansa duk kin gigice." "Sa'ida kada ki fad'a min magana mana kin san dai ba zan bar nawa na na za'be shi ba, ni nafi kaunar ki auri Khalid amma da babu maganarsa a tsakani zan baki goyan baya d'ari bisa d'ari ki auri Alhaji Nura domin ya cancanta.'' Nace."Wallahi har mamaki kike bani idan naji kina cewa wai na auri Khalid gwaggo kina tunanin ko maza sun'kare a duniya zan auri wannan yaron........"Shima ba zai aureki ba tsohuwar guzama dake." Muryar Ummatu ce ta katse maganar da nake. duk muka juya muna kallonta....Fuska a murtuke ta karaso inda muke tsaye tace."Sa'ida ke har wata cikakkiya ce da har zaki dinga k'yamatar auran Khalid me kike dashi na matantaka bayan duk kin gama rabawa abokanan aikin ki maza." Gwaggo tace."Rabi wannan wace irin banzar magana ce."? Da sauri tace."Gwaggo ranar wanka fa ba'a 'boyan cibi ke kin sani kuma kin fad'a da bakinki hakanan kuma jama'ar gari sun sani Sa'ida bata da kamun kai to me zai sanya kice lallai sai Khalid ya aureta." Rai a 'bace Gwaggo tace."Rabi kada ki 'kara yi mata 'kazafi ni kaf zuriyata babu lalatacce idan Allah ya kaddara auran Sa'ida da Khalid babu yanda zakiyi sai hakuri." Murmushi takaici tayi tace."Gwaggo sai dai kuwa idan bani na haifi Khalid ba." Tana gama maganarta ta bar gurin tana wani irin huci! Ido jawur! na kalleta nace."Kinga abinda kika janyo min ko."? ''Kinga Sa'ida rabu da Rabi bata da cikakken hankali kuma wallahi sai na fad'awa Ibrahim ayi muku tsakani da ita kada ta 'kara jifanki da mummunar kalma." Nace.''Gwaggo da Ummatu ba taji kina fad'a min haka ba to ba zata fad'a ba tun farko ke kika nuna kina zargina da iskanci a gurinki taji gashinan kin janyo min cin mutumci." Tace."Kiyi hakuri na fad'a miki zan had'ata da Ibrahim zata gane bata da wayo." nace"Gwaggo kada ki had'ata da mijinta a kaina ki kyaleta kawai ni zan yanke hukunci da zakuyi farin ciki." Tace."Sa'ida wane irin hukunci zaki yanke."? Murmushin takaici nayi nace."Idan na yanke zaki gani." barin gurin nayi naje ina duba abinda yake cikin ledojin .....kayan tea ne komai da komai sai uban kayan miya da nama mai yawan gaske a cikin wata katuwar takarda. Kallonta nayi nace.'' Kinga nayi wanki na gaji ba zan iya dukan sakwara ba zan dafa miki ita kawai kici da miya." Tace."To shikkenan had'a kayan miyan ni da kaina sai na miqa markad'an gidan Lubabatu." Mi'kewa nayi na dauko d'an maidaidaicin baho da wuka na zauna ina gyara kayan miya ta nufi daki tana fadin" bari na 'karasa d'an abinda nake kafin ki gama." To duk k'ulafucin Gwaggo ba taci doyar da yawa ba duka -duka uku taci ta ajiye wa mutumin nata miya cikin silba duk ta kwashe masa naman 'kyaleta kawai nayi domin ni nasan abinda na shirya mata. Ganin tana gyangyad'i nace."Gwaggo ki gyara kwanciyarki mana." Da sauri ta bude ido tana kallona tace."Ina jiran Ibrahim ya shigo ne shiyasa ki kaga bankwanta." Nace."Gwaggo Ummatu ni ta ciwa fuska kuma gani tayi ki nayi min saboda haka dan Allah kada kice zaki fad'awa mijinta ki had'asu." Ta'be bakinta tayi tace."Ai sai kiyi Sa'ida Sai fa na fad'a masa fa Ummatu zata san da ni take zancan." Shuru nai ina kallonta.........ta cigaba da gyangyadin tana nema ta tintsira nace."To ki kwanta idan ya shigo zan tashe ki." Ajiyar zuciya ta sauke tace."To mi'ko min fillo na d'an matse." da sauri na mi'ka mata ta kwanta tana kiran sunan Allah. Shuru dakin yayi na tsayin minti goma sha biyar na tabbatar tayi bacci na mike a tsanake nasa hijabina jakar dana san na had'a dukkanin kayana na dauka a hankali na fita daga d'akin.......Kai tsaye babban titi na nufa ina addua a kan Allah yasa ina fita na samu adaidaita sahun da zai kaini hotoro gidan Mahaifiyata...... *Masoya a taimaka da Sharing👏🏼* *IDAN KINA BUKATAR BIYAN KUDIN LITTAFIN GA YANDA ABIN YAKE....VIP GRUOP#600 NORMAL GRUOP#300.....ACCOUNT...0542382124.....BINTA UMAR GTBANK...IDAN KATI ZAKI TURO #400 NE SAI KIYI MIN MAGANA TA WHATSAPP DA WANNAN NUMBER.* *07084653262* *08089967176* *BINTA UMAR ABBALE* [3/6, 8:46 AM] 💜: *GA IRINTA NAN!!!🙆🏼‍♀️* _(LOVE STORY🌺)_ *NA* _BINTU UMAR ABBALE🍒_ *MANAZARTA WRITES ASSO🖊️📚* *SADAUKARWA NE GA IYAYE NA GUDA BIYU* *FATIMA MUSA (MOMY NIJAR)* *TARE DA* *USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)* *(HAJIYA BABBAH)* _*Ina kaunar ku iyayena ina kuma alfahari da irin kaunar da kuke nuna min💜🥰*_ *13* A daran ranar Gwaggo kasa rintsawa tayi asubar fari ta tashi tai alwala tayi sallah da carbi a hannunta ta fito kai tsaye gurin baba iro ta nufa ta shiga bubbuga musu kofa. Lokacin shi yana massalaci bai shigo ba, bugun kofar da take ya tashi khalid a firgice ya mike zaune dama shima sai dab da asubah baccin ya daukeshi agogon da yake kafe a bangon dakin ya kalla shida da rabi da sauri ya dauki brush dinsa ya fito.....kallo ta bishi dashi da fadin."Kada dai kace sai yanzu ka tashi."? kansa ya daga mata ya ratseta ya wuce bayansa tabi da kallo kafin tace."Khalid me yasa kake wasa da sallah ne."? ba tare da ya tanka mata ba ya dauki buta ya shiga bandaki, sai itama ta bar gurin ta nufi dakinta ta zauna cikin alhini da damuwa. Baba Iro ne ya shigo dakin da carbi a hannunsa suka gaisa yace."Gwaggo ya kike ganin za'ayi ne."? Tace."Ibrahim ni da kaina zani gidan Alhaji Shamsun dan bana tantama can ta nufa kome suke ji dashi na rantse ni nafi karfinsu Sa'ida ikona ce dan haka tilas ta dawo gabana ta cigaba da zama." Yace."Gwaggo kada ki fusata komai cikin nutsuwa za'ayi Alhaji Shamsu babban mutum ne mai mutunci bai kamata kije har gidansa gaban iyalinsa kici masa mutunci ba." "Ibrahim bafa zan zauna nayi lako-lako ba wato ka manta irin d'auki ba dad'in da mukayi dasu a wacan karon ko wane irin abune baiyi ba akan lallai Sai Sa'ida ta zauna a hannunsa to wannan karon ma ko yafi 'kuda naci ba zata zauna a gidansa ba domin bamu gaza dayi mata komai ba." Baba Iro yayi shuru yana mamakin halin mahaifiyarsa yasan halinta da rashin tsinkaye da hangen nesa zata iya zuwa gidan mutum gaban iyalinsa ta tsinka shi wannan dalilin yasa yayi wani tunani....."Gwaggo ki nutsu ki kwantar da hankalin ki insha Allahu Sa'ida zata dawo gida da kaina nake so naje gidan mu tattauna da Alhajin yana ganin mutuncina sosai itama Sa'idar haka da yardar Allah tare da ita zan dawo gida." "Aa Iro gwara mu tafi tare ayi komai a gabana wallahi nake fada maka jiya kewarta hana ni rintsawa tayi.'' Yace." Ai bake kad'ai ba Gwaggo ni kaina banyi bacci ba amma insha Allah komai zai zo da sauki kiyi hakuri naje ni kad'ai din." Shuru tayi alamar bata gamsu da maganarsa ba...Khalid ya shigo dakin suka gaisa da mahaifin nasa tace."Khalid kaje ka aro adaidaita sahun abokin ka kazo ka dauke ni ka kai ni gidan Alhaji Shamsu." Babu walwala a fuskarsa yace."Me zakije kiyi."? da sauri tace."Zanje na dauko Sa'ida ne." Yace."Gwaggo babu inda zakije aunty Sa'ida zata dawo da kafafunta bayan haka kuma shi wanda zai bani aron adaidaita sahun nasa ya fita aiki da ita saboda haka ki zauna a gida zamuje nida Baba." Da sauri tace."Zakuwa ku gan ni a gidan domin kuwa Allah ya hore min kudin mota.'' Baba Iro cikin rarrashi yace."Gwaggo abinda nutsuwa bata bayar ba to tashin hankali ma ba zai bayar dashi ba dan Allah ki nutsu kada kizo ki aikata abu daga baya kizo kina jin kunya Alhaji Shamsu bai cancanci tozarci a gurin mu ba yana kuma da ikon ri'ke Sa'ida a hannunsa tunda yana matsayin mijin mahaifiyarta. Tace."Ai kaji abinda nake gudu dama nasan ko kaje ba wani mataki zaka dauka ba karshe ma ka dawo gida kai kadai ba tare da ita ba to sai naje na fada maka." Khalid yace."To kije d'in kina shiga gate din zan sa masu gadi su saki karnuka kin san zan iya ko." shuru tayi tana kallonsa, Yace."An fada miki cewa komai a hankali da nutsuwa ake binsa amma kin kasa ganewa." tasa kuka da fad'in "Khalid bana son Sa'ida tayi nesa dani shiyasa kaga duk hankalina ya tashi bana so wannan karon Alhaji Shamsu ya samu galaba akan mu." Yace."Ba zai samu ba insha Allahu." hawaye ta share tace."Khalid shiyasa nake so ka aureta na dinga ganinku a gabana inaso ku haifa min zuria mai yawa." Tausayi ta bashi yace."To Allah ya amsa adduarki ina fata dai yanzu kin janye maganarki ta zuwa gidan." Tace."Tunda kunfi karfina na hakura ina zuba ido kuje ku dauko min ita." Baba Iro yace."To Alhamdulillahi bari na kimtsa na fito, yana kokarin fita ta kira sunansa, juyowa yayi yana kallonta tace."Maganar Rabi baka ce min komai ba." Yace."Tun jiya tana gidansu ai." girgiza kanta tayi tace."To wannan hukuncin daka yanke ni yayi min daidai na kuma ji dadi gobe ma sai ta sake aikatawa amma inaso yau idan Sa'ida ta dawo gida kaje kayo bikon matarka." Yace."To Gwaggo yanda kika ce hakan za'ayi.'' ya juya da niyar fita sai ya tsaya da fad'in ."Me zaki karya dashi na aika a siyo miki." Tace."Ibrahim ba sai kayi asarar kudin ka ba ina da d'umame gashi can a jibge yanzu zan d'umama kafin ku tafi sai kuci." Yace."To shikkenan Gwaggo." Bayan fitarsa daga dakin sai ta fara janyo kwanukan abincin tana dubawa doyar babu abinda tayi sannan itama farar shinkafar da Ummatu ta dafa a daran ranar ba tayi komai ba ta mike ta fita da kwanukan abincin a hannunta tana fad'in "Ruwan zafi kawai zan sa na turara shinkafar tunda da abincin ai ba sai anyi hidimar siyan wani abu ba." Tsaf ta gyara abincin ya dawo tamkar sabo ta dauko ta kawo daki....cikin plate ta zuba masa ta zuba masa miyar nama da yawa.....yace." Gwaggo a'ina kuka samu nama haka."? Tace."Kasan duk sati Alhaji Nura yakan kawo mana cefane to jiya da ya kawo sai Sa'ida tayi mana miya harda kayan shayi ma watakila ta tafi da abunta." 'Bata fuska yayi yace."Gwaggo nayi sha'awar abinci amma ba zanci ba." tace."Sabida me Khalid."? Hankalinsa nakan wayarsa yace."Saboda ina kishin mutumin na tsaneshi wallahi." Tace."Khalid ka kwantar da hankalinka kai zaka auri Sa'ida Alhaji Nura kuwa shi yaga zai iya wahalar da kansa mu dai duk abinda ya kawo hannu biyu zamu sa mu 'karba. Yace."Gwaggo idan kina bukatar farin ciki na to ki daina cin abinda mutumin zai kawo wa aunty Sa'ida wannan shine abinda nake bukata dake." Shuru tayi tana girgiza kanta bata tsammanin zata daina cin kayan dad'in da Alhaji Nura zai kawo musu amma saboda ta kwantar masa da hankali tace."To shikkenan tunda baka so na daina." Mikewa yayi zai fita tace."Yanzu Khalid kana kallon abinci da kyau amma kace ba zaka ci ba." Girgiza kansa yayi yana ta'be bakinsa yasa takalmansa ya fita..........Baba Iro ya shiga dakin cikin shiri yace."Ina Khalid din." tana tsotse 'kashin hannunta tace." Wata'kila ya tafi gurin mai shayi.'' da mamaki a tare dashi yace."Wannan abincin fa."? Tace."Ibrahim kasan Khalid da zuciya da kishin kansa wai ba zai ci ba saboda yana kishi da wanda ya kawo cefanan." Baba Iro ya zauna kusa da ita yana girgiza kansa mamaki yake sosai akan irin tarangahumar d'an nasa in banda abinsa inashi ina Sa'ida ko da yake Namiji komai 'kan'kantarsa mutukar ya balaga to mace duk girma da shekarunta bata gagararsa.....Gwaggo ta zuba masa abincin tasa masa miya da uban nama akai." Yace."Gwaggo ki rage naman." Tace."Ibrahim kaci ka 'koshi ka barshi.'' Bisimillah yayi ya fara cin abincin. dakin yayi shuru na tsayin minti biyar yace."Gwaggo ya kamata mu samu zama da mutumin nan idan da gaske yake akan yarinyar nan ya fito ayi abinda za'ayi." Da sauri tace."Ko da gaske yake ba zamu bashi Sa'ida ba tunda Khalid ya nuna yana so hausawa na cewa gida bai koshi ba ba za'a kai dawa ba." Yace."Gwaggo duk da Sa'ida budurwa ce to bai cancanci ayi mata dole ba shin da bakinta kinji ta furta tana san auran Khalid."? Girgiza kanta tayi tace."Aa bata furta ba asali ma kullum cikin fad'a da juna suke sam basa jituwa dalilin ma kenan da yasa naje na kar'bo taimaiko gurin mai magani Ibrahim yarinyar nan Sa'ida na tare da iskokai kaga kuwa idan ba na gida ne ya aureta ba to babu shakka akwai matsala shiyasa kaga sam! bana sha'awar wani na waje ya aure ta." Baba Iro shuru kawai yayi ya cigaba da cin abincinsa, shi kam ba zai iya da rigimar mahaifiyarsa ba mutukar shine madaurin auran Sa'ida to ba zai daura mata aure da wanda bata so ba. To Cikin nutsuwar zuciya na wayi gari a gidan mahaifiyata, sai da nayi wanka tsaf na shirya jikina sannan ta shigo dakin fuska a sake tace."Sa'ida kinji shuru ko." Murmushi kawai nayi nace."Umma ai nasan inda kike ina fata kin tashi lafiya."? Tace."Lafiya kalau alhamdulillahi Jiya duk na shedawa Alhaji abinda yake faruwa shima al'amarin bai masa dadi ba ko kad'an dan haka ya yanke hukuncin kan cewa ko zaki koma can gidan sai kin kwana biyu anan kin samu nutsuwa tukkuna." Ajiyar zuciya na sauke cikin zuciyata ina jin dadin hukuncin da ya yanke. tace."Ki tashi kije ku gaisa dan fita zaiyi bayan kin fito daga dakin nasa sai ki shiga dakin matan gidan ku gaisa.'' Nace."To shikkenan Umma." hanyar fita ta nufa da fad'in "Bari na shiga kicin na taimakawa Asabe da aiki kada ya yara su makara a makaranta." Nace."Umma ai yau Lahadi babu skull.'' tace."Ai yaran gidan nan suna zuwa islamiyya tahafiz in suka tafi sai yamma suke dawowa." Bayanta nabi da fad'in "To bari nima nazo ayi aikin dani." Mirmushi tayi ba tare data ce komai ba ta nufi hanyar babban kicin din nasu dake tsakar gidan. A nutse nayi sallama cikin dakin nasa......Ya amsa min tare da kiran sunana." Na karasa cikin dakin sosai ina amsawa har 'kasa na tsuguna na gaishe shi. Ya amsa cikin sakin fuska da kulawa ya d'ora da fad'in "Sa'ida jiya mahaifiyarki duk tayi min bayanin abinda ke faruwa da rayuwarki naji rashin dad'i sosai kuma raina ya 'baci dalilin da yasa ma kenan na yanke hukuncin kan cewa ko zaki koma can gidan to ba yanzu ba sai kin samu nutsuwa saboda haka ina so ki kwantar da hankalinki ki cire duk wata damuwa dake ranki insha Allahu Allah zai kawo miki miji nagari ki aure." Cikin rauni gami da tausayin kaina nace"Nagode Alhaji insha Allahu kuma zan cire al'amarin daga cikin raina." Yace."To Alhamdulillahi ya aikin ki ina fatan komai lafiya."? nace."Alhamdulillahi komai lafiya Alhaji."' Yace."To masha Allah Allah ya taimaka." Na amsa da ameeen tare da kokarin mikewa yace."Kyace ina kiran mahaifiyar taki." Nace."Tom zan fada mata yanzu. Ina fita na nufi kicin din na sheda mata kiran da yake mata, cikin sakin fuska muka gaisa da mai aikinsu Asabe har tana tambayata yaushe nazo. nace "Shigowar dare nayi shiyasa ba kowane yasan da zuwana ba." Sai bayan mun kammala aikin ne na samu nutsuwar shiga d'akunan abokan zaman nata muka gaisa dasu cikin mutunci da girmamawa Famliy d'in Alhaji Shamsu suna da kirki sosai Mussaman Babban d'ansa Mai suna Aminu mun saba dashi sosai yana da kirki da saukin kai kud'in sa sam bai rufe masa ido ba babbar matsalar Yaya Aminu rashin aure anyi anyi dashi yayi aure ya'ki ga uban kudi da yake samu dan kasuwa ta nayi dashi sosai yake fita 'kasashe ya shigo da kaya amma duk kudinsa da tsayin shekarunsa bashi da mace... mahaifiyarsa har magunguna take 'karbo masa cikin dubara take bashi a ganinta ko bashi da lafiya shiyasa baya sha'awar auran shi kuwa ba tare da yasan maganin menene ba zai kar'ba yasha tunda yasan mahaifiyarsa ce ba zata cutar dashi ba. To Alhaji Shamsu na fita da kamar minti ashirin su Khalid suka isa gidan.....su gaisa da maigadi cikin mutunci Baba Iro yace "Munzo gurin maigidan ne." Maigadi yace."Ayya wallahi kun doki gurbi Alhajin bai jima da fita ba sai dai idan kasuwa zaku bishi." Gabad'ayansu jikinsu yayi sanyi....Baba Iro yace."Babu damuwa insha Allahu zamu dawo da daddare ko kuma gobe da safe idan yaso idan ya dawo sai ka sheda masa zuwanmu." Maigadi yace."To shikkenan babu damuwa wane suna za'a fad'a masa."? Yace."Kace masa Ibrahim ne Kawun Sa'ida daga Mandawari." Yace."To shikkenan za'a fada masa insha Allah." Sallama sukayi da juna Maigadin ya rufe gate din....Khalid a sanyaye yace."Baba mai zai hana mu bishi kasuwar.''? Baba Iro ya girgiza kansa da Fad'in "Khalid al'amarin yana bukatar sirri bai kamata mu bishi gurin sana'arsa ba tunda dai maigadinsa yasan da zuwanmu nasan idan ya dawo zai fada masa." Jiki a mace yace."Hakane." Adaidaita sahu suka shiga Baba iro yace."Ni Kasuwa zan wuce yanzu yana da kyau kazo muje ." Jim! yayi yana nazari kafin yace."Baba kasan gobe zan koma skull so inaso na koma gida nayi shirye-shirye." Yace."To shikkenan Khalid idan ka koma gida ka taushi zuciyar Gwaggo nasan dai yau akwai rigima a gidan amma kai tunda taku tazo da d'aya ka rarrasheta kafin na dawo." Yace."To shikkenan Baba." Direban yace." Ina zan kaiku ne naga kamar tafiyar taku ta bambamta." Khalid yace." Kasuwar sabon gari zaka kaishi ni kuma Mandawari." Direban yace."Ai hanyar ta baud'e ni yanzu kai tsaye Sabon gari na nufa." Yace."Okey to sauke ni na samu wata." ya tsayar da babur din ya fito hannu yasa a aljihu ya dauko kudi ya mik'a masa......Baba Iro yace."Kana da kudi wadatacce a jikinka ne."? Yace."Eh baba kada ka damu Kuje kawai Allah ya kiyaye." Direban yayi saurin sa kudin cikin d'an bankin dake gaban babur din yaja da sauri suka bar gurin. Ajiyar zuciya ya sauke bayan barin su a gurin ya tari wani babur din gidan Alhaji Shamsun zai koma. Maigadi ya bude karamar kofa yana tambayar waye ganin Khalid yasa yace ''Ka dawo kenan."? Khalid yace."Inaso zanyi magana ne da Auntyna Sa'ida." Jim! yayi kafin yace."Khalid kayi hakuri da abinda zan fada maka Alhaji ya hana kowane namiji shiga cikin gidansa ko masu yi musu hidima iyakar su bakin gate saboda haka nake baka shawarar kiranta a waya ita sai ta fito ku gaisa." Yace."Okey to bude min na zauna a gurin zamanka sai na kira wayar tata." Maigadin ya bude masa ya shiga ya zauna kan kujerarsa shi kuma ya mayar da gate din ya rufe... *Masoya a taimaka da Sharing🥰👏🏼* *IDAN KINA BUKATAR BIYAN KUDIN LITTAFIN GA YANDA ABIN YAKE......VIP GRUOP#600....NORMAL GRUOP#300.....ACCOUNT.....0542382124.....BINTA UMAR GTBANK.....IDAN KATI ZAKI TURO...#400 NE SAI KIYI MIN MAGANA TA WHASAP DA WANNAN NUMBER* *07084653262* *08089965176* *BINTA UMAR ABBALE* [3/6, 8:46 AM] 💜: *GA IRINTA NAN!!!🙆🏼‍♀️* _(LOVE STORY🌺)_ *NA* _BINTU UMAR ABBALE🍒_ *MANAZARTA WRITES ASSO🖊️📚* *SADAUKARWA NE GA IYAYE NA GUDA BIYU* *FATIMA MUSA (MOMY NIJAR)* *TARE DA* *USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)* _*Ina kaunar ku iyayena ina kuma alfahari da irin kaunar da kuke nuna min💜🥰*_ *14&15* Wayarsa ya d'auko daga aljihun shart din dake jikinsa sai ya nemo number ta ya shiga kira. lokacin ni kadaice zaune a falon Ummah ina karyawa, jin kira ya shigo wayata dake gefena a ajiye yasa da sauri na kai hannuna kan wayar kwata-kwata ban kawo shi bane sai da na duba naga number sa akan wayar. tsaki naja na mayar da ita na ajiye a nutse na cigaba da abinda nake. Ya kira kusan sau hudu bata dauka ba jikinsa yayi sanyi sosai kuma ransa ya 'baci da abinda tai masa yanke shawarar tura mata text yayi kamar haka." _*Aunty Sa'ida ina fatan kin tashi lafiya na kira wayarki babu adadi sabida wulakanci kin'ki dauka kin tafi kin bar baya da kura a gida saboda ke Baba ya kori Ummatu gidansu bayan haka kuma Gwaggo tana nan cikin damuwa ko abinci ta kasa ci kiyi hakuri ki dawo gida idan ni nake takura miki to ina mai tabbatar miki da cewa gobe i yanzu ina skull saboda haka ki dawo gida saboda farin cikin masu kaunarki.*_ Text din na duba jikina yayi sanyi jin cewar Ummatu na gidansu me yayi zafi da Kawu Iro zai yanke irin wannan hukuncin sai duk naji banji dadin al'amarin ba. Dakin ta shigo ta sameni a zaune ga kayan break din a gabana na kasa ci tace."Lafiya kika zabga tagumi haka."? A sanyaye nace."Umma wai kinji Ummatu tana gidansu saboda abinda tayi min Kawu Iro ya yanke mata wannan hukuncin." Cikin rashin jin dadi tace."Ikon Allah me yayi zafi shi kuwa da zai yanke irin wannan hukuncin a gaskiya ban Ji dadi ba wallahi." Nace."Nima gabadaya jikina ya mutu wallahi a cewarsa wai ba zata dawo ba har sai na koma gidan.'' Umma shuru tayi tana girgiza kanta kafin tace."A gaskiya Ibrahim ya yanke hukuncin da bai da dace ba ai bai kamata da girmanta da komai yayi mata haka ba."A sanyaye nace." Nima dai haka na gani." tana kokarin bud'e wardrobe d'inta tace."To Allah ya shiga cikin al'amarin ya sasanta tsakaninsu." na amsa da "ameeen ya Allah." Khalid kai tsaye can babban gida ya nufa gidansu mahaifiyar tasa dake unguwar dala gidan yawa ne irin na gado duk wanda ya tashi a gidan yake aure ya zauna kafin Allah yayi masa nasa shiyasa gidan kullum yake a cike da yara kowanne da nasa . Kai tsaye bangaran su Mahaifiyarsa ya nufa ya same su suna karyawa da koko da awara zama yayi kusa da kakarsa mai suna Baito yana tsokanarta ganin yanda ta tasa bokitin koko a gabanta tana sha. Tace."Kai ma idan kana sha sai na zuba maka badan halin Ubanka ba." Yace."Aa bana shan koko kashe min jiki yake." shuru tayi ta cigaba da kur'bar kokonta yace."Baito naga kamar haushina kike ji." A fusace! tace" Ba dole naji haushi ba Khalid jiya da bakin cikin kakarka da babanka na kwana saboda tsabar rashin mutunci su koro min yarinya cikin dare mai tayi musu da zafi da har zasu yanke mata wannan hukuncin."? Yace."Baito dan Allah ki samu nutsuwa muyi magana ta fahimta yanzu ina Ummatu take."? Tace."Tana Bandaki." shuru yayi na minti biyu kafin yace." Baito Ummatu bata fad'a miki laifinta ba ko."? Tace."Ta fad'a min akan wannan lalatacciyar yarinyar ubanka ya koro ta.'' Khalid yaji kamar ta soka masa wu'ka a ma'koshi yace."Baito bai kamata ba abinda kukeyi kuma fa kun haifa kina da 'ya'ya da jikoki bai kamata ki dinga aibata d'an wani ba yau ko gaskiya ne zargin da kukewa auntyn Sa'ida bai kamata ku dinga zaginta kuna la'antar ta ba kamata yayi kuyi mata adduar shiriya.'' "Allahu akbar! Khalid ka gama nasihar ko baka gama ba."? Tafad'a tana masa wani kallo. yace." Da alama maganata bata gamsar dake ba." Da sauri tace."Ta ina kuwa zata gamsar dani bayan nasan karya kake kana fada ne kawai dan ka kareta nan Jamila take sheda mana irin lalatar da takeyi da maza a makarantarsu saboda haka maganar Jamila ba karya bace Sa'ida bata da kintsi da kamun kai." Jamila 'yar yayan Ummatu ce da suke zaune a cikin gidan Jamila budurwace 'yar kimanin shekara goma sha takwas tana zuwa makarantar da Sa'ida take koyarwa ta *Hajara Buhari* dake goran dutse. Khalid yace."Jamilan ce tazo tana fad'in wannan maganar."? Baito na kokarin yin magana Ummatu ta karaso gurin da sauri tace."Rabi kinga Khalid daga zuwansa ya soma kalubalantata akan na fadi gaskiya ashe har Sa'ida ta fiki kima da mutumci a gurinsa." Ummatu ta ajiye butar dake hannunta rai a 'bace tace."Baito aini tuntuni na gama magana wallahi tallahi duk ranar da yaron nan ya sake shiga sabgar Sa'ida to sai yaga abinda zai faru dashi." Khalid yace."Ummatu dan Allah ki daina wannan maganar aunty Sa'ida 'yar uwata ce bai kamata ki raba zumuncin dake tsakanina da ita ba." Tace."Ai nima dama ba zumuncin ku nace zan raba ba abinda nake nufi shine ka raba kanka da ita tunda duk wasu alamu ka nuna kana sonta in banda rashin hankali irin naka Khalid me zakayi da wannan yarinyar tsohuwa gata mara daraja da kamun kai kai yanzu ba zakaji kunyar auranta ba." Yace."Ummatu babu kunya a cikin abinda ya zamanto halas dan aunty Sa'ida ta girme ni hakan ba zai hanani na aureta ba tunda ba haramun bane.'' Baito tace."To ba zaka aureta ba d'in Khalid ba zaka lalata mana zuria ba kaje ka nemo wata ka aura idan baka samu ba kazo gida ka duba gamu nan da 'yan mata kyawawa masu da kyau da duk abinda ake bukata." Shuru yayi ransa duk a 'bace ya tsani yaga suna nuna k'yamarsu akan auntynsa a ganinsa sam bata cancanci haka a gurinsu ba. A cunkushe yace."Dama ni nazo ne domin nayi muku sallama idan Allah ya kaimu gobe zan koma makaranta'' Baito tace."Wace makaranta kuma? dama baka gama karatun ba."? Yace." Akwai sauran kad'an." Tace."To Ubangiji Allah yasa daga ka gama ka samu aiki kaga sai kayi auranka da hujja ni nafi so ma kazo gida ka duba wallahi ina yi maka sha'awar Jamila." tana 'yar dariya ta 'karasa maganar. Hararar gefan ido yayi mata yana kokarin mi'kewa yace."Baito ni dai Namiji ne babu wanda zai yi min auran dole." Ummatu tace."Khalid magana kake so ka fad'a mata saboda baka da kunya."? Girgiza kansa yayi yace."Aa Ummatu kiyi hakuri dan Allah abar maganar amma ni kada a 'kara yi min maganar wata Jamila bana ra'ayinta." Ummatu ta fusata sosai tace." 'Yar d'an uwan nawa kake k'yamata? meye aibun Jamila yarinya kyakykyawa fara mai kuruciya a jika." Shuru yayi bai tanka ba yasa takalmansa Baito tace."Ai ni mamaki ma ya hana ni magana 'kiri-'kiri yaron nan yana nuna yafi kaunar dangin Ubansa akan na uwarsa." Khalid dai baice komai ba ya kama hanya ya fita daga gidan gabad'ayansu suka bishi da kallon mamaki!! bayan fitarsa Baito tace."Rabi hak'ika zama bai ganki ba tilas ki fara neman taimako akan yaron nan idan ba hakaba anan gaba cewa zaiyi ba ke kika haifeshi ba." Ummatu ta sunkuyar da kanta ranta idan yayi dubu ya 'baci tace."Baito maganarki gaskiya ce Khalid kwata-kwata baya ganina da mutunci baya jin maganata sai ta kakarsa duk abinda Gwaggo tace shine daidai a gurinsa ni ya raina ni alhalin ni na haifeshi kuma mutukar za'a zagi Sa'ida a gabansa sai ya nuna 'bacin ransa saboda haka dole na nemi taimako a gurin malamai su karkarto da hankalinsa kaina dan na rantse ba zai auri Yarinyar nan ba." Baito tace."Abinda ya kamata kiyi kenan kada kiyi sanya idan anjima ki shirya sai muje gurin Malam Saminu zai taimaka miki akan lamarin." _Allah kasa mu dace jama'a wai uwa ce take d'ora 'yarta a hanyar zuwa gurin malami a maimakon tayi wa d'anta kyakykyawar addua sai mugun baki take masa 'karshe ma zata kaishi gurin malami Allah ya kyauta yasa mu gane_ Khalid na daf da fita sukayi karo da Jamila zata shiga gidan washe baki tayi da fadin"Laa Yaya Khalid ina wuni."? Kallon banza yayi mata kafin ya ratseta ya wuce ba tare da ya amsa gaisuwarta ba, haushinta yake ji sosai akan k'azafin da tayi wa auntynsa.....Jamila a sanyaye tabi bayansa da kallo gabanta na faduwa itakam ya zatayi ne Allah ya d'ora mata kaunarsa a cikin ranta...jiki a mace ta shiga cikin gidan. Gwaggo na zaune a tsakar gida ita kad'ai tayi suguri abin duniya duk ya isheta Sa'ida kawai take tunani idonta akan kofar shigowa gidan daga taji motsi zata zabura ta kalli kofa.....Uwale ta rangad'a sallama cikin gidan. Gwaggo ta amsa mata tare da gyara mata gefanta ta zauna suka shiga gaisawa....Uwale tace."Dama nazo ne naji inda aka kwana shin ina fatan kuna ganin kyawun maganin nan."? Gwaggo ta sauke ajiyar zuciya rai a 'bace! tace." Ai Uwale Yarinyar nan ta'ki bani had'in kai wallahi da 'kyar ma ta bari aka turara maganin sau biyu daga nasa turaran a wuta zata dinga masifa ta fita daga dakin ta barni a ciki ina shakar haya'kin ke a takaice ma ta gudu daga gidan tun jiya." Uwale ta rike ha'ba cikin mamaki tace."Kinji ko ai alamun da akwai iska a tare da ita kenan tunda gashi sun hanata zama a gidan saboda turaran da kikeyi musu." Gwaggo tace."To hakan zata iya kasancewa amma ni ina tunanin abinda Rabi tai mata ne yasa ta tattara kayanta ta gudu." Cikin son jin gulma Uwale tace."Oh! me kuma Rabin take mata."? Gwaggo ta shiga bata labarin abinda ya faru...Uwale tace."Ai kinga Rabi ko gado tayi dan mahaifiyarta Baito mara mutunci ce babu irin sharri da kazafin da ba tayi wa kishiyoyinta ba ni dama tuntuni nasan Baito ba mutuniyar kirki bace." Gwaggo tace.''Kice dai Rabi gadon mugun hali tayi."? Uwale ta 'bantari gora ta mi'ke kafarta a kan tabarmar tace"Wallahi kuwa Sau nawa muna had'uwa da ita a zauran malam ai shiyasa kullum nake fad'a miki cewar sai kin tashi a tsaye akan Rabi domin ita da mahaifiyarta biye-biyen malamai suke." Gwaggo tayi shuru tana jimanta al'marin.....Uwale ta yunkura da fad'in "Gwaggo ni zan tafi dama unguwa zani nace bari na shigo mu gaisa na kuma tambayeki halin da ake ciki." Gwaggo tace."To Uwale nagode sosai sai kin dawo nazo gidan naki domin mu yanke shawarar yanda za'ayi domi gaskiya maganar Rabi da mahaifiyarta ya tsaya min a rai." Uwale tace."To shikkenan ai babu damuwa sai kinzo din." Sallama sukayi da juna...Uwale na kokarin fita daga gidan Khalid ya shigo da kyar ya gaisheta yana dauke kansa ya shige gidan. Gwaggo na ganinsa shi kadai fuskarsa kuma babu annuri sai tasha jinin jikinta.....Ya zaune kusa da ita yana matse gumin goshinta a sanyaye tace."Jarumi ya ake ciki ne ina Sa'idar.''? Nannauyar ajiyar zuciya ya sauke kafin yace."Gwaggo lokacin da muka isa gidan Alhajin ya fita sai na yanke shawarar kiran wayarta Gwaggo nayi nayi ta daga ta'ki haka na hakura na kyaleta. Tace."Yanzu dai baku samu nasarar daukota ba." Kansa kawai ya daga mata ya lumshe idonsa damuwa ce mai tsanani take damunsa. Gwaggo shuru tayi na minti biyu kafin tace."Idan anjima da yamma zanje gidan ayi wacce za'ayi." Idonsa ya bude da sauri yace."Kada kije musu gida ki bari Baba yace zai koma da daddare insha Allahu komai zaizo da sauki amma ni bana so kije gidan kiyi wani abu suji haushinki ko kuma daga baya kiyi nadama kiyi hakuri abi komai a hankali." Shuru tayi ba dan maganarsa ta gamsar da ita ba, yace." kin san gobe ni zan koma skull ko."? Girgiza kanta tayi tace."Bani da labari aini na dauka ka gama karatun ganin wannan karan ka dade a gida." Yace."Yajin aiki malamai suka tafi karatu kuma da yardar Allah na kusa kammalawa ki cigaba dayi min addua idan na gama na samu aiki." Tace."Insha Allahu zan cigaba dayi maka addua." Mikewa yake kokarin yi tace."Zaka ci abinci ko."? kallonta yayi kafin yace."Idan yanzu kika girka zanci." Tace."Sai dai na dauki taliya d'aya a cikin kayan abincin Sa'ida nayi maka dafaduka da daddawa irin wacce kakeso." Girgiza kansa yayi yace."Kada ki ta'ba mata kayan abinci bari nai wanka na fita na siyo sai kiyi min." Tace."Khalid kada ka 'batar da kudinka zasuyi maka amfani a makaranta ka bari a d'auka tunda da akwai." Yace."Gwaggo bana bukata na fad'a miki ki kyaleni naci aljihuna bana fatan wata mace ta ciyar dani." Tace."To shikkenan bari naje na siyo kayan miyar da zanyi maka girkin." Yace."Ki zauna ki huta duk zan had'o komai da zaki bukata gurin girkin." Shuru tayi tana kallonsa har ya shige gurinsu....Ta sauke ajiyar zuciya cikin ranta take masa fatan alkairi. Tsaf tayi masa jallop din taliya irin ta mutanan da taji daddawa da manja da kifi sosai yaji dadin abincin ya dinga ci yana santi ita kuma sai dariya take masa dama haka take so ya sake ya cika cikinsa da abinci......Bayan ya kammala cin abincin a nutse ya kalleta da fad'in "Gwaggo ni zan fita nayi sallama da abokaina dan gobe da wuri nake so na tafi." Tace."To shikkenan Jarumi sai ka dawo." Khalid yasa takalmansa ya fice daga gidan ita kuma ta juye ruwan zafin dake kan wuta ta surka ta shiga bandaki tayi wanka a gurguje ta shirya jikinta cikin atamfa (nicam) riga da zani da mayafi ta daura dankwalin (disco) a kanta pose dinta da dan mukkuli ta dauka ta fito ta kulle dakin takalmanta na dan'ko tasa a 'kafafunta ta fita daga gidan......Bakin titi ta fita tana addua akan Allah yasa kada ta hadu da Khalid din cikin ikon Allah kuwa har ta shiga adaidaita sahu bata ganshi ba. Har bakin gate din gidan Alhaji Shamsu aka ajiyeta ta fito tana gyara lullu'bin mayafin atamfar dake jikinta, Pose din ta bude ta dauko dari biyu ta mika masa ya kar'ba tare da dauko hamsin ya bata a matsayin canjin ta.. karba tayi da sauri tasa a cikin jakarta tana masa godiya yaja babur dinsa yayi gaba. Gate din gidan ta nufa ta bubbuga maigadin ya bude ganin kamar yasan fuskarta yasa ya gaisheta tace."Ina fata ka sheda ni ko."? Maigadin yace."Eh na sheda ki Gwaggo bisimillah shigo mana." Gwaggo ta shiga gidan tana hamdala a cikin zuciyarta...............Gyaran kayan miya mukeyi da Asabe kawai naji sallamarta nai saurin daga kaina ina kallon bakin kofa. Ido muka had'a da ita tace."Babu shakka Sa'ida wato ke kina nan hankalin ki a kwance kin bar mu cikin damuwa ko."? Bagarar da maganarta nayi nace."Gwaggo sannu da zuwa ki shigo mana." Tace."Ai ko baki fad'a ba." Asabe na murmushi ta gaisheta ta amsa tana bin gurin da kallo sai ta'be baki take. Sanin halinta yasa nayi saurin mi'kewa da fad'in "Shigo mana." Ba tare da tace komai ba ta biyo bayana...Ummah kawai sai ganin mu tayi a tare. Da sauri tace."Gwaggo kece kike tafe da yamma haka."? Tana kokarin cire takalmanta domin shiga falon tace."Aikuwa dai nice nake tafe ko dai ba'a maraba dani."? Ummah Habiba tace."Aa Gwaggo ana maraba dake shigo ga guri ki zauna." Ta shiga ta zauna kan kujera tana gyara yafan mayafinta. Cikin mutunci da girmawa Ummah ta gaisheta ta amsa babu cikakkiyar walwala a tare da ita. Nace."Gwaggo sannu da hanya." tayi saurin fad'in "Ai bazan amsa gaisuwarki ba Sa'ida tunda kin nuna mana iyakarmu." Nace."Gwaggo wace irin magana ce wannan."? Fashawa tayi da kuka tace."Wato Sa'ida saboda Ibrahim bashi da kudi baya baki shayi da biredi baya siyo kayan miya da nama shine kika tattaro kayan ki kika gudo gidan mijin mahaifiyarki to komai talaucin mu mune gatanki sabida haka 'kafata k'afarki zamu koma gida dan ba zan zauna ayi min 'karfa-'karfa ba." Cikin aljabi da mamaki nake kallonta lallai Gwaggo ta iya sauya lamari wato tanan ta 'bullo kenan." Umma Habiba tace."Haba Gwaggo banji dad'in wannan magana ba wallahi Sa'ida bata da gata sai ku kuma duk rashi da taulacin Kawunta bai gaza da ita ba yana iyakacin bakin kokarinsa akanta to me zai sanya kiyi wannan maganar." Shuru tayi bata tanka ba.Umma Habiba ta cigaba da cewa" Sa'ida tazo gidan nan jiya da daddare cikin damuwa da tashin hankali ta sheda min irin cin mutuncin da Ummatu take mata wannan dalilin yasa nace ta zauna ta huta idan ta samu nutsuwa sai ta koma." Gwaggo tace."Eh hakane abinda tazo ta fad'a miki Ummatu taci mutuncin ta amma kuma Kawunta Ibrahim ya dauki mataki dan yanzu zancan da nake miki Rabi tana gidansu kuma yace ba zata dawo ba sai Sa'ida ta dawo saboda haka idan ke 'yar halak ce sai ki had'a kayanki mu tafi gida idan kuma kikayi sanadiyar raba auran Ibrahim da matarsa to zaki shiga bakin duniya." Sa'ida da mahaifiyarta jikinsu yayi sanyi! Gwaggo ganin duk jikinsu ya mutu sai taji dadin hakan ta cigaba da zuzuta al'amarin.....Ummah Habiba tace."To shikkenan Gwaggo magana ta 'kare Sa'ida zata biki amma sai mun jira Maigidan ya dawo." Gwaggo wani irin kallo ta watsa mata a fusace tace..... *Masoya a taimaka da sharing👏🏼🥰* *IDAN KINA BUKATAR BIYAN KUDIN LITTAFIN GA YANDA ABIN YAKE.....VIP GRUOP#600 NORMAL GRUOP#300....ACCOUNT.0542382124....BINTA UMAR GTBANK.....IDAN KATI ZAKI TURO #400 NE SAI KIYI MIN MAGANA TA WHATSAPP DA WANNAN NUMBER* *07084653262* *08089965176* *BINTA UMAR ABBALE* [3/6, 8:46 AM] 💜: *GA IRINTA NAN!!!🙆🏼‍♀️* _(LOVE STORY🌺)_ *NA* _BINTU UMAR ABBALE🍒_ *MANAZARTA WRITES ASSO🖊️📚* *MUTANAN NIJAR IDAN KUNA BUKATAR BIYAN KUDIN LITTAFIN GA NUMBER DA ZAKU NEMA......22790899076* *SADAUKAWA NE GA IYAYE BIYU* *FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)* *TARE DA* *USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)* *(HAJIYA BABBAH)* _*Hakika ina alfahari dadu Iyayena🤝🏻🥰*_ *16&17* *'KARSHEN FREE PEGE* "Wane irin sai maigidan ya dawo kuma Habiba kina nufin zanyi ta zama a gidan nan har sai mijinki ya dawo ya bada umarni."? ta'karashe maganar tana hararar ta. Umma Habiba taji rashin dadin maganar Gwaggon amma sai ta daure ko a fuska bata nuna ba tace."Gwaggo abinda nake nufi kenan a bari ya dawo a bashi hakkinsa a matsayinsa na mijina tunda tamkar uba yake a gurinta saboda haka dan Allah kiyi hakuri kada ki dauki maganata da wata manufa ta daban." Ta'be bakinta tayi tace."Saboda kawai nice sarkin zargi sai na dauki maganarki da wata manufa shikkenan ai tunda kince haka sai na zauna na jira shi ya dawo na dai fad'a miki 'kafata 'kafar Sa'ida dan ba zan yarda da raina da lafiyata jinina yayi agolanci a wani guri ba." Cikin takaici nace."Wai Gwaggo wace irin magana ce wannan kike yi dan Allah kiyi shuru haka ki daina d'aga mirya da tada jijiyar wuya magana ta 'kare zan koma gidan ko dan saboda Ummatu ta dawo d'akinta." Shuru tayi min ba tanka ba. Umma ta sauke ajiyar zuciya da fad'in "Ai maigidan ma yana kan hanya shida na yamma suke dawowa daga kasuwa." Tace."To Allah ya kawo su lafiya." Umma Habiba ta amsa da "ameen tare da mi'kewa domin fita daga falon Gwaggo ta dakatar da ita, da fadin " Nace ko kina da goro ki bani wallahi garin sauri na manta nawa a gida." Tace."Gwaggo ni bana cin goro amma bari na tambayar miki Hajia Hansatu.'' tana nufin uwargidansu. tace."To nagode Habiba ina jira wallahi sha'awar cinsa ce ta taso min a yanzu idan ma babu a gurinta ga kudina a siyo min." Umma Habiba tace."Ba za'a rasa ba insha Allahu bari na tambayar miki ita." Fita tayi daga dakin da sauri. Nace."Gwaggo ba zaki daina cin goro ba ko."? Kallona tayi cikin kulawa tace."Sa'ida ai ina jin sai ranar da numfashi ya bar gangar jikina zan hakura da goro ya zame min masifa ni kaina so nake na daina amma na kasa." Nace."Abu ne da kuka sanyawa ranku wanda kuke ganin idan baku ci ba wata matsalar zata iya faruwa daku kuma ba haka bane da zaku yi sati guda baku ci ba babu abinda zai same ku sai ma lafiya da kuzari da zakuyi amma dan jaraba kuyi ta cin abinda zai cutar daku." Shuru tayi bata ce komai ba. nasan duk surutan da zanyi akan al'amarin ba zata d'auka ba cin goro ya zame mata jinin jikinta. "Gwaggo zan koma gida amma da akwai sharad'i." Da sauri ta kalleni, na sha kunu da fad'in "Kiyi min tsakani da Khalid babu ni babu shi yaron bai da kirki da tarbiya akwai abubuwan da suka faru a tsakaninmu wanda idan na fito na fad'a miki hankalinki zai tashi ko kuma ma kice nai masa sharri to wannan dalilin yasa nayi shuru da bakina inaso ki zauna dashi kija masa kunne sosai ya fita daga sabgata maganar yana sona ya ajiyeta a gefe guda dan na rantse ba zan aureshi ba koda kuwa zan rasa mijin aure keda kike goya masa baya akan lamarin ki cire kanki domin ke zakiji kunya. abu na biyu kuma kina d'ora min lalurar aljanu ni lafiyata kalau kamar yanda nasha fada miki aure lokaci ne sabida haka Uwale ta daina janki gurin masu magani kina asarar kud'in ki bayan haka kuma idan kin san akwai ragowar wannan turaran da kike turnuk'awa a daki to da mun koma ki zubar dashi dan wallahi duk ranar da kika sake kunnawa zan bar gidan kuma komai abinki ba zan dawo ba guduwa ma zanyi ku rasa inda na nake. Gwaggo gabanta ya fad'i! ta tsira min ido nace." Wallahi Gwaggo wannan maganar da nake miki har cikin zuciyata nake miki ita Khalid ba tsaran aure na bane ki daina tatsuniya ba zan aureshi ba sannan ni lafiyata kalau aure kuma lokaci ne insha Allah cikin satin nan Alhaji Nura zai turo da magabatansa. "Sa'ida meye aibun Khalid da zaki dinga gudunsa ko dan bashi da kudi ne."? A sanyaye take magana dan na lura jikinta yayi sanyi da maganata. Girgixa kaina nayi ina kokarin magana Umma ta shigo falon hannunta da farar leda cike da goro manya masu kyau Gwaggo da sauri tasa hannu ta kar'ba da fad'in " Kai amma naji dadi sosai Habiba Allah yayi miki albarka." Umma Habiba ta amsa da "ameeen ya Allah." Ta fita daga falon. Ledar ta kwance ta dauko daya ta 'bantara ta fara taunawa. Nace."Gwaggo Khalid ko ya kai *Dangwate* kud'i a duniya baya cikin tsarina yaje can ya auri daidai dashi nima na auri daidai dani magana ta mutu a gidan nan kada ki Sake yi min maganar Khalid." Tace."Ai shikkenan Sa'ida tunda kinqi Khalid har kina kokarin yi masa sharri zanyi masa magana ya rabu dake tunda bakye kad'ai ce autar mata ba insha Allahu Allah zai bashi wacce ta fiki kyau da 'kuruciya." Nace "Nima zan taya shi da adduar samun macan data fini." Shuru tayi min ta cigaba da tauna goronta kallonta kawai nayi na gane maganata ta kashe mata jikinta, nace."Ko na kawo miki abinci."? Girgiza kanta tayi tace."Bana bukata saboda inda na baro da akwai abinci." Nasan magana ta fad'a min a fakaice oho! ni dai na fad'a mata abinda yake raina sabida haka ita da Khalid din duk su shiga hankalinsu. Tace."Khalid d'in ma gobe zai koma makaranta." Nace."Allah ya bada sa'a." ta amsa da "ameeen ya Allah." Umma ce ta shigo dakin da fad'in "Gwaggo Alhajin ya dawo tashi muje nayi miki jagora ku gaisa." Da sauri ta miqe tana gyara yafan mayafinta suka fita tare. Alhaji Shamsu yana zaune a kan kujera yana lissafi da wayar hannunsa sukayi sallama a dakin nasa....cikin kulawa ya amsa da fad'in"Gwaggo sannu da zuwa ga guri nan zauna."yafada yana nuna mata kujerar dake kallonsa Gwaggo ta zauna kan kujerar tana amsawa tare da fad'in "Ai na jima a gidan ina jiranka da fatan ka dawo lafiya."? Yace." Lafiya lau gwaggo ai ban sani ba da tuntuni na dawo gidan sabida ke koda na shigo ma maigadi yake sanar dani zuwan Ibrahim bayan fita ta hakika banji dadin faruwar hakan ba." Tace."Aikam dole kaji rashin dadi dan muma jiya haka muka kwana zuciyoyinmu Babu dadi wannan dalilin ne ma yasa shi Ibrahim dako sammako yazo gurinka domin ku tattauna magana sai kuma akayi rashin sa'a ka fita kasuwa shine nace to ni bari idan rana tayi sanyi sai nazo gidan na sameka mu tattauna maganar dan nazo tafiya da Sa'ida ne matarka Habiba tace lallai sai ka dawo ka bada umarni shine nace to komai dare kuwa zan zauna har ka dawo domin naji uzirinka akan yarinyar." Alhaji Shamsu yayi gyaran murya yana kallonta ya riga yasan halinta 'yar taratsatsi ce yace."Hakane Gwaggo Sa'ida tazo gidan nan cikin halin damuwa tana kuka ta sheda mana abinda yake faruwa acan gidan al'amarin ya tayar min da hankalina sosai Gwaggo shi ai aure lokaci gareshi mai zai sanya ku tayar da hankalinku akan yarinyar nan har ku dinga d'ora mata lalura irin ta aljanu bayan haka kuma har a samu masu yi mata 'kazafi na zina wannan al'amari baiyi min dadi ba gaskiyar lamari raina ya 'baci dajin wannan magana shine dalilin da yasa ma na yanke hukunci kancewa ba zata koma gidan ba sai an kwana biyu kuma dole ne mu samu zama dashi Ibrahim din akan maganar yana da kyau ya jawa matarsa kunne ta guji jifan yarinyar nan da muna nan kalamai domin hakan bai dace ba." Gwaggo tace."To ai Alhaji Ibrahim ya tauna tsakuwa dan aya taji tsoro inaso na sheda maka cewar duk yanda kake kaunar yarinyar ba kamar shi ba tunda Ubanta ne ya saki nono shi ya kuma ya kama kaga dole yayi kishinta ya kuma nunawa matarsa 'bacin rai dan yanzu maganar da nake maka Rabi tana gidansu tun jiya ya koreta daga gidansa yace mutukar ba Sa'ida ce ta dawo gidan ba to ya gama zama da ita." Alhaji Shamsu yace."Subahanallahi Me yayi zafi Ibrahim zai yanke wannan hukunci." Ummah Habibatan tace."Nima haka na gani Alhaji Iro ya yanke hukuncin da bai kamata ba ai komai a sannu a hankali ake binsa." Gwaggo tace."To ai shine nake so ku fahimta Ibrahim zai iya rabuwa da matarsa akan yarinyar nan to tun kafin hakan ta faru yasa nazo domin tafiya da ita." Hankali a tashe ya dauki wayarsa da fad'in "Bari na kira wayarsa idan da hali sai yazo domin mu tattauna maganar a tsakanina dashi amma banji dadin wannan lamari ba." Gwaggo tace."To shikkenan ai yanzu nasan ya dawo daga kasuwa idan ma bai dawo ba to babu shakka yana kan hanya. Kawu Iro na adaidaita sahu kira ya shigo wayarsa ganin number Alhajin yasa da sauri ya daga suka gaisa a tsanake Alhaji Shamsu ya sheda masa uzirinsa....Kawu Iro yace."To babu damuwa Alhaji ganin zuwa insha Allahu." Wayar ya kashe ya umarci direban daya juya baya ya kaishi hotoro. Yace."Amma dai zaka 'kara min kudi ko."? Kawu Iro yace."Eh 'kwarai kuwa idan ma ka samu fasinja ka dauka." yace."to shikkenan. Sai magariba Kawu Iro ya isa gidan kuma basu samu zama ba sai da suka gabatar da sallah tukkuna suka fito daga massalaci a tare wani 'kebantacan guri suka samu suka zauna suka sake gaisawa cikin mutumci kana suka shiga tattauna abinda ya had'asu. Kawu Iro ya sauke ajiyar zuciya da fad'in "Alhaji ka kwantar da hankalinka insha Allahu hakan ba zata sake faruwa ba maganar mai d'akina kuma ni a ganina hukuncin dana dauka a kanta shine daidai kaga gaba zata kiyaye jifan yarinyar nan da wata mummunar kalma." Alhaji Shamsu yace."Hakane Ibrahim to amma inaso dan Allah ka sake sanya ido akan yarinyar nan sannan idan da wani wanda kaga alamun da gaske yake sonta to kayi masa magana ya fito kawai domin hakan shine ya dace." Kawu Iro yace."Insha Allahu hakan za'ayi akwai wani mutumin anan gaban inda muke yana son ta koga yanayin hidimar da yake mata to saboda haka idan na koma gida zan sameshi da maganar domin mu tattauna." Alhaji Shamsu yace."To Alhamdulillahi Allah yasa sanya alkairi.'' Kawu Iro ya amsa da ameeen ya rabbi.'' To muna zaune a falo har gwaggon muna hira ya shigo. gwaggo tayi saurin fad'in "Ina fatan Ibrahim din yazo." Yace."Eh Gwaggo yazo ina fita da niyyar shiga massalaci na hangi zuwansa tare ma mukayi sallah masha Allah mun tattauna magana dashi ta fahinta saboda haka ke Sa'ida zaki koma gida magana ta wuce insha Allahu hakan ba zata sake faruwa ba sannan kuma Ibrahim ya sheda min cewa akwai wani mutumi da yake sonki a Cikin unguwar to nace masa yayi magana dashi idan da gaske yake sai yayi magana ayi abinda za'ayi." Gwaggo har ta bud'e baki za tayi magana sai kuma ta fasa. Yace."Gwaggo kamar akwai magana a bakinki." girgixa kanta tayi tace."Aa babu magana Alhaji." Ya kalleni da fad'in "Kinji hukuncin dana yanke ko."? Nace." Eh naji Alhaji dama nima inaso nayi masa magana kan cewa ya turo magabatansa ayi maganar aure idan da gaske yake." Alhaji yace."To Alhamdulillahi hakan yayi kiyi masa magana shima Ibrahim din yayi masa sai ya dauki maganar da muhimmanci." Nace."To shikkenan Alhaji." hannu yasa a aljihu ya dauko kudi kimanin dubu biyar ya mikawa Gwaggo da fadin "Gashi kya sayi goro." Babu yabo babu fallasa ta kar'bi kudin dan Taji masifar haushin yanda yake nuna ikonsa akan Jikarta wai duk muna nan maganganun data ya'ba masa ba suyi masa zafi ba sai wani za'kal'kalewa yake. Bayan fitarsa daga falon Ummah Habiba tace"Gwaggo bari na kawo miki abinci kici sai ku taf......tun kafin ta 'karasa tayi saurin katseta da fad'in "Bayan wanda naci d'azu kuma zaki sake d'ubga min wani Aa bana bukata tafiya za muyi." kana jin yanda tayi maganar kasan a fusace take......mi'kewa tayi tana gyara yafan mayafinta, nida Umma muka bita da kallon mamaki. A cunkushe tace."To gimbiya ina jakar kayan naki take na d'aukar miki.'' Murmushi takaici nayi ba tare dana tanka mata ba na mi'ke Umma ma ta mi'ke tana 'yar dariya nasan ita da gwaggo ne....Hijabina na gyara na dauki jakar kayana na ri'ke ta ta'be bakinta tai tayi gaba tana surutai! Umma tace."Gwaggo ga mayafi da takalmi kayi amfani dasu." Juyowa tayi tana kallon ledar hannunta murmshi tayi wanda be kai ciki ba tace."Habiba kin manta ni tunda jajayen sawuna bana yafa wani gyale idan ba na atamfa ba." Umma tace."Kwarai hakane na manta wallahi to ki kar'ba dai ko kyautarsa sai kiyi.....Nace."Umma ki ajiye mayafin ki zaiyi miki amfani idan ta kar'ba ma munafukar matar nan zata bawa Uwale." Umma ta ri'ke bakinta cikin mamaki tana kallon Gwaggo tace."GwaggoAshe har yau kina tare da Uwale."? Da sauri tace." 'Kwarai kuwa ba kuma mai rabani da ita sai mutuwa." Tana gama maganarta tasa takalmanta ta fita ta barmu...Umma tace."Sa'ida ki cigaba da hakuri kinji ko watarana sai labari." Nace."Umma Insha Allah zan cigaba dayi nasan Allah yana kallo." Ta mi'ka min ledar da fad'in " 'Karbi ki ri'ke mata tunda nayi niyya bazan fasa ba babu ruwanki da wanda zata bawa." ledar na kar'ba da fad'in "To shikkenan." sallama mukayi da ita tace."Lallai idan na fita na shiga d'akunan kishiyoyinta nai musu sallama. Nace."To insha Allah zan shiga. bakin gate na same su a tsaye ita da Baba Iro suna jiran fitowa ta ina ta kici-kici da jakar kayana yazo ya kar'bi jakar yana fad'in " Sai kiji da ledojin hannunki." Nace."Haba dai Kawu dan Allah ka ba kawo dik zan iya ri'kewa." Gwaggo tace."Au! ashe kayan naki suna da yawa tunda ga wasu nan a ledoji." Nace"Aa wannan ledar taki ce su kuma wannan yanzu akayi min kyautarsu amma ni ba dasu nazo ba." hannu ta mik'a ta kar'bi ledar kayanta tayi gaba nabi bayanta ina mamakin 'karfin halinta. Direba ya kar'bi jakar kayana yasa a bayan mota Gwaggo ta shiga ta zauna Kawu ya zauna kusa da direba ina kokarin shiga........Motarsa ta shigo gidan tsayawa nayi har direbansa yayi parking ya fito a nutse cikakken mutum kamili dogo ba'ki da kyau daidai misali saboda yanayin hutu da jin dadi yasa bakar fatarshi tayi wani freesh sai daukar ido take...... kwata-kwata Yaya Aminu baida izzah irin ta masu kudi dalilin ma da yasa kenan nake 'kara mutunta shi. Fuska a sake ya 'karaso inda nake yace."Ranki ya dade dama kina nan."? murmushi nayi a nutse nace."Ina nan Yaya Aminu ya kake ya al'amura."? Yana min wani irin duba yace."Alhamdulillah wato dai ba zaki tambaye ni Iyali ba ko."? Dariya na d'anyi nace."Yaya Aminu kenan to Ya Iyali." Cikin sigar tsokana nayi maganar ya amsa min da "Suna nan lafiya kalau kamar gaske. Dariya nasa ina kallonsa shima sai yasa dariyar Gwaggo ta le'ko kanta da fad'in " Wannan kuma waye kike ta ya'ke masa baki." Da Sauri nace."Yaya Aminu ne babban yaron Alhaji." "Au! koda naji." abinda ta fada kenan ta dauke kanta......Motar ya dafa cikin nutsuwa ya gaisheta ta amsa kamar bata so Ya mi'kawa Kawu Ibrahim hannu suka gaisa a mutunce, Ya dawo da hankalinsa kaina da fad'in "Tafiya zakuyi ne."? Nace." Eh wallahi." Jim! yayi kamar da magana a bakinsa kawai ya basar yasa hannu cikin aljihu sabbin kudi ya dauko ya mi'ko min. Nace."Dan Allah ka barshi." girgiza kansa yayi yace."Ki kar'ba mana ko katin waya kyasa ko." hannu biyu nasa na kar'ba da fad'in "Nagode Yaya Aminu Allah ya 'kara arziki. A nutse ya amsa da ameeen to sai gani na biyu ko."? nace" Aikuwa dai tunda kai ganinka ha'bo ne baka zama a gari." Yace."To ya za'ayi Sa'ida taurari na masu zagaye ne nima ba a san raina nake zurga zurga nan ba. Nace."Hakane to Allah ya taimaka." Ya amsa da "ameeen tare da daga min hannu da sauri ya wuce cikin gidan......Ina shiga motar ta rufe ni da fad'a " Sa'ida wato kin mai damu marasa galihu ko kinga kudi duk kin gigice kin barmu zaune a mota to bari kiji wallahi komai abunki ba zaki sanjawa towo suna ba." Uffan bance mata ba ta cigaba da sababi tana fadin" Yana fama da 'bakar fuska yazo ya tsayawa mutane to idan ma sonki yake sai dai yayi hakuri dan ba zaki aureshi ba ehe! ba naji ubansa na wata magana ba Kai Ibrahim kada ka kuskura ka tunkari Alhaji Nura da wata magana Sa'ida bata da miji sai Khalid da yardar Allah." Nida Kawu Iro shiru mukayi mata uffan ba muce ba ta 'karaci surutan ta ta gaji tayi shuru tana gyangyadi. sai da muka isa gidan na tashe ta ta fito tana mita......Khalida dake can tsallaken gidansu Salim ya karaso gurin, hannunta ya ri'ke suka shiga gidan sai magana take masa 'kasa-'kasa...Yace." To shikkenan Gwaggo magana ta wuce zan fita daga harkarta. har daki ya kaita ya karkade mata shimfidarta ta kwanta tana mita wai kafafunta ciwo suke mata da sauri yace."Bari naje na siyo Roob sai na shafa miki a kafafun. Yana kokarin fitowa daga dakin ni kuma ina 'kokarin shiga mukayi karo dauke kaina nayi tare da bashi hanyar wuce wa.....ba tare da ya kalleni ba ya fice daga gidan. Tana mitar ciwon kafafu tana fama da redio sai shuuuuuu! takeyi ta'ki kamawa da alama batir din yayi sanyi, da 'kyar ta yunkura ta mi'ke tsaye da fad'in "Ai dole na fita na siyo batir." Da sauri na kalleta tana kokarin yafa mayafi nace."Gwaggo yau d'aya dai ai sai ki hakura kuma yanzu fa Khalid ya fita mai yasa bakice ya siyo miki batir din ba." Tace."Sa'ida bana san takurawa Khalid bashi da kud'i shiyasa bance ya siyo min ba." Nace"Idan kika bashi kudinki zai siyo miki ba lallai sai da kud'insa ba.'' Girgiza kanta tayi tace."Bai zama lallai ya kar'ba." Nace." Ki daiyi hakuri da jin redion ki barwa gobe." "Aa ba zan hakura da jin taskar labarai ba." Hanyar fita ta kama cike da mamaki na bita da kallo maganarta naji a tsakar gida tana fad'in "Eh fita zanyi na siyo batir na redio na yayi sanyi ta'ki kamawa." Muryar Kawu naji yana fad'in "To koma ki huta bari naje na siyo miki.'' Tace." To yawwa Ibrahim nagode Allah yayi maka albarka." Dakin ta dawo ta zauna tana dai sake mummurd'a redion sai shuuuuuu take amma taki hakura. Khalid ya shigo dakin da sallama a bakinsa itace ta amsa masa dan ni ko inuwarsa ma ban kalla ba....ya mika mata batir din da fad'in "Gashi Baba yace a kawo miki." kar'ba tayi ta fara sawa a redion ya zauna kusa da ita tare da mi'kar mata da 'kafafunta a nutse ya bud'e Roob din ya fara shafa mata. addua ta shiga yi masa kafin naji sun fara magana 'kasa-'kasa 'karamin tsaki naja na fita daga d'akin buta na dauka na shiga band'aki ina jin takaicin abinda suke. "Gwaggo na fad'a miki fa magana ta 'kare zan fita daga harkata amma kuma ba zan daina so da kaunarta ba wannan nasan a jinin jikina yake......Tace." Kuma ka kwantar da hankalinka idan ka koma makaranta kayi karatunka lafiya maganar Alhaji Nura Gaibu ce. Murmushin takaici yayi yace."Gwaggo qaddara ma Akawai aure a tsakaninsu to ni kuma mutukar ina raye sai na hanata jin dad'in aure wallahi." Shuru tayi ba tace masa komai ba ya mike da fad'in "Ni zan tafi kallon ball." tace."To dan Allah kada kayi dare." yana kokarin fita daga dakin yace."Da wuri zan shigo gida insha Allahu. Ri'ke da buta na fito daga band'akin santsin ruwa dana takalmin 'kafata yayi yun'kurin kayar dani salati nasa nayi saurin ri'ke kyauran bandaki dik da haka sai da nayi zaman da'baro a gurin. 'Kuguna ya buge sosai na rintse ido ina kiran sunan Allah. Gurin ya 'karaso kawai naga ya sunkuya yana kokarin dauka ta....duk yanda naso dana hanashi kasawa nayi saboda naji jiki sosai jikina sai kyarma yake......har bakin kofar dakin ya ajiye ni ba tare da yace min komai ba ya juya ya fita daga gidan. Jiki a sanyaye na bishi da kallon mamaki! To washe gari da safe kadaran kadahan muka tashi gaisuwa ce kawai ta had'ani da ita sai da na shirya tafiya makaranta nayi mata magana, tace."Ba zaki tsaya ki karya ba ga ruwan kunu na d'ora a wuta." Nace."Gwaggo idan na tsaya karyawa zan makara zan samu wani abu naci a ofis." Tace."Ai ke idan ba dan kina da kurman jiki ba to da tuni kin zabge kiyi ta zama da yunwa ko damuwa bakya yi." Murmushi kawai nayi na gyara jakata dake kafad'a nace"Sai na dawo." tace."Allah ya bada sa'a." na amsa da "ameeen." Ina kokarin fita yana kokarin shigowa dakin baya na koma na bashi hanya ina d'an satar kallonsa yana sanye da 'kananun kaya ya goya jaka a bayansa kafarsa sanye da boot ya taje tarin sumar kansa sai kamshin turare mai sanyi yake.....babu walwala a fuskarsa yace."Auntyna barka da asuba." Ba tare dana kalleshi ba nace."Barka kadai ka tashi lafiya."? a tsanake ya amsa yana kallona da fad'in "Zan koma skull yau." nace."Allah ya bada sa'a." da sauri na fice daga dakin dan bana son wata duguwar magana a tsakaninmu. Gwaggo kamar za tayi kuka haka sukayi sallama ta rakashi har soro tana ta zabga masa addua.....a daidaita sahun Salim ya shiga yana daga mata hannu shima yasan zaiyi kewar kakar tasa sosai ya sha'ku da ita akan mahaifiyarsa. *BAYAN KWANA BIYU* gidan ya samu nutsuwa domin a washe garin ranar dana koma gidan Ummatu ta dawo da daddare babu laifi dai zaman da akeyi a gidan tsakaninta da Gwaggo gaisuwa ce dan har yanzu ta kasa sakewa a gidan ni kuwa kullum idan mun had'u na gaisheta bata amsawa hakan bayayi min ciwo saboda dama tuntuni na riga na saba.....sosai naji dad'in tafiyar Khalid domin na sake a gidan ina abubuwan da raina yake so kai tsaye zanyi daurin kirji na fito tsakar gida ba tare da fargabar wani abu zai faru ba..Gwaggo kuwa ta hakura da turara haya'kin tunda na gargad'e ta a gidan Ummana ta kiyaye muna zaune lafiya yanzu sai dai amma kullum cikin zagin Alhaji Nura take tana kwashe masa albarka idan kuma yayi min ake tare da ita muke cinyewa. To koda Kawu Iro ya samu Alhaji Nura da maganar sai ya nuna farin cikinsa sosai yace dama shima abinda yake ta sauraro kenan saboda haka tunda lamari ya kasance a haka zai turo da kudin sadaki i dan yaso in ya dawo daga tafiya sai ayi hidimar biki." Kawu Iro yace."Hakan yayi insha Allahu kuma zamu saurari zuwan wakilan ka." Cikin mutunci suka rabu da juna Kawu Iro ya kira wayar Alhaji Shamsu ya sheda masa duk yanda sukayi dashi.....sosai yaji dadin hakan kuma yayi fatan alkairi tare da jimirin jiran zuwan wakilan nasa. Gwaggo kuwa a ranar Yini tayi tana sababi! har taso ta saka min ciwon kai 'bacin ran abinda take yasa na fito na bar mata dakin Tabarma na shimfida a tsakar gida na zauna ina duba jarrabawar yara kira ya shigo waya ta a nutse na dauka ina dubawa murmushi nayi ganin sunansa akan wayar Alhajin Allah kenan tun ranar da sukayi magana da Kawu Iro yake farin ciki a rana sai ya kira ni sau hudu ko biyar....gaishe shi nayi ya amsa yana tambayata aiki nace."Alhamdulillahi Alhaji na." Mirmushi yayi mai sauti da fad'in "Gimbiyar mata ina jin dadin yanda kike kula dani nasan idan aka daura auran zan zama d'angatan ki." 'Yar dariya nayi nace."Aikuwa dai zaka sha lele a hannuna Alhaji saboda ni a rayuwata ina son mutum mai saukin kai ha'kika naji dadi sosai daka amince da maganata inaso ko bayan auranmu na cigaba da aikina ba wai dan ka gaza ba Aa ni kawai ina bukatar naga ana amfanuwa da ilmina." Yace."Kada ki damu gimbiya insha Allahu duk abinda kike so nima inaso zaki cigaba da zuwa aiki da yardar Allah." Cike da farin ciki nace."To nagode sosai My love." sai ya hau 'ba'b'baka dariya da alama yaji dadin sunan dana kirasa dashi. To cikin ikon Allah wakilan Alhaji Nura suka kawo kudin Sadaki dubu dari cas Kawu Iro yayi kara da kawaici ya bawa Alhaji Shamsu yace ya rike a gurinsa, aikuwa Alhajin yaji dadin karamcin da yayi masa. Gwaggo yini tayi tana kuka ko abinci ta'ki taci sai 'kunci da 'bacin rai take koda Kawu ya dawo daga kasuwa rufeshi tayi da fad'a! akan lallai sai an mayarwa da Alhaji Nura kud'insa....Kawu ya 'bata lokaci gurin nusashe ta ya d'ora da fad'in "Wallahi gwaggo idan baki daina adawa da auran nan ba sai rabo ya kashe ki kika san abinda Allah ya lullu'be a cikin alamarin to saboda haka dan Allah ki daina damuwa ki cigaba dayi wa yarinyar nan addua shi kuma Khalid Allah ya bashi daidai shi." Gwaggo jikinta yayi sanyi sosai da irin maganganun Kawun sai kawai ta hakura ta zubawa sarautar Allah ido amma a zahirin gaskiya tana tausayawa khalid ganin yanda ya 'kwallafa ransa akanta. Ummatu kuwa kamar ta zuba ruwa a 'kasa ta sha saboda dadi tunda dai har an riga an kar'bi sadakin Sa'ida sai ta kwantar da hankalinta tasan tayiwa Khalid nisa sai dai ya nemi wata kuma. Wata shida aka tsayar da maganar daurin aurana da Alhaja Nura wanda kuma a daidai lokacin Khalid zai kammala karatunsa ya dawo gida dan duk wainar da ake toyawa bashi da labari duk da suna waya da mahaifinsa amma ko kad'an bai fad'a masa komai ba. Ya kasance saura wata biyu daurin auran Alhaji Nura ya tafi Chana domin shigo da kaya kuma a qalla zaiyi kusan wata guda ko fiye da haka sosai naji rashin dadin tafiyarsa dan kusan kullum muna tare da juna a yanzu ni dashi munyi wata irin sha'kuwa kuma ina jin sonsa sosai a cikin raina saboda yana da saukin kai kuma duk abinda nake so to shima yana so wannan dalilin yasa nake marmarin auransa domin ina ganin zan samu duk wasu muradan da nake bukata a gurin d'a namiji. To koda ya tafi kusan kullum muna tare a waya yana d'auke min duk wata kewarsa dake damuna. Satinsa Uku da tafiya Khalid ya dira a gida ya dawo cikin farin ciki da nasara dan gabad'aya takardunsa sunyi kyau yanzu abinda ya rage masa aikin yi ne......Khalid 'bangaran zane-zane ya karanta duk da kafin ya fara karatun sai da aka dinga bashi shawara akan ya canza cos ya'ki yace shi wannan ne ra'ayinsa to yanzu gashi yayi ya gama sai fafutukar neman aiki shin yanzu wane company ne zai d'aukeshi aiki? wannan fargabar tasa tunda ya dawo bai zauna ba kullum yana yawon neman aiki babu labari duk inda ya nufa babu nasara sai kawai ya ajiye takardun abokinsa Salim ya samar masa adaidaita sahu ya fara ja...sai sannan hankalinsa ya kwanta dan ya tsani ya zauna garjeje dashi a gida yana d'orawa mahaifinsa wahala. *BAYAN SATI UKU* Da dawowarsa da safe ya fito da shirin fita yana tsaye a kofar dakin Gwaggo suna magana tace."Khalid sabgogi yasa har yanzu ka kasa zama na sheda maka abinda yake faruwa." Ba tare da ya bawa maganarta muhimmanci ba yace."Me kuma ya faru a gidan bayan bana nan."? Tace."Shigo ciki ka zauna muyi maganar. agogon hannunsa ya duba kafin ya tu'be takalminsa ya shiga dakin. A nutse ta kalleshi tace."Kasan an kar'bi sadakin auran Sa'ida ko."? da wani irin sauri ya kalleta bakinsa na rawa......"bangane ba gwaggo."? Cikin takaici tace."Alhaji Nura dai ya samu galaba akanka dan wata hudu da suka wuce ya bada sadaki magana tuntuni tayi nisa nake fada maka gobe ma idan Allah ya kaimu zasu kawo lefe." Wani irin gumi ne ya tsinke masa ya dinga katse goshinsa yana girgiza kansa yace."Gwaggo Alhaji Nura bai samu galaba akaina ba wallahi ni nake da galaba akansa." A sanyaye tace."Khalid kayi hakuri ka kwantar da hankalinka kaji ko watakila babu alkairi a tsakaninka da ita shiyasa Allah ya......"Gwaggo ya kike wannan maganar ne? wallahi akwai alkairi a tsakanina da ita ki daina fadar wannan maganar zuciyata zata tarwatse." Suguri tayi tana kallonsa jikinsa sai kyarma yake....Alhaji Nura ya bada sadakin auransa da Sa'ida yana zaune lallai dole ya dauki mataki dan yayi rantsuwa sai yayi aika-aika mutukar ba ta janye auran mutumin ba. Mikewa yayi ya fita Gwaggon nata kiransa ko waiwayowa baiyi ba. Tunda na doso layin na hangoshi a zaune a kofar gidan gabana yake faduwa na dinga mamakin zaman da yake a gurin shi kad'ai bayan yana da abin yi.....koda na karasa ban kalli inda yake ba na shige soron yayi saurin biyo bayana....hanya ya tare min yana min wani lalataccan kallo. Rai a 'bace nace."Meye haka ko iskancin zaka gwada min."? girgiza kansa yayi a cunkushe yace."Soyayyata kika yi wa haka ko? Aunty Sa'ida ni Khalid kika watsa wa 'kasa a ido ko ashe har kin kar'bi sadakin wancan 'katon mutumin kin barni ina dakon! soyayyarki a cikin zuciyata aunty Sa'ida ni zaki yaudara ko."? A fusace! nace."Khalid baka da hankali ko? ka dube ni ka dube ka dan Allah dan Annabi me zan samu a tare da kai? nace ka fad'a min idan na aureka me zaka bani!? me kake dashi idan na aure ka!! suwa zan nunawa nace musu wannan ne mijina."!!? cikin hargagi gami da d'aga murya take maganar tana nunashi da hannunta.....aikuwa a fusace! ya kama hannun ya murd'e! jikinsa na rawa yana huci! da zufa! yace."Ni kike fadawa wannan maganar ko."? Hannuna na fizge a tsorace nayi nufin shigewa gida...ya fizgo ni na fad'a saman kirjinsa na dinga jin kirjinsa na sama da 'kasa! "Wallahi sai na shayar dake ruwan mamaki! sai na karya alkadarin ki aunty Sa'ida kin raina ni ko? har kina nuna ni da hannu kina min kallon 'kas'kanci to ki rubuta ki ajiye cewar Khalid Namiji ne kuma Jarumi ne a cikin maza." Fizgewa nayi daga jikinsa da mugun sauri na shige gidan gabana na dukan uku-uku wannan bala'i da masifar ya isheni. Zamewa yayi ya zauna a gurin yana huci! da mayar da numfashi babu shakka zai nuna mata shi ba tsaranta bane. "Ke kuma me ya faru kika shigo kina huci."! Gwaggo ce take wannan maganar tana bin ta da kallo a lokacin data shigo gidan. Raina a 'bace nace." Gwaggo wato baki dai baki jawa Khalid kunne ba ko."? da sauri tace."Wane Khalid kuma Sa'ida a ina kuka had'u bayan tun safe ya bar gidan nan." Nace." Khalid ya dawo daga duk inda yaje sabida ya riski dawowata ya kuma tare ni a soro yana yi min wasu zantukan banza Gwaggo inaso ki ja masa kunne wallahi tallahi idan bai daina yi min shirme ba zan dauki mataki mai tsauri akansa." A sanyaye tace."Mai da wu'kar Hakima kiyi hakuri kada ki dauki mataki akansa idan ya shigo zanyi masa magana." Ajiyar zuciya na sauke na shige dakin raina duk a 'bace da irin iskancin da yaron yake min kawai ya dinga da'kumar jikina ba tare da yayi shakka ba. Sai wajejan goma da rabi ya shigo gidan dan ni har bacci ma ya soma daukata naji muryoyinsu 'kasa-'kasa suna magana...."Khalid kasan Alhaji Nura yana da kudi ina jin tsoron ta fada masa ba zaka iya sharia dashi ba." Cikin takaici da ba'kin kishi yace."Ai dama shi yayi kad'an nayi shari'a dashi da Ubansa zanyi."! Gwaggo ta bud'e bakinta tana kallonsa da fad'in "Khalid me ya kawo zagi kuma."? Yace." Kinga Gwaggo maganar nan ta isa haka Allah ba zan yarda ba." yana 'kare maganarsa ya mi'ke ya fita, gurinsu ya nufa yana wani irin tangad'i kamar wanda yasha kayan maye ya bude dakinsa ya fad'a kan katifarsa yana fitar da wani irin numfashi mai wahalar gaske. Gwaggo kuwa bayan fitarsa daga dakin addua ta shigayi masa muryarta sai rawa tace tace"Allah ka sassautawa yaron nan wannan jarraba Allah ka mu sanya masa da alkairi." Tausayi ta bani a lokacin da take adduar nayi shuru ina sauraranta har ta 'kare kusurkusur d'inta ta kwanta tare da kara redio a kusa da kunnanta. Washe gari da safe da yake Asabar ce ina karyawa na kwanta sabida na tara bacci inaso na rama....muryarta naji tana fad'in "Sa'ida kin san yau bikin 'yar gidan Jummai 'kanwata wacce muke 'yan maza zur da ita saboda haka ki tashi ki shirya mu tafi ni na gama shiryawa." Cikin bacci nace."Gwaggo kuje kawai da yamma zan shigo gidan bikin inaso nayi bacci ne." tace."To ai shikkenan zamu tafi tare da Rabi da Uwale." nace"To sai nazo." kwanciyata na gyara na cigaba da baccinta ban san lokacin data gama kujiba-kujibar ta ta fita daga dakin ba. Rana gatse-gatse ya dawo gidan domin yayi wanka Khalid sam baya son zafi shiyasa kullum sai yayi wanka sau biyu ko sau uku mussaman da zafi ballantana kuma yanzu da yake jan adaidaita sahu......shuru yaji gidan kai tsaye gurinsu ya nufa sai yaga kofar dakin mahaifiyarsa a kulle da 'kwado jallabiyar jikinsa ya cire ya dauko dan abinda yake sa sabulun wankansa ya duba gabadaya ya manta sabulunsa ya kare hannunsa rike da abun ya fito ya ajiye shi bakin rijiya kai tsaye dakin Gwaggo ya nufa daga shi sai gajeran wandon da ya bari yana so ya dauki sabulunta yayi wankan dashi dan baya so ya 'kara fita sai yayi wanka..........Gabansa yayi wani irin fad'uwa ganinta a kwance ita kadai a d'akin babu riga a jikinta tayi daurin kirji da zanin atamfa tayi kuma kwanciyar rigingine ta dogare 'kafafunta a kasa zanin jikinta ya 'bantare cinyoyinta duk a waje bacci take sosai da mafici a hannunta da alama idan zafi ya farkar da ita take firfita dashi......lafiyayyar ajiyar zuciya ya sauke idonsa 'kur a kanta yayin da yake jin wani irin abu da jarumarsa take a cikin wando! A yau ne zai nunawa mata shi Namiji ne a yau ne zai wargaza duk wani shiri da sukayi bayan baya nan, wallahi yayi rantsuwa sai ya nuna mata shi ba kanwar lasa bane. Fita yayi daga dakin da sauri yaje ya rufe babbar kofar gidan ya dawo dakin ya sa sakata kai tsaye ya durfafeta!!!!!!! *'KARSHEN FREE PEGE🥰🤝🏻* Compilied By Abubakar Saleh AlQuyraemey Whatsapp Number 08138873799 Visit www.rumbunlabarai.com For More Complete Documents *TIR'KASHI!!* *Wai shin me yake shirin faruwa ne? me Khalid zai aikata da ya kulle kofar gidan? 🤔 Tofa!! ni har na rasa bakin magana? Jama'a Khalid zai samu nasara kuwa ko kuma auntyna nasa zata iya kwatar kanta a hannunsa.....Akwai bada'kala Jama'a Khalid fa zaiyi aika-aika bayan da sadakin wani🙆🏼‍♀️.....Idan ha'kansa ya cimma ruwa wane al'amari ne zai faru a gaba shin auntynsa zata janye maganar auran Alhaji Nura ko kuwa? Wane irin matakin nasara Khalid zai taka anan gaba? Jama'a idan Alhaji Nura ya auri Sa'ida da wata matsalar me zai faru a zamantakewar auran nasu? shin anya kuwa Khalid zai iya samun galaba akanta kuwa?😅 ku muje dai zuwa labari yanzu aka fara akwai badakala a gaba.....#400 ko #600 ta biya miki bukata 'yar uwa kada kiyi ganin kyashi gurin biyan kudin littafin nan domin yana dauke da darrusa masu amfani bayan nishad'antarwa........Kuyi maza ku garzayo ku biya domin ayi tafiyar tare daku.🤝🏻* *PAID BOOKS* *NANA KHADIJA* *YARO DA KUDI* *GIMBIYA BALARABA* *BABBAN YARO* *SADAUKI OMAR* *LADIDI KWADAGA* *TSANTSAR BUTULCI* *NIDA YAYA SADAM* *'YAR BANGAR SIYASA* *DA WATA A KASA* *MADADI* *'KWARYA TABI 'KWARYA* *GA IRINTA NAN!* Wannan books din duk na kudi ne ga mai bukatar siya sai ya tuntu'bi number ta da nake WhatsApp *07084653262* *08089965176* *BINTA UMAR ABBALE*