: BABBAN YAYA Writing By Amnah El Yaqoub Dedicated to Fauziyya S Madaki Real Esha Special Gift to Its Sadeek ********************** ? ************************** ********** Ai Hausa Novels **************** *************************? ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ? ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ? ************************** Bismillah... Ina farawa da sunan Allah Mai Rahma maijin qai, BABBAN YAYA qirqirarran labari ne, yanda muka fara wannan littafi lafiya, Allah yasa mu gama lafiya, Allah ka haneni da rubuta abinda bazai amfani al'ummah ba, idan anga labari yayi daidai Dana rayuwar wata, to akasi aka samu, Allah yasa mudace A taqaice, Babban Yaya labarin soyaiya ne,yan'uwan juna makusanta, kwatsam soyaiya tashiga tsakanin su, akwai rikitarwa aciki, saikin karanta Zaki gane wanene masoyinki na gaskiya acikin samarin ki? Saikin karanta Zaki gane ta wacce hanya ne namiji zaibi Dan gujewar auren yarinyar da bayaso salin Alin batare da damuwa ba? Abubuwan sunada yawa, koda kudin ka saida rabonkaπŸ’ƒπŸ’ƒ PAID BOOK 1&2 "Wato Alhaji Umaru Naga alama saboda Ina zaune aqauye ban'isa na fadi magana a aiwatar da abinda nayi umarni ba" Daga d'ayan bangaren Wanda aka kira da Alhaji Umaru yadafe goshinsa,(πŸ€¦πŸ»β€β™‚οΈ?) waye Kuma yata6o musu Babban yayan nasu? Ajiyar zuciya ya sauke tareda gyara Zaman wayar dake kange a kunnansa yace "Yaya meyake faruwa? Kaida waye?" "Au tambayata ma kake meyake faruwa? Umaru dakai da Usmanu kunfi kowa sanin abinda kuka aikata, tayaya zaku bar yaro agabanku shekara da shekaru yana zaune babu iyali? Shekara d'ai d'ai har shekara Talatin da shida NAUFAL yana zaune yana abinda yaga Dama yaqi aure, kukuma saboda ku 'Yan boko ne kun rabu dashi yana abinda yaga Dama, ni danake Nan qauye ba zance kuyi abu kuyiba, a'a Sai abinda kukai niyya" Cikin ladabi Alhaji Umar yace "Wallahi tallahi Yaya Bahaka bane, mu kanmu muna bakin kokarin mu akansa, bamu San Yaya zamu yi masa ba, munyi munyi dashi yakawo yarinyar dayake so Amma yaqi" Cikin fishi Wanda aka kira da Yaya yace "zancen banza zancen wofi, kunje can qasar turawan dayake rayuwa ne kunganshi akame awaje daya? Tayaya yaro baligi irin NAUFAL zaku zuba masa ido? Yafada muku shi gunki ne kokuma dutsi da bazai buqaci mace ba? Jinake haka muke ganinsu a TV tsangal tsangal da gajeran wando suna tamola Waida sunan sana'ah, to Kana katse wayata, ka kirashi kafada masa cewa ni Abubakar yayan mahaifinsa Kuma me iko da fada aji acikin dangin Arabo, nace yakira yarinyar Amini na su daidai ta, idan ma 'yar bokon yake nema irinsa itama yarinyar ba'a qauye tatashi ba bare ya rainata kamar yanda ya raina ni, zan sako Maka lambarta katura masa " Alhaji Umar yace"To Yaya, insha Allah zanyi yanda kace, ga Alhaji Usman ku gaisa" Yafadi maganar yana kokarin janye wayar daga kunnansa Cikin sauri Yace "A a, barshi kawai, ai duk bakinku d'aya" daga haka yakashe wayar sa. Alhaji Umar yadago Kansa ya kalli Usman batare da yace komai ba, kallo daya zaka musu ka tabbatar su din jini daya ne, kama suke da juna sosai kamar harta 6aci, basuda jiki sosai kasancewar su asalin buzaye Alhaji Usman yace"magana yake akan Naufal ko?" Alhaji Umar ya daga masa Kai, sannan yafada masa yanda sukayi dashi, batare da damuwa ba yace" Babu damuwa, katura masa number kawai, ya kira yarinyar, idan munyi sa'ah Wannan Karon andace shikkenan, mu Dama fatanmu ace yayi auren " *** ** *** Sanye yake da Jessy ajikinsa fara tas me dogon wando,kafarsa na d'aukeda farin kambos, kunnansa d'aukeda wani Bluetooth fari me shegen kyau, jogging yake Kansa aqasa, Amma duk da haka mutane Sai magana suke masa yana daga musu hannu kasancewar sa marar son surutu, wayar sa tafara qara yana duba Screen din wayar yaga ansa My Dady, dole ya dakata da gudun dayake tareda riqe waist dinsa yana Dan qaramin haki, dago Kansa yayi tareda amsa wayar bakinsa d'aukeda sallama Sai a lokacin nasamu damar qare masa kallo, fari ne sosai ko'ina na jikinsa farine tass, hadaddan Gaye ne na fitar Hankali, yanayin tsarin idonsa ma kadai ya'isa yasa Nan take yasiye zuciyar yanmata, inde ka Kalle shi sau daya, dole saika sake waigawa domin sake kallon sa, gaida mahaifin nasa ya farayi Amma yana magana dimples dinsa suna futowa. Alhaji Umar yace "akwai number wata yarinya Habiba Dana turo ma yanzu, kakirata ku daidaita, Yaya ne yace abaka number, yarinyar aminin sace, idan kun gama daidaita wa saika samu lokaci kadawo gida a tsaida maganar aure, banason jin wata magana Kuma daga baya" Yana gama yimasa Wannan jawabin yakashe wayarsa yasan dalilin dayasa Dady yakashe wayarsa, duk lokacin dasuka masa maganar aure Sai yasan irin maganar da yayi yaroqesu akan su qara masa lokaci, to lokaci har yanzu shiru yaqi zuwa πŸ€” Wata zazzafar is'ka ya furzar daga bakinsa, cikin wata daddad'ar murya wadda daqyar zakaji meyake fad'a yace "ita Kuma wannan ta wacce hanya zanbi narabu da'ita?" wani tunani yayi, Nan take ya dauki shawarar zuciyar sa yayi Dialing number da'aka turo masa ta Habiba Bugu uku ta dauka, batare da tayi sallama ba tace "Hello waye" Sai yaji wani iri banbarakwai, kamar shi ace yakira waya Ana tambayarsa waye, Kuma ba kowa ke tambayar sa waye ba Sai budurwa, shida a koda yaushe yanmata sune suke bibiyarsa saboda su samu kusanci dashi Amma basa gabansa,ya tabbatar inda ace tasan asalin Wanda yake kiranta to babu makawa zata Iya zuba ruwa aqasa Tasha saboda tsananin murna. Jin shiru har yanzu ba'ayi magana ba yasa tace "Hello wake magana ne?" Saida yaja wasu second sannan yamotsa pink lips dinsa yace "Sunana Naufal Umar Arabo" Saida taji yace Arabo sannan tace "Okay, ko kaine Yaron Dan'uwan Alhaji Habu Wanda yake zaune a qauye?" "Yes" Shine kawai abinda yace Daga Nata bangaren tace "Ai sunyi magana da Abbanah, yace zai turomin d'ansa naganshi idan yamin Sai manya su shiga cikin maganar" (πŸ˜±πŸ˜‚) Baqin ciki ne yakama shi,ya yatsina fuskar sa, yaso ace yayi tozali da wannan yarinyar yaga me take taqama dashi har haka, har shi zatacewa idan yayi mata? Takuwa San waye shi? Lumshe Idonsa yayi, hakan da yayi saiya Bawa gashin Idonsa damar bayyana, Zara-Zara dasu dogaye kamar na mace, fuskar Nan tasa murtuk babu alamar fara'ah yace "Yes, nine" Itama tace "Sai cewa kake kaine kaine, kakasa cewa komai, kana magana kamar me koyon magana, yanda baka son had'in Nan nimafa baso nake ba, karkayi tsammanin sonake, kanamin magana daqyar Kanata wani yauqi saikace mace, fadamin zakai yaushe zaka zo naganka, bawai Kiran waya ba, saboda ni ba'acemin zaka kirani ba, ance min ne zaka zo naganka ko zakamin " Zuwa wannan lokacin Kam ransa yagama 6aci,(πŸ˜–πŸ˜–) Amma wani bangaren na zuciyarsa dad'i yakeji, ko babu komai yasan yarinyar bazata bashi matsala wajan rabuwar su ba tunda itama bata so, sassauta muryarsa yayi, ya dedeta Kansa, kamar me koyon magana yafara magana a rarrabe"Mene..ne yauqi?" "Uhm au bakama San menene yauqi ba? Tabdi jam, Allah kenan mehada budurwa da samari Kala Kala,yau Kuma da Wanda nahadu kenan, nikuwa naso ace naganka bawan Allah,Inga mutumin dabai San menene yauqi ba, kafadamin yaushe zaka zo?" Be damu da wannan dogon surutun Nata ba, asali ma so yake su qarqareta ayau dinnan kowa yakama gabansa, ahankali yace"ni... ni banda lokacin zuwa" Daga Nata bangaren tace "to Ahaka zamuyi aure bakada lokacin kaina?" Wani irin murmushin gefen baki yayi, cikin ransa yace anzo wajan, a fili kuwa saiyace "Banda lokaci, Ina wajan neman kudi, kinsan kudi sune gaba da komai, ni kaina banda lokacin kaina bare in samu lokacin wani, kawai neman kudi nasa agabana" Tace "Okay, kana so kacemin kudi sune abin so fiye da komai arayuwarka?" "No, ba rayuwa ta kadai ba, harma da rayuwar Wanda yake kokarin shigo wa cikin rayuwa ta, kudi sune gaba da komai awajena" Tace "to Malam Naufal Umar Arabo, inban manta ba haka kacemin sunanka ko? to Ina ganin Bama Sai kazo ba, kayi zamanka kawai, Allah yahada kowa da rabonsa" qit takashe wayar ta Baisan lokacin da wani farinciki ya lullubeshi ba, har dimples dinsa suka lotsa, cikin murna yace "yessss" sannan yaci gaba da Jogging dinsa *** ** *** Labarinsu Alhaji Abubakar Arabo,Alhaji Umar Arabo, dakuma Alhaji Usman Arabo, uwarsu daya ubansu daya, 'Yan asalin qasar Niger ne, buzayen dasuke rayuwa cikin Sahara, sunada mutuqar dukiya da Tarin shanu, sau Tari mutanan Nigeria suna zuwa wajan su siyan shanu domin su kiwata su siyar dasu da tsada, kasancewar inda suke rayuwa babu isasshen abincin dabobi, daga baya sukai hijra suka dawo Nan Nigeria, sukaci gaba da juya dukiyar su har Allah yayi mata Albarka suka zama manyan masu kudi da ake damawa dasu ayau. Alhaji Abubakar shine Babba, suna kiransa Baba Habu, yana zaune a Jigawa shida matarsa da yaransa maza guda biyu sa'annin Naufal ne Amma sun dade da aure harma sunada yaransu Saikuma Alhaji Umar shine na biyu, suna kiransa da Dady yanada Yara guda bakwai, NAUFAL shine Babba, Suna kiransa da Babban Yaya, Sai Yan biyu maza,Sa'ad da Sa'eed, Sai Anty Maryam, tayi aure tanada yaro daya,me sunan Naufal, suna kiransa da junior, Sai Yan biyu mata, intisar da ihsan, saikuma yar auta WAHEEDA Sai Alhaji Usman Arabo, shine Dan qaramin su,suna kiransa da Uncle Usman, Allah bai bashi haihuwa ba, yanada matarsa guda daya, suna cemata Hajiya Anty, ma'aikaciyar Asbiti ce Dukansu mutum ukun Nan Abubakar, Umar, Usman, suna kyautatawa junansu, matansu na can Niger sune de har yanzu atare dasu, suna mutuqar girmama juna, gaba dayansu kama suke da juna daga matan, har mazan, dakuma yayansu, duk fararene, saide na wani yafi wani, Amma dukansu farare ne, kana ganinsu zaka San buzaye ne na asali, tsabar kyawun dasuke dashi ne yasa ake Kiran Family din nasu da Suna (Arab Family) , Amma dasuka dawo Nan gida Nigeria, Sai Yan Nigeria suke cewa Arabo Family πŸ˜ƒ Kamar yanda nafada Naufal shine babba acikin yaran Alhaji Umar (Dady) shekararsa Talatin da shida, beyi aure ba, iyayen sunaso yayi aure kasancewar sa babba a gidan, yana kula da qannansa yanda me karatu baya zato, shiyasa ko wani abu ne yafaru saide kawai iyayen su fada masa, shikuma zai warware komai, kwata kwata baya wasa da yan'uwan nasa, idan kaga ya ware yana fira wasa da dariya to da abokan sa ne, musanman yayan Baba Habu dasuke jigawa, koda yaushe fuskarsa a daure take, bala'in tsoransa sukeji musanman qannansa mata, kana laifi kadan zai daka Maka tsawa, shiyasa suna ganinsa kowacce take shiga taitayinta, babu ruwansa duk wacce tayi masa laifi zaneta yake, suna komai duk abinda suke so, saide yahanasu kula Samari, yahanasu saka mayafi, saide Hijab, Kuma suna kiyayewa mutum daya ce take bashi ciwon Kai acikin qannansa, itace auta WAHEEDA, itace tafara kiransa da BABBAN YAYA, daga Nan kowa yake fada masa, babu Wanda zakaji yace Yaya Naufal, saide BABBAN YAYA.πŸ‘ŒπŸ» Cikakken Dan qwallon qafa ne Wanda akeji dashi afadin qasar tamu ta Nigeria dakuma kewayen ta, lokacin daya gama Degree dinsa na biyu, (Masters) iyayen sunso yayi aiki a qarqashinsu, domin su qara habbaka kasuwancin su, Amma BABBAN YAYA yace inaaa! Shifa harkar qwallo zai fara, saboda Dama can tun yana qarami abinda yake so kenan, daga Alhaji Habu na qauye har mahaifin sa Alhaji Umar Qin bashi goyon baya sukayi, daqyar Alhaji Usman yadage akan su harya shawo kansu suka yarda, da farko Yan kano pillars yabugawa Ball, daga baya wata qasar ta daukeshi, daga Nan Kuma yakoma qasar Spain, Bayan wasu shekaru yakoma qasar dayake a yanzu yana buga musu Ball inda yake daukar albashin sa Mai tsoka duk sati. Lokacin dazai fara Ball babu sunan daya fad'o masa Arai sai Wanda fitnanniyar qanwar sa WAHEEDA tasaka masa, BIG BROTHER, shiyasa jikin Jessy dinsa, p-cap dinsa,sunan BIG BROTHER ne ajiki, Yan gari, Yan unguwa, fan's dinsa na ko'ina kowa Big Brother yake ce masa, inde yashiga cikin jama'ah kawai haquri yake, saboda yanada masoya masu dimbin yawa, kawai Yan gidansu ne suke kiransa da BABBAN YAYA, Amma jama'ah kowa da kowa Big Brother ake ce masa,yanmata kuwa kullum cikin kiransa suke, yana alfahri da hakan. Iyayensa sunaso yayi aure saboda shekaru irin nasa, Amma yace shi har yanzu baiga wacce ta kwanta masa ba, tun yana qarya yana cewa zai kawo wacce yake so aqara masa lokaci, har iyayen suka dawo daga rakiyarsa suka fara hadashi da yaran abokai da Kuma yan'uwa, Amma har yanzu duk wadda aka hadashi da'ita yasan irin dabarar dazai mata Dan su rabu cikin hikima, kamar de yanda ya kasance a tsakanin sa da Habiba Yanzu πŸ€ͺ Duk cikin yanmatan da'ake hadashi dasu babu wadda yataba baiyana mata Kansa, inde yakira wayar su yana fada musu cewa sunansa Naufal, baya cewa Big Brother saboda yasan cewa muddin yafadi wannan sunan, to babu Wanda bai sanshi ba, wannan kenan *** *** *** Tafe suke hannunta dauke da wani yaro Wanda bai wuce shekara uku ba, Sanye take da hijab pink colour, me hula, ta gaban hijabin kadai zaka iya sanin cewa Allah yayi mata tarin suma da yawa, kasancewar wuyan yayi mata yawa kadan, yarinya ce bazata wuce 18 years ba, ranar datake dukansu itada Yaron yasa ta yatsina fuska, Amma duk da haka kyawun fuskarta yana Nan, duk da babu kwalliya kodaya a fuskar, Sai haki take da alama Yaron yamata nauyi, suna zuwa bakin get din gidansu ta sauke Yaron, kudi tafuto dashi daga cikin handbag taware 5k tabawa Yaron sannan taja hannun sa suka qarasa gida, babu kowa afalon nasu, Kai tsaye dakinsu tashige, mutum uku ne zaune a Dakin, 'Yan biyu daya tana yiwa daya tsifa, saikuma wata Babba tana duba littafin azkar, gaba dayansu kama suke da juna, kana ganinsu kasan jini daya ne, hijabin jikinta ta cire ta wullar dashi anan, lokaci daya tsantsar dirin jikinta ya baiyana, mace ce har mace, gata yar qarama Amma Allah yamata baiwar kyakykyawan jiki. Yaron yatafi da gudu wajan mamansa yace "Momy munje Kuma anbamu kudi da yawa, Nima anty Waheeda tabani, kingani?" ya qarasa maganar yana nuna mata kudin hannun sa Murmushi tayi tace "Lalle Waheeda kice kudi kuka samo keda junior" Zama tayi a bakin gadon tareda cire ribom din kanta, hakan yabawa dogon gashinta damar zubowa gadon Bayan ta Tace "eh Anty maryam, dubu goma aka bamu, shine naraba mana" Kafin wadda aka kira da Anty Maryam tayi magana, daya daga cikin Yan biyu tace "Qarya kike Waheeda, Anty wallahi qarya take, kawai cutar Yaron tayi, kamar bakisan halin Waheeda ba, Allah qwace masa kudin zatayi" Cikin rashin kunya ta kalli me maganar, duk tsananin kamar dasuke kasancewar su identical twins Sarai Waheeda take ganesu, tace "to Ihsan na qwace din, ai tare aka aikemu da junior din ko? Kiyi abinda zakiyi" Anty Maryam ta kalleta tareda riqe ha6a, tace "lalle Waheeda wuyanki ya'isa yanka, yayun naki kike fadawa haka?" Wadda ake yiwa tsifar ce tatashi ta nufi Waheeda tace "Na hanaki daukar min hijabi na Amma kinqi yarda ko, tsabar masifa da naci kinada hijabai bazaki saka ba kin goge su kin 6oye saide ki dinga daukar namu kina sakawa saboda Kin raina mana Hankali, nayi Miki last warning karki sake daukar min hijab, sannan Ihsan ba sa'arki bace karki sake mata rashin kunya " Cikin tsiwa tace"wallahi yanzu nafara saka hijabi saide in bangani ba, baki Isa kimin in qyale kiba intisar" Anty Maryam tace "Waheeda kanki daya kuwa? Dama rashin kunyar Taki haryakai haka?" Ihsan tace "rabu da'ita Anty, ai taga kanmu daya ne,Mp muke itama shi take yi, brezia muke sakawa itama shi take sakawa,taga ta girma tafimu nonuwa, tayi tsawon qafa, Gani take shekarunma daya muke da'ita, yau kuwa zakici ubanki, zaki San kin mana rashin kunya" Tashi tayi tsaye ta kallesu ta watsar tace "ai Dama ba yau kuka fara hademin Kai ba, Naga su Sa'ad ma qarewa, balle ku Yan biyun qarshan zamani, qarqari kumin taron dangi kumin duka, to bazaku birgeni ba saikun kasheni kun kaiwa uwata gawata" Anty Maryam tatashi tsaye tace "lalle Waheeda kullum girma kike kina sake zama marar kunya, zan fadawa ummah abin naki yayi yawa, yanzu har takai su Yaya Sa'ad ma sunansu kike fada" tana fadar haka tafice daga Dakin cikin fishi Ihsan ta kalli Intisar, basu tsaya wata wataba suka rufe Waheeda da duka, intisar takama gashin ta tanaja, Ihsan kuwa Sai dukanta take, dama haka suke, hadin kaine dasu sosai, duk lokacin da Waheeda tamusu rashin kunya haduwa suke suyi mata shegen duka Hajiya Anty ce tashigo gidan, tana Sanye da kayan likitoci komai fari, tana Sanye da glass fari a'idonta, kana ganinta kaga mace yar Gayu, da alama daga Asbiti take wajan aikinta, da kukan Waheeda tafara cin Karo, Kai tsaye Dakin nasu ta nufa, 'Yan biyu suna ganinta suka daina Dukan Waheeda, haka tadago kanta idonnan yayi jajir tace "Kuma wallahi saina Rama, bashi kuka dauka" Hajiya Anty batace dasu komai ba taja Dakin tarufe, tawuce wajan ummah, Sai a lokacin ummah tashigo Dakin nasu taji ba'asin fadan, da alama Hajiya Anty ce ta turo ta, Dan lokacin dazata shiga Dakin nasu ma mita take tana cewa fitinar Waheeda ta isheta☹️ Da yamma sukai baqi daga qauye, a lokacin hajiya Anty tana nan bata tafi ba, megadi ne yayi musu jagora har cikin falon gidan, Anty Maryam de Takoma gidanta, Amma gaba dayansu yaran suna Nan, 'Yan biyu suna zaune waje daya suna ganin wani abu a wayar ihsan, Waheeda kuwa tana zaune agefe cikin kujera ita daya, tunda 'yan'uwan suka daketa taketa kumburi, taso ace ummah da Hajiya Anty basa Nan, dasai tahada wa 'yanbiyu wata muguntar da bazasu taba mantawa da'ita ba, yanda ta zauna waje daya tayi shiru zaka rantse wata kamilar yarinya ce, saboda ta nutsu sosai kamar ba'ita ba,itace tafara tashi takawo musu lemuka da ruwa, sannan ta gaishe su, aikuwa suka amsa cikin girmama wa, tasake komawa wajan zamanta ta zauna, Ummah takalle su cikin sakin fuska tace "Saide kuyi hakuri fa, Amma bamu gane Kuba" Namijin ne yafara dariya yace "Hajiya ai 'yan'uwan kune daga wani gari Kaburma, ai Alhaji Habu ne yace duk lokacin da muka shigo Garin naku, mu qaraso mu gaisa nida iyalina, aini kamar qani nake awajansa" yafadi maganar yana Kallan Waheeda Waheeda ta Kalle shi dakyau, Bama qanin bane kenan, kama ce, tunda yace kamar qani yake a wajan Baba Habu, Kai Shima de Baba Habu da yayime-yayime yake, ita Kuma umma Sai washe musu baki take Hajiya Anty tace "Amma kun kyauta wallahi, ai Gara daban wuce gida ba, yanzu gashi munga juna" Matar datake gefen namijin tace "Eh wallahi, ai Baba Habu akwai zumunci, Amma wadannan Yan biyu ne ko?" Ta qarasa maganar tana Kallan Yan biyu Dariya sukayi sannan suka amsa mata, Tajuya tasake Kallan gefen da Waheeda take zaune tace "kekuma fa qawata kinyi shiru babu ruwanki da kowa" 'yanbiyu ne suka hada ido suka kwashe da dariya, Wai Waheeda ce babu ruwanta, shine abunda ya basu dariya Matar tace "yakuke mata dariya, ai Naga tayi shiru da alama zatayi hakuri,qawata ya sunanki?" Waheeda tayi murmushi tace"sunana Waheeda" Kallan mijinta tayi tace "Baban Halima kaji suna me dadi, idan nasake haihuwa Nima ka sakawa yarmu irin wannan sunan" Dariya yayi, ya kalli Yan biyu, ya kalli Waheeda, yace "yanzu Nan duk 'ya'yanane?" Dariya sukayi kawai, babu wadda tace masa komai, yace "toku Yan tagwaye wayece babba acikin ku?" Ihsan tace "nice babba, Sai Intisar, Sai qanwarmu Waheeda" Washe baki yayi yace "ikon Allah kenan, toke ashe kece Gambon su" Waheeda tace "Uhm..." Daga Nan tatashi tayi daki Matarsa tace "Allah sarki, kunga ita tatafi daki ma babu ruwanta baiwar Allah, Baban Halima Bari naje wajanta musha hira" Tatashi tabi Bayan Waheeda, duk yanda taso share matar hakan bai iyu ba, Dan dolenta tasaki jiki da'ita suka Sha hirarsu, Sai yamma lis suka tafi, Hajiya Anty taje gidanta takawo wa matar atamfa da kudi, ummah Kuma tabasu kayan abinci sannan tasa driver yamaidasu har gida. Da daddare suna zaune afalo gaba dayansu, Ummah da Yanbiyu maza Wanda suke bin Babban Yaya, Sa'ad da Sa'eed,, saikuma yanbiyu mata su Ihsan, kowa Assignment dinsa yakeyi, mazan ne daya yana kallo a TV daya yana danna wayarsa, Sa'eed ne ya kalli Waheeda yace "ke tashi ki daukomin bread a kitchen, yana Nan akan fridge" Hankalinta yanakan rubutun assignment dinta tace "qarami ko babba?" Lokaci daya shida Dan'uwan nasa suka kalleta, mamaki ya kama Sa'eed, harshi zai aiki yarinyar Nan Amma tana tambayar shi qarami ko babba? Miqewa yayi tsaye yanufeta, tana dago kanta ta ganshi yanufota tatashi da gudu tayi kitchen, yanda take gudun yasa dogon gashin kanta yake bazuwa a fuskarta,hips dinta kuwa Sai rawa yake, haka tadinga tsaki cikin ranta, saboda bata so idan tana tafiya taji suna rawa Waheeda kyakykyawa ce ta qarshe, tanada kyau Wanda kallo daya zaka mata kagano hakan,duk cikin yan'uwanta tafi kowa kama da Babban Yaya, yanda yake magana dimples suna futowa haka itama, musanman idan tayi dariya, kana ganin ta ka ganshi, shiyasa ko ba'a fadaba inde kagansu basai ka tambayi waceba, kaima kasan jininsa ce, kamar su tayi yawa, saide basa zama inuwa daya, baya sakar mata fuska, inde tayi laifi tana ganinsa jikinta yake rawa, saboda tasan watan azabar ta yakama, tayi laifi yakamata ya daketa hakan bazai Hana gobe tasake yin wani laifin ba,babu Wanda bai Santa ba a school dinsu, kana cewa Waheeda Virus za'a nunama ita, wannan shine Nikname dinta, dazaran tayi laifi anyi mata hukunci batada wata Sara saide tace baza'a birgeta ba Sai an kashe ta ankaiwa Ummah gawarta 🀣, Amma bata taba fadawa Babban Yaya ba, saboda tasan karonsu babu dadi, Amma yasani Sarai tana fadawa mutane hakan. Waheeda tanada kyawun sura, hips dinta da breast dinta yafi qarfin shekarun ta, harma tafi yan'uwan Nata, Kuma tana tafiya suna rawa, sauqin ta daya dokar da Babban Yaya yakafa musu tasaka hijabs. Washe gari Sunday babu makaranta, gaba dayansu suna tareda Ummah a kitchen suna hada breakfast, gaba dayansu tasosu take su shiga kitchen tare, wani lokacin Kuma tabarsu su kadai suyi, wayar Ummah ce tafara qara, tana dubawa taga Baba Habu ne daga jigawa yake kiranta, cikin mamaki tace "Yaya Habu da wannna safiyar lafiya kuwa?" Dauka tayi, Bayan sun gaisa yace "munyi magana da Malam Iliyasu, Dan kaburma, Wanda naturo su suka kawo muku ziyara jiya, yayimin waya yanaso abashi auren gambo" Umma duk saita kasa gane kan maganar tasa, tace "Wacece gambo Kuma Yaya?" "gambo nawace daku Binta? Gambo de qanwar yanbiyu, Waheeda, yacemin yanaso abashi ita yaqara ta biyu" Ummah tayi murmushi tace "Haba Yaya, ai tsakanin da kunya, abar maganar Nan kawai, jiya fa bakaga yanda matarsa tasake da yaran Nan ba, musanman ma Waheeda, ta daukemu kamar yan'uwa, Kuma yanzu taji mun dauki 'ya mun Bawa mijinta ai abun babu dadi Yaya" "a a yazakice babu dadi, ai be haramta ba, zai iya auren ta, Sai suyi zamansu, kude bakwa so yaranku su rayu a qauye, kiyi magana da yarinyar idan tana so shikkenan Sai awanketa a kaita Dakin mijinta" Umma ba tasake musu dashi ba, tace masa "to shikkenan Yaya, Allah ya tabbatar da Alkhairi" daga Nan ta kashe wayar Yanbiyu ne suka kalleta, Intisar tace "Ummah Wai meyake faruwa?" Ummah tace "Ina baqinmu najiya, Wanda su kazo daga kaburma?, to shine yace Yanaso abashi Waheeda, zai aure ta, shikuma yarasa wazaiso Sai wannan shashashar" Yanbiyu suka kwashe da dariya Cikin sauri tadago kanta ta kalli Ummah tace "Tabdi, Amma Yama raina min Hankali, yana Kaburma yarasa wazai Burma aqauyensu Saini? Ni wallahi Bana sonsa" Ummah tace "aikuwa Yaya Habu yace inde kin amince za'a bashi" "Ummah Bana sonsa, Kuma ai Babban Yaya yahanamu kula kowa" Da wannan maganar Tata Ummah ta gamsu, saboda tasan Burin yayan nasu bai wuce ace yaga sunyi karatu Mai tsawo ba. Washe gari da safe, qarfe bakwai daidai, aharabar gidan tayi musu,gaba daya compound din gidan interlock ne, Sai wasu manyan motoci masu numfashi guda hudu dasuke parking space, daga can Gefe Kuma wani waje ne aka ware aka qawata shi da grass masu yawa, Sai ball dasuke zube a wajan, da alama suna buga ball ne wani lokacin. kowacce tana Sanye da uniform dinta, uniform din yayi musu kyau sosai musamman Waheeda, farar Riga ce me dogon hannu Wanda yake d'aukeda links,tareda Dan qaramin hijab Wanda da kadan yarufe musu breast dinsu, Sai siket ruwan toka da kadan ya wuce gwiwarsu, Bai sakko qasa sosai ba kasancewar makarantar bata musulmi bace, Yan biyu Kam sun saka doguwar safa fara, taboye musu qafarsu, Waheeda kuwa bata saka safar ba Shiyasa farar qafarta ta baiyana sosai tamkar baturiya, safar tana hannunta, saikuma school bag dinta me shegen kyau data rataya a hannunta guda daya, Hips dinta ya futo sosai acikin siket din dukda buje ne, dukansu babu me dankwali saide hijabin kowa akwai hula ajiki, ta Bayan hijab dinta kuwa kana iya hango duhun gashin kanta Wanda ta nannadeshi tayi acuci maza dashi. bataje kusa da yan biyu ba,Dan tasan bakoda yaushe suke zama inuwa daya ba Driver ne da Kansa yabude musu Bayan motar suka shiga, yarufe sannan yaja sukabar harabar gidan, yana sauke su a makaranta yajuyo, Dama haka yake idan ya sauke su juyawa yake, saikuma an tashi zaizo ya dauke su. Kowa Class dinsa ya nufa, yanbiyu suka nufi Ss3 duka su biyun, ita Kuma Waheeda tayi Ss2, takusa shiga aji Aryan yasha gabanta, cikin sauri taja baya ta tsaya tace "Haba Aryan miye hakan?" Yanbiyu suka juya suka kalleta, sukayi qwafa tareda shigewa aji, jiya jiyan Nan tagama cewa Ummah Babban Yaya yahanasu kula Samari, saboda Dan Kaburma yace yana sonta, Amma gashinan kullum saita kula wannan tatsitsin Yaron me kama da lagwani, sunmata magana akansa Amma taqi ji, ajinsu daya itada Yaron, saboda maza da mata ahade suke, saide kowa da layinsa. Hannunta yakama suka shiga cikin ajin, ko kadan batayi yunkurin qwace hannunta ba, ajin babu kowa saisu kadai, kasancewar sun shigo da wuri, Kallan ta yayi yace "Waheeda jiya kwana nayi Ina mafarkinki, Kuma kinsan de bazan iya Bari har Aunty tashigo ajin Nan batare danayi tozali da kyakykyawar fuskar ki ba" Fararen idanunta tajuya tace "Allah da gaske? To in hakane Bani labarin mafarkin Naka" "bazan baki labarin mafarkin danayi ba saikinmin alqawari Zaki barni na tabbatar da abunda yafaru acikin mafarkina" Tayi tunanin wani labarin daban zai bata, Kai tsaye tace "nayima, Ina jinka" Hannunta yasake kamawa duka biyun yana shafa tafin hannunta, yarage murya cikin sigar rada yace "Waheeda Ina sonki sosai, karki Bari arabamu kinji" ya qarasa maganar yana turata jikin bango, idanun tane sukai wuri-wuri tafara kallon qwayar Idonsa, tace "Aryan miye hakan ne? Mekake yi haka?" Kallan idonta yayi yace "abinda nagani amafarki zan tabbatar dashi a yanzu" yana gama fadar haka ya Dora hannunsa akan Boobs dinta yamatsa da qarfi, lokaci daya taji wani irin shock ya kamata, tunda take ba'a taba taba mata nono ba Sai yau, kokarin dauke masa hannunsa take daga qirjinta Amma takasa saboda yanda ya musu ruqo Bana wasa ba, kana ganin yanda yake matsawa da qarfi kasan sabon shiga ne, hannunsa guda daya tabige saboda azabar zafin datake ji, maimakon yasake ta saiya maida hannun kanta, ya riqe tudun gashinta da tayi acuci maza dashi yahade bakinsu waje daya (😱) Adede lokacin Uncle Tunde yazo wucewa ta Bayan window na ajin, anan yayi tozali dasu, ihu yasaka yana kururuwa tare da nuna su Waheeda da hannu, Nan da Nan malamai suka taru, Kai tsaye office din Director aka tafi dasu,kan kace me, har labari ya watsu cikin makaranta, saida aka kira yanbiyu agabansu aka kwantar da Waheeda da Aryan aka zanesu, sannan director da Kansa yace ya Koresu daga makaranta, da'ita da Aryan dasu kansu Yan biyun, yace baya buqatar ahalinsu acikin makarantar sa Kuka Yanbiyu suka fara, suna bashi hakuri, idanunsu yayi jajir kasance warsu farare, Amma Haka sukaqi hakura, Waheeda tatashi takade jikinta tace "aikin banza aikin wofi,babu tambaya babu komai kawai za'a rufe mutum da duka,kukuma kun tsaya Sai wani koke-koke kuke Kuna basu haquri, ai bazaku nunamin ranku yabaci ba saikun kasheni kun kaiwa uwata gawata, idan kun gama kukan saiku taho mutafi" tana fadar haka tafice daga office din, babu Wanda yamata magana acikin malaman, saboda sunsan batada kunya, Waheeda Virus zata fadi abinda yafi haka. a bakin titi suka hadu da'ita,basuce mata komai ba Sai sharar hawaye kawai suke, itace ta tare musu adedeta suka shiga, haka Kuma itace ta fada masa inda zai kaisu, har lokacin yanbiyu kawai hawaye suke sharewa. Amma kana Kallan fuskar su kasan cewa akusa suke, sun cika sunyi fam, kawai neman fashewa suke, suna hanya Sai tsaki take saki ita kadai, saboda gaba daya breast dinta bala'in zafi suke mata,damuwar ta daya, kar Babban Yaya yaji, ta tabbatar idan yaji wannan labarin ta mutu! sukuma yanbiyu sunyi tunanin dasu take wannan tsakin, saboda haka Saita qara tunzura su, Ana ajiyesu daga napep din tayi gaba, suka biyo bayanta tajuya taga yanda suke tafiya atsorace, ita kanta tsoron yanda zatayi bayanin abinda ta aikata take yi bare Kuma su, Amma yanda taga jikin Intisar yana rawa Sai abun yabata haushi, lokaci daya tasaki wani tsaki zataci gaba da tafiya Yanbiyu suka hada ido, dama gashi taja ankoresu daga makaranta, aikuwa basu tsaya sauraren komai ba suka rufeta da duka, megadi hankalinsa yanakan radio Sai ihun Waheeda yajuyo, cikin sauri yanufesu yafara rabiya Ummah tana zaune afalo tana break fast, tunda su Waheeda suka tafi school Sai yanzu tasamu ta zauna tana cin abinci, wayarta dake Gefe ne tayi qara, number Hauwa'u tagani matar Iliyasu Dan Kaburma, ta dauka suka gaisa cikeda kulawa, umma tace "Hauwa ashede Zaki kiramu, yagida yame gidan naki dasu Halima?" Hauwa tayi dariya tace "Hajiya wanne megida? Ai kwanan mu daya da zuwa garinku tunda muka dawo narasa gane Kansa, Sai nemana yake da tashin Hankali Ina rabuwa dashi, qarshe ma yace natafi gidanmu ya sallameni, Sai daga baya nakeji ashe neman aure yake, shiyasa yasakeni, ai Bama tare Ina gidanmu hajiya " Gaban Ummah ne yayi mummunar faduwa, haqiqa idan zancen Hauwa'u ya zama gaskiya to akan Waheeda mijinta yasake ta, tunda shine yayiwa baba Habu magana yana son yaqara auren, salati tafara a fili takasa dainawa har Hauwa'u ta kashe wayar Dan itakan tayi tunanin saboda zancen sakin da aka mata ne yasa Ummah wannan dogon salatin πŸ˜‚ Wayarce tasake qara, sunansa ne yake yawo akan screen din wayar NAUFAL SON,tayi tunanin Hauwa'u ce tasake kira shiyasa Bata duba taga me Kiran ba kawai ta daga, megadi ne yashigo da gudu yana fadin"Hajiya! Hajiya!! Hajiya yarafa suna harabar gida suna fada, gaba dayansu suna Dukan qanwar tasu, narabasu sunqi rabuwa" Ummah batace komai ba tafuto compound din gidan anan taga yanbiyu suna kuka suna Dukan Waheeda, jikin Ummah har rawa yake saboda bata gama fita daga alhinin labarin da Hauwa'u tabata ba na saki,tsawa ta daka musu "Intisar, Ihsan miye hakane? Meta muku?" Cikin shashshekar kuka Ihsan tace "Ummah kamata akai da saurayinta a aji yana shan bakinta, shine director yakoremu gaba dayanmu, Kuma yace baya son ganin ahlinmu acikin makarantar sa" Lokaci daya idanun Ummah yakawo ruwa, cikin rawar murya tace "innalillahi wa inna ilaihirraji'una Waheeda!!!" Duk abinda yake faruwa Babban Yaya yanaji ta wayar, saboda bai kashe ba, ita Kuma Ummah tama manta ta daga waya, yana jin yanda muryarta take rawa alamun tana gab da fashewa da Kuka yayi sauri yakashe wayar To.... da alamade yau sarar Waheeda zata tabbata, za'a kashe ta akaiwa Ummah gawarta πŸ˜‚πŸ€£ To masu karatu, Yaya kukaji wannan chapter? 200 ne kacal πŸ‘ŒπŸ» VIP 400 posting biyu a rana Kullum zamu dinga posting insha Allah harmu gama Duk wanda ya shirya biya tun yanzu ya tuntu6i wannan numberπŸ‘‡πŸ» 08033300034 Fan's ya kwana biyu? Amnah El~Yaqoub ✍πŸ? 1/28/22, 20:49 - Ummi TandamaπŸ˜‡: BABBAN YAYA Writing By Amnah El Yaqoub Like my Page On Facebook πŸ‘‡πŸ» https://www.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493/ 3&4 Wajan training yake shirin tafiya saboda after 2 day's akwai match din dazasu buga a Qatar, dafe Kansa kawai yayi,πŸ€¦πŸ»β€β™‚οΈ? yarasa Yaya zaiyi da wannan yarinyar, dole gida zai tafi yaje ya dauki mataki akan maganar, tun kafin baqin cikinta yakashe musu uwa Gara yaje yayi maganinta Wayarsa ya dauka yayi booking flight sannan yashiga toilet a gurguje yayi wanka, yafuto daureda towel a qugunsa, gaba daya jikinsa a murde yake musanman hannun sa, kasancewar sa farin mutum Sai hakan yaqara wa lallausan gashin qirjinsa kwanciya akan faffadan qirjin nasa, fatar sa Sai glowing take tana wani irin qyalli saboda yanda hutu ya ratsa ta,towel din dake jikinsa yacire ya wullashi kan gadon πŸ™ˆπŸ™ˆ Sannna yafara feshe ilahirin jikinsa da perfume Wandon jeans yasaka Amma be sakko masa har can qasa ba, tsawon Wandon be qarasa har qasa ba, daga gwiwar Wandon Kuma yadan tattare kadan, yasaka farar Riga me hadeda hula, ya dauki Kambos dinsa fari yasaka, dakuma facemaks baqi, banda baqin gashin Kansa dakuma baqin maks din daya saka babu wani abu baqi atare dashi brief case dinsa ya duba, yana ganin ta yabude ciki yaqara gyarawa dollars din dasuke ciki zama, sannan yarufe ko'ina ya futo daga gidan. *** ** *** Dago kanta tayi ta kalli Ummah, cikin kuka tace "Ummah wallahi qarya suke, ni babu Wanda yasha bakina, Allah Ummah qarya suke miki" Ummah ta wanka mata Mari tace "ashe bakida kunya yayun naki kike cewa suna miki qarya?, innalillahi wa inna ilaihirraji'un yanzu Waheeda har kinsan kibawa namiji baki yasha?" ta qarasa maganar tana zama aqasan compound din, yanbiyu suka kamata suna bata haquri sannan suka jata domin su qarasa falo , tafiya suke Amma Ummah gaban ta banda faduwa babu abinda yake,tana tunanin Anya kuwa Waheeda bazata saka mata hawan jini ba wata Rana? Sai yanzu tasake yarda da irin yanda Babban Yaya yake musu tsauri akan samari yaran, yanzu ma da aka hanasu kula samari yarinya tana kiss idan kuma anbasu damar kula samari menene zai faru? πŸ€” To Amma Yaya zatayi? Idan ta tsine mata ma sake tambadewa zatayi, saide kawai tayi addu'ah Allah ya shirya mata ita Suna qarasawa falo daki Ummah ta wuce, suma yanbiyu suka wuce dakinsu, Waheeda kuwa Dakin Ummah ta wuce ta tsugunna tana bata haquri kamar tagari, duk abinda yafaru can Qasan ranta wani irin Sanyi takeji tunda ba taga Ummah ta dauki waya ta fadawa Babban Yaya ba (πŸ€£πŸ˜‚) Daqyar tasamu tashawo kan Ummah tayi hakuri, Amma tabbas jira take Dadynsu ya dawo ta fada masa yasan irin matakin dazai dauka akan Waheeda Dakinsu tashiga tafara cire uniform din jikinta, wani zoben gold tagani me kyau akusa da Qasan gadonsu, ta kalli Ihsan tace "natsani mutum yarasa abunsa yace nice nadauka masa, mutum ya zauna yanata tsinuwa akan zobe, irin haka bashida dadi, haba, mutum ya dinga tsinewa Kansa?" Intisar tace "Ihsan dake take fa" Ihsan tace "inti waye yafada miki Ana kula marar Hankali ta6a66e?" πŸ˜‚ Intisar tace "Hakane Kam, kika Sani ko maganin haukar tatane yaqare take takeso kibata wani?" Kallan su tayi tace "ai mahaukaci shine Ana masa magana yake Kai duka, danhaka saiku banbance tsakanin nida ku waye mahaukaci Kuma ta6a66e?" Tana fada musu haka ta daura towel ajikinta, sannan tafara cire botir din gaban rigarta, hannunta yana dungurar breast dinta taji zafi, qaramin tsaki tasaki tashige toilet dinsu ta danna makunnar ruwan zafi, yana zuwa tacire rigar sannan tacire brezia din ahankali, boobs dinta ta kalla taga nipples din sunyi jajir, cikin ranta tace bazan taba yafe maba Didat, da wannan ruwan dumin tagasa jikinta sannan tafuto tasaka doguwar Riga marar nauyi batare data maida brezia dinba Karfe uku da rabi a Airport tayi masa, cikin aji yake sakkowa daga cikin jirgin yana gyara Zaman agogon hannunsa, fuskar sa babu yabo babu fallasa,wayarsa yatura cikin aljihun wandon Jeans dinsa,idan bakasan Shiba bazaka taba cewa yana jin hausa ba, yana gama sauka mutane sukace salamu alaikum, Nan da Nan samari suka cika agaban sa, tafiya yake Amma selfie wasu suke masa Ahaka,dole saida ya tsaya domin su gaisa, Amma Sai daga Kai yake yanaso ya hango su Sa'eed domin yariga yasanar dasu zuwansa, mutane kuwa basu fasa yimasa godia dakuma jinjina akan temakon dayake yiwa talakawa ba, daga masu cewa Allah yatemaki Big Brother Sai masu yimusu video tare dashi, wata budurwa kyakykyawa yar Gayu ta Matso tace "Yalla6ai zan iya samun saka hannun sanaiya?" Murmushi yayi mata, dimple dinsa suka futo, batare da yayi mata magana ba ya karbi takardar hannunta yasaka mata hannu, Bai bata iya takardar ba saida yahada mata da dala Dari biyu, aikuwa Nan da Nan aka dauki ihu anata masa kirari, saida yayi kyautar kudade a Nan Airport din sannan su Sa'ad suka hangoshi suka qaraso suka janye shi, mutane Sai addu'ah suke masa shikam saide yayi murmushi yace "Amin" Sa'eed ne ya karbi Brief case din hannunsa yace "Sannu da zuwa Babban Yaya" Yace "Sannu Sa'eed, kaje da wannan kudin ka can zasu zuwa Naira Please" Yace "to Babban Yaya angama" Sa'ad yabude masa Bayan motar yashiga, yana shiga ya Lumshe idonsa tareda dafe Kansa Su Sa'ad da Sa'eed suka shiga gaba, suka tada motar Sai hanyar gida, suna hanya Sa'ad dake driving yajuyo ya Kalle shi yayi murmushi tareda fadin "sannu Babban Yaya, gidanka zamu wuce ne kokuma gida?" Batare daya bude lumsassun idanunsa ba yace "no, muwuce gida kawai, I want to see my mother" Babu Wanda yasake magana acikinsu, saida suka qarasa gida sannan Sa'eed yafice daga motar yashiga wata motar yafita wajan canji, Babban Yaya da Sa'ad Kuma suka tsaya gaisawa da ma'aikatan gidan. Karfe hudu daidai, gaba dayansu yanmatan su uku suna falo kowacce Sanye cikin uniform din islamiya Mai launin light blue, sungama shirya wa Ihsan ce kawai bata saka hijab ba Intisar tadubi Waheeda "Waheeda Dan Allah ki Ara mata hijab din, inda taga Nata ai bazatace ki Ara mata naki ba" Yatsina fuska tayi tace "tabdi, ai saikuyi Kuma,dazu dazunnan tagama cemin marar Hankali ta6a66iya, tayaya zata saka kayan ta6a66iya?, kunifa Bari kuji banida mutunci akan kayanaaaaaa" taja naaa din sosai sakamakon tozali datayi tashi a bakin kofa yana qoqarin shigo wa falon nasu,dayake itace take kallon bakin qofa, sukuma ita suke kallo suna roqarta hijab,lokaci daya taji tanemi nutsuwar ta tarasa, taji kanta yasara tundaga qeyarta har zuwa goshinta, fuskar Nan tasa atamke, yahade girar sama data qasa, shikkenan magana ta qare, tasan yau takade har ganyenta, yaji labarin meta aikata lokaci daya tanutsu, cikin tsananin ladabi ta kalli Intisar tace "kidauki hijab din nabaki duka, kinga wannan dayan bashida guga, Bari nadaukeshi, kekuma saiki dauki gogaggen" πŸ˜‚ Cikin falon ya qaraso, qamshin turaren sa ne yasa yanbiyu juyawa cikin sauri,suna ganinsa suka juya suka kalli Waheeda, Sai yanzu suka gane abinda yasa ta basu Aron hijab din. Wajan sa suka nufa cikin ladabi sukace "Babban Yaya sannu da zuwa" Hannunsa ya daga musu kawai,tareda zama acikin kujerun dasuka qawata falon nasu masu launin dark green, cikin murna suka tafi Dakin Ummah suna qwala mata kira, suna zuwa suka tarar tana toilet Kallan Waheeda yayi wadda ta qame a wajan tun shigo war sa, yamiqe tsaye batare daya kalleta ba yace "ke biyoni" Gabanta ne yake wani irin bugawa dak! dak!, tafiya take tana binsa Amma jitake kamar batada nauyi, jitake kamar iska zata Iya dagata sama,suna shiga Dakin nasa wani irin qamshi yadaki hancinta,Dakin ya qawatu da manyan pictures dinsa, dayawa daga cikinsu duk da kayan ball yayi photon, qamewa tayi daga Nan bakin qofa saboda bai bata iznin qarasowa tsakiyar Dakin ba, takunkumin dayasa a hancinsa yafara cirewa sannan ya kalleta yace"Kneel Down here" Cikin sassarfa taqaraso cikin Dakin tazube gwiwarta aqasa tareda daga hannayenta sama, zama yayi agefen gadon yafara cire takalmin qafarsa, sannan ya tashi tsaye yacire rigar jikinsa, farar fatar jikinsa ta bayyana, murdaddan Hannunsa yasake futowa sosai, duk abinda yake idon Waheeda quriiii akansa, tunda taga yafara cire Kaya take qarewa surar jikinsa kallo, cikin ranta tace tunda Naga yafara cire Kaya inaga yau zamu raba raini, hukuncina nayau yafi qarfin duka saide dambe πŸ˜‚ Wayarsa ce tayi qara ya dauka tareda bude fridge din Dakin ya dauki ruwan gora, sannan ya dawo ya zauna, cikin aji yayi sallama yana fadin "wake magana?" Daga d'ayan bangaren akace "ranka yadade Big Brother, Shema'u ce, Shema Lady, yanzu na bude data ne, sainaga Ana bada labari kazo, ashe ka shigo gari yau" "no, qaryar Yan media ne kawai Shema, banzo ba" Fari tayi da idanunta, taji shi ne kawai, Amma bata yarda ba, cikin salon yaudara tace "Big B. Kenan, saika ganni kawai" qit takashe wayarta, wayar ya janye daga kunnansa ya kalli screen din wayar, aiko saboda wayar data kashe masa yanzu koda ace tazo, bazai saurareta ba, saboda ba'a kashe masa waya saide yakashe Tashi yayi yafara kokarin janye dogon wando jeans din jikinsa, har boxer din yafara bayyana yajuya ya kalli Waheeda yaga ta qwara masa ido tana Kallan sa πŸ˜‚, saiya fasa cirewa yamiqe tsaye yana mata wani irin kallo, cikin sauri ta runtse idonta, saida yaga tarufe idonta sannan ya qarasa cire jeans din, dagashi Sai gajeren wando yashige cikin toilet dinsa, tanajin shigarsa tayi wata irin ajiyar zuciya sannan tasauke hannunta qasa, sau dayawa tana mamaki sosai dangane da tsakanin ta da yayan Nata, kamar bashine yayanta me sonta ba, bazata taba manta lokacin dazai dauketa ya goyata abayansa yana zagaye compound din gidan da'ita ba, Amma tunda ta girma, komai ya sauya, yadena wasa da'ita, yahanasu kula Samari, yahanasu saka mayafi, idan tayiwa Ummah complain tace ai saboda bataji ne shiyasa Shima ya sauya mata, Kuma mema take aika tawa dazaibi ya tsaneta? 😏☹️Idan akan samari ne tayaya za'a Hanasu kula samari Bayan sun kusa yin candy, idan suka gama makaranta babu saurayi qarshan zancen ace za'a hadasu da samarin dangi, ayi musu auren zumunci, Kuma a wannan zamanin waye zaizo auren cushe, auren zumunci? Tanajin alamun bude kofar toilet din tayi sauri ta daga hannun ta sama Be kalli inda takeba, Kai tsaye gaban mirror ya wuce yana gogo lallausar sumar Kansa ta buzaye da wani Dan qaramin towel, saikuma wani dayake daure a qugunsa, nocking din Dakin akayi, ya dakata da abinda yake ya kalli kofar tareda fadin "shigo" Sa'eed ne yashigo da wata leda ahannunsa me d'aukeda kudade Yan dubu dubu, ya rissina cikin ladabi yace "BΓ bΓ Γ± Yaya an canzosu" Turare yafara fesawa a jikinsa yace "kaje kaida Sa'ad ku rabasu dubu goma goma, a saka kowacce dubu goma cikin Envelope, anjima idan mun fita masallaci Sai arabawa mabuqata" Waheeda tanajin zancen dubu goma tayi sauri tabude idonta, kudin ta kalla tagansu dayawa yanzu duk wannan mabuqata zai bawa?jitayi kamar taje ta qwace, Gata, gasu yanbiyu agida suma ai mabuqata ne πŸ˜ƒ Sa'eed ya kalli Waheeda yadaka mata harara sannan yafice daga Dakin yaja musu qofa,tunda yaganta a Dakin yasan laifi tayi Kallan Babban Yaya tayi taga ya Dauko wasu kayan zai saka, maimakon ta dauke idonta saita qura masa ido, yana Kallan yanda take kare masa kallo tagefen idonsa, ya tabbatar Waheeda raini takeji, tunda har zata Iya zuba masa ido har haka tana Kallan sa to yasan cewa Dan ance namiji yasha bakinta ba za'ayi qarya ba, da niyya yajuyo ya fuskanceta sannan yafara kokarin cire towel din guqunsa, idan wani abun take so tagani saita Gani da hujjaπŸ˜‚ Gaban Waheeda ya yanke yafadi, cikin sauri ta runtse idonta, cikin qasa qasa da murya yace "Ashe ke qaramar 'yar'iska ce" Ita Kuma tayi tunanin magana yamata, tunda Dama haka yake magana qasa-qasa kamar baiso, gudun kartayi laifi yace yayi mata magana ta qyaleshi shiyasa ita Kuma ta daga murya tace "Na'am Babban Yaya Dani kake?" Dawowa yayi ya zauna agefen gadon, Bayan yagama shirya wa tsaf ya kalleta yace "badake nakeba qaramar marar mutunci, kullum aka ganni a Nigeria ta dalilin ki ne nake zuwa, haka kawai Ina Kan har kokina saikin aikata abinda zaisa dole sainazo qasar Nan, ke wacce irin mahaukaciya cene? Kwata kwata bakida aji bakida Hankali irinna yanmata, anturaki makaranta ashe soyaiya kike harda su kiss, nakafa doka a gidan Nan kina take wa yafi a qirga, saboda ga sa'anki, to yau idan jikinki yagaya miki, ko ance ki kalli samari ma bazaki kallesu ba, dangane da makaranta Kuma nasan matakin dazan dauka a kanki" Yana kaiwa Nan ya tashi yafice daga Dakin, Waheeda tafashe da Kuka, cikin kuka tace "Nashiga uku na, ashe yaji, shikkenan Aryan yacuceni, Allah ya'isana" haka taci gaba da kneel down tana kuka, babu damar tatashi yazo yaga tatashi nanma taqara wani laifin, tun yanzu ma jitake gwiwowinta harsun fara zafi Yana futowa daga Dakin yatarar da Dady da Ummah a zaune, gaida su yayi cikin ladabi sannan yakoma gefen Ummah ya zauna tareda Dora Kansa akan kafadarta yace "Ummah" Murmushi tayi tace "Yayansu ya hanya, maza tashi muje Kaci abinci, gashi can na shirya ma" babu musu ya tashi, saboda yayi missed girkin umman tasa, saboda aturai koda yaushe baida abinci saina gwangwani, Daddy ya kallesu itada Yaron yace "idan kin gama bashi abincin inason magana dashi" Ummah tace "to Alhaji" Ita da kanta ta dinga bashi abinci abaki, kowa ya kallesu yasan akwai tsantsar soyaiyar uwa a tsakanin su, Sai shagwaba yake mata abu kadan yace Ummah, ita Kuma Sai lalla6ashi take Saida ta tabbatar ya qoshi sannan suka koma falon, wajan Alhaji Umar, Babban Yaya ya Kalle shi yace "Daddy nagama, meyafaru?" Kallan sa yayi yace "menene zai faru banda maganar Aurenka?ai tunda Naga kazo yau nasan kun daidai tane kaida ita Habiban ko? Yaya kukai da'ita?" πŸ˜‚ Sunkuyar da Kansa yayi yana Sosa girarsa, yama kasa dagowa ya kallesu Ummah tayi ajiyar zuciya tace "wacce Habiba Kuma Alhaji? Yarinyar da harma munyi magana da mahaifiyar ta awaya sunce sun janye batun auren, nabawa mahaifiyar yarinyar hakuri Amma Sai tace ai habiba tace bazata iya zama da mutumin da bazai bata kulawa ba, to tunda naji haka, kawai saina bata hakuri tunda bansan me suka Tattauna ita dashi a wayar ba, shi yasan meya qulla "tana fadar haka takawar dakanta Gefe tana girgiza qafa Alhaji Umar ya Kalleshi yace"Naufal" Ahankali yace "Na'am Daddy" "bakada lafiya ne irinta maza?" Maganar tayi masa nauyi, saiya kasa dago Kansa ya kalli mahaifin nasa, Ahankali ya girgiza Kansa yace "A a Daddy" Daddy yace "okay, iskanci ne yake damunka kenan?" Nanma yakasa bashi amsa ya girgiza Kansa yayi shiru Daddy ya ajiye Jaridar hannun sa yace "kaiba 6oyaiyan mutum bane dakake tunanin mutane bazasu saka Maka ido akan aure ba, muna zaune lafiya bazaka ja mana zagi agari ba, zamusa qafar wando daya dakai tunda haka kaza6awa rayuwar ka, Kuma neman aure yanzu muka fara nema Maka, idan ma wani abun daban kake fadawa yaran mutane har suke gudunka kaika Jiyo, mude bazamu fasa nema Maka aure ba, har a wajan Allah muna neman fita haqqin ka ne a matsayin mu na iyayenka akan kayi aure gudun aikata Zina, mutumin banza mutumin wofi, katashi kabamu waje Kuma aure dolen dole Sai kayi " Runste idonsa yayi, maganganun Daddy sun shige shi sosai, yaji zafin maganar Daddy sosai, tayaya ne zai futo fili yafada musu yarinyar dayake so Bayan tarin matsaloli dakuma qalubalan dazai fuskanta ? Tayaya? Ahankali ya tashi daga gabansu yanufi dakinsa, zuwa yanzu magrib har tayi Yana shiga dakinsa yaga Waheeda yanda yabarta, gaba daya cinyoyin ta sun sage, Saitayi kamar zata fadi qasa, saita dawo baya taci gaba da abinda take, bacin ran dayake ciki ne yasa yanemi belt yanufeta gadan gadan, tana ganin haka tatashi tsaye tanaja baya, kuka take wiwi tana bashi hakuri Amma idonsa sun rufe saida ya lafta mata belt dinnan ajikinta, qara tasaki tana fadin "Dan Allah kayi hakuri, wallahi tallahi nadena Babban Yaya, Dan Allah kayi hakuri" Cikin 6acin rai yace "kifadamin waye wannan Yaron dayake neman lalata ki?, harkinashan bakin wani saboda bakida mutunci ko? " Belt din tariqe idanunta cikeda hawaye tace "Dan Allah kayi hakuri, wallahi bazan sake ba, idan nasake Kamin komai ma nayarda" Fizge belt dinsa yayi yasake zuba mata shi ajikinta, zafin dataji ne yasa batamasan lokacin data tashi ta rungume Shiba,yana jin yanda Albarkatun qirjinta suke tsikarinsa saboda bata saka bra ba, lokaci daya jijiyoyin jikinsa suka kar6i saqon, πŸ™ˆAmma tsananin 6acin ran dayake ciki yasa baza'a gane hakan ba Fizgeta yayi daga jikinsa yasake Dora mata wani belt din, cikin kuka tace "Akofar fada yake, gidan Alhaji Hamza" Tsaki yasaki tareda wullar da belt din qasa yace "Stupid" Ummah tana Jiyo kukan Waheeda tata6e baki tace kanku akeji kunfi kusa, Daddy ne yake tambayar ta meta masa, anan ta fada masa komai ciki harda wayar Babban Yaya data daga batare data saniba Futowa yayi daga Dakin yabarta anan, su Ummah suna zaune har lokacin, suna ganinsa yafuto fuskar sa a daure, yana shirin fita daga falon, anan yaci Karo da Yanbiyu harsun dawo daga islamiya kasancewar anfara Kiran sallar magrib, yanda sukaga fuskar sa sunsan ransa a6ace yake, cikin sauri suka bashi waje yafice daga falon Suna qarasowa falo suka gaida Daddy, Shima ya tashi yayi shirin tafiya masallaci, Dakin Babban Yaya aka bude ahankali, kamar me koyon tafiya hake take takawa, idanunta sun kumbura sunyi jajir, Sai yarfe hannunta take, hawaye wani nabin Bayan wani, Ahaka tashige cikin dakinsu babu Wanda yace da'ita uffan daga Ummah har Yan biyu, tana zuwa daki wani irin zazza6i yafara kokarin rufeta, kawai zubewa tayi agadonsu taja Bargo tarufa.πŸ˜‚ Da daddare duk suna zaune afalo gaba dayansu suna kallo, har wajan karfe takwas da rabi Waheeda bata futo falo ba Babban Yaya yana zaune yana danne danne a wayarsa, Sa'eed da Sa'ad Kuma suna gefen sa suna bashi labarin 'yanmatan dasuka hadu dasu wasu yanbiyun suma, magana suke masa Amma hankalinsa yanakan wayar dake hannun sa, ahankali yake amsa musu, su yanbiyu suna zaune suma, suna Kallan film din da'akeyi, Ummah da Daddy suna can Gefe suna zance qasa qasa, Daddy ya kalli Babban Yaya yasake yin qasa da murya yace "ke baki lura da abinda nafada miki ba? Ki lura dashi sosai qarya yake mana bashida lafiya"🀣 Itama Ummah Kallan sa tayi tace "Aina yarda Alhaji, kunyar fada mana kawai yake, Amma duba fa yanda 'yan' uwan suke bashi labarin yanmatan su Amma yayi mursisi, maza dason zancen yanmata Amma shi kaduba kagani fa suna masa magana kamar sunayi da dutsi" Daddy ya girgiza Kansa yace "dole zan dauki mataki hajiya" Shikuwa Babban Yaya baisan sunayi Bama πŸ˜‚Kallan intisar yayi yace "ke tashi ki kira wannan yarinyar tazo tayi kallo" Intisar tasan da Waheeda yake, ita kadai ce bata futo falo ba, cikin sauri ta nufi dakinsu, tana shiga tahau kan gadon ta yaye bargon da Waheeda tarufa, bude idon ta tayi ta kalleta, duk yanda Waheeda take gane yanbiyu, take banbancesu dukda tsananin kamar dasuke, yau kasa ganesu tayi,🀣 intisar ce tazo kiranta Amma Waheeda tana qare mata kallo cikin wahala tace "Ihsan Dan Allah ki temaka ki taro ruwan zafi a toilet kizo ki gasa min cinyoyina, jikina yayi tsanani bazan iya tashi ba" Dariya ta kama Intisar, saita danne gudun karsuzo suna fada, tace "Babban Yaya ne yace kifuto kiyi kallo kowa yana falo banda k....." kafin ta qarasa magana taga Waheeda ta duro daga kan gadon πŸ˜‚ Kokula sauran zancen batayi ba tafice daga Dakin, tana zuwa falon babu Wanda ta nufa Sai shi, har gefen qafarsa ta zauna, hawaye yazubo daga idanunta, a Hankali tace" Babban Yaya Dan Allah kayi hakuri kaji.... " Babu Wanda yasan metake fada masa, saboda ahankali tayi masa maganar, Shikuwa banza yayi yarabu da'ita, hawayen tasake gogewa tace"kaji" memakon yabata amsa saiya tashi daga falon yashige dakinsa, haka ta zauna a wajan tana Kallan dole, saida takusa minti talatin tana kallo Amma bata fahimtar komai, Dan haka tatashi Takoma dakinsu tafara gabatar da sallah Karfe bakwai daidai afalo tayi masa,yayi kyau sosai cikin manyan Kaya, yanda yaqara cika da kamala zakace yanada aure, agogon hannun sa ya kalla yadubi Ummah yace "kice musu Idan sun gama Ina waje Ummah" Ummah tayi dakin yaran tace "kuyi sauri kufita yayanku fa kuyake jira" Yanbiyu ne suka futo sun shirya cikin uniform dinsu, suna zuwa compound din suka hangeshi yana Dukan tayar motar da qafarsa yana Kallan agogo, suna ganin haka suka qara sauri suka shige motar, shida Kansa yayi driving din, Kai tsaye yanufi makarantar su Suna zuwa kuwa Kai tsaye yanemi iso zuwa office din director, teachers dinsu maza Wanda suke harkar ball suna ganinsa suka fara zuwa suna gaisawa dashi, yana gaisawa da director yanemi afwa akan yanbiyu, babu bata lokaci sukace komai ya wuce Yara sukoma aji, Amma waccan dayar de kar akawota bazasu karbeta ba Duk da haka saida yaqara basu hakuri sannan yayi musu ihsani yafuto daga makarantar, daga Nan ma ba gida yakoma ba, kofar fada ya nufa, yana tambayar gidan Alhaji Hamza aka nuna masa, futowa yayi ya jingina da motar yace ayi masa sallama dashi, Alhaji Hamza yana futowa yaga farin buzu a kofar gidansa, qarasa wa yayi yabashi hannu suka gaisa, Babban Yaya yace "Alhaji sunana Naufal, da Alhaji Hamza nake magana ko?" Alhaji Hamza yace "nine samari, ba kaine yaranmu suke cewa Big Brother ba?" "nine Alhaji, dama nazo ne akan maganar qanwata dakuma Yaron wajanka Aryan" Alhaji Hamza yace "to menene yafaru?" "Alhaji, Yaron wajanka yana soyaiya ne da qanwata, shine nazo muyi magana akan yaturo iyayensa idan aure zaiyi yanzu" Alhaji Hamza yace "Wai Aryan wannan Dana Sani Dan wajena kake magana akansa?" "shide Alhaji" Murmushi Alhaji Hamza yayi yace "samari Aryan fa shekararsa goma shatara ne Idan nayi lissafi daidai, tayaya za'ayi masa maganar aure yanzu?" Babban Yaya yace "hakane, to ita yarinyar dayake nema aurenta zamuyi, saboda haka Dan Allah Alhaji ajawa yaro kunne yadena bibiyarta, jiya matsala ce tafaru a makarantar su har hakan yasa suka Koreta daga makaranta, so aja masa kunne please" Alhaji Hamza yace "Subhanallah, ashe yar'uwarka ce yaro, to kuyi hakuri Dan Allah, insha Allah zanyi wa tufkar hanci" Babban Yaya baice dashi komai ba yajuya yashiga motarsa yatafi gida Yana zuwa gida ya tarar da Hajiya Anty da Ummah afalo, can ya hangi Waheeda a dinning tana cin abinci kwanciya yayi akan doguwar kujera ya Dora Kansa akan cinyar anty yasaki wani irin murmushi dimples dinsa suka lotsa duka biyun yace "Anty nah ta kaina" Sumar Kansa ta shafa tace "yayansu nayi fishi, kazo Amma koka leqoni, yanzu ma sannu da zuwa nazo yima dakuma wani albishir" Hannunta datake shafa sumarsa yariqe yayi kissing Bayan hannun sannan yace "Ina jinki Hajiya Anty" Tace "wallahi wata yarinya ce take zuwa Asbiti Ina dubata lokaci zuwa lokaci, shine nayaba da Hankalinta, nace zan turo mata Dan yayata su daidai ta ko Allah zaisa ayi abun da'ita" Cikin sauri ya tashi daga kan cinyarta yace "Anty me kikace?" "abinda kaji nace" Kansa ya shafa yace "Anty Kode neman Kai kuke Dani ne?" Tace "mekake nufi yayansu?tayaya zamu nemi Kai dakai?" Bata rai yayi cikin shagwaba yace "to Anty gashinan Kuma arasa da wadda za'a hadani Sai majinyaciya?" Ummah ce tasa musu baki tace "tunda kaqi lafiyayyu ai sai kakoma kan majinyata" tajuya ta kalli hajiya Anty tace "ki fada masa komai, kidena wani Lalla bashi" Hajiya tace "yayansu harna yiwa uncle dinka maganar yarinyar shida Dadynka, Amma Kai Yaya kagani?" Ummah tace "Yaya zai Gani kuwa? Yama amince kawai" Tashi yayi daga wajan su yace "to Anty idan nasamu lokaci zanje naganta" Ummah tace "yaushe zakaje?" Kansa yadafe da hannun sa πŸ€¦πŸ»β€β™‚οΈyace " wayyo Allah Ummah, zanje wallahi, anjima zanje" Anty tace "to idan katashi zuwa ga wannan kayan kwalliyar kakai mata" Uwar ledar data turo masa gabansa ya kalla, cikin ransa yace Dama de sun shirya komai Yace "to" Bai dauki ledar ba ya wuce ta gaban Waheeda yayi dakinsa,yanaaji yana cewa "good morning Babban Yaya" Amma ya shareta wani qullutun taqaici ya to kare mata maqoshi, tasan yanzu Babban Yaya ya tsaneta, gashi ya maida yanbiyu makaranta Amma banda ita. Hajiya Anty tana tafiya gida Waheeda taje wajan Ummah ta zauna, Ummah ta kalleta tace "Lafiya Waheeda?" Girgiza kanta tayi tace "Ummah, Babban Yaya baya sona yanzu, ya tsaneni" Ummah ta kalleta tace "yayanki uwa daya uba daya tayaya zakice baya sonki Waheeda? Halinki ne baya so, Waheeda bakya jin magana, saikin masa laifi Kuma kizo abun ya dameki, yanzu ni me zanyi muku akan haka?" Idanunta ne yayi qwalqwal hawaye yana shirin futowa tace "to Ummah kinajifa nagaidashi Amma ya share ni" "bai gama hucewa bane, kibari zuwa anjima ai zai sauko" Hawayen data riqe ne ya silalo daga idanunta, tasa hannu ta share, sannan tayi dakinsu domin ta watsa ruwa Umma na ganin tafiyar ta ta nufi Dakin Babban Yaya, yana kwance agadon sa yayi mata shi da hannayensa, duniyar tunani yatafi ita wannan yarinyar ta wacce hanya zaibi yarabu da'ita? Turo kofar tayi tashigo, yana ganin shigowarta ya tashi zaune, zama tayi akusa dashi tace "Yayansu, magana nakeso muyi" Nutsuwa yayi yace "to Ummah" Tace "akan Waheeda ne, yakamata kadinga Jan 'yan'uwanka ajiki, qannanka ne bakada kamar su, idan Bama Raye kaine zasu kalla a matsayin ubansu, yarinya qanqanuwa Waheeda har tana min magana akan rashin kula da'ita da bakayi, tacemin yanzu kadena sonta, hannunka fa baya ru6ewa ka yanke kayar, yakamata kadinga janta ajiki kanuna mata fari da baqi, tunda Dukan bazaisa ta sauya ba saika dinga yimata nasiha " Kallan ta yayi yace"Ummah nasiha bazata shiga qwaqwalwar yarinyar nanba, batajin magana, kullum itace takemin sanadin zuwana Nigeria " Ummah tatari numfashinsa tace" kaikuma gashi baka son zuwa Nigeria saboda kar muyi ma maganar aure ko? " Qasa yayi da Kansa yace" Bahaka bane Ummah, insha Allah zan jasu ajikin kamar yanda kikace " Tashi tayi tsaye tareda fadin" Allah yamaka Albarka " Cikin jin dadi yace"Amin Ummah tah" Dayamma suna kallo afalo, Amma dukansu su ukun suna saka kayan makarantar islamiya, jira suke kawai lokaci yayi sutafi, futowa yayi daga dakinsa yayi wankan qananun Kaya kamar ka saceshi kagudu, wandon Jeans yasaka baqi, Sai Riga me kama jiki ruwan toka, dakuma yar sama me ratsin baqi, yasaka kambos Shima baqi me ratsin brown, yayi kyau sosai sumar Nan tasa Sai sheqi take, Ummah ta Kalle shi tace "masha Allah, yayansu Sai ina?" Kansa ya shafa yace "inda hajiya Anty tace naje" Fara'ah ce ta wanzu a fuskar Ummah, tace "kace gidan surukar tawa zakaje, irin wannan wanka haka ai dole a dedeta, Bari in Dauko Maka kyautar Tata" Baice komai ba, yanemi kujera ya zauna, tareda daukar remote ya maida tashar Kallan ball, Kallan Waheeda yayi, suna hada ido tayi qasa da kanta, yace "4 o'clock kuke tafiya islamiya ko?" Atare suka amsa da "eh" Yasake dubanta yace "tashi ki rakani" Cikin murna tatashi tayi dakinsu, farinciki take yayan Nata da alama yahuce, uniform dinta tacire tasaka doguwar Riga, sannan ta dauki dogon hijab dinta tasaka, tana futowa Ummah ma tana futowa daga daki, ta bashi ledar kayan, ya nuna mata Waheeda ataqaice yace "bata" Ummah tace "yanaga kincire uniform din ko tare zakuje zancen?" Waheeda tasaki wani murmushin jindadi, tace "eh Ummah" Kallan ta yayi sosai, sautari idan yarinyar tayi wani abu saiya ga Takoma photocopy dinsa sak, musanman idan tayi dariya ko murmushi duk dimples dinta suka bayyana kamar de nashi, kauda tunanin yayi daga ransa yafita daga falon ita Kuma ta Mara masa baya, saida tajuyo tayiwa yanbiyu gwalo πŸ€ͺSannan tafita Ummah ta girgiza kanta cikin ranta tace gaskiyar sane daya ce bazata sauya ba Motar dasuka shiga glass din motar tint ne, ba zakaga naciki ba, mafi yawan lokaci irinta yake Hawa saboda shi mutum ne na mutane, ko Yaya yafuto awaje dole ne kasamu Wanda yasan shi Suna cikin tafiya ya kalleta yace "Bani labari" Kallan sa tayi tace "Babban Yaya wanne labari gashinan muna shirin zuwa Naga Anty" "wacece Anty?" "Babban Yaya wadda zamuje wajan ta, budurwarka, harna matsu naganta wallahi" Haushi ne yakama shi, yace "to naji Dan Allah, ni labari nace kibani bawani shirme ba" Kallan sa tayi, cikin ranta tace zancen budurwar tasa yake cewa shirme to in hakane komai ma ta fada bazai birgeshi ba, duk da haka saita Juyo tana fuskantar sa tace "Babban Yaya inaso Naga kana Ball, ka'iya ball sosai, wani lokacin idan ka saka qwallo araga Sai inji jikina yana tsuma kamar nice nasaka" Dariya tabashi, saida yayi dariyar sa sannan yace "ke meyasa bazaki Koya ba?" "Bayan wacce kake Koya mana agida?" "yes, idan kinaso saina sake Koya muku" "muna so wallahi Babban Yaya,nafiso nafi yanbiyu iya Ball" Kallan ta yayi kawai yayi shiru, saboda qarasowa dasukai gidan yarinyar da Hajiya Anty tabashi address, a kofar gida suka tsaya yakira Hajiya Anty ya tambayeta sunan yarinyar tace masa naja'atu, daga Nan yakashe wayar yatura wani yaro Akira masa ita Yaron ya dawo yace ance su shigo, har falo suka shiga suka zauna, babu laifi gidan sunada rufin asiri, kusan minti biyar da zamansu Sai gata tafuto tana Sanye cikin atamfa Riga da siket, Sai wani Dan qaramin mayafi data saka, da farko tsorata tayi data ganshi, saboda lokaci daya yadaki zuciyarta, gayen yahadu dayawa, fatanta daya Allah yasa Shima ta masa Zama tayi tareda gaidashi, ya amsa cikin kulawa, acan Qasan ransa yaji dadi dabata ganeshi ba da alama bata ganin ball, Waheeda ce itama ta gaidata fuskar ta d'aukeda murmushi, ta amsa mata Shiru Waheeda tayi tana jira taji irin kalaman soyayyar da Babban Yaya zai tsara mata kamar yanda Didat yake mata idan sun hadu a school, saitaji yace "Naja'atu Anty nace taturo ni wajanki, basai nayi Miki dogon bayani ba nasan kinsan dalilin zuwana wajanki" Murmushi tayi tace "Hakane, nide daga wajena babu wata matsala, Ina fatan kaima haka?" Babban Yaya yace "a a, banda wata matsala Nima, saide inaso namiki tambaya guda daya" Kafadunta ta dagaπŸ€·πŸ»β€β™€οΈtace "babu damuwa Ina jinka fadi duk maganar dakake so" Yace "Kina school ne yanzu?" Tace "a a, tunda nayi candy bankoma makaranta ba" Yace "masha Allah, Nima banda burin yarinya tayi dogon karatu batare da aure ba, but meyasa ke kinyi candy Amma bakiyi aure ba har kika dade agida kina neman tsufa? Waheeda ta zaro ido 😳ta Kalle shi da sauri Itama naja'atu ta Kalle shi tace"me?, nice na tsufa babu aure? " Batareda damuwa ba yace"idan bakiyi shekara ar'ba'in ba tokin kusa, tunda Naga idanunki na tabbatar kedin Nan sa'ata ce, bazan girmeki ba, nikuma gaskiya nafison na auri yarinya qarama, wadda zan Koya mata komai" Haushi yakama naja'atu, ta jinjina kanta tace "ni Dama nasan babu wani namijin Arziqi daza'a dinga neman Kai dashi haka kawai, na tabbatar kaima kyan Dan maciji ne dakai tunda har ake neman Kai dakai duk wannan kyan Naka, tunda kana tareda P.A dinka ai shikkenan saikaje ka aure ta"taqarasa maganar tana Kallan Waheeda Cikin sauri Waheeda tace "kaiiii Yaya nane fa" Naja'atu ta miqe tsaye tace "Au...to Allah yasa gware kukai kuka futo" πŸ˜‚ Waheeda ta kalli Babban Yaya ko zai dakatar da naja'atu daga tafiyar datake shirin yi, taji yayi shiru, ahankali tace "Haba Babban Yaya" Kallan ta yayi ya daga murya yace "Naja'atu" Cikin fishi naja'atu tajuyo tace "kutashi kubar mana gida tun kafin nakira Yara su tule ku da qasa"πŸ˜‚ Dafe Kansa yayi πŸ€¦πŸ»β€β™‚οΈ?, sannan yadago yace "Dama wannan ledar ce kika manta bakidauka ba, Inji Anty tace akawo miki" Tsaki naja tasaki tace "kuje da tsiyarku" daga Nan tashige tabar su afalo, ita kanta Waheeda taji babu dadi, tayi tunanin haquri zai bata Wai ashe leda zai bata, wannan rashin mutuncin ko ita akayiwa Allah ne kadai zai rabata da saurayin ranar πŸ˜– Haka suka futo daga gidan Waheeda jiki a sanyaye, shi kuwa ransa fes Amota kasa magana Waheeda tayi, Shima bece da'ita uffan ba, cikin ranta tana so ta tambayeshi meyasa yake gudun aure? Amma tarasa ta'ina zata fara? Duk cikin iyayensu babu Wanda yataba zama dashi yaji menene dalilin sa naqin matan da'ake hadashi dasu, kawai sude iyayen burisu suga yayi aure kawai, tana so taji menene matsalar sa, meyake so? Amma tana tsoron abinda zai biyo baya, saboda zai iya cewa ta raina shi Tunanin tane ya tsaya lokacin dataga sun tsaya awani super market, p-cap dinsa ya dauka yasaka me d'aukeda sunansa ajiki, sannan yashiga wajan, itade Waheeda tana binsa Abaya taga Sai provision yake yi, itama yace tayaya shi haka suka dauki , su suger, cornflakes, madara, Maggi, kayan zaqi dangin su biscuit da chocolate, saida yagama hada komai tsaf, har tana mamakin Ina zaikai wannan uban kayan,? Wasu yanmata ne suka ganshi su kazo sunaso yayi photo dasu, babu musu ya tsaya sukayi sannan suka nufi wajan biyan kudin, a lokacin wani saurayi Shima yana wajan zai biya nasa kudin, ganin Babban Yaya yasa farinciki yarufe shi, Yama Rasa inda zai Dora ransa, Sai magana yake masa, Babban yaya yayi murmushi Shima yasake da saurayin kamar ya sanshi, shida Kansa ya biya kudin saurayin danasu kayan sannan yamasa sallama suka tafi gida Suna zuwa gida taga yabawa Sa'eed wannan kayan dasuka zo dashi, sannan suka wuce Dakin Ummah, tare suka gansu itada hajiya Anty Sai hira suke da shewa kamar ba facaloli baπŸ˜ƒ a lokacin biyar da rabi har tayi, Ummah ta kallesu cikin farinciki tace "harkun dawo? Jinake ai sai dare" Hajiya Anty tace "yayansu nasan de Najaatu tayi hundred percent" Zama sukai gaba dayansu babu Wanda yayi magana, Ummah ta kalli ledar kayan kwalliyar dasuka tafi dashi tace "yanaga kunyi shiru, meyafaru ko bakuje bane?" Waheeda ta janye hannunta daga tagumin da tayi tace "hmm Ummah cewa tayi mutashi mutafi tun kafin tasa atule mu da qasa, gashi mayafi take sakawa, shikuma Babban Yaya baya son mayafi, shine ya tambayeta meyasa ta tsufa batayi aure ba, ranta ya6aci tace masa yaje ya aureni tunda ni p.a dinsa ce, Wai ai Dama neman Kai kuke dash.... " Hajiya Anty ce ta katse Waheeda cikin tsawa" ke dallah can rufe mana baki shashasha kawai. Yen yen yen Sai magana kike Babban Yaya baya son kaza, Babban Yaya baya son kaza, kunhada Kai kunje kunci mata mutunci kun dawo toshknn Hankalinku saiya kwanta, ita yar'iskace dabaza tace yaje ya aureki ba? Ina aka taba tafiya zance , ganin farko adiba atafi da qanwa? Saikune zaku nuna mata ku yan'uwan jini ne, banji dadi ba dabatasa anmuku wanka da qasa ba, tashi kibawa mutane waje manya suna magana kin tsomo baki kamar maganar aurenki ake " Sum sum Waheeda tatashi tabar Dakin, shi kuwa Babban Yaya kasa hada ido yayi dasu Ummah tace"ashe abinda kake fadawa yaran mutane kenan shiyasa kowacce Sai tace bata sonka, Toda kake cewa ta tsufa batayi aure ba kaidin shekarar ka nawa?" πŸ€” Shiru yayi yakasa Bawa Ummah amsa, Ummah tace" dakai nake, nace Kai shekararka nawa bakayi aure ba? " Kansa aqasa yace" Ummah kuyi hakuri, Nima ba laifi na bane " daga Nan ya tashi yafuto daga Dakin Shima Yana fita hajiya Anty tace" Yaya kinji me yace kuwa? Ba laifin sa bane Anya kuwa Yaron Nan kalau yake ba Sanyi da basir ne sukai masa mugun kamu ba? "🀣 Ummah tace" to Hajiya Anty tayaya zan Sani? Kuma yaqi yayi auren balle mugani kalau yake koba kalau yake ba "πŸ˜‚ Hajiya Anty tace" kaiii ninama Rasa mezance wallahi, tunani na ya tsaya Hajiya, Bari inje gida, idan nasake wani tunanin saina dawo " Washe gari da sassafe ya shirya cikin qananun Kaya, so yake yabar qasar saboda jibi sunada match a Qatar, sannan muddin yaci gaba da zama to bazasu daina hadashi da yanmata ba, suna gama bresk fast, ya kalli Ummah da Daddy yace" Ummah, Daddy, zan wuce England yanzu, jibi munada match a Qatar, kuyimin addu'ah " Atare sukace" Allah yabada sa'a " Ya Juya ya kalli Waheeda, yabata 10k yace" gashinan, kiyi amfani da wannan idan kinje makaranta, anjima su Sa'ad zasu kaiki Boarding school, nariga nayi magana da principal din ta waya, Shopping din da muka iyo jiya nasan komai yamiki tunda ke kika za6o da kanki, Tunda bakya jin magana Dan Allah kisake aikata wani laifin Wanda zakisa nasake dawowa Nigeria saboda ke kinji..... " Spoon din hannunta ne yafadi qasa tace" nashiga uku Babban Yaya Boarding Kuma? " Kallan qwayar idonta yayi yace"yes, nafiso a kaiki inda zasu kasheki su kawo mana gawarki" Duk me buqatar Babban Yaya yakirani kokuma yamin magana ta whtsapp 08033300034 Share please πŸ™πŸ» Amnah El Yaqoub ✍πŸ? 1/28/22, 20:49 - Ummi TandamaπŸ˜‡: BABBAN YAYA Writing By Amnah El Yaqoub Like my Page On Facebook https://www.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493/ 5&6 Tanajin abinda yace tayi dakinsu da gudu tana kuka, Shima yajuya yafita daga falon, wannan Karon driver ne yakai shi Airport, Bai dade da zuwa ba jirginsu ya tashi A wannan safiya Waheeda breakfast din da batayi ba kenan, tana daki tana kuka, Sa'ad ne yashigo Dakin yace ta shirya kayanta karfe goma zasu tafi, tanajin abinda yace tasake rushewa da Kuka, harta Bawa yanbiyu tausayi suma suka fara share hawaye πŸ˜₯, sune suka shirya mata kayanta tsaf, sannan Ummah tazo ta lalla6ata taci cake da madara, sannan suka tafi, tabawa kowa tausayi a gidan, Hajiya Anty Kam dataji labari kasa zuwa gidan tayi, zuciyarta bazata dauki hakan ba, gashi babu damar Hana tafiyar Tata tunda Babban Yaya ne ya yanke hukuncin, iyayen nasu sun bashi power sosai babu yanda za'ayi ya yanke hukunci aqetara shi. Lokacin dasuka kaita,riqesu tayi tanata kuka, saida principal din yasa wata yar ss3 ta riqeta suka tafi hostel tareda kayaiyakinta. Wunin ranar haka Waheeda take addu'ah cikin ranta Allah yasa karsu Babban Yaya suci match din dayace zasu bugaπŸ˜‚ Wannan yar Ss3 din data kaita hostel, Mai suna Rabi'at itace ta dinga bata hakuri ranar, Sai lalla6a Waheeda take tana kwantar da'ita ajikinta, tun Waheeda tana daukar abun na Hankali Sai kuma taga abun yafara wuce Hankali, taga agida ko jinya take yanbiyu basa kwantar da'ita ajikinsu, bare yanzu da lafiyarta kalau, Kuma bawani girman ta tayi ba, Kuma ita a aji biyar din datake anan aka Barta, duka duka tsiran aji dayane a tsakanin su bare ta nuna mata wani abu. Duk wani abu da tasan ba'a sakawa a makaranta doka ne, tahana Waheeda sakawa, su ribom, zobe, Dan kunne, dasu kwalliya, duk tayiwa Waheeda bayani Kuma ta hanata sakawa. Washe gari karfe biyar da Minti goma na asuba aka tashe su, Bayan sallar asuba gari yana haske aka sakasu share share, wasu wankin toilet, tun a lokacin Waheeda tafara raina kanta, agida basa irin wannan aikin, Sai yanzu tasake tabbatar wa Babban Yaya yana mata tsana mafi muni, mutumin dazai kawoka wannan muhallin ba qaramin maqiyinka bane,πŸ˜–πŸ˜ƒ Daqyar tayi sati daya, kafin tafara sakewa da sauran dalibai, acikin sati dayan da tayi harta hada group na qawaye irinta marasa jin magana,Neenah da zuly. Kansu ahade yake, kudin datazo dashi makarantar shi take sakar musu suke yin komai da komai yanda ransu yakeso, shiyasa tana basu umarni sukebi. yau data tashi da safe Bayan tagama komai zobunan gold dinta da wannan yar Ss3 din tasata tacire ta6oyesu, suta Dauko tasaka tatafi aji Malaminsu yana karatu yaga hannunta Sanye da zobe yace "ke ba'a fada miki ba'a zuwa da zobe ko Dan kunne aji ba?" Tace "Malam hannu nane yayi wani iri sungul babu kyan Gani shiyasa nasaka" Malamin yace "kwalliya kikazo yi kenan" daga fadar haka ya ajiye littafinsa yafita waje yanemi bulala, yana fita ta daga kanta ta kalli silin din ajin taga wani ya6ule, tatashi tataka kan bancin dasuke zaune tasaka zoben aciki, ta kalli Yan group dinta tace "duk Wanda yafada ku gane min shi, nadena bashi ko sisina" Malam yana zuwa yace ta bashi zobe tace ita babu wani zobe awajanta, ya tambayi Yan ajin kowa yayi shiru, qarshe baqin ciki ne yasa malamin yahadasu yadakesu gaba daya, ya dauke littafinsa yafice daga ajin😟 Washe gari da abincin ta tafita class bataci a hostel ba saboda ta makara, Kuma an hanasu zuwa da abinci class, tana hango malama tayi sauri tajefa flas din abincin Bayan window, duk wani Salo na6oye abu idan aka zo qwacewa tasan yanda zatayi ta6oye Saida yagama karatun sa yafita, sannan tasake haurawa ta window tadauko abincin ta taci, tana gama ci senior master dinsu yashigo da wata qawar Rabi'at Wadda Waheeda ta dauketa suka tafi hostel ranar da tazo, agaban allo ya zauna yace "duba minsu daya Bayan daya, principal yace akwai Wanda suke zuwa da waya acikinsu, jiya an tsinci sim card, Kuma zasu iya aikata wa, maza maza duba minsu" Qawar Rabi'at tazo tafara dubawa, ko'ina saita laluba ajikinsu ko sun 6oye wayar, tana zuwa kan Waheeda taji wani farinciki ya kamata, dama tunda taga Rabi'at tazo da'ita taji tana son yarinyar, ta yiwa Rabi'at magana akan ta Amma taqi bata goyon baya, saboda itama so take takafa Tata gomnatin acikin zuciyar yarinyar, malamin yace "dubamin ita mana, me kike jira ne?" Cikin sauri ta nufi Waheeda tafara shafa jikinta, hips dinta take shafawa har matsawa take cikin wani irin Salo, malamin yajuya yana amsa waya tafaki idon sauran dalibai tazura hannunta cikin hijabin Waheeda da sunan duba waya tafara matsa mata boobs dinta, Kallan Waheeda tayi takashe mata ido tana sake murza mata nashanunta, Waheeda ta taqarqare tabige mata hannu cikin tsawa tace "Dalla malama Niki Bari, kawai sai wani lalube min jiki kike" Tsoro ne yakamata, malamin yakashe waya yajuyo ya kalleta cikin fada yace "kunji min marar kunyar yarinya, mezata laluba a jikin ki qwaila dake? Idan kinsaba yiwa sauran malamai rashin kunya to ni duka zakici" Murmushi tayi tace "malam ai kasan yarinya ce qarama, saida lallama, babu wayar ma ajikinta" Tsaki yasaki yace mata"muje" fita sukai daga ajin suka shiga wani Bayan sun koma hostel sunacin abinci da qawayenta ta Kalle su tace "nifa barin Dakin da Rabi'at dinnan take zanyi, saboda abinda take min yafara isata, saita dinga Jana ajikinta tana wani shafani, haka dazu ma qawarta ta dinga ta6amin Nono, nayi magana malam yayi fada"πŸ˜” Neenah tace "tabdi kece kika yarda, kitsaya suna lalube miki, qirjinki yazube, sun Riga mijinki ta6awa" Tsaki tasaki tace "tun yaushe wani tsinanne yata6a? Ai bazan taba yafe wa Aryan ba, inda ace Babban Yaya yaji, nasan kasheni kawai zaiyi" Zulaihat tace "wani term din kawai kibar Dakin kidawo namu, qaro mana abincin Dan nikam ban qoshi ba, banaso yunwa ta kamani narame" Waheeda tace "to waye yace miki cin abinci ne takesa mutum qiba? Ai kwanciyar Hankali ne" Zulaihat tace "to idan bancin ba tayaya Hankali na zai kwanta?" Haka suka gama firarsu da yamma sukai class Washe gari suna aji babu malami a ajin, ta hango wata malamar hausa, yar Gayu ce malamar tanata taku daidai, Waheeda ta daga murya tace "Wanka yabi jiki malama" Cikin sauri malamar tajuyo tace "me kikace?" Waheeda tace "wanka yabi jiki" Bulala ce a hannun malamar aikuwa ta Juyo tashiga ajin saida tayiwa Waheeda Bulala shida, Ana gama mata Bulalar takade hannunta tace "aibaki birgeni ba tunda baki kasheni kinkaiwa su Babban Yaya gawata ba" Malamar ta kalleta tayi qwafa tafice daga ajin Ita Kuma Waheeda Takoma ta zauna,6acin rai ne yasa malamar tatafi staff room ta fadawa sauran malamai, anan kowanne malami yake fadar irin rashin jin datake masa, malamin Qur'an ne kawai bata masa ba Shima period dinsa tana shiga, yazo ajin yafara biya musu Qur'an suna karanta wa, Waheeda tafara surutu ahankali yana ganin ta ya shareta, dataga bai dauki mataki akan ta ba kawai saitaci gaba da surutun ta, saboda already tariga ta'iya wajan tun a islamiya, tsayawa yayi da karatun yace "inada wani uzuri yanzu, next week zan dawo muci gaba" yana fadar haka yafita daga ajin, yaga alama yarinyar bataji, idan yayi mata magana Kuma zata Iya masa rashin kunya agaban sauran Yara, Kuma hakan babu dadi, danhaka ya haqura dabiya musu karatun yafita ☹️ Da yamma suna hostel yau labour day ne, kowa share share yake makarantar tayi tsaf wata yarinya ce yar js1 ta kawo mata wasiqa, tana dubawa taga qawar Rabi'at ce ta aiko mata wasiqa tana sonta, yaga wasiqar tayi a wajan, tayi wani irin tsaki Haka Nan taji gaba daya makarantar tafita daga ranta, kullum addu'arta daya Allah yasa su Babban Yaya sudena cin qwallo,πŸ˜… Jira take gari ya waye ta kira Ummah a wayar wani malamin ta fada mata abinda yake damunta Da daddare tana bacci cikin dare taji kamar Ana shafa mata wuya, tayi juyi tasake shigewa cikin Bargo, taci gaba da bacci can taji anriqe mata nipples dinta Ana murzawa, gabantane yafadi tabige hannun tatashi cikin sauri tana dube dube, Dakin duhu qirin babu abinda take Gani, jikinta tafara ta6awa sannan tayi addu'ah Takoma ta kwanta, bacci me dadi yafara daukarta taji an toshe mata hanci da baki andanneta Ana matsa mata qirjinta, kokawa tafara Amma babu riba saboda mutum biyu ne, tanajin yanda aka cire mata Riga Sai murza mata nipples dinta ake kamar za'a cire mata su,kuka tasa tana motsi tana so ta qwace jikinta Amma takasa, Sai hawaye take babu damar numfashi babu damar magana, jitayi kwata kwata bata numfashi kamar zata mutu, ba tasan lokacin da tasa qafarta tahauri wata aciki ba, anan tayi nasarar qwace Boobs dinta daga hannun su, tana jin ansaki bakinta takurma wani uban ihu, aikuwa Yan dakinsu suka tashi, masu a'uziyya nayi masu kunna torch light nayi, daki ya dauki hayaniya, kowa yazo kanta yana tambaya menene, kasa magana tayi Sai zare idonta take tana Kalle Kalle, tahade jikinta waje daya, bata samu damar rera kuka Bama saide hawaye πŸ˜₯ A Daren, kasa komawa tayi ta kwanta, takuma sa a ranta tabar wannan Dakin daga yau, dakinsu Neenah zata koma, da safe kasa saka brezia tayi, saboda gaba daya kan nonon ciwo suke mata, jitake kamar ta ciresu ta jefar, gashi babu Ummah akusa, babu yanbiyu bare ta fada musu ko zataji dadi, haka tafita aji babu brezia Amma tasaka hannunta acikin hijabi babu Wanda zai gane Period din farko malamin qur'an yashigo ajin, yana ganin Waheeda gabansa yafadi, fatansa daya Allah yasa su wanye lafiya, yana biya musu, Bayan kowa ya karanta saiyace "akaranta mutum d'aid'ai" Layin farko sun fara biyawa, Waheeda takasa nutsuwa saida tafara yiwa Neenah magana akan abinda aka mata daran yau, tace "Neenah, yau dakinku zan dawo, jiya bakiji yanda akamin ba, aka kama kan Nono na aka riqe kamar za'a cire, har yanzu zafi nakeji yanda kikasan namutu wallahi, Kuma Ina tunanin su Rabi'at ne itada qawarta, saboda jiya da yamma qawartata har wasiqa ta aikomin tana sona, Kuma...." Kafin ta qarasa magana,ya mu'allim yace "ke..." Wata daga cikin yaran tajuyo ta kalli su Waheeda tace "Virus Ana magana" Waheeda tace "au Dani yake? Bansani Bama saboda ba daidai nakeba yau" Kallan ta yayi yace "ke futo Nan" Babu musu tafuto, ya dauki dorinar dake gefensa yafara tsula mata ajikinta, gashi jiki babu vest bare taji sauqin saukar bulala🀣, tun tana mazewa harta dawo tana kuka,haquri tafara bashi Amma ya mu'allim Sai dukanta yake, data gaji da shan azaba kawai saita tashi tayi masa ta Babban Yaya, ta cacimeshi ta rungume shi,πŸ™†πŸ»β€β™€οΈ? Aji aka dauki ihu, wasu daga cikin su suna cewa "Virus mu'allim ne" Sai ihu suke, mu'allim yayi azama yacireta daga jikinsa yatafi staff room ransa abace, yana zuwa yasamu principal cikin fishi yace "ranka yadade daga yau nayi resigned, nabar makarantar Nan, harni da girmana da komai yarinyar Nan zata rungume ni?" "wacce yarinya?" cewar principal "yarinyar Nan marar kunya mana Waheeda Virus, gaba daya ta addabi kowa,last week Ina karatu tanamin surutu a aji, ta ganni mun hada ido Amma taci gaba da surutu, to bazan iyaba, saide ku za6a koni ko ita" Principal yace Akira masa Waheeda, tana zuwa ta tsugunna agaban sa tace "Gani sir" Yace "Waheeda Yaya akai kika rungume ya mu'allim a aji? Kinada Hankali kuwa?" Hawayene ya silalo daga idonta tace "sir, dukana yayi, naji zafine sosai bansan na riqeshi ba" Principal ya kalli ya mu'allim yace "tokaji abinda tace, kaikuma metayi har akai mata irin wannan Dukan dahar yarinya zata kasa sanin ta rungume malami?" Ya mu'allim yace "surutu take muna karatun alqur'ani" Principal ya kalli Waheeda yace "meyasa kikai masa surutu yana aji, bakisan girman malamin ki bane?" Idonta ta goge tace "Sir jiyane da daddare Ina bacci ake ta6amin qirjina, shine nake Bawa Neenah labari a aji, shine ya ganni yace nafuto, Ina futowa Sai ya kama dukana" Gaba daya malam wajan ne suka hada baki tareda tafa hannu suna fadin "la'ilaha illallah....." Principal yazaro ido😳yace "aka ta6a miki me? Waheeda har sharrin naki yakai haka? Acikin makaranta ta ake aikata wannan ta'asar? To Bari kiji, saboda ke bazan yarda malami ya ajiye aikinsa ba, hakan bai isheki ba saikin hada kinyiwa dalibaina sharri, malamai sun gama complain akan ki bakya jin magana kwata kwata, saboda haka kitafi gidanku Sai iyayenki sunzo "πŸ™†πŸ»β€β™€οΈ? Waheeda tayi shiru tana nazarin maganar sa,gaba dayama satinta uku acikin karantar mezatacewa su Ummah agida idan suka ganta tadawo gida yau? Mezasu fadawa Babban Yaya? Bata gama tunani ba taji principal yace Akira masa mama mairo, matar datake kula dasu a hostel Mama mairo tana zuwa, yace "ga kudin mota Nan, kidauki wannan yarinyar, da duk kayanta, kikai ta gaban iyayenta kifada musu hukumar makaranta tace akawota gida Sai iyayenta sunzo" Mama mairo tacika umarnin principal, akaje aka debo kayan Waheeda, suka kama hanyar garinsu itace ta dinga nuna mata hanya har suka qaraso get din gidan, karfe goma shadaya daidai agida tamusu Ummah tana kitchen tana kokarin Dora abincin rana saboda yanbiyu suna makaranta, saiji tayi anfado jikinta Ana kuka Dafarko tsorata Ummah tayi, saboda tasan cewa ita kadai ce a gidan, tana juyowa taga Waheeda duk tayi baqi, cikin tsananin mamaki tace "Waheeda?!!!" 😱 Amnah El Yaqoub ✍πŸ? 1/28/22, 20:49 - Ummi TandamaπŸ˜‡: BABBAN YAYA Writing By Amnah El Yaqoub Like my Page On Facebook https://www.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493/ 7&8 Mama Mairo taqaraso kitchen din itama "Hajiya Ina kwananmu?" Ummah tasaki Waheeda ta kalli matar, ta manyan ta sosai, aqallah zatayi shekara hamsin dawani abu, tace "Sannu baiwar Allah, mu qarasa falo mana" Falo suka dawo suka zauna, Ummah ta nufi fridge zata kawo mata ruwa da lemo, mama mairo Sai jinjina Kai take tana qarewa falon nasu kallo, idan banda abu irinna iyayen wannan yarinya mezaisa 'yarsu tana rayuwa acikin wannan daula zasu dauketa su kaita boarding? Gashi Ana nema a lalata yarinya, koda yake kowa da halinsa Ummah tadawo ta zauna tabud'e lemon ta zubawa mama mairo tana cewa "ga lemo Kisha mama, meyake faruwa ne Naga Autata agida? Wani laifin ta aikata ko?" Mama mairo ta ajiye cup din hannunta Bayan tagama shan lemon tace "hajiya kinsan sha'anin Yara Sai hakuri,hukumar makaranta ce tace a dawo da'ita gida Sai iyayenta sunje" Ummah ta dauki waya tana fadin "subhanallah, Bari nakira Yayansu" Gaban Waheeda yafadi, tasan cewa inde yaji ankorota tabbas zai dawo qasar Nan, Kuma yayi mata gargadi karta yarda ya dawo qasar Nan saboda ita, saboda Dama can matsalar tane yake sakawa ya dawo, shide akaran Kansa yana dadewa kafin yazo gida, saboda yasan indai ya dawo to maganar aure zasu masa, cikin sauri ta riqe hannun Ummah tace "Ummah Dan girman Allah karki kirashi, kibar Yaya Sa'ad da Yaya Sa'eed sumin komai, Dan Allah Ummah kirufamin asiri kar Babban Yaya yaji" Ummah tazuba mata ido tana Kallan ta, tunda taga haka tasan cewa to Waheeda ta yi wani laifin ne, tace "saina kirashi Waheeda, shine daidai dake tunda ba zakiyi Hankali ba, Anya ma kuwa kina wanka Waheeda? Sati uku da tafiyar ki duk kinyi baqi kamar baki ta6a ganin ruwa ba?" πŸ€” Mama mairo tayi murmushi tace "Hajiya Bari nawuce kar rana tayi" Ummah tace "Ina zuwa mama" tashiga daki takawowa mama Mairo kudi dakuma turamen atamfa guda uku, cikin murna mama mairo takar6a tayi godia tayi musu sallama sannan tatafi Sai yabawa tsarin gidan nasu take Ummah ta zauna a kujera, tana zama Waheeda tadawo jikinta ta maqalqaleta,jitake kamar za'a sake maidata wannan makarantar, kwata kwata batajin dadi, Kuma batajin zata sake komawa saide tagudu ranar da'aka ce za'a maidata Ummah tace "Waheeda, kifadamin abinda kikayi aka koroki, rashin kunyar kika sake musu ko?" Kuka ta Fashe dashi,takasa magana, Ummah tazuba mata ido tace "ikon Allah, bazaki min magana ba kin tsaya kina kuka?" Cikin kuka tace "Ummah Dan Allah karku maidani, please karki fadawa Babban Yaya" Ummah tayi shiru batace da'ita komai ba, tasake daukar wayar ta tayi dialing number Naufal, har wayar tagama ringing ta katse bai dauka ba, Sai daga baya yakirata, Ummah ta dauka tace "Yayansu toga Waheeda Nan andawo da'ita gida, sunce Sai iyayenta sunje" "what?" abinda yace kenan Ummah tace "to haka de matar data rakota tace, hukumar makaranta sunce akawota gida Sai iyaye sunje" Shiru yayi yakasa cewa komai, itama Ummah tayi shiru, tayi tunanin ma bazai ce komai ba Sai can taji yace "Bata wayar" Umma ta miqawa Waheeda waya tace "ga waya inji yayanku" Cikin kuka tace "Ummah Allah Zagina zaiyi" tatashi tashige dakinsu da gudu cikin kuka Ummah ta maida wayar kunnanta tace "to taqi kar6a,Kuma Nima taqimin bayanin abinda tayi, matar data kawota Kuma tatafi, itama bata tsaya tamin bayani cikakke ba, Kuma tunda kaga ta 6oye ai kasan laifin Waheeda ne" "Allah yarufa asiri" abinda yace kenan Ummah tace "Amin" tareda kashe wayar, tasan dole zaizo, Kuma zai dauki mataki akan haka Waheeda saita taji Ummah tadena wayar sannan tadawo falon, Ummah ta kalleta tace "saikije kicire kayan ai, kiyi wanka, nasan bakya wanka Waheeda" dariya ce ta kamata, tayi murmushi ta wuce dakinsu, wanka tayi sosai, sannan ta kwanta bacci, bata tashi ba Sai daya saura, tana futowa falo taga Ummah tana waya da Hajiya Anty, tana fada mata Waheeda tayi Hali andawo da'ita gida πŸ˜‚ Kitchen ta wuce ta yanka salat, tafuto falo zata hada taci, yanbiyu sukai sallama, suna ganin Waheeda suka saki ihu, suka rungume juna Ummah ta Kalle su tayi murmushi tace "yauga wasu irin yayu, kunganta agida bazaku tambayi dalili ba kawai saide kuhau ihun murna?" Babu Wanda yabawa Ummah amsa, duk sun riqe Waheeda suna murna, Ihsan tace "Waheeda kinga yanda kikai baqi? Ko wahala kikesha?infada miki Waheeda tunda kika Dena zuwa makaranta qawarki Maya tazama shiru shiru, abun tausayi kamar anmata mutuwa, saide tazo wajanmu ta zauna" Waheeda tace "hmm kede Bari kawai Ihsan, Nima nayi missed dinku,boarding babu dadi" Intisar ta kalli salat din dake gaban Waheeda tace "to aqara yanka wani tumatir din mana" Waheeda tasake yanka tumatir taja flet din gabanta zata fara Ci, suma suka matso, wani irin kallo tamusu ta kalli Intisar tace "waida harda ku kike nufi?" Basu kulata ba suka fara ci, ganin haka yasa itama kawai ta sharesu sukaci salat din gaba dayansu Wunin ranar, haka su Waheeda sukayi shi cikin marmarin juna, babu fada, sun had'e kansu, Sai labarin makaranta take basu kamar basune kullum cikin fada ba. Kwananta uku agida, Babban Yaya yazo, wannan Karon zuwan dare yayi, shiyasa baisamu cikowar mutane sosai ba, wayar Ummah ce a hannun Waheeda tana yin game, su yanbiyu suna ta Bawa Ummah labarin qawayensu, Sa'ad da Sa'eed suna dinning suna dinner, cikin falon yashigo bakinsa d'aukeda sallama, yana Sanye cikin qananun Kaya dasuka kar6i jikinsa, lokaci daya qamshin turaren sa yacika falon, Waheeda tadago kanta sukai ido biyu dashi, yasaka p-cap yasaka facemask, dakuma wani glass Jan duhu, kwata kwata idan a hanya kuka hadu ba zakace shine ba, ya 6oye kamar sa ne saboda kar mutane su ganeshi suhanashi tafiya, shikuma yagaji sosai hutu yake buqata, ko awanne Hali yake ciki Waheeda zata ganeshi,duk da ya6ata mata rai ya kaita boarding bata jin zata Iya fishi dashi, tanajin sa sosai acikin ranta, ta dauke shi tamkar aboki kokuma wani Amini Nata na daban,yanada mutuqar muhimmanci acikin rayuwar ta Ahankali ta ajiye wayar Ummah agefenta, cikin dakiya tanufeshi tace "Babban Yaya sannu da zuwa" Tayi maganar tana qasa da fuskarta, Dan tayi tunanin zataji saukar Mari, Amma ga mamakin ta saiyace "Yauwa" Yabata wata leda me kyau tareda nuna mata yanbiyu yace "kibasu" Juyawa tayi cikin ladabi, tabawa yanbiyu ledar tana jira su bude taga menene aciki, suna budewa kuwa sukaga Kayane English wears masu kyau riga da siket, komai iri daya babu banbanci a kayan, murna sukai hauyi kamar qananun Yara, Waheeda tacika tayi fam, Takoma Gefe ta zauna 🀣 Babban Yaya ya qarasa wajan Ummah yazauna,tareda Dora Kansa akan kafadarta, Ummah ta Kalle shi tace "ya Hanya?" Kafin yabata amsa su Sa'ad su kazo wajan sa suka zauna, suna masa sannu da zuwa, sumar Kansa ya shafa Bayan ya amsa musu ya kalli Ummah yace "Ummah nagaji wallahi, bacci nakeji" "to meyasa kataho da daddare? Dakayi zamanka da safe kataho" Cikin shagwaba yace "Ummah sonake naganki wallahi" "yau Kuma shagwabar ce tatashi?" cewar Ummah Dariya yayi, dimples dinsa suka futo, yace "Ummah, yarinyar can ta fada miki abinda yasa suka dawo da'ita gida?" Ummah ta juya ta kalli Waheeda taga Sai fishi take, tace "gatanan ka tambayeta ko zata fadama, nide ba tacemin komai ba" Fuskarsa ya daure yace "babu abinda zan tambayeta Ummah, ta shirya kawai gobe zan maidata da kaina, nakira principal din but bai dauki wayata ba" Ummah ta kalli Waheeda tace "kinji meya ce ai ko? To saiki shirya" Babu musu Waheeda tace "to Ummah Allah yakaimu" Amma cikin ranta tariga tagama shirya yanda zata gudu tabar gidan, bazata dawo ba Saitaji labarin Babban Yaya yakoma Tashi yayi zai wuce dakinsa,cikin shagwa6a Waheeda tace "Babban Yaya Toni Ina nawa kayan?" Juyo wa yayi ya kalleta,yaso Ummah bata Nan dasai yadaki yarinyar Nan, to babu halin duka yanzu, tunda Ummah tamasa fada last time cewa ya dinga jansu ajikinsa, saida ya daure sannan yace "bakiga iri d'ayane kayan ba? Ke yanbiyu ce? Suma nagani ne Kuma su kenan qwaya biyu, shiyasa na Dauko musu" Tace "to nifa?" "kiduba irin Wanda kike so" yana fad'a mata haka ya wuce d'akinsa, Ummah ta kalleta tace "tashi ki had'a abinci kikai masa" Babu musu Waheeda ta nufi kitchen cikin farinciki batare da damuwar komai ba,Dama Babban Yaya takeji, Kuma taga alamun bazai daketa ba Sosai ta nutsu wajan had'a masa abincin, yanda take had'a komai cikin tsafta zaka iya rantse wa mijinta take hadawa abincin, d'auka tayi ta nufi d'akin nasa, daga bakin kofa ta tsaya tayi masa nocking, saida ta dade a tsaye sannan yazo ya bude mata 'kofar, saura kadan tasaki tiren dake hannunta, sakamakon yanayin data ganshi, dagashi Sai wani Dan gajeran wando, da alama ma wanka zai shiga, gabanta yake faduwa ahankali, cikin nutsuwa ta qarasa gabansa tayi azamar ajiye abincin saboda hannunta rawa yake tsaf zata Iya zubarwa, tarasa meyasa Babban Yaya yake abinda yakeso agaban ta, kwata kwata bayajin kunyar cire Kaya agaban ta, bayajin kunyar su zauna tareda ita dagashi Sai towel din wanka, tasan inda yanbiyu ne cewa zaiyi raina shi zasuyi idan suka ganshi Ahaka, to meyasa ita yake mata haka? Wata zuciyar tace da'ita, may be Dan kun shaqu ne, tunda yana iya hira dake Amma ba yayi da Yanbiyu, ajiyar zuciya ta sauke tafara zuba masa abincin, saida tagama sannan tanemi waje ta zauna, Kallan ta yayi yace "Lafiya?" "Babban Yaya Dan Allah kayi hakuri" tafad'i haka hawaye yana silalo wa daga idanunta "laifin me kika aikata dazaki Bani hakuri?" "Babban Yaya nasan na takura ma, wallahi Nima ba laifi na bane, yarinyata ce take damuna kawai" πŸ˜₯ Yace "are you serious?, 18 yrs Amma kina cewa yarinta ce take damunki, me kikayi a school din suka koreki?" Shiru Waheeda tayi, tayaya zata masa bayani? Ce masa zatayi tana yiwa malaman makarantar rashin kunya kokuma dayan maganar zata fada masa? Tayaya zata Iya fada masa magana me nauyi irin haka? Yayanta uwa d'aya uba d'aya shi zata kalla tace wasu suna ta6a mata nonuwa Aida kunya Hawaye ne suka zubo daga idonta, tasaka hannu ta share tace "kayi Hakuri Babban Yaya" Kallan ta yayi cikeda mamaki, kawai daga tambaya Sai kuka? Ajiyar zuciya yayi yace "shikkenan, tunda haka kika za6awa rayuwar ki, kina ganin yan'uwanki, banta6a zuwa gida ta dalilin matsalar suba, koda yaushe kece sanadin zuwana, Kuma tunda kika girma kikai wayo babu ranar farinciki dakikamin sanadin zuwanta, kullum matsalar kice takesa nabar aikin danake nazo, kwata kwata bakya tausayi na kamar sauran yan'uwanki,duk zuwan da zanyi Sai iyayena sunmin maganar aure, Bayan kinsan banaso,to saboda me danna Sai musu Kaya zakiyi fishi " Kanta aqasa tace" kayi hakuri Babban Yaya" Yace "hmm kamar gaske, Bani abinci na kitashi kitafi" Abincin tabashi, Amma takasa hada ido dashi, kar6a yayi yafara ci ahankali kamar yaro qarami Wanda baisan abinci, d'agowa tayi ta Kalle shi, ahankali tatashi tahau kan gadon, ta zauna dab dashi, spoon din hannun sa tariqe, ya kalli yanda tariqe masa spoon din yace "miye haka?" Cikin shagwa6a tace "to Babban Yaya bakacin abincin fa sosai" wani irin abu yaji tundaga Kansa har zuwa tafin qafarsa,kamar bashi ba, Sai gashi ya gagara yimata musu, sakar mata spoon din yayi, tafara bashi abincin yanaci,Kallan ta yake yana mamakin yanda tayi kama dashi sosai, komai nashi ta Dauko, babu wani qarin bayani idan kaganta ka ganshi kasan cewa jini daya ne. Yace "kishirya da wuri gobe" Maimakon tabashi amsa Sai tace "Babban Yaya induba rigar danake so a internet saina kawo ma kagani?" Yace "kiduba" Mamaki yahanashi kasa yimata wata maganar ta makaranta, tunda yaga alamun akwai abinda take 6oye masa Saida tagama bashi abincin haryana mamakin yawan abincin dayaci,fita tayi da kwanukan, shikam toilet yashiga yayi wanka,yayi sallolinsa, sannan ya kwanta Waheeda kuwa wayar Ummah ta d'auka tabud'e data, daga Nan tashige dakinsu tafara browsing din rigar datake so, Sai wajan shadaya nadare taga rigar, da'inda zaka tura musu kudin su aikoma da rigar,Hankalinta yanakan wayar tace "Ihsan Dan Allah kalli rigar Nan batayi kyau ba?" Taji Ihsan tayi shiru babu amsa, tana juyawa taga duk sunyi bacci ita kadai suka Bari, tashinta ta farayi tace "Ihsan, Ihsan tashi kigani" Ihsan tabude idonta ahankali cikin bacci ta kalli photon rigar, ta kalli Waheeda, tace "wannan yar'iskar rigar duk nonuwa awaje zaki nuna masa? Shi Babban Yayan mahaukaci ne zai siya miki irinta?" taja tsaki Takoma baccin ta Waheeda tace "to ai saiki hanashi siya" Takoma wajan intisar tafara tashinta, Bayanta tafara duka tace "inti, kinga rigar danake so Babban Yaya yasiyo min, tayi kyau ko?" Intisar tabude idonta tace "waike Waheeda Dalla Sai mutum yana bacci kibi kidameshi" Waheeda tace "maida wuqar, niba masifa ce ta kawo ni ba, duba rigar kigani" tsaki intisar taja sannan ta kar6i wayar ta kalli rigar tace"waheeda bakida Hankali riqe wayar Nan Dan Allah " Fizge wayar tayi tafice daga Dakin ta nufi Dakin Babban Yaya, zuciyarta d'aya tatura kofar Dakin tashiga, duhu ya mamaye ko'ina, Sai sanyin esi dake ratsa ko'ina acikin Dakin, Lumshe idonta tayi sakamakon qamshin data shaqa me dadi, fitilar wayar ta kunna, ta qarasa gadon, ta zauna adede Kansa tana qare masa kallo, Babban Yaya yahadu sosai, babu macen da zata qi yayanta, tarasa meyasa yake gudun aure? Inama ace Allah zai bata Miji, Mai kamar yayan Nata, ta tabbatar datafi sauran mata sa'ah,baccin sa yake Hankali kwance, duk wannan sanyin esin dayake ratsa Dakin shikam babu riga ajikinsa, gajeren wando ne ajikinsa Amma ba Wanda ta ganshi dashi dazu bane, ya sauya wani. ajiyar zuciya tayi, sannan tafara bubbuga Fillon daya d'ora Kansa tace "Babban Yaya, Babban Yaya ga photon rigar nakawo" Cikin baccin sa yaji kamar a mafarki Ana Kiran sunansa, hannunsa yasa ya fuzgo ta tafad'o Kansa, wayar Ummah dake hannunta tafad'i can Gefe kan kafet d'in dake malale atsakar 'Dakin nasa Gabantane yafad'i, idanunta yayi tsilli tsilli, ta zubawa qwayar idonsa ido tana kallo,Sanyi yana ratsa tafin hannunta data Dora akan lallausar farar fatarsa Shima anasa 6angaren kallon ta yake cikeda mamaki Kowa yana jin yanda bugun zuciyar dan'uwansa yake gudana, sunkai kusan minti biyu Ahaka, sannan yabude pink lips dinsa, cikin wata irin murya tamkar bashi ba yace "meyakawo ki Nan?" In-ina tafara tace "Babban Yaya... Dama... Dama rigar nazo in nuna....." kafin ta qarasa magana yace "Shiiiiii" tareda Dora hannun sa akan lallausan lips dinta hakan yasa tajita kwance akan fatar jikinsa da babu riga "mugani" shine abinda yace Wayar Ummah dake Gefe ayashe ta Kalla, sannan tasaka hannu tazare nasa hannun daya rufe mata baki tace "kayarda wayar ai" Idanunsa ya Lumshe yace "d'agani" Yana jin yanda take sake had'a jikinsu tana kokarin tashi, runtse idonsa yayi tareda sakin wani irin zazzafan numfashi, wayar ta Dauko ta nuna masa photon, ya kalleta yace "nagani,tashi kitafi" Babu musu tafice daga Dakin nasa, Hankalinta kwance Tana fita ya runtse idonsa, hannunsa yad'ora akan mararsa tareda rungume fillon dake gefensa, daqyar yazubo qafafunsa qasa, yabud'e bedside drower ya dauki wani magani yazuba cikin bakinsa, gorar ruwan da Waheeda ta kawo masa abinci d'azu ita ya d'auka yakafata a bakinsa saida ya shanye ruwan tas, sannan yafara maida numfashi kamar Wanda yayi gudu, Idanunsa suka kad'a sukai jajir, ahankali yakoma kan gadon yayi kwanciyar rub da ciki,wata irin muguwar sha'awa yakeji, maganin Nan ne kawai yake taimakon sa, rufe idonsa yayi sannan yasamu bacci yayi nasarar sace shi. Baisamu sallar asuba ba, saida gari ya waye sannan yayi, alokacin Waheeda harta gama shirya wa, kawai hanyar guduwa take nema, to Ummah kamar tasan shirin da take, danhaka takira ta dakinta tasakata gyara mayukan dasuke Saman mirror dinta kafin yayansu ya shirya Duk yanda taso guduwa gaba daya tarasa mafita, Sai wajan karfe goma da rabi yafuto, Sanye yake cikin qaramar Riga, dakuma wando three quarter, zama yayi afalo ya Lumshe idonsa, yanayin jiyane yake dawo masa, gaba daya jikinsa a mace yake, koda yaushe yana mata umarni Amma bata son bin dokarsa, kullum idan yayi mata fada yace ta daina rashin kunya dakuma laifi to saita sake aikata wani laifin, but meyasa jiya yana cewa tatashi daga jikinsa tatashi? Meyasa bata bijremasa ba taqi tashi?meyasa tabi umarninsa Akaro nafarko? πŸ˜³πŸ™†πŸ»β€β™€οΈ? Cikin sauri ya kawar da wannan tunanin nasa tareda dafe Kansa yana jijjiga Kai πŸ€¦πŸ»β€β™‚οΈ? "kaikuma lafiya ka zauna anan kana jijjiga Kai kamar marar lafiya?" cewar Daddy daya shigo tareda Uncle Usman Uncle Usman yayi murmushi yace "to inbanda abunka Alhaji, Ina za'a samu lafiya ga tuzuru? Ai duk abinda yayi saide ayi masa uzuri, rashin aure ne yake damunsa" Firgigit yad'ago da Kansa ya kalli iyayen nasa, cikin kunya yafara Sosa qeyarsa, sannan ya sakko daga kan kujerar yana gaida su Uncle Usman yace "Baku tafi bane?" Cikin girmamawa yace "uncle Ina jirantane" Daga murya yayi yace "Waheeda me kike jirane tun dazu yayanki yana jira?" Gabanta ne yafadi dataji muryar uncle din Nata yana kira, kode ta fada musu gaskiya ne? Kai bazata iyaba, Gara tasamo wata mafitar kawai Futowa tayi jikinta a sanyaye, idanunta na taruwa da qwalla, Ummah ta riqe hannunta tace" kiyi shiru mana Auta, ai kamar yaune zakiga kinga ma, ko so kike Nima nayi kukan? " Cikin sauri ta girgiza kanta, lokaci daya tafashe dawani irin kuka, daga Daddy har Uncle Usman, Babban Yaya, Ummah, su Sa'ad da shigo war su kenan, babu Wanda mamaki bai kamashi ba, haqiqa akwai abinda take 6oyewa, Babban Yaya ya tashi zai futo daga falon, Uncle Usman ya Kalle shi yace "Da wannan wandon zaka tafi makarantar ne?" Kansa ya kalla, shi Yama manta three quarter ne ajikinsa, kafin yace wani abu Daddy yace "tosuda suke ball da gajeran wando duniya tana Kallan su, surukansu suna Kallan su Ahaka, inane ba zaije da Wando three-quarter ba?" Babban Yaya ya sunkuyar da Kansa tareda shigewa d'akinsa ya sauya Kaya zuwa wani lallausan yadi milk colour, yad'ora wata had'ad'd'iyar hula wadda ta kar6i kyakykyawar fuskar sa, ba qaramin kyau yayi ba kasancewar baya saka manyan Kaya, idan ka Kalle shi tsaf zakace wani hamshaqin magidancin ne Sallama yayiwa iyayen nasu yafice zuwa compound, wani Dan qaramin remote ya danna motar ta kawo wuta, Ummah ta rako Waheeda har gaban motar, sannan tajira saida taga tafiyarsu sannan Takoma cikin gida ranta duk babu dadi. Sunyi Nisa cikin tafiya bakajin qaran komai Sai sautin karatun qur'ani dayake tashi, Waheeda taga de da gaske Babban Yaya maidata school dinnan zaiyi, tatuna Irin yanda su Rabi'at suka danneta suna mata mugunta, tajuya taga Babban Yaya kawai driving yake, tarasa Yaya zatayi kawai saida d'ora kanta akan cinyoyin ta tafashe masa da Kuka Juyowa yayi ya kalleta, yasamu gefen titi ya faka motar, yasake juyawa yana fuskantar ta sosai, cikin wata irin murya kamar me rad'a yace "meya faru Kuma?" Kuka take sosai harda sheshsheka, ta gagara bashi amsa, Dan qaramin tsaki yasaki yafara kokarin tada motar, cikin sauri taruqo hannunsa tace "Dan Allah Babban Yaya karka kaini" Kallan ta yayi sosai yace "nace kifadamin dalili kinqi, nace kifadamin me kika yi suka koreki kinqi, mekikeso Kuma?" Cikin kuka tace "Allah Babban Yaya idan ka mayar Dani kasheni zasuyi, har yanzu abinda sukamin bai daina min ciwo ba" Zaro idonsa yayi, cikin faduwar gaba yace "mesuka miki?" Hijabin jikinta tacire, Babban Yaya yazuba mata ido yana Kallan ikon Allah Hijabin ta ajiye agefe tace "Babban Yaya wasu ne saisu dinga ta6amin Boobs dina, rannan cikin dare suka danne ni, suka rufemin hanci na, nipples dina kamar zasu cire haka nakeji, Sai ciwo sukemin, kagani ma" Taqarasa maganar tana kokarin nuna masa breast dinta, duk yanda yaso kaucewa yana rufe idonsa Dan karya Gani, saida yagansu,farare dasu sosai, nipples din Nata yayi ja sosai shima, cikin sauri ya runtse idonsa, gabansa banda wata irin faduwa babu abinda yake, wata irin muguwar kunya ce tarufe shi, meya aikata haka? Waheeda cefa.... Jikinsa har rawa yake cikin tsawa yace mata "kirufe jikinki malama, nace ki nunamin ne?" Cikin sauri ta maida hijabin ta, tana share Hawayen idonta, gaba d'aya yanayinsa yafara sauyawa, yaji mararsa tana nema ta qulle, cikin sauri yafara dube dube a motar, saida yaga maganin sa Sannan ya6alli guda biyu yasha, yajinginar da Kansa ajikin kujerar, tareda Lumshe idonsa Waheeda tace "Babban Yaya bakada lafiya?" "Lafiya" abinda yace kenan, sannan ya data motar, babu musu yajuya kan motar zuwa tsohuwar makarantar su, inda yanbiyu suke, haqiqa yaso ya tafka Babban kuskure, inda ace yarinyar Nan tayi shiru ya maidata makarantar me nene zai faru agaba? Idan ta lalace wa Allah zai hukunta Bayan shi? Tunda iyayensu sun dauki yarda da komai sun bashi, tsaki kawai yake saki, gaba daya yaji duniyar tamasa zafi, suna cikin tafiya taji yataka wani mahaukacin birki, tsoro ya kama Waheeda, tajuya ta Kalle shi ta kasa magana saboda tsantsar 6acin ran data Gani a fuskar sa, Juyowa yayi ya kalleta tare da fadin "menene sunayen yaran dasuka miki haka?" Cikin sauri ta zayyano masa sunayen, wayarsa ya dauka ya turawa principal din makarantar sunayen sannan yayi masa qarin bayani aqasa, dago Kansa yayi ya kalleta yace "saboda ke mahaukaciya ce, ashe a makarantar ma zuwa kike kina nuna musu jikinki ko? Ban hanaki yawo babu hijabi ba?" Girgiza kanta ta farayi cikeda tsoro tace "Allah Ina saka hijab dina" "qarya kike bakya sakawa, idan kina sakawa ma to cirewa kike, yanzu inda da abokina muke tafe haka Zaki budemin nagani agaban sa ko? Kinaso ki kasheni kiga bayana kihuta, ai haka kike so ko?" Hawayene suke zuba a'idonta, wani nabin wani, ta girgiza masa Kai tace" Allah Babban Yaya bazan nunawa kowa ba, kaima bansan na nuna Maka ba, Kuma babu wani namiji danake fatan yagani a yanzu" Cikin 6acin rai yace "koma de menene, karki sake min maganar wani agabana, nafada miki" Haka Waheeda taja bakinta tayi shiru, har suka qarasa school dinsu ta da bai qara mata magana ba itama bata masa ba, Kai tsaye office din director sukaje, yasaka Waheeda ta tsugunna tabasu hakuri, Sannan yaroqi alfarma abarta Taqarasa karatun ta, kasancewar yanzu sun huce da laifin data musu, dakuma yanda suke ganin qimar Yayan Nata, shiyasa babu 6ata lokaci suka kar6eta, yawancin malamai suna aji shiyasa wannan Karon bai tsaya sauraren mutane masu masa magana ba, dakuma irin yanayin dayake ciki na 6acin rai. Waheeda tana bayansa,zata rakashi wajan motar sa, Maya ta hango tana tahowa wajan su, Waheeda tace "Babban Yaya kaga qawata Maya" Yana kokarin shiga mota yajuyo ya kalleta yace "Sunanta kenan?" Tace "Yes, Maryam Ahmad, Yusuf Amin, shine muke ce mata Maya" Kafin Yayi magana ta qaraso, cikin murna ta rungume Waheeda, tasake ta ta gaida Babban Yaya cikin ladabi, Nan da Nan yayaba da Hankalin yarinyar, yasan idan Waheeda tana tareda ita, zata qara Hankali, amasawa yayi yace "kudinga karatu sosai" Dariya takama Waheeda Amma saita danne, Wai kudinga karatu sosai, wannan shine fadan da akewa dalibai, Maya tace masa "insha Allah Babban Yaya" Ta kalli Waheeda tace "Waheeda zan tafi gida, Sai wani lokacin" Waheeda tace "Naga ba'a tashi ba, meyasa Zaki tafi?" Idanunta ne suka kawo ruwa tace "Waheeda kudin School fee's ne baba bai kawo ba, shine sukai kora" Tausayinta yakama Waheeda, tasan Maya da naci akan karatu, tanason karatu sosai, cikin sanyin jiki tace "kiyi hakuri Maya karkiyi kuka" Babban Yaya yata6e bakinsa tareda ajiyar zuciya, Yara qanana suna wani Iyayi saika ce Wanda suka San ciwon kansu 🀣 Motarsa yabude ya Dauko kudi dami biyu yan dubu dubu, aqalla zasu Kai kusan dubu Dari biyu, yabawa Waheeda yace "kibata" Daga Nan yashige mota tareda ficewa daga makarantar Maya ta kalli Waheeda suka rungume juna cikeda murna, daga Nan suka tafi Class dinsu Tafiya yake amota yanaso yaje gidan hajiya Anty tun kafin ta masa qorafi baya zuwa, wayarsa ce yaji tana ringing, dauka yayi tareda karawa a kunnansa, daga d'ayan ban6aren principal yace "Kayi hakuri yalla6ai, abun baikai da Sai ansako hukuma aciki ba, insha Allah zansa Akira yaran a yimusu hukunci daidai da abunda suka aikata, sannan dole iyayensu zasu San abunda suke aikata wa, ni bazasu 6atamin makaranta taba" Babban yace "Yarage Naka, Amma muddin baka dauki mataki akan yaran nan ba, to zaka ganni a cikin makarantar ka" yana fada masa haka yakashe wayarsa Wata wayar ce tasake shigo wa, yayi tunanin principal ne yasake kiransa, cikin masifa ya daga yace "Wai ya akayi ne Kuma?" Daga d'ayan bangaren akace "babu abinda akayi Saide wadda za'ayi yanzu, Naga alama baka gane me magana ba, to Abubakar ne yayan mahaifin ka Umaru" πŸ˜‚ Babban Yaya yadafe Kansa, ya tsaida motar agefe titi yace "Baba Ina kwana?" "daban kwanaba zaka ganni ne Naufal balle harna kiraka awaya?" Babban Yaya yace "kayi hakuri baba" Baba Habu yace "Magana nakeso muyi dakai ta fahimta, nasan idan ka 6oyewa iyayenka Toni bazata 6oyemin ba, tunda nasan cewa akwai alkunya tsakanin d'a da mahaifi, Naufal kafadamin gaskiya idan kasan bakada lafiya munan damuke qauye akwai sassaqe yana Nan Kala Kala saina had'o Maka shi na aiko kafara gwadawa ko za'a dace "πŸ˜… Girarsa guda d'aya ya Sosa da key din Motarsa , yace"Baba lafiya ta kalau" "to idan lafiyarka kalau meyasa kake gudun aure?" "Akwai wacce nakeso Baba" Yafadi hakan Kansa tsaye Baba Habu yace "to Alhamdulillah, masha Allah, to kokai fa, a'ina yarinyar take? Yar wanne Gari ce?" Shiru yayi, yakasa Bawa yayan mahaifin nasa amsa, Sai can yace masa "Baba Nima bansan inda take ba" Cikin masifa Baba Habu yace "zancen banza zancen wofi, wannan ai shirme ne, tunda haka kake so ai shikkenan, ka shirya kaje kaga Nadiya yar gidan abokin uncle dinka Usman, Usman yacemin yarinya Tariga tasanka, saboda haka Sai kaje kaganta kaima" dif yakashe wayarsa, yabar Babban Yaya da waya Akunne To koyaya zata Kaya tsakanin sa da Nadiya? Masoyan BABBAN YAYA Ina godia sosai, nayi tunanin bazaku sayi littafin ba ☹️☹️ Amma abun mamaki tun kafin free page yaqare masu turo 400 sunfi masu 200 yawa, nagode Allah yabar zumunci Amnah El Yaqoub ✍πŸ? Amnah El Yaqoub ✍πŸ? 1/28/22, 20:49 - Ummi TandamaπŸ˜‡: BABBAN YAYA Writing By Amnah El Yaqoub Like my Page On Facebook https://www.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493/ 9&10 Bakomai ne ya tsaya masa Arai ba Sai yanda yace yarinyar tariga tasan shi, hakan yana nufin idan yaje zata soshi tunda Dama tariga tasan shi, shine bai Santa ba, duk yanmatan da ake had'ashi dasu babu wadda ta sanshi, koda sun ganshi ma baya fadar sunan da aka sanshi dashi saide yace musu sunan sa Naufal, Amma ita wannan ta wacce hanya zaibi yarabu da'ita? Bashida burin auren mace biyu, kamar yanda ya tashi yagani a gidansu Ummansu ita kadai ce, Hajiya Anty ma ita kadai ce, to ita da bata haihuwa ma mijinta yayi hakuri ya zauna da'ita, to shida ba mazauni ba tayaya zaiyi ta aurar 'ya'yan mutane yana tafiya harkar qwallo? Ajiyar zuciya ya sauke, yanufi gidan Hajiya Anty, gidan yayi kyau sosai,tsarin gidan komai da komai irinna Ummah ne, saide furnitures dinne kawai suka banbanta Tana Sanye cikin atamfa, tariqo mayafin a hannunta, wuyanta da yatsun hannunta duk sunsha gold,tayi kyau sosai abinka da mace yar Gayu, Car key ne a hannunta tana kokarin fita sukaci Karo da Babban Yaya, tace "A a, yaushe agari?" Bai bata amsa ba Sai kokarin shigo wa falon da yake, bayansa tabiyo suka dawo falon suka zauna, Kallan ta yayi yace "Anty fita zakiyi ne?" "eh zan fita, akwai meeting din da zamuyi karfe daya" Ajiyar zuciya yayi "ke Anty babu ruwanki bakida damuwar komai"πŸ˜” "Kai din damuwar menene a ranka?" Goshinsa ya dafa yace "gatanan dayawa Anty, yau matsalar Waheeda gobe matsalar ku" Dariya tayi tace "To Waheeda matsalar ta ai takace, kaida ita ai qawaye ne, Kuma inda Sabo kun saba, qanwar kace babu yanda zakayi da'ita, mukuma tamu matsalar ai bazaka kirata da matsala ba, tunda mune akan gaskiya, Naufal har wanne lokaci zaka dauka babu aure? Ko so kake Sai yanbiyu maza sunyi aure sannan zakayi? Maryam fa tayi aure harda takwara anyi Maka, kaikuma gaka Nan gemai gemai dakai babu aure " "Anty shi aure lokaci ne" yafadi hakan cikin damuwa Tace "Hakane, Allah ya nuna mana Naka lokacin, yaushe kazo qasar?" "jiya nazo Anty, nazo na maida Waheeda school, sannan Baba Habu yamin waya naje Naga yar abokin Uncle, Wai Nadiya" "aiya wuce 'Wai' Naufal, Nima nasan yarinyar tun tana qarama, nasan wannan Karan insha Allah baza'a samu matsala ba, mun kusa shan biki" ta qarasa maganar cikin murmushi Ajiyar zuciya yayi yace "Anty kenan, ni yanzu babu wacce nakeso, Kuma bazan iya auren yarinyar da banaso ba, maganar gaskiya kenan, idan kema kin gaji da ganina haka saiki Bani 'yarki" (tofa) Kallan sa tayi, jikinta yayi Sanyi, hannun sa takama ta riqe tace "inda ace na Haifa ai zan baka Naufal, ka daure kaje kaga Nadiya, insha Allah zata Maka" Yace "to Anty insha Allah anjima da yamma zanje" Tare suka futo daga gidan, saida yaga tashiga motar ta tafita, sannan ya qarasa wajan Maigadin gidan, sallama yayi masa, Baba yusha'u yace "Yalla6ai ko akwai abinda kake buqata?" "kayanka nakeso kabani Baba, zanyi amfani dasu" "kayana Kuma Yalla6ai,kaida kanka? lafiya dai ko?" Murmushi yayi yace "karka damu baba, nine zanyi amfani dashi, kahada mun harda wayar ka" Jiki na rawa Baba yusha'u ya 'Dauko masa kayan, tareda wayar " Ya kalli kayan yaga sunyi yanda yakeso, sannan ya kalli Baba yusha'u yace" Baba wannan wayar ai kalau take, babu wadda tafita tsufa? " Baba yusha'u yace" eto, saide wata tsohuwar wayata data lalace idan aka kirani banaji Kuma ba'a Jina, Kuma murfin wayar baya zama da kyauro nasa nariqeta, kafin hajiya ta sauya min wannan "🀣 Babban Yaya yace "yawwa, Bani ita" Baba yusha'u ya Dauko yabashi, yakar6i kayan yajuya yashiga motarsa sannan yabar gidan Kai tsaye Gida yakoma, yabar kayan acikin motarsa, yanbiyu da Waheeda suna falo sunacin abinci, Ummah tayi masa sannu da zuwa tana Bawa yanbiyu magani, zama yayi a kujerar yace "Ummah wace ba lafiya Kuma?" Yanbiyu ta nuna masa tace "gasunan, kasan halin jinyarsu ai, idan daya tafara dayar ma Saitayi, Wai cikin su ne yake ciwo" "ok Allah yasawaqe" Ya kalli Waheeda yace "ki gama nakai ki islamiya tunda su babu lafiya" Ranta ne ya6aci cikin shagwa6a tace "to Babban Yaya subazasujeba saini kadai? Lafiyarsu kalau wallahi, tsabar sharri ne kawai" Wani irin kallo yamata, Nan take tayi shiru ko qwaqwqwaran motsi bata sake yiba Dinning ya nufa da Kansa, yazuba abincin yanaci yana Kallan TV sama sama, har Waheeda tagama taje daki tafuto cikin shirin islamiya, ta kalli Ummah tace "Ummah zan tafi, saimu dawo tareda Maya, tunda yanbiyu bazasuje ba yau" Ummah tace "saikun dawo" Tashi yayi zai fita, ya kalli Ummah yace "Ummah naje gidansu Nadiya" Murmushi Ummah tayi tace "Aida kabari Sai gobe, yanzu Naga alamun Garin akwai hadari, Amma idan kaje gobe zakufi sakewa ku Tattauna" Yace "no,Ummah zanyi sauri naje insha Allah" Cikin farinciki tace "to a dawo lafiya, ka kula da kanka" Waheeda tace "to Ummah karki damu Nima zan kula dashi" Ummah tace "Allah ya shiryeki Waheeda" Waheeda tashiga gidan gaba taja murfin motar tarufe, tajuyo taga Babban Yaya yana Kallan ta, idanunta tajuya tace "Babban Yaya lafiya?" "meyasa kikasa Ribom a kanki?" Dariya tayi tace "laaa Babban Yaya bafa Ribom bane" Muryarsa ya rage kamar yana tsoron wani yaji sannan yace "qarya kike yi, to mugani" Hannu tasa tajanye hijabin daga kanta, dogon gashinta Mai tsantsi ya baiyana, ta dago tana Kallan sa tace "kagani?" Ahankali yakai hannunsa kan gashi Nata, ya gyara matashi, sannan yace "nagani, mayarda hijabin" Kallansa tayi tace "Babban Yaya idan baka so nadinga acuci da gashina kabani kudin kitso" Kafadarsa yadaga yace "no, karkiyi kitso, kibarshi haka yafi" Babu musu tace masa "to, mutafi karna makara" Gyara zama yayi yace "kinsan de Banason aure yanzu ko?" Mamaki yakama Waheeda, takasa magana saita gyada masa Kai kawai, ajiyar zuciya ya sauke, yakai hannun sa Mai laushi yakamo Nata hannayen yace "su Baba Habu sun hadani da wata yarinya Nadiya, idan na saukeki a islamiya wajan ta zanje yanzu, inaso na gwada sa'a ta ko Allah zaisa narabu da'ita" Waheeda ta kalli qwayar idonsa, tana so ta tambayeshi abinda yadade Yana yawo a ranta, Amma tana tsoro karya mata fada, dakewa tayi, tayi jarumtar cewa "to Babban Yaya meyasa baka son auren? Sune baka so kokuma auren ne duka baka so?" Kai tsaye yace "sune banaso" Cikin mamaki tace "towa kake so?" Kallan manyan idanunta yayi yakasa bata amsa, Waheeda taga Sai Kallan ta yake tace "Babban Yaya kayi shiru kana kallona" Hannunta yasake riqewa cikin nasa hannayen yace "Aike qanwata ce, damuke uwa daya uba daya hakane ko?" Waheeda ta gyad'a masa kanta alamun hakane Yaci gaba da fadin "tunda ke qanwata ce, ke jini nace, idan kika kalli qwayar idona, zakiga yarinyar danake so" (tofa) Matsowa tayi kusa dashi haryana jin saukar nunfashin ta akan fuskar sa, tazuba masa ido tana so ta tabbatar da maganar sa, Sai can tadawo ta zauna yanda take da, tace "banga komai ba Babban Yaya banda baqi dayake cikin fari na idonka" πŸ˜‚ Murmushi yayi dimple dinsa suka futo, yace "naji, wannan maganar tazama sirri tsakanin mu, banaso kowa yaji, sannan baqin gawayi nakeso kisamomin acikin gida yanzu" 😳Zaro ido tayi tareda rufe bakinta da hannunta tace "nashiga uku Babban Yaya qona Nadiyar Zakayi idan kaje?" "banason shirme Dan Allah, amfani zanyi dashi, guda daya nakeso kisamomin" Tunani tafara saida tagama ta Kalle shi tace "Babban Yaya ai kasan Bama qona gawayi, Amma Naga Ummah tanada wani na leda Wanda take sakawa akan gas idan yayi zafi saita saka turaren wuta, saide inje in Dauko mashi, Amma idan kaji tana jaje karkace nice" Yace "nida kika kawo min tayaya zan fada? Yi sauri kije ki dauko" Cikin sauri tafice daga motar tashiga falon da gudu, taje Dakin Ummah Allah yaso tana toilet, tayi sauri ta dauko ledar gawayin guda daya, ta6oye acikin hijab,ta kawo tamiqa masa tace "gashi" Cikin mamaki tasake Kallan sa tace "Laaaa Babban Yaya yanaga ka sauya Kaya kasaka wannan tsumman? Cemata zakayi Kai mahaukaci ne?" πŸ˜‚πŸ˜‚ Kallan ta yayi yace "saide in kece mahaukaciya" ya dauki gawayin guda daya yarabashi abiyu, yafara shafawa a fuskar sa da hannun sa, ya dauki wani rawani ya nada a Kansa,yacire agogon hannun sa, yanda yayi baqi ba zakace shine ba, Waheeda tayi shiru tana Kallan ikon Allah, saida yagama 6oye kamar sa sannan yaja motar suka tafi, agaban islamiyar ya faka motar yaqi fita, saida ta Kalle shi tayi murmushi sannan tayi masa bye bye tafice daga motar Gidansu Nadiya ya nufa Kafin ya qarasa ya tsaya yafaka motarsa acan nesa da gidan, sannan yafuto yatare wani Dan adedeta yace "Aron Napep din nake nakeso" Dan adedeta ya kalli adedetan sa Sabo fil dashi, sannan ya kalli Babban Yaya yace "kamarya aro?, malam bansan kaba tayaya zan dauki sabon adedeta na nabaka?" Babban Yaya yace "kaga mota na Nan, ka tsaya anan kajirani yanzu zan dawo" Dariya Dan sahun yayi yace "hauka nake zan yarda dakai? Tayaya zaka mallaki wannan motar? In hakane meyasa zaka nemi Aron abun Hawa?" Kansa yadafe, ya nufi motar ya Dauko agogonsa yabashi yace "yanzu kaga shaida mota tace ai ko? Kariqe wannan agogon idan ban dawo ba kaje ka saida shi zai iya siya Maka sabon adedeta harda Yan canji" Dan adedeta yayi shiru yana nazari, badan ransa ya soba yafuto yabawa Babban Yaya, Nan da Nan Babban Yaya yahau yatuqa da bissmillah aikuwa adedeta yafara tafiya, baiyi gudu ba ahankali yake tafiya harya qarasa gidan, yana zuwa yahango wata budurwa tana tsaye dawani saurayi me mota, motar ya kalla ya kalli wayar hannun sa, wayar hannun sa kadai zata Iya siyan motar gayen, cikin sauri yakashe ta, yasaka acikin aljihu, sannan yafuto daga adedetan nasa ya tsaya yana Kallan su yana daddanna wayar baba Yusha'u megadi wadda taji wahala harda kyauro ajikinta Kallan sa budurwar tayi suka kwashe da dariya itada saurayin, Babban Yaya ya qarasa wajan su tareda Bawa saurayin hannu yace "Salamu Alaikum" Saurayin ya Kalle shi daga sama har qasa yaga wani fatattakekken takalmi aqafarsa, yaga fuskar Nan tayi wani irin baqi, ya girgiza Kai tareda dauke Kansa, budurwar ta Kalli saurayin suka hada ido suka sake kwashewa da dariya Babban Yaya yasosa girarsa guda daya da key din adedeta dayake hannun sa, abunda yariga ya zama dabi'arsa Ya kalli Budurwar Yace "Dan Allah Ina neman Nadiya ne" Tace "nice Nadiya, ya akayi?" Kai tsaye yace "Ina son magana dake" Yatsina fuska tayi tace masa "me?" Saurayin Nata yace "a a Beby, jeki kiji abinda yazo dashi, kika Sani ko neman sadaka yake?" Babban Yaya baice dashi komai ba yajuya yakoma jikin adedetan sa,Nadiya ta biyo bayansa tana mamaki gashi talaka futuk daga Gani Amma yanayin tafiyarsa kamar ta manyan masu kudi, suna zuwa jikin adedetan ya kalleta yace"Nadiya inason ki, idan bazaki damu ba inaso mu qulla alaqa dake, alaqa ta har abada,Amma ni banida kudi, talaka ne ni idan har kina sona tsakanin ki da Allah, ni banida matsala, bazan 6oye miki komai ba, gidanmu munada yawa kusan mu talatin ne, sannan Mahaifiyata batada lafiya, Paralyze take yi, aikinsan Paralyze ko? "πŸ˜³πŸ™†πŸ»β€β™€οΈπŸ˜? Nadiya ta jinjina masa Kai tana jin wannan labari nasa,inbanda rainin Hankali meyake nufi da mahaifiyarsa babu lafiya? Tsayuwa ta gyara tace"kana nufin nice zanyi jinyar mahaifiyar ka kenan idan ka kaini gidanka? Sannan acikin mutum talatin din zanyi rayuwa?" Babban Yaya yace "Allah yamiki Albarka, nasan tunda kinada Hankali Zaki kula da Mahaifiyata, sannan kinga wannan adedetan?" yafadi haka yana buga jikin adedetanπŸ˜‚ Nadiya ta daga masa Kai tace "Nagani" Yaci gaba da fadin "to sojan hayane, banawa bane, kudin nake Tarawa idan suka cika dubu Dari shida saina Bawa meshi, kinga shikkenan daga Nan yazama nawa" πŸ˜‚πŸ˜± Nadiya tasake jijjiga Kai tace "cigaba Ina jinka" Babban Yaya yace "idan kika amince Dani, ba zakiyi DANA SANI ba (My First Novel DANA SANI) tun lokacin Dana fara ganinki naji duk duniya babu wadda nakeso saike, insha Allah namiki alqawari idan kika amince Dani, ba zakiyi nadama ba, saboda zan hada miki lefe nagani nafada, Sai Wanda yagani, sannan Kuma.... " Kafin yaci gaba da magana Nadiya ta daga masa hannu βœ‹πŸ»tace" dakata malam, nayi ma kama da wadda zatayi jinyar mahaifiyar ka?,konayi ma kama da wadda zata auri Dan adedeta? Bari kaji, ni matar manya ce, akwai Wanda nakeso, Big Brother yana Nan zuwa, kar yazo yaganni dakai ya raina min Hankali, danhaka Sai anjima... " tajuya tayi gaba, Babban Yaya yafara kiranta yana fadin "Nadiya! Nadiya!!" Amma tayi banza dashi,Shima Dama Kiran Nata dayake qarfin Hali ne kawai, dama baya so tajuyo πŸ˜† Babu musu yashiga cikin adedetan yatafi, yana zuwa wajan Dan adedetan ya futo yabashi key dinsa yace "nagode gashi" Dan adedeta yace "Wai harka gama? Naga ko Minti talatin bakayi ba" Motar sa yabude yashiga yace "nagode" Cikin sauri Dan adedeta yace "toga agogon Naka" Babban Yaya yace "Kabarshi kawai" yarufe motarsa yatafi,saboda hadari ne yake San tasowa, Kuma yanaso yaje ya Dauko su Waheeda a islamiya *** ** *** Tafiya suke ahankali suna zancen su gwanin sha'awa, Maya tace "Waheeda ki dinga sauri mana, ko bakya ganin hadari" "ke barni inyi tafiya ta yanda nakeso, idan sauri nakema jikina ya dinga rawa kenan, nikuma banason wannan rawar" Maya ta kwashe da dariya tace "su Waheeda manyan yanmata, zan so Naga mijinki Waheeda" "Zaki Gani Maya, kijira munayin candy Sai aure nikam, banaso naci gaba da karatu, nafiso nayi aure na indinga kula da mijina, in shaga6ashi inyi masa abinda yakeso, kinga lokacin saina tafi makaranta, tun yanzu ma mata suna nemana, idan natafi University wakike tunanin zai nemeni? " Kai tsaye Maya tace"Maza, Amma Kuma kinsan de Babban Yaya baya so ki dinga kula samari ko? Tayaya Zaki samu mijin? Bayan munkusa gama makaranta?" " can ta matse muku keda Babban yayan, nikam daga Candy Sai aure insha Allah " Maya tace"gaskiya yarinyar Nan wuyanki ya'isa yanka, nikam yanzu Ina Bayan Babban Yaya, tunda yabani kudin makaranta bazan taba mantawa da alkhairinsa agareni ba, Dan haka dole indinga tuna miki dokarsa a kanki " Kafin Waheeda tace wani abu anfara yaiyafi, neman wajan 6uya suke Amma sun Rasa, abun Hawa suka fara tarewa Amma kowanne baya tsaya wa, ruwa yaqara karfi Nan da Nan mutane suka fara gudu musanman maza, ruwa yayiwa su Waheeda duka saboda babu mafaka, suna cikin wannan halin Babban Yaya yaqara so, yana zuwa yafuto daga cikin motar yanufesu, Waheeda taga ya sauya wannan kayan daya saka na dazu, murmushi tayi, cikin shagwa6a tace "Babban Yaya shine kaqi zuwa da wuri gashinan ruwa yamana duka nida Maya" Bece da'ita komai ba, kawai gaban motar yabude mata, tareda fadin "I'm sorry, shiga" Maya tana tsaye tana Kallan su, lalle Babban Yaya yana son Waheeda, wanne Yaya ne zai budewa qanwar sa mota saikace wata budurwar sa? Anya kuwa yayanta ne? Saida Waheeda tashiga sannan yarufe, itama Maya tayi sauri tabude gidan baya tashiga, zagayawa yayi yashiga motar, yajuyo yana fuskantar Waheeda, cikin sigar lallashi yace "Sorry" Bakinta ta turo gaba taqi magana, yasaka hannu yakamo kyakykyawar fuskarta yace "kinji" Murmushi tasaki, dimple dinta suka futo, tace "shikkenan, Kuma alqawarin dazu, bazan fadawa kowa ba" Murmushi yayi Shima yace "good girl" Maya tayi gyaran murya, Dan taga alamun sun manta tana motar πŸ˜‚ Tace "Babban Yaya Ina wuni" Firgigit ya dawo haiyacinsa, shaf ya manta tana cikin motar, a taqaice yace "Lafiya" Sannan yaja motar suka tafi, suna hanya Waheeda Sai zuba masa surutu take, Amma amsar dayake bata batada yawa, har suka qaraso gidansu Maya, suka ajiye ta sannan suka dauki hanyar gida, Bai wuce dasu gida ba saida yashiga tawani shago yasai mata waya qirar iPhone, ya ajiye agaban motar sannan yaja motar suka qarasa gida Yana tsaida motar a compound din gidan nasu, Waheeda tafara kokarin fita, tana kama handle din kofar taji taqi buduwa, tajuyo tace "Babban Yaya bude" Wayar daya siyo ya Dauko ya 'Dora mata akan cinyarta yace "Gashinan, nasan inda kinada waya Zaki kirani kicemin kun tashi, bazan Bari ruwa yamiki duka ba kamar yau" Waheeda tafara kokarin budewa, tana Ganin wayar tasaki wani ihun murna ta rungume shi, yana jin yanda tudun qirjinta yake mintsininsa cikin ransa yace "yasalammmm!" Daurewa kawai yayi, ahankali yazareta daga jikinsa yace "bansan yaushe zakiyi Hankali ba, kina ta6ani any how kamar wani muharraminki" Kwata kwata Waheeda batama kalli inda yakeba bare tayi nazari akan kalamansa, cikin murna tace "Toda menene inba Shiba? Babban Yaya, nagode, Allah yasa kadinga cin ball a koda yaushe, Allah yaqara girma" Saida ya hadiye wani irin yawu, sannan yace "Amin" yabude mata motar tafita dagudu tanaso ta nunawa yanbiyu itama tayi waya Da daddare suna kallo gaba dayansu, Waheeda tana saka number Yan gidan tana saving dinsu cikin sabuwar wayarta, yanbiyu suna nuna mata wasu abubuwan da bata Sani ba, su Sa'ad da Sa'eed tareda Babban Yaya Sai labarin qwallo suke, Babban Yaya anta6o masa inda yakeso, wato zancen qwallo, Sai hira suke sunata dariya kamar bashi ba, Ummah ta Kalle shi tace "Yayansu Yaya kukai kaida Nadiya ne?" Kallan ta yayi yace "Ummah naje tace bata sona" Gaba dayansu Yan falon suka Juyo suna Kallan sa, wacce yarinya ce zatace bata son yayansu? Ummah tace "kamarya?" Juyowa yayi yasake Kallan Ummah yace "Ummah ki tambayeta kiji, naje nace mata Ina sonta, kifada mata nine naje da adedeta saboda motata tasamu matsala a hanya, Kuma tace koda na aureta bazata iya kula dakeba Ummah,sannan tare naganta dawani Gaye suna zance, kinga kenan itama tanada Wanda takeso,to menene amfanin auren ta? Ummah duk wadda bazata iya kulawa da mahaifiyata ba, bazan iya auren taba " (Kai Babban Yaya irin wannan batu haka πŸ€£πŸ˜‚) Ummah tadauki wayarta takira wayar maman Nadiya, Bayan sun gaisa maman Nadiya tace " Hajiya Baqon namu Kuma baizo ba, muna ta jira angama shirya masa abin motsa baki Amma Nadiya tacemin baizo ba Kuma bai kira wayarta ba" Ummah tace" Yanzu nake tambayar sa yacemin yazo tace masa bata sonsa, Wai tace bazata iya kula daniba koda ya aure ta" Maman Nadiya yace "Anya hajiya itace kuwa? Amma Bari inkirata" Ummah tanaji maman Nadiya ta daga murya takira Nadiya, nadiya tana zuwa maman ta tace "Big Brother yazo kince masa bakya sonsa, kince kokin aure shi bazaki kula da umman saba, anyi haka ko ba'ayi ba?" Nadiya tanajin wannan bayani tatuna mutumin dayazo wajan ta dazu a adedeta, ta d'ora hannunta aka πŸ™†πŸ»β€β™€οΈtafashe da Kuka tace "wallahi mama bansan shibane, yaudara ta yayi, Allah Ina sonsa" cikin kuka tanufi dakinta da gudu Maman Nadiya ta sassauta murya tacewa Ummah "Hajiya komai fa ya lalace, zamuyi magana daga baya" daga Nan ta kashe wayar Babban Yaya ya kalli Ummah yace "Ummah kinji da kunnanki ai naje ko?" Cikin bacin rai Ummah tafara girgiza kafarta tace "naji Naufal, ai banyi tunanin yarinyar zatace bazata kula daniba, bansan haka tarbiyar ta takeba" Wani farin ciki ne ya mamaye shi, yaga Ummah ta yarda da komai, to tun kafin waccan Nadiyar tazo ta musu bayanin komai ta fada musu 6oye kamarsa yayi, Gara yagudu yabar qasarπŸ˜‚ Cikin ladabi yace "Ummah, muna shirye-shiryen fara World cup very soon, zan fara training Jibi, Insha Allah gobe da Asubar fari zan wuce" πŸ˜‚πŸ˜‚ Ummah tace "Allah yakaimu Son" Firar da ba'a qarasa dashi ba kenan, ya wuce dakinsa ransa fessπŸ‘ŒπŸ» Sonake agano min iyayen wadannan taurarin guda biyu NAUFAL DA WAHEEDA To Babban Yaya yatsira wannan lokacin, kome Waheeda zata aikata ya dawo dashi qasar? Amnah El Yaqoub ✍πŸ? 1/28/22, 20:49 - Ummi TandamaπŸ˜‡: BABBAN YAYA Writing By Amnah El Yaqoub Like my Page On Facebook https://www.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493/ 11&12 Suna tashi da safe sukahau shirin school,awajan break fast Waheeda taga babu Babban Yaya, anan taji cewa yatafi tun asuba kamar yanda yafada jiya da daddare Bataci wani abincin kirki ba, Sai tea me kauri, ta kalli 'yanbiyu taga Sai lokacin zasu fara cin abincin, tatashi tayi d'akinsu da gudu Kowa yabita da kallo Amma babu Wanda ya tanka mata, wayarta tad'auko ta kunna ta sannan takira Babban Yaya, a lokacin suna cikin jirgi har anfara sanarwa a kashe waya jirgi zai tashi, yayi mamakin ganin number ta tana kira, already yanada number tun jiya yayi saving d'inta a wayarsa Dauka yayi tareda cewa "Lafiya ko laifin kika sake yi?" Dariya tayi tace "Babban Yaya,Aina Dena laifi yanzu, nayi Hankali Nima" Yace "Allah yasa, kinga de wannan Karon munrabu lafiya dake, banaso wani abu yasake faruwa kisa in dawo qasar Nan kwana kusa, kinga yanda nasamu narabu da rigimar su Ummah akan yarinyar Nan Nadiya, to banaso kisake aikata wani abun dazaisa nadawo Nigeria ta dalilin ki " Bakinta ta turo gaba kamar yana Kallan ta, sannan cikin shagwa6a tace" Babban Yaya to ai wannan dinma ba nice da laifi ba, Basaida na nuna ma abinda akamin ba?" Runtse idonsa yayi, Waheeda zata kashe shi, yadade da mantawa Amma saida tasa ya hango cikakkun breast dinta a'idon zuciyar sa, cikin sauri yace"naji,naji, menene Kuma saikin tuna min?" πŸ˜‚ Tace "to Babban Yaya kayi hakuri, yaushe zaka dawo?" Kai tsaye yace "Babu rana, kuma nafada miki banaso kema kiyi sanadin zuwana Nigeria" "Angama Babban Yaya, Allah yakiyaye hanya" daga haka ta kashe wayar Tata, Takoma falo,Ummah ta kalleta tace "lafiya?" Tace "Da Babban Yaya nayi waya" Sa'eed yace "um kaji masu waya" Dariya tayi kawai, ta jira yanbiyu suka gama sannan suka fita compound driver ya daukesu suka tafi Bayan uncle ya fita daga ajin nasu,Maya ta kalli Waheeda tace "Waheeda waiya kuke da Babban Yaya ne?" Kallan Maya tayi tace "Kamarya ya muke? Mekike nufi?" Maya tace "Ina nufin Wai Ummah ce ta haifeku dukanku?" Kai tsaye tace "itace mana, me kikaga?" "babu abinda nagani Waheeda, kawai de Naga kinshaqu dashi fiyeda yanbiyu, sannan Shima yana sonki sosai, shine nace koba Ummah ce ta haifeku ba" Waheeda tayi mata wani banzan kallo tace "toba Ummah ce ta haifemu ba waye yakawo mu duniya Kenan? Nasan nashaqu dashi yanda bakya zato, saboda tun Ina qarama nasaba dashi, sannan dakika ce yanaso na wannan Kam Ina tantama, saboda idan yana sona ma, to wannan soyaiyar dayakemin bata hanashi yamin hukunci, idan nayi laifi zaneni yakeyi wallahi, kinbani mamaki Maya, ashe zarginmu kike " Maya tace" innalillahi.... Waheeda zargi Kuma? Meyasa zan zargeku Bayan yayanki ne uwa d'aya uba d'aya? Kawai de kun birgeni ne jiya danaga yanda yake baki kulawa, harfa mota yabude miki, shine nayi tunani idan ku masoya ne abun zaifi dadin Gani, yana miki soyaiya kina maida masa martani " Cikin masifa Waheeda tace" A'uzubillahi.... Maya kamar wata marar Hankali Zaki dinga dangantani da yayana?" Maya ta kamo hannunta tace" yi hakuri qawata, nabata miki rai, kiyi hakuri Dan Allah " Waheeda tayi banza ta qyaleta, har wani uncle din yashigo ajin yafita, bata sake kula Maya ba, Sai tsaki take saki ita kad'ai Bayan sun koma tana duba wayar ta taga missed call dayawa da wata number, cikin mamaki tace "to waye wannan ya kirani har 5 missed call da number daya?" Kiran number tayi, cikin zazzaqar muryarta tace "Naga kirane waye?" Cikin salon yaudara akace "kira Kuma? Da wannan number?, Kai may be mistek ne" Ba tace komai ba ta kashe wayarta Bayan kusan minti biyar wannan number tasake kiranta, harta d'aura towel tana shirin shiga wanka, tadawo ta d'auki wayar, "Amincin Allah ya tabbata agareki sarauniyar kyawawa" "Amin, Lafiya?" abinda tace masa kenan Yace "bekamata mace kamar ki, tayimin wannan tambayar ba kyakykyawa, ai kinsan ta tsuniyar gizo bata wuce ta qoqi, wallahi tunda kika amsa wayata dazu, naji hankalina ya kwanta dake, nasan aduk inda kike, ke mace ce Mai nutsuwa, me tarin Hankali da cikar haiba, uwa uba tare da kyau " Kalamansa sun ratsa Waheeda, da atsaye take, Amma yanda taji yana zubo Nata kalamai, saita nemi bakin gado ta zauna Yanbiyu suka shigo Dakin kowacce tana ajiye Jakarta, Ihsan tayi toilet da gudu saboda fitsarin daya matseta, inti Kuma ta kwanta agadon Waheeda tajuya idanuwanta tace "nagode, naji dadin yabonka agareni, kafadamin meyafaru?" Intisar tadago daga kwanciyar da tayi, ta kalli Waheeda, taji tawani sauya murya tana waya da alama da wanine Daga nasa bangaren yace "zan so kibani Dama indinga jin wannan zazzaqar muryar Taki koda sau daya ne a rana" Kai tsaye tace "inde Dama ce nabaka, menene acikin muryar tawa?" Yace "bakisan menene acikin muryarki ba? Muryarki tana d'aukeda wani sinadari, duk Wanda yajita, dole ne tatafi da Imaninsa" Dadi yakama Waheeda, ashe muryarta tanada dadi shiyasa Babban Yaya yahanasu kula Samari, ashe Dan karsu hadu da samari su dinga yabon baiwar murya me dadi irin tasu shiyasa yaqi dadi yahanasu kula samarin Cikin jin dadi tace "Nagode sosai, baka fadamin sunan ka ba" Yace "Af... Aina manta ban fada miki sunana ba, gaba daya nagama shagaltuwa dajin wannan daddad'ar muryar Taki ne, sunana Hassan, Ana kirana Sas, ni soja ne, iyayena da kowa da kowa nawa suna zaune a kaduna, iyayena suna damuna inyi aure, nikuma har yanzu ban hadu da wadda nake soba, tun Bayan rabuwa ta da budurwata ta farko " Waheeda tace" Allah sarki, Allah yabaka mace tagari, nikuma sunana Waheeda, Ina Garin kano, Ina zaune a unguwar, Amma inaso kabani labari menene yahada ka da budurwarka har kuka rabu? " Yace" Waheeda sunanki nada dadi kamar yanda muryarki Takeda dadi, zan baki labari anjima idan kin Bani damar sake kiranki Akaro na biyu, saboda alfarmar Dana nema shine indinga kiranki sau daya a rana " Waheeda tace"nabaka Dama ka kira" Cikin farin ciki yace "yanzu kin amince indinga kiranki sau biyu kenan a rana?" Kai tsaye batare da tunanin komai ba tace "Na'amince" Yace "nagode Yar'uwata, gaskiya kinada hali Mai kyau, please ki kula da kanki karki Bari ko quda yata6a ki" Cikin farin ciki tace "to shikkenan" sannan ta kashe wayar Ihsan da Intisar da tun dazu suke Kallan ta sukace "dawa kike waya Waheeda?" Harararsu tayi tace "miye naku? To da saurayi nake waya, soja ne, Kuma ni tundaga yanzu ya kwanta min araina, so kuke naqi kula samari kamar ku daga qarshe a hadani da wani a dangi? To banason auren had'i, danhaka samari na zan kula" Intisar tace "aikuwa wallahi baki isaba, bazakija Babban Yaya yazo ya qwace mana wayoyin muba, tunda yahanamu, kega me kunnan qashi ko?" Waheeda tace "kunnan qarfe Bana qashi ba,nide saina kula samari, ku Kuma dakuka tsaya Babban Yaya yamuku hud'uba, to saikuje kuyi tayi, bakusan halin Babban Yaya bane, kaiku zaiyi yabaro" Ihsan tace "Waheeda idan kika kuskura kika sake fadar wata magana dangane d Babban Yaya na rantse da Allah Sai munyi miki duka a Dakin Nan, qarqari kice Ummah zatazo cetonki, to wallahi kulle kofar zamuyi saimun nuna miki jiki, banza marar kunya" tafadi haka tareda kokarin cire uniform dinta. Waheeda tace "ku kasheni ku kaiwa uwata gawata, qarshe kenan" tafadi haka, tareda shigewa toilet domin watsa ruwa Sas soja bai sake Kiran Waheeda ba Sai dare, a lokacin harta matsu ya kirata, a zaune suke afalo yakira, tana dagawa tayi cikin dakinsu da gudu, kowa yabita da kallo gaba dayansu sunyi tunanin Babban Yaya ne ya kirata, yan biyu ne kawai suka San abinda take 6oyewa, kwanciya tayi akan gado,tana yi masa sallama, Bayan sun gaisa tace "Ina jinka, tun dazu nake jiran kiranka, Amma baka kiraba" "kiyi hakuri sarauniyar kyawawa, oganmu ne ya kirani, kinsan sojoji babu zama" Murmushi tayi tace "Ina jinka, kabani labarin abinda yarabaka da budurwarka" Yace "Mun dad'e tareda yarinyar,kinga nide soja ne, Amma bantaba yin kuka ba Sai akan yarinyar Nan, nayi kuka kamar zanyi hauka, Waheeda muna cikin soyaiya da yarinyar Nan har ankai kudin gaisuwa da komai, mamanta tace ai akwai Wanda ta yiwa alqawarin auren ta, waje daya suke aiki dashi, haka aka bamu hakuri, akwai gida na bakiga yanda na tsara Shiba, Sai hakura nayi dashi nabawa qanina shi, gashi nine Babba a gidanmu, kowa so yake nayi aure, yanzu haka lefen Dana hadawa yarinyar suna Nan, kawai wasu qananun abubuwan ne ba'a saka ba, yanzu gashi narabu da'ita komai ya zama tarihi, saide in nemi alfarma awani waje ko za'a Bani Dama " Waheeda ta Lumshe idonta tace" wacce irin alfarma kenan?" Yace" Alfarma mana, nasamu Dama nashiga cikin zuciyar ki, kibani key dinta na kulleta, ta yanda babu wani d'a namiji dazan iya bud'ewa bare yasamu damar shiga " Tace"to inde wannna ne, nabaka Dama, Allah ya tabbatar mana da alkhairi " Farinciki yakama Sas, yace"amma inaso namiki wata tambaya guda daya" Tace "Ina jinka" Yace "gashi bamu taba ganin junaba har mun qulla alaqa, meyasa kike sona?" Ajiyar zuciya tayi tace "gaskiya nayaba da Hankalinka, dakuma tarin nutsuwarka, wannan kawai shine" Murmushi yayi yace "zakici gaba da sona Waheeda idan kikai tozali Dani? Karnaje dadin baki kikemin, saboda nide baqi ne, banida d'iqon fari kod'aya ajikina, ni baqi ne" Waheeda tayi shiru tatafi tunani, tatuna wata hira dasuka ta6ayi dasu Neenah aboarding, sunce mata maza baqaqe sunfi lafiya ko a wajan aure, sunfi fararen mazaje bada himmaπŸ™Š Sas yace "kinyi shiru Waheeda" Cikin sauri tace "ai nafison irinsu, Allah yabarmu tare" Yace "Amin, yaushe zanzo naganki kiganni? Banaso ki ganni awaya kiji bakya sona Waheeda, Gara nazo ki ganni a zahiri, sannan inyi magana da babanku cewa Ina sonki, inaso na aureki idan kin kammala makaranta" Waheeda tasake yin qasa da murya tace "Allah yakawo ka lafiya" Yace "to shikkenan, ki kulamin da kanki, karki manta kiyi alwala sannan kiyi addu'ah kafin ki kwanta" Waheeda tayi hamdala cikin ranta, ta San cewa tabbas tayi dace da samun Miji na gari Duk abinda take 'yanbiyu suna ganin ta, basuce mata komai ba saboda idan sunyi mata magana ma rashin kunya zata musu, kawai de sunsa aransu duk lokacin da taja Babban Yaya yahanasu riqe waya Sai sunyi mata dukan mutuwa πŸ˜‚ Tsawon sati biyu Waheeda ta d'auka tana waya da soja, ba tareda kowa nagaidan yasani ba, daga ita Sai yanbiyu ne kawai suka sani, zuwa wannan lokacin Hankalin Babban Yaya ya kwanta, yanayin ball d'insa cikin nutsuwa bashida damuwar komai, tunda yaga yayi sati d'aya, yayi biyu, har uku, ba'a kirashi agida akan matsalar Waheeda ba yasan cewa taqara Hankali, idan yaga Kiran Ummah har d'auka yake cikin nishadi, yasan cewa kawai gaisawa zasuyi. Cikin sati na hud'un ne Sas yace mata zaizo yaganta ranar asabat, ranar kuwa tun safe takasa zaune takasa tsaye, yanbiyu tun kafin su tashi daga bacci tafara tashinsu, cikin ladabi tace "Inti yau Soja zaizo, mezan shirya masa?" Intisar tace "waida gaske zuwan zaiyi? Bakya tsorone Waheeda?" Bakinta ta turo gaba tace "Toni Ina sonsa, Dan Allah Kuna 'yan'uwana mata idan Baku Bani goyon baya nafita kunyar sa ba, wakuke so yabani?" Tausayin ta yakama Intisar, tajuya ta kalli Ihsan, Ihsan tace "kinga Inti babu ruwana, idan Babban Yaya yaji, mezamu ce masa?" Waheeda tace "Kai Ihsan Dan Allah, idan Ummah ta tambaye ku karkuce saurayina ne, kawai kuce mata Dan makarantar mu ne, ba shikkenan ba?" Nan take,Waheeda ta kalallame zuciyar 'yan'uwan Nata, suka d'auki shawarar data basu,Waheeda ta wuce kitchen tafara hadawa soja kayan makulashe Karfe hudu na yamma, soja yazo, d'an sahu ne yakawo shi har unguwar ya ajiyeshi, yakira wayar Waheeda yasanar da'ita yazo Rabonta da saka mayafi harta manta,saboda Babban Yaya yahanasu, Amma yau haka taci kwalliya cikin Riga da siket, kayan ya kar6i jikinta sosai, tayi kyau nesa ba kusa ba, fuska taci kwalliya, tadauki mayafi Dan qarami ta yafa, sannan tadauki kayan data had'a masa tafita dashi compound din gidan, Ummah tana daki ba tasan Wainar dasuke toyawa ba. Kamar yanda yafada dinne kuwa, domin kuwa Waheeda tana zuwa ta ganshi baqiqqirin dashi, gashi gajere, Amma duk da haka Saitayi murmushi ta qarasa wajan sa tace "qaraso gidan mana" Babu musu yabiyo Bayan ta Sai qarewa tsarin gidan nasu kallo yake yana jijjiga Kai, komai da komai na tsarin gidan yamasa kamar tsarin ginin turawa, daga Gani yarinyar 'Yan manyan mutane ce Gidan suka shiga, baba maigadi dayasan cewa basa saka mayafi Kuma basa kawo samari, Sai mamaki ya kamashi, Dan haka yanufi cikin gidan zai fadawa Ummah abinda yake faruwa yaji koda sanin ta haka zata tafaru Sas yana ganin shigar maigadi ya kalleta yace "ashe da gaske banyi qarya ba Dana saka miki suna sarauniyar kyawawa" Waheeda tayi murmushi ta rufe fuskarta da tafukan hannunta cikin kunya, sannan tace "tun dazu nake jiran zuwanka, ashe saukar yamma zakayi" Yace "eh wallahi,Ina hanya ma wayata ta dauke babu charge, yanzu ma kunna ta nayi na kiraki,kinga harta sake mutuwa, gashi ban kira mama na nace mata na'iso wajanki lafiya ba, kinsan me ma? Jiya fa dazan taho wajanki saida tace idan nazo na kula dake sosai, sannan tamin lissafin abubuwan da babu acikin kayan lefen Dana had'awa budurwa ta tada, Wai babu takalmi da jaka, yakamata aqara guda uku uku akan nada, da ansaka dozin d'aya, idan aka qara uku akai, kinga ya zama Sha biyar kenan, yakamata ace nakira ta nasanar da'ita nazo wajan Mai kyau,gashi wayar tawa tamutu,Bani Aron taki wayar nakirata" Waheeda tanajin wannan dogon bayanin nasa taji dad'i, gashi de bashida wani kyau na azo agani,Amma ita a haukan ta bataga laifin sa ba, babu tunanin komai ta bashi wannan sabuwar waya tata, tace"gashi kakirata to" Sas ya kar6i wayar yabata wata leda a hannun sa yace"ga kyautar Dana kawo miki, nayi niyyar kawo miki Riga irintamu ta sojoji, sainace idan zan sake dawowa saina kawo miki rigar, Amma yanzu ga wannan" Waheeda ta kar6a tace"nagode" Yace "Bari inkira mama" yamatsa jikin get din gidan zaiyi wayar, Hankalin Waheeda yanakan kyautar daya bata, taji de abu yana yawo aciki, Amma bata San menene ba, saboda anyi wrapping din abun da wata leda me kyau, tana d'ago kanta, taga wayam! Babu Sas babu dalilin sa πŸ™†πŸ»β€β™€οΈ? Gabanta ne yafad'i, cikin ranta tace"wannan mutumin fa ba saninsa nayi ba, kar naje yagudu da wayata, ba kowa ne ya fado mata araiba Sai Babban YayaπŸ˜‚ Ledar da Sas yabata ce tasulale tafadi daga hannunta, cikin sauri ta bude get din gidan tafita, mayafin data yafa yafad'i qasa Amma batabi ta Kansa ba, haka tafuto titi tana waige waige, Amma abu kamar wasa, babu soja babu dalilin sa, awajan ta tsugunna ta Dora hannunta aka πŸ™†πŸ»β€β™€οΈtace "nashiga uku na, namutu na lalace!, wallahi Babban Yaya saiya kasheni" πŸ˜‚ Baba megadi yazo da gudu shida Ummah, Ummah ta dakata daga bakin get din, baba megadi ya qarasa wajanta yariqo hannunta yana fadin "Waheeda lafiya? Me yayi miki? Ina baqon naki yake?" Waheeda bata Bawa baba me gadi amsa ba, saboda kuka dayaci qarfin ta, cikin kuka tace "innalillahi wa inna'ilaihirraji'un, shikkenan namutu, nakade har ganye na, Wallahi barin garin Nan zanyi tun kafin Babban Yaya ya dawo" Baba megadi haka yakamota suka shigo gidan, suna zuwa compound din gidan tazube awajen tana ihun kuka, yanbiyu suka qaraso da gudu suna tambayar ta menene, Ummah ta riqeta tace "kimin bayani mana, Wai menene?megadi yacemin kinyi baqo, Wanne irin baqo kika kawo gidan? Kuma me yayi miki?" Waheeda de takasa magana, Dan Gani take idan ta fad'awa Ummah to zata kira Babban Yaya ta fad'amasa Yanbiyu suka dauki Ledar da Waheeda ta yar, Ihsan tabude Ledar da'aka yi wrapping dinta, tana budewa saiga chesee ya bayyana, 'Yan hamsin hamsin guda biyu, hada baki sukai sukace "Laaaa Cizi ne" Kallan Waheeda sukayi, intisar tace "meya miki ne?" Cikin kuka tace "Yagudu da wayata, naduba ko'ina baya Nan, wallahi gidan Nan zan Bari" tana fadar haka ta kwasa da gudu tayi cikin gida Anan Ummah ta fahimci komai, Kai tsaye tabi Bayan Waheeda har d'akinsu, tana zuwa ta rufeta da duka, daqyar yanbiyu suka ceceta, Ummah taja kofar Dakin ta kulle Waheeda aciki, Dan tayi alqawari wannan Karon Waheeda tadena fita bare taja mata wata masifar Har dare Waheeda tana d'akinsu akulle, Ummah tahana kowa yabudeta, Daddy ne ya dawo daga wajan aiki Sai masifa yake, ta inda yake shiga batanan yake fita ba Duk sunyi shiru babu Wanda ya tanka masa, ita kanta Ummah ba tasan me zatace ba Kallan 'yanbiyu yayi yace "kuje ku budeta tazo Nan Ina nemanta" Inti taje ta bude Waheeda, akan gadon su taganta har lokacin kuka take, ta kifa kanta akan cinyoyin ta,dogon gashin kanta yazubo gadon Bayan ta, wani Kuma yarufe mata fuska kamar de mace me aljannu, kanta har ciwo yake saboda kuka, yanzu shikkenan wayarta tatafi, wayar ko wata daya Babban Yaya baiyi da siya mata itaba, ta Ina zata Iya Kallan idonsa tace takawo saurayi gida shikuma ya sace mata wayar? Intisar tace "kije Daddy yana kiranki" Ahankali tataso, suna zuwa falon kowa yabita da kallo, su Sa'ad jisuke kamar Su make ta, Daddy ya kalleta yace "Dan wanne gidane Yaron? A wacce unguwa yake?" Cikin kuka tace "Dadday bansan gidansu ba, ni bansan shi ba, yau nata6a ganinsa, Dan girman Allah Daddy karka fadawa Babban Yaya, Allah kasheni zaiyi" Cikin fishi Daddy yace "yau kika fara ganinsa har kika d'auki waya kika bashi saboda ga yayanku me kudin banza yasiya miki waya ko?" Ihsan tace "Daddy kayi hakuri, insha Allah bazata sake ba" Sa'eed yakalli Ummah yace "Ummah kikira Babban Yaya kifada masa Dan Allah, sonake ya dawo ya kakkarya yarinyar Nan, Danni idan nakamaki saina miki Dukan mutuwa, inyaso nakawo gawarki, tunda haka kike so Dama" Waheeda de tayi shiru, takasa cewa komai, Sai Jan zuciya take, fuskar Nan tayi jajir saboda kuka Ummah tace "bazan kirashi ba Sa'eed, kullum Waheeda cikin janyo mana masifa take, kullum ninake kiransa nafada masa, yanzu Kam, bazan kirashi ba, idan kullum zan dinga kiransa Ina fada masa matsala ai Kuma idan yaga kirana gabansa faduwa zai dinga yi,sannan Kuma bance kufada masa ba, kubarshi yayi aikinsa, Daddynku zai dauki mataki akan haka" Haka suka zauna a falon kowa yayi jugum, anrasa takamaimai Wanda zai kira Babban Yaya yafada masa abinda yake faruwa πŸ˜‚ Washe gari Waheeda bataje school ba, haka ta zauna tayi shiru adaki kamar marar lafiya, ko sunan Babban Yaya taji an ambata gabanta faduwa yake,yanda ta nutsu awaje daya, Sai gidan yayi shiru, idan ka kalli Waheeda saita baka sha'awa yanda tazama wata kamila, saide kowa taciki na ciki Tsawon kwana biyu kenan da 6atan wayar Waheeda, har yanzu babu Wanda ya fad'awa Babban Yaya, sannan daddy bai d'auki wani qwaqwaqwaran mataki ba, asalima fishi yake da'ita, Kuma a kwana biyun Nan Waheeda bataje makaranta ba, tana zaune agida abun duniya yataru yayi mata yawa, yau da yamma suna zaune, Anty Maryam tashigo gidan cikin tashi Hankali, tana zuwa ta nufi Ummah tace "Ummah yajikin Waheeda? Ashe batada lafiya Amma Ummah kukasa fadamin? Awanne asbitin aka kwantar da'ita?" Kafin Ummah tasake magana, Maya tayi sallama cikin falon nasu tana sharar hawaye, ta qarasa wajan Ummah tace "Ummah ashe Waheeda batada lafiya? Shiyasa Bata shiga makaranta kwana biyu? Na tambayi 'yanbiyu sunce min lafiyarta kalau ashe 6oyemin sukayi" Kan Ummah ya d'aure, ta kalli Maryam dinta dakuma Maya tace "Wai wacce Waheeda kuke magana a kaine?" Wayar Ummah ce tayi qara, ta d'auka tare fadin "sa'ad ya akayi?" Yace" Ummah, wannan gayen daya sace wayar Waheeda fa inaga Dan damfara ne, ba'iya wayar yakeso ba, harda damfara a tsarin nasa, yanzu Ina zaune yaturo min saqo Wai me wannan wayar batada lafiya, tana kwance agadon Asbiti, Ana buqatar tallafin kudi, Sai kuma account number aqasan saqon" Ummah tace "innalillah.... Sa'ad shiyasa na kulleta Adaki fa, saboda muna Zaman zamanmu wata Rana zatasa azo har gida a sacemu" Sa'eed ne yake Kiran wayar, Ummah tace "Sa'ad kashe, ga dan'uwanka Nan Shima yana kira" Tana daukar wayar Sa'eed din, Shima abinda yafada mata kenan, Ummah ta kashe wayar ta kalli su Maryam "wallahi lafiyar Waheeda kalau......" anan Ummah ta basu labarin abinda yake faruwa, Maya tace "Kai Amma wannan anyi tsinanne, yazo har gida yasace mata waya sannan ya dinga turawa mutane cewa batada lafiya aturo Masa kudi?, Ummah Ina Waheedan?" Ummah ta nunawa Maya d'akinsu Waheeda, tatashi ta nufi Dakin, anan taga Waheeda ta zauna tayi shiru tana tunani Maya ta dafata tace" Alhamdulillah, har hankali na ya kwanta wallahi qawata, text fa akamin bakida lafiya, kina gadon Asbiti a kwance, Wai Ana buqatar tallafin kudi ta wani account Number dayake Qasan saqon " Waheeda tayi shiru takasa Bawa Maya amsa, Maya tace" Waheeda kalau kike kuwa? Inata magana kinyi shiru? Yanzu Waheeda shawarar Dana baki ashe baki d'auka ba saida kika kula saurayi?" Waheeda tacire hannunta daga tagumin da tayi tace"Maya Babban Yaya"πŸ˜‚ *** ** *** Motsa jiki yake cikin nutsuwa da kwanciyar Hankali, wayarsa dake ajiye acan Gefe yaji tana ringing, kafin ya dauka harta katse, dakatawa yayi da abinda yake ya d'auki ruwa yasha, sannan ya d'auki wayar, number datake kiransa ma baisan taba, saikuma saqo guda daya, daga Waheeda, yayi mamakin ganin saqon ta, saboda yasan bata masa text message, Kiran ma ba sosai take neman saba, shiyasa saqon ya d'auki Hankalinsa, wajan zama ya nema, sannan ya bud'e saqon Nata, abinda yagani ne yasashi yatsina fuskar sa, kamarya yatura kudi ta wannan account din? Waheeda ce batada lafiya Amma akasa fada masa har wani account number ake turowa atura tallafin kudi tanan? Account number waye wannan din? "mashirmaciya" yafadi hakan a fili Sannan yayi Dialing number Tata, har ta kusa katsewa sannan aka d'auka, memakon yaji muryar Waheeda, Sai yaji muryar wani, lokaci d'aya yanayin fuskar sa ta sauya,wani irin baqin kishi yataso masa, cikin 6acin rai,yace "waye?" Daga d'ayan bangaren Sas soja yace "yayan me wayar ne, dama batada lafiya ne, tana kwance agadon Asbiti, muna neman tallafin kudi ne Wanda za'a mata aiki dashi, shine mukabi list din contact dinta muka tura musu" Sumar Kansa ya hargitsa, cikin ransa yace Waheeda zata kasheni, Amma a fili saiyace "za'a turo" daga Nan yakashe wayar Yana kashewa wani Kiran yasake shigo wa, number da'aka kirashi da'ita d'azu ne, ya d'auka tareda sallama, daga d'ayan bangaren akace "dawa muke magana?" Kai tsaye yace "Naufal Umar Arabo,a.k.a Big Brother" "Ok ikon Allah, ashe Big Brother ne, wato yalla6ai abinda yake faruwa shine, akwai wata yarinya da akai kidnapping dinta, kidnappers din sun nemi atura musu kudi, Kuma iyayen yarinyar sun tura musu kudin, daga qarshe Sai suka aikowa iyayen yarinyar da gawar 'yarsu, to Wanda aka turawa kud'in mun bibiyi Sim card din dayake amfani dashi mungano yana waya da iyayen yarinyar ne ta wata number waya, munyi bincike akan number, mungano number wata yarinya ce sunanta Waheeda Umar Arabo, kamar yanda mukagani a rigister Sim card din, saboda haka munyi tracking number Waheeda Umar Arabo mun dauki wasu daga numbers din dayake kira, aciki muka Gani harda taka number,yanzu haka ma kunyi waya, shine mukeso ka temaka mana, kafada mana inda yarinyar take, zamuje da'ita office dinmu, domin ta amsa mana wasu tambayoyi dangane da wannan Mai laifin ko Allah zaisa mu kamashi " Babban Yaya yayi shiruuuu yadafe goshinsa da hannunsa πŸ€¦πŸ»β€β™‚οΈ?,Yama Rasa abinda zaice, har sukaji yayi shiru sukace"yalla6ai lafiya dai ko?ko bakasan yarinyar ba?" Ajiyar zuciya yayi yace"nasanta, she's my Sister, kuyi hakuri kubani awa hudu, zanzo qasar, saina Baku ita" Godia sukayi masa dangane da had'in kan daya basu,sannan suka kashe wayar Yajima a zaune a wajan, Yama Rasa wazai nema domin qarin bayani? Menene yahad'a ta da wani har zata d'auki waya ta bashi? Tashi yayi yaje ya shirya, yayi mutuqar kyau cikin qananun Kaya, saida ya toshe kunnansa da Bluetooth sannan ya d'auki wayarsa ya futo daga gidan Karfe hudu na yamma ne yakawo shi gida, yana zuwa yakirasu, yafad'a musu yazo,su qara so sutafi da yarinyar, tun karfe uku yakamata ace yazo, but saida yagama da jama'arsa sannan yaqara so cikin gidan, kowa ganinsa yayi afalo kamar anjefo shi, gaba d'ayansu suna Nan 'Yan gidan, zama yayi akan kujera, cikin mamakin ganinsa Ummah tace "Son, lafiya naganka agida?" Kansa a qasa yace "aina Dena zuwa ko'ina Ummah, haqura zanyi da aikina, saboda idan natafi ma, Waheeda Virus zata dawo Dani"β˜ΉοΈπŸ™ŠπŸ˜‚ Ummah tayi shiru kamar andoka mata sanda, cikin ranta tace yaji komai kenan, su Ihsan ne suka tafi da gudu d'aki suka fad'awa Waheeda Babban Yaya yazo Gabantane yafadi, ahankali tatashi tad'auko hijab d'inta ta6oye shi abayanta, tare suka futo falo, Waheeda tafara bin bango zata gudu, a lokacin Yan sanda sukai sallama cikin falon Babban Yaya yad'ago Kansa ya Kalle su, idanunsa sunyi jajir saboda tsantsar 6acin rai, ba taredaya Kalle taba yace "ke Zonan" Hawayene suka fara sintiri akan kyakykyawar fuskar ta, agaban sa ta tsugunna tafara sheshshekar kuka,but takasa magana,kwata kwata taqi d'agowa ta kalli qwayar idonsa, cikin 6acin rai yace "ni Baban kine?" Cikin kuka ta girgiza masa Kai hawaye wani nabin wani Yace "to tunda ban haifeki ba, bazai iyu ki kasheni da raina ba" qafarsa takama tariqe, cikin kuka , tace "Babban Yaya, Allah natuba, bazan sake ba, Babban Yaya kayi hakuri karka sa sutafi Dani, wallahi Allah bazan sake ba" Kuka ne yakama 'yanbiyu, su kansu Waheeda tabasu tausayi, sukuwa 'yanbiyu maza Sa'ad da Sa'eed, wayarsu suka d'auka suke dannawa, Ummah ma tayi shiru tana Kallan su Gaba d'aya falon ya kaure da kukan Waheeda dakuma na 'yanbiyu, Babban Yaya ya kalli 'Yan sandan dasuke tsaye a bakin qofa yace "Yalla6ai gatanan kutafi da'ita" Volume din kukansu ne yaqaru, wata daga cikin police din mace, tazo takama hannun Waheeda tana janta, cikin kuka Waheeda take fadin "wayyo Allah na zasu tafi Dani, Babban Yaya! Babban Yaya!! Babban Yaya!!" Har suka jata, suka tafi da'ita, bata daina kiransa ba. Amnah 1/28/22, 20:50 - Ummi TandamaπŸ˜‡: BABBAN YAYA Writing By Amnah El Yaqoub Like my Page On Facebook https://www.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493/ 13&14 'Yanbiyu ne sukai d'akinsu da gudu suna kuka, Ihsan ta d'auki wayarta cikin kuka ta fad'awa Anty Maryam halin da ake ciki. Kwantar da Kansa yayi ajikin kujera ya Lumshe idonsa, yanda take qwala masa kira har yanzu muryarta takasa barin kunnansa, Ummah ta Kalle shi tace "kaje Kaci abinci kahuta" Ajiyar zuciya yayi, sannan ya bud'e idonsa yatashi yanufi qofa Ummah tace "Ina zakaje Kuma?" Cikin damuwa yace "Zanje ayi bincike akan Yaron ne" Sa'eed dake danne danne awaya yad'aga Kansa yace "Babban Yaya Dan Allah ka rabu da yarinyar Nan, kaje ka huta" Wani irin kallo yayiwa Sa'eed ba tareda yace komai ba yafice daga falon, Ummah tayi ajiyar zuciya tareda miqewa, tana mamakin irin wannan shaquwa ta Naufal da Waheeda, tasan bazai iya barinta acan ba,haqiqa yana kula da qannansa yanda ya kamata, Albarka tashiga saka masa acikin zuciyarta, tasan cewa tayi sa'ar samun sa acikin a matsayin Babba, koda babu ransu, zai iya riqe qannansa sa. Yana zuwa compound driver ya d'auke shi suka fita, saboda yagaji Kai tsaye mtn office suka nufa, yasa aka rufe layin Nata, sannan sukaje police station sukai report,sannan yayiwa d.p.o magana akan abinda yake faruwa,d.p.o ya basu wani 'Dan sanda suka nufi banki dashi, acan banki ma Kai tsaye yanemi ganin manajan bankin, yayi sa'ah kuwa yana Nan, saide yana shirin fita ne, kasancewar sa sananne Sai kowa yake Kallan sa acikin bankin, suna qarasa wa office din manaja, yafad'a masa abinda yakawo shi, manaja yanemi account din da gayen yake turawa, sukayi bincike akan account din, anan aka Gano asalin sunansa, da sunan iyayensa dakuma sauran bayanai, Babban Yaya yayi masa godia sannan yasa driver yakai shi inda aka Kai Waheeda, suna zuwa aka basu wajan zama, d'aya daga cikin ma'aikatan yace "yalla6ai yarinyar Nan fa tunda mukazo take kuka, daqyar da lallashi muka samu tabamu amsar abinda mukeso" Babban Yaya yace "Baku daketa bane, inda taji duka zata muku bayani ai" Murmushi yayi yace "ai hakan ma mungode sosai wallahi, ta fad'a mana itama damfarar ta yayi, yanzu zaku iya tafiya,mukuma zamuci gaba da bincike, idan wani abun yataso, insha Allah zamuyi Maka waya" Babban Yaya yabashi wata takarda yace "ga wannan, abinda na bincika ne Nima, nasan insha Allah Shima zai taimaka muku" Cikin farinciki yad'ago kansa yana Kallan Babban Yaya Bayan yagama ganin bayanan dasuke jikin takardar yace "taimako kuwa, sosai da sosai, godia muke yalla6ai" Kawai d'aga masa kai yayi batare da yace komai ba, Dan muguwar gajiya yakeji, bacci kawai yake buqata,gashi magrib har tayi Wata matace dake Sanye da uniform din kaki, tazo tareda Waheeda, ta rissina ta gaida Babban Yaya Sannan tajuya, Babban Yaya bai kalli inda Waheeda take ba yayi wucewar sa gaba, driver ya Mara masa baya 🀣 Gashi de shine Babban yayansu, Amma muddin tafiya ta had'ashi da'ita shine yake bude mata mota, tarasa dalili, Amma baya barinta tabude mota da kanta, yau kuwa yana zuwa yashiga baya ya zauna, yasa hannu yarufe motar, Waheeda ta tsaya tayi shiru tana ganin ikon Allah, wato in taga Dama ta6ude kofar ta da kanta kenan, yau ba mutunci, batayi gigin bude gefen dayake ba, tayi sauri ta zagaya daya gefen tabude tashiga, tana shiga wani Sanyi da qamshin turaren sa ya bugeta, tasa hannu tarufe motar, driver yaja suka tafi Lumshe idonsa yayi yana sauke wata irin ajiyar zuciya, lokaci d'aya wata irin nutsuwa take shigarsa wadda baisan dalilin taba, Waheeda ta Kalle shi da jajayen idanuwanta, cikin sanyin murya wadda take nuna tayi laushi, ta zubar da makaman yaqinta tace "Sorry Babban Yaya...." Yana jinta yayi shiru, hannunta dake rawa saboda tsoro ta 'Dora akan tsintsiyar hannun sa wadda take cike da gashi, cikin fishi yasa hannu yabige hannun ta yajuya mata baya yana Kallan window, lokaci d'aya ta rushe da wani irin Kuka Driver ya d'aga murya yace "kiyi hakuri Waheeda, ba gashi kin futo ba, gaki ga yayanku, ai kuka yaqare"πŸ˜ƒ Waheeda tayi shiru tana goge hawaye, Amma kamar ruwa tana gogewa wanine yake sake sakkowa, har cikin ransa kukan ta yana ta6a ransa, Amma dole ne ya nuna mata kuskuren ta Suna zuwa gida ma kafin a dedeta parking yafice daga motar yayi ciki,itama tafuto tana goge idonta tabi bayansa jiki a sanyaye, gaba d'ayansu family din na Arabo suna falon, daga kan iyayen har 'ya'yan, yana shiga qannansa suka fara yimasa sannu da zuwa daga mazan har matan, fuskar sa a d'aure yake amsa musu, yanemi waje ya zauna yana gaida su Hajiya Anty da Uncle Usman, saikuma Daddynsa, Waheeda tana shigo wa 'yanbiyu da Anty Maryam sukayi kanta suka rungume ta, cikin farin ciki suke fadin "Thank you Babban Yaya" Saida suka saketa, sannan ta kalli kowa na falon, bata nufi kowa ba Sai hajiya Anty, tana zuwa ta fad'a jikinta tasaki wani irin kuka, Hajiya Anty ta rungume ta aqirjinta, tanajin soyaiyar yarinyar har cikin ranta, kasa bata hakuri tayi, Sai Bayan ta datake bubbugawa, Ummah ta Kalle shi tace "sannunku, ai jinake acan zata kwana"πŸ˜… Daddy yace "Nima abinda naso kenan, tunda bata jin magana" Uncle Usman yayi murmushi baice komai ba, Ummah tajuya ta kalli Waheeda datake kuka a jikin Hajiya Anty tace "kitashi kije kisaka muku abinci keda yayanku" Har zuwa lokacin fuskar sa a daure take, cikin sauri yace "A a Ummah tabarshi kawai" Waheeda tanajin irin amsar daya bayar tasake riqe hajiya Anty tana fashewa da sabon kuka, Hajiya Anty tayi qasa da muryarta tace "sorry Baby na menene Kuma na kukan? Ba gashi kin dawo ba?" Cikin kuka tace "To ai Babban Yayan yaqi ya huce" Anty tayi murmushi tace "rabu dashi, anjima kije d'akinsa kibashi hakuri" 'Daga mata Kai tayi, sannan tatashi daga jikinta ta wuce d'akinsu domin watsa ruwa. Sai a lokacin 'Yan falon suke fara'ah, kana Gani kasan akwai had'in Kai dakuma jituwa a tsakanin su, anan sukaci gaba da zama Bayan mazan sun iyo sallah sun dawo,'yanbiyu ne suka had'a abinci, suka kawo falon aka baje anacin abinci, uncle Usman ya kalli Sa'ad yace "Kai jeka kiramin yayanku a d'akinsa" Sa'ad yaje yakira shi, yana Sanye da jallabiya fara qal, daga Gani kasan Sai mutum Ma'abocin tsafta ne zai saka ta, tsugunna wa yayi agaban iyayen nasa, uncle Usman yace "munyi waya da Yaya Habu, yanata tambayar ku, to tun kafin yafara korafi, yakamata ka shiryawa qannanka tafiya,suje suyi masa kwana biyu" Wani irin farinciki ne yakama Babban Yaya, yaji dadi da Uncle Usman yace ya shirya wa qannansa tafiya,hakan yana nufin banda shi kenan, dama damuwar Waheeda duk ta isheshi, Gara su tattara sutafi subar masa gidan dagashi da ummah πŸ˜‡ Kafin yabada amsa Daddy yace "Usman yakake cireshi daga ciki? Yashirya su tafi gaba d'aya kawai, Sai suyi sati d'aya,su huta saisu dawo" Uncle Usman yace "ba aiki yake ba Yaya? Yaje qauye ya zauna har sati d'aya?" Daddy yace "wanne irin aiki? Ai yayi retired, d'azu dayazo yace bazai sake komawa ba, saboda idan yakoma ma matsalar Waheeda zata dawo dashi, to idan ya zauna anan ma babu abinda zaiyi, Gara suje qauyen" Uncle Usman yayi Daria yace "a a, suyi kwana biyar de, idan sukaga dangi saisu dawo" Yana jin yanda suke tattaunawa yaji ransa ya6aci, baya son zuwa wajan baba Habu, saboda idan yaje ya dinga masa maganar aure kenan, shikuma ba auren yake soba, lallausar sumar Kansa ya shafa yace "zamuyi kwana biyu uncle, ya'isa, saboda aiki na" πŸ˜‚ Daddy yace "zaka koma aikin kenan" Babban Yaya duk ransa babu dadi a taqaice yace "eh" Ya tashi zai nufi d'akinsa, Ummah tace "bazakaci abincin ba? Kowa yana zaune shine zaka koma d'aki ka zauna kamar sabuwar amarya?" Yace "Ummah na qoshi" "kamarya ka qoshi? Ban fahimta ba? Kadawo daga wannan doguwar tafiyar kace bazakaci abinci ba? Yi hakuri Dawo ka zauna nabaka" Yanbiyu suka had'a ido sukai murmushi, Daddy yace "a a, Usman kaji fa, ni banta6a ganin uwar da bata 6oye son d'anta nafarko ba sai Hajiya, qarara take nunawa Yaron Nan soyaiya" Uncle Usman yayi murmushi yace "ya qwace wa Waheeda kujerar tane, ga auta,me za'ayi da tsohon tuzuru" Babban Yaya yayi murmushi yace "Ummah Nasha madara, saida safenku" Ummah Tajuya ta kalli hajiya Anty tace "kinga fishi yake, tun dazu nake masa maganar abinci yaqi ci" Hajiya Anty takalli Waheeda,tuni Waheeda ta d'auki haske, tatashi tafara zuba abincin tace "Bari nakai masa Ummah" Ummah tace "jeki Kai masa, idan yaqi ci kirabu dashi, shiyasan meyake damunsa Kuma" Waheeda tadauki abincin ta nufi d'akinsa dashi Gaba d'ayansu 'Yan falon Saida furucin Ummah ya basu dariya, Wai shiyasan meyake damunsa Anty Maryam ta shirya zata tafi, Sa'eed ya d'auketa shida Sa'ad, zasu rakata gidanta Waheeda na zuwa kofar d'akin nasa batama nemi izni ba tatura 'Dakin nasa tashiga, yana zaune agefen gadonsa abun duniya yataru yamasa yawa, ga zancen tafiyar su qauye gakuma 6acin ran Waheeda Yanayin data ganshi aciki ne yasa tayi sauri tayi qasa da idonta, daga shi zai gajeran wando da alama bacci zaiyi, inde yayi wannan shigar Dama tasan bacci zaiyi, agaban sa ya ajiye abincin kanta aqasa tace "gashi Wai inji Ummah" Tafad'i haka Sannan ta takure awaje d'aya kamar wata baquwa Yace "ki d'auka kimaida mata, ai nace Nasha madara" Muryarta ce tafara rawa tace "Dan Allah Kaci" "kindamu dacin abinci nane? Inda bakya son damuwata ai bazaki dinga batamin rai ba, idan aure kike so saiki futo fili kifadamin aure kike so Sai Amiki" Cikin sauri tace "Allah Bahaka bane, ni banason aure, Dan Allah kayi hakuri Kaci abincin" "nafada miki bazanci ba, Ummah ce ta aikoki kikawo min, Kuma nariga nafada mata banajin yunwa" Kanta aqasa tace "qarya fa nake, nice nakawo ma" "to saiki koma dashi, bazanci ba" Kukane yazo mata, ahankali hawaye ya silalo daga idanunta, cikin kuka tace "Babban Yaya Dan Allah kayi hakuri kadena fishi Dani, wallahi bazan sake ba, kakawo paper da biro muyi dakai arubuce bazan sake 6atama raiba" "ko gaban alqali mukaje bazaki daina halinki ba, kitashi kije kawai, rayuwa ce, ta'ishi kowa" Tanajin wannan furucin nasa tasake fashewa da Kuka, da sauri ta nufeshi tad'ora kanta akan cinyarsa tana bashi hakuri cikin kuka 😳😳Zaro idonsa yayi, cikin sauri yahad'e qafafunsa waje d'aya, sannan ya janye kanta daga wajan,gudun karta sake aikata abinda tayi yanzun, ta6aro masa aiki, yasa cikin sauri yace "naji... Naji, Nina haqura, shikkenan komai ya wuce, Bani abincin" Cikin sauri ta bashi abincin, sannan tace "kona baka Babban Yaya?" Yace "a a, tashi kije, zanci da kaina" Tashi tayi tsaye sannan tace "thank you" tafuto daga Dakin, shikuma yasaki wata nannauyar ajiyar zuciya Bata dad'e da futowa daga falon ba su hajiya Anty suka tafi, suna fita Maya tazo gidan, Bayan sun gaisa dasu Ummah, Waheeda tajata sukayi cikin d'aki, zama sukai akan gado Maya ta qarewa Waheeda kallo, tace "lalle Waheeda kinga rayuwa, 'yanbiyu suka cemin 'Yan sanda sun tafi dake bakiji yanda gabana yafadi ba" Waheeda tayi ajiyar zuciya tace "Maya ai rayuwa Kam Ina kan ganinta, Babban Yaya nefa yace sutafi Dani" πŸ₯Ί "ai Dama saida nace Miki ki dinga jin maganar sa" cewar Maya Waheeda tace "to Maya mutum saiya zauna babu saurayi? Candy fa muke shirin yi, idan ya hanani kula samari shine zai aure ni?" Maya tace "kika Sani" Cikin masifa ta hayaiyaqowa Maya tace "kamarya nasani,? Me kike nufi? Koji kike agarin maguzawa muke?" Maya ta dafata tace "maida wuqar qawata, ke kinsan da hakan meyasa zakice min idan bakiyi samari ba shizai aure ki?" Tashi tayi tsaye ta nuna wa Maya qofa da hannunta, tace "tashi kifice daga 'Dakin Nan kafin namiki rashin mutuncin Dana saba Maya, nasan irin Zaman da zanyi dake wallahi" 'Yanbiyu ne suka shigo 'Dakin suka tarar da drama, Ihsan tace "kema de Maya da naci kike, Ana wulaqantaki kina liqewa, ai shikkenan" Tana fad'ar haka tatada kabbarar sallah duk da ba tasan menene dalilin fad'an nasu ba Intisar tace "Maya muje na rakaki hanya, mungode, Dakin Sani ma bakizo ba, Dan waheeda ba'a mata gwaninta, gobe ma qauye zamu tafi muyi kwana biyu" Maya ta kalli Waheeda tayi murmushi tace "a dawo lafiya qawata" daga Nan suka futo daga 'Dakin, Waheeda kuwa ko uffan ba tace musu ba, tayaya ma Maya zata dinga had'ata da Babban Yaya? Yayanta uwa d'aya uba d'aya saikace wasu kafirai ba musulmai ba? Tsaki tasaki Bayan fitarsu tashige toilet domin d'auro alwala Washe gari haka suka had'a kayansu, kowa ya shirya Amma banda Babban Yaya, yana d'akinsa yaqi futowa, kwata kwata baya son zuwa, Amma babu yanda ya'iya, haka yafuto suka had'u afalo, sukayi wa Ummah sallama Suna zuwa compound yaja ya tsaya, jiyake kamar yafashe da Kuka, Sa'ad ya Kalle shi yace "Babban Yaya ya za'ayi ne?, Naga kamar mota d'aya tayi mana kadan" Waheeda tayi zuruf tace "eh wallahi, aqaro mana wata, kowa yabaje son ransa" πŸ˜ƒ Babban Yaya ya kalleta, sannan ya kalli Sa'ad yace "bawata mota daza'a qara, mushiga Prado din can kawai muje, babu driver acikin mu ai bare muyi kayan motoci" Waheeda tayi qasa da kanta, cikin ranta tace wannan Dani yake, sukuwa yanbiyu dariya suka saka, ta Kalle su ta share su Sa'ad ne zaiyi driving, Babban Yaya yana gefansa, Bayan motar Kuma Sa'eed da Yanbiyu da Waheeda suka shiga, kasancewar glass din motar baqi ne Sai sukai tafiyar su cikin salama babu Wanda yake ganin Babban Yaya bare masoyansa su tsayar dasu Tafiya tayi tafiya yanmatan duk sunyi shiru kowa yana danna wayarsa banda Waheeda, ☹️ Saisu Babban Yaya dasuke fira shida yanbiyu maza, Waheeda taga kowa harkar sa yake ba'a Tata, ta kalli Babban Yaya tace "BΓ bban Yaya yunwa nakeji" Sa'eed yace "Ina abincin dakuka Dauko?" Waheeda tace "wanne abinci? Ai bamu Dauko komai ba" Babban Yaya yajuya ya Kalle su gaba daya yace "waiku wanne irin mashirmata ne? Ku baku iya komai na mata ba komai Sai ance kuyi? Babu irin shirin Nan da mata suke yi kamar su snaks? Saide kici babu kuwa" ya qarasa maganar yana hararar Waheeda Cikin sauri tayi qasa da kanta, saida suka yi gaba sannan yaga wani yaro yana saida qwai, suka dakata yasauke glass din qasa kadan ya cewa Yaron "basu su juye subaka bucket din" Waheeda ta leqo kanta tace "BΓ bban Yaya nikam guda uku ma ya isheni, bazan iyacin sama da uku ba" Cikin mamaki ya kalleta yace "Toda nawa zakici ya isheki inba ukun ba?" Bakinta ta turo gaba tayi shiru, kowa saida ya Debi qwan yanda yakeso, sannan yabawa Yaron kudin da yafi karfin qwan gaba daya harna bucket din, sukaci gaba da tafiya, Waheeda ta 6are guda daya tad'an tashi kadan daga wajan zamanta, tamiqawa Babban Yaya saitin bakinsa tace "Babban Yaya haaa" Dafe Kansa yayi da hannunsa yayi shiru πŸ€¦πŸ»β€β™‚οΈ? Cikin fada Sa'eed yace "ke Dalla malama kimana shiru, haba, duk kin damemu, yarasa qwan dazaici saina bakin titi saikace ke?" Babban Yaya yayi murmushi, yasaka hannun sa ya riqe hannun Waheeda data miqo masa qwan, sannan ya karyi Dan kadan, yasaki hannun Nata, Waheeda Takoma wajan zamanta ta zauna, tanacin sauran Wanda Babban Yaya ya karya, har suka kusa Garin, bata sake magana ba, daga qarshe ma bacci ne ya dauketa, saida suka qarasa Garin sannan suka tasheta Sosai Baba Habu da yayansa sukai murna da zuwansu, Sai Nan Nan ake dasu, matarsa mama Haajara ta shimfida musu tabarma a tsakar gida kowa ya zauna, Ana sake sabuwar gaisuwa Shayinsu na buzaye tatashi tadora musu,suna fira tana ajiyewa kowa agabansa,ta miqe tace "Bari adora muku abinci, ga miya Nan nagama ta tun safe, Waheeda tatashi tacire hijabin jikinta tace"zauna mama, zan Dora" Tafadi haka tana nufar inda aka ajiye tukwanen gidan, Babban Yaya ya daga Kai ya kalleta, cikin ransa yace kamar me Hankali Baba Habu ya dauki wayarsa yafara magana "gasu sun qara so mekuke jirane Baku zoba?" Daga daya bangaren akayi magana, saiya sake cewa "wanne irin zabbi? Ga kaji Nan tun jiya Haajara take aikin su, zasuci, kutaho kuga yan'uwanku, banason rashin zumunci ni" 🀣 Kallan mama Haajara yayi yace "su Yahya ne, Suda yakamata ace suna gidan Nan dasu zamu karbi baqi Amma ke kiji Wai sun tafi neman zabbi zasu kawo asoya musu" Murmushi sukayi dukansu, yajuya ya kalli mazan yace "to ku aiba zama zakuyi ba, tashi zakuyi mutafi ku gaisa da yan'unguwa, daga Nan muje na nuna muku gonakin mu, nida iyayenku" Babban Yaya ya sunkuyar da Kansa baice komai ba, Dan tsoro yake yasan halin tijarar baba Habu karya jaji6o masa wata yarinyar awannan qauyen Sa'eed yace "Baba yanzu fa kagama cewa baqi,inamu Ina Gona? tokuje dasu Babban Yaya ni zan d'anyi wani abu" Baba Habu yace "kaji wani sakarci, tokai kana namiji Ina kaga ta zama? Sa'adun ne ko Sa'eedu? Namiji baya zama, kutashi muje" Sa'ad yayi dariya yace "Sa'eed ne baba, ka ganeshi dakyau" Haka suka fita badan ransu yasoba, mama Haajara ta kalli tukunyar da Waheeda ta 'Dora, tace "Waheeda wannan tukunyar a6ule take" Waheeda hankalin ta yana kan girki batajiba Ihsan tace "Waheeda tukunyar da kika Dora a6ule take fa" Juyowa tayi ta Kalle su, dama aciki take dasu, suna ganin ta tana aiki Amma babu Wanda ya taso acikinsu,sun Barta tana Fama da hayaqi, dankwalinta ta turo gaba, tulun dogon gashinta yafuto ta qeyarta, tace "kibarta taita zuba, Ina wuta tana ruwa, Sai muga wa Allah zai Bawa sa'ah" Mama Haajara tayi dariya tace "a a Waheeda, ba za'ayi hakaba" tatashi ta nufi wajan girkin, suma yanbiyu suka taso, saita basu salat da tumatir su yanka Majalissa Majalissa Baba Habu yake yawo dasu Babban Yaya yana nunawa abokai da yan'uwan Arziqi su, kan kace me, matasa sun taru a wajan Babban Yaya, wasu suyi photo wasu Kuma videos, wasu Kuma kawai binsa suke sunata zance, ayawon zaga Garin dasuke suka hadu dasu Yahya, sune suka janye Babban Yaya kasancewar su sa'anni,sannan suka nufi gonar dashi, daga baya baba Habu ya qaraso tareda su Sa'ad, gonakin yafara nuna musu yace "wannan Babbar gonar ta Usman ce, gata Umaru can agaba, duk ni nake kula musu dashi, dazaku iya da munje wasu gonakin daku duk kun Gani" Babban Yaya yace "Baba gobe Sai muje ai, Sai muga gari ma" Baba Habu yayi fara'ah yace "eto Kuma kaima kace wani abu, yanzu to riqe wannan fartanyar, gyara min Nan wajan kacire ciyawar nan data futo" πŸ˜‚ Sa'ad yace "baba muda mukazo ganin gona Kuma saimu fara aiki?"πŸ€” "aiku ba mazaje bane, kubar namiji yayi aiki" Babban Yaya yarasa abinda yake masa dadi, haka ya karba yafara cire ciyawar dasuka futo, abokan baba Habu ne sukazo wuce wa ya daga murya yace "malam idi, ku qaraso ku gaisa da yarana Yan birni" Su malam idi suna zuwa sukace "masha Allah, Wai duka Nan yaran Usman da Umaru ne?" Baba Habu yace "a a, duka yaran Umaru ne, shi Usman ai babu yaro awajansa" Ya nuna musu Babban Yaya da Kansa yake sunkuye yana Fama da fartanya, yace "ga Babban yayansu Nan nasashi aiki, kuduba kuga qwanjinsa fa, inda zai haqura da wannan tamolar ya dawo Nan mudinga noma Aida yaji dadi, dashi kadai zanbarwa wannan gonar ya nome min ita, haba meza'ai da wata tamola" ☹️ya qarasa maganar yana yatsina fuska Shide Babban Yaya baice komai ba, Sai abokan baba Habu dinne dasuke dariya dakuma su Sa'ad Baba Habu yasake Kallan sa yace "kunji yayi shiru kamar salihi, Nan kuwa qungurmin tuzuru ne" Babban Yaya baice komai ba yanzun ma, Shide fatansa yarabu da wannan tsohon lafiya, abokan nasa ne sukace "ai yanada Hankali, yanzu awannan zamanin ba kowanne Yaya ne zai debo qannan sa yakawo su ganin dangi ba"πŸ˜‚ Baba Habu yace "Eto tanan Kuma yayi qoqari" Ya kalli Babban Yaya yace "dago haka, muje gida muci abinci kun debo hanya" Sai a lokacin Babban Yaya yadago, fuskar Nan tasa a daure, babu wasa, haka suka tafi gida, yanbiyu da Waheeda suka zubawa kowa abinci, duk da yaran baba Habu suna zaune aqauye ne hakan baya Hana ganin tsantsar kamar dasuke dasu Babban Yaya, kana ganinsu kaga jini daya. Baba Habu ya kalli Babban Yaya yace "Ai kamata yayi daga Nan kunufi gida can Niger, can ma kuje kuga yan'uwa" Sani yayan Yahya yace "qwarai Kam baba, kaga Yan biyu da Waheeda ma Sai suhau a male, nasan basu taba Hawa ba" Babban Yaya yace "saide wani lokacin baba, saboda makarantar su, idan aka musu hutu, Sai muje" Uzurin daya basu ne yasa suka amince da maganar tasa, Amma badan makaranta ba, yasan Sai sunje. Washe gari suka fita ganin gari da safe, Waheeda wani Riga da wando tasaka, kayan sun kamata sosai, amma data saka dogon hijabi babu Wanda yake ganin ta, sunga gari sosai, sune har Rafi ganin ruwa, su Sa'ad suna tareda su Yahya, shikuma Babban Yaya yana bayansu Waheeda yana tafiya yana danna wayarsa. Fakar Idonsa Waheeda tayi, tacire hijabin Nata,hips dinta yacika wandon taf, sannan ta tattare qafar wandon, tashiga ruwan tafara wasa, suma yanbiyu da sukaga Babban Yaya hankalinsa yana kan waya suma suka shiga, dago Kansa yayi ya gansu suna wasa, bece musu komai ba yanemi waje ya zauna yaci gaba da abunda yake Cikin tashin Hankali yanbiyu suka fara Kiran sunansa, suna nuna masa Waheeda, yana dago Kansa ya hango Waheeda acan tsakiyar ruwa tana mututuwa idonta Sai juyawa suke ruwa yana gaba da'ita, baisan lokacin da yayi jifa da wayar ba, ya qwala mata kira, sannan yanufe ta da gudu Yanbiyu suka futo da gudu sukayi wajan su Yahya da Sa'eed zasu fada musu Batare da tunanin komai ba, Babban Yaya yafad'a cikin ruwan, kafin ma ya qarasa wajan ta hartasha ruwa ta suma, d'aukota yayi tamkar ya dauki jaririya Cikin tashin Hankali yafara tatta6a jikinta yaji shiru, jikinsa ne yad'auki rawa, fuskarta yakama yariqe yana fadin "ke! ke!! Dan Allah karki tafi" Jijjigata yake yana fadin haka Amma Waheeda shiru ko motsi takasa, gaba d'aya yanemi nutsuwar sa Yarasa, gabansa yafara fad'uwa kana Kallan faffad'an qirjinsa zaka tabbatar da haka, ta hanyar bugun zuciyar sa, shiru yayi yarasa abin yi, tunani yayi Ana danna cikin Wanda yasha ruwa, yasaka hannunsa akan shafaffan cikinta ya danna Amma ruwa be futo ta bakinta ba, zuciyarsa ce take bashi wata shawara yana yakicewa, daga qarshe Sai ra'ayin zuciyar tasa yabi, saida ya qarewa lallausan pink lips d'inta kallo, sannan ahankali ya sunkuya yahad'e bakinsu waje d'ayaπŸ™†πŸ»β€β™€οΈ? Duk yanda zuciyarsa take gargad'insa akan kar yayi komai Bayan iska dazai hura cikin bakin Nata, hakan bai samu ba, laushi da Kuma santsi irin na lips din Waheeda ya d'ebeshi yafara kissing dinta,wannan ne Karon farko daya ta6a kissing din mace a rayuwar sa,wani irin dad'i yaji sosai,saida ya tsotsi lips dinta son ransa, sannan yahura mata iska cikin bakinta da qarfi, sannan ya d'auke lips d'insa daga kan Nata. wani irin Tari ne yataso mata, a Hankali tafara bud'e idonta, harta bud'esu gaba d'aya, ta d'orasu akan Babban Yaya daya zuba mata ido yana Kallan ta, babu Wanda ya tankawa d'an'uwansa acikinsu, Sai ido dasuka zubawa juna, kowa yana tunani cikin Ransa, tsantsar kyawun dan'uwan Nata take kallo, haqiqa yahad'u harya gaji da had'uwa, shi abin sone ta kowanne fanni,ita kanta tana sarawa yayan nasu wajan iya Gayu dakuma d'aukar wanka. idanunta Babban Yaya yake kalla a zahiri, Amma abad'ini yayi Nisa cikin tunani, inama zata soshi kamar yanda yake sonta?koda yaushe zuciyarsa tana fad'a masa cewa, bashida mata Sama da'ita, ita din tasa ce shi kad'ai, but tayaya hakan zai kasance? To Alhamdulillah free page yazo qarshe πŸ₯± Gashi zan Dena yimuku posting Baku fadamin suwaye iyayen Naufal da Waheeda baπŸ˜‚πŸ˜‚ Dama nafada muku BABBAN YAYA na kudi neko? Ina Wadanda suke buqatar jin qarshan labarin? Kwamacala tana gaba aradu, yanzu aka fara wasan πŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒ Da abaka labari gwara ka bayar πŸ‘‡πŸ» 200 posting daya a rana VIP 400 posting biyu a rana 0164549488 Amina muhammad GTbank Zaku turo shedar biya ta wannan numberπŸ‘‡πŸ» 08033300034 Ga masu kira, text message, whtsapp, duk ku nemeni ta wannan numberπŸ‘‰πŸ» 08033300034 Next Novel SHAHAB..... Salonsa daban yake, zaizo muku bada dadewa ba πŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒ Amnah El Yaqoub ✍πŸ? 1/28/22, 20:50 - Ummi TandamaπŸ˜‡: Jikinsa ne yayi Sanyi Bayan tunawa da irin qalubalen dayake gabansa akan hakan, ahankali yakawar da fuskar sa Gefe, sannan ya tashi zaune yakama hannunta yariqe yana kokarin tashinta, jitayi kamar bashida qarfi, taga jikinsa yayi Sanyi, shi kuwa Babban Yaya yanayin daya shiga ciki ne bai gama sakinsa ba, ashe haka akeji? Kokuma de shine yaji dadin sosai saboda wadda yake soce yayiwa kiss din? Tashi tayi zaune, har zuwa lokacin hannunta cikin nasa, tana 'Dan qaramin Tari kad'an, a taqaice yace "Sannu" 'Daga masa Kai tayi tace "Babban Yaya da yanzu na mutu, nide mubar Garin Nan, tsoro nakeji" Fuskarta yariqe yana Kallan qwayar idonta yace "kidena cewa Zaki mutu, banaso" Murmushi tayi masa, kafin tace wani abu su Yahya suka qaraso,'yanbiyu suka jata zuwa gida,tafiya suke a hanya gaba d'ayansu suna jajantawa juna akan abinda yafaru Da daddare kasa bacci yayi, haka ya dinga juyi akan gado hannun sa yana kan mararsa datake masa wani irin mugun ciwo, yana tuno laushin lips din Waheeda saiyaji kamar yaje yaqaraπŸ˜³πŸ™†πŸ»β€β™€οΈ?, Sai gab da asuba yasamu bacci ya d'auke shi Bayan ya kwanta rub da ciki, saida ya makara sallar asuba, baida tsarki, saida yayi wanka sannan yayi sallah sakamakon wani irin mafarki da yayi na Waheeda me dadi. Sai wajan shad'aya 'yanbiyu suka kawo masa abinci, yanaci kuwa yafuto tsakar gida d'aukeda kayansu, koda ace Waheeda batace tanajin tsoron Garin ba, ya zama dole sutafi, bazai juri rashinta atare dashi ba, idan ta mutu a wannan qauyen shi waya kama kenan? πŸ˜‚πŸ€” Baba Habu yace "a a, ya naganka da Kaya? Ina zakaje" Kasa yayi da Kansa yace "baba anmin waya ne a wajan aiki, Ana nemana, shiyasa zamu tafi" "to Amma tafiya babu shiri Naufal? Meyasa bazaku Bari Sai goben ba?" Murmushi yayi yace "baba zamu sake dawowa" Haka yahad'a kan qannansa kowa yahad'a kayansa, suna saka kayansu cikin booth din motar wasu samari suka qaraso wajan Babban Yaya suka bashi wata latter, dubawa yayi sannan yayi murmushi, ya Kalle su yace "inde kayan Ball ne, zan turo muku dashi, harda takalma" Ihu suka Hau yi kowa yana qara yimasa godia, inna Haajara tacika su da kayaiyakin qauye su manshanu da Kuka, dakuma kindirmo, haka suka tafi cikeda kewar 'yan'uwan su su Yahya. Washe Garin ranar dasuka dawo daga qauye, Daddy da Ummah da Uncle Usman suna zaune afalo suna kallo, Sa'ad da Sa'eed suka shigo falon kansu aqasa, agaban Ummah suka zauna, uncle Usman yace "to 'yanbiyu mekuke sone Naga Kuna sunkuyar da kanku?" Sa'eed ya Sosa qeyarsa yace "Uncle Dama... Dama uncle..." saikuma yayi shiru yana zungurin Sa'ad Daddy yayi dariya yace "tunda kaga haka ai zancen bazai wuce na neman kudi ba zasu sauya mota, aikinsu kenan, kuje wajan yayanku yabaku, shine me kudi" Murmushi sukayi, Sa'eed yace "Daddy Bahaka bane, dama gidansu Hassana ne akace muturo akai kudin gaisuwa" Uncle Usman ya gyara zama yace "a a, babbar magana, kuce abun yazo" πŸ˜ƒ Sake sunkuyar da kansu sukai cikin kunya Daddy yayi murmushi yace "Kundage de Kuma yanbiyu zaku aura kamar ku,kuje ku kiramin yayanku, ai dashi yakamata kufara magana, shikuma saiya fad'a mana" Tashi sukai suka nufi wani daki kusa da 'Dakin Babban Yaya, babu komai acikin 'Dakin Sai kayan Ball, dagashi Sai qananun Kaya da ball, yana bugawa shi kadai, zama sukai suna Kallan sa, daina abinda yake yayi, ya dawo kusa dasu ya zauna yace "twins ya akayi ne?" Sa'eed yace "Babban Yaya mun dade bamuyi Ball bafa" Kallan sa yayi yace "shine matsalar?" Sa'ad yace "Babban Yaya wallahi ba'ita bace, gidansu Hassana da Hussaina sunyi magana, mu turo akai gaisuwa, Dan Allah Babban Yaya kacewa su Daddy a saka harda ranar ma gaba daya" Babban Yaya ya saki murmushi yace "um Um... Ashe aure kukeso shine kuka qi magana?" Dariya sukayi dukansu, yace "to shikkenan, idan nagama zanyi magana dasu Daddy" Godia sukayi masa sannan suka fice daga Dakin, yana ganin fitarsu yazube a wajan, yafada duniyar tunani, Sai yaushe ne matsalar sa zatazo qarshe ne? πŸ€” Ko awa d'aya bai qaraba yanufi wajan su daddy Bayan yayi wanka yagama shirya wa, Kansa yana qasa, Bayan yagama yimusu bayanin abinda yakawo shi, uncle Usman yace "yanzu Kai haka kaza6awa rayuwar ka? Maryam qanwar 'yanbiyu tayi aure, abar wannan maganar ma, ita mace ce, toga 'yanbiyun suma sunyi magana, Naufal, yakamata ace ka nemawa kanka mafita, zamanka haka bazai iyu ba, musuka fara fad'awa maganar, muka turo su wajanka, munyi tunanin hakan zaisa kaima ka kawo taka Sai ahad'a ayi gaba d'aya, ashe har yanzu kana Nan kakasa tsaida magana d'aya, maganar gaskiya bazai iyu su Sa'eed su Riga ka aure ba, muna so Kai kafara saboda kaine Babba, tayaya zasu auri Yara sukawo su gidan Nan, Yara su dinga gaisheka a matsayin yayan mijinsu suna ganinka babu aure ba?, saboda haka mun yanke shawara, bazamu hanasu Kai gaisuwa ba, Amma babu maganar sa rana, saka rana Sai Bayan bikinka, kaikuma za'a saka ranar ka yanzu, Kai saka rana, sukuma Kai gaisuwa, Bayan bikinka Sai ayi nasu, akwai yarinya me Hankali sunanta Ummi, kama Santa, Nan maqo tanmu take, Bama saikaje ganintaba bare Asamu matsala, kawai za'a saka ranar, tashi katafi " Tunda Uncle Usman ya fara masa magana yarasa gane Ina yake zaune? Jiyake kamar a mafarki Wai shi za'a had'a da ummi, yarinyar da kowa ya Santa batada kunya, sude burinsu shine yayi aure Amma babu ruwansu da yarinyar ta dace dashi ko bata dace ba, tasa qaddarar kenan kullum idan yazo Nigeria Sai anyi masa maganar aure, Bai iya cemusu komaiba Sai "to Uncle" daga Nan yatashi yanufi d'akinsa yana tafiya yana had'a hanya, domin kuwa wani irin baqi-baqi yake Gani, yana bude kofar d'akinsa yana kokarin shiga har bige goshinsa yake, Amma baidamu ba, abinda yake ji acikin zuciyar sa yafi bige goshin zafi,kulle Dakin yayi yafad'a kan gadon sa, wani irin hawaye me zafi ya silalo daga idanunsa, lokaci daya yaji duk duniyar tafita a ransa Bashida wata sauran dabara illa ya kar6i ummi a matsayin matarsa, basu bashi Dama yaje ya ganta Bama bare yayi wata dabarar daya saba yarabu da'ita, tabbas yasan Ummi, yarinyar akwai muni ba laifi, ga rashin kunya, jikinta ne kawai me kyau, tsakanin gidansu da gidansu Babban Yaya gida uku ne a tsakani *** Abu kamar wasa washe gari aka saka ranar Babban Yaya da Ummi ,wata uku kacal,Amma ba'a saka date din Daurin auren ba, Sai ankai lefe,duk wani hidima da akeyi na al'ada Daddy ne dakansa yayi ta yau su yanbiyu sukai candy Sai abun yahad'u ya zama kamar wani 'Dan qaramin biki ake, har zuwa lokacin Babban Yaya yana d'a kinsa a kwance, duk abinda yake faruwa hajiya Anty ta fad'a masa ta waya saboda taje 'Dakin nasa taji shi a rufe,saide duk text din data masa babu guda d'aya da yayi mata replay Acan makaranta kuwa, Waheeda saida ta jira su 'yanbiyu suka gama party a school sannan suka taho, yau driver bai d'auko suba, da kansu zasu taho, suna futowa daga get din makarantar, wani matashi me cikar kamala da kyau, gashi 'Dan Gayu, ya doko musu sallama, Ihsan ce ta amsa masa, yajuya yana Kallan Waheeda yace "qanwata idan babu damuwa Dan Allah inaso kibani number ki" Waheeda ta tuna karonta da Babban Yaya saita qi bashi amsa tajuya masa baya, murmushi yayi yace "haba qanwata, kamar Wanda zan sace ki?" Intisar tayi murmushi tace "Gaskiya Yayanmu yahanamu kula samari, Amma zamu baka number sa, idan ya amince shikkenan" Murmushi yayi yace "gaskiya kun birgeni, daga Gani daga gidan tarbiya kuka futo, insha Allah zan nemeshi, yabani Dama indinga zuwa muna gaisawa da qanwata" Yaqarasa maganar yana Kallan Waheeda, itade ba tace masa komai ba, saboda idan ta tuna Babban Yaya da police station din dataje, da 6atan wayarta, saitaji duk samarin sun fice mata Arai Number Babban Yaya Intisar ta bashi, sannan suka tafi, duk inda sukabi Sai an Kalle su, kyawawan yanmata su uku, kana ganinsu kasan ba hausawa bane, napep suka Hau yakaisu har 'kofar gida, suna shiga falo suka tarar da Hajiya Anty taci kwalliya, wuyan ta da kunnanta Sai qyallin gold suke, matar ta'iya daukan wanka na fitar Hankali,yar Gayu ce ta qarshe, raba Goro da alawa take, ga Kuma kudi Nan agaban ta dami dami, zama Waheeda tayi akusa da ita, jikinta yana gogar Nata. Tad'auko alawar guda d'aya tana sakawa a bakinta, sannan tacire hijabin jikinta, dogon gashinta ya baiyana,kwanciya tayi tareda d'ora kanta a cinyar hajiya Anty,sannan tace "Anty kayan me kike rabawa" Ummah tace "bansan yaushe zakiyi Hankali ba waheeda, kin sameta tana aiki memakon ki temaka mata, saide kihau cinyarta" Bakinta ta turo gaba cikin shagwa6a tace "Ummah Anty cefa" "eh saboda Anty ce saiki kashe mata cinya" Hajiya Anty tayi murmushi tace "Goron saka ranar Yayanku ne, yau ansaka masa rana,su Sa'eed Kuma ankai musu gaisuwa" Da Waheeda da 'Yanbiyu lokaci d'aya suka matso kusa da Hajiya Anty sukace "Babban Yaya?" Hajiya Anty ta d'aga musu Kai, haba ai da gudu Waheeda tayi d'akinsa, tura kofar tayi tashiga ta ganshi a kwance, ya rungume Fillo a qirjinsa, cikin murna ta fad'a Kansa tana sakin ihun murna, yana jin yanda aka fad'o Kansa yasan ba kowane zaiyi masa hakaba Sai ita, yatsina fuska yayi sannan ya tureta daga jikinsa yace "Yaushe zakiyi Hankali ne?" Cikin farin ciki tace "Babban Yaya, Dan Allah da pink colour da blue, dakuma green wanne ne yafi kyau?" Cikin mamaki ya daga Kansa ya kalleta batare daya tashi ba, yace "meyafaru?" Dantsan hannun sa takama ta riqe, tace "sonake kafadamin wanne ne yafi kyau saimu dakko ankon bikinka" Wani irin baqin ciki ne yakama shi,cire hannunta daga jikinsa yayi,ya maida Kansa fillo cikin damuwa yace "ni banason auren" Bata lura da yanda yake rabata da jikinsa ba tasake matsawa jikinsa tace "Meyasa Babban Yaya?" Juyowa yayi yana Kallan ta, yace "Akwai yarinyar danake so" Cikin farinciki tace "wayyo Allah, Babban Yaya Dan Allah wacece?" Kallan ta yayi yakasa magana, zuciyar sa ce take zugashi akan yafad'a mata, to Amma tayaya zata dauki maganar?, qalubalen dayake gabansa dangane da fad'a mata wannan maganar ba qarami bane Waheeda tace "Babban Yaya nikake kallo, wacece yarinyar?" Ajiyar zuciya yayi yace "Sunanku d'aya, kamar ku d'aya" Wani irin fari tayi da idonta tace "Dan Allah Babban Yaya kakaini wajan ta mugaisa, ka nuna mata ni, kafad'a mata nice qanwarka wadda kafi so" Lumshe idonsa yayi yabud'e, sannan yace "zan kaiki, Amma karki fad'awa kowa wannan maganar, sirri" Dariya tayi tace "bazan fad'a ba, Babban Yaya kasan me? Wallahi inaso kayi aure, sonake Naga matarka ta haihu, muga dawa yaran zasuyi kama" Tashi yayi zaune ya kalleta yace "ke har farinciki kike da bikin ne?" Tace "sosai ma, wallahi inaso kayi aure" Cikin wata irin gigitacciyar tsawa, wadda bata ta6ajin yayi mata irinta ba yace "tashi kibarmin dakina, tunda farinciki kike da aure na" Tace "Babban......" kafin ta qarasa yatashi tsaye cikin fishi kamar zai rufeta da duka, tana ganin haka tatashi tsaye, jikinta yafara tsuma saboda tsoro, qwalla ce tataru a idonta, tafuto daga Dakin cikin sanyin jiki Ayi hakuri da wannan ba yawa, muna tayaka murna Babban Yaya πŸ˜‚ Bazanyi zagi ba, Amma duk wacce ta karanta batare data biyaba, nabarta itada mahaliccinta, saboda babu yafiyata aciki Amnah 1/28/22, 20:50 - Ummi TandamaπŸ˜‡: Tana fita daga d'akin ya zauna akan gadonsa tareda dafe Kansa da hannun saπŸ€¦πŸ»β€β™‚οΈ? Ita farinciki ma take, meyasa bazata fahimceshi ba? Yace sunansu d'aya, yace suna kama, tayaya zai futo fili yafad'a mata gaskiya? Tayaya zata fahimce shi? Mezai fad'awa iyayensu idan suka ji daga inda maganar tafuto? Kansa ne ya Sara, yazube akan gadon yana fadin "hasbunallahu wa ni'imal Wakeel" Bayajin zai iya rayuwa batare da Waheeda ba, wasu hawaye ne masu zafi suka zubo masa, ya cusa Kansa cikin fillo yana kuka babu me lallashi kamar ba Babban Yaya ba πŸ˜‚ Tana barin 'Dakin nasa, d'akinsu tashige, ta zauna agefen gado tana Kallan p.o.p din 'Dakin, 'yanbiyu ne suka shigo, intisar tace "kekuma lafiya kikayi wani iri kamar marar lafiya?" Cikin damuwa tace "Babban Yaya ne" Ihsan da intisar sukasa dariya, Ihsan tace "to me yamiki Kuma?, kema da rawar Kai daga jin ansa masa rana kika d'iba da gudu kikaje" Kallan su tayi cikin damuw tace "Wai baya son auren ne" Inti tace "to yanzu ke menene naki aciki? Hanawa zakiyi? Mema za'ai da wannan Ummin, ni wallahi Bana sonta, kullum kaganta tana magana da maza" Ihsan tace "wallahi kuwa, inajin su Daddy basu Sani bane shiyasa, nifa shiyasa banyi murna ba danaji ance itace, Amma Waheeda uwar rawar Kai harda tafiya wajan sa da gudu, dama yasani yamiki shegen duka" Waheeda tayi shiru tana tunani, tana so tace musu yafada mata yarinyar dayake so to Amma Kuma data tuna yace mata sirri, Saitayi shiru, tayi ajiyar zuciya tace "nikam Ina sonta, tunda Babban Yaya zata aura, mutumin dayake taimako na aduk halin Dana kasance tayaya zanqi matarsa?" Ihsan tace "to Allah yabada sa'a Waheeda, ke kikaga Zaki iya" Daga Nan sukai shiru kowa da abinda yake saqawa Aransa Ita Waheeda tana tunanin Babban Yaya, duk yanda zaiyi mata fad'a tana shiga damuwa muddin ta ganshi acikin damuwa, saboda Shima baya barinta acikin matsala, ta damu da damuwar sa sosai, batasan meyasa ba, wani lokacin zai mata hukunci akan laifin da tayi, gashi de shine ya6ata mata rai ta hanyar yimata hukunci, Amma Hankalinta baya kwanciya Sai ta bashi hakura taga ya haqura tukunna, gashi yanzu yana wani Hali saboda auran Ummi, batasan ta wanne Hali zata taimaka masa ba,zuciyarta tabata shawara akan tatayashi da addu'ah, haka ta dauki shawarar zuciyarta Haka Babban Yaya ya wuni ad'aki yaqi futowa, Ummah Kota Kansa batabi ba, saboda tasan fishin nasa akan aure ne, Kuma aure Kam babu fashi Washe gari yafuto daga d'akin nasa, yana Sanye da kayan ball, suma 'yanbiyu maza shine ajikinsu, zama sukai afalo kowa yana kokarin saka safa, yanmatan ne suka futo daga d'akinsu suma de kayan Ball d'inne ajikinsu, Amma nasu wandon dogo ne, rigar ma me dogon hannu ce, sa6anin na mazan dayake qanana, fita sukai zuwa filinsu na qwallo dayake gidan, shikuma Babban Yaya yana falon yana saka takalmin sa, gaba d'aya iyayen nasu suna compound suna shan shayi, da hajiya Anty da Ummah dakuma Daddy da Uncle Usman, akan idonsu yaran suka futo zasu fara buga Ball din, Amma babu Babban Yaya, a lokacin harya gama saka kambos dinsa, yana zaune ne yana amsa wayar Abokinsa dayake tambayar sa yaushe zai dawo, yana gama waya da abokin nasa wata wayar tashigo, yayi mamaki da'aka kirashi ta wannan number, saboda ba kowane yasan wannan number tashi ba, dauka yayi tareda sallama daga dayan bangaren akace "Yayanmu Ina wuni? Sunana Didat, qanwarka ce tabani number ka,Ina neman alfarma ne awajanka, maganar Gaskiya Ina sonta, idan kabani Dama inaso na nemi aurenta" Babban Yaya ya Sosa girarsa guda d'aya yace "Sister na kuma?" Daga d'ayan bangaren Didat yace "eh Yayanmu, na gansu ne abakin get d'in school d'insu, akwai mutum biyu masu kama d'aya, toba suba, d'ayar nake nufi" Babban Yaya yana jin haka ya Lumshe Idonsa, cikin ransa yace "Waheeda" Dafarko har yayi niyyar dakatar da Yaron, but Saiyayi tunani tayaya rayuwa zataci gaba da tafiya Ahaka? Yaushe ne zai daina hanata huld'a da samari? Duk Daren dad'ewa dole zatayi aure, wazai fara fuskanta da maganar datake damunsa?qalubalen dazai fuskanta akan haka ba d'an qarami bane, Kuma itama da alama sonsa take, tunda gashinan ta yarda harta amince a tambayeshi? Cikin Yan seconds yayi wannan tunanin, wani irin huci yayi yafitar da iska me zafi daga bakinsa sannan yace "Babu damuwa zaka iya zuwa" daga Nan yakashe wayar tashi yafita zuwa compound da d'an gudunsa irin na 'Yan qwallo, acan Gefe ya hangi su Ummah sun baje suna shan Shayi, yana zuwa kuwa suka fara buga ball din mazan da matan, kusan mintuna talatin suka d'auka sunayi Amma Babban Yaya baici ko sau d'aya ba, mamaki ya kama iyayen nasu dasuke Kallan abinda yake faruwa, shida a qasar waje ma suke alfahri dashi akan iya ball, tayaya wad'annan yaran zasu dinga cinsa? Ada idan sunayin ball d'in kowa saduda yake, saboda sunsan comfirm 'Yan team din Babban Yaya sune da nasara, Amma yau Sa'ad da Babban Yaya, da intisar Sai sunci su Waheeda da Ihsan da Sa'eed suke yi. Sunkuyawa yayi yariqe gwiwarsu, damuwa tataru tamasa yawa, idan ya tuna da maganar Ummi, yatuna da wayar da gayen Nan yamasa akan Waheeda, saiyaji gabansa yafad'i, daga qarshe ma kawai juyawa yayi zuwa falon su, intisar datake jin haushi anata cinsu, tayi sauri ta hura Whistle tace "wasa yatashi" πŸ˜‚ Akan idanun iyayen Babban Yaya ya wuce falo yabar yan'uwan nasa, Waheeda tariqe hips d'inta cikin damuwa tana Kallan sa, daga Nan tabi bayansa, saide tana zuwa 'kofar 'Dakin nasa tayi nocking din duniya yaqi bude mata, dole Sai haqura tayi, ta wuce dakinsu. Washe gari da yamma Ummah tana zaune ad'akinta tana tunani akan rayuwar Naufal, damuwar dayake ciki haqiqa itama tana ciki, yaqi yafuto fili yafad'a mata me yake tsoro dangane da aure a matsayin ta na mahaifiyar sa, duk sa'anninsa sun dad'e da aure, Sai yaushe ne shi zaiyi? Tun yanda ta ganshi jiya cikin damuwa har yanzu Hankalinta yaqi kwanciya, duk yanda yake dason Ball yamaqi yakoma bare tace ball din zata d'ebe masa kewa, Waheeda ce tashigo Dakin tana Sanye da dogon hijabi tace "Ummah zanje bakin get nayi baqo" Ummah ta kalleta tace "Baqo kuma? Daga Ina kenan?" Murmushi tayi tace "shekaran jiya nahad'u dashi abakin get din school dinmu, sunyi waya da Babban Yaya ma, shine yace yazo" Ummah tace "kin tabbatar abinda kika fad'amin gaskiya ne Waheeda yayanku yasan da maganar sa?" "Allah Ummah yasani" "to shikkenan kije, Amma karki dade" cewar Ummah Waheeda tafuto daga d'akin, ta qarasa wajan Didat, yana Sanye cikin shadda Light blue, hular daya saka ta dace da kalar kayan nasa, qarasa wa tayi tareda sallama, ta ajiye masa ruwan roba guda biyu da Lemo guda daya, baba maigadi yataso da sauri yasake gaida shi, sannan suka qarasa wajan wasu kujeru masu kyau Wanda aka qawata wajan da yar qaramar rumfa domin shan iska, Didat ya kalli Waheeda Bayan ya zauna yace "Ranki yadade gimbiya" Waheeda tace "mudade tare" Murmushi yayi yace "bakice nayi kyau ba, Bayan duka wankan naki ne, kinsan kafin nafuto daga gida saida nafadama mamana wajanki zanzo, tace nayi kyau sannan tana miqa saqon gaisuwar ta zuwa gareki" Tace "nagode sosai, Ina amsawa, idan kakoma kace ina gaisheta" "zataji insha Allah,ni sunana Didat" Tace "nikuma Waheeda" Kallan ta yayi yace "sunanki yanada dadi Waheeda, Ina fatan ace kin zamo wani bangaren na cikin rayuwa ta idan kin amince" Tace "kamarya?" "Ina nufin kibani Dama Nima adama Dani acikin Jerin masoyanki, Amma maganar gaskiya itace inada kishi sosai akan abinda nakeso, shiyasa ma nakawo miki wannan kyautar" Yafadi haka yana bata wata leda, saida ta karba Sannan yace "hijabi ne da niqab, dakuma safa, gaskiya Ina kishinki Waheeda, aurenki nakeson yi bawai soyaiya ce ta kawo ni wajanki ba, banaso muyi shekara daya batare da munyi aure ba" Murmushi Waheeda tayi tace "gaskiya ne, nayarda kanada kishi, tunda gashi kyauta ta farko daka fara min itace da hijab da safa da niqab, Amma Kuma duk kishinka baka Kai Babban Yaya ba" πŸ™†πŸ»β€β™€οΈπŸ˜³πŸ™? Cikin mamaki ya gyara zama sannan ya kalleta yace "waye Kuma Babban Yaya?" Murmushi Tayi tace "nasan cewa kasan Big Brother ko?" Yace "sosai ma kuwa, waye zaice baisan Shiba? Aini shine 'Dan qwallon dayake mugun birgeni" Tace "to shi nake nufi, ai shine Babban Yayanmu" Didat yace "ok, Allah sarki, haba shiyasa Naga gidanku unguwa guda gashinan aljannar duniya" yafad'i hakan cikin sigar tsokana Waheeda tace "Shima yanada kishi, yafi son muyi karatu karmu kula samari" Yace "ya kyauta min, inda yabarku Aida Nima bazan sameki ba, nasan da tuni wani alhajin ya dauke ki" Murmushi tayi tace "nagode, zan koma gida, Ummah tace karna dad'e" Shima tashi yayi tsaye, ya ajiye mata rafar kudi Yan hamsin hamsin guda daya, aqalla zasu Kai dubu hamsin, daqyar da Fama Waheeda ta d'auki kudin, sannan suka rabu akan zai sake dawowa gobe ko jibi, tanada son kudi Amma Bana hannun mutane ba, saide na Babban Yaya, tasan yayanta ne bazai taba goranta mata a kan hakaba, abinda ta lura dashi shine, shi mutum ne me kishi kamar yanda yafad'a, sannan daga Gani bashida matsala ko kad'an Da daddare gaba d'ayansu suna zaune banda Daddy, Ummah ta kalli Babban Yaya dake danna waya yana qara Bawa Corch dinsu hakuri akan dad'ewar da yayi,Kallan Ummah yayi yace "Ummah nanda kwana hudu yaran Nan zasu tafi Umarah insha Allah, gaba d'ayansu" Cikin farinciki Ummah tace "Alhamdulillah, Allah yayima Albarka, to Allah yakaimu lokacin, Kai banda Kai ne?" Girgiza mata Kai yayi sannan yace "su kad'ai" Ummah tace "To madallah, Allah yaqara hore Maka," Murna suka hauyi gaba d'ayansu, Nan take suka fara zuba masa ruwan godia, Waheeda kuwa jitake kamar taje ta rungume shi Dan murna, Amma babu Dama yanda taga ya d'aure fuskar Nan tana zuwa kusa dashi tsaf zai maketa πŸ˜‚ Ummah ta sake Kallan sa cikin farinciki sannan tace"Yauwa yayansu ga wannan kud'in, saurayin Waheeda ne yabata dazu" Kallan kudin yayi Asheqe sannan yace "ok" Ummah tace "bangane Okay ba, bazaka kar6a kasa mata Albarka ba?" Yatsina fuska yayi yace "Ummah dubu hamsin d'in kamar Wanda yayi kyautar bajinta?" ☹️ Mamaki yakama Ummah, sukuwa su Sa'eed dariya suka saka, Sa'ad yace "haba Babban Yaya, dubu hamsin fa, kodan Kai mekud'i ne shiyasa, wallahi Ummi tahuta"πŸ˜ƒ Wani irin banzan kallo yamasa, lokaci d'aya yashiga taitayinsa Kafin su qara cewa komai wata yarinya 'yar kimanin shakara 11 tashigo da sallama hannunta d'aukeda wani flask na abinci, ta tsugunna ta gaida su Ummah sannan tace "Wai gashi inji Anty Ummi abawa Yaya Naufal" πŸ˜… Haushi yakama Babban Yaya, ya kalli yarinyar yayi tsaki a ransa, ko'ina ya zama yayanta harda wani Yaya Naufal,? Ummah ta saki ranta tace "Allah sarki, to kice ya gode, zai kawo mata kular da Kansa kinji, Allah yamiki Albarka," tad'auko fos dinta dake Gefe tabawa yarinyar dubu biyar, yarinyar cikin murna ta karba tafice daga falon Waheeda ce tataso tabud'e flask din taga abinda yake ciki, sannan tayi murmushi ta kalli Babban Yaya tace "Babban Yaya farfe...." kafin ta qarasa cewa farfesu ne, yatashi cikin fishi, yabar falon gaba d'aya, Ihsan da intisar suka zabgawa Waheeda harara suma sukai d'aki, Waheeda ta kalli Ummah cikin shagwa6a kamar zatayi kuka, Ummah ta janyo ta jikinta tace"rabu dasu, idan sun gama fishin zasu sakko" Washe gari da safe, suna break fast, wayar Daddy tayi qara, yayi mamakin me Kiran nasa, domin kuwa ba kasafai suke waya da minister of Education ba, d'auka yayi Bayan sun gaisa, Daga d'ayan bangaren minister Abdullahi Wakili yace "Alhaji Umar Arabo" Daddy yayi murmushi yace "ranka yadad'e, kwana dayawa ba'a jinka" Minister yace "wallahi kasan koda yaushe muna ta Fama da jama'ah, yanzu ma yarona ne Huzaifa yasaka ni agaba lalle lalle saina kiraka" Daddy yace "a a ikon Allah, Huzaifa ya dawo qasar ne?" Minister yace "wallahi ya dawo, cikin ikon Allah ya kammala karatun sa lafiya ya dawo, yazo ya sameni ne akan maganar 'yar wajanka, last week yaje 'Dauko sisters d'insa daga school sunyi party na candy, anan yaga yar wajanka Waheeda yace yanaso, shine da yayi bincike yagano 'yarka ce, Kuma kasan akwai sanaiya a tsakani, shine yace ayi masa tambaya aji ko an yiwa wani alqawari? " Daddy yace"A a babu alqawarin kowa, Allah ya tabbatar musu da alkhairi " Daga d'ayan bangaren minister yayi godia tareda kashe wayar Babban Yaya yanajin wayar da Daddy yake jikinsa yabashi akan Waheeda ake magana, Bai nuna komai akan fuskar saba, lafiya kalau suka gama cin abincin sannan ya dauki key din mota yafice daga gidan Da yamma Didat yazo tareda abokinsa Mukhtar, yau wankan qananun Kaya yayi, ba qaramin kyau yayi ba, suna cikin zance da Waheeda yace "Gimbiya inaso kije gida ki fad'awa Ummah zamuje shopping idan ta amince" Babu musu Waheeda ta wuce gida ta fad'a wa Ummah abinda Didat yace, Ummah tace "to karki tafi ke kad'ai, kuje keda yan'uwan ki" 'Dakinsu ta wuce, ta tarar Ihsan na wanka, Sai intisar dake karatu, tare suka futo da intisar basu jira Ihsan ba, suna zuwa kuwa Didat yace "lalle babbar Yaya, yanzu ashe Kuna ciki kun 6uya, ko sau d'aya bantaba ganinku ba" Intisar tace "Wallahi muna Nan, abubuwa ne sukai yawa, yakake" "Alhamdulillah, Ina lafiya kamar yanda gimbiya Waheeda take, dafatan de tare dake zamuje shopping din?" Intisar tace "babu damuwa muje" Tsayawa sukai suna jira yabud'e musu kamar yanda Babban Yaya yake musu, shikuma harya shiga motar, saida yajuya ya gansu a inda suke sannan yayi murmushi yazo ya bud'ewa Waheeda gaba, intisar Kuma suka zauna Abaya tareda abokinsa, suna hanya abokin Sai Jan intisar yake da zance, tana amsa masa kad'an kad'an, a wajan shopping d'inma Didat Kam kawai binta yake yana aikin kallon ta kamar wani sakarai, itace me za6ar komai, saida yakashe mata kud'i me yawa sannan suka Juyo gida, tun a hanya yaga tana amsa masa daqyar, Sai yatsina fuska take, suna qarasa wa gida kuwa intisar tayi ciki, ita Kuma Waheeda ta tsaya suna sake tattaunawa, Kallan ta yayi yace "Meyake damunki ne? Naga kamar bakya jin dadi" Yatsina fuska tayi tace "wallahi jinake zazza6i yana son kamani" Cikin rud'ewa Didat yace "Subhanallah, Amma shine kikai shiru? Meyasa baki fad'amin ba muje Asbiti?" Tace "Babu damuwa, zansha pracitamol agida" Didat yace "no, ga Mukhtar Nan yayi miki injection mana, akwai saura acikin motata Ina siya Dama saboda 6acin rana, idan kikaje gida saiki kwanta kihuta, Shima doctor ne" Cikin damuwa Waheeda tace "no, karka damu wallahi" Didat yace "a a, tsaya yayi miki please" Bud'e motar yayi, ya 'Dauko allurar yabawa Mukhtar, Mukhtar ya kar6a yafasa ruwan allurar, ya kalli Didat yace "Ina sirinji?" Didat yace "aikuwa na manta wallahi babu, but ga Wanda akamin allura dashi ban yarda shi ba, kayi mata dashi kawai"πŸ™†πŸ»β€β™€οΈ? Kallan Waheeda Mukhtar yayi yace "babu damuwa ayi miki gimbiya?" Tace "babu damuwa" Kar6ar sirinjin yayi yazuqe ruwan allurar, sannan yayi mata a hannunta, basu qara ko minti biyar ba, sukai sallama, tajuya zata tafi gida, adede lokacin Babban Yaya ya dawo gidan, fuskarsa ad'aure take babu wasa, ya gansu Amma saiya nuna baima gansu ba, Didat da baisan da shigo war Babban Yaya ba, ya qwalawa Waheeda kira, tana juyowa yayi kissing hannun sa, sannan yahura mata tareda kashe mata ido, yashige cikin motarsa Babban Yaya yana Kallan su, yakashe motarsa Bayan ya ajiye ta a parking space yafuto, adede kofar shiga falon suka had'u da juna, cikin ladabi tace "Sannu da zuwa Babban Yaya" Cikin 6acin rai yace "aikece za'ayi wa sannu,mahaukaciyar banza mahaukaciyar wofi, Kin tsaya yana miki hauka Amma ko ajikinki, kwata kwata bakya kishin kanki, idan kikai wasa naqara ganin qafar Yaron Nan a gidan Nan saina kakkarya qasusuwanki ...." "Subhanallahi .... Naufal?" Cewar Hajiya Anty da shigowarta kenan taga yana zazzaga wa Waheeda masifa Kallan ta yayi, yayi qasa da Kansa, idanun Nan nasa sunyi jajir tsabar 6acin rai, Sai huci yake kamar zai Fashe, ita kanta hajiya Anty ta tsorata da yana yinsa, ta kalli Waheeda datake share hawaye tace "Ke wuce ciki" Kallan sa tayi tace "Kayi hakuri" sannan ta wuce cikin falon nasu Hajiya Anty ta kalli Babban Yaya tace "yanzu bakaji kunya ba? Kagama yimata fad'a Amma daga qarshe haquri take baka ko kallo bata isheka ba? Hakan dakayi daidai ne kenan?" Yace "Anty kissing dinta fa yayi" yayi maganar kamar zai Fashe da Kuka Hajiya Anty tace "to naji tayi laifi wannan fad'an dakake mata shine zaisa ta nutsu? Qanwarka cefa, jininka ce tayaya bazakaja yarinya a jikinka ba zakadinga mata fada irin haka,?to tun tana jin tsoron ka, watarana zata daina, kaja Qanwarka a jikinka kaji nafada ma, fad'a ko duka basa shiryar da yaro" Qwalla ce take son futowa daga idanunsa yana dannewa, idan yatuna yanda Didat yake huro mata kiss, jiyake kamar yayi ihu, cikin 6acin rai yace "Anty niba qanwata bace, kidena cewa Qanwata" Hajiya Anty tayi sakare tana Kallan sa, a fili tace "ikon Allah, to ba Qanwarka bace, karka jata a jikinka, gata Nan ka kashe ta" Daga haka tajuya cikin gida tabarshi a wajan, Shima shigewa yayi ransa a6ace Tunda yashigo 'Dakin yakasa sukuni, tunani yayi masa yawa, daga qarshe ma tashi yayi yafara had'a kayansa, gobe da safe zai koma England bakin aikinsa, kwata kwata bayajin zai iya zama yana ganinta tana mu'amula da wani namijin bashi ba Cikin qanqanin lokaci yagama had'a komai,kawai jiran wayewar gari yake Kamar wasa Waheeda tana kwanciya bacci ya dauketa marar dadi, sakamakon abinda yafaru tsakanin ta da Babban Yaya , haka Shima anasa bangaren, baiji dadin baccin ba, har yanzu wannan kiss d'in ya tsaya masa aqahon zuciyar sa,washe gari kalau tatashi babu wani alamun zazza6i atare da'ita, 'yanbiyu basa 'Dakin Sai ita kad'ai take juyinta akan gadon, doguwar Riga ce ajikinta ta bacci Amma me kauri, bata nuna shape dinta ba kwata kwata, saide kana iya ganin tsayayyun breast dinta yanda suka tsaya a tsaye cak tacikin rigar, brush taje tayi tadawo 'Dakin nasu taga Maya na kiranta awaya, d'auka tayi tace "uwar 'Yan Fassara ya akayi?" Maya tace "ke dalla malama yau babu Fassara,Wai baqi mukai daga Abuja, shine wani daga cikin su yace yanaso na, ya tambayi mama yaushe zan gama karatu tace masa nanda wata shida, nikuma gaskiya Waheeda banason aure yanzu, nafison nayi karatu me zurfi, sannan baki ganshi ba Babba nefa, yakai Babban Yaya girma da shekaru, ko kunya babu waini yakeso, Dan Allah tayaya zan iya Zaman aure dashi Aida kunya" Waheeda takwashe da dariya tace "lalle ma Maya, to miye abun kunya? Tab wallahi karkiji kunya, ba aurenki zaiyi ba? Aiba haramun bane" Ummah ce tashigo 'Dakin zata fad'awa Waheeda taje gidan Hajiya Anty takira mata 'yanbiyu, Sai tajita tana waya, saboda haka saita dakata tagama wayar sannan ta fad'a mata Aiken, ita Kuma Waheeda kwata kwata bataji shigo war kowa Dakin ba Daga d'ayan bangaren Maya tace "ke bazaki gane ba, novel damuke karantawa duk fa abinda akeyi a novel idan akayi aure Nima fa haka zanyi, wallahi bazan amince ba babu ruwana, ni kunyarsa nakeji, gashi qato" Waheeda tasake fashewa da dariya tace "nikuma idan nice keko wallahi amincewa zanyi, tabdi to menene aciki ba mijina bane? Har wankansa zan dinga yi, keni har abar tasu zan kama na wanke, qarshe de kenan....." πŸ™ŠπŸ™ˆπŸ™†πŸ»β€β™€οΈ? Hawaye ne ya silalo daga idanun Ummah, innalillahi wa inna ilaihirraji'un yanzu Waheedanta ce take wannan maganar?Har abar zata kama ta wanke? Cikin kuka Ummah tace"Waheeda?" Gaban Waheeda ne yayi wata irin bugawa, kanta ya Sara, cikin sauri ta kashe wayar jikinta yana rawa,ko'ina na jikinta kyarma yake tama kasa yiwa Ummah magana Sai kanta datake girgizawa alamun Bahaka bane Ummah tayi kukan kura ta kamata tafara dukanta, ihu take tana neman temako Amma babu kowa a gidan, cikin ikon Allah tasamu tafuto daga 'Dakin, Ummah ta zauna a wajan tana kuka. tana zuwa compound adede lokacin shikuma yashiga motarsa kenan zai rufeta, ganinta yayi aguje ta nufoshi, kanta babu ko dankwali Sai dogon gashinta daya bazu agadon bayanta, kana ganinta kasan tana cikin mutuqar tashin Hankali,saboda fuskarta ma kadai gumi ne yake futowa ga hawaye sha6e-sha6e tanayi, duk ta rikice jikinta yana rawa kamar mazari, hakan yabawa cikakkun Breast dinta damar rawa kamar Wanda take kad'asu da niyya, tunawa da tayi jiya ransa ya6aci saboda ita, Sai taja ta tsaya cak a wajan tana waigen Bayan ta ko Ummah zata biyota, saboda tasan cewa Shima tana zuwa wajansa Dukan ta zaiyi. tausayi ta bashi, lokaci d'aya jikinsa yayi Sanyi, duk yanda akai ba qaramin laifi tayi ba, shiyasa take neman mafaka, dama shine Mai taimaka matan, to Shima yanzu tsoron zuwa take, tana tsoron tunkararsa saboda tasan confirm zaiyi mata hukunci, tunowa yayi da fad'an Hajiya Anty, Kuma yasan idan Yabarta ma zataci gaba da haduwa da wannan Yaron ne, yanzu yana hura mata kiss, to gaba gaba kiss din zaiyi mata a aikace, Gara ma sutafi tare kowa ya huta, ahankali tamkar baya son magana yace mata "shigo mutafi" Ai kamar jira Waheeda take , cikin sauri ta fad'a cikin motar, yayi mata key suka bar gidan 1/28/22, 20:50 - Ummi TandamaπŸ˜‡: BB Har sukai Nisa da gidan jikinta bai daina rawa ba, yana Kallanta ta gefen Idonsa, Amma be tambayeta wanne irin laifi ta aikata hakaba, Kai tsaye boutique suka wuce, Yabarta a motar yashiga yasiyo mata doguwar Riga dakuma hijab, kawo mata yayi, yafita daga cikin motar yabata damar sauya kayan, dube dube tafara ganin motar me baqin glass ce saita sauya kayan cikin kwanciyar Hankali, saida tagama komai sannan ta qwanqwasa glass din motar, yashigo suka tafi, kwana kwata ko awa daya basu qara ba, jirginsu ya Lula qasar England, acikin jirgin ma tana kusa dashi, saide har yanzu baice da'ita komai ba, itama haka, saima fad'awa da tayi cikin duniyar tunani, haqiqa Babban Yaya yana kaunarta, laifi nede idan tayi masa tasan cewa babu fashi Sai Tasha duka, yau da ace bai dauketa ba ta tabbatar Sai tafi kwanaki bata iya had'a ido da Ummah ba, maganar tayi nauyi ace itace ta fad'a, Amma Kuma akwai abinda zaka iya magana akansa kaida qawarka, wannan tsakanin kune,babu kunya babu 6oye-6oye, ajiyar zuciya tayi, Tajuya ta kalli Babban Yaya taga Hankalinsa yanakan jarida yana karantawa, matsowa tayi jikinsa tariqe dantsan hannunsa na Dama sannan tad'ora kanta akafad'ar sa ta Lumshe idonta, yanajin yanda hannunsa yake taba gefen breast d'inta, Sai a lokacin yatuna bai sako mata da brezia ba, jaridar hannun nasa ya ajiye akan cinyarsa, yajingina Kansa jikin kujerar tareda Lumshe Idonsa, yanajin yanda numfashin ta ya sauya yasan cewa bacci take, duniyar tunani yafad'a,inama ace wannan tafiyar sunada aure Honeymoon zasu tafi? πŸ€” Wani irin haushi yaji daya tuna Didat, dakuma Huzaifa da babansa yakira Daddy akan maganar Waheeda, jiyayi komai ya jagule masa, haka yayi shiru daga qarshe Shima baisan lokacin da bacci ya d'auke shi ba. Da yamma suka sauka, hannunta yana cikin nashi suka shiga mota, sannan suka qarasa gidansa, yanayin tsarin gidan kad'ai Waheeda ta kalla tazama yar qauye, gidan yayi matuqar kyau sosai, an tsarashi yanda ya kamata kamar baza'a mutu ba, motoci Kala Kala kusan guda shida a ajiye a compound, ga wani waje da aka qawata shi da dutsina ruwa yana gudana daga jiki, tafiya suke Amma hankalin Waheeda yana can tana Kalle Kalle har suka qarasa cikin falon bata Kallan gabanta, suna zuwa ta qwace hannunta ta fad'a cikin kujerun falon masu matuqar kyau da tsari tace "gaskiya Babban Yaya gidannan yayi kyau sosai" Zama yayi akusa da'ita Amma aqasan kafet, ita Kuma tana kan kujera, Kallan ta yayi yace "idan kinaso ai saiya zama mallakinki" Kallan sa tayi tace "Dan Allah? To Bani shi zakayi?" Murmushi yayi, dimple d'insa suka futo, yace "sosai ma, saiya zama mallakinki keda yaranki" Cikin rashin fahimta tace "Babban Yaya, abar wannan maganar, nasan kawai fad'a kake,tab! wayaga Waheeda da Yara, hmm ni yanzu ma yunwa nakeji" Babban Yaya ya kalleta yace "laifin me kikayi?" Shiru tayi tafara wasa da yatsun hannunta, ita de bazata iya fad'a masa magana me nauyi irin wannan ba, tayaya zata kalli idon yayan Nata tabashi labarin komai? Aida kunya, qarshan ta shima idan yaji yasaka ta a jirgi yau d'innan ya maida ta gida Kallan sa tayi tace "babu komai" Kafad'a ya d'aga yace "shikkenan tunda haka kika so" daga Nan yatashi yafita daga falon yayi waje domin Nemo musu abinda zasuci Tana ganin fitarsa tatashi ta dinga zagaye gidan tana santinsa, wayar Ummah datake hannunta ta kalla tasaki wani irin murmushi, ko Yaya suka qare agida? πŸ€” *** *** *** Ahaka Daddy yashigo yasamu Ummah ta zabga tagumi tana sharar hawaye, ga yanbiyu agefenta suna bata haquri, ganin shigo war Daddy yasa suka tashi suka nufi d'akinsu Daddy ya kalleta yace "mekuma yafaru kike kuka Hajiya?, inata Kiran wayar ki Amma najita a kashe" Hawayen ta share tace "wayar tana hannun Waheeda" Cikin mamaki daddy yace "to Ina ita Waheedan take?" Girgiza Kai tayi tace "bansan inda take ba, Amma megadi yace sun fita tareda yayansu, shikuma munyi sallama dashi zai koma England, bansani ba ko tare suka tafi" Kafin yabata amsa hajiya Anty tayi sallama cikin falon tashigo, zama tayi Bayan sun gaisa da Daddy tace "Anga Waheedan?" Ummah tace "ba'a ganta ba,tana tareda yayansu" Hajiya Anty tafara kokarin Kiran Naufal, Amma wayar taqi shiga, haka ta haqura, bata dade da zama ba tatafi gida saboda Daddy yana Nan tace zata dinga try ko wayar zata shiga Ummah naganin fitar Hajiya Anty ta kalli Daddy sannan ta zayyane masa komai babu abinda ta rage akan wayar dataji Waheeda tana yi. Daddy yadafe Kansa yace "ita Waheedan ce tafad'i haka?" Ummah ta 'Daga masa Kai alamun hakane, cikin damuwa yace "Hajiya, yanzu kiwon mutum ake ba dabba ba, tun kafin yarinyar Nan ta lalace Gara ayi mata aure, zaifi sauqi" Ummah tace "Nima abinda nayi tunani kenan, amma muddin mukai ido hudu da Waheeda sainasa Sa'eed yayi mata Dukan tsiya, duk inda suka tafi ai zata dawo" Daddy yace "matsalar yarinyar Nan bame qarewa bace, Allah yasa de yanda take fad'a a wayar bawani tata6a yiwa hakan ba" πŸ˜–πŸ˜‚ Cikin jimami Ummah tace "Amin" *** *** *** Anan falon ya dawo ya sameta, hannun sa d'aukeda ledoji, ajiye mata yayi yazube akan kujera, duba kayan tafarayi, leda d'aya ta abinci ne daya siyo musu, d'ayar Kuma kayane yasiyo mata nasaka wa, abincin ta zuba sannan Shima tazuba Masa nasa, saukowa yayi daga kan kujerar yaja Nata abinci yafara ci, Kallan sa tayi cikin mamakin abinda taga yayi tace "Babban Yaya ga Naka fa" Wani irin kallo yayi mata Mai d'auke da ma'anoni, sannan yace "ni wannan nake son ci, kisa hannu muci" Babu musu tasaka spoon din tafara cin abincin, wani abincin ya 'Debo a spoon me yawa, yaci 'Dan kadan, sannan ya nufi bakinta da sauran, yace "meyasa bakyaci dayawa ne?" Murmushi tayi tace "Babban Yaya ai kaima haka, bakaci" tafadi hakan tareda bud'e bakinta, babu musu yasaka mata,haka ya dinga yimata, Sai yaci kad'an saiya bata sauran, Waheeda bata d'auki hakan da wata manufa ba, zuciyar ta d'aya take cin abincin dayake bata, Kallan bakinta yake yanda take tauna abincin cikin nutsuwa, yanda lips dinta suka hadu da maiqon Mai suke wani irin shinning, Sai hankalin sa yafara tashi, yatuna ranar dayayi kissing d'inta Jiyake inama ace ita d'in tazama mallakin sa? Da babu abinda zai hanashi kasacewa da'ita a wannan Daren, yamaidata cikakkiyar mace, ajiyar zuciya yasauke, ya kawarda wannan tunanin daga cikin ransa, tashi yayi yanufi d'akinsa ba tareda yace mata komai ba. Yana zuwa 'Dakin shirin wanka yayi, ya wuce toilet ya watsa ruwa tareda d'auro alwala, 'Dakin tashigo hannunta d'aukeda ledar kayan daya siyo mata, ganin zaiyi sallah tayi saurin ajiye ledar tashiga toilet ta d'auro alwala tazo ta bishi, saida suka idar sannan tashiga wanka, shikuma yacire jallabiyar jikinsa ya kwanta akan gadon dagashi Sai gajeren wando, tareda 'Dauko wani diary yana rubutu aciki cikeda damuwa, daga shi har Waheeda babu Wanda yake tunanin Kiran Yan gidaπŸ˜‚ Futowa tayi daga wanka tana Sanye da rigarta ta bacci, turare kawai ta fesa tanufoshi ta zauna aqasan kafet din, shikuma yana kan gado ya rungume diary din a qirjinsa, Kallan ta yayi yaga tasa shi agaba tana aikin kallon sa kamar tasamu TV harda tagumi, yace "lafiya?" Murmushi tayi tace "Babban Yaya wallahi kana birgeni, babu ruwanka da neman tsokana, Kai haka rayuwar ka take, inajin Kai ka haqura da duniya ma" 😳 Kwata kwata baya cikin yanayin farinciki Amma jin wannan maganar Tata Sai dariya ta kamashi yace "na haqura da duniya Kuma?" Fari tayi da idonta tace "Emana, gashinan to babu ruwanka da shiga harkar kowa, rayuwar ka cikin kwanciyar Hankali" Juyowa yayi yana Kallan ta, har zuwa lokacin dairy din yana rungume a faffadan qirjinsa, yace "tayaya zan haqura da rayuwa Bayan bansamu abinda nake soba?" Tace "zaka samu Babban Yaya,nasan saboda me kama da nine kace haka, Bari kaji ai dole ma ka sameta ko tana so ko bata so,nikam yanzu banida damuwar komai" Yace "Serious?" Wani iri farrrrrr tayi da Zara zaran gashin idonta, sannan ta 'Dora hannunta akan qirjinsa tana so taja littafin daya rungume, shikuma yahana, saima Qasan fillo daya turashi ciki Bata d'auki hakan a matsayin komai ba, batasan cewa baya son taga dairy din bane, batayi tunanin wani abu na sirrinsa yake rubuta wa aciki ba, shiyasa Bata damu da saita ganiba, saita share, saima hannunta data d'ora akan faffad'an qirjinsa take shafa gashin da yayi kwance akan farar fatarsa, sannan tace "I'm serious Babban Yaya, banda damuwar komai, kana tsaya min akan komai,nasan cewa nafi kowa sa'ar samun Yaya me kula da qanwarsa, shiyasa bayansu Ummah da Daddy banida Wanda yafika" Kwata kwata Babban Yaya baiji abinda Waheeda take fad'a masa baπŸ˜‚ idanunsa a Lumshe suke, shi Kansa ba zaice ga duniyar dayake ciki ba, wani irin dad'i yakeji yanda take shafa qirjinsa, Waheeda bata lura da yanayin data jefa yayan Nata aciki ba, kawai qirjinsa take shafawa tana wasa da gashin qirjinsa me mutuqar laushi, ahankali tace "Babban Yaya Wai meyasa bakasan aske gashin kirjinka? Yafara yawa fa...." Babban Yaya baima bud'e Idonsa ba bare yabata amsa, baya so yayi magana ta daina abinda take masa, yafiso taci gaba, Kallan sa tayi taga Idonsa a Lumshe, tayi murmushi tad'auki wayar Ummah data gudo da'ita ta kunna, sannan ta kunna masa tasa wayar, kamar jira ake, tana kunna wayar Babban Yaya kira yashigo da wata number,tsabar nacin da me number take masa ne yasa ya rubuta wa ne number Ummi Nigeria , Waheeda ta janye hannunta daga kan qirjinsa tace "Babban Yaya Ummi Nigeria tana kira, wacece?" Cikin takaici yabud'e Idonsa, yaji haushin shigo war Kiran wayar, gashinan ta katse masa jin dad'insa, Kansa tsaye yace "Ummi ce" Cikin murna Waheeda tace "Bari in d'aga mugaisa" Cikin sauri yatashi zaune yace "kice mata me? Karki d'aga, ni Bana d'aukan wayarta, me kikeso nace mata idan nad'auka?" Waheeda takama dariya yanda taga ya rikice shi baza'a daga wayar Ummi ba,Sai hakan yasake bata dariya, tace "Toni kabarni in d'auka saimu gaisa" Ganin zata d'auki wayar yasa yamatso kusa da'ita zai qwace wayarsa,ita Kuma tana ganin haka tahanashi, kokawa suka fara irinta masoya tana d'aga hannunta sama Dan karya qwace wayar shikuma yanaso ya qwace, saura qiris wayar ta katse Waheeda tayi nasarar picking ba tareda ta saniba Daga d'ayan bangaren ummi tayi gyaran murya tareda lanqwasa harshe tace "Hello Dear" Taji shiru, tasake cewa "Hello my Dear..." nanma taji shiru Sai alamun ma kokawa dataji anayi tacikin wayar, kasa kunne tayi taji Babban Yaya yana cewa "Kibani wayata nace...." Waheeda ta hanashi Sai dariya take, tana tsaye akan gadon shikuma yana tsugunne bai tashi tsaye ba, cikin dabara yariqo Hips d'inta da duka hannayensa, cikin dariya tayi baya zata fad'i saiya tareta tafad'o qirjinsa, breast d'inta Wanda ko bra babu, yasauka akan fuskar sa, cikin ransa yace "Ya Salam.......wayyo Allah nah...." jiyayi gaba d'aya jikinsa ya mutu, yaso ace yanada Dama da saide yasake rungume ta a qirjinsa,zaiso ace yasake cusa Kansa acikin nashanunta, lokaci d'aya yana yinsa yafara sauyawa Daurewa yayi, yayi ta maza sannan ya qwace wayarsa, yasake ta tafad'a kan gadon tana dariya, wayar ya kalla yaga har anyi minti uku da d'auka.... Ba tareda yayi magana ba yakashe wayar Daga d'ayan bangaren Ummi tasaki ajiyar zuciya cikin bacin rai tace "Kan ubancan!, da wacce shegiyar yake tare? Ni za'a nunawa bariki?" πŸ€₯😠 1/28/22, 20:50 - Ummi TandamaπŸ˜‡: WN Sake Kiran wayar Ummi tayi, Amma Naufal yana Gani yayi mursisi yaqi dauka, saima wuta daya kashe, yayi shirin bacci, saboda gaba d'aya yanayinsa ba daidai yake jinsa ba Waheeda ma fillo taja zata kwanta akan gadon, yana jin alamun kwanciyar ta kamar an tsikare shi yayi sauri yatashi zaune, yace "mezakiyi?" Kallan sa tayi cikin duhu tace "Bacci mana Babban Yaya" "ok" abinda yace kenan, sannan ya sauko daga kan gadon ya shimfid'a wani blanket Mai laushi, yaja fillo d'insa ya kwanta, yana d'auke fillon Waheeda taga wannan dairy din, batayi masa magana ba saida taji shiru alamun yayi bacci sannan ta d'auka tafara bud'ewa, 'Dakin yayi duhu bata ganin komai,saita janyo wayar Ummah ta haska tafara karantawa, shafin farko Zanan heart ne ajiki, yayi kyau sosai Zanan,har ya d'auki Hankalinta sosai, shafi na biyu ta bud'e tafara karantawa inda ya rubuta (Rayuwa Mai sauyi,a koda yaushe zata Iya sauya Maka, daga qaddara Mai kyau ko marar kyau,akoda yaushe qaddarar mutum tana iya sauyawa,banajin zan'iya rayuwa ba tareda itaba, Abaya kafin zuwanta komai nawa cikin nutsuwa da kwanciyar Hankali nake yi, tunda tashigo cikin rayuwa ta, komai ya sauya, Abaya Ina rayuwa ne tareda 'yan'uwana cikin kwanciyar Hankali, haihuwar ta ne...... " "mekikeyi ne bakiyi bacci ba? " Waheeda ta tsinci maganar Babban Yaya, cikin sauri tarufe littafin ba tareda ta qarasa karantawa ba Tasowa yayi ya d'auke Dairy d'insa, sannan yakoma ya kwanta, fatansa d'aya, Allah yasa bataga komai ba Itama rufe wayar tayi tareda Lumshe idonta, akan me yake magana? Wacece wannan d'in? Yace mata me kama da'ita yakeso, but yanzu akan wa yake magana? Kanta ne ya d'aure gaba d'aya Shima anasa 6angaren kwata kwata yakasa nutsuwa, yana tsoron ace taga abinda ya rubuta, ahankali yayi maganar qasa qasa yace "Kin karanta?" Kamar daga sama ta tsinci maganar tasa, girgiza kanta tayi kamar yana ganin ta tace "A a" Beqara cemata komai ba, itama haka, kasa runtsawa yayi saida yaga tayi bacci sannan yatashi yayi toilet yayi wankan tsarki, sannan ya 6oye dairy din yakoma ya kwanta Washe gari yariga ta tashi, lokacin data tashi bata ganshi ba, Dakin ta gyara tayi wanka, tasaka wani Riga da wando data Gani acikin kayan daya siyo mata, kayan taketa juyawa tana mamaki Babban Yaya ne da Kansa yasiyo mata wannan kayan?shida baya son su dinga yawo babu hijabi Amma shine da siyo wannan kayan? (hmm yo bashi za'a sakawa ba🀣) Wandon crazy ne, Amma yagar jikin batada yawa, Sai Riga marar hannu yar qarama wadda da kadan ta wuce mata cibiya, Bayan rigar kuwa abude yake, Amma gaban rigar wajan breast din a rufe yake, mamaki ne yakamata sosai, haka tayi parking gashin kanta, tadauko bra din data Gani a kayan tasaka, tayi mata cif kamar Wanda ya gwada ta, ko Yaya akai yasan size dinta? πŸ€” Saida tagama shirya wa tsaf sannan tafita falon, tad'an gyagygyra, daga Nan tayi kitchen tafara hada break fast, tana cikin soya qwai yashigo kitchen din, abakin kofar kitchen din ya tsaya tareda rungume hannun sa yana qare mata kallo tundaga sama har qasa, hips dinta yafi komai daukar hankalin sa, kayan sunyi mata kyau jiyake kamar yaje ya rungume ta, wayarsa ce tayi qara cikin sauri Waheeda ta juya, tana ganinsa tasaki ajiyar zuciya tace "wallahi harna tsorata" Bece da'ita komai ba Sai falon daya koma ya zauna, ya dauki wayar cikin farinciki, dimple dinsa har lotsawa suke, yace "Anty na takaina" Hajiya Anty tace "Sai yanzu kaga damar bude wayar kenan, Ina Waheeda?" Kitchen din ya kalla sannan yace "gatacan tana hada mana breakfast, wallahi anty naji dadin tafiya da yarinyar Nan, kinga da, duk lokacin da zanyi girki da kaina, to Bana fita ball, saide in zauna agida, inyi shara, inyi mopping, inyi wanke wanke, in goge kwanukan, sannan na maida su kitchen, Kai Ina shan wahala fa " Hajiya Anty tayi shiru tana mamakin yanda Babban Yaya yake cikin farinciki, shida ba gwanin surutu ba, Amma Sai zuba yake kamar kanya, ajiyar zuciya tayi tace" kaide kawai kace sakalci ne yayi Maka yawa, idan kana shan wahalar aiki Aida tuni kayi aure " Cikin shagwaba yace"wayyo Allah Anty kidena maganar auren Nan Dan Allah, yanzu de yakike? Ina Ummah? " "Ummanku tana nan lafiya, Nima kira nayi in tabbatar Kuna tareda Waheeda ne ko bakwa tare? " "muna Tare Anty" Tace" to shikkenan, kakula da'ita, zan tafi hospital Sai anjima " Sallama sukayi, adede lokacin Waheeda ta ajiye musu abincin, tana zama taji wayar Ummah tana ringing, tashi tayi tatafi Dakin da gudu saboda kar wayar ta katse, Babban Yaya yabita da kallo yanda Hips dinta suke rawa kamar da niyya take kad'asu, wani irin yawu ya hadiye, sannan ya kunna TV danta dauki Hankalinsa dubawa tayi taga Didat ne, murmushi tasaki sannan ta zauna abakin gado tareda daukan wayar"Yaya Didat...." "Ina kika tafi nazo gidan akace bakya Nan?" "wallahi Bana Nan Ina England tareda Babban Yaya" Yace "what! mezakiyi acan? Kuma kirasa dawa Zaki tafi Saida namiji?" Cikin rashin fahimta tace "mekake nufi?" Kansa yadafe da hannun sa, sannan ya seta Kansa yace "kiyi hakuri Waheeda, inada kishi ne, please Wai yayanku yaushe zaiyi aure ne?" Tace "menene hadin aurensa da soyaiyar mu?" Wayancewa yayi yace "haba My dear, Yaya nanefa kamar yanda yake yayanki, laifi ne danna tambaya yaushe zaiyi aure? Ai abun farinciki ne" Murmushi tasaki taji dadi yanda ya dauki yayanta, tace "yakusa aure, ansaka rana nanda wata uku, Amma ba'a tsaida date ba, Sai ankai lefe" Wata irin wawuyar ajiyar zuciya ya sauke da yaji komai, sannan ne yasa ki ransa suka gaisa sosai, yasake fada mata takula masa da kanta, sannan sukai sallama Takoma falon suka fara break fast itada Babban Yaya Suna gama cin abinci yafita, baidawo gidan ba har dare, haka ta wuni ita kadai, idan ankira wayar Ummah bata dauka, bataga Kiran yanbiyu ba, tasan cewa sun tafi Saudia, kamar yanda Babban Yaya ya fad'a Kallo suke cikin kwanciyar Hankali, baya tareda wata aba Wai ita damuwa, asalima yau yabuga Ball wadda bai taba jin dadinta kamar yau ba. Acan Nigeria kuwa, Su Hajiya Anty da Uncle Usman suna gidan Daddy, babu kowa a gidan duk sun tafi Saudia, Sai iyayen su kadai, Kallan labarai suka gama yi, Uncle Usman ya sauya Tasha, anan yaga Babban Yaya yana buga Ball yanda ransa yakeso kamar ba shine yake qunci saboda ance za'a bashi Ummi ba, Murmushi yayi ya kalli Hajiya Anty yace "kinga d'an wajanki fa" Murmushi tayi tace "ai qwazon nasa awaje yake, yanzu kwanaki dasukayi da Yara ai kasawa yayi" Ummah tayi shiru tana tunani, itade bata tanka ba, domin kuwa a cike Takeda Waheeda, Daddy ne ya dauki wayarsa yakira Babban Yaya, tana shiga yace "idan kun gama 6oye 6oyen naku kakawota gida, muna son ganinta, sannan kaima ka tabbatar kataho lefenka yana Nan angama hadawa yakamata kazo kagani, idan kagani komai yayi yanda kakeso Sai akai musu, su tsaida mana ranar auren" Jikinsa ne yayi Sanyi, cikin ladabi yace "to shikkenan Daddy" daga Nan yakashe wayar ya kalleta yace "kishirya gobe Zaki wuce gida" Kallan sa tayi tace "Babban Yaya kaifa?" Shiru yayi yana tunani, shide bayajin zai iya zuwa haka kawai saboda ganin kayan lefen Ummi, to waye ma yace su hada masa wani lefe? Kansa yadafe da hannun sa yace "nikam bazani ba" Yanda taga yabata amsa ransa duk adagule kawai Saitayi shiru karta sake magana yahuce akan ta Haka suka wuni ranar babu walwala atare dashi, tana so tace masa yakaita yawo Amma bataga fuska ba, haka tayi shiru tana gudun aikata laifi yahuce akanta, washe gari da safe tare suka tafi club dinsu da'ita,tana Sanye cikin doguwar Riga Abaya, saita yafa mayafin abaryar akanta, idan ka ganta bazaka taba cewa tanajin hausa ba, saita zama kamar wata balarabiya, hannun sa cikin Nata suka futo daga motar da aka kawo su, yana futowa mutane suka yanyameshi yanmata turawa Sai rungumeshi suke, wasu Kuma suna shaking din hannu, yanda yake murmushi dimple dinsa na futowa Sai hakan yabawa Waheeda haushi, suna zaune gida daya kullum yana daure musu fuska Amma Jiba yanda yake sakarwa yanmata jikinsa da fuskarsa, saida yagama photuna dasu sannan sukayi ciki, Waheeda de nemanta ma yayi yarasa, tun tuni wasu daga cikin masoyansa suka janyeta, dressing room dinsu yayi, Bayan Dan wani lokaci suka futo aka fara buga ball, tun tanajin haushinsa tana Kallan yanda yake buga ball din harta dawo ta daina ganin yanda dubban mutane suke murna idan Dan'uwan Nata yajefa qwalla araga Saida suka gama sannan yayi abinda zaiyi ya dauketa suka wuce airport, a Airport dinma Gani tayi yayi shiru kamar akwai abinda yake damunsa, kasa hakura tayi tace "Babban Yaya meyafaru?" "banason tafiyar kine" Baisan lokacin da wannan maganar tafuto daga bakinsa ba kamar Wanda aka qwatota, Kallan sa tayi cikeda farinciki tace "Allah?" Wayancewa yayi yace "ke wasa nake miki, banason shirme, kawai.... Kawai de... Banji dadin yanda Daddy yamin maganar lefe bane" Ya qarasa maganar a rarrabe fuskar sa cikeda fishi "nikuma Babban Yaya banga abun fishi anan ba, zaka iya auren wadda kakeso daga baya" Cikin 6acin rai yace "Kina tunanin zan hada abinda nakeso dawani abu daban? Kinga banason damuwa, muje kunfara shiga jirgi" Kanta ta gyada masa batare datace komai ba suka tafi, saida yaga jirginsu yatashi sannan yakoma gida Jirginsu yana sauka taga driver yana jiranta, mamaki ya kamashi ya kalleta dakyau yace "Waheeda yanaga kin sake kyau? Me yayan naku yake baki?" πŸ€” Harararsa tayi tace "shafa kaji, ka bude min mota kawai, Kuma gidan Hajiya Anty zaka kaini" Jinjina Kansa yayi, yasan rashin kunyar Waheeda, zatayi yafi haka, jakar hannunta ya kar6a sannan yace "lalle Waheeda idan kikai shekara a qasar waje bazamu ganeki ba, cikin abunda baifi 'Yan kwanaki ba kikai irin wannan kyau haka?"πŸ€” Tana jinsa tasaki wani Dan qaramin tsaki, damuwar ta daya yanzu shine Ummah, bata Isa taje wajan Ummah ba, Gara ta gudu gidan Hajiya Anty yafi sauqi Suna hanya ta turawa Babban Yaya text cewa ta sauka, Saukarsu gidan Hajiya Anty keda wuya taci Karo da wasu akwatuna masu shegen kyau guda ashirin da hudu, dozin daya pink colour, dozin daya blue, akwatunan ne suka dauki hankalin ta, tafara ta6a jikinsu tana qwalawa hajiya Anty kira, futowa tayi daga d'akin ta tayi mutuqar kyau cikin atamfa dinkin Riga da siket, kullum cikin Gayu take bata gajiya Tana ganin Waheeda tace "Oyoyo daughter" tafadi hakan tareda bude hannayenta, babu musu Waheeda tashige jikinta, Hajiya Anty ta rungume ta tanajin qaunar yarinyar acikin zuciyar ta Zama sukai akan kujera Waheeda tasake Kallan kayan tace "Anty lefen Babban Yaya ne wannan?" "lefensa ne, Uncle dinku ne yayi order su daga Dubai, abubuwa kad'an muka qara anan, Amma ba'a saka mata pant da brezia ba, zan Mai magana saiya tambayeta size dinta" Waheeda tayi ajiyar zuciya "Anty Babban Yaya fa baya son auren Nan, kukuma Naga kun dage" "zaiso ne Idan akayi, ai kinsan qiyaiya tana komawa soyaiya" "to Anty, Allah yarufa asiri" Anty tace "Amin ya Allah, kibude kigani mana" "a a Anty, basai nagani ba, Allah ya basu Zaman lafiya" Hajiya Anty tayi murmushi, takasa gane yanayin yarinyar, shin kishi take, kokuma kawai 6acin raine Dan taga yayan Nata ma baya son auren? πŸ€” A gidan Hajiya Anty tayi Zaman ta har kusan sati daya da dawowar ta, koda wasa bata nufi gidan Ummah ba, sauqin ta daya, suna cikin hutu Ranar da tayi kwana Tara, ranar su yanbiyu suka dawo daga Saudia, murnar dawowar yan'uwan Nata ne yasa tatafi gidansu, Hajiya Anty tarakata suka tafi tare, lafiya kalau suka gaisa da kowa, anan falon aka baje Ana hira, Ihsan ta kalli Waheeda tace "shikkenan Waheeda kin luser bakije Saudi ba" tafadi hakan cikin sigar tsokana Waheeda ta yatsina fuska tace "ai zuwa makkah Kiran Allah ne, dama can banda ni yakira, Nan da lokaci kadan kunaji Kuna Gani zamu tafi nid Babban Yaya" tana fadar haka tatashi ta wuce dakinsu Sa'ad da Sa'eed suka bita da kallo, Sa'eed yace "Sa'ad kasaka yarinyar Nan acikin addu'ah kuwa da mukaje Saudia?"πŸ€” Kafin Sa'ad yabawa dan'uwan nasa amsa, Ummah tatashi taciro wayar charger tabawa Sa'eed tace "jeka zanemin yarinyar can" Babu musu kuwa Sa'eed yanufi Dakin nasu, adede lokacin Waheeda tacire Kaya zata shiga wanka, daga ita Sai towel, lokaci daya taji saukar duka ajikinta, ihu tasaki, su Ihsan suka qaraso Dakin suna temakon ta, memakon ya qyaleta, saiya had'a dasu yakama duka, aikuwa babu shiri suka futo kowacce tana Sosa jiki (duk Wanda ya karanta min littafi be biya ba shida Allah) Saida yayi mata lilis sannan Yabarta, yana futowa daga d'akin Daddy yashigo, ya zauna a kujera, cikin ladabi hajiya Anty ta gaishe shi sannan tayi musu sallama tatafi, Kallan Ihsan yayi yace "jeki kiramin qanwarku" Dakinsu tashiga, Waheeda tana kwance aqasan Dakin tana kuka, duk jikinta yayi ja inda wayar tata6a ta,idanunta har sun kumbura gashi sunyi jajir dasu, fada mata saqon Daddy tayi, cikin kuka Waheeda tace "Dan Allah Ihsan d'agani, wallahi bazan iya tashi ba" Ihsan ta kamata tatashi zaune har towel din yana kokarin cirewa, hijabi tabata tasaka, sannan suka futo falon, zama tayi aqasa tana sheshshekar kuka ahankali, Ummah ta kalleta tace "marar mutunci Ina wayata take?" Cikin kuka tace "Dan Allah Ummah kiyi hakuri, wayar tana daki, Dan Allah karku fadawa Babban Yaya" Daddy yace "Waheeda zancen Babban Yaya aiya qare, kifada wa shi wannan Yaron dayake zuwa wajanki yafuto ayi muku aure inda gaske yake, idan Kuma bakya sonsa to akwai huzaifa Yaron Abokina zaizo Shima ki ganshi idan yamiki shikkenan, bazaki gama karatu kamar yan'uwan kiba, aure zan miki " Waheeda najin haka ta rushe da Kuka tafara Bawa Daddy hakuri, Amma mursisi haka Daddy yatashi yayi daki Yabarta anan, intisar ce ta kamata suka koma daki harda Ihsan ma, suna zuwa Dakin suka fara bata haquri, Amma Inaaa Waheeda Sai kuka take har kanta yazo yafara ciwo, daga qarshe, wani irin zazza6i me zafi yarufe ta Da asuba daqyar tayi sallah Takoma ta kwanta, ko Yaya ta motsa jikinta saita runtse ido saboda yanda ko'ina na jikinta yake mata ciwo, qarfe goma da rabi Ummah taga abun na Waheeda gaba yake, tun jiya jiki yaqi dadi, Nan da Nan Kuma Hankalinta yatashi, tasa Sa'ad yakaita Asbiti, yanbiyu ne suka shirya ta suka tafi gaba dayansu. Suna fita wayar Ummah tayi qara, number tagani, ta dauka tareda sallama, daga d'ayan bangaren akace "Mama Huzaifa ne" Ummah ta fada da fara'art tace "Au Huzaifa, ashe kaine, ya mutanan gida" "suna Nan kalau Alhamdulillah" daga Nan Kuma Sai yayi shiru baice komai ba Ummah data fahimci inda yasa gaba, saitace "Huzaifa Waheedan bataji dadi bane, sunje Asbiti yanzu, Amma idan suka dawo, zata kiraka" Cikin tsantsar damuwa yace "subhanallah.... Ummah meyake damunta? Suna wanne Asbiti, meyake damunta....?" Ummah ta jijjiga Kai ganin yanda Yaron yarikice lokaci d'aya, tace "suna wani private Hospital Annoor" Godia yayi mata, sannan yakashe wayar (idan kinsan bada yardata kika karanta wannan littafin ba, keda Allah, nabarki da Allah, koba yauba karkizo neman yafiya ta ehe) *** *** ** suna zuwa Asbitin Waheeda ta yanke jiki tafadi,bayan likita ta dubata tace "yarinyar Nan akwai qarancin jini ajikinta, dole zamu qara mata jini leda d'aya zuwa biyu" Nanfa hankalin 'yan'uwan Nata yatashi, Sa'ad ya kira Ummah yafad'a mata halin da ake ciki, cikin tashin Hankali tace "gatanan zuwa" Gidan Hajiya Anty tatafi, daga Nan suka nufi asbitin, suna zuwa adede lokacin Shima Huzaifa yazo, had'ad'd'en Gaye ne nabugawa a jarida, wankan tarwada ne, yanada tsayinsa daidai misali, kana ganinsa kasan hutu da jin dadi sun zauna masa, tare suka shiga Dakin da aka kwantar da Waheeda, suna zuwa kuwa numfashin ta yafara yin sama kamar zata suma, hankalin Ummah yatashi, Nan da Nan tafara hawaye, Hajiya Anty tace "Haba Hajiya, idan kina kuka sukuma yaran mezasuyi kenan?" Kafin Ummah tabata amsa tajuya ta kalli likitar tace "doctor me kuke jirana Baku saka mata jinin ba?" Likita tace "wallahi hajiya bamuda irin jininta, anje asiyo har yanzu basu dawo ba, group o gareta, jinin yana mana wahalar samu" Cikin 6acin rai tace "jini yana wahala kenan haka Zaku Barta tamutu mune da asara kenan?" Likitan tace "Hajiya Bahaka bane kiyi hakur...." Gyaran murya Huzaifa yayi yace "A a, Anty kiyi hakuri, zanbata, irin jinina ne" ya kalli doctor yace "muje lab din ku d'iba" ********************** ? ************************** ********** Ai Hausa Novels **************** *************************? ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ? ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ? ************************** Tafiya sukai,ya kwanta aka 'Debi jininsa, zasu gwada ko akwai wata cutar, tunani huzaifa yayi hakanma qarin wani 6ata lokacin ne, yafada musu su dauka kawai a saka mata, shi lafiyarsa kalau, haka ya kwanta aka Debi jininsa leda biyu, sannan taje ta daurawa Waheeda tareda allurar bacci, shikuma ya kwanta zuwa wani lokaci sannan yatashi yakoma Dakin da aka kwantar da Waheeda yaharde hannun sa a qirjinsa yana qare mata kallo, Sai yanzu nema yake sake ganin tsantsar kyanta, lokaci daya yaji sonta yana sake qaruwa acikin zuciyar sa, idan bai sameta ba, bayajin zai iya yin aure a rayuwar sa Sai dare sannan Waheeda taji Dama Dama aka sallameta tareda alqawarin hajiya Anty zataci gaba da dubata agida. har zuwa wannan lokacin Huzaifa yana Nan bai tafi ba, su 'yanbiyu Sai Kallan sa suke afakaice suna gulma ganin yanda yake komai nasa cikin aji da kamun Kai, saida sukaje gida lokacin karfe Tara nadare, sannan yayi musu sallama yatafi Washe gari da safe ya dawo dubata, babu laifi jikin Nata akwai sauqi sosai, har falo aka shigo dashi, ta zumbula hijab dinta tafita, kallanta yayi yace "Baby yajikin?" Wasa take da yatsun hannunta kanta aqasa tace "Alhamdulillah Yaya" Yatsina fuska yayi yace "Yaya Kuma Waheeda? No.. No... Banason sunan Nan, ki sauya min wani" Daga Masa Kai tayi, ledar dake hannun sa ya ajiye agabanta, yace "dazan taho ne nashiga super market namiki shopping, nasan bakinki babu dadi tunda rashin lafiya kikayi" Kanta yana qasa tace "to nagode" Dan qaramin murmushi yayi yace "Waheeda bazaki Kalle niba?" Dagowa tayi ta Kalle shi, Saitayi saurin sunkuyar da kanta qasa, sakamakon wani irin abu dataga yana futowa daga Idonsa yana shiga Nata, gabantane yafadi, harta kasa 6oyewa saida tasa hannunta a setin qirjinta, huzaifa yana ganin haka yayi tunanin ko jikin Nata ne yatashi, ahankali yace"sorry na tsaida ke, nasan kin gaji ko? " Hannunsa yasaka acikin aljihu ya Dauko wani zobe na gold me kyau, yamiqa mata tafin Hannunsa yace" Bani hannunki " Kallan sa tayi da mamaki, shikuma ya Dan daure fuska yace"bani mana" Ahankali tad'ora tafin hannunta akan nasa, yatsun hannun ya kalla Zara Zara dasu dogaye, akwai zoben gold a hannunta Wanda Babban Yaya yasiya musu, saiya cire shi yasaka mata nasa yace"wannan yafi kyau, karki cire shi"πŸ™ŠπŸ™†πŸ»β€β™€οΈ? Daga masa Kai tayi, ya dauki wayarsa yayi kira, Ana dauka taji yace "Momy ga Waheeda ku gaisa" Daga bangaren ta tace "to bata wayar" Waheeda yabawa wayar yace "ga momy na zaku gaisa" Waheeda ta karba suka gaisa da'ita cikin mutunci, sannan ta bashi wayar, shikuma yayi mata sallama yatafi Bayan sati daya Waheeda ta warke sosai, Hali ya dawo, tana waya da huzaifa dakuma Didat, saide har yanzu bata fada musu suturo ba, kwata kwata tama manta da maganar (idan kinsan baki biya littafin nanba kika karanta nabarki keda mahaliccinki) Daddy ne yasa Ummah tasake yimata maganar, haka ta zauna adaki tayi shiruuu abun duniya yafara yimata yawa,cikin sauri ta turawa huzaifa text, tayi masa maganar, Amma shiru bai turo mata amsa ba,tayi tunanin ko baiga text dinba ta kirashi ya dauka Amma saiya bata haquri cewa zai nemeta,har akai kwana biyu Didat bema kirata ba bare suyi maganar. Yauma kamar kullum tana daki a zaune tana aikin tunani, Maya ce tazo gidan suka hadu dasu yanbiyu suka shigo Dakin, Sai mita take musu basa son zuwa gidansu Zama sukai a Dakin Sai hira suke, Amma Waheeda tayi shiru, Maya ce ta kalleta tace "qawata meyafaru ne?" Waheeda tayi ajiyar zuciya tace "Daddy yasake min maganar auren Nan, na turawa Didat text yaturo iyayensa, Amma har yanzu banji yacemin komai ba" Wani irin yatsina fuska Maya tayi tace "Didat Kuma? Ke a ganinki wannan sonki yake? Kawai be'iya komai ba Sai kishi, dama Huzaifa kika Bawa Dama" Ihsan tace "ato fada mata de, danma bakiga yanda yake bane Maya, wallahi yahadu" Intisar tace "kuka Sani ko Didat din tafuso?" Waheeda ta murgud'awa intisar baki tace "waye yafada miki Ana mantawa da first lover?" Inti tace "to karki min rashin kunya, inde Didat ne keda shi, Ina soyaiya abinda kusan sati kikai a kwance babu lafiya Koya leqo qi, gashinan Huzaifa yazo, kije ki qarata da Didat d'in" Maya tace "Gaskiya Nima Ina ganin Gara Huzaifa, kawai ki share Didat d'innan kiza6o mana Huzy" Waheeda ta d'aga musu hannu tace "tonaji,kawai zanyi shawara da Babban Yaya" Ihsan tace "bakida Hankali Waheeda, kirasa dawa zakiyi maganar saurayin ki Sai Babban Yaya Dan raini?" "Bazanyi maganar dashi ba? Yanda yake yayanki Nima Yaya nane, in'aka bibiyama yafi sona a kanki" Ihsan tace "to kirashi, Wanda baiji Bari ba yaji hoho...." Maya tayi shiru tana wani tunani a ranta,addu'ah take a ranta Allah yasa tasamu amsar tambayar tunanin datake, cikin sauri tace "eh wallahi, kira Babban Yaya muji, shawarar tasama itace daidai" Tajuya ta kalli yanbiyu tace musu "koba haka ba?" Ihsan tace "hakane wallahi, Kuma a saka mana ita a hands-free" Waheeda ta dauki wayarta takira Babban Yaya, yana zaune ad'akinsa a lokacin yana tunanin kiranta, tunda tatafi rabonsa da'ita, yayi missed dinta sosai, ya jira ya jira kozaiga kiranta Amma shiru bata kiraba, yasan cewa idan ta kirashi tayi kewarsa ne, yana duba wayar yaga kiranta yana shigo wa, cikin sauri Yad'aga yace "Sai yau kenan" Yan biyu da Maya suka hada ido sukai murmushi kowa yayi shiru yana jira aji amsar Babban Yaya. Waheeda tayi murmushi tace "Babban Yaya wallahi inason kiranka, kayi hakuri" Yace "okay, Ina twice?" Tace "suna Nan kalau, suna falo, yauwa Babban Yaya kasan me? Daddy ne yace zaimin aure, nabashi hakuri yaqi ji, tunde laifin danayi wa Ummah , to nayi wa Didat magana naji shiru, shine nakeso kabani shawara ko in yiwa huzaifa magana... Huzaifa de ai kasan huzaifa, zaka sanshi ma, Dan gidan minister ne maici a yanzu... " Tunda tafara magana Babban Yaya ya runtse Idonsa, jiyake kamar ana watsa masa garwashi ajikinsa, ajiyar zuciya yayi yabude Idonsa, sannan yace"to Ina ruwana Kuma? Miye nawa aciki? Wato Waheeda na lura babu Wanda kika raina sama Dani duk cikin qanne na, nizaki kira kina fadamin hauka, saboda raini, wato ga sa'anki,ni karki sake kirana..... " ya qarasa maganar tareda kashe wayarsa, dama bashi tayi niyyar gaidawa ba? Bakira tayi dantaji muryarsa ba? Wata zuciyar tace dashi saboda samarin ta takira ka, idanunsa ne sukai jajir baisan lokacin da yaji hawaye yazubo masa ba, yasaka hannu ya hargitsa sumar Kansa,ya kalli wayar sannan yayi jifa da'ita ta had'u da bango ta tarwatse 1/28/22, 20:50 - Ummi TandamaπŸ˜‡: UD Ihsan da intisar ne suka kwashe da wata irin dariya, dariya suke suna nuna Waheeda da hannu,Waheeda takasa cemusu komai Sai kanta datake jinjinawa alamun gaskiya ne. Maya kuwa jijjiga kanta take ahankali tana sake gaskata tunanin ta akan Babban Yaya, haqiqa Dama ta dad'e tana wannan tunanin, Sai gashi yau ta tabbatar da abinda take zargi ** *** ** Hawayen Idonsa ya share, yayi shiru yafad'a duniyar tunani, Mutum d'aya ce tafad'o masa Arai,yasan idan ya kirata zaiji 'Dan Sanyi a ransa, babu 6ata lokaci ya d'auki wata wayar yayi Dialing number ta, bugu d'aya tad'auka muryarta can ciki, Shima cikin shagwa6a yace "Anty...." Hajiya Anty tace "Na'am d'an Ummah ya akayi" Cikin damuwa yace "banajin dad'i Anty , narasa meyake damuna..." ya qarasa maganar qwalla Nason taruwa a'idonsa Tashi tayi daga kwanciyar da tayi, cikin yanayin rashin lafiya tace "meyake damunka?" Cikin tashin Hankali yace "Anty ya naji muryarki haka? Lafiya kike kuwa?" Runtse idonta tayi tace "wallahi zazzabi nakeji Naufal, Amma nayi allura ma, nasan anjima zanji sauqi insha Allah, Ina Ummi? Kuna waya deko?" "Bama waya Anty, Amma zanyi mata magana yakamata tazo ta duba ki" Murmushi tayi "a a karka damu, karabu da'ita tahuta" "a a Anty dole zatazo taganki, please kikula da kanki, Sai anjima" yana fad'ar haka yakashe wayar tareda Dialing number ummi πŸ˜ƒ Tayi mamakin ganin Kiran Babban Yaya, har wayar takusa katsewa kasa d'auka tayi, saboda wani irin dad'i dataji Wai yau itace Big Brother yake kiranta, haqiqa tana d'aya daga cikin mata masu sa'a a duniya, cikin sauri ta d'auka tareda fad'in "Big Brother, My Husband to be ...." Runtse Idonsa yayi, jiyake kamar ta watsa masa ruwan zafi a qirji, Wai husband to be.... πŸ˜– Ajiyar zuciya yayi yace "Ummi... Anty nah batada lafiya, kisa lokaci kije kiganta" Yatsina fuska tayi tace "mene? Wai Dama ba kirana kayi domin kaji muryarta Kuma mu Tattauna akan batun auren mu ba?" Cikin 6acin rai yace "Duba lafiyar matar Nan yafimin komai ummi, idan kika d'auke mahaifiyata, duk duniya babu wadda nakeso sama da'ita" Cikin haushi ummi tace "to ai Kai kace, wannan a kanka kake magana, kaine kake sonta Bayan mahaifiyar ka, tunda aka had'ani dakai maganar arziqi bata ta6a shiga tsakanin muba, kawai sai yau Ina murna kakirani,babu tambayar lafiya ta babu komai shine zakace inje Inga wata mata, gaskiya bazaka takuramin ba,Kai Bama lalle naje ba...." ta qarasa maganar cikin rashin kunya Cikin masifa yace " muddin kikace bazaki mutunta iyayena ba,to bazan iya zama dake ba, ke ko wani daga cikin 'Yan gidan mu kikace bazaki mutunta ba, to babu dole, dama can banida ra'ayin auren yarinyar da banaso, inaso kisani dole akamin a kanki, danhaka bazaki samun ciwon Kai ba...."dif yakashe wayarsa Ummi ta qulu iya quluwa, Sai huci take tana hura hanci, inbanda tana so duniya tasan ta'auri mutum mashahuri babu abinda zaisa ta tsaya wannan gayen yana fad'a mata baqar magana, badan taso ba, haka ta shirya ta nufi gidan Hajiya Anty. Tunda suke unguwa d'aya bata ta6a shiga gidan ba, Sai yau, lokacin data qarasa megadi yatare ta yana tambayar ta wajan wa tazo, cikin Isa da gadara ta fad'a masa cewa itace matar da Naufal zai aura, cikin girmamawa megadi yabud'e mata gidan tashiga Duk irin shigar da tayi ta alfarma tana ganin hajiya Anty a hakimce afalo duk Sai taji ta raina kanta, saida tagama qarewa hajiya Anty kallo taga mace har mace ga kyau ga kwalliya, ga Kuma irin daular datake ciki, saita yatsina fuska sannan tace "Sannu yajikin?" Hajiya Anty tana kallon ta, duk taga abinda tamata,babu maganar gaisuwa kawai sai sannu πŸ˜’, Saita shareta ba tace mata komai ba Saima murmushi da tayi tace "A a kice yau amare ne a gidan namu, sannu da Zuwa Daughter" Ummi ta kalli hajiya Anty asheqe, Wai Daughter, matarda ko haihuwa bata ta6a yiba itace zata kalleta qatuwar budurwa da'ita tace mata Daughter 😏 Saitayi yaqe ta kawar dakai, Hajiya Anty tatashi takawo mata ruwa da lemuka, sannan tayi kitchen takawo mata kaji cikin flet, babu musu ummi ta zage ta dinga cin kajin Nan saida taji tayi qat, sannan tayi mata sallama tatafi,Hajiya Anty tabita da kallo, babu Allah yasawaqe babu komai kawai cikinta yana cika taqara gaba, kwata kwata babu alamar Hankali a wajan yarinyar, babu kunya ko kara atare da'ita, ajiyar zuciya tayi a fili tace "Allah yabasu Zaman lafiya" Sannan ta d'auki wayarta takira Babban Yaya, yana d'auka tace "Ummi tazo, kakirata kamata godia" "ashe tazo" abinda yace kenan, domin beyi tunanin zatazo dinba Tace "tazo wallahi, yanzu tatafi, nayi tunanin ma anan zata wuni, Amma duk da haka naji dad'i sosai, Allah yamuku Albarka Allah yahad'e kanku" Memakon yace Amin, saiyace "Anty inada aiki yanzu, akwai horar war da'ake mana, zan kashe waya" Murmushi tayi tace "yakamata kazo kaga lefen Nan, idan akwai abinda baiyi maba, Sai a sauya, sannan nace ka tambayeta size d'inta na pant da bra, Shima har yanzu bakace min komai ba" Cikin shagwa6a yace "Anty zanzo... Shikkenan?" Tace "eh, shikkenan" daga haka, sukai sallama Wayar Ummah ce kange a kunnan ta, tana zaune afalo tana waya dashi cikin nutsuwa, tun Bayan da Babban Yaya yawatsa mata qasa a'ido yanbiyu suka mata dariya, bata sake bi takansa ba, ta nutsu ta ajiye Didat agefe, takama Huzaifa πŸ˜ƒ Huzaifa yasake lanqwashe muryarsa yace "Waheeda bazaki Bani Dama naturo iyayena gidanku ba? Kinsan kuwa yanda na matsu naganki a gidana?" Murmushi tayi ta dauki cup din dake gabanta me cikeda fresh milk tayi sipping sannan tace "idan lokaci yayi ai zan baka damar, saurin me kake?" Dariya yayi yace "Me kikeci?" Tace "Madara ce, ko zaka Sha?" Daga d'ayan bangaren Huzaifa yace "banashan madara, idan Nasha wahala take Bani da daddare, Saide inzaki Bani da hannunki saina sha..." Kunya ce takama Waheeda, tasaka hannu tarufe fuskarta kamar yana ganin ta πŸ™ˆ Uncle Usman ne yashigo falon yazo wajan Daddy, yaga yarinya Sai rufe fuska take ita kadai, ga Kuma waya a kunnan ta tanata murmushi Qarasowa falon yayi cikin sigar tsokana yace "anata wayar ne Waheeda? Kode da sirikin nawa kike waya?" Waheeda tayi sauri ta kashe wayar, sannan cikin kunya tace "Uncle Huzaifa ne..." tana fada masa haka, tashige dakinsu cikin kunya Uncle Usman ya qarasa Dakin Daddy Bayan sun gama abinda zasuyi, Uncle Usman yace "Yaya yakamata fa Yaron Nan Huzaifa idan da gaske yake yaturo,inda zai iyu da anhada bikin Waheeda Dana Naufal" Daddy yace "Eh da munji dadin hakan gaskiya, Bari zanyi magana da mahaifin sa, tunda Naga yanzu ta bashi Dama yana zuwa zance a koda yaushe nasan sun dedeta, zanyi magana da mahaifin sa, Saisuzo ayi magana kawai" Kamar yanda suka yanke wannan shawarar kuwa, haka akayi, cikin satin iyayen Huzaifa suka zo neman aure, Daddy da Uncle Usman da baba Habu sukace sun basu πŸ˜₯πŸ€— Waheeda dataji wannan labarin bata damu ba, asali ma murna taitayi cikin ranta, saboda har aqasan ranta tanajin soyaiyar Huzaifa, tana sonsa sosai, idan ta zauna ta dinga tunanin sa kenan, shiyasa tadauki zuciyarta gaba daya ta damqa ta ahannunsa ** *** ** A kwatuna ne a shirye daya kan daya guda goma Sha biyu masu launin brown Minister ne a tsaye yana kokarin Kiran waya, tsaki yayi ya zauna tare da fadin "inaga babu network ne, tun dazu nake gwadawa Amma taqi tafiya, ai Gara afada musu lefe yahadu, yaushe suke ganin yadace akawo musu?" Hajiya Babba mahaifiyar Huzaifa, tajuya ta kalli huzaifa dayake Sanye cikin kayan shan iska, yana danna laptop din gabansa, tasake juyawa ta kalli minister tace" yanzu Alhaji baka ganin wannan kayan sunyi yawa? Ina laifin ma a kwatuna hudu ko biyar? " Kallan ta yayi yace" kinsan me kike fada kuwa? Kinsan matsayina awannan jihar kuwa? A kwatuna shabiyu ai sunyi kadan hajiya, ko bakisan gidan da za'a Kai bane? " Cikin 6acin rai tace" nasani mana Alhaji, ba gidan buzayen Nan bane? Ni kwata kwata yarinyar Nan bata minba, kana ganinta daga ita har yan'uwan Nata kasan irin sadaka yallar Nan ne..., duk abi a rabaka da danka ta hanyar asiri "β˜ΉοΈπŸ˜” Huzaifa ya kalleta yace" Momy.... Ni inason Waheeda, Kuma gaskiya bazan iya barinta ba " Minister yayi Dariya yace"to kinji, Kuma nikaina nasan idan Huzaifa ya auri yarinyar Nan zan samu jikoki kyawawa... Kisawa yaro Albarka kawai acikin auren sa" Hajiya Babba takama jijjiga kafarta, ranta in yayi dubu ta ya6abaci.... Daga Dan har uban haka suka qyaleta, minister yaci gaba da neman number Daddy ** *** ** Washe gari karfe Tara nasafe, a Nigerian tayi masa,Kai tsaye wajan shopping yaje yasiyo panties da Bra, lokacin dazai za6a tunani yake wanne size zai d'auka mata? Shide bai ta6a ganinta azahiri ba,bare yayi hasashe ya d'auka mata Kuma pant da Brezia babu size din wadda yasani saina Waheeda, danhaka batare da tunanin komai ba ya 'Dauko mata daidai size din Waheeda πŸ™†πŸ»β€β™€οΈ? kasancewar sa mutum na mutane bai samu zuwa gidan Hajiya Anty ba, Sai karfe goma Sha shad'aya, Kai tsaye gidan yashiga, kasancewar tana takura masa da waya yazo yaga lefe, yasan cewa idan ya wuce gidansu baizo yaga lefe ba, to zata dinga yimasa Mita ne, shiyasa Kai tsaye ya wuce gidan Nata, maigadi Sai washe masa haqora yake yana kwasar gaisuwa, saida yayi masa yayyafin kudi sannan yabarshi yasamu ganawa da Antyn nasa. Gabansa tacika da kayan break fast, Sai Nan Nan take dashi kamar zata saka shi ajikinta, waya yake amsa wa cikin farinciki, yau yana jin wannan zuwan nasa na musanman ne, tunda har yazo Nigeria dan rad'in Kansa ba fitinar Waheeda ce ta kawo shi ba πŸ˜ƒ Yana ajiye waya, wata wayar tasake shigo wa, Kuma gaba d'ayansu masoyansa ne, tun yana amsawa harya fara gajiya, Amma duk da haka bai fasa d'aukar wayar masoyan nasa ba, saida Hajiya Anty taga abin nasa Bana qare bane, kawai saita kwashe wayoyin ta kashe su, sannan tafara bashi break fast din da kanta, saida yaci yaqoshi sannan tajashi zuwa wani d'aki, photunan Waheeda ne birjik acikin Dakin, saikuma na Babban Yaya dasu Sa'eed, saikuma na dukansu yaran gidan dasuka had'u suka d'auka tace "toga kayan lefenka..." A kwatunan ya kalla guda ashirin da hud'u, ya kawarda da Kansa yace "nagani, sunyi" Cikin mamaki ta Kalle shi tace "tayaya kasan sunyi Bayan ko bud'ewa bakayi ka Gani ba?" Kallan inners d'in daya kawo tayi tace "sannan wannan kayan daka siyo sunyi wa ummi yawa, na ganta ai rannan, wannan bra din tamata yawa, bansan de pant d'inba, kaida nace ka tambayeta size dinta meyasa zaka siyo?" "ai itace tace haka ne size din Nata" ya qarasa maganar cikin d'aure fuska Hajiya Anty tace "to shikkenan, zanyi magana da ummanku, Sai muji ranar daza'a saka akai musu kayan" Yana jin ta d'auko hanyar maganar auren sa, ransa yaqara 6aci, babu shiri yayi mata sallama yabar gidan yanufi gidansu. Tun abakin get mutane suka masa cincirundo, Sa'ad da Sa'eed suka tar6eshi suka qaraso gidan, Ummah bakinta Qin rufuwa yayi, babu Wanda yayi tunanin zuwansa, Sai gashi ya basu mamaki yazo, Ummah ta Kalle shi duk farinciki ya cikata, ganin yanda yasaki ransa tasan cewa may be ya yarda da auran ne tace " 'Dana,me zakaci? Me kakeso nayi ma?" Kallan ta yayi,yayi murmushi dimple d'insa ya lotsa, su yanbiyu da Waheeda Sai dariya suke musu shida Ummah, ganin yanda duk ta rikice ganin Babban Yaya kamar sudin ba sauran yaranta bane, kafin Babban Yaya yayi magana Daddy ya kalleta yace"haba Hajiya,Naga alama yakamata nadinga tuna miki cewa Naufal bashine auta ba " Waheeda ta turo Dan qaramin bakinta gaba tace"Bayan Ummah tafi sonshi Dani" Ummah ta kalli Waheeda ta kalli Babban Yaya tace "rabu dasu Dana, me zakaci nadafa ma dakaina? Karka damu da surutun su Dama can kishi suke dakai" Fuskarta yakama yariqe yace "Ummah tah ta kaina, inason ki Ummah, naci abinci a gidan Anty, can nafara zuwa Naga Kaya, karki damu kanki, banajin yunwa, anjima de keda kanki Zaki Bani abinci da wannan hannun naki" ya qarasa maganar yana kissing hannunta, Ummah ta kalli Daddy alamun bata gamsu da maganar da Babban Yaya yafad'a mata ba, Daddy yace "yace miki ya qoshi hajiya,ai yana Nan a gidan babu inda zaije, anjima saiki bashi abincin" Sai a sannan Hankalinta ya kwanta, ta kalli Naufal dayake Kallan ta cikin murmushi tace "to shikkenan, kaje daki ka kwanta ka huta, Kuma ka kashe wayoyinka kajiko" Yace "to Ummah nah" daga Nan yatashi yayi dakinsa, Waheeda ta kalli brief case dinsa daya manta bai tafi da'ita ba, tasan Kuma kudi ne aciki, idanuwanta Tajuya, tana fatan ace yabata ko 50k ne, cikin sauri ta dauki jakar tabi bayansa Tana shiga 'Dakin ta ganshi yana kokarin cire Kambos d'in kafarsa, Kallan ta yayi ba tare daya Dena abinda yake ba, cikin murna dajin dadin ganinsa tayi saurin qarasa wa wajan sa ta ajiye Brief case din akusa dashi tace "Babban Yaya ga kud'in ka" πŸ˜ƒ Murmushi yayi, ya kalleta yace "kud'i na kuma? Waya fad'a miki kud'i ne aciki?" Hannun sa takama tacire daga kan takalmin nasa dayake so yacire, ta qarasa cire masa takalmin kamar wani mijinta, sannan tacire masa safar tana cusata cikin takalmin, takama dogayen yatsun kafarsa masu laushi tanaja ahankali sannan tace "ai nasan kudi ne aciki, Dan Allah Babban Yaya ka temaka kabani kudi ko dubu hamsin ne" Ba tareda tunanin komai ba yace "bude ki d'auka" Kafarsa tasaki tabud'e jakar, da daloli tayi tozali, cikin mamaki ta d'ago ta Kalle shi tace "Kai kai Babban Yaya ashe kudin ne aciki? Allah jinake ba kudi bane, kawai fad'a nayi" tafad'i hakan tana rufe jakar, sannan tatashi Takoma kan gadon ta zauna kusa dashi Babban Yaya ya kalleta yace "ki d'auka duka nabaki" Cikin mamaki tace "me? Wai kudin?" Yace "Emana, kid'auka nabaki" Kanta ne ya d'aure tace "Babban Yaya, daloli ne fa aciki, me zanyi dasu?" Juyowa yayi yana fuskantar ta, yace "tome kike so? Idan kud'in kike so kitafi dashi, saiki saka cikin account dinki" Murmushi tayi, dimple dinta yafuto kamar nasa tace "Babban Yaya kana magana kamar ranka a6ace, please kasaki ranka mana" Murmushi ne ya qwace masa ba tareda shirya ba, yace "naji, tashi kibani waje, Ummah nah tace na kwanta nahuta" Bakinta ta turo gaba, cikin shagwa6a tace "Babban Yaya Dan Allah mu 'Dauko anko? Wallahi Dama kud'in danace inaso d'in sonake naje kasuwa mu 'Dauko anko" Dariya ce ta kamashi yace "kuma anko da dubu Hamsin?Bari kiji, babu wani anko da zakuyi, tunda bason auren nake ba, Kuma ta shafeku" Tace "Dan Allah Babban Yaya kaji, wallahi muna so, Dan Allah muyi? To wai Kai meyasa baka son auren?" Cikin damuwa yace "nafad'a miki Bana burin zama da wadda banaso, karki sake min wannan tambayar, Sai me Kuma kike so Bayan wannan?" Lallausan Hannun sa takama tariqe cikin Nata, Kallan ta yayi cikeda mamaki ya kasa magana haka Kuma ya kasa qwace hannun sa, cikin nutsuwa tafara yimasa magana tace"nikam ai nagama samun abinda nakeso a rayuwa Babban Yaya, iyayena suna sona, Babban Yayanmu yana sona, sannan Huzaifa yana sona, Bana tunanin komai akansa, nasan ko Bayan munyi aure zai riqeni Amana kamar Babban Yayanah, saide Kuma naso ace nasamu me kama dakai Babban Yaya" Gabansa ne yake Dukan Tara Tara, tunda tafara yimasa wannan maganar, kwata kwata yafita haiyacinsa, zuciyar sa ce take zigashi akan yafad'a mata komai, karyayi wasa da damar sa, karya Bari abinda yadad'e yanaso yakufce masa Cikin sauri kamar Wanda aka mintsineshi yace "koda nine....?" Kallan idanunsa tayi, cikin rashin fahimta tace "kamarya?" Shima Kallan qwayar idonnata yayi yace "Zaki iya auren me kama Dani, meyasa ni bazaki aure niba....?" Kuyi hakuri Dan Allah πŸ™πŸ»πŸ™πŸ» 1/28/22, 20:50 - Ummi TandamaπŸ˜‡: SM BB Cikin sauri ta d'ago ta Kalle shi, tsananin mamakin abinda yayan Nata yafad'a ne yasa takasa rufe bakinta, gabanta yafara fad'uwa ganin yanda fuskarsa ta nuna kamar da gaske yake, wata zuciyar tace da ita ke mahaukaciya ce? Tayaya hakan zata faru tsakanin ku?yayanki uwa d'aya uba d'aya tayaya? Dariya ta kwashe da'ita tace "Babban Yaya aure Kuma? Tayaya? Tayaya zan aure ka? Please Mekake so kace? Nasan inajin sonka acikin raina fiyeda yanda nake jin huzaifa acikin zuciyata, saboda Babban Yaya ubane, Kuma ba'a sauya uba,shi kuwa Miji Ana sauya shi" Kansane yasara har saida yariqe goshinsa, lokaci d'aya ya dawo cikin haiyacinsa, yatuna irin kato6arar da yayi, cikin sauri yace "lokaci ya quremin, Sorry....kuje kuyi ankon tunda Kuna so, tashi kije" Cikin murna Waheeda ta rungume shi tareda manna masa kiss agoshi, tafice daga d'akin Tana fita yazube akan gadon nasa, duk yanda yake jin dad'i idan jikinsu yahad'u yau baiji komai ba kasancewar yasan cewa akwai Babban aiki a gabansa, idan yarinyar ta amince da auren sama Tofa bata sonsa, soyaiyar jini take masa,ba soyaiya ta masoyi da masoyiya ba wani irin huci yayi yafitar da iska daga bakinsa,kwanciyar da baiyi ba kenan, ya wuce toilet duk da safiya ce, ya d'auro alwala yafara kaiwa ubangiji kukansa. Washe gari da safe Bayan sun gama break fast, compound suka fita buga ball, kowa yana Nan banda Waheeda data tafi makaranta Sun dad'e sunayi sannan suka koma ciki, abinci sukaci kowa yakama harkar gabansa, Babban Yaya kuwa shirya wa yayi zaije wajan abokinsa mashkur, Wanda Dama can shine de abokinsa guda daya, sun dad'e tare, hatta 6angaren sana'ah ma Shima mashkur ball yake bugawa, saide kowa da Club d'insa, Amma duk a England suke rayuwar su, yana barin d'akinsa anan falo yaga baqi maqota suna shigowa gidan nasu, Sai a lokacin Ummah take fad'a masa kayan lefen Waheeda ne za'a kawo, ba qaramin kokari yayi ba wajan saita Kansa, daga qarshe yafice yabar gidan, domin kuwa abubuwan qara ta6ar6are masa suke πŸ˜– Baidawo gidan ba saida yamma, a lokacin baqi Wanda sukazo aka kar6i Kaya dasu suntafi, daga Sa'ad da Sa'eed Sai 'yanbiyu da Hajiya Anty da Ummah ne a falon, ga akwatunan Nan agefe hajiya Anty tana duba kayan da aka zuba aciki, Sai kuma uwar gayya wato Waheeda tana zaune kusa da Hajiya Anty tana shan tea da waya a hannun ta tana karanta saqon Huzaifa Sai murmushi take, gabansa ne yafad'i, ganin da gaske de ankawo kayan lefen Nata, lokaci d'aya ransa yayi baqiqqirin Shigowa falon yayi duk da yanda yake ganin duhu-duhu kamar Idonsa yana son rufewa πŸ™†πŸ»β€β™€οΈ? Adede lokacin daya qaraso tsakiyar falon yaji hajiya Anty tana cewa "Hajiya yaushe zamu saka rana akai na Naufal ne? Tunda sunbar mana komai a hannun mu ai yakamata mukai musu kokuwa?" Cikin sauri yayi hanyar d'akinsa, Babu Wanda ya lura da yanayin sa Sai hajiya Anty, ta Kalleshi cikin tsananin mamaki, yashigo falo babu Wanda yayiwa magana Kuma ya wuce cikin d'akinsa da wannan sauri haka,tasake juyawa ta kalli Waheeda, kanta ta jijjiga tareda cizon lips d'inta, yau d'aya de yakamata ace tayi wani abu akan wad'anan 'ya'yan nata a matsayin ta na uwa 😳(tofa) Kallan Waheeda tasake yi, tana jin qaunarta acikin zuciyarta, koda wasa bata son abinda zai ta6a lafiyarta balle yasaka ta cikin wani Hali, Amma Yaya zatayi.....? Ahankali tatashi tabi Bayan Naufal, tana tura kofar 'Dakin tana shiga ta ganshi a tsaye yana Kallan p.o.p din d'akin, Kansa ne yaji yasara lokaci d'aya jiri ya d'ebeshi zai fad'i, cikin sauri hajiya Anty ta qarasa tatareshi yafad'o kanta "subhanallah....Naufal lafiyarka kuwa?" Idonsa ya runtse, yasaka hannu yadafe goshinsa, but kwata kwata yakasa magana, janyo shi tayi ta kwantar dashi akan gadon, itama ta zauna sannan tad'ora Kansa akan cinyarta Lallausar sumar Kansa take shafawa, saida taji yad'an nutsu sannan tasake tambayar sa "meyake damunka?" Hawaye ne yafuto daga idanunsa, mamaki yakama hajiya Anty, Naufal ne da Kuka yau? πŸ€” Tun yana hawaye harya dawo yana kuka harda shashsheka,bata hanashi ba, rabuwa tayi dashi bata hanashi ba, saida yayi me isarsa, sannan yayi shiru Sai Jan zuciya yake, ajiyar zuciya tayi akaro na biyu tace "meyake damunka?" Cikin rawar murya tamkar ba Babban Yaya ba, yace "Allah idan na rasata mutuwa zanyi....." Gaban Hajiya Anty yayi wata irin fad'uwa, cikin sauri ta Kalleshi tace "what....? Wacece?" Sai a lokacin Babban Yaya yatuna abinda yafad'a, hawaye ne yazubo masa, Sannan yace "Anty ni bazan iya rayuwa da wadda banaso ba, bazan iya Zaman aure da'ita ba...." Ajiyar zuciya tayi, Amma maganar sa ta farko Sai yawo take mata acikin qwaqwalwarta, karfa tunaninta ya zama gaskiya.....idan hakan ta tabbata Yaya zasuyi da wannan tsohon al'amarin da wannan Yaron yake son tado musu shi? Kallan sa tayi tace "shine damuwar?" Kasa magana yayi, Sai Kansa daya d'aga mata kawai Tace "to shikkenan, zan samu ummanku muyi magana da'ita, ka kwantar da hankalin ka banason wannan kukan" Sake d'aga mata Kai yayi, Ajiyar zuciya tayi, sannan ta rungume shi sosai ajikinta, ta sunkuya tayi kissing goshinsa, sannan tad'ora masa Kansa akan Fillo tafita daga d'akin Tana futowa daga d'akin taga yaran basa Nan,Sai Ummah kad'ai tana kallo, godia tayi wa Allah cikin ranta, sannan ta qarasa wajan ta tace "Yaya a Kwai matsala fa, nasamu yayansu yanzu, maganar gaskiya baya son auren Nan har yanzu" Cikin tsananin damuwa Ummah tadafe kanta πŸ€¦πŸ»β€β™€οΈ?"nashiga ukuna,Yaya zanyi da wannan Yaron ne, banaso Naga Naufal cikin damuwa, Bari inje in sameshi...." tafad'i haka tana kokarin tashi Cikin sauri hajiya Anty tace "Zauna Yaya, Wai meyasa bazaku zaunar da Yaron Nan yafad'a muku wadda yake so ba?" Ummah ta kalleta cikin damuwa tace "to inda zai fad'i wadda yakeso d'in ai zanji dad'i Nima...., idan an tambayeshi fa cewa yake shi har yanzu babu wadda yakeso, ayi namiji baligi Amma ace kullum babu wadda yakeso?" Anty tace "to yanzu ya za'ayi?" Cikin damuwa Ummah tace "tunda ke yafara sakewa dake har yana fad'a miki damuwar sa, kifad'a masa zai iya qarawa da yarinyar dayake so d'in, yanzu su Alhaji sun Riga sunyi magana tayaya zamu ce a banje wannan auren mu maida su qananan mutane?" Hajiya Anty tace "Eh hakane Kuma, tunda yanada damar dazai iya qara auren shikkenan, Allah ya tabbatar musu da Alkhairi, Allah ya basu Zaman lafiya Kuma" Ummah ta jijjiga kanta kad'an, ba tareda tace komai ba. Bayan kwana biyu aka shirya aka Kai lefen Babban Yaya,su Daddy sunyi magana da iyayen kowa daga cikin su, Ummi dakuma Huzaifa, danhaka aka tsaida date din 'Daurin aure sati hud'u masu zuwa😒 Su kuma su Sa'ad da Sa'eed aka tsaida nasu bikin Bayan shekara d'aya πŸ‘ŒπŸ» Yau duk suna zaune afalo gaba d'ayansu,yana jin yanda intisar take cewa "akai musu wannan uban kayan Amma abada tukwicin dubu ashirin?"πŸ€” Ihsan tace "ai sai kiyi tayi, kanki akeji, tunda sude bazasu qara komai ba, ni dazu danahau Instagram ma kayan nagani anata turawa, mutane Sai cewa suke anyi almubazzaranci dayawa, Kuma nasan Yan gidan sune suka saka kayan a internet" Babban Yaya Ko Kallan su baiyi ba,bare ya tanka, yasan suna magana ne akan 'Yan gidansu ummi, wayarsa ce ahannunsa yana Kallan pictures din Waheeda, wasu tun tana zama, wani Kuma ahannunsa take yana bata fida tana Sha, wani Kuma tana cikin baho yana mata wanka, wani Kuma yad'agata sama yana kissing Kumatunta, a lokacin tafuto daga d'akinsu wayar Ummah tana hannunta, Kai tsaye wajan sa ta nufa ta zauna, yana ganin ta yayi saurin rufe wayarsa kartaga abinda yake Gani, wayar Ummah ce tasake qara, cikin 6acin rai ta dauka tace "Wai Dan Allah Didat mekake so nama? Nafad'ama gaskiya kadena kirana anriga ankawo kayan aure na" Daga d'ayan bangaren Didat yace "wallahi Waheeda idan kika kuskura kika auri wani baniba wallahi saikin kashe auren kin futo kin aure ni...." Cikin 6acin rai tace "au haka kace?" "eh haka nace, Dan renin hankali kince min Inturo iyayena baki tsaya kinji abinda zan fad'a miki ba kawai saiki cemin yanzu ankawo miki kayan aure.... A a, sadaki aka kawo miki ba Kaya ba, wallahi idan kika yarda aka miki aure da wanina dagani harke Sai ran kowa ya6abaci " Dif... Yakashe wayarsa Waheeda tasaki tsaki ba tareda tace komai ba, tajuya ta kalli Babban Yaya har zata masa magana saitaga ya daure fuska, dolenta taja bakinta tayi shiru 😬 Da daddare abokinsa mashkur yazo,zaune suke akan had'ad'd'iyar motar Mashkur din, wadda yayi parking dinta a compound din gidan, mashkur 'Dan Gayu ne na gaske, akwai d'aukar wanka tamkar Babban Yaya, Ihsan ce ta kawo musu lemuka ta ajiye akan 'Dan qaramin wani dinning table dake gabansu,ta gaida mashkur sannan tajuya, har tayi Nisa Idonsa yana kanta, bata dad'e da tafiya ba intisar takawo musu cups, cikin mamaki ya kalleta yace "kaiii, Wai daga shigar ki har kika sauya Kaya kika futo?"πŸ€” Murmushi tayi tace "a a, Bani bace, Ihsan ce dazun" Murmushi yayi tareda shafa qeyarsa,intisar tajuya tatafi, mashkur ya dubi Babban Yaya yace "tsakani da Allah kunada wannan kyawawan yanmatan Amma kabarni Ina shan wahalar neman matar Aure? Gaskiya Allah yamuku kyau Abokina, Wannan kyanta ace zan'iya had'asu duk su biyun, da lokaci d'aya zanyi wuf dasu" Babban Yaya ya Kalle shi yace "banason is'kanci mashkur...." Mashkur ya d'auki lemo guda d'aya ya tsiyaya acikin cup sannan yace "to na tambaye ka meyakamata mu tsara na bikin kaqi cewa komai, to bagara inyi abinda ya shafeni ba, Kai kasamu matar ne shiyasa kake mana is'kanci, nikuwa Sai yanzu nagani, Dan Allah Bro wannan ta farkon datazo, Ina ciki...." Babban Yaya yayi ajiyar zuciya, cikin ransa yafara godewa Allah daba Waheeda ce takawo musu lemon ba 🀣 Yatsani yaji wani namijin yana cewa yana sonta Ya kalli mashkur yace"ni bazaka Jamin raini awajansu ba, kamusu magana da kanka, sannan babu abinda zamu tsara, ayi bikin haka, mashkur inaji araina matsawar narasa yarinyar danake so, to wallahi mutuwa zanyi...." Mashkur dayakai cup din lemo bakinsa cikin sauri yafasa Sha ya ajiye, sannan ya Kalle shi da mamaki yace"kasan mekake fad'a kuwa Naufal?" "yes, bazan iya daina sonta ba" Mashkur yace "wacce me sa'ar ce wannan? Why not kafad'a mata? Mekake jira?" Babban Yaya yace "lokaci yaqure min mashkur, bazan iya fad'a mata ba, Amma wani bangaren inaji ajikina ita d'in tawa ce" Cikin sanyin jiki mashkur ya bubbuga kafad'arsa, yace "kayi hakuri Abokina, yanzu meka yanke akan hakan? Wanne irin mataki ka d'auka?" Cikin damuwa yace "band'auki kowanne mataki ba, kawai Ina addu'ah de..." "no, hakan ai yayi kad'an Friend, saura sati hud'u bikinka fa, kamata yayi mushirya muje Saudia, Nima zan tayaka da addu'ah Allah yabaka za6inka, idan har zai kasance alkhairi agareka, idan Kuma ba alkhairi bane Allah yabaka haquri da juriya akan rashinta " Ransa duk adagule ya kalli mashkur yace "mashkur lokaci yariga yaquremin.... Itama aure zatayi, tayaya za'a fasa dawani ayi Dani? Tayaya zan rabu da wannan nacacciyar yarinyar ummi? Wallahi haushin ta nakeji, idan ta kuskura ta aure ni ko.... Wallahi saina mata filla-filla aranar da aka kawota kuma da niyya" Mashkur ya kwashe da wata irin dariya sannan yace "Abokina bakada Dama wallahi, kadena wannan tunanin, kasa aranka zaka yarda da qaddara mekyau ko marar kyau, sannan karka manta komai yayi zafi maganin sa Allah, a lokacin daka shiga cikin matsala kadinga tunawa cewa akwai Allah.... Saboda haka yanzu ma shi zamu kaiwa kukan mu, me muke yanzu a qasar? Mushirya gobe mutafi Saudia, daga Nan kawai muwuce England.... " Sai a lokacin Babban Yaya yasaki wata irin ajiyar zuciya, yace " nagode Friend" cikin farinciki suka rungume juna Washe gari karfe goma a compound tayiwa Babban Yaya, sunyi waya da mashkur zasu had'u a Airport, Waheeda da Yanbiyu ne suka rakoshi har wajan motar dazai shiga, wayar Ummah tana hannun Waheeda, Huzaifa ne ya kirata cikin murna ta d'auka tafara masa magana Sai wani kashe murya take.... Babban Yaya yabude motar zai shiga ya kalleta yace "mahaukaciya..." 🀣 Yanbiyu sunji abinda yace, sunsan cewa akusa yake, danhaka sukai murmushi suka juya ciki Waheeda ta katse wayar sannan ta Kalle shi tace "Babban Yaya mekace?" Cikin 6acin rai yace "bansani ba" Jikinta ne yayi Sanyi, ta qarasa wajan sa tace "nayi laifi ne Babban Yaya? Kayi hakuri...." Fasa shiga motar yayi, yafuto tareda d'ora hannun sa akan murfin motar, cikin masifa yace "au tambaya tama kike me kikayi? Kullum kina liqewa mutum saikace kaska, kwata kwata baki iya Jan aji ba, to Bari kiji, namiji tsanar mace me naci yake, marar aikin yi kawai..." Kukane yakama Waheeda, ita tarasa meta masa tun ranar da aka kawo lefen ta yake daure mata fuska,komai tayi saiya dinga Jin haushinta, bata iya haqura ba saida ta rushe da Kuka Sannan tayi cikin gidan da gudu Tsaki yasaki yanajin haushin zuciyar sa Kuma, Dan me zaisa Waheeda kuka? 🀣Yanzu haka kukan ma ya haddasa mata ciwon Kai, wani tsakin yasake saki, yarufe motar zaibi Bayan ta, domin yabata haquri "Salamu Alaikum" Juyawa yayi yaga meyi masa sallama, budurwa ce Babba, wankan tarwad'a, tanada tsayi had'eda jiki, saide babu alamun kyau atare da'ita, hannunta d'aukeda wani flask d'in abinci,Kallan rashin Sani yayi mata, beyi mata magana ba yajuya zaiyi cikin gida Cikin sauri Tariqo rigarsa tace "Husband baka ganni bane?" Cak! Yaja ya tsaya a'inda yake, sannan ya Juyo cikin nutsuwa yacire hannunta data riqe masa Riga, ya kalli idonta yace "Dama kece?" Ummi tayi farrrr da idonta, cikin yanga tace "nice, meyafaru ne Naga kamar kana cikin 6acin rai? To kayi hakuri ga girkina nakawo ma da hannu na nayishi, idan Kaci zakaji dadi" Cikin tsananin 6acin rai yanunata da hannu yace "Ummi!!!, kidena damuna, kidena shiga cikin rayuwa ta, waike Ana so dole ne? Sau nawa zan fad'a miki Bana ra'ayin ki? Ba girki ba, ko kanki Zaki Bani bazanyi ra'ayin ki ba" Cikin rashin kunya tace "qarya kake wallahi, Kai d'in wa? Dazaka dinga fadamin baqar magana, cemaka akai ni dinma sonka nake? Inaso na aure ka ne saboda duniya tasan cewa eh Nima na auri mashahurin mutum, Naga alama bakasan darajar mace ba, Amma duk lokacin daka aureni saina koyama yanda ake...... " Cikin 6acin rai yakai hannu zai wanketa da Mari tareda wata irin tsawa yace"Ummi!!!" Tsananin tsoro ummi ta tsorata da yana yinsa,jikinta ya d'auki rawa batasan lokacin da flask din hannunta yafad'i qasa ba, jallop rice din ciki ta zubeπŸ˜‚ Idanunsa harsun sauya Kala sun koma ja saboda 6acin rai, cikin sauri Hajiya Anty taqaraso wajan su tariqe hannunsa, shigowarta kenan gidan, ta tarar da wannan drama, cikin 6acin rai ta Kalle shi tace "Duka Kuma Naufal....?" Yanda yaji tafad'i kalmar duka d'in kamar zatayi kuka duk Sai jikinsa yayi Sanyi, Amma sai huci yake, tunda yake ba'a ta6a yimasa rashin kunya kamar yanda ummi tamasa ba yau, Hajiya Anty ta maida Kallan ta wajan Ummi tace "kiyi hakuri, d'auki flask d'inki kitafi" Ummi ta tsugunna ta d'auka, sannan ta d'ago ta kalli Hajiya Anty sannan tasakar mata tsaki, ta wuce tabar gidan Babban Yaya yana ganin abinda Ummi tayiwa Hajiya Anty yabi Bayan ta zai damqo ta, Hajiya Anty ganin yabi Bayan ummi tasan tsaf zai lakad'a mata duka, Dan haka cikin sauri ta ruqoshi, tace "karabu da'ita nace" "Amma Anty... Kina.... Kina ganin abinda tamiki fa..." Yafad'i maganar a rarrabe cikeda qunan rai Murmushi tayi tace "naji, karabu da'ita" Jijjiga Kansa yayi, sannan yashiga motar sa yamata key yabar gidan,wajan Waheedan ma fasa zuwa yayi πŸ€— πŸ˜‡πŸ˜‡πŸ˜‡ 1/28/22, 20:51 - Ummi TandamaπŸ˜‡: QN Kwanan su uku a Saudia suna gudanar da addu'ah shida mashkur, gaba d'aya kashe wayoyinsu sukayi, ibada kawai suka sa agaba,Sai akwana na hudun ne sannan suka koma England. Kwanansu hud'u da komawa England yakira wayar Hajiya Anty, Bayan sun gaisa yace "Anty kiyi hakuri akan abinda yarinyar Nan tamiki, na lura kwata kwata batada kunya...... Sannan duk laifin ku ne dakuka liqa min ita" Murmushi tayi "son rigima, to kayi hakuri mana watarana zata dena, karka damu babu komai, baka fita wajan aiki bane Naga kiranka da wannan safiyar?" "Ina gida Anty, yau babu inda zanje, zan zauna agida inyi shara, inyi mopping, inyi wanke wanke, Anty Allah nagaji...." ya qarasa maganar cikin shagwa6a Murmushi tayi tace "yau Kuma shagwa6ar ce tatashi?, ko Inturo ma Waheeda?" tafad'i hakan tana so Tasha cikinsa ko zataji wata maganar Murmushi yayi, yasan Sarai da biyu tayi masa wannan maganar, yaganota, cikin dakiya yace "tazo tamin me? Anty wannan yarinyar ai damuwa ce... Nayafe tayi zamanta" Murmushi tayi tace "to shikkenan, yaushe zaka dawo?" Yatsina fuska yayi sannan yace "ai kinsan zuwan nawa yana hannun Waheeda.... Idan tayi wani abun to zaku ganni, but nide ara'ayina bazan dawo ba Sai biki" Dariya tayi tace "Haka Waheedan tazama? Karka yimata sharri" πŸ˜ƒ Sun dad'e suna zance, daga baya sukai sallama. ** *** ** Cikin hawaye yake yiwa Baban nasa bayanin komai, Alhaji Attahir ya Jinjina Kansa cike da 6acin rai, duk abinda d'ansa yakeso Tofa Shima yanaso, wacce irin yarinya ce wannan da zata rusa farincikin d'ansa? Kallan sa yayi yace "ita yarinyar bazata iya hakuri harna dawo daga tafiya ba, insamu iyayenta muyi magana dasu? Yar gidan wacece ne?" Cikin kuka Didat yace "yarinyar Alhaji Umar Arabo ce" Alhaji Attahir yace "Nasan Alhaji Umar, ka kwantar hankalinka, zamuje dakai ayi magana, dole a warware wannan maganar auren datace anyi dawani, dakai za'ayi wannan auren, ka kwantar da hankalinka kaji?" Kakar Didat dake zaune agefe tayi murmushi, ganin mahaifin nasa zai samo masa abinda yake so, haqiqa tana tsananin son Didat, bata son abinda zai shiga tsakanin sa da farincikin sa, tun Bayan rasuwar mahaifiyar sa, itace taci gaba da Kula dashi, shiyasa take jinsa har cikin zuciyar ta ** *** ** Tafiya suke ahankali agefen titi suna hirarsu ta qawaye, Maya ta kalli qawar tata, "gaskiya qawata na gode da ziyara, naji dad'in zuwanki gidanmu" Waheeda tace "Dama rashin dama ne yasa Bana zuwa ai" Maya ta kalleta tace "yanaga yanayin ki kamar kina cikin damuwa?" Ajiyar zuciya tayi "wallahi Maya, Babban Yaya ne, fishi yake Dani, narasa yanda zan masa, ya cika rigima wallahi"πŸ˜” Maya tayi wani murmushi Mai d'auke da ma'anoni tace "inyee saikace wani Babynki Babban yayan kike cewa yacika rigima? Meya miki to?" "tunda akai maganar auren Nan, narasa gane Kansa, kwata kwata baya sakarmin fuska kamar baya, sannan Bahaka yakewa 'yanbiyu ba" Maya ta riqe hannunta tace "qawata ki kirashi kibashi hakuri, nasan yana jin maganar ki, sannan ki marairaice masa kamar Zaki masa kuka, aikin gane dai, shagwa6a Zaki masa duk ki haukata shi" Zare hannunta tayi daga cikin na Maya tace "me kike nufi? Waike Dan Allah meyake damunki ne? Saurayina ne dazan dinga masa wannan abun? Maya Babban Yaya fa nace Miki ba Huzaifa ba" Maya ta yatsina fuska ganin plan d'in Nata bai samu kar6uwa ba tace "toki rabu dashi kawai, ai zai huce ne, yaushe Zaki fara gyaran jiki ne? Biki Sai matsowa yake, Gara fa tun yanzu kifara shan abubuwa Wanda zasu sa kifara tsiyaya, sonake kisa Huzaifa kuka a Daren farkon ku" Ajiyar zuciya tayi tace "Anty tace gobe zan fara zuwa, kitaho da safe ki sameni a gidan Hajiya Antyn, saina yiwa Huzaifa magana yazo yakaimu gidan, namanta ma ban fada miki ba, Su Daddy sunce muje Asbiti ayi mana text, na jini, kinsan yanzu yanayin rayuwar ya sauya komai Sai ahankali " Maya ta Jinjina kanta, tafara wani tunani, ta kalli Waheeda tace"hakane Kam, saikaje ka auri me sikila ma baka Sani ba, Gara kuje din Kam, wanne Asbiti zakuje? " Zuciya d'aya Waheeda tace"na fad'awa Huzaifan de, yacemin tunda gobe zamuje wajan gyaran jiki,jibi Sai muje asbitin, akwai asbitin da ake duba 'Yan gidansu, (Al'islah Hospital) private ne, can nake tunanin zamuje" Maya tace "to shikkenan, Allah yakaimu goben, saina shigo" Daga Nan sukai sallama, kowa yatafi gida ** *** ** Washe gari da safe Maya a gidan Hajiya Anty tasamu Waheeda, anan sukayi breakfast sannan Waheeda takira Huzaifa yazo yad'aukesu suka tafi Maya tana gidan baya, Waheeda da huzaifa suna gaba, Sai kashe mata murya yake suna soyaiya, hankalin Maya yana kan wayarta tana daddannawa, a gidan da Hajiya Anty ta fad'a musu yasauke su, sannan yatafi, gidan suka shiga aka fara yimata gyaran jikin yanda ya kamata, tsawon lokaci suka d'auka ana mata abu d'aya,Bayan angama gyaran jiki matar tabata wasu magungunan na mata, ta zaunar da'ita a gabanta, saida taga ta Shanye sannan,wani irin qyalli Waheeda tafara, gyaran yau ma kenan, ita kanta Maya Kallan ta take tana mamakin yanda tayi kyau, to rana d'aya ma kenan idan kuma aka gama gyaran gaba d'aya Yaya Waheeda zata kasance? πŸ€” basu gama da wuri ba Sai wajan yamma, sukayi mata sallama saikuma gobe idan sun dawo Allah ne kawai yakawo su gida lafiya, domin kuwa Huzaifa yana ganin irin gyaran da akayi Waheeda saiya susuce bashida aiki saide yajuya ya kalleta, yana driving yana Kallan ta, Maya ta godewa Allah data ganta a kofar gidansu sunzo lafiya, tana futowa daga motar ta leqasu ta window tace "to wallahi ango kakula da qawata sosai, nide na godewa Allah tunda ankawoni gida lafiya" Dariya huzaifa yayi ya shafa sumar Kansa, yasan Sarai taga halin daya shiga ne shiyasa tayi masa wannan maganar, Waheeda ma tayi mata murmushi tace "to Sai munyi waya qawata, gobe karki shirya da wuri, saida yamma zamuje, saboda da safe, Asbiti zamuje" Maya tace "to shikkenan qawata, Allah yakaimu, kikula mana da angon namu" Ta qarasa maganar cikin tsokana Huzaifa yaja motar suka tafi, har zuwa lokacin Maya tana tsaye a'inda suka sauketa, saida taga sunbar layin gaba daya,memakon tashiga gidansu sai ta tare adedeta tashiga,tayi masa kwatance sukad'au wata hanyar ** *** ** Tafiya suke cikeda nishadi, kana ganinsu kasan suna cikin tsantsar farinciki, qamshin turaren sa yahad'u da Nata ga Kuma sanyin esi Sai abun yaqara bada armashi Kallan sa tayi "Bae kadinga sauri muje mana, kana driving kamar baka so" Kallan ta yayi "so kike nayi sauri Dan muje asbitin mugama da wuri kitafi kibarni ko?" Murmushi tayi batare da tace komai ba, yasake Kallan ta yace "inason murmushinki Waheeda, yana birgeni, musanman idan Naga wannan dimple din...." Kallan sa tayi "da gaske? Aikuwa koda yaushe zan dinga yima ka shi, saboda inci gaba da birgeka a koda yaushe, Dan banasan wata Rana kaga wata yarinyar itama ta birgeka" Kafad'a ya d'aga yace "ai Bana tunanin akwai yarinyar dazata birgeni Bayan ke Waheeda, nifa banga amfanin zuwa wannan text din namu ba, saboda nasan kede lafiyarki kalau, Kuma Nima haka,idan kinada wata cuta ma ai saide in nine nasaka miki, tunda nine nabaki jini batare da angwada jinin nawa ba " Cikin rashin damuwa tace"dansu Daddy sun matsa ne ai, Amma yanda nake jin ka acikin zuciyata ko wacce irin cuta ce dakai, zan iya zama dakai Bae" Murmushi yayi ba tareda yace mata komai ba, suna qarasa wa asbitin sukayi wa nurse bayani,dayake tasan Huzaifa tun tuni, Nan asbitin suke zuwa duka family d'insu, cikin qanqanin lokaci aka d'auki jininsu aka basu wajan zama Basuyi awa d'aya ba, doctor yakirasu zuwa office d'insa, zama sukai ya Kalle su yayi murmushi yace "Huzaifa kace ankusa angoncewa" Murmushi Huzaifa yayi, "Eh wallahi Doctor, ga madam Nan" Yace "To Allah yasanya alkhairi, Allah yabaku zuri'ah Dayyiba" Ahankali Waheeda dake wasa da yatsun hannunta tace "Amin" Takarda ya miqawa Huzaifa yace "toga result d'inka, Congratulations, baka d'aukeda kowacce irin cuta...."πŸ˜ƒ Huzaifa ya kar6a yana fadin "to Alhamdulillah" Kallan ta Doctor yayi yace "Waheeda" 'Dagowa tayi ta Kalle shi sannan tace "Na'am" Yayi ajiyar zuciya yace "Waheeda duk abinda kikaga yasamu Bawa, to anaso ya yarda da qaddarar sa, ita cuta ba mutuwa bace, sannan idan kin yarda da shawarwarin dazan baki Zaki zauna lafiya, sannan Zaki rayu kamar kowa idan nad'oraki akan magani,kuma....." "dan Allah dakata Doctor Mahmud, mekakeso kace ne?" Cewar huzaifa daya dakatar da doctor Doctor ya kalli idon Waheeda da yayi tsilli-tsilli tana Kallan su duka su biyun, sannan yace "Waheeda kiyi hakuri, Amma abunda bincikenmu ya nuna shine kina d'aukeda qwayar cuta me karya garkuwar jiki" Lokaci d'aya, Waheeda da Huzaifa suka miqe tsaye Huzaifa yace "What...? HIV fa doctor, tayaya?" Gaban Waheeda yayanke yafad'i, tasaka hannu tadafe qirjinta, kanta take girgizawa kwata kwata takasa magana, lokaci d'aya jiri yad'ebeta tazube qasa sumanmiya " Cikin sauri Huzaifa yabita, jijjigata yafara yi, yana fad'in" Waheeda!! Waheeda kitashi Dan Allah!! " Office d'in aka turo, wata matashiyar budurwa tashigo, taci Gayu iya Gayu, tana ganin Huzaifa tace"Yaya Huzaifa lafiya Kuma? Meyasame ta?" Huzaifa ya kalleta baice mata komai ba yasaka hannu ya d'auki Waheeda cancak, yafice daga office d'in Yana fita matashiyar budurwar ta kalli doctor tace"meyake faruwa ne doctor?" Kai tsaye yace "ta tsorata ne sakamakon gwajin da muka mata, muka Gano tana d'aukeda cutar qanjamau,but ni banga abun suma ba, kowanne Bawa da irin qaddararsa,Kuma ba lalle saika yi iskanci ne zaka sameta ba, akwai hanyo yi dayawa, wasu a wajan mahaifiyar su suke dauka, wasu ta hanyar hada jini Dame irin cutar, kokuma ayima allura da sirinjin Wanda yake d'aukeda cutar, kokuma sex, ko amfani da wani qarfe kamar su kibiya, to gashi ita tun kafin ma nafada mata magungunan daya kamata ta dinga Sha harta sume" Cikin razani budurwar tace "mene? Wallahi saina fad'awa Hajiya, Kuma akan me qanjamau din yake wannan rawar jikin?Huzaifa d'an'uwana ne, cousin d'inane, bazamu Bari ya auri me wannan cutar ba, ta shafa masa masifa, ita tasan inda tasamu cutar ta" Tana fad'ar haka, tafice daga office d'in, Doctor yayi murmushi sannan yabud'e wani file yaci gaba da rubuce-rubuce Motar ya bud'e yasaka ta aciki,har zuwa lokacin Waheeda bata farfad'o ba, Shima yashiga, dube dube yafara anan yaga wayarta cikin hand bag dinta , Kai tsaye contact d'in wayar ya duba, mutum d'aya ne yafad'o masa, dayake wayar Ummah ce yana ganin Ansa Naufal Son,yakira wayar, Babban Yaya yana gida yana motsa jiki, yaga Kiran Ummah, dayake ringing d'inta daban ne, saiya daina abinda yake ya d'auki wayar Cikin damuwa Huzaifa ya zayyane masa komai, Babban Yaya yadafe Kansa da hannun saπŸ€¦πŸ»β€β™‚οΈyakasa cewa komai,banda innalillah wa inna ilaihirraji'un babu abinda yake maimaita wa a ransa, lokaci d'aya yarasa a'ina yake, a zaune yake ko a tsaye, gabansa banda Dukan uku uku babu abinda yake,Hiv Kuma? Hasbunallah..... yana jin Yanda Huzaifa yake fad'in "hallo hello, baka jinane?" 'Dif yakashe wayar, cikin tashin Hankali yazura kayansa yanufi Airport, ko wanka bai tsaya yiba ** *** ** Suna zuwa gida yad'aukota a hannun sa yafuto da'ita daga cikin motar, yanbiyu dasuke daukan photo a compound sukaga Huzaifa ya 'Dauko Waheeda, cikin sauri suka nufesu, Adede lokacin Didat da kakarsa da babansa suka shigo gidan, ta window din motar ya hango Wani ya dauki Waheeda a hannun sa, tun kafin babansa ya qarasa tsayawa da motar, yabud'e yafuto ya nufesu, yana zuwa ya cakumi wuyan Huzaifa "ubanwa yace ka d'auki wannan yarinyar...?" Huzaifa ya kalli gaban rigarsa, yaga yanda Didat ya riqeshi cikin 6acin rai yasaki Waheeda tayi qasa, 'yanbiyu suna ganin haka sukai kan yar qanwar su suka cacimeta Sai jijjiga ta suke, Ihsan tayi gudu cikin gida ta fad'awa Ummah abinda yake faruwa, intisar Kuma tayi wajan fomfon da'ake bayin fulawa ta 'Debo ruwa ta watsa mata, lokaci d'aya ta farka tareda sakin wani irin kuka Huzaifa yakama Didat, suka fara dambe πŸ™†πŸ»β€β™€οΈ? Baban Didat ya kamashi yace "wuce mutafi gida, banason tashin Hankali son" Ummah ta qaraso wajan itada Ihsan cikin tashin Hankali take tambaya ''menene yafaru?"Didat dayake ta haki da kumfan baki yace "Ummah saboda me wannan banzan zai dinga d'aukar Waheeda? saboda me Ina son yarinya wani qato zai dinga riqeta" Cikin 6acin rai Huzaifa yace "nafi karfin a kirani qato, tunda nine Nan zan aure ta" Didat yanuna shi da hannu yace "Dan zaka aure ta shine hakan yabaka damar ta6a jikinta? Aibaka aure taba" Hajiya Anty tashigo gidan ta shirya tsaf zata wuce Asbiti, tabiyo wa Ummah zasu gaisa,kamar yanda tasaba, tana zuwa batabi takan kowa ba tanufi Waheeda, datake kuka kamar ranta zai fita, tambayar ta take "meyake faruwa?" Amma Waheeda tayi shiru tama kasa magana. kakar Didat ce ta matso ta kama hannun sa tace "muje" ta sake Kallan Ummah tace "Hajiya zamu dawo daga baya"tana fad'ar haka tajuya tashiga motar su, shikuma Didat babansa yakama hannun sa, yayinda Huzaifa yake sake gyara gaban rigar sa da Didat ya cukwikwiye masa, mutuqar tashin Hankali Hajiya Anty tashiga, jikinta Sai rawa yake tana kallon Waheeda, bata taba ganinta tana irin wannan kukan ba, gashi taqi yimata magana, Cikin 6acin rai ta make Waheeda da duka,tace"Dan ubanki bazaki fadamin abinda yake faruwa ba? " Cikin kuka tace" Wai... Waii.... Ninn nice nake da qanjamau... "ta qarasa maganar tana rushewa da Kuka Yanbiyu suka zaro ido😳 suna fad'in"qanjamau Kuma?" Didat da babansa suka juyo da sauri, kowa Idonsa akan Waheeda sunaso suji ta amsa abinda yanbiyu suke tambaya, ahankali ta daga musu kanta alamun hakane Didat ya kalli Waheeda ya jijjiga Kansa, sannan yayi gaba, babansa ma yabi bayansa suka tafi Yanbiyu ne suka ja Waheeda sukayi ciki da'ita, gaban hijab dinta duk ya jiqe da hawaye, hannunta ta dora aka, tana rusa uban kuka, Hajiya Anty tabiyo bayansu cikin wani irin yanayi, kwata kwata bata sanin inda take jefa kafarta, kawai tafiya take, Ummah kuwa jitayi kamar tana tafiya akan is'ka, kalmar qanjamau d'innan Sai yawo take acikin zuciyar ta,Huzaifa yashiga motarsa yaja yabar gidan ihun da Waheeda take ne yafuto da Daddy daga cikin daki cikin sauri, Nan yafara tambayar ba'asi, Amma kowa yakasa bashi amsa, da Yanbiyu da Waheeda kowa Sai kuka yake, su Sa'ad da Sa'eed ma suka futo daga daki kowa yana tambayar ba'asi Hajiya Anty tadauko wayarta ajaka takira Uncle Usman tace "Alhaji gidannan fa babu lafiya, katashi daga baccin Nan kazo" tana fada masa haka muryarta na rawa alamun kuka zata fara, daga Nan ta kashe wayar ta Ko minti biyar ba'ayi ba saiga uncle Usman yashigo dagashi Sai jallabiya, Daddy yace "Hajiya, mu duk munzo Nan mun zauna, muna tambayar ku meyake faruwa kunyi mana shiru, Yara suna kuka kunbarsu babu Wanda yake lallashin su" Ummah ta Kalle shi "Alhaji Wai Waheeda ce me qanjamau..." tana fad'a masa haka hawaye yazubo daga idonta Daddy da Uncle Usman suka nemi waje suka zauna suna fadin "innalillahi wa inna ilaihirraji'un...." Hajiya Anty tadafe kanta daya ke ciwo kamar zai fado,Waheeda tanajin furucin Ummah tafara girgiza kanta,cikin kuka tace "wallahi ni banida komai, Allah sharri akamin" yanda take kukan abin tausayi shine yasake karya zuciyar yan'uwan Nata ma, Nan da Nan falon nasu ya kaure da koke-koke, Ahankali Hajiya Anty tatashi ta janyo ta jikinta ta rungume ta, idanun Waheeda yayi jajir, fuskarta ma haka, Sai ajiyar zuciya take, Hajiya Anty ta kwantar da kanta a qirjinta tana bubbuga Bayan ta, Amma kwata kwata takasa cemata komai, ita kadai tasan metake ji acikin zuciyar ta Maya ce takira wayar yanbiyu, cikin kuka intisar ta d'auka, Maya tace "Inti nakira wayar Ummah zanyi magana da Waheeda to ba'a d'auka ba, Dan Allah ki had'ani da'ita" Cikin kuka intisar tace "Maya Waheeda babu lafiya" Maya tace "innalillahi.... Kinga Bari kawai Gani Nan zuwa, tunda naji kina kuka nasan ba lafiya ba" Ko awa daya Maya bata qaraba tazo gidan, yanda taga qawar Tata ta haukace tasan babu lafiya, haka sukaci gaba da zama sun kasa ta6uka komai, Uncle Usman yayi ajiyar zuciya ya kalli Daddy "yanzu Alhaji menene abin yi?" "Salam Alaikum" yayi sallama ciki-ciki tareda shigowa falon Gaba d'ayansu suka d'aga Kai suka Kalle shi, Waheeda tana ganin Babban Yaya tatashi da gudu ta fad'a jikinsa tareda sakin wani irin sabon kuka,ahankali ya Lumshe Idonsa sannan yabud'e su,yaso ace su kad'ai ne daya sake rungume ta ya lallasheta, ahankali yad'ora hannun sa abayanta yana bugguga Bayan ta kad'an kad'an , but duk da hakan yana jin yanda nonuwan ta suke bugar qirjinsa Maya ta Kalle su, itade wad'annan mutanan suna birgeta, cikin sigar rad'a yaace "kiyi hakuri, is ok, kukan ya'isa haka" Cikin kuka tace "Babban Yaya Allah banida komai" Zareta yayi daga jikinsa Yaruqo hannunta suka zauna a falon, Kallan Daddy yayi yace "Daddy ni Hankali na bai kwanta da wannan asbitin da suka jeba, why not Akira family doctor yazo gida ya dauki jinin Nata agaban mu saiya kawo mana result d'in mugani" Daddy yace "to Son.... Tun dazu ma mu bamuyi wannan tunanin ba, munkasa aikata komai, hakan ma yayi" Maya ta dauki wayarta tayi kira, ahankali tatashi ta kalli yanbiyu tace "Ina zuwa, zanyi waya" Yanbiyu suka d'aga mata kai, ita Kuma tafita cikin sauri Babban Yaya yakira family Doctor d'insu, yayi masa bayanin komai ta waya, cikin qanqani lokaci doctor khamis yazo gidan, yanda yaga family din duk sun had'u waje daya, yasan cewa haqiqa akwai abinda yake faruwa, Babban Yaya ya nuna masa Waheeda, doctor khamis ya qarasa ya dauki jininta, sannan ya musu sallama cewa zaije ya dawo Har doctor khamis yatafi, banda addu'ah babu abinda mutanan Nan suke yi, kowa yayi shiru Sai zancen zuci, Waheeda kuwa Hankalinta ne ya kwanta, tasan cewa yanzu ne gaskiya zatayi halinta, zasu yarda da abinda take fad'a musu, kusan awa biyu suka d'auka suna jiransa, Sai gashi yashigo falon fuskarsa Sai had'a gumi take, suna ganinsa kowa ya miqe tsaye kamar Wanda suke jiran me naquda Babban Yaya ya qaraso wajan sa, yariqe hannun sa yace "doctor ya ake ciki?" Doctor khamis ya kalli Babban Yaya yace "kuyi hakuri yalla6ai, Bahaka naso fad'a ba, Amma tabbas akwai wannan cutar" Babban Yaya yasake shi tareda dafe KansaπŸ€¦πŸ»β€β™‚οΈ? yace "Oh my God" Sai hawaye nanfa hankalin su yasake tashi, falon ya kaure da Kuka, musanman da basu ta6a ganin tashin hankalin dayasa Babban Yaya kuka ba Amma yau sunganshi da idonsu yana kuka, Babban Yaya yayi kan Waheeda yana cewa "Daddy zan kaita wani asbitin, ni qanwata batada komai" Jin shiru Waheeda bata tashi ba yasa ya kalleta, Sai a lokacin ya lura ta suma πŸ™†πŸ»β€β™€οΈ? Gabansa ne yafad'i, cikin tashin Hankali yafara jijjiga jikinta "ke.... Ki Tashi.... Please kitashi ninasan bakida komai Waheeda" Yajuya ya kalli Ummah yace "Ummah kice mata batada komai...." Magana yake yana kuka da Idonsa, kwata kwata kamar ma baya cikin hayyacinsa Hajiya Anty ta share Hawayen idonta tatashi tadauko ruwa a fridge ta shafa mata, da Kuka tafarka, muryarta harta fara dashewa Babban Yaya ya zauna, yadafe Kansa da hannayensa biyu tareda rufe Idonsa, Daddy ya kalli Waheeda yace "ke zonan" Ahankali tatashi taje gabansa ta tsugunna tana sharar hawaye, Daddy ya kalleta yace "nasan bakya ji Waheeda, kifadamin a gidan ubanwa kika Dauko mana wannan masifar?" Wani irin kuka ne yataso mata, hawaye masu zafi suka zubo daga cikin idonta, kanta tafara girgizawa tace "wallahi tallahi Daddy bansani ba.... Ni bansan zan dauki cuta ba" Gaba d'ayansu Sai suka maida Kallan su wajan Waheeda, Daddy yace "ni nasan akwai abinda kika aikata, kifadamin kokuma yanzu yanzun Nan namiki illa a wajannan...." ya qarasa maganar cikin tsawa Cikin kuka tace "anta6a yimin allura da sirinjin da akayiwa Didat dashi, sannan d'azu muna hanya Huzaifa yace min Wai jinin daya Bani a Asbiti ba'ayi masa text ba, haka aka Sakamin ba tareda an gwada jinin ba" Wani irin kishi ne yakama Babban Yaya,shi yana can yana hauka akanta ashe ita tana Nan soyaiyar ta takeyi da samarin ta. Cikin 6acin rai yatashi tsaye yace "What....?, ashe bakida Hankali bakisan mutum ba kawai saboda wata banzar soyaiyar ku Zaki yarda ayi miki amfani da sirinjin da aka masa allura?, sannan anfad'a miki ansaka miki jini batare da text ba so yarufe miki ido kikasa daukan qwaqwaqwaran mataki akai? Kifadamin ke wacce irin mahaukaciya ce? " Kallan sa tayi tafara girgiza masa Kai tahad'e hannunta biyu waje d'aya πŸ™πŸ»alamun yayi haquri Babban Yaya bai saurareta ba ya d'aga hannu ya wanke tada mari, zai qara mata wani Marin cikin sauri Uncle Usman yace"Naufal" Cak yaja ya tsaya yafasa dukanta, Uncle Usman yace "kayi Hakuri" Sannan yajuya ya kalli Sa'eed da Sa'ad, yace "kuje kuzo mana da Huzaifa dakuma Didat, ga doctor khamis Nan bai tafi ba, saiya dauki jininsu aga waye yasaka mata cutar acikinsu" ❀️❀️❀️ 1/28/22, 20:51 - Ummi TandamaπŸ˜‡: GG Daga Huzaifa har Didat, babu Wanda ya sauya Kaya daga cikin kayan da sukai fad'a d'azu 🀣 Dama kowa kamar jira yake, shiyasa su Sa'eed suna zuwa suka biyo bayansu, suka taho gaba d'aya Uncle Usman ya kalli doctor khamis yace "dauki jininsu doctor" Doctor yamatso jikinsa Sai rawa yake yanata had'a gumi, yad'auki jininsu, Hajiya Anty tatashi ta kalli Naufal tace "muje kasa driver yakaishi, saboda yayi sauri ya dawo karmu tsaidasu Huzaifa dayawa" Didat sarkin kishi ya kalli hajiya Anty yayi qasa da Kansa, wato kar Asa su huzaifa jira, shi bata ambaci sunan saba, Huzaifa kawai tasani πŸ˜‚ Babban Yaya yatashi, suka futo su uku, dashi da doctor dakuma Hajiya Anty,suna zuwa compound Babban Yaya yakira driver, yasa shi yad'auki doctor khamis suka tafi. Ummi ce tashigo gidan, Babban Yaya yana ganin ta yad'auke Kansa kamar bai ganta ba, yarasa uban me yakawo ta gidan Kuma, kwata kwata mace babu aji babu kara kullum kina yawo a gidan surukanki? Ummi ta kalli hajiya Anty ko gaishe ta batayi ba, ta shareta,Anty tayi murmushi kawai, Babban yayama ya ganta, Kuma Sarai yagani bata gaida Hajiya Anty ba, Shima bata gaishe Shiba, har Gara shi Dama yasan kar take ganinsa πŸ˜ƒ Amma hajiya Anty fa?πŸ€” Gaba d'ayansu falon suka dawo suka zauna, dasuka shigo falon ma yayi tunanin zata gaida Hajiya Anty nanma yaji shiru, Kuma yaga ta nemi kujera ta zauna ta kame, saikace yar gida, jijjiga Kansa kawai yayi, inbanda rashin Hankali tayaya zakiga family sun taru gaba d'ayansu, Amma kizo ki zauna ai daga Gani kinsan ba lafiya ba Yanda kowa na falon yayi shiru haka ummi ma tayi shiru tana jira taga abinda yake faruwa,su doctor basufi awa d'aya ba suka dawo, yana shigowa kuwa kowa ya maida hankalin sa Kansa, Uncle Usman yace "doctor ya akayi?" Cikin rashin damuwa yace "Alhaji naduba babu...., kowa lafiyarsa kalau acikinsu, daga Didat d'in har Huzaifa, babu Wanda yake d'aukeda HIV" Ummi ta zaro ido😳 tareda rufe bakinta da hannunta tana sake zare ido tana Kallan 'Yan falon taga to waye yake da qanjamau d'in? πŸ€” Daga Daddy har Uncle Usman sunkuyar da kansu qasa sukai, to daga Ina wannan matsalar take? Tayaya akai Waheeda tasamu wannan cutar kenan? Huzaifa ya miqe tsaye, ya kalli kowa da kowa na falon yace "Alhamdulillah... Tunda gaskiya ta bayyana, ni Dama temako naso yi, lokacin Dana tarar batada lafiya nad'auki jinina nabata,ashe bansaniba tunanin da kuke min daban ne, saboda tozarci mu za'a kawo a ajiye anan Ana jira aga waye me qanjamau acikinmu ayi masa ruwan bala'i saboda shine yasakawa 'yarku cuta, to ai yanzu kunji komai, Kuma gaskiya ta futo bamune muka saka mata ba, saboda haka nikam na haqura da Waheeda.... Maganar gaskiya, bazan iya auren me qanjamau ba, duk soyaiyar danake mata...." Tunda yafara magana gaba d'aya falon yayi tsit, kowa kallansa yake cikeda mamaki, musanman su Daddy yanda suka d'aukake shi,Babban Yaya kuwa baiji komai ba, asali ma dad'i yaji yanda gaskiya ta bayyana,sukaga halin Huzaifa na zahiri, inda ace ya fad'a musu karsu bashi Waheeda ya tabbatar babu Wanda zai saurareshi, ko d'ago Kansa baiyi ya kalli Huzaifa ba,harya gama maganar sa yafice daga falon cikin 6acin rai Waheeda kuwa d'agowa tayi da jajayen idonta ta zubawa Huzaifa ido, ko kad'an takasa ce masa komai, yanbiyu kuwa kuka suke sosai saboda furucin huzaifa, bakajin komai Sai kukansu daya cika falon Ummi ta Jinjina kanta tareda ta6e baki☹️ Didat yatashi tsaye ya qarasa wajan Waheeda tareda miqa mata hannu yace "Waheeda, kiyi hakuri kinji, Ina tare dake a koda yaushe, wannan shine abinda nake nuna miki, nine nake sonki ba Huzaifa ba....." "kakeson wa?" maganar kaka ta karad'e falon nasu, juyawa yayi yaga kakarsa da babansa a tsaye, Kai tsaye yace mata "inason ta, saboda me zan rabu da'ita dan qaddara tahau kanta?" "to saide ka za6a koni ko ita, haka kawai yarinyar data qika tun tuni,kana bibiyarta akan ta saurareka taqi, tazabi wani a kanka, itace yanzu saboda rashin Hankali zakazo kace kanaso ka aura Bayan tagama yawon duniya takwaso qanjamau? To bada niba bada irin gidana ba, wuce mutafi kona tsinema Albarka yanzun Nan" Hawaye Didat yafara yace "Amma Ina sonta..." Babansa yayi ajiyar zuciya yace "kayi hakuri son, Amma nima bazan barka kana da cikakkiyar lafiya ka sauri me HIV ba" Didat ya kalli Waheeda, itama ta Kalle shi,bayajin zai iya daina son Waheeda har qarshan rayuwarsa, tanada cuta ko bata da cuta abinda yasani shine yana qaunarka tsakani da Allah, cikin kuka yafice daga falon da sauri, iyayensa suka Mara masa baya Hawaye kawai tsiya ya yake a'idon Waheeda,wannan shi ake kira sai masifa ta sameka ne zaka san me sonka da gaskiya, yanzu duk soyaiyar da Huzaifa yake iqrari yana mata ashe qarya ne? Ashe saboda cuta ta sameta zai iya gudunta? Didat din datake wulaqantawa shine ya tsaya tsayin daka akan yana sonta duk da haka, lokaci d'aya taji numfashin ta yana sama kamar zai d'auke, yanbiyu da Ummah da Hajiya Anty, kuka suke sosai, duk falon anrasa Wanda zaiyi magana guda d'aya Gabansa ne ya tsanan ta fad'uwa, ya d'ago Kansa ya kalli iyayen nasa, daga Daddy har Uncle Usman kansu yana qasa sun kasa d'agowa kamar Wanda suke jin kunyar had'a ido da yaran nasu Ya kalli Ummah yaga tana goge hawaye Ya kalli 'yanbiyu yaga Sai gunjin kuka suke duka su ukun har Waheeda Ya kalli su Sa'eed yaga kansu aqasa suma Ya kalli Hajiya Anty yaga ta zubawa waje d'aya ido hawaye yana silalo wa daga idonta, idan akwai Wanda yaqi jinin yaga kukan ta Aduk duniya to Hajiya Anty ce, zai iya jure kukan kowa Amma banda Nata, har zuwa lokacin Hajiya ummi tana falon, ita bata tafi ba, Kuma takasa Bawa kowa haquri Zuciyar sa ce take zigashi akan yafad'i abinda yake ransa, tayaya za'azo har gida, harcikin falon su aci mutuncin su kawai saboda maganar Aure? Tayaya zaiguji Waheeda? Tayaya zai raba zuciyar sa da soyaiyar ta Bayan da soyaiyar Tata aka halicce shi? Lokaci d'aya yad'auki shawarar zuciyar sa, yanaso yafad'i abinda yake ransa Kuma Yana tsoron abinda zai biyo baya, gabansa yaqara tsananta fad'uwa, cikin sauri kamar an fuzgo maganar daga bakinsa ya kalli inda Daddy da Uncle Usman suke zaune yace "Daddy nizan Aure ta" 'Diffff...... Sai aka nemi masu kuka a falon aka Rasa,falo yayi shiruuu, kowa ya d'ago Kansa yana Kallan Babban Yaya, falon yayi tsit kamar babu wata halitta acikinsa, kowa Kallan sa yake cikeda mamaki, gaba d'ayansu yaran gidan babu Wanda mamaki bai kamashi ba Sai iyayen ne kawai dasuke Kallan sa cikeda d'inbum almara Ummi ta miqe tsaye cikin tashin Hankali tace "ka auri wa? Wallahi saide ka za6a koni ko ita, Amma Bazan ta6a yarda ka aure ta ka shafamin qanjamau ba, saide mu rabu...." Ummah ta kalli Babban Yaya tace "Naufal meyasa....?meyasa zaka fad'i wannan maganar?" ta qarasa maganar tana dafe kanta dayake barazanar rabewa gida biyu πŸ€¦πŸ»β€β™€οΈ? Cikin tashin Hankali Waheeda ta zaro idonta😳 Wanda yayi jajir kamar gauta saboda kuka, kamar ba itace take ihun kuka yanzu ba Kallan Ummah tasake yi ko zata qarya ta maganar da Babban Yaya yafad'a, Amma saitaji Ummah tayi shiru, ta kalli su Daddy har yanzu kansu yana qasa sun kasa kallan mutanan falon, cikin tashin Hankali tace "Zaman Zina? Ni wallahi bazan yarda ba, banason sa, bazan iya Zaman aure dashi ba....." tatashi tayi d'akinsu da gudu cikin tsananin kuka Wani irin kuka ne yataso masa, yau shi Waheeda take cewa bata sonsa, wani irin abu yatokare masa maqoshi, ko yawu yakasa had'iyewa. Ummi ta Kalle shi tace"Naufal jiranka nake, nabaka za6i tun d'azu kayi shiru, kana tunanin zan yarda kahad'ani kishi da wannan yarinyar ne? Wallahi bazai iyu ba saide asan nayi, zanje in fad'a agida yanzu yanzu " Baqin cikin kalmar da Waheeda tafada masa ne yake addabar zuciyar sa, jiyake kamar yafashe da Kuka kozaiji sauqi Amma kukan yaqi zuwa, ga Kuma wannan yarinyar datake qara masa wata damuwar. Cikin 6acin rai Shima yatashi tsaye, cikeda tsawa yace" toki fad'a mana, so what....? Idan kin fad'a musu kiqara musu da cewa Bana sonki, Bana qaunarki, bazan iya zama dake ba, saboda bakya respecting iyayena " Yajuya ya nuna mata Hajiya Anty sannan yaci gaba da fad'in"matar dakika raina kike mata Kallan sa'arki itad'in mahaifiyata ce..." Lokaci d'aya ummi ta qame a wajan, gabanta yafad'i, cikin mamaki ta bud'e bakinta, takasa rufe shi Babban Yaya yahad'e hannun sa waje d'aya πŸ™πŸ»ya kalleta yace "Dan Allah Ummi kifita daga cikin rayuwa ta, na roqeki" Cikin kuka ummi Tajuya tafice daga gidan, Shima Babban Yaya batare daya kalli iyayen nasu ba yafice cikin sauri, saboda zuciyar sa tagama karyewa, qiris yake jira yafashe da kuka, yana zuwa compound yashiga motar sa yamata key yabar gidan a d'ari da Sittin, Kai tsaye gidansa ya nufa, yanda yake danna Hon yasa maigadinsa yabud'e masa da sauri, shigowa had'ad'd'an gidan nasa yayi tareda parking din motar sa, yad'ora Kansa akan sitiyarin motar yayi shiru, har yanzu maganganun Waheeda yawo suke masa a ransa, yana jin yanda wayarsa take qara Amma yaqi dubawa, saida kira na uku yashigo sannan ya d'auka Daga d'ayan bangaren Mashkur yace " Bro... Ina kabar wayar ne?" Sai a lokacin kukan dayake dannewa agida yataso masa, fashewa yayi da Kuka harda shashsheka, daqyar maganar sa take fita, cikin kuka yace "Mashkur bata sona..." ❀️ 1/28/22, 20:51 - Ummi TandamaπŸ˜‡: GG Daga Huzaifa har Didat, babu Wanda ya sauya Kaya daga cikin kayan da sukai fad'a d'azu 🀣 Dama kowa kamar jira yake, shiyasa su Sa'eed suna zuwa suka biyo bayansu, suka taho gaba d'aya Uncle Usman ya kalli doctor khamis yace "dauki jininsu doctor" Doctor yamatso jikinsa Sai rawa yake yanata had'a gumi, yad'auki jininsu, Hajiya Anty tatashi ta kalli Naufal tace "muje kasa driver yakaishi, saboda yayi sauri ya dawo karmu tsaidasu Huzaifa dayawa" Didat sarkin kishi ya kalli hajiya Anty yayi qasa da Kansa, wato kar Asa su huzaifa jira, shi bata ambaci sunan saba, Huzaifa kawai tasani πŸ˜‚ Babban Yaya yatashi, suka futo su uku, dashi da doctor dakuma Hajiya Anty,suna zuwa compound Babban Yaya yakira driver, yasa shi yad'auki doctor khamis suka tafi. Ummi ce tashigo gidan, Babban Yaya yana ganin ta yad'auke Kansa kamar bai ganta ba, yarasa uban me yakawo ta gidan Kuma, kwata kwata mace babu aji babu kara kullum kina yawo a gidan surukanki? Ummi ta kalli hajiya Anty ko gaishe ta batayi ba, ta shareta,Anty tayi murmushi kawai, Babban yayama ya ganta, Kuma Sarai yagani bata gaida Hajiya Anty ba, Shima bata gaishe Shiba, har Gara shi Dama yasan kar take ganinsa πŸ˜ƒ Amma hajiya Anty fa?πŸ€” Gaba d'ayansu falon suka dawo suka zauna, dasuka shigo falon ma yayi tunanin zata gaida Hajiya Anty nanma yaji shiru, Kuma yaga ta nemi kujera ta zauna ta kame, saikace yar gida, jijjiga Kansa kawai yayi, inbanda rashin Hankali tayaya zakiga family sun taru gaba d'ayansu, Amma kizo ki zauna ai daga Gani kinsan ba lafiya ba Yanda kowa na falon yayi shiru haka ummi ma tayi shiru tana jira taga abinda yake faruwa,su doctor basufi awa d'aya ba suka dawo, yana shigowa kuwa kowa ya maida hankalin sa Kansa, Uncle Usman yace "doctor ya akayi?" Cikin rashin damuwa yace "Alhaji naduba babu...., kowa lafiyarsa kalau acikinsu, daga Didat d'in har Huzaifa, babu Wanda yake d'aukeda HIV" Ummi ta zaro ido😳 tareda rufe bakinta da hannunta tana sake zare ido tana Kallan 'Yan falon taga to waye yake da qanjamau d'in? πŸ€” Daga Daddy har Uncle Usman sunkuyar da kansu qasa sukai, to daga Ina wannan matsalar take? Tayaya akai Waheeda tasamu wannan cutar kenan? Huzaifa ya miqe tsaye, ya kalli kowa da kowa na falon yace "Alhamdulillah... Tunda gaskiya ta bayyana, ni Dama temako naso yi, lokacin Dana tarar batada lafiya nad'auki jinina nabata,ashe bansaniba tunanin da kuke min daban ne, saboda tozarci mu za'a kawo a ajiye anan Ana jira aga waye me qanjamau acikinmu ayi masa ruwan bala'i saboda shine yasakawa 'yarku cuta, to ai yanzu kunji komai, Kuma gaskiya ta futo bamune muka saka mata ba, saboda haka nikam na haqura da Waheeda.... Maganar gaskiya, bazan iya auren me qanjamau ba, duk soyaiyar danake mata...." Tunda yafara magana gaba d'aya falon yayi tsit, kowa kallansa yake cikeda mamaki, musanman su Daddy yanda suka d'aukake shi,Babban Yaya kuwa baiji komai ba, asali ma dad'i yaji yanda gaskiya ta bayyana,sukaga halin Huzaifa na zahiri, inda ace ya fad'a musu karsu bashi Waheeda ya tabbatar babu Wanda zai saurareshi, ko d'ago Kansa baiyi ya kalli Huzaifa ba,harya gama maganar sa yafice daga falon cikin 6acin rai Waheeda kuwa d'agowa tayi da jajayen idonta ta zubawa Huzaifa ido, ko kad'an takasa ce masa komai, yanbiyu kuwa kuka suke sosai saboda furucin huzaifa, bakajin komai Sai kukansu daya cika falon Ummi ta Jinjina kanta tareda ta6e baki☹️ Didat yatashi tsaye ya qarasa wajan Waheeda tareda miqa mata hannu yace "Waheeda, kiyi hakuri kinji, Ina tare dake a koda yaushe, wannan shine abinda nake nuna miki, nine nake sonki ba Huzaifa ba....." "kakeson wa?" maganar kaka ta karad'e falon nasu, juyawa yayi yaga kakarsa da babansa a tsaye, Kai tsaye yace mata "inason ta, saboda me zan rabu da'ita dan qaddara tahau kanta?" "to saide ka za6a koni ko ita, haka kawai yarinyar data qika tun tuni,kana bibiyarta akan ta saurareka taqi, tazabi wani a kanka, itace yanzu saboda rashin Hankali zakazo kace kanaso ka aura Bayan tagama yawon duniya takwaso qanjamau? To bada niba bada irin gidana ba, wuce mutafi kona tsinema Albarka yanzun Nan" Hawaye Didat yafara yace "Amma Ina sonta..." Babansa yayi ajiyar zuciya yace "kayi hakuri son, Amma nima bazan barka kana da cikakkiyar lafiya ka sauri me HIV ba" Didat ya kalli Waheeda, itama ta Kalle shi,bayajin zai iya daina son Waheeda har qarshan rayuwarsa, tanada cuta ko bata da cuta abinda yasani shine yana qaunarka tsakani da Allah, cikin kuka yafice daga falon da sauri, iyayensa suka Mara masa baya Hawaye kawai tsiya ya yake a'idon Waheeda,wannan shi ake kira sai masifa ta sameka ne zaka san me sonka da gaskiya, yanzu duk soyaiyar da Huzaifa yake iqrari yana mata ashe qarya ne? Ashe saboda cuta ta sameta zai iya gudunta? Didat din datake wulaqantawa shine ya tsaya tsayin daka akan yana sonta duk da haka, lokaci d'aya taji numfashin ta yana sama kamar zai d'auke, yanbiyu da Ummah da Hajiya Anty, kuka suke sosai, duk falon anrasa Wanda zaiyi magana guda d'aya Gabansa ne ya tsanan ta fad'uwa, ya d'ago Kansa ya kalli iyayen nasa, daga Daddy har Uncle Usman kansu yana qasa sun kasa d'agowa kamar Wanda suke jin kunyar had'a ido da yaran nasu Ya kalli Ummah yaga tana goge hawaye Ya kalli 'yanbiyu yaga Sai gunjin kuka suke duka su ukun har Waheeda Ya kalli su Sa'eed yaga kansu aqasa suma Ya kalli Hajiya Anty yaga ta zubawa waje d'aya ido hawaye yana silalo wa daga idonta, idan akwai Wanda yaqi jinin yaga kukan ta Aduk duniya to Hajiya Anty ce, zai iya jure kukan kowa Amma banda Nata, har zuwa lokacin Hajiya ummi tana falon, ita bata tafi ba, Kuma takasa Bawa kowa haquri Zuciyar sa ce take zigashi akan yafad'i abinda yake ransa, tayaya za'azo har gida, harcikin falon su aci mutuncin su kawai saboda maganar Aure? Tayaya zaiguji Waheeda? Tayaya zai raba zuciyar sa da soyaiyar ta Bayan da soyaiyar Tata aka halicce shi? Lokaci d'aya yad'auki shawarar zuciyar sa, yanaso yafad'i abinda yake ransa Kuma Yana tsoron abinda zai biyo baya, gabansa yaqara tsananta fad'uwa, cikin sauri kamar an fuzgo maganar daga bakinsa ya kalli inda Daddy da Uncle Usman suke zaune yace "Daddy nizan Aure ta" 'Diffff...... Sai aka nemi masu kuka a falon aka Rasa,falo yayi shiruuu, kowa ya d'ago Kansa yana Kallan Babban Yaya, falon yayi tsit kamar babu wata halitta acikinsa, kowa Kallan sa yake cikeda mamaki, gaba d'ayansu yaran gidan babu Wanda mamaki bai kamashi ba Sai iyayen ne kawai dasuke Kallan sa cikeda d'inbum almara Ummi ta miqe tsaye cikin tashin Hankali tace "ka auri wa? Wallahi saide ka za6a koni ko ita, Amma Bazan ta6a yarda ka aure ta ka shafamin qanjamau ba, saide mu rabu...." Ummah ta kalli Babban Yaya tace "Naufal meyasa....?meyasa zaka fad'i wannan maganar?" ta qarasa maganar tana dafe kanta dayake barazanar rabewa gida biyu πŸ€¦πŸ»β€β™€οΈ? Cikin tashin Hankali Waheeda ta zaro idonta😳 Wanda yayi jajir kamar gauta saboda kuka, kamar ba itace take ihun kuka yanzu ba Kallan Ummah tasake yi ko zata qarya ta maganar da Babban Yaya yafad'a, Amma saitaji Ummah tayi shiru, ta kalli su Daddy har yanzu kansu yana qasa sun kasa kallan mutanan falon, cikin tashin Hankali tace "Zaman Zina? Ni wallahi bazan yarda ba, banason sa, bazan iya Zaman aure dashi ba....." tatashi tayi d'akinsu da gudu cikin tsananin kuka Wani irin kuka ne yataso masa, yau shi Waheeda take cewa bata sonsa, wani irin abu yatokare masa maqoshi, ko yawu yakasa had'iyewa. Ummi ta Kalle shi tace"Naufal jiranka nake, nabaka za6i tun d'azu kayi shiru, kana tunanin zan yarda kahad'ani kishi da wannan yarinyar ne? Wallahi bazai iyu ba saide asan nayi, zanje in fad'a agida yanzu yanzu " Baqin cikin kalmar da Waheeda tafada masa ne yake addabar zuciyar sa, jiyake kamar yafashe da Kuka kozaiji sauqi Amma kukan yaqi zuwa, ga Kuma wannan yarinyar datake qara masa wata damuwar. Cikin 6acin rai Shima yatashi tsaye, cikeda tsawa yace" toki fad'a mana, so what....? Idan kin fad'a musu kiqara musu da cewa Bana sonki, Bana qaunarki, bazan iya zama dake ba, saboda bakya respecting iyayena " Yajuya ya nuna mata Hajiya Anty sannan yaci gaba da fad'in"matar dakika raina kike mata Kallan sa'arki itad'in mahaifiyata ce..." Lokaci d'aya ummi ta qame a wajan, gabanta yafad'i, cikin mamaki ta bud'e bakinta, takasa rufe shi Babban Yaya yahad'e hannun sa waje d'aya πŸ™πŸ»ya kalleta yace "Dan Allah Ummi kifita daga cikin rayuwa ta, na roqeki" Cikin kuka ummi Tajuya tafice daga gidan, Shima Babban Yaya batare daya kalli iyayen nasu ba yafice cikin sauri, saboda zuciyar sa tagama karyewa, qiris yake jira yafashe da kuka, yana zuwa compound yashiga motar sa yamata key yabar gidan a d'ari da Sittin, Kai tsaye gidansa ya nufa, yanda yake danna Hon yasa maigadinsa yabud'e masa da sauri, shigowa had'ad'd'an gidan nasa yayi tareda parking din motar sa, yad'ora Kansa akan sitiyarin motar yayi shiru, har yanzu maganganun Waheeda yawo suke masa a ransa, yana jin yanda wayarsa take qara Amma yaqi dubawa, saida kira na uku yashigo sannan ya d'auka Daga d'ayan bangaren Mashkur yace " Bro... Ina kabar wayar ne?" Sai a lokacin kukan dayake dannewa agida yataso masa, fashewa yayi da Kuka harda shashsheka, daqyar maganar sa take fita, cikin kuka yace "Mashkur bata sona..." ❀️ 1/28/22, 20:51 - Ummi TandamaπŸ˜‡: SQ Cikin sauri mashkur yace "wacece? Wacce yarinya ce wannan tasaka friend d'ina kuka haka?" Kai tsaye Babban Yaya yace "Waheeda!" Mashkur ya gyara zamansa yace "Waheeda Kuma? Ba sister d'inka ce ba?" "Sister nace" Cikin mamaki mashkur yace "but... tayaya...." Babban Yaya ya katse shi yace "she's my Cousin Sister" "Amma friend abun ya d'auremin Kai dayawa, Wai kanaso kacemin Dama itace wadda kake cewa kanaso bazaka iya rayuwa batare da'itaba? Itace wadda akanta mukaje Saudia muketa ruwan Addu'ah?" πŸ€” Ahankali Babban Yaya yace "itace...., inason ta mashkur, but nafad'awa su Daddy d'azu, shine tace musu Wai ita bata sona..." "dakata Bro,tayaya kake tunanin zatace tana sonka dan Allah? Koni Nan nayi tunanin Kai yayanta ne uwa d'aya uba d'aya, haka kawai Kai tsaye yarinya taji kace zaka aure ta, Dan Allah tayaya kake tunanin zata amince Karon farko? Kaine kake mata Kallan masoyiya, ita Kallan yaya take Maka, Amma kayi hakuri, kabar komai yalafa, insha Allah zata fahimce ka, kayi hakuri " Babban Yaya yakashe wayar, ba tareda yace komai ba, sannan yafuto daga motar yashiga ciki ** *** ** Sa'eed ya kalli Ummah yace "Ummah ku fitar damu daga duhu mana" Yasake Kallan iyayen nasu maza yace "Daddy, Uncle Dan Allah kuyi mana bayani, me Babban Yaya yake nufi? Tayaya zai iya auren Waheeda Bayan shi Yayanmu ne?" Daddy yayi ajiyar zuciya yace "Naufal zai iya auren Waheeda" Yanbiyu da Sa'eed da Sa'ad suka maida Kallan su wajan Daddy Daddy yaci gaba da fad'in, "koda ace Naufal bai bud'i baki yace zai auri Waheeda ba Toni dakaina zan d'auketa nabashi, saboda banta6a tunanin Yaron Nan Huzaifa zaimin haka ba, ashe bashida tarbiya tunda har zai iya Kallan idonmu, a matsayin mu na iyayensa, ya fad'a mana irin wannan maganganun,abinda yake faruwa Wanda ku Baku saniba shine.... Tun muna Yara nida Usman ne kawai mukai karatun boko, Yaya Habu baiyi ba, shiyasa Lokacin da muka bar nijar muka dawo Nigeria da zama, a lokacin muka zauna da Yaya Habu akan Garin dazamu Yada Zango, a lokacin ya nuna mana shi yana jin dadin Zaman Garin jigawa, saboda haka mubashi wata dukiyar tamu da mukai gado a wajan iyayen mu, ya zauna yaci gaba da juya mana ita acan qauye, mukuma muje birni muyi abinda muka ga yadace A lokacin babu Wanda ya haihu acikin mu duka mu ukun, Bayan mun dawo Nan da zama a lokacin muka qara karatu, mukasa iyayenku mata a a makaranta, Antynku tana fara karatu Sai Allah yabata ciki, Tasha wahala a lokacin, Yaya Habu yazo ganinta, anan yake sanar damu cewa Shima me d'akinsa tasamu juna biyu, munyi farinciki sosai, Bayan wasu watanni Matar Yaya Habu ta sauka, Aka sakawa yaro suna Yahya, a lokacin muka shirya muka tafi jigawa Wajan suna, tun muna hanya Ummanku take cikin damuwa, saboda tasan zata had'u da danginmu na Niger a gidan Yaya Habu, Kuma sha'anin surutun dangi, tabbas Sai sun fad'a mata magana akan haihuwa, na tambayeta dalilin damuwar ta, ta fad'a min komai bata 6oyemin ba, ashe aloakcin Uncle d'inku dakuma Hajiya Anty, suna jinmu, munje anyi taron suna lafiya angama lafiya, abinda Ummanku take gudu saida yaso yafaru, domin kuwa duk Wanda yaga Anty Da tsohon ciki ita Kuma bata dashi saide su dinga yimata wani Gani-Gani, saida na tsawatar musu Washe Garin haihuwar Yahya a ranar Antynku ta haifi Naufal, Halaccin da bamu ta6a tunanin zasu mana ba itada Usman shi suka mana, saida suka kira Yaya Habu Dani da umman ku, sannan suka d'auki Naufal suka bamu shi halak Malak, Dafarko naqi yarda nakar6a, saboda suma shi kad'ai suka mallaka, Amma sai Yaya Habu yace mana mukar6a tunda sune suka bamu, tunda ita Antyn tafara haihuwa insha Allah zata sake Haifar wani, Amma yanzu mubarshi ta shayar dashi, saimu kar6eshi, tunda muka dawo gida Ummanku take kula da Naufal, tsakanin sa Da Antynku shine shayarwa dakuma wasa irin na d'a da uwa, har Allah yasa aka yaye Naufal, tazo da kanta ta kawo mana shi,a lokacin yaqi yarda ya zauna damu duk da yasaba da ummanku, dare yanayi zai fara kuka yana Kiran Anty, haka muka haqura saida ya tasa, sannan ummanku ta kar6eshi, a lokacin da hankalin sa Sarai ya dawo gidannan, yasan komai, yasan bamu ne muka haife shi ba, Amma abun mamakin koda wasa baita6a nunawa wani cewa bamune iyayen saba. Ahankali ahankali soyaiya take sake shiga tsakanin sa da ummanku, har suka saba babu inda zasuje ace shi ba d'anta bane, cikin dangi kowa yasan Yaro na Ummah ne Amma Anty ce ta haifeshi Bayan wani lokaci tun muna jiran Antynku tasake haihuwa har muka gaji muka barwa Allah, muka d'auki son duniya muka d'ora wa Naufal duka mu hud'un, har tsawon shekara goma A lokacin kamar wasa ummanku tafara zazza6i muna zuwa Asbiti akace tanada juna biyu, a lokacin Nan gidan Antynku tatare take kula da komai, har Allah yasa ummanku ta sauka ta haifi Yan biyu maza, nida Usman Muka sanya musu Suna Sa'ad dakuma Sa'eed Daga baya tasake samun wani cikin muka sanya mata sunan mahaifiyar mu, wato Maryam, Bayan shekara biyar tasake haihuwar wasu yanbiyun muka sanya musu suna Intisar dakuma Ihsan, a lokacin munyi tunanin Usman da Antynku zasu kar6e Naufal daga wajanmu, Dan har Ummanku tafara zazza6i tana tsoron arabata dashi saboda yanda yashiga ranta, tasaba dashi fiye da 'ya'yanta na cikinta, Amma koda wasa basu ce mu basu Shiba, Bayan shekara biyu da haihuwar su Ihsan muka sake Haifar Waheeda. Tunda aka haifi Waheeda Naufal ya liqe mata, tun alokacin muda kanmu mukasan cewa yana qaunar ta sosai, shaquwar su ta daban ce, shine meyi mata wanka, shine goyo, shine siyo mata sweet, gashi ita Kuma batajin magana, Amma haka zai zaneta yamata hukunci yanda ya kamata, Dafarko munyi tunanin soyaiyar dayake mata ta aure ce, to damukaga yanda yake zaneta idan tayi laifi, yake mata hukunci irin Wanda koda ace mune zamu mata hukunci to irinsa zamu mata, Sai muka saduda muka daina tunanin komai akan alaqar su, muka bar komai a matsayin shaquwa,tunda yanbiyu maza kansu yana had'e, suma yanbiyu mata kansu ahad'e yake, Maryam kuwa tana d'akin mijinta, shiyasa bamu damuba Dan shaquwa me qarfi tashiga tsakanin Naufal Waheeda, to yanzu Kuma ga abinda Allah yasa ya kasance, wannan shine labarin. " Shiru falon yayi, Ummah de tana mamakin Naufal Wai yau shine yake cewa yana son Waheeda, inda tasan cewa haka abubuwa zasu faru, da tuni Waheeda ta dad'e a gidansa, Hajiya Anty kuwa farinciki takeji acikin ranta, Allah yagani tana mutuqar kaunar Waheeda, tanaji da yarinyar sosai, Sai gashi yau Naufal d'inta yafad'i abinda yake ransa, dama ta dad'e tana wannan zargin, to Abaya tana tsoron ace ya nuna yana son Waheeda, saboda su kansu ba Susan tayaya zasu yiwa yaran bayanin abinda yafaru Abaya ba, Amma yanzu da Allah yasa hakan tafaru, ai shikkenan. Yanbiyu sukai ajiyar zuciya, yanzu ashe Babban Yaya Yaron hajiya Anty ne? Sukuwa su Sa'eed kasa magana sukai, haqiqa idan hakane sunfi kowanne qanne sa'ar samun Yaya nagari kamar Babban Yaya, Kuma Waheeda da taqi data so, Zaman aure dole πŸ€— Wayar Daddy tayi qara, ya d'auka tareda fad'in, "minister yaya gida ya iyali?" "Alhamdulillah Alhaji Umar, ashe Kuma abinda yasamu Waheeda kenan..." Daddy yace "wallahi" "kayi hakuri Alhaji Umar, kasan Yaron yanzu ka haifeshi ne baka haifi halinsa ba,Nan uwarsa ta zaunar dashi tagama hure masa kunne, Amma ba laifin Huzaifa bane, kuyi hakuri Alhaji Umar" Daddy yayi wani murmushi me ciwo yace "Babu damuwa Alhaji, ai har wanima yafuto, Kuma mun bashi" Cikin sanyin jiki minister yayiwa Daddy sallama, shi Kansa baiso Huzaifa yamasa haka ba, da har yana murna zai samu jikoki kyawawa πŸ₯Ί 'Yanbiyu ne suka tashi sukabi Bayan Waheeda d'aki, suna zuwa suka ganta a kwance akan gadon ta zubawa waje d'aya ido tana kallo tana zubar da hawaye Zama sukai kusa da'ita, inti tace "Waheeda kiyi hakuri, nasan abinda ciwo mutum kana soyaiya dashi Amma saboda wata cuta ta sameka yagujeka, wallahi Huzaifa yabamu mamaki, Allah yasaka miki, Amma tunda bakida haqqinsa, ai gashinan yanzu kin samu Wanda yafi shi komai da komai, ga kud'i, ga kyau, ga aji, ga kwalliya, ga Kuma farin jini, sannan kinsanshi kinsan halinsa, uwa uba ma d'an uwanki ne " Ihsan tace" wallahi kuwa, Allah sarki Didat Shima yabani tausayi wallahi, ashe da gaske yake yana son Waheeda, kiduba kiga yanda ya yarda zai aure ta a hakan, Amma yanzu tunda ga Babban Yaya Nan Shikkenan, saikiyi hakuri ki aureshi, Su Daddy sun fad'a mana Hajiya Anty ce ta haifeshi, saboda haka saiki daina cewa zakiyi Zaman Zina dashi... " "Dan Allah kurabu Dani, waiku idan ku akace zai aure ku zakuji dad'i ne? Tayaya zan iya Zaman aure dashi? Yayana? Tun Ina qarama da wannan fuskar nake Kallan sa" Ihsan tace "to Sai menene Dan kin Kalle shi a matsayin yayanki? Nawa akayi hakan?" Waheeda ta goge Hawayen idonta, tatuna lokacin data nuna masa Breast d'inta, da yanda take rufa masa asiri idan ya had'a plan d'in rabuwa da yanmatan da ake had'ashi dasu tatuna lokacin dayake fad'a mata zata Iya auren me kama dashi meyasa shi bazata aure shi ba? Tatuna lokacin dayake cemata wadda yakeso suna kama da juna, Kuma sunan su daya , Amma karta fad'awa kowa tatuna yanda take fad'awa jikinsa any how, ta rungume shi yanda takeso, gaba d'aya yagama jin d'umin qirjinta tasake tuna yanda take kokarin nuna masa Breast d'inta yana kauda Kai Amma saida ta nuna masa, baqin ciki yakamata, cikin kuka tace "yacuceni,yagama Dani, shikkenan yagama ganin komai...." Su intisar da basu fahimce ta ba sukace "me kike nufi?" Cikin rashin kunya tace "bansani ba, Kuma ai bayansa kukebi, bakwa sona Dama can nasani" Ihasan tasaki dariya tace "inti, dole ne muje muyi anko, muna murna da wannan aure" Waheeda tace "uwar anko zakuyi ba anko ba" Intisar tace "to karde kimana rashin kunya yarinya" Tace "Nayi..., ku kashe ni idan kunso" Intisar tayi murmushi tace "da ace Dane, zamu kashe ki mukai wa Ummah gawarki, Amma yanzu ba zamu kashe kiba, saide mu barki araye danki auri Babban Yaya" Daga Nan suka fice suka bar mata d'akin Suna fita ta kalli hannunta, tacire zoben da Huzaifa yasaka mata tayi jifa dashi, taci gaba da gunjin kuka. Washe gari Hajiya Anty da qawayenta suka shirya aka maidawa su Huzaifa lefen su, ko tsinke basu d'auka aciki ba. Har tsawon sati d'aya, Waheeda bata sake da kowa ba a gidan, tun yanbiyu suna bin kanta, har suka daina, Ummah ma tayi Tata nasihar Amma a banza, Waheeda Gani take sun kasa fahimtar tane, tayaya zata Iya Zaman aure da Babban Yaya? Su kwanta gado d'aya,ta tsotsi bakinsa, tamasa romance, abinda take karantawa a littafi Shima tayi masa, ta'ina zata fara hakan? Ina taga fuskar dazata masa duk wad'annan abubuwan? Kwata kwata falo ma Dena futowa tayi, duk inda tasan zata had'u da Babban Yaya gujewa shiga wajan take, gyaran jikin data fara zuwa ma Shima tadena zuwa, Daddy daya ga abin Nata Bana qare bane, saiyace surabu da'ita, yasamu Uncle Usman sukai magana, washe gari kuwa Yaya Habu yazo, suka gama abinda yadace, Aranar aka d'aura mata Aure da Babban Yaya akan sadaki naira dubu 'Dari, Babban Yaya yana tareda Mashkur Wanda yazo qasar shekaran jiya, yana jin farinciki a ransa but idan yatuna da Waheeda, jikinsa yana yin Sanyi Yan gidansu Ummi sunajin labarin 'Daurin auren suka tattaro kayan su na lefe da aka Kai, suka dawo dashi, saboda suma anasu bangaren babu yanda basuyi da Ummi ba, Amma tace ita bata shirya kar6ar qanjamau ba Da yamma gidan baqi sun zazzo duk da bawani taro zasu yi ba, Amma maqota sun shigo musu,gakuma tawagar Baba Habu, Waheeda tanajin labarin 'Daurin aurenta da Babban Yaya taji wani irin zazza6i yakamata, lokaci d'aya tafara rawar Sanyi, jikinta yayi zafi zau..., Hajiya Anty da taci kwalliya cikin wani leshi me mutuqar tsada, Sai walwali take, tashigo 'Dakin ta dubata, sannan tayi mata allura, ruwan Sanyi ta d'ebo zata koma d'akin ta goge mata jikinta, saiga Babban Yaya yashigo gidan kana ganinsa kasan yana cikin damuwa, Kallan sa Anty tayi, duk ya fad'a saboda tunani, bashi ruwan tayi tace "wuce kaje ka gogewa matarka jiki,jikinta yayi zafi dayawa, zazza6i takeji" Kansa ya Jinjina ya kar6i ruwan da towel yace "to Anty" Kofar d'akin yatura yashiga, tana tareda 'yanbiyu, idonta biyu, Amma tanajin qamshin turaren sa ta Lumshe idonta kamar me bacci, yanbiyu suna ganin shigowar sa suka fice daga d'akin, ajiye Robar hannun sa yayi, yacire Babbar rigar jikinsa, ya ajiye ta agefe, sannan ya zauna agefen gadon setin kanta Zuba mata ido yayi yana kallanta, d'an qaramin pink lips d'inta ya Kallah yaji ya birgeshi kamar yad'ora nasa akai yayi kissing. Hannun ta yakama yariqe cikin nasa, yaji zafi sosai, ya sunkuya yayi kissing goshin ta, rigar jikinta yad'age sama, yafara goge mata cinyoyin ta,sannan yafara kokarin cire mata rigar gaba d'aya, Bayan yacire rigar tanajin yanda yake 6alle mata hook d'in brezia d'inta, Amma kwata kwata taqi bud'e idonta ta Kalle shi, wani irin takaici takeji a zuciyar ta, Wai yau Babban Yaya ne yake mata haka, kuka take son yi Amma tahana kanta, saboda bataso ma yasan cewa idonta biyu Wata irin wawuyar ajiyar zuciya ya sauke lokacin da yayi tozali da cikakkun nashanunta,qare musu kallo yayi ko'ina yacika sosai, Yan qananun nipples d'inta ya Kallah yaji kamar yad'ora bakinsa akai yayi ta tsotsa, hannun sa har rawa yake yad'ora mata towel din a wajan yana gogewa, ahankali yake gogewa baya son yadaina Kuma baya son ya tasheta daga bacci, tun yana gogewa cikin hayyaci harya fara dannawa kad'an kad'an batare daya Sani ba, qaran da wayarsa tafara ne yasa ya dawo hayyacinsa, Bai dauki wayar ba, Sai yayi sauri ya qarasa goge mata jikin, yabude sif d'insu yad'auki wata rigar yasaka mata, sannan yafuto daga d'akin Tanajin fitarsa wani irin hawaye yazubo mata, tasaka hannu ta share, taja Bargo tashige ciki gaba d'aya, har kanta. Su Ihsan ne suka dawo 'Dakin, bargon intisar ta janye, suka ganta da wani kayan, cikin murna Ihsan tace "Laaaa kinga ma jikin da sauqi, harta sauya Kaya" Intisar ta kalleta tace "Waheeda, kukan me kike ne? Waike Dan Allah bakya gajiya da wannan kukan ne? Haba ayitayin abu kusan sati d'aya? Duk kinsa Babban Yaya yarame, saikace wata autar mata, shine ma yake bin kanki wallahi..." Cikin masifa tatashi zaune tace "eh ai Dan bake yayiwa abinda yamin bane, kinsan me yamin ne dazaki hanani kuka? Kun zo kun dameni, aikin banza..." Intisar tace "yau Kuma? Keda kike mana iyayi kina cewa yayanki ne in'aka bibiyama yafi sonki akan mu shine Kuma yau Zaki na cewa muka San meya miki? Da yau kuka fara fad'a Kuna shirya wa dazaki mana wannan tambayar?" Waheeda ta rushe da Kuka, kwata kwata hankalin ta ba'a kwance yake ba, idan tatuna yanda yagama lugwigwita mata qirji yanzu, saitaji inaaa! bazata iya zama dashi ba, tama manta dasu Ihsan take magana, cikin kuka tace "Allah idan yasake min irin abunnan bazan yarda ba saina rama, ba duka ba saide ya kasheni......." ta qarasa maganar cikin tsawa! Ihsan da intisar suka had'a ido sukayi murmushi tareda barin d'akin, Dan sunga alama an shiga fagen Daba nasu ba πŸ˜‚ Washe gari da safe, Maya tazo gidan itada yayanta Safwan, a lokacin duk family d'in Suna Nan, Daddy da uncle suna duba wasu takardu, Babban Yaya yana Kallan wasa a TV, Sa'ad da Sa'eed sunata dariya ganin yanda wasan yake gudana, Hajiya Anty da Ummah suna gyara kayan lefen Babban Yaya da aka dawo dashi, duk an cire wasu abubuwan, Anty tana rubuta abunda aka d'auke zata sake siyowa Waheeda wasu, Yanbiyu suna Kallan waya suna dariya, Waheeda ce kawai batanan Ummah ta Kalle su tace "A a Maya,kune a gidan namu kenan, sannunku da zuwa" Hajiya Anty cikin tsokana tace "Su Maya amare"πŸ˜ƒ Murmushi Maya tayi tace "Anty Ina take ne?" Hajiya Anty tayi murmushi tace "tana d'aki kishiga mana" Maya ta sunkuyar da kanta qasa tace "A a Anty, ai wajanku nazo gaba d'ayanku" Babban Yaya yajuya ya kalleta, shide yarinyar tana birge shi, saboda tanada Hankali sosai ga nutsuwa, shiyasa ma ya aminta da qawancen su itada Waheeda, yasan Waheeda zata koyi abubuwa dayawa a wajan yarinyar Ihsan tace "to Bari nakira miki qawar Taki" Tana zuwa d'akinsu taga Waheeda a kwance da waya a hannun ta, tace "kizo Maya tazo" Cikin sauri Waheeda ta miqe, dama tana so taga Maya, tana so ta fad'a mata abinda yake damunta ko zata bata wata shawarar Cikin sauri kuwa ta iyo gaba Ihsan ta take mata baya, suna zuwa falon ta ganshi a zaune tareda su Sa'eed, gabanta ne yafad'i, cikin sauri tayi qasa da kanta, Shima yana ganin futowarta gaba d'aya saiya Rasa nutsuwar sa, yama manta yana zaune ne da iyayensa da Kuma qannansa a falon, yazuba mata ido yakasa d'auke Idonsa akanta, Hajiya Anty datake gyara Zaman inner wears acikin akwati ta Kalle shi tayi murmushi, dama de tana tunanin da niyya Naufal yasiyo wannan Brezia d'in manya daidai Waheeda, kamar yasan da'ita za'ayi auren. Sa'ad da Sa'eed suka kalli Babban Yaya suka had'a ido suna Daria qasa-qasa, Sa'ad yayi qasa da murya yanda Babban Yaya bazai ji ba ya cewa Sa'eed "sainaga kamar Dama yana ciki..." πŸ˜‚ Sa'eed yace "nima tunanin danake kenan, Sai yanzu nake ganin alamun hakan" 'Dagowa sukai daga gulmar suka fuske kamar basu ba😎 Har Waheeda ta zauna kusa da Maya Babban Yaya bai daina kallon ta ba, ahankali yad'auke Kansa daga gareta, yana juyowa suka had'a ido da Uncle Usman daya zuba masa ido tun d'azu yake Kallan sa πŸ˜‚ cikin kunya yafara shafa lallausar sumar Kansa tareda sunkuyar da Kansa qasa Waheeda ta kalli Maya tace "Sai yau kika ga damar zuwa qawa" Maya ta kalli Waheeda tace "qawa Ina tsoron zuwa wajanki ne, nasan namiki laifi, bansan tayaya zan miki bayani ba..." Cikin rashin damuwa Waheeda tace "menene yafaru?" Maya ta kalli kowa na falon tahad'e hannunta biyu waje d'ayaπŸ™πŸ» cikin rawar murya tace "Daddy, Uncle, Ummah, Anty, Babban Yaya, Qawata, Dan girman Allah ku yafemin, haqiqa nasan na aikata muku laifi, nasaka ku cikin wani Hali, Amma ba komai ne yasa nayi hakan ba Sai saboda taimakon da Babban Yaya yata6a yimin lokacin da muka shiga cikin wani hali nida iyayena, yatemaka mana a lokacin da muke buqatar temakon,.... " Jin wannan furucin Nata yasa hankalin kowa ya dawo kanta, Sai kowa yazuba mata ido yanaso yaji abinda zatace, Daddy yace"menene yafaru Maryam, fad'amana muji" Kanta ta sunkuyar tace "Gaskiya Waheeda bata d'aukeda kowacce irin cuta, lafiyarta kalau, tun muna ss2 nafahimci cewa Babban Yaya yana sonta, tundaga lokacin naci d'amarar temaka masa akan Waheeda, Ina bata shawara sosai akansa duk Dan naja ra'ayin ta, to Amma Naga hakan bata samu ba, saboda koda yaushe abinda take fad'a min d'ayane shid'in yayanta ne, Ina tunanin mafita saina ji har ankawo mata kayan lefe, narasa yanda zanyi in rabata da Huzaifa, kawai rannan Sai take fad'amin zasuje Asbiti ayi musu text, da wannan damar nayi amfani nasamu family Doctor d'inku wato Doctor Khamis, na fad'a masa komai, anan Shima yabani goyon baya, ya tambaye ni Dame nakeso ya temaka min, Kai tsaye nafad'a masa tunda shi Babban likita ne nasan yanada alaqa da wasu hospital d'in dayawa, inaso duk asbitin da Waheeda taje a fad'a mata cewa tana d'aukeda cutar qanjamau, ta wannan hanyar ne kawai zan gane wannan Huzaifan datake rawar Kai akansa shin yana mata soyaiyar Gaskiya ne kokuma ta qarya? Idan soyaiyar gaskiya yake mata to zanji dad'i nasan koda qawata ta aure shi zaici gaba da sonta, idan Kuma duk qarya ce, to lokaci zai nuna, Doctor khamis yabani goyon baya sosai, Kuma Alhamdulillah yanzu gashi gaskiya tayi halint...... " Kafin Maya ta qarasa magana Sai ganin Waheeda sukai tatashi tsaye tashaqe mata wuyaπŸ˜‚πŸ™ŠπŸ™†πŸ»β€β™€οΈ? Sosai suka kama dambe, Maya tana kokarin qwatar kanta Waheeda kuwa idonta yarufe takama Maya Sai dukanta take Su Ummah ne suka tashi da Anty da Kuma yanbiyu suka fara rabiya, Amma Waheeda tayi wa Maya wani irin ruqo kamar ba qawa da qawa ba πŸ˜‚πŸ˜‚ Cikin kuka Waheeda tace "daga yau babu ni babu ke, karki qara zuwa inda nake, dama can kema nasan bakya sona, tun tuni nagane take takenki..." Wani irin murmushi Babban Yaya yayi,haqiqa dole ya kyautatawa Maya, tayi masa abinda bazai ta6a mantawa ba,dama ta dalilin tane Waheeda bataje Saudia ba saboda Ummah taji suna waya, yanzu kuwa yayi alqawarin had'ata da qawar Tata sutafi Saudia tare, saisuci gaba da damben acan πŸ˜‚ Ummah ta kalleta tace "bazaki saketa ba?" Cikin kuka Waheeda tace "to Ummah meyasa zatasa a aura min Wanda banaso? Ita uwata ce?" Uncle Usman ya kalli Babban Yaya yace "Kai tashi kaja matarka kubar gidannan" Ummah ma tace "eh wallahi, ni nagaji da fitinarki Waheeda, memakon ki godewa Allah bakida cutar komai, saide ki kama dambe? Wuce kibishi kutafi gidanku mun yafe zamanku a gidannan, Allah yabada Zaman lafiya" Ahankali yatashi yanufeta, har zuwa lokacin hannunta yana jikin hijabin Maya Wanda taqi saki, yana zuwa yasaka hannu yacire mata Nata hannun, sannan yajata zasu bar falon, ihun kuka Waheeda tasa tana fad'in " Ummah dan Allah kuyi hakuri, ni wallahi Bana sonsa, daku zan zauna, Ummah!, Anty!!" Ummah ta d'aga murya tace "Nayafe Waheeda, kuje can ku qarata" Haka suka futo daga falon har zuwa wajan motar sa, yana zuwa yabud'e mata tashiga, sannan yarufe Shima yashiga, fita sukai daga gidan suka d'auki hanyar gidansa, tunda tashiga motar takifa kanta acinyar ta tana gunjin kuka, yanajinta bai hanata ba, sunyi Nisa da tafiya yayi tunanin zatayi shiru Amma yaji shiru yarinya Sai kuka take masa, mamaki ya kamashi, Wai shine yau Waheeda take gudu. πŸ˜– jikinsa ne yayi Sanyi, ahankali yafaka motar agefen titi yakifa Kansa akan sitiyarin motar, Waheeda tana kuka taji sun tsaya, batareda ta d'ago kanta taga dalilin tsaiwar tasu ba taci gaba da Kuka, Ahankali takejin wata shashshekar kukan tana tashi acikin motar, cikin mamaki ta d'ago kanta tazuba masa jajayen idonta, mamaki yasake kamata ganin Babban Yaya yana kuka da Idonsa, abinda bata ta6a ganiba a tarihin rayuwarta, lokaci d'aya ta nemi Nata kukan tarasa, cikin zuciyarta tace "Kuka?" πŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒ 1/28/22, 20:51 - Ummi TandamaπŸ˜‡: WN Rikicewa tayi tarasa Yaya zatayi? Babban Yaya da Kuka? Tome aka masa dazai kama yimata kuka? Ita yanzu Yaya yakeso tayi ne? Bata ta6a ganinsa yana kuka ba, Sai hakan yasake d'aga mata hankalin ta tasake fashewa da Kuka,cikin kuka ta kalleshi takasa bashi haquri, cikin taqaici ya d'ago Kansa, Idonsa duk hawaye yace "bazaki min shiru ba saina bige bakinki anan?..." Itama cikin kuka tace "toba kaine kaqi yin shiru ba..." Hannunsa duka biyun yasaka yarufe fuskarsa, saida yagama kukansa ma'ishi, sannan yaja motar suka qarasa gidan Maigadi yazo ya gaishe su cikin ladabi, ganin yanayin uban gidan nasa ba daidai ba yasa yajuya yakoma mazauninsa Suna shiga falon ya nuna mata d'aki yace "gashinan" 'Dakin tashiga Wanda yaji kayan komai na more rayuwa, fad'awa tayi kan gadon ta Fashe da Kuka, wanne irin aure ne wannan? Babu masu rakiya babu komai ko kayan sakawa Ummah bata bataba, tayaya zata rayu dashi awannan gidan a matsayin ma'aurata? Kuka take sosai saida taji kanta yafara ciwo sannan tayi shiru Tunda sukazo gidan bai leqo d'akin datake ba, itama bataje inda yake ba, ko kitchen d'inma bata shiga ba bare yasaka ran zata dafa musu wani abun, damuwa tataru tayi masa yawa yarasa ta'ina ma zai fara lallashin ta? Ada yana lallashin tane a matsayin ta na qanwar sa wadda yakeso, yanzu Kuma zai bata kulawa da lallashi ne a matsayin ta na matarsa, to gashi tana cewa bata sonsa, Yaya zaiyi ne? Da tunani yafara yimasa yawa saiya dauki waya zai kira Ummah ya fad'a mata a aiko musu da abinci, yana kira Ummah ta d'auka tace "Yayansu yagida" "lafiya Ummah, Am... Ummah idan yaran Nan sungama abinci, sutaho mana dashi" "to zasu kawo muku, zanzo Nima nasake ja mata kunne nasan Waheeda batajin magana, karka fita ko'ina ka zauna agida ka huta Sai anjima..." Babban Yaya yariqe wayar yayi shiru, yanaso yace mata Kozai dawo da Waheeda gidane idan tagama hucewa Saisu kawo ta, to Amma yaji kwata kwata Ummah taqi bashi wannan damar ma bare yayi mata doguwar magana, kashe wayar zaiyi, saiyajiyo muryar Anty tana cewa "Amma Yaya da kun Bari yarinyar Nan tad'an sake dashi kafin sutafi, kwata kwata bamu yi mata shirin komai ba, kamar batada gata?" Ummah tayi tunanin Naufal yakashe waya, shiyasa tana cewa Sai anjima kawai ta ajiye wayar, Babban Yaya kuwa fasa kashe wayar yayi, yayi shiru yana jiran amsar da Ummah zata bayar Ummah ta kalli Hajiya Anty tace" wanne irin sakewa Kuma Antynsu? Yau tafara zama da Naufal d'in? Tafi kowa sanin halinsa acikinsu, taje tayi ta kukan idan tagaji zata daina, yanzu Hankali na ya kwanta tunda tana d'akin mijinta, kwanaki kamata nayi tana waya da Maya, bansan de kan zancen nasu ba, Amma saina ji ita Waheeda tana hurewa Maya kunne Wai wallahi ta yarda ayi mata auren, inda ace itace yarda zatayi, ai har wanka ma ita zata dinga yiwa mijin, har abar zata kama ta wanke.... " Babban Yaya yazaro Idonsa 😳, dariya ta kamashi cikin sauri yakashe wayar kar Ummah ta d'auka taga waya a kunne Hajiya Anty tace"mun shiga uku Yaya, yaran yanzu ka haifesu baka haifi halinsu ba, to ai yanzu saitaje ta wanke ta yayansu" πŸ˜‚ Ummah tace "shiyasa na dage akan ayi mata auren, Hankali na zaifi kwanciya" Babban Yaya yadinga dariya ad'aki shi kad'ai,yana mamaki Waheeda ce tafad'i irin wannan maganar? πŸ€”Shiyasa daya tambayeta laifin me tayiwa Ummah tayi shiru taqi fad'a masa? Ummah bata Bawa yanbiyu abincin sun kawo ba, Sa'eed tabawa yakai musu,Bayan tafiyarsa Babban Yaya yaje yayi nocking d'akin tanajinsa taqi bud'e masa haka ya haqura yajuya Abu kamar wasa kwata kwata Waheeda taqi bud'e d'akin, inde taji alamun yana gida saita rufe d'akin ta, babu abinda take a gidan, tanajin yafita, saita futo tayi harkokinta Takoma d'aki, abinda tasa aranta shine itade bazata iya wannan rashin kunyar da Babban Yaya ba, domin kuwa rayuwar aure daban, rayuwarsu kafin aure daban, Gara suci gaba da tafiya Ahaka Babban Yaya tun yanabi takanta harya dawo ya share ta, yau tanajin qaran TV afalo tafuto daga d'akin, lemo ne a gabansa dakuma computer yana typing, d'agowa yayi ya kalleta sau d'aya yamaida Kansa ga rubutun dayake Zama tayi aqasan kujerar dayake zaune, ta sunkuyar da kanta qasa, batare daya kalleta ba yatashi daga wajan zai wuce d'akinsa, cikin sauri tatashi tabi bayansa, d'akinsa yashiga zai rufe kofar saigata kamar an jefota, d'aure fuska yayi yace "menene Kuma? Inace gudu na kike?" Wasa tafara da yatsun hannunta, idonta yaciko da qwalla tace "Dan Allah Babban Yaya ka temaka ka sakeni...." Cikin sauri ya kalleta, Kansa ya Sara kamar an doka masa guduma, cikin sauri yace "meyasa?" Hawaye ne yazubo mata, tace "haka Nan..." Yace "hakanan? To kiyi hakuri, bazan iyaba, because.... I luv you, sannan karki kuskura kisake min wannan maganar" Yafad'i hakan tareda juyawa zai shige d'akinsa, kuka tafashe dashi tace "Dan Allah Babban....." kafin ta qarasa maganar Tata yajuyo yahad'e bakinsu waje d'aya Lumshe idonta tayi, hawaye masu zafi suka silalo daga idanuwanta, tanajin yanda yake tsotsar lips d'inta kamar yasamu sweet, daga baya yakama harshen ta yana musu wata irin tsotsa kamar ba Babban Yaya ba, bud'e Idonsa yayi yaga yanda take hawaye kamar anbud'e famfo, ahankali yasaka Hannunsa yakama kanta yariqe,ya Lumshe idonsa yacigaba da kissing d'inta, abunda yadad'e yana mafarkin samu Sai gashi yau yayi mata shi, tana cikin hayyacinta Kuma a matsayin matarsa saida yasha bakinta sosai sannan yasake ta, yana sakinta Tajuya d'akin ta da gudu tana kuka, Shima jingina yayi da jikin kofar d'akin yana sauke numfashi, ga wata irin sha'awa datake taso masa, jiyake kamar yaje wajan Waheeda Mararsa ce ta murd'a yasaka hannu yadafe, ahankali ya qarasa kan gadon, tareda d'aukan wayarsa, yarasa wazai kira Ummah kokuma Hajiya Anty? Wazai fad'wa matsalar sa? Ummah de da'ita yasaba, yasaba fad'a mata komai, Dan haka yanzun ma ita zai nema, Ahankali yayi Dialing number ta, tana d'auka ya Lumshe Idonsa yace "Ummah, Waheeda taqi hakura har yanzu, Ummah me zanyi mata tasoni?, Ina sonta Ummah, yanzu cemin tayi insaketa fa Ummah... "ya qarasa maganar cikin rawar murya Ummah tayi murmushi tace "kashirya katafi England, zanyi maganin komai son" Kai tsaye yace "to Ummah" sannan yakashe wayar Waheeda ma anata 6angaren cikin kuka takira Hajiya Anty, saboda tasan Kota kira Ummah ba goyon baya zata samu ba πŸ˜ƒ Anty tace "Daughter lafiya?" "Anty Allah nagaji...." abinda tace kenan, tafad'i maganar cikin kuka Anty tace "subhanallah, meyafaru ne? Kimin bayani Waheeda duk Hankali na yatashi" Hawayen tashare tace "Anty ni bazan iya zama dashi ba, haka kawai saiya dinga min wasu irin abubuwa, aishi Yaya nane, meyasa zaimin haka" Anty ta dafe kantaπŸ€¦πŸ»β€β™€οΈtareda murmushi tace "to kiyi hakuri yadena, zanyi masa magana karya sake 6ata miki rai, kinji Daughter" 'Daga kanta tayi kamar ba waya take ba, sannan tace "to" tareda kashe wayar Kamar yanda Ummah ta bashi shawara rabuwa yayi da Waheeda, washe gari da safe ya shirya zai koma bakin aikinsa Driver ne yad'aukeshi, Kai tsaye yace "muje gidansu Maya" Suna zuwa driver yafuto da sari yabud'e masa motar, yaro yatura Akira masa Maya, babu 6ata lokaci kuwa Sai gata tafuto, tana ganinsa ta qarasa wajansa tace "Babban Yaya Ina kwana" Idanu yazuba mata yace "Lafiya Maya, zuwa nayi inyi miki godia" Murmushi tayi tace "babu komai wallahi, Allah yabada Zaman lafiya" Envelope yamiqa mata cikeda kud'i yace "ga wannan ki kaiwa mamanku, sannan ki shirya Bayan qawarki tagama fishi zaku tafi Saudia tare insha Allah" Cikin murna Maya tace "Babban Yaya mungode, Allah yasaka da alkhairi" Yace "Amin, idan kinsamu lokaci kije gidan ki lallasheta, kibata shawara" yafad'i hakan yana Sosa girarsa d'aya πŸ˜ƒ Tace "to insha Allah zanje" Murmushi yayi yashiga motar, yana fatan ace ta fahimci shawarar dayake nufi abawa Waheeda, fatansa d'aya Allah yasa tabata shawara irin wadda Ummah taji suna fad'a awaya πŸ™ŠπŸ™ˆπŸ™ŠπŸ™Š Kafin su qarasa Airport yaga text yashigo wayarsa daga Ummi naban haquri, shareta yayi baiyi mata replay ba, ya goge number ta daga wayarsa, ya tabbatar taji labari ne cewa Waheeda lafiyarta kalau, shiyasa takeso ta lalla6o tadawo πŸ˜‚ ** *** ** Sai wajan azahar Maya takira wayar yanbiyu suka kwatanta mata gidan da Waheeda take, sannan ta shirya tatafi, tana zuwa megadi yatareta yana mata tambayoyi tayi masa bayani sannan Yabarta tashiga A falon ta dinga doka sallama Waheeda tana kwance ad'aki tana jinta taqi futowa, Maya dataji shiru saita fara bud'e qofofin tana dubawa sannan tayi nasarar bud'e na Waheeda Mamaki ya kamata ganin Waheeda idonta biyu, qarasawa tayi ta zauna akusa da'ita tace "qawata kiyi haquri, nayi tunanin kin huce shiyasa nazo, ashe har yanzu Ina Nan acikin ranki" Ba tareda ta kalleta ba tace "aina fad'a miki NI DAKE har abada Maya" Maya tace "subhanallah, Waheeda me yayi zafi haka?nad'auka namiki gata ne akan aurenki da Babban Yaya, ashe Bahaka bane Wai Waheeda harni kika shaqe duk qawancen mu" Tashi tayi zaune, cikin masifa tace "eh na shaqe kin, kiyi abinda zakiyi, ai wallahi Maya Kin bani mamaki, banta6a tunanin dake za'a had'a baki a auramin Babban Yaya ba, kin cuceni kuma kin gama Dani" Cikin sanyin jiki Maya tace "ban cuceki ba Waheeda, temakon d'an'uwanki nayi, Duk Wanda ya zauna daku zaisan cewa Babban Yaya yana sonki, Kuma nasan cewa bazaki ta6a samun masoyi kamar saba, Babban Yaya yana qaunarki Waheeda, Kuma kun dace da juna sosai" "yanzu ke Maya idan kece akace ki auri yayanki Safwan zakiji dad'i?" Maya tace "to menene aciki? Abu d'ayane zai dameni yanda zan sake inyi masa abubuwan soyaiya na aure, Kuma Shima lokaci ne ahankali zan saba, kema kuma idan wannan ce damuwar ki toki daina,Babban Yaya zaisa ki manta da cewa shi yayanki ne, sannan karki manta da qaddara, kowa da irin tasa,Kuma munyi alqawari zamu yarda da'ita me kyau ko marar kyau" Waheeda tana jijjiga qafa cikin damuwa tace "shikkenan ya wuce, Amma karki sake min irin haka, ni banaso, Shima Kuma bazan iya zama dashi ba, saboda tsabar abun kunya rannan har kiss yamin, Ina zan Kai wannan rashin kunyar?" Maya tasaki dariya tace "yakaiki rashin kunya ne? Keda kowa yasan halinki ne haka bakida kunya? To menene ma danya miki kiss? Haka zakiyi haquri ki yarda, kema kiyi masa, wannan shawarar dakika Bani de akan za'amin aure itace zata dawo kanki, haka Zaki kama abun mijinki ki wanke" "Dan girman Allah Maya kidena min wannan maganar, kodan kinga na kulaki? Ni banason jin wannan abun kunyar,inrasa wazanyi wa hakan Sai Babban Yaya?" Maya tace "aikuwa saiki maraba da kishiya" Cikin rashin damuwa tace "kofa abud'e take, tazo ta zauna ban hanata ba" Kafin Maya tace wani abu yanbiyu suka shigo d'akin, sunci kwalliya iri d'aya ko ganesu bakayi, abinci suka ajiye mata Ihsan tace "ke ga abincin ki Nan inji Ummah" Kallan abincin tayi tace "wannan ai yayi mana kad'an, ko Babban Yaya zai iya cinyewa, yanda yake cin abinci idan yasamu waje to wallahi shi kad'ai ma zai cinye wannan" Intisar tace "wanne Babban Yaya Kuma shida yatafi England? Ni jinake ma dake zai tafi, ashe shi kad'ai yatafi, ke yanzu Waheeda ba abun kunya bane wannan? Sabon aure Amma kibar ango yatafi shi kad'ai? Kyaje yakula wasu matan acan wallahi, tunda yanzu ya d'and'ana yaji dad'in mace "πŸ™ŠπŸ˜‚ Cikin 6acin rai Waheeda tace" uwar me ya d'and'ana? Inti banason rashin mutunci wallahi, ba England ba, yatafi kafi England ma,dayau yafara huld'a da mata? Da idona na ganshi mata suna yanyameshi Sai yage musu baki yake, da idona nagani " Ihsan tace" to babu so menene Kuma yakawo kishi? Keda kike cewa bakya sonsa miye dankinga mata suna yanyameshi? d'an ball nefa, ba mata ba mazama yanyameshi zasuyi, malama kinaso kina yiwa mutane ihu ke bakya so " Tace" eh banaso, ba Kuma zan so ba, da yau yafara kula matan dazaku zo Kuna cewa nabarshi yatafi, inda ace nasan baya gidan ma da tuni Nima na kama gabana, Zaman me zanyi yanzun Ina masa gadin gida? Saikace wacce batada galihu, Nina tafi gida idan kun gama kwa taho "tafadi haka tana Jan hijabin ta tafice daga d'akin πŸ˜‚πŸ˜‚ Babu yanda suka iya haka suka futo suka biyo bayanta, saida sukazo gida sannan Maya tamusu sallama tatafi gida, sukuma suka shige cikin gida, megadi Sai tsokanar Waheeda yake yana fad'in"Amarya kinsha qamshi" Yau kwananta hud'u agida, Amma kamar bata gidan, Dafarko tayi tunanin zasu kulata, shiyasa take wuni ad'aki, dataga babu Wanda yake shiga harkar ta, saita fara futowa tana abin gabanta, daga Ummah har Daddy idan ta gaishe su daga sun amsa basa qara cemata komai, haka yanbiyu ma tun lokacin dasuka mata fad'a tamusu rashin kunya suka tattara ta suka watsar, Hajiya Anty tahad'o mata magungunan mata masu kyau, ta zaunar da'ita ta mata bayanin yanda zata dinga amfani dasu, sannan tabata haquri akan Takoma gidan mijinta, Amma Waheeda tayi mursisi taqi komawa, magungunan ma ta ajiye su taqi shan kod'aya aciki. Yau satinta uku agida, Kuma har zuwa wannan lokacin bata kira Babban Yaya ba, Shima bai kirata ba, Kuma babu Wanda yace tattara kayan ki kikoma, kowa yazuba mata ido kawai. Yau suna break fast afalo gaba d'ayansu, banda Daddy, Sa'eed ya kalli Waheeda sannan ya kalli Ummah yace "Wai wannan yarinyar Zaman me take a gidannan Ummah?" Ummah ta Kalle shi tace "gatanan ka tambayeta" Kallan Waheeda yayi yace "keme kikeyi har yanzu baki koma ba?" Idonta ne yayi qwalqwal yakawo ruwa, tana juya spoon acikin cup d'in tea d'in dake gabanta tace "ni Bana sonshi...." Sa'ad yayi sauri yace "to cemiki akai shid'in sonki yake? Banda qaddara ma me Babban Yaya zaiyi dake? Ga yanmata Nan had'ad'd'u suna bibiyarsa zai tsaya anan Ana Rena masa Hankali" Sa'eed ma yace "okay bakya sonsa ko? To Alhamdulillah, Ummah kawai idan yazo kibashi shawara yasake ta kawai" Ummah ta ajiye bread d'in hannunta tace "na fad'a masa tun shekaran jiya da mukai waya, idan yasamu lokaci Yazo ya rubuta mata takardar, saisu koma makaranta itadasu Ihsan" Sa'eed yace "Hakan ma yafi, Dan wannan yarinyar Dama ba ajin auren sa bace, kawai de Dan Allah ya rubuta Sai anyi ne, ni Gara ma dayake shirya abinda yafi masa, abinda Yayanke d'in yayi daidai, yanzu ne yasan zaiyi aure" Gaban Waheeda yayanke yafad'i, ahankali ta zaro idonta 😳batare datace komai ba Shima Sa'ad yace "eh gaskiya Kam ya kyauta" Hajiya Anty ce tashigo falon zata yiwa Ummah sallama kamar yanda tasaba idan zata tafi wajan aiki, tajisu suna fad'in eh ya kyauta Kam tace "waye ya kyauta?" Ummah tayi murmushi tace "Wai suna magana ne akan auren yayansu, kinsan jiya Daddynsu yamasa waya yace idan zai taho yahad'o wasu kayan lefen Sai akai gidansu ummin, tunda tabada haquri Kuma Shima Naufal d'in yace ya haqura zai aure ta" πŸ˜‚ Waheeda taji numfashinta yana yin sama kamar zai d'auke, gabanta Sai fad'uwa yake, takasa d'agowa ta Kalle su, sukwa yanbiyu Sai lodar abinci suke ko bakinsu ba'aji Hajiya Anty ta kalli Waheeda tace "yanzu Yaya ba zakuyi haquri da maganar Ummin nanba? Ayita yin abu de? Duka duka yaushe yayi aure dazaku sake da'aura masa wani auren?" Ummah tace "to Antynsu Yaya zanyi dashi? Jiyafa kirana yayi kamar zaiyi kuka shide ayi ayi a aura masa Ummi,yanaso yazo gobe ko jibi ayi agama magana, so yake yazo yatafi da'ita England, ita Kuma Waheeda tunda tana zaune agida, saitaci gaba da Kula da gidan, idan sukazo hutu kinga har saga gida tsaf dashi 'yar aiki ta gyara musu " Waheeda tacika tacika tazo wuya, batasan lokacin data Fashe da Kuka ba, cikin gudu tayi d'akinsu tad'auki wayar inti takira Maya, bugu biyu Maya ta d'auka tace"inti ya akayi Ina qawata? " Waheeda tasaka mata kuka tace" Maya yanzu kowa baya sona, Shima Babban Yaya yadena sona, Wai ummi zai aura, Kuma Daddy yace yazo yakawo kayan lefe idan anyi auren yatafi da ummi, Nina shiga uku na Maya ya zanyi? " taqara sa maganar cikin kuka Maya tace" kema Waheeda kinada laifi, bakya bashi kulawa dole hankalin sa yakoma kan wata" "to ya yakeso namasa Maya? Rannan fa kuka yakemin saikace qaramin yaro, ni wallahi yafi qarfina bazan Iyawa shagwa6ar saba" "babu Wanda yazo da iyawa Waheeda, kowa dakika Gani Koya yayi, kikasan me Ummin ta qulla masa? Tayaya za'ai ki zauna kinada kamar Babban Yaya?" Cikin hawaye tace "to tashi zanyi?" Dariya takama Maya, ganin duk tsiwa irinta qawar Tata yanzu Babban Yaya kad'ai yana nema ya rikita ta, tace "ni bance ki tashi ba, ba zama ba kiyi kwanciyar ki ma, lokacin dakika ce yana kuka kamata yayi kijashi ajikinki, ki rungume abinki ki lallashe shi, na tabbatar bakiyi hakan ba, Waheeda dole saikin ajiye wannan yayan agefe ki d'aukeshi as mijinki, inba hakaba wallahi tunda kikaji maganar Ummi tashigo to tsaf zai aure ta, Dan maza idan sukai niyyar qara aure ba'a hanasu,kikama hanya kitafi gidanki, kikirashi awaya kibashi haquri kiyi masa shagwa6a,tunda kince Ummah tace zaizo to idan yazo kicire kunya kinuna masa soyaiya tsantsa, sonake yanda yace zai auri ummi ya dawo da Kansa yace yafasa " Waheeda tayi ajiyar zuciya tace"zan iya kuwa Maya? " "Mezai Hana? Wai Waheeda Ina wayonki yake ne? Naga kece me Bani irin wannan shawarar, kitashi kiyi abinda nace kawai, wannan gidan naki ne ke kad'ai insha Allah qawata, babu wadda zata shigo " Ahankali tayi ajiyar zuciya tace"to Maya" sannan ta kashe wayar Kai tsaye truly d'inta tad'auko, magungunan da Hajiya Anty tabata shita fara d'auka tasaka a jakar πŸ˜‚ Sannan tadauko duk kayanta, tasaka aciki, ta janyo jakar tafuto falo Suna zaune Sai ganin Waheeda sukai tafuto da jaka Mamaki ya kamasu, basuyi tunanin wannan plan d'in dasuka had'a zaiyi tasiri akanta ba, ko sallama bata musu ba tafice daga falon cikin fishi Tana fita suka kwashe da dariya, Hajiya Anty ta kalli Ummah tace "lalle Yaya kin kawo point" πŸ˜‚ ✍πŸ? 1/28/22, 20:51 - Ummi TandamaπŸ˜‡: AL Driver tasa yakaita gidan, suna zuwa kuwa megadi ya kar6i kayan hannunta yakai mata shi har ciki, sannan yajuya yakoma gate. A falon tabar kayan Nata ko d'aki bata shiga dashi ba, tacire hijabin ta tafara gyara gidan, bata gama ba Sai wajan azahar, takai kayan d'aki sannan tayi wanka tasaka Riga yar qarama, iyakarta gwiwarta, tadafa indomie ta zauna tanaci tana kallo a TV, d'aki tashiga tad'auki magungunan ta Tasha, sannan ta kwanta tahuta, Sai wajan qarfe uku tadafa musu fried rice, ta kaiwa megadi sannan ta kulle falon tayi kwanciyar ta, kullum haka takeyi, idan tadafa abinci zata kaiwa megadi nasa, sannan tarufe falon saikuma washe gari, magungunan ta kuwa bata wasa dasu kullum Sha take, ita kanta tanaji ajikinta, yanda maganin yake mata aiki Saboda magungunan sunada kyau sosai, satinta d'aya da komawa da sukaga bata dawo ba, Sai hankalin su ya kwanta, ganin haka yasa Hajiya Anty tatura mata Dame gyaran jiki take zuwa har gida takeyi mata, kullum Maya zatazo tatayata aikin gida, ita Kuma ta zauna ayi mata gyaran jiki, wataran yanbiyu suzo suhad'u su hud'u a gidan sutayata hira, kasancewar gyaran jikin yanzu a zaune take agida babu inda take zuwa Sai yafi kyau fiyeda na wancen Karon, jikinta yayi wani fresh, ko'ina yasake cika saboda yanda Hajiya Anty tahad'ata da magungunan ingantattu masu kyau, tsawon sati uku suka d'auka anayi mata gyaran jiki da turere Kala Kala na jiki dakuma na tsugunno, yau matar tagama aikinta danhaka bata zoba, suma su Ihsan basu zo ba, gyaran gidan tayi, ko'ina yad'auki qamshi, tayi abinci daidai cikinta, ta zauna taci Sannan ta wuce d'aki, bacci ne ya d'auketa, bata tashi ba Sai wajan shad'aya, futowa falon tayi zata je kitchen ta d'ora abinci, d'azu bata Bawa megadi ba, 'yar qaramar Riga ce ajikinta, iyakarta gwiwarta, bata saka brezia ba, kana ganin yanda boobs d'inta suke a tsaye ta cikin rigar, kanta babu kitso duk gashin ya bazu a fuskarta, fatarta Sai qyalli take tana d'aukan ido kamar ka latsata jini yafuto Tana bud'e kofar d'akin tana futowa falo ta tsaya tayi wata irin miqa tareda hamma, kwata kwata bata lura da mutum a falon ba, Babban Yaya dayake zaune yad'ora kafa d'aya kan d'aya yana waya da mashkur, lokaci d'aya yanemi nutsuwarsa yarasa, soyake ya d'auke Idonsa akanta Amma yakasa, yanda ta turo qirjinta gaba yafi komai Jan hankalinsa, daqyar ya sunkuyar da Kansa yana Sosa girarsa d'aya sannan yace "inaji" Daga d'ayan bangaren mashkur yace "Dan Allah Abokina katemaka kabani number yarinyar Nan, yanzu tun dad'ewa Ina bin kanka akan yarinyar Nan Amma ka hanani number ta?" Tun lokacin daya ce inaji, Waheeda taqame a falon tana kallon sa, yaushe yazo? Duk saita rikice tarasa me zata masa, inda ace dane da gudu zataje ta fad'a jikinsa, Amma yanzu meyasa ta kasa? Anya zata Iya amfani da shawarar Maya kuwa? Kalli yanda ya shareta Shima kamar be ganta ba, ahankali ta juya zata nufi kitchen Babban Yaya ya kalleta qasa-qasa, yaga yanda hips d'inta suke juyawa, wani irin yawu ya had'iye sannan ya sauya wayar dayake da mashkur, yayi kamar da Mace yake waya, memakon yabawa mashkur amsa saiyace "na fad'a miki ko awa d'aya bazan iya a gidannan batare Dana ganki ba, tun jiya nake mafarkin had'uwa dake, ko minti talatin banyi da zuwa Bama, yanzu zanzo naganki, kibani abinda kika tanadar min" Waheeda ta tsaya cak, gabanta yana fad'uwa, sake Kallan ta yayi, yayi tunanin zata taho da gudu ta fad'o Kansa kamar yanda tasaba, yaga ta tsaya ko juyowa batayi ba, mashkur yace "man ni zakayi wa wulaqanci ko? Zamu had'une, inama magana kanamin wani irin zance" cikin sauri Babban Yaya yasake cewa "a a, karki damu wallahi, qanwata tana zaune agidan, dama itace me kula da gidan, shara, wanke wanke, da duk ayyukan gida, zata kula da wannan, Gani Nan zuwa" Qitt yakashe wayar sannan yatashi yafice da sauri, gidan Ummah ya nufa, Dama yayi tunanin zai samu kar6uwa ne a wajan Waheeda, da babu abinda zaisa Ummah ta ganshi yau ☹️ Amma tunda bai samu hakan ba, Gara yanemi Ummansa Kota d'ebe masa kewa da hira Tana ganin fitarsa ta tsugunna a wajan tafashe da Kuka,d'aki tashiga da gudu, wayar inti data manta a gidan ita ta d'auka takira layin Ihsan, Ihsan tace "Waheeda yagida" Fashewa tayi da Kuka tace "Wai Babban Yaya ne zai tafi wajan Ummi, ko magana bemin ba, yatashi yabar gidan, saboda yanzu baya qauna ta" Ihsan tace "yazo qasar ne? Kiyi hakuri Bari infad'awa Ummah, kiyi shiru" Kashe wayar Waheeda tayi, gaba daya saitaji komai ma yafice mata Arai, girkin ma fasa dorawa tayi, ta zauna a wajan tana kuka ** *** ** Ihsan tafuto daga d'akinsu, saita tsaya turus ganin Babban Yaya zaune agaban Ummah tana bashi abinci, Sai hirarsu suke cikin nishad'i Qarasawa tayi tagaidashi, sannan ta kalli Ummah tace "Ummah Waheeda ce take kuka, Wai Babban Yaya yatafi Wajan Ummi, ko magana beyi mata ba" Ummah tayi murmushi tace "jeki Ihsan" Ahankali Ihsan ta juya, Saida yaga tatafi sannan ya kalli Ummah yace "Ummah tana kallo nafa, ko sannu da zuwa batamin ba, shine na nuna mata da Ummi nake waya, nikuma da mashkur muke magana akan Ihsan, yadage Wai yana sonta" Ummah tayi murmushi me ciwo, duk da yafad'a mata abinda zaisa taji dad'i akan maganar mashkur da Ihsan, hakan baiyi tasiri a ranta ba, tafi damuwa da batun Waheeda, taga alama Waheeda bazata sauya ba, Naufal yadad'e baiyi aure ba, yana buqatar kulawar matarsa, inbanda itan ce ta sameshi ta tabbatar idan wata ya aura da tuni yafara kula wasu yanmatan,ajiyar zuciya tayi tace "to Allah ya tabbatar da alkhairi, Son kaje kakaiwa Waheeda takardar ta...." Cikin sauri ya d'ago ya kalleta yakasa magana, beyi tunanin wannan maganar daga bakin Ummah ba, haushin Kansa yaji, daya Sani be fada mata laifin Waheeda ba, cikin sauri yace "Ummah Dan Allah kiyi haqurrr....." Hannu ta daga masaβœ‹πŸ? tace "kaje kayi abinda nace kawai" Beqara ce mata komai ba yafice daga gidan, driving yake Amma baya tareda nutsuwa, tayaya ummah zatace yaje yasaki Waheeda? Ko batasan cewa sakin Waheeda daidai yake da sakin zuciyar sa ba?Anya kwa Ummah tasan irin wahalar dayasha akan Waheeda? Har yazo gidan yarasa abinda zai aikata takameme, falon yashigo anan ya ganta zaune kan kujera tana share hawaye, wucewa yayi d'akinsa, ya kwanta akan gado tareda fad'awa cikin duniyar tunani, wani tunani ne ya fad'o cikin ransa, cikin sauri yatashi yanemi paper da biro yayi rubutu aciki, ya ninke takardar sannan yafuto daga d'akin, Kai tsaye wajan ta ya nufa, yad'aure fuskarsa yace "idan ban manta ba, last time kince min in temaka in sakeki ko?" Cikin sauri ta Kalle shi takasa magana, ya kalli qwayar idonta tayi jajir da alama Tasha kuka, cikin kuka tace "Bana baka haquri ba?" Dariya ce taso kamashi, Amma sai yayi fuska yace "lokaci yaqure Waheeda, akwai wadda zatamin abinda narasa awajanki, har abada bazata iya neman saki awajena ba, saboda tana amfani da ilmin ta, ga takardar ki Nan" ya ajiye mata takardar yajuya zai fita Ihu tasaka tace "wallahi ban saku ba, babu wadda zaka aura, wallahi bazan bud'e wannan takardar ba garama kazo ka d'auke abarka, Allah ban saku ba...." kuka take sosai tana fad'a masa hakan Juyowa yayi ya kalleta yace "to idan kin gama kukan ki kulle min gidan,kitafi gidanku, Nima natafi wajan masoya yi ta" Yana fad'ar haka yafice daga falon yanata dariya, be koma gidan Ummah ba, Kai tsaye gidan Hajiya Anty ya wuce ** *** ** Cikin kuka takira Uncle Usman, yana zaune a office d'in Daddy yayi tunanin Intisar ce saboda number ta yagani, d'auka yayi tareda sallama, saiyaji shiru da alama kuka ake, zamansa ya gyara yace "Intisar meyake faruwa? Lafiya kike kuka?" Cikin shashshekar kuka tace "Ba inti bace.... Wa... Wahee.... Waheeda ce, Uncle Babban Yaya ne yasakeni, gashinan yabani takarda ta...." Uncle Usman yatashi tsaye cikin tashin Hankali yace "innalillahi wa inna ilaihirraji'un...., innalillahi wa inna ilaihirraji'un....,kina Ina yanzun?" "Ina gidansa" cewar Waheeda cikin Jan zuciya Uncle yace "Kije gidan gamu Nan zuwa" Daddy ya Kalleshi yace "meyake faruwa?" Cikin damuwa uncle Usman yace "Wai Naufal ne yasake ta" Gaban Daddy yafad'i, yace "what?! muje gidan, bari in kirashi, muje muje da sauri" Cikin hanzari suka fita ko office d'in basu rufeba Suna hanya Uncle Usman yakira Babban Yaya, yana d'auka ko amsa sallamarsa baiyi ba yafara magana cikin fad'a "ashe bakada Hankali?" πŸ˜‚πŸ™†πŸ»β€β™€οΈ? Babban Yaya dayake kwance a cinyar Hajiya Anty yace yatashi da sauri yace "Innalillah.... Uncle me nayi?" Cikin fad'a Uncle Usman yace "nikake tambaya me kayi? To duk abinda kake kabari kazo gidanku ka sameni yanzu yanzun Nan" Babban Yaya yayi shiru bece komai ba, Uncle Usman yakashe waya, Daddy yace "dabaka kirashi ba Usman, na tabbatar laifi tayi masa shiyasa yakawo qarshan Zaman nasu, shiyasa Nima ban kirashi ba, koma menene muje gidan zamuji komai ai" Uncle Usman yayi shiru Sai hura hanci yake,tunanin irin yanda zai 6atawa Babban Yaya rai yake, tayaya za'ai yasaki yarinya yamaidata qaramar bazawara? Babban Yaya yamiqe tsaye yace "Anty zanje gida, uncle yana nemana, da alama nayi masa laifi bansani ba" Cikin damuwa Anty ta d'auki wayarta tace "A a, me zakayi wa Uncle d'inka? Kaide kayi tunani me kayi masa?, kokuma inkirashi? " Kwata kwata Babban Yaya ya manta da batun Waheeda, asalima tunani yake irin dad'in da zaiji idan yakoma gidan, saboda yasan idan ta bud'e takardar daya bata taga abinda yake ciki zataji dad'i Kuma yau zasuyi kwanan farinciki, saboda haka baya tunanin wannan Kiran yanada alaqa da Waheeda Girgiza Kansa yayi yace "karki kirashi, nasan banyi masa komai ba, Bari inje kawai" Tashi tayi tace "saide mutafi, muje gidan kawai" Futowa sukai dukansu, suka tafi gidan Ummah, suna zuwa shida Hajiya Anty sukaga kowa a zaune, Daddy, Uncle, Ummah, dasu Sa'eed tareda yanbiyu, Kowa jiran zuwan Waheeda yake Babban Yaya yazauna aqasa tareda gaida iyayen nasa, Daddy ne kawai ya amsa, Amma uncle Usman kawarda Kansa Gefe yayi, mamaki yasake kama Babban Yaya, meya aikata haka ne? 'Dago Kansa yayi ya Kalle shi yace "Uncle Gani, meyake faruwa ne?" Cikin 6acin rai yace "abinda kayi ka kyauta kenan? Harme Waheeda zata Maka kasake ta?" Zaro ido Hajiya Anty dasu Sa'eed sukayi, yanbiyu kuwa har sun fara kuka, Sai yanzu ne suka San dalilin taruwar iyayen nasu Babban Yaya d'ago Kansa yace "Uncle wallahi ni ban...." Katseshi yayi batare da yaji abinda zaice ba "babu abinda zaka fadamin" Yanbiyu ne suka tashi zasu wuce d'akinsu ganin yanda ran iyayen nasu ya6aci, kuma basa masa fad'a agaban su, Amma yau Idonsu ya rufe da masifa harsun fara yimasa Ummah tace "Alhaji Usman ninace yasake ta saboda iskancin Waheeda yayi yawa" Uncle Usman yace "kuma saiya saketa? Yanzu kamar shi idan akace yafad'a wuta saiya fad'a?" Kafin Ummah tayi magana saiga Waheeda tashigo gidan hannunta aka, tana runtuma ihun kuka, ita kuka yanbiyu kuka, su Sa'ad jikinsu duk yayi Sanyi qalau Waheeda tana zuwa ta fad'a jikin Hajiya Anty tana kuka,kwata kwata bata lura da Babban Yaya dayake falon ba, idonta ya rufe take fad'in"Anty Babban Yaya yasake ni, wallahi Ina sonsa, Allah bazan dawo gidaba " Hajiya Anty ta goge Hawayen daya zubo idonta tace" kiyi hakuri, wallahi saiya maidake d'akin ki " Babban Yaya ya shafa sumar Kansa tareda dafe Kansa πŸ€¦πŸ»β€β™‚οΈ?, Sai yaushe ne Waheeda zatayi Hankali? πŸ€” Daddy ya kalli Babban Yaya yace"Naufal, kar6o min takardar " Babu musu ya qarasa wajan Waheeda yazare takardar daga hannunta, Hajiya Anty tazabga masa wata irin harara, bece da'ita komai ba Sai qeyarsa daga Sosa, ya ninke takardar yariqe ahannunsa yaqi basu, saboda yana kunyar suga abinda ya rubuta a takardar Uncle Usman yace"kabamu takarda akace malam, kariga kayi abinda kaga yadace ai saika bamu takardar muga saki nawane " Babu musu Babban Yaya yabashi takardar, saboda bazai iya jayaiya dashi ba Uncle Usman ya bud'e takardar ya karanta abinda yake ciki, Gani yayi anyi rubutu da Babban baqi cewa I LOVE YOU SO MUCH BABY WAHEEDA Tsaki yasaki, yayi wata irin ajiyar zuciya yace "af..., Alhaji Allah ya shiryi yarinyar Nan, duk ta d'aga mana Hankali" Daddy ya kar6a Shima ya karanta, ya jijjiga Kansa, sannan ya kalli Uncle Usman yace "muje Alhaji Usman" Hajiya Anty tabisu da kallo, ta janye Waheeda daga jikinta tatashi ta d'auki takardar, a fili ta karanta abinda yake ciki tace "I LOVE YOU SO MUCH BABY WAHEEDA" Su Sa'ad ma sukai murmushi suka koma d'akinsu, yanbiyu kuwa Waheeda suka kalla, haushi yakamasu kamar su daketa, tasa sunyi asarar Hawayen su a banza πŸ˜‚ Waheeda ta d'ago da sauri ta kalli Babban Yaya, taga yana mata wani irin Kallan soyaiya ko kunyar su Ummah bayaji, wata irin matsanan ciyar kunya ce ta kamata, tatashi tayi d'akin Ummah da gudu tana rufe idonta da tafin hannun ta Dariya su Anty sukayi mata tareda yanbiyu.πŸ˜ƒ Ganin hankalin su Ummah baya kansa yasa ya shafa sumar Kansa,sannan yabi Bayan Waheeda Dakin Ummah Yana shiga 'Dakin ta d'ago kanta ta Kalle shi, cikin sauri tatashi ta fad'a qirjinsa ta rungume shi, tareda sakin kukan shagwa6a Sake rungume ta yayi sosai, yafara magana qasa-qasa cikin rad'a ita kad'ai ce zata Iya jin abinda yake fad'a Sunkuyowa yayi da Kansa, dede Setin kunnan ta yace "kiyi shiru mana, menene abun kukan?" Kukan shagwa6a tasake sakar masa tace "uhm... Uhm..." tareda Dukan faffad'an qirjinsa ahankali Murmushi yayi yasake rage murya yace "nine ko?, nine nayi Miki laifi ko?" Kasa d'ago kanta ta Kalle shi tayi, tanata mamakin sa Dama Babban Yaya ya'iya magana haka ahankali irinta masoya? πŸ€”Kawai d'aga masa Kai tayi, takasa had'a ido dashi Cikin sigar lallashi Yace "to kiyi haquri... Bazan sakeba kinji?" Sake d'aga masa Kai tayi,bata yarda sun had'a ido ba yace "kin haqura?" Yanzu ma sake d'aga kan tayi πŸ˜‚ Murmushi yayi yace "kiyi magana mana" Ahankali ta motsa lips d'inta, cikin sigar shagwa6a tace "nifa naqura, ni bakamin komai ba" Tunda tafara magana ya zubawa lips d'inta ido yana kallo, ahankali yasaka hannun sa biyu yariqo fuskarta, yahad'e bakinsu waje d'aya, ahankali yafara tsotsar lips d'inta, wannan Karon wani irin dad'i Waheeda taji, ahankali ta Lumshe idonta tana kar6ar saqon, kusan minti biyar yad'auka yana kissing d'inta, ahankali yacire bakinsa daga Naga, ya kalli qwayar idonta, cikin muryar rad'a yace "your turn..." Wata irin kunya ce takama Waheeda, mamaki yagama kashe ta kamar ba Babban Yaya ba, tunani tafara kode ya manta acikin d'akin Ummah suke? πŸ€” Babu yanda ta iya haka takama lips d'insa na qasa tafara Sha ahankali, wani irin dad'i Babban Yaya yaji, ahankali yasake rungume ta yana sakar mata wani irin numfashi, tun yana haquri yanajin yanda take tsotsar lips d'insa harya kasa haquri ya qwace lips dinsa, tareda kama Nata yanasha cikin fitar haiyaci Kwata kwata mutanan falon sun manta dasu, Ummah ta kalli Hajiya Anty tace "Antynsu Bari inje toilet in dawo...." πŸ™†πŸ»β€β™€οΈ? Zuciyarta d'aya takama handle d'in 'Dakin tabud'e, a tsaye ta gansu cikin wannan hali, cikin sauri taja musu kofar tarufe gabanta yana fad'uwa πŸ™Š ✍πŸ? 1/28/22, 20:52 - Ummi TandamaπŸ˜‡: JH Qaran rufe qofar kawai Waheeda taji, tayi tunanin zai daina abinda yake, Amma saitaga yaqi daina wa, cikin sauri ta qwace bakinta, Kallan ta yake da idanunsa dasuka fara canjawa,duk jikinsa yafara mutuwa, Waheeda ta Kalle shi cikin tsoro tace "kamar qaran rufe kofar nanfa naji, waye yashigo?" Kafad'a ya d'aga yace "Ina zan Sani? Ni banji Bama" Zaro ido tayi 😳"bakaji ba? Yanzu yanzu inji qara kacemin Kai bakaji ba?to d'an bud'e ka duba kagano mana waye" Wata irin dariya yasaki yace "nizaki yiwa wayo?ke Kifita kiduba mana,nasan ma babu wata qaran qofa dakika ji, kawai kunnanki ne, kije kiduba mana may be ma basa falon" Qafafunta tafara bugawa aqasa cikin shagwa6a tace "to wayace kabiyoni? Allah saide ka duba, ni nace kabiyoni?" Murmushi yayi yahard'e hannun sa a qirjinsa yana Kallan ta yace "matata tana d'aki sainaqi binta? Kinga yanzu de abinda za'ayi shine, tunda kince kinji qaran bude qofa, kawai kiyi fuska kifita, tunda ai bamusan waye yashigo ba, idan kinada kayan dazaki d'auka kije kid'auko kawai mutafi gidanmu" Kanta ta d'aga masa, sannan ta nufi qofar takama handle d'in ahankali kamar wata 6arauniya Hajiya Anty ta kalli Ummah tace "Yaya, yanaga kin dawo? Lafiya kuwa?" Ummah tace "hmm, 'ya'yanki ne a d'akin, Dan Allah kije kifad'a musu suzo sutafi gida, Zaman ya'isa haka" πŸ˜‚ Hajiya Anty tayi murmushi, ta tabbatar akwai abinda Ummah tagani, shiyasa tafad'i haka. tace"yaya Aida kin fad'a musu, tunda ke kin Riga kinshiga"πŸ˜‚ Cikin sauri Ummah tace "A a, a a, mezai maidani Kuma? Idan sun gaji da zama zasu fito sutafi" Kafin Hajiya Anty tayi magana, Waheeda tafuto daga d'akin kanta aqasa, sum sum ta wuce tagabansu tayi d'akinsu, ummah ta kalleta tayi ajiyar zuciya, bata Jima da futowa ba Shima yafuto, hankalin sa yana kan wayarsa yana danna wa, ya maze kamar ba Shiba, Ummah ta Kalle shi, cikin ranta tace oh kamar bashi ba,ashede Yaron nawa yanada lafiya da alamaπŸ˜‚ Wajan su ya qaraso ya tsugunna sannan yace "Ummah zamu tafi" "to Son Allah yakaiku lafiya, idan kunyi mantuwa basai kun dawo ba, za'a biyoku dashi" Hajiya Anty tayi murmushi ba tace komai ba Ahankali yatashi yana Sosa Kansa cikin kunya, yafice daga falon, yana fita yasaki ajiyar zuciya, a fili yace "Allah yasa de basu gane ba"☺️ A wajan motar sa ya tsaya yana jiran Waheeda Hajiya Anty tamiqe tsaye tace "Bari intura ta sutafi" tafad'i hakan tareda wucewa d'akinsu Waheeda Tana shiga ta gansu suna hira Sai dariya suke kamar basu ba, afili tace "yau 'Yan zumuncin ne akusa kenan, Waheeda taso" Waheeda tatashi tabiyo Bayan ta, Hajiya Anty takama hannunta suka nufi compound, kafin su qarasa wajan Babban Yaya ta kalleta tace "Kina amfani da magungunan Dana baki ko?" Cikin sanyin jiki tace "inayi Anty" Hajiya Anty tace "to shikkenan kidinga Sha kullum, Kuma karki Bari yasani" 'Daga mata Kai tayi sannan tace "to Anty" Itama tace "to shikkenan Daughter Allah yakaiku lafiya kudinga haquri kinji ko?" Waheeda tace "to" Saida suka kusa zuwa wajansa Sannan tasake ta tareda juyawa, Waheeda Kuma ta qarasa wajan Babban Yaya daya zuba musu ido tundaga nesa yana kallonsu, yaso yaji me ake fad'a mata haka suke tafiya ahankali kamar basaso Kanta aqasa har tazo kusa dashi ta tsaya takasa had'a ido dashi, Kuma mamaki yaqi barinta Wai Babban Yaya ne mijinta, shine yabud'e mata qofar tashiga sannan yarufe yashigo suka tafi, a hanya ma kasa nutsuwa tayi, kwata kwata taqi Kallan inda yake, Sai window take kalla, Shima anasa 6angaren baiyi mata magana ba, wani irin nishad'i yakeji, Sai juyawa yake yana Kallan ta yana murmushi, yanzu Kam yana jin Kansa a matsayin kowanne ango, abu kad'an yarage masa,πŸ‘ŒπŸ» Suna qarasawa gida, megadi yabud'e musu, Babban Yaya yayi parking suka futo, yabud'e booth d'in motar yad'auko wata babbar jaka, megadi yana hango su daga nesa, mamaki ya hanashi magana, dazu dazu fa Hajiya tafita tana kuka Kuma yanzu ikon Allah gata tadawo lafiya, dama ance mata da Miji Sai Allah πŸ₯° Babban Yaya yaja kayan suka shiga ciki, afalo ya zauna, ya ajiye jakar agefensa,Waheeda kuwa tunawa tayi d'azu zata d'ora abinci wannan abun yafaru bata d'oraba, danhaka tayi sauri zata wuce kitchen Hannun sa yasaka ya fuzgota, ta fad'o Kansa, kunya ce ta kamata, ta6oye fuskarta a qirjinsa Kallan ta yayi yace "Ina zakije kibar mijinki?" Cikin qaramar murya tace "Babban Yaya zan dafa mana abinci ne" "no, karkiyi komai, nine zanyi mana, waye ya fad'a miki amarya tana abinci?" Cikin rashin fahimta tace "tana yi mana, Toni tun yaushe nake yi? Tun lokacin daka tafi kabarni" Murmushi yayi yace "ai yanzu qafata qafarki, kibud'e wannan kayan, tsarabar kice keda Ummi, nataho muku dashi" yafad'i hakan cikin sigar tsokana 6ata fuska tayi tace "Babban Yaya banso" Mamaki ya kamashi,yanda lokaci daya take nuna kishin sa qarara, da gaske de tana sonsa itama, hannun sa yahad'e waje d'aya πŸ™πŸ»yace "Tuba nake, ni wasa nake miki, nakine ke kad'ai" Cikin murna tace "duka gaba d'aya cikin akwatin?" Yace "yes, kiduba, zanje wajan megadi in dawo" Yana fad'ar haka ya ajiye ta d'am akan kujera shikuma yafuto, Yabarta tana bud'e jakar Yana zuwa compound, yakira megadi, cikin sauri ya qaraso wajan sa yana fad'in "yalla6ai Gani, akwai aikene?" Hannu yasaka cikin aljihunsa, yamiqa masa kud'i masu yawa yacey"ga wannan kaje gida kaga iyalanka, idan kagama hutawa idan zaka dawo saika min message " Hawaye ne yafuto daga idon megadi, yafara yimasa godia, har Babban Yaya yagaji da amsawa yajuya, Shima megadi yanufi d'akinsa yana fad'in"dole intafi gida wallahi, irin wannan kud'i haka? Ai ko baka turani gidaba, dole ne inje inbarku kusha Amarci" πŸ˜‚ Waheeda kuwa akwatin kayan tasa agaba tayi tagumi hannu bibbiyu πŸ™‰Ahaka yazo ya sameta yace "lafiya?" "Babban Yaya wannan kayan fa dukansu sunyi shara shara dayawa,Kuma...." Cikin sauri ya katseta yace "Kuma me?, ni su nakeso kina Sakamin, kefa yanzu ba yarinya bace, kinfi su Ihsan, kawai abinda yarage kizama cikakkiyar mace, saboda haka kindena saka Kaya masu kauri, inde Ina gidannan" Waheeda taji ya kurantata,yayabeta yabata girma Sai kanta yaqara nauyi, ita Ala dole tafi su Ihsan,πŸ˜‚ Cikin sauri ta d'aga kanta tace "to shikkenan zan saka" "kizo muje muyi wanka, nasa megadi yatafi" 😳Zaro ido tayi tace "wanka Kuma?" Kansa yadafe da hannunsaπŸ€¦πŸ»β€β™‚οΈ? ya manta da sabon shiga yake tare, yace "eh, akwai kayan wanka aciki, kisaka ki sameni a swimming pool, Ina jiranki..." Yana fad'in haka ya tsugunna yaduba cikin kayan Nata yad'auki na wankan yad'ora mata akan cinyarta, sannan yafita Waheeda ta bishi da kallo cikin ranta tana fad'in wannan mutumin bashida kunya AllahπŸ₯Ί Tad'auki kusan minti talatin tana tunanin fita da wannan kayan Rigace me launin ja, tsawon ta iya gwiwa, batada hannu Sai d'an siriri, gaban rigar normal wuya ne, saide daga wajan Boobs d'in anyenke wajan, anyi d'an qaramin round a wajan, Ana Iya ganin Boobs d'in sosai Futowa tayi tana tafiya Sai Kalle Kalle take kamar tana jin tsoron wani yaganta Ahaka, tana zagayawa baya inda swimming pool yake ta hango shi dagashi sai d'an qaramin wando dakad'an ya wuce pant, yana kwance cikin ruwan akan katifar roba, waya tana kange a kunnansa yana magana ahankali, gabanta ne yafad'i ganinsa haka, tasan de koda yaushe tana ganinsa da gajeren wando tunda a TV ma kowa haka yake ganinsa, Kuma idan yazo gida ma shi yake sakawa wani lokacin idan zasuyi ball tare, Amma bata ta6a ganinsa da wannan d'an fificin wandon ba, cinyoyinsa ta kalla farare tas kamar sauran jikinsa, Sai gashi dayawa daya kwanta me laushi kamar na qirjinsa,kamar wacce batada laka haka ta qarasa wajan taja ta tsaya,tareda sunkuyar da kanta qasa. d'agowa yayi da Idonsa ya kalleta,hannu ya miqa mata, babu musu tasaka qafarta a matattakalar dazata kaika cikin ruwan, tana shiga ya janyo ta zuwa jikinsa tareda Lumshe ido, ahankali yace "mashkur zansa yarinyar Nan takira ka Dan Allah, banda lokacin turoma number, inaso na Gana da amarya ta Sai anjima" yafad'i haka tareda kashe wayar Waheeda ya kalla yaga tacusa kanta cikin qirjinsa, yad'ebi ruwa ya watsa mata a fuskar, cikin sauri tabud'e idonta, murmushi yayi yace "kinyi kyau sosai, idan kinaso ki hanani fita kiyimin irin wannan shigar" yafad'i haka yana kissing wuyanta Cikin shagwa6a tace "Babban Yaya babu abinda zamu cifa" "zanyi mana oder abinci, Naga alama mecin abinci na aura" Bakinta ta turo gaba tace "Allah kafini cin abinci" Dariya yasaki yace "Alhamdulillah tunda kinsani, kinga saiki sake d'aura d'amarar girki, natural duk d'an qwallo yanada cin abinci, Bani kad'ai bane, nasan kin iya girki irinna Ummah, so banda matsala akan haka" Murmushi tayi ba tace komai ba,hanunsa yasaka yaruqo fuskarta yace "Waheeda,Ina sonki dayawa, nikaina bansan irin son danake miki ba, natsani inji kina min maganar wani,Ina shiga cikin tashin Hankali sosai, please ki riqeni, ki mallakeni ke kad'ai, banaso daga yau idan Zaki fita ki yarda wani namiji ya Kalle ki, zan'iya masa wata illar Allah...." Waheeda tasaki ajiyar zuciya, Sai yanzu ne take tunanin duk lokacin data kawo masa maganar wani yake 6ata mata rai, bata Isa takula wani ba Sai yafara fishi da'ita yana 6ata raiπŸ˜‚ Ashe wannan ne dalili, to amma Kuma soyaiya lokaci daya haka? To kode dama can yana sonta? Bata tambayeshi ba, tayi murmushi tace" to Babban Yaya, insha Allah zan kiyaye, kaima Kuma ka kiyaye kula mata, da idona na gansu Sai rungume ka suke " Murmushi yayi, ganin tafara sakewa dashi tana zance, yace"to matata taqi ta rungume ni, yanzu ma ki kalli yanda kika takure waje d'aya, kamar ba jikin mijinki ba" Cikin sauri Waheeda ta matsa ta rungume shi, wata irin ajiyar zuciya yasaki, yasaka hannunsa yasake rungume ta sosai Cikin kunnansa tace"Babban Yaya nide nagaji da ruwan Nan" yace"toki Bani abun dad'i saimu fita yanzun Nan" yafad'i hakan yana sake shigar dasu cikin ruwan, sake riqeshi tayi tace "mekake so to?" Hannun sa yad'ora akan nashanunta yace "gasu" Kunya ce takama Waheeda, tasaka hannu tarufe idonta, tace "ai suna cikin Riga" Inda aka yanke tagaban rigarta Nan yad'ora hannun sa yace "to hannu baya shiga?" Wata irin kunya tasake kamata, ahankali tace "baya shiga" Murmushi yayi yace "saide in ba'a Bani damaba, Amma zan'iya sakawa ta Nan" ya qarasa maganar yana tura hannun sa cikin rigarta,bebata damar motsi Bama bare ta qwace jikinta, yakama nipples d'inta yana murzawa ahankali, tsikar jikinta ce tatashi, taji wani irin dad'i, ahankali taja wani irin numfashi, Kallan ta yayi, yaga yanda take Lumshe ido, cikin rad'a yace "Kina jin dad'i? Kobakya ji na daina?" Idonta a Lumshe takasa magana, illa hannunta data d'ora akan nasa hannun tasake danne hannunsa alamun karya daina, yana ganin haka yaja hannunta yad'ora akan nasa nipples din, Amma kasa yimasa komai tayi, saide shafawa da takeyi ahankali, a hakan ma yaji dad'i sosai Shiru sukayi dagashi har ita, sun d'auki tsawon lokaci Ahaka, sannan Waheeda tafara janye hannunsa, ganin hankalin sa yafara barin jikinsa yana yamutsa ta cikin zafin nama, kallanta yayi da shanyaiyun Idonsa, muryarsa harta fara sarqewa yace "meyasa?" Cikin shagwa6a tace "zafi.... fa" Hannunsa yacire, yasake rungume ta tareda fad'in "sorry nadena" Saida yaji yad'an samu nutsuwa sannan yad'aukota, suka futo daga ruwan. Shine yayi musu oder abinci kamar yanda ya fad'a, suna gama cin abinci suka sauya shiga, yasaka ta ajikinsa suna kallo, da yamma kuwa cewa yayi tasaka kayan Ball sufita su buga, babu 6ata lokaci kuwa tasaka suka futo compound d'in gidan, inda ake buga ball d'an qaramin fili me kyau ,Nan suka shiga suka fara buga ball d'in, anan yaga tasake warewa kamar ba'ita ce take noqewa ba, yana son yaga tasaki jiki dashi sosai, shiyasa yake mata abubuwa irin wannan, da niyya yake mata wayo beciba yace yaci, ita Kuma Nan da Nan zata dauki rantsuwa tana fad'in beciba saide asake β€οΈπŸ‘ŒπŸ» 1/28/22, 20:52 - Ummi TandamaπŸ˜‡: IO Kwata kwata ya manta da wata aba damuwa,jinsa yake cikin farinciki da annashuwa,sun dad'e suna buga ball d'in, sannan suka koma ciki, Waheeda tashige d'akinta, Shima yashige nasa, wanka yayi yatafi masallaci, baidawo ba Sai Bayan sallar ishsha'i hannun sa d'aukeda abinci, yana shigowa ya ganta afalo tana kallo taci uban wani hijabi har qasa, zama yayi aqasa ita Kuma tana kan kujera,ya kalleta yace "wannan hijabin yayi girma dayawa acireshi mana" "Babban Yaya hijab nefa...." Tafad'i hakan cikin mamakin maganar sa, shida kullum bashida magana Sai ta hijab, bayason su saka mayafi "yes, nasan hijab ne, Amma na fad'a miki irin kayan danake so kidinga Sakamin ai ko? Shima hijab d'in ai zaiyi amfani idan Zaki fita unguwa" Cikin ladabi tace "to" "kicireshi, kisakko muci abinci, banason ganinki dashi" Ahankali tafara janye hijabin, bataso yaganta da kayan baccin data saka, saboda sunyi shara shara sosai, babu abinda baka Gani, Amma haka tacire shi ta ajiye akan kujerar, sannan ta sakko tabud'e take away d'in daya shigo dashi, kaza ce Sai shinkafa dakuma ganye agefe,binta yake da kallo kamar ya cinyeta, harta tsargu duk takasa ta6uka komai, ahankali tatashi taje kitchen tad'auko flet tazuba musu abincin sannan tace "gashinan nazuba" Yace "nagani, ai aikinki bai qareba, tunda baki Bani ba" Inda ace Dane tun kafin yafad'i haka zata fara bashi, Amma yanzu saita tsinci kanta dajin kunyar hakan, spoon tasa zata fara bashi yahanata, dole saida hannu ta dinga bashi, tana Kallan yanda yake wani Lumshe ido,shi kuwa Babban Yaya dad'i yakeji, da niyya yake had'awa harda hannunta yana tsotsa, sannan Yabarta ta d'ebo wani, saida yaji ya qoshi sannan yad'auketa, yad'ora ta akan cinyarsa, yafara bata abincin, tanacin abincin yana Kallan pink lips d'inta yanda suke shinning,kaza ya karyo yasaka mata a bakinta, cikin qasa-qasa da murya tace "Babban Yaya naqoshi" Wani irin yarrrr yaji ajikinsa, salon yanda tayi maganar ya birgeshi, Shima ahankali yace "d'an qara kad'an to....nima saiki ragemin" Tayi tunanin ta cikin flet d'in zata rage masa, shiyasa yana kawo kazar Setin bakinta saita bud'e bakin sosai tana so yasaka mata duka, saitaga yasaka mata yar kad'an, ya had'a goshinsa danata yace "ki ragemin to" Yana fad'in haka yasaka bakinsa akan Nata, Shima yafara karyar kazar, ita tanaci shi yanaci, suna cinyewa yahad'e bakinsu, saida yayi kissing d'inta, sannan yatashi tsaye itama ya miqar da'ita, yakama fuskarta ya riqe da hannayen sa, yace "meyasa tunanin ki yazama tamkar fitar numfashi na? inaso banaso dole sainayi" Murmushi tayi ta 6oye fuskarta a qirjinsa, d'ago da kanta yayi yace "meyasa bazaki kalleni ba?" Nanma murmushi tasake yi ba tace komai ba,fuskarta yasaki, sannan yakama hannunta suka nufi d'akinta ko kad'an Bebarsu sunyi kallo ba, Gani tayi yana gyara blanket zai kwanta tace "bazaka tafi d'akinka ba?" Wani irin kallo yayi mata yace "korata kike?" "a a" abinda tace kenan Ba tareda yayi magana ba yamiqa mata hannu, babu musu takama hannun sa, yasaka ta cikin jikinsa, sannan yakashe musu wutar d'akin Cikin kunnanta yace "bazaki min addu'ah ba?" "wacce iri?" cewar Waheeda "ta bacci" Shima yabata amsa Batare da tace komai ba yaji tafara karatu ahankali, can Kuma yaji tana Tofa masa, cikin sauri yabud'e Idonsa yace "yahaka? Shafawa fa ake a jikin mutum...."πŸ˜³πŸ™ŠπŸ™ˆ Batare da tunanin komai ba Waheeda tafara Tofa addu'ah ahannun ta tana shafa masa, ahankali yafara sakin sirrintacciyar ajiyar zuciya, tazo zata shafa masa a qafafunsa yaja hannun ta yad'ora akan cinyarsa, cikin wata irin murya yace"baki shafa anan ba" Jijjiga kanta tayi, sannan tashafa masa acinyar,yaso ya daure amma saiya kasa, cikin wani irin yanayi kafin Waheeda ta farga taji yad'ora hannunta akan mararsa, yariqe hannun a wajan , wani irin ihu tasaki Wanda yasa Babban Yaya bud'e Idonsa cikin sauri, hannunta ta fizge, Shima Kallan ta yayi yaga tana zaro idonta, jikinta Sai rawa yake,kamo hannunta yayi, tayi tunanin a wajan zai sake d'ora mata hannun, Sam taqi yarda, ta qanqame hannunta, cikin wata irin murya yace "meyasa?" Hawaye ne yazubo daga idonta, bata ta6a tunanin Babban Yaya zai iya d'ora mata hannunta anan wajan ba, Hawayen ta share tace "kayi hakuri Dan Allah...." Yace "so kike na mutu ko?" Cikin sauri ta girgiza masa kanta, cikin sigar lallashi yace "to kizo ki riqemin please...." Ahankali ta Kalle shi ta gefen idonta, taga yanda ya riqe abun da hannun sa, yana cewa itama tazo ta riqe masa, wani irin kuka ne yazo mata, dama wannan ne auren? Anya zata Iya kuwa? Gaskiya Gara ta gudu gida, wannan rashin kunyar har Ina? Shiru tayi, ita batajeba, Kuma ita bata gudu ba, ajiyar zuciya yayi yafusgota jikinsa, ya birkitata Takoma qasansa, shikuma ya kwanta ajikinta yace "kinaso narabu dake?" Cikin sauri ta d'aga masa kanta, murmushi yayi yace "to kibani twince dinki , da kanki..." Shiru tayi tana nazari, Sai zare ido take cikin duhu, ganin yanda tayi shiru yace "saiki za6a, koki riqemin abuna kokuma kibani Breast d'inki da kanki Nasha" Gabanta ne yafara faduwa, ga qoshi ga kwanan yunwa, babu yanda ta'iya, haka tasaka hannu ta gaban rigarta, tafuto da Breast d'inta guda d'aya, Babban Yaya yana ganin abinda take yawani lashe lips d'insa, jikinsa har rawa yake kamar mazari, yanaso yaga yanda zata bashi Boobs d'inta da kanta tamkar Babyn ta. Waheeda ta Kalle shi tace "to gashinan" tafad'i hakan muryarta na Rawa Cikin sarqewar murya yace "kibani da kanki mana.... ko so kike nakama dakaina kice nakama miki abunki da zafi?" Kallonsa tayi, idonta yaqara cikowa da hawaye, hannunta ta dora akan Breast din,tariqe shi, sannan ta kamo Kansa ta d'ora masa nipple dinta akan lips dinsa, cikin sauri yakama kamar Yaron da uwarsa ta dad'e bata bashi nono ba, iya nipple d'in kawai yake tsotsa ahankali,tareda gatsawa kad'an kad'an, daqyar yabud'e Idonsa ya kalleta yace "nine Babynki ko....?" Waheeda data fara kar6ar caji ta daga masa Kai tana sakin numfashi ahankali Ganin tafara jin dadin abinda yake mata saiya kama dayan Breast din Nata yana matsawa ahankali, dayan Kuma yana tsotsa, Waheeda tayi wata irin miqa, tana sakin numfashi me sauti Cikin sigar rad'a yace "kullum Zaki dinga Bawa Babynki yanasha miki ko....?" Cikin sauri ta daga kanta, wata irin tsotsa yasake yi mata, sannan yace "bazaki min magana ba?" Cikin wata irin murya tace "zanbaka" Bakinsa yacire daga kan Breast d'inta, yakama nipples dinta duka biyun da hannayensa, yana murza mata su ahankali, cikin fitar hayyaci yace "Zaki dinga Bani ko....?" Tace "eh" Wani irin yawu ya hadiye yace "to waye nidin? Wazaki dinga Bawa yanasha miki?" Cikin jin dadin abinda yake mata, dakuma kalaman dayake mata na tsokano sha'awa takama Kansa tariqe da hannunta, dayan hannun tashafa lallausar sumar Kansa dashi sannan tace "kaine Babyna, Kai zan Bawa" Yana jin wannan furucin Nata, yamaida Kansa Kam Breast dinta yanasha sosai da zafi zafi, hannun sa yasaka yabud'e kafarta, ahankali yayi qasa da gajeren wandonsa, yafara neman hanya, Waheeda tana can wata uwa duniya taji zafi zafi aqasan ta, hannunta tasaka a wajan anan taji abinda Babban Yaya yake qoqarin tura mata jikinta, tsoro ne yakamata, tayaya wannan uban abun nashi zai shiga? tureshi tafarayi Amma ko gizau beyi ba, Sai kokarin shiga yake, Amma abar taqi shiga, kuka tafara tana tureshi, Shima zuwa lokacin wani irin Hawayen dadi yake yana addu'ah Allah yasa tashiga, kokawa suka fara shida Waheeda, yakama hannayenta yariqe duka biyun, yana qoqarin shiga, kuka Waheeda take sosai, Nan tafara roqonsa yayi haquri, cikin qwaqwalwar sa yaji kukan Nata yayi yawa, ko kadan baya son kukan Waheeda a rayuwar sa, ahankali ya haqura, yadena neman hanyar, yajata ya rungume ajikinsa kamar zai 6allata, kissing din ko'ina yake ajikinta, saida yaji yadan samu nutsuwa sannan ya sassauta ruqon da yayi mata, Waheeda Tasha kuka tagaji Sai ajiyar zuciya take, duk da tasan beyi abinda yakeso dinba, hakan bai hanata jin zafi a wajan ba Washegari kuwa kasa kallan sa tayi πŸ˜‚ Yana Kallan ta yana murmushi, ko yayi mata magana kanta a sunkuye take bashi amsa, duk ta takura kanta kamar ba Waheedan muba πŸ’ƒ Yau tsawon kwana hudu kenan, kullum Sai Babban Yaya yanemi haqqin sa awajanta, Amma Waheeda taqi yarda, yana farawa zata fara yimasa kuka, shikuma baya son kukan ta, yana ganin tafara kukan saiya haqura, cikin kwana na biyar d'inne wajan aikinsu suka masa waya zasu buga wasa tsakanin su da Algeria, Kuma harda shi aka za6a acikin Wanda zasu buga qwallon Baqin ciki yakama Babban Yaya, kawai to ya cewa couch d'in nasu, saboda beso hakan ba, yaso ace yamaida Waheeda cikakkiyar mace kafin ya dauketa sutafi honeymoon dinsu. yauda safe suna gama cin abinci ya kalleta yace "kishirya zan maidake gida" Cikin sauri ta Kalle shi, tayi tunanin wani laifin tayi, tace "meyafaru Babban Yaya?" Kafad'a ya d'aga yace "an kirani ne, a wajan aikina" Ajiyar zuciya ta sauke, tayi tunanin wani laifin tayi, zaice zai maida ta gida,ahankali tace masa "to yaushe zaka dawo?" "babu rana" yafad'i hakan ransa a6ace, itama tanajin wannan furucin taja bakinta tayi shiru, tasan cewa ransa a6ace yake Bata d'auki komai ba, kawai hijabinta tasaka, suka tafi, suna zuwa compound din gidan Ummah yayi parking,kafin suyi sallama yajuyo ya kalleta yace "karki dinga wasa dasu Ihsan har kuzo Ana rabaku akan abinda baikai yakawo ba,nasan halinki bakida kunya, kikama girmanki, da da dayanzu ba daya bane, duk abinda kike buqata kidauki ATM dina kije ki siyo kokuma kisa su Sa'eed su siyo miki" Tace "Babban Yaya, kaida kace yanzu na girmi Ihsan nikuma tayaya zan kulasu har muyi fad'a?" Cikin sauri yace "tayaya kika girmesu? Bayan kinqi Bani damar dazan maidake Antyn su?, Ina ta6abaki Sai kuka, ko bakya jin dad'in abinda nake miki?" Yafadi hakan yana Lumshe Idonsa Wata irin kunya ce takama Waheeda, tasaka hannunta tarufe fuskarta, Sai yanzu ne tagane inda yadosa, ashe Dama Abaya haukanta take tana hura hanci ita tazama babba, ashe wannan abun ne girman, cikin sauri ta6ud'e motar tatafi da gudu, ajiyar zuciya yasaki yanabin Bayan ta da kallo harta shige falo, sannan yayiwa driver magana yazo yajashi suka tafi Satinsa d'aya da tafiya Waheeda taci gaba da zuwa makaranta dayake exam ma suke, yanzu tayi Hankali ta nutsu ta daina hauka, ko agida haka zaka ganta a zaune waje d'aya, wani lokacin har kunyar Ummah take ji saboda Gani take duk abinda yafaru tsakanin ta da Babban Yaya Ummah tasani, haka kawai saita dinga tsarguwa idan tana cikin su, da daddare kuwa kasa bacci take, tana ganinsu Ihsan suna kwasar baccin su Amma ita saide taita juye-juye, Kuma ba komai ne yake damunta ba Sai tunanin mijinta, Ida tunanin yayi yawa harji take kan nononta yana mata qaiqayi, saide tasa hannu ta Sosa Amma hakan bazai Hana anjima tasake jin wani qaiqayin ba, idan ta kirashi da wayar su Ihsan baya d'auka, saboda yasan itace, Sai yanzu ne take DANA SANI (first novel) akan hanashi haqqinsa da tayi ta dinga wahalar dashi, Sai yanzu yake bata tausayi, yau Satinsa biyar da tafiya, a ranar ne Kuma su Waheeda suka gama makaranta, sannan a ranar ne zasu buga wasansu, Hajiya Anty da Uncle Usman duk sunzo gidan antaru za'a kalli ball d'in, Anty Maryam itama tazo harda junior me sunan Babban Yaya, gaba d'ayansu sun nutsu kowa hankalin sa yana kan TV, Waheeda tana Gefe tana kallo itama,carbi ne a hannun ta Sai addu'ah take cikin ranta Allah yabawa mijinta nasara, dayake addu'ar mata akan mijinta batada hijabi a wajan ubangiji,cikin ikon Allah Ana fara wasa kuwa Babban Yaya shine mutum nafarko daya fara Ci, yana ganin yaci ya tsugunna yayi sujud shukr. su Sa'eed suka tafa shida Sa'ad, falo kowa yafara murna Wasa yayi wasa kowanne team sunaso sunga sunci, har tsawon wani lokaci sannan wani d'an team d'in su Babban Yaya yaciyo musu, Babban Yaya yana kar6ar Ball d'in ya dinga Sakata araga, saida yaci Sau uku ajere, Bayan guda d'ayan daya faraci, gudu yake sosai yana d'aga hannu, Yan team dinsu suna binsa Abaya, cikin murna suka rungume shi, Ummah bakinta yaqi rufuwa, Sai murmushi take idonta yana kan TV, su Daddy da uncle ma sunyi shiru kowa yana Gani, Hajiya Anty de addu'ah take cikin ranta Allah yakare mata d'annata, Allah yasake d'aukakashi yad'ora shi akan maqiyansa. anci gaba da wasa kenan Babban Yaya yasake nasarar kar6ar qwallo daga wajan d'ayan team din, ya d'aga qafa zai bugata kenan Shima wani yakawo tasa qafar jikake qassss, yabige qafar Babban Yaya, lokaci daya jama'ar dasuke studio din suka fara fadin ohhhhh! Lokaci daya hankalin masoyansa yatashi, suka miqe tsaye, cikin azaba Babban Yaya yariqe qafarsa yana runtse ido Waheeda taji kunnanta yayi mata wani dimmm haka kamar bataji, kamar Kuma a mafarki, miqewa tayi tsaye tanufi gaban TV, gabanta yana fad'uwa, tuni hawaye suka wanke wa Ummah fuska ganin ankawo wani irin gado marar qafa, andora Babban Yaya akai, anfita dashi daga filin wasa Kallan Daddy tayi cikin kuka tace"Alhaji tafiya zanyi, sun kashemin Dana " Cikin tashin Hankali daddy yace" Ina zakije Hajiya? Kiyi hakuri mana " Uncle Usman yafara neman wayarsa, Hajiya Anty ta Kalle shi cikin rawar murya tace" bazaka sameshi ba, yacemin kashe wayarsa zaiyi idan zasu fara wasan " tana fad'in hakan hawaye yazubo daga idonta, su yanbiyu ne suka janyo Waheeda, Sai girgiza kanta take tana hawaye Amma takasa magana, Sa'ad yatashi yakashe Kallan, Anty Maryam tariqe Waheeda tace" kiyi hakuri Waheeda, insha Allah zaiji sauqi " Cikin kuka tace"niku rabu dani, ku d'in shiru zakuyi idan mijinku ne?, Dan Allah Dan Annabi Daddy kabarni natafi, dama fishi yake Dani, qilama nice sila....." tafadi hakan tana fashewa da wani irin kuka Hajiya Anty ta rungume ta tana bubbuga Bayan ta, babu Wanda baiyi kuka ba acikinsu, saisu Daddy kawai, suna mutuqar qaunar d'an'uwan nasu, haka suka zauna shiru suna faman addu'ah, shide ba'a Nigeria yake ba bare sutafi koba visa, a wata qasa yake, Kuma yanzu dare ne dole zasu jira suga wanne mataki qungiyar tasu zasu dauka akan ciwon da yaji Babu Wanda yayi yunqurin kwanciya acikinsu, kowa wayace ahannunsa yana try number Babban Yaya ko zata shiga, Waheeda ce kawai babu waya Sai faman kuka take har numfashin ta yana sama kamar wadda take shirin suma, Sai wajan karfe biyu sannan cikin sa'a Daddy ya sameshi, cikin sauri ya miqe tsaye yace "Alhamdulillah tashiga, yabud'e wayar" Kowa Matsowa yayi kusa da Daddy duk suka taru suka yanyameshi, Daddy daya ga haka saiya saka wayar a hands-free, harta katse bai d'auka ba, saida yasake kira Akaro na biyu sannan yada'auka, kuka yafara ji yana tashi sama sama Kuma ba kukan mutum d'aya ba, cikin ransa yace sunga abinda yafaru kenan Daddy yace "Son, kana lafiya? Yaya jikin Naka?" Kafin Babban Yaya yayi magana Ummah ta qwace wayar, cikin kuka tace "kafadamin halinda kake ciki, Hankali na yakasa kwanciya, sonake nataho, bazan iya zama ba" Ahankali yace "Ummah...., ki kwantar da hankalinki, anduba min qafar, harma sun Bani injury, zan dawo gida insha Allah" Cikin kuka Ummah tace "karka dawo in kasan jikin babu sauqi, mu saimu biyo ka"β€οΈπŸ˜‚ Memakon yabata amsa saiyace "Ummah Ina Anty? Ina Waheeda?" Wayar tamiqawa Hajiya Anty, Anty ta share Hawayen idonta, sannan takar6i wayar tace "sannu Naufal, yajikin naka?" Ahankali yace"jiki da sauqi Anty, kikulamin da Waheeda nasan Hankalinta yatashi " Anty batayi magana ba, saita Bawa Waheeda wayar, saboda tasan yana jin nauyin ta bazai iya cewa tabawa waheedan waya ba, Waheeda kuwa tana kar6ar wayar Takoma Gefe, kuka take sosai takasa magana, cikin sanyin murya yace"kiyi shiru..., ba sosai bane ciwon" Cikin kuka tace "kayi hakuri nadena, daga yanzu nadena hanaka komai, naji tsoro sosai, jinake kamutu" Wani irin dad'i yaji ya ratsashi, yanzu Kam yagama tabbatar wa Waheeda tana sonsa, saboda haka wannan ciwon Koya warke bazai nuna mata hakan ba, yasamu mafaka ta yanda zai dinga zuba mata shagwa6a son ransa Ahankali yace "I luv you so much.......muahhhh,, muahhhh" πŸ’‹πŸ’‹ Yasakar mata kiss har biyu ta cikin wayar, sannan yaci gaba da fad'in "kimin addu'ah kinji, insha Allah zanji sauqi, jeki kaiwa su Daddy wayar Tace"to" sannan tatashi takai musu wayar, Sai a lokacin Hankalinta ya kwanta, Sai ajiyar zuciya take, jikin Hajiya Anty Takoma ta lafe kamar wata mage, bata Jima da kwanciya a jikin nataba bacci yasoma d'aukarta Yana gama wayar dakowa acikinsu harda junior, sukai sallama Bayan yagama kwantar musu da Hankali, Kiran mashkur ne yashigo wayar tasa, d'auka yayi tareda sallama, mashkur yace "friend mutanan nanfa sun hanamu shigowa Dakin, sunce har yanzu kana buqatar hutu, Sai lalla6a ka suke kamar qwai"πŸ˜‚ Murmushi yayi yace "rabu dasu mashkur, zamu hadu ai idan nafuto insha Allah, ciwon fa Bana kirki bane, kawai tsagewar qashi ne, da niyya na langwa6e musu, nagaji da ball d'in Dama hanyar guduwa wajan amarya ta nake nema, to Kuma Sai haka tafaru....." πŸ™Š Mashkur ya kwashe da dariya yace"wato me jiran kukane aka jefeshi da kashin awaki, banga laifin ka ba Abokina,Naga ma sun sanar katafi injury, Kasha Amarci lafiya...." Babban Yaya yayi murmushi yace "thanks Friend" Pls kuyi hakuri Dan Allah πŸ™πŸ»πŸ™πŸ»πŸ™πŸ»πŸ™πŸ» 1/28/22, 20:52 - Ummi TandamaπŸ˜‡: RD Basu sukabar falon ba Sai wajan karfe uku da rabi, a ranar daga Waheeda, har Ummah da Hajiya Anty, basu runtsa ba, su Waheeda suna zuwa daki alwala tayi tazo tafara sallah tana yiwa mijinta addu'ah Allah yakare mata shi, su kansu yanbiyu da Anty Maryam sunyi mamakin Waheeda, sun kuma tabbatar lalle aure yana saka mutum nutsuwa da Hankali, gashi de kamar ba Waheeda ba πŸ˜‚ Da safe wani irin zazzafan zazza6i yarufe ta, babu 6ata lokaci Hajiya Anty tayi mata allura, sannan bacci me nauyi ya d'auketa Koda suka sake Kiran wayar Naufal yana tambayar su ita, suka fad'a masa tana kwance batajin dad'i Wasa wasa saida Waheeda ta kwashe kusan sati d'aya a kwance batada lafiya, kullum tana d'aki a kwance cikin blanket, Hajiya Anty duk ta damu,yau shiryawa sukai suka tafi Asbiti, suna zuwa tayi mata awon fitsari tayi tunanin ko ciki ne πŸ™Š Amma da result yafuto saitaga babu komai, akayi mata text aka Gano typhoid ne, anan suka had'o magunguna suka dawo gida Tana fara amfani da magungunan kuwa cikin ikon Allah ta warware πŸ‘ŒπŸ» Amma kana ganin fuskarta zakaga tayi wani irin haske, ita kanta Ummah tayi tunanin cikin ne, saida taga result d'in Nata sannan ta yarda batada ciki Kwanan Babban Yaya Tara, yaji dad'in jikinsa, dama Allah Allah yake ya dawo gida, aikuwa Ana sallamar sa yayiwa Ummah waya yafad'a mata gashinan zuwa Waheeda tanajin labari tafara had'a Kaya πŸ˜‚ Ihsan dake maqale da waya a kunnan ta tana magana da mashkur ta kalleta tace "Ina Zaki ne?" Kai tsaye tace "gidana" Intisar ta kwashe da dariya tace "su Waheeda masu gida,yau Kuma keda kanki kike cewa gidanki Zaki tafi?" Cikin gundura da zancen nasu tace "to saina zauna anan haka kawai Bayan ga mijina can yana hanya? Sai in zauna yazo yaganni Ahaka ya rainani?" 😳Zaro ido inti da Ihsan sukai, sunji abun mamaki Wai Babban Yaya ne zai rainata, kafin suyi magana Waheeda tasaka hijabin ta tad'auki jaka tafuto tareda ja musu qofar Afalo Ummah da Hajiya Anty suna zauna, suna Magana akan abincin da za'a tsara wa Babban Yaya, sukaga Waheeda tafuto, Hajiya Anty tace "Ina zakije Daughter?" Cikin qasa qasa da murya tace "gida" Hajiya Anty ta girgiza kanta alamun batajiba, sannan tace "mekika ce?" Ummah tace"cewa tayi gida zata tafi, tana nufin gidanta, gidan mijinta"πŸ˜‚ Turo baki gaba Waheeda tayi cikeda shagwa6a, batace musu komai ba,Hajiya Anty tace "to kije driver yakaiki, Allah yakiyaye hanya" Daga musu Kai tayi, sum sum tafice daga falon, Hajiya Anty ta kalli Ummah tace "Zamani,mu muna shirin tar6arsa anan, kinga ita Kuma tatafi gidanta" Ummah tayi dariya tace "hmm ai kad'an kika Gani" πŸ˜ƒ Kafin Hajiya Anty Tayi magana, wayar Babban Yaya tashigo wayar Ummah, cikin sauri ta d'auka tana fad'in "kinga ma yana kirana,inaga sun sauka" Dauka tayi tareda fad'in "Son kun sauka?" Daga nasa 6angaren yace "eh Ummah, Gani tareda su Sa'eed...." "a a, to me kuke jira? Ku qaraso gida mana, karka tsaya mutane su dameka dayawa nasan idan kahad'u da mutane bazaka qaraso dawuri ba" Cikin kunya yace "a a Ummah... Dama... Dama zan fad'a miki ne, na wuce gida, idan nahuta zanzo" πŸ™ŠπŸ˜‚ Ummah tasaki baki tana Kallan Hajiya Anty, ita batayi masa magana ba, ita bata kashe ba, Sai can taji yace "Ummah bakya ji?" Cikin mamaki tace "inaji yayansu, to Allah yakiyaye hanya saika shigo d'in" Cikin farinciki yace "Amin Ummah, I miss you" dif yakashe wayar Hajiya Anty data gama jin komai ta kwashe da dariya tace "Hajiya, yaran nanfa Dama bakinsu ahad'e yake, gaba d'ayansu magulmata ne, kinga Shima damuke shirin tar6a ya wuce wajan matarsa,kinji magulmaci harda cewa I miss you, ai shikkenan Nima Bari intafi gidana, babu amfanin Zaman" tafad'i haka tana miqewa tsaye Ummah bata iya magana ba Sai cewa tayi "to Antynsu Sai munyi waya" πŸ˜ƒ *** ** *** Tana zuwa gida tagama gyara komai, gida yayi fes ko'ina yad'auki qamshi, tasaka doguwar Riga ta leshi me mutuqar tsada, ta zauna ta tsara kwalliya, tasaki dogon gashinta gadon Bayan ta, abinci ta had'a masa d'an kad'an dede yanda tasan idan yagani zai birgeshi, sannan ta zauna afalo tad'auki littafin addu'ah tana dubawa, wajan minti talatin taji tsayuwar mota, littafin ta ajiye tatashi ta nufi qofa, tana bud'ewa suka kusa cin Karo da juna cikin tsananin murna tayi wani irin tsalle ta rungume shi, murmushi yasaki, Shima yasaka hannu yasake rungume ta tsam ajikinsa tareda Lumshe ido yana sakin wata irin ajiyar zuciya Sa'eed yayi murmushi tareda shafa sumar Kansa ya ajiye masa kayansa yajuya yafice daga falon Wani irin kukan shagwa6a tasakar masa, ita kanta batasan dalilin kukan nataba, kona murna ne ta ganshi lafiya? Oho Ahankali yafara bubbuga Bayan ta, yad'ora bakinsa asetin wuyan ta ya sakar mata kiss, sannan yad'ora harshansa yana tsotsar wuyan Nata Wani irin yarrr taji ajikinta, batasan lokacin data sake rungume Shiba, yajima yana tsotsar wuyan ta, Sai numfashi yake sauke wa, tanajin yanda yake gangarowa zuwa qirjinta,tasaka hannu ta d'ago da Kansa, cikin shagwa6a tace "Babban Yaya muje kayi wanka mana" Yatsina fuska yayi ya kalli gefensa yaga babu Sa'eed yace "Ina Sa'eed d'in?" Tace "au tare kuke ne?" "tare muka shigo, ai duk kece kika rikitani, shikkenan yanzu kinsa girma na zai fad'i a'idon yayanki" Tace "yayana Kuma? Kamarya?kaiba Yaya na bane?" Murmushi yasaki,yasan cewa har qarshan rayuwarsu Waheeda zataci gaba da kallon sa ne kamar yayanta, ahankali yace "a a nikam mijinki ne ba yayanki ba" Murmushi tayi tarufe idonta da hannunta cikeda kunya, taja hannun sa zasu qarasa ciki, cikin shagwa6a yace "Auchhh! Kina Jana ahankali mana, qafata ciwo" Yafadi hakan da niyya bawai Dan yaji ciwon ba, lokaci daya ta rikice, cikin damuwa tafara tatta6a jikinsa zuwa qafarsa tana fad'in "sannu, na Fama ma ciwon ka ko? Yi hakuri to taka ahankali" Wani irin dad'i yaji acikin ransa, yafara d'ingisa qafar yana tafiya daqyar, suna zuwa d'akinsa yafad'a kan gadon, tace "Babban Yaya wanka fa" Cikin shagwa6a yace "nifa bazan iya ba....,saide in zakimin" Cikin sauri ta kalleshi, murmushi yasaki sannan yamiqa mata hannu, babu musu takama hannayen nasa tana jansa, Amma takasa d'agashi, ahankali ya fuzgota tafado Kansa, yariqe fuskarta da hannun sa yace "I love you Waheeda" 6oye fuskarta tayi a qirjinsa cikin kunya, cikin rad'a yace "bazaki iyamin wankan ba?" Ahankali ta d'aga masa Kai, murmushi yayi,yace "nayi tunanin zakimin, har abar kikama ki wanke"πŸ˜ƒ Rufe idonta tayi da hannunta, kunya ta kamata, tana tunanin Ina yaji wannan maganar? Murmushi yasaki sannan ya kwantar da'ita akan gadon, yashiga wankan cikin sauri, satar kallon sa tayi, mamaki yakamata, ba yanzu taga yana d'ingisa qafarsa ba? πŸ€” Daya futo daga wankan ma lafiya kalau yafuto ya manta dawani d'ingisa qafa dayake, kawarda kanta tayi Gefe, tad'auki wayarsa tana Kallan photuna, tayi mamaki sosai ganin photunan yawanci duk Nata ne aciki, wani tasan anyi mata, wani kuwa bata Sani ba, lotion yad'auko zai shafa ya zauna akusa da'ita, ahankali ta ajiye wayar tatashi zata bar d'akin, hannunta yaruqo yace "Ina Zakije Kuma?" Kanta aqasa tace "zan had'a abinci ne..." "to wakikeso ya shafa min man? Bayan kinsan banajin dad'in jikina ba komai zan iyaba?" Cikin mamaki ta Kalle shi tace "Dama baka warke ba?" "ni ban warke ba, kawai daurewa nake Ina komai, Amma idan zan takura miki shikkenan, Bari in shirya naje mu gaisa da Ummah kar tace nadawo banjeba" Waheeda tayi shiru tana nazari, wata zuciyar tace kyaje kina zaune agida daga wajan Ummah kiji shi a wajan Ummi πŸ˜‚ Cikin sauri tadawo ta zauna, tad'auki man ta shafa a hannunta, sannan tafara shafa masa ahannunsa zuwa kafadar sa da wuyansa Laushin hannun ta, da Laushin jikinsa, yahad'u da Laushin man hakan yasa Babban Yaya ya Lumshe Idonsa, tana shafa masa a qirjinsa yaji wani irin dad'i, ahankali yasaki wani Dan qaramin numfashi, man tasake lakutowa ta murza a hannunta sannan tad'ora hannun dede nipples dinsa tana shafa masa man, wata irin qara Babban Yaya yasaki yace "ohhhhh......" Kallan sa tayi da sauri tace "harda Nan ciwon?" Cikin sauri ya daga mata Kansa yace "harda Nan mana, da qafata da qirjina, da cinyata" Mamaki yakama Waheeda, to ai ko lokacin da yaji ciwon iya qafarsa taga yana riqewa, cikin sanyin jiki da tausayawa tace "sannu, Bari inyi sauri Kaci abinci saika kwanta ka huta" Daga mata Kai yayi, taci gaba da shafa masa man harda su fuskar sa, Amma bata shafa masa acinya ba, ta Kalle shi tace "yayi?" Murmushi yayi mata yace "yayi" sannan yatashi yanufi toilet, yanxu kawai tsarki zai sake, ya tabbatar idan akaci gaba da shafa man Nan to gaba dayama saiya sake wankan Da daddare suna zaune afalo suna kallo, Waheeda tana zaune shi kuwa yayi matashi da cinyarta, wayarsa ce tayi qara, yana dubawa ya runtse Idonsa, Waheeda tace "menene?" "Anty ce take kirana, banje ba, kunya nakeji wallahi, kullum nazo a ranar nake zuwa" Tace "toka dauka mana kaji menene" "um Um bazan iya dauka ba, ke ki dauka Sai muji" Waheeda tad'auki wayar, Hajiya Anty tace "Yaya jikin Naka?" Waheeda tayi murmushi tace "Anty bacci yake fa, Amma da sauqi jikin Alhamdulillah" Naufal ya gyara kwanciyar sa a cinyarta yana Kallan ta Sai murmushi yake dimples dinsa suna futowa, Hajiya Anty tace "to Alhamdulillah, kina Jina ko? Karkiyi wasa da magungunan ki, kici gaba da amfani dasu, idan Kuna buqatar wani abu saikimin magana" Ahankali tace "to shikkenan Anty, saida safe" Wayar ta ajiye ta Kalle shi tace "kawai cewa tayi yajikin naka, nace mata kayi bacci ma Kuma da sauqi" "Tome tasake cemiki? Naji ai tanata magana kekuma kinyi shiru" πŸ™ŠπŸ˜ƒ Murmushi tayi tace "cewa tayi na kula dakai, Kuma duk abinda muke buqata nayi mata magana" Jijjiga Kansa yayi, sosai ya gamsu da bayanin Nata, beyi tunanin ta6oye masa wani abun ba, cimak ya d'auketa suka nufi dakinta, suna zuwa yakashe musu wutar Dakin, sannan yasaka ta ajikinsa sukai shirin bacci Waheeda tayi shiru tana jin wani irin dadi Wanda batasan dalilin saba, Amma ta tabbatar hakan baya Rasa nasaba da zuwan dan'uwan Nata, nipples dinta ne taji yana mata Dan qaiqayi tasaka hannu ta Sosa, sannan tasake gyara kwanciyar ta A kunnan ta yad'ora bakinsa, cikin rad'a yace "mezan samu ne?" Murmushi tayi cikin kunya tace "babu komai" "kin tabbata?" "eh" Hannun sa yad'ora akan nashanunta yashafa yace "wannan basuyi kewata ba?" ya qarasa maganar yana murza mata kan nonon ta Ahankali Waheeda ta Lumshe idonta tana hamdala acikin zuciyarta, kamar yasan Dama qaiqayi suke mata, cikin fitar hayyaci tace "sunyi" Sake murza matasu yayi yace "sosai?" Ahankali tace "um" Kissing din wuyan ta yayi yace "Nasha?" Daga masa Kai tayi ahankali, cikin sauri yajanye mata rigar tayi sama, sannan yad'ora harshansa yana tsotsar su ahankali, lokaci daya Waheeda tafita hayyacinta, Sai shafa lallausar sumar Kansa take, hannun sa yasaka cikin private part dinta yashafa wajan, cikin jin dadi tace "wayyo...." Murmushi yayi, yacire mata pant dinta, yaci gaba da shafa wajan, kwata kwata Waheeda sakin ihun dadi take, tamanta da Babban Yaya take tare, shi kuwa Babban Yaya, haqqin sa yake son kar6a awajanta, cikin dabara yafara neman hanya, tanajin abinda yake kokarin saka mata tadawo hayyacinta, kuka tafashe dashi, cikin wata irin murya yace "bakyaso?" Cikin sauri ta amsa masa, ahankali yafasa abinda yayi niyya, yajata jikinsa ya rungume ta sosai, kamar zai maida ta cikin jikinsa, cikin sauri tace "Babban Yaya zafi" Ahankali ya sassauta mata ruqon, sannan tasamu bacci me dadi ya d'auketa, shi kuwa kasa baccin yayi, daqyar da Fama sannan yayi sa'ah bacci ya dauke shi Da asuba, shine yafara wanka, sannan yatasheta tayi wanka, suka gabatar da sallah, yayi musu addu'o'i sosai, sannan yacire rigar sa, itama tarage kayanta, suka koma gado suka kwanta, Amma duk wannan abun da ake Waheeda taqi hada ido tashi, Shima yana lura da hakan, kwata kwata yau bayajin zai iya fita ko nanda bakin get, saboda mararsa wani irin murdawa take tana masa ciwo Suna kwanciya, bacci yad'auki Waheeda, shi kuwa shiru yayi yana tunanin dabarar dazai mata ta amince da buqatar sa, bayason yayi mata ta qarfi, yafi son ta amince da kanta, abun zaifi bada armashi, yana cikin wannan tunanin yaji wayarsa tana qara,qaran wayar ne yatada Waheeda, Amma Saitayi shiru bata nuna masa tafarka ba Dauka yayi tareda fadin "mashkur ya akayi?" "yanzu danna kiraka mu gaisa shine zaka cemin ya akayi? Kodan yanzu kana angonci shine zakace baka son kira?to kayi hakuri, kawai kira nayi inji Yaya jikin Naka dafatan de babu wata matsala?" Babban Yaya yace "Kuma kira da wannan asubar?" Dariya mashkur yayi "wallahi ni na manta ma Nan asuba ce, sorry ango" "Dan Allah mashkur kadena min maganar angoncin Nan, har yanzu de shiru ne, babu bayani" Waheeda datake cikin Bargo ajikinsa, ta zaro ido, gabanta yana faduwa, lokaci daya Kuma taji wani irin tausayin sa ya kamata, Gara ta bashi haqqin sa, tunda yanzu ya fadawa abokinsa to tun kafin ya fadawa su Ummah Gara ta bashi Mashkur yace "kayi hakuri, kasan abun saida lallama" Ajiyar zuciya yayi yace "babu abinda zai faru mashkur insha Allah, komai saita amince, zan kiraka back, bacci nakeso nayi" Yana kashe wayar, ya Lumshe Idonsa tareda sake rungume ta, tausayi yasake bata, ahankali tad'ora hannunta a qirjinsa tad'an shafa kad'an, Babban Yaya yayi tunanin bacci take, ya gyara mata hannun, yasake matsowa da'ita jikinsa, Waheeda tanajin yanda fuskarta take kan qirjinsa, ahankali ta dora bakinta akan nonon sa takama Sha ahankali kamar yanda yake mata Shima Wata irin miqa yayi yace "Baby kibari fa" Memakon ta Bari saita dora hannunta akan dayan nonon tana matsa masa kan ahankali, rungume ta yayi ajikinsa yana sakin numfashi, cikin wata irin murya yace "so kike ki kasheni da dadi ko? Bayan ba Bani abun dadin zakiyi ba" Wata irin kunya ce takama Waheeda, har yanzu idan Babban Yaya yafada mata wata maganar, jitake kamar qasa ta tsage tashige ciki Dan kunya, cikin sauri tadena abinda take tarufe idonta Shima murmushi yayi, yacire hannunta daga fuskarta yace "to inyi?" Daga masa Kai tayi, yace "kin amince?" Tace "um" Yace "to karkiyi kuka kinji? Nima ahankali zanyi miki, zakiji dadi sosai" Tace "to" Tana rufe bakinta, yahade bakinsa da Nata yana nuna mata zazzafar soyaiya, sosai yake kissing dinta cikin salon qwarewa, saida yayi wasa da'ita sosai, yakaita matakin qarshe najin dadi, Waheeda taji yace zataji dadi sosai Dan haka tasaki jikinta sosai tana jiran jin dadin,tanajin sa yana neman hanya, memakon taji tsoro Sai wannan kalmar tajin dadi daya fad'a ta yaudare ta, tayi tunanin dadin ne zaizo, Dan haka tad'an bude masa qafar, aikuwa Babban Yaya yana samun hanya yafara shiga, yaji wajan a rufe, yasake dannawa da qarfi, aikuwa hanya tasamu, lokaci daya wani irin dadi yarufe shi, Hankalinsa yabar jikinsa, nutsuwarsa ta gudu, Yama manta da yar qaramar qanwar sa yake tare, yafara shiga da fita kamar yasamu babbar mace, tun lokacin da Waheeda taji wata irin azaba, ta runtse idonta, bata sake sanin inda kanta yake ba, ta suma Tafiya tayi tafiya Babban Yaya ko alamun gamsuwa ba yayi, dadi kawai yakeji, besan lokacin daya Fashe da Kuka ba, kuka kawai yake yana aiki, saida yad'auki lokaci me tsawo sannan yasamu gamsuwa, a lokacin gari ya waye, safiya tayi, rungume ta yayi ajikinsa yana sakar mata kiss ta ko'ina, har yanzu hawaye yake yakasa magana, haqiqa Sai yanzu ne ya gane iyayen sa gata suke masa da suka dage akan saiya yi aure, ashe abinda akeji kenan Amma yabar Waheeda tsawon wannan lokacin tana wahalar dashi, sake rungume ta yayi, cikin kuka yace "Baby...." Yaji shiru, Hawayen Idonsa ya share ya kalleta, anan ya tabbatar bata hayyacinta, ta suma, zaro Idonsa yayi, cikin sauri ya d'auketa Sai toilet Ruwan zafi ya had'a ya Sakata aciki, cikin sauri tabude idonta, wata irin qara tasaki tace "Ummah.... Zai kasheni, Ummah kizo, Allah Babban Yaya zai kasheni, Anty!!!" Runtse Idonsa yayi, haqiqa yayiwa Allah godia da wannan abun ba acikin gidan Ummah yafaru ba 🀣 Fuskarta yariqe da hannun sa yace "nine fa Baby, bude idonki ki kalleni, bazan sake miki haka ba, nadena kinji, yi hakuri, yi hakuri Dan Allah...." Kuka tafashe dashi, cikin kuka tace "ba kaine kace zanji dadi ba, shine Kamin mugunta" "yi hakuri, Aina baki hakuri ko, kiyi hakuri Baby na, kinji?" Shiru tayi, Sai kuka take tana ajiyar zuciya, saida yaji tadena kukan sannan yagasa mata jikinta, Shima yayi wanka, sukai wankan tsarki, sannan suka futo, gadon ya kalla gaba daya ya6aci da jini, tausayi ta bashi, cikin sauri yacire zanin gadon ya sauya wani, kayanta yadauko yabata tasaka, sannan Shima yasaka jallabiyar daya cire, ruwa yakawo mata da paracetamol Tasha, sannan ya Dora ta acinyarsa yana lallashin ta, "kiyi hakuri kinji? Wannan na farkon ne me zafi, Amma na biyu babu abinda akeji, keda kanki ma zakiyi" Cikin hawaye ta Kalle shi, gabanta na faduwa tace "dakaina zanyi me?" kafin yabata amsa, tatashi daga kan cinyarsa cikin tsoro,gaba daya tsoransa takeji,cikin d'ingisa qafa ta nufi gadon zata kwanta Sai bubbude qafa take, d'is jini yadiso akan tiles din Dakin Waheeda tana Gani tasake fashewa da Kuka, ta tsugunna a wajan tana runtse idonta, tace" shikkenan nashiga uku na, yoyon jini nafara" Yana ganin jinin Shima yace"ya Salam, kinga yi hakuri, Bari muje Asbiti aduba kinji? Yi shiru" 'Daga masa Kai tayi, sannan ta share Hawayen idonta, daukar ta yayi cimak suka futo daga d'akin, suna zuwa compound yabude mota yasaka ta aciki, sannan yazagaya zai shiga, Sai a lokacin ya kalli jikinsa yatuna ko gajeren wando bai saka baπŸ™ŠπŸ˜‚ Kansa yadafe da hannun sa πŸ€¦πŸ»β€β™‚οΈyarasa ya zaiyi? Cikin sauri yakoma ciki, ya wuce dakinsa yasaka wandon sannan yafuto suka nufi hanyar Asbiti Suna hanya Waheeda tayi shiru qwalla Sai taruwa take a'idonta, Sai yanzu take Dana Sani Dama bata Kai kanta ba, dagajin yana Waya taje tabashi hadin Kai ita Nan zatayi gwaninta Wayarsa tayi qara, yadauka tareda fad'in "Ummah" Tace "na'am son, yagida, mekukeso adafa akawo muku?" Cikin damuwa yace "Ummah, abar abincin Nan kawai" Tace "meyasa? Meyake faruwa kafadamin mana" "babu komai Ummah, Waheeda ce bata danjin dadi, zazza6i ne yake damunta, shine zan kaita asibiti idan mun dawo zan fada miki, Sai akawo mana abincin" Ummah tace "wannan zazza6in Nata ne na kwanaki ya dawo kenan, kakai ta wajan Antynku, tana mata allura zataji dadi, kwanaki ma itace tayi mata komai Sai gashi ta warke"πŸ˜‚ yazaro Idonsa yayi😳cikin sauri yace "Ummah......Anty Kuma?, a a kawai basai munje ba, zamu wuce Asbiti kawai" Ummah tace "wanne irin Asbiti gamuda doctor agida? Nafadama kaje ka kaita wajan Antynku" Kamar zai Fashe da Kuka,badan yasoba yace "to Ummah" ❀️☹️ 1/28/22, 20:52 - Ummi TandamaπŸ˜‡: IO Kwata kwata ya manta da wata aba damuwa,jinsa yake cikin farinciki da annashuwa,sun dad'e suna buga ball d'in, sannan suka koma ciki, Waheeda tashige d'akinta, Shima yashige nasa, wanka yayi yatafi masallaci, baidawo ba Sai Bayan sallar ishsha'i hannun sa d'aukeda abinci, yana shigowa ya ganta afalo tana kallo taci uban wani hijabi har qasa, zama yayi aqasa ita Kuma tana kan kujera,ya kalleta yace "wannan hijabin yayi girma dayawa acireshi mana" "Babban Yaya hijab nefa...." Tafad'i hakan cikin mamakin maganar sa, shida kullum bashida magana Sai ta hijab, bayason su saka mayafi "yes, nasan hijab ne, Amma na fad'a miki irin kayan danake so kidinga Sakamin ai ko? Shima hijab d'in ai zaiyi amfani idan Zaki fita unguwa" Cikin ladabi tace "to" "kicireshi, kisakko muci abinci, banason ganinki dashi" Ahankali tafara janye hijabin, bataso yaganta da kayan baccin data saka, saboda sunyi shara shara sosai, babu abinda baka Gani, Amma haka tacire shi ta ajiye akan kujerar, sannan ta sakko tabud'e take away d'in daya shigo dashi, kaza ce Sai shinkafa dakuma ganye agefe,binta yake da kallo kamar ya cinyeta, harta tsargu duk takasa ta6uka komai, ahankali tatashi taje kitchen tad'auko flet tazuba musu abincin sannan tace "gashinan nazuba" Yace "nagani, ai aikinki bai qareba, tunda baki Bani ba" Inda ace Dane tun kafin yafad'i haka zata fara bashi, Amma yanzu saita tsinci kanta dajin kunyar hakan, spoon tasa zata fara bashi yahanata, dole saida hannu ta dinga bashi, tana Kallan yanda yake wani Lumshe ido,shi kuwa Babban Yaya dad'i yakeji, da niyya yake had'awa harda hannunta yana tsotsa, sannan Yabarta ta d'ebo wani, saida yaji ya qoshi sannan yad'auketa, yad'ora ta akan cinyarsa, yafara bata abincin, tanacin abincin yana Kallan pink lips d'inta yanda suke shinning,kaza ya karyo yasaka mata a bakinta, cikin qasa-qasa da murya tace "Babban Yaya naqoshi" Wani irin yarrrr yaji ajikinsa, salon yanda tayi maganar ya birgeshi, Shima ahankali yace "d'an qara kad'an to....nima saiki ragemin" Tayi tunanin ta cikin flet d'in zata rage masa, shiyasa yana kawo kazar Setin bakinta saita bud'e bakin sosai tana so yasaka mata duka, saitaga yasaka mata yar kad'an, ya had'a goshinsa danata yace "ki ragemin to" Yana fad'in haka yasaka bakinsa akan Nata, Shima yafara karyar kazar, ita tanaci shi yanaci, suna cinyewa yahad'e bakinsu, saida yayi kissing d'inta, sannan yatashi tsaye itama ya miqar da'ita, yakama fuskarta ya riqe da hannayen sa, yace "meyasa tunanin ki yazama tamkar fitar numfashi na? inaso banaso dole sainayi" Murmushi tayi ta 6oye fuskarta a qirjinsa, d'ago da kanta yayi yace "meyasa bazaki kalleni ba?" Nanma murmushi tasake yi ba tace komai ba,fuskarta yasaki, sannan yakama hannunta suka nufi d'akinta ko kad'an Bebarsu sunyi kallo ba, Gani tayi yana gyara blanket zai kwanta tace "bazaka tafi d'akinka ba?" Wani irin kallo yayi mata yace "korata kike?" "a a" abinda tace kenan Ba tareda yayi magana ba yamiqa mata hannu, babu musu takama hannun sa, yasaka ta cikin jikinsa, sannan yakashe musu wutar d'akin Cikin kunnanta yace "bazaki min addu'ah ba?" "wacce iri?" cewar Waheeda "ta bacci" Shima yabata amsa Batare da tace komai ba yaji tafara karatu ahankali, can Kuma yaji tana Tofa masa, cikin sauri yabud'e Idonsa yace "yahaka? Shafawa fa ake a jikin mutum...."πŸ˜³πŸ™ŠπŸ™ˆ Batare da tunanin komai ba Waheeda tafara Tofa addu'ah ahannun ta tana shafa masa, ahankali yafara sakin sirrintacciyar ajiyar zuciya, tazo zata shafa masa a qafafunsa yaja hannun ta yad'ora akan cinyarsa, cikin wata irin murya yace"baki shafa anan ba" Jijjiga kanta tayi, sannan tashafa masa acinyar,yaso ya daure amma saiya kasa, cikin wani irin yanayi kafin Waheeda ta farga taji yad'ora hannunta akan mararsa, yariqe hannun a wajan , wani irin ihu tasaki Wanda yasa Babban Yaya bud'e Idonsa cikin sauri, hannunta ta fizge, Shima Kallan ta yayi yaga tana zaro idonta, jikinta Sai rawa yake,kamo hannunta yayi, tayi tunanin a wajan zai sake d'ora mata hannun, Sam taqi yarda, ta qanqame hannunta, cikin wata irin murya yace "meyasa?" Hawaye ne yazubo daga idonta, bata ta6a tunanin Babban Yaya zai iya d'ora mata hannunta anan wajan ba, Hawayen ta share tace "kayi hakuri Dan Allah...." Yace "so kike na mutu ko?" Cikin sauri ta girgiza masa kanta, cikin sigar lallashi yace "to kizo ki riqemin please...." Ahankali ta Kalle shi ta gefen idonta, taga yanda ya riqe abun da hannun sa, yana cewa itama tazo ta riqe masa, wani irin kuka ne yazo mata, dama wannan ne auren? Anya zata Iya kuwa? Gaskiya Gara ta gudu gida, wannan rashin kunyar har Ina? Shiru tayi, ita batajeba, Kuma ita bata gudu ba, ajiyar zuciya yayi yafusgota jikinsa, ya birkitata Takoma qasansa, shikuma ya kwanta ajikinta yace "kinaso narabu dake?" Cikin sauri ta d'aga masa kanta, murmushi yayi yace "to kibani twince dinki , da kanki..." Shiru tayi tana nazari, Sai zare ido take cikin duhu, ganin yanda tayi shiru yace "saiki za6a, koki riqemin abuna kokuma kibani Breast d'inki da kanki Nasha" Gabanta ne yafara faduwa, ga qoshi ga kwanan yunwa, babu yanda ta'iya, haka tasaka hannu ta gaban rigarta, tafuto da Breast d'inta guda d'aya, Babban Yaya yana ganin abinda take yawani lashe lips d'insa, jikinsa har rawa yake kamar mazari, yanaso yaga yanda zata bashi Boobs d'inta da kanta tamkar Babyn ta. Waheeda ta Kalle shi tace "to gashinan" tafad'i hakan muryarta na Rawa Cikin sarqewar murya yace "kibani da kanki mana.... ko so kike nakama dakaina kice nakama miki abunki da zafi?" Kallonsa tayi, idonta yaqara cikowa da hawaye, hannunta ta dora akan Breast din,tariqe shi, sannan ta kamo Kansa ta d'ora masa nipple dinta akan lips dinsa, cikin sauri yakama kamar Yaron da uwarsa ta dad'e bata bashi nono ba, iya nipple d'in kawai yake tsotsa ahankali,tareda gatsawa kad'an kad'an, daqyar yabud'e Idonsa ya kalleta yace "nine Babynki ko....?" Waheeda data fara kar6ar caji ta daga masa Kai tana sakin numfashi ahankali Ganin tafara jin dadin abinda yake mata saiya kama dayan Breast din Nata yana matsawa ahankali, dayan Kuma yana tsotsa, Waheeda tayi wata irin miqa, tana sakin numfashi me sauti Cikin sigar rad'a yace "kullum Zaki dinga Bawa Babynki yanasha miki ko....?" Cikin sauri ta daga kanta, wata irin tsotsa yasake yi mata, sannan yace "bazaki min magana ba?" Cikin wata irin murya tace "zanbaka" Bakinsa yacire daga kan Breast d'inta, yakama nipples dinta duka biyun da hannayensa, yana murza mata su ahankali, cikin fitar hayyaci yace "Zaki dinga Bani ko....?" Tace "eh" Wani irin yawu ya hadiye yace "to waye nidin? Wazaki dinga Bawa yanasha miki?" Cikin jin dadin abinda yake mata, dakuma kalaman dayake mata na tsokano sha'awa takama Kansa tariqe da hannunta, dayan hannun tashafa lallausar sumar Kansa dashi sannan tace "kaine Babyna, Kai zan Bawa" Yana jin wannan furucin Nata, yamaida Kansa Kam Breast dinta yanasha sosai da zafi zafi, hannun sa yasaka yabud'e kafarta, ahankali yayi qasa da gajeren wandonsa, yafara neman hanya, Waheeda tana can wata uwa duniya taji zafi zafi aqasan ta, hannunta tasaka a wajan anan taji abinda Babban Yaya yake qoqarin tura mata jikinta, tsoro ne yakamata, tayaya wannan uban abun nashi zai shiga? tureshi tafarayi Amma ko gizau beyi ba, Sai kokarin shiga yake, Amma abar taqi shiga, kuka tafara tana tureshi, Shima zuwa lokacin wani irin Hawayen dadi yake yana addu'ah Allah yasa tashiga, kokawa suka fara shida Waheeda, yakama hannayenta yariqe duka biyun, yana qoqarin shiga, kuka Waheeda take sosai, Nan tafara roqonsa yayi haquri, cikin qwaqwalwar sa yaji kukan Nata yayi yawa, ko kadan baya son kukan Waheeda a rayuwar sa, ahankali ya haqura, yadena neman hanyar, yajata ya rungume ajikinsa kamar zai 6allata, kissing din ko'ina yake ajikinta, saida yaji yadan samu nutsuwa sannan ya sassauta ruqon da yayi mata, Waheeda Tasha kuka tagaji Sai ajiyar zuciya take, duk da tasan beyi abinda yakeso dinba, hakan bai hanata jin zafi a wajan ba Washegari kuwa kasa kallan sa tayi πŸ˜‚ Yana Kallan ta yana murmushi, ko yayi mata magana kanta a sunkuye take bashi amsa, duk ta takura kanta kamar ba Waheedan muba πŸ’ƒ Yau tsawon kwana hudu kenan, kullum Sai Babban Yaya yanemi haqqin sa awajanta, Amma Waheeda taqi yarda, yana farawa zata fara yimasa kuka, shikuma baya son kukan ta, yana ganin tafara kukan saiya haqura, cikin kwana na biyar d'inne wajan aikinsu suka masa waya zasu buga wasa tsakanin su da Algeria, Kuma harda shi aka za6a acikin Wanda zasu buga qwallon Baqin ciki yakama Babban Yaya, kawai to ya cewa couch d'in nasu, saboda beso hakan ba, yaso ace yamaida Waheeda cikakkiyar mace kafin ya dauketa sutafi honeymoon dinsu. yauda safe suna gama cin abinci ya kalleta yace "kishirya zan maidake gida" Cikin sauri ta Kalle shi, tayi tunanin wani laifin tayi, tace "meyafaru Babban Yaya?" Kafad'a ya d'aga yace "an kirani ne, a wajan aikina" Ajiyar zuciya ta sauke, tayi tunanin wani laifin tayi, zaice zai maida ta gida,ahankali tace masa "to yaushe zaka dawo?" "babu rana" yafad'i hakan ransa a6ace, itama tanajin wannan furucin taja bakinta tayi shiru, tasan cewa ransa a6ace yake Bata d'auki komai ba, kawai hijabinta tasaka, suka tafi, suna zuwa compound din gidan Ummah yayi parking,kafin suyi sallama yajuyo ya kalleta yace "karki dinga wasa dasu Ihsan har kuzo Ana rabaku akan abinda baikai yakawo ba,nasan halinki bakida kunya, kikama girmanki, da da dayanzu ba daya bane, duk abinda kike buqata kidauki ATM dina kije ki siyo kokuma kisa su Sa'eed su siyo miki" Tace "Babban Yaya, kaida kace yanzu na girmi Ihsan nikuma tayaya zan kulasu har muyi fad'a?" Cikin sauri yace "tayaya kika girmesu? Bayan kinqi Bani damar dazan maidake Antyn su?, Ina ta6abaki Sai kuka, ko bakya jin dad'in abinda nake miki?" Yafadi hakan yana Lumshe Idonsa Wata irin kunya ce takama Waheeda, tasaka hannunta tarufe fuskarta, Sai yanzu ne tagane inda yadosa, ashe Dama Abaya haukanta take tana hura hanci ita tazama babba, ashe wannan abun ne girman, cikin sauri ta6ud'e motar tatafi da gudu, ajiyar zuciya yasaki yanabin Bayan ta da kallo harta shige falo, sannan yayiwa driver magana yazo yajashi suka tafi Satinsa d'aya da tafiya Waheeda taci gaba da zuwa makaranta dayake exam ma suke, yanzu tayi Hankali ta nutsu ta daina hauka, ko agida haka zaka ganta a zaune waje d'aya, wani lokacin har kunyar Ummah take ji saboda Gani take duk abinda yafaru tsakanin ta da Babban Yaya Ummah tasani, haka kawai saita dinga tsarguwa idan tana cikin su, da daddare kuwa kasa bacci take, tana ganinsu Ihsan suna kwasar baccin su Amma ita saide taita juye-juye, Kuma ba komai ne yake damunta ba Sai tunanin mijinta, Ida tunanin yayi yawa harji take kan nononta yana mata qaiqayi, saide tasa hannu ta Sosa Amma hakan bazai Hana anjima tasake jin wani qaiqayin ba, idan ta kirashi da wayar su Ihsan baya d'auka, saboda yasan itace, Sai yanzu ne take DANA SANI (first novel) akan hanashi haqqinsa da tayi ta dinga wahalar dashi, Sai yanzu yake bata tausayi, yau Satinsa biyar da tafiya, a ranar ne Kuma su Waheeda suka gama makaranta, sannan a ranar ne zasu buga wasansu, Hajiya Anty da Uncle Usman duk sunzo gidan antaru za'a kalli ball d'in, Anty Maryam itama tazo harda junior me sunan Babban Yaya, gaba d'ayansu sun nutsu kowa hankalin sa yana kan TV, Waheeda tana Gefe tana kallo itama,carbi ne a hannun ta Sai addu'ah take cikin ranta Allah yabawa mijinta nasara, dayake addu'ar mata akan mijinta batada hijabi a wajan ubangiji,cikin ikon Allah Ana fara wasa kuwa Babban Yaya shine mutum nafarko daya fara Ci, yana ganin yaci ya tsugunna yayi sujud shukr. su Sa'eed suka tafa shida Sa'ad, falo kowa yafara murna Wasa yayi wasa kowanne team sunaso sunga sunci, har tsawon wani lokaci sannan wani d'an team d'in su Babban Yaya yaciyo musu, Babban Yaya yana kar6ar Ball d'in ya dinga Sakata araga, saida yaci Sau uku ajere, Bayan guda d'ayan daya faraci, gudu yake sosai yana d'aga hannu, Yan team dinsu suna binsa Abaya, cikin murna suka rungume shi, Ummah bakinta yaqi rufuwa, Sai murmushi take idonta yana kan TV, su Daddy da uncle ma sunyi shiru kowa yana Gani, Hajiya Anty de addu'ah take cikin ranta Allah yakare mata d'annata, Allah yasake d'aukakashi yad'ora shi akan maqiyansa. anci gaba da wasa kenan Babban Yaya yasake nasarar kar6ar qwallo daga wajan d'ayan team din, ya d'aga qafa zai bugata kenan Shima wani yakawo tasa qafar jikake qassss, yabige qafar Babban Yaya, lokaci daya jama'ar dasuke studio din suka fara fadin ohhhhh! Lokaci daya hankalin masoyansa yatashi, suka miqe tsaye, cikin azaba Babban Yaya yariqe qafarsa yana runtse ido Waheeda taji kunnanta yayi mata wani dimmm haka kamar bataji, kamar Kuma a mafarki, miqewa tayi tsaye tanufi gaban TV, gabanta yana fad'uwa, tuni hawaye suka wanke wa Ummah fuska ganin ankawo wani irin gado marar qafa, andora Babban Yaya akai, anfita dashi daga filin wasa Kallan Daddy tayi cikin kuka tace"Alhaji tafiya zanyi, sun kashemin Dana " Cikin tashin Hankali daddy yace" Ina zakije Hajiya? Kiyi hakuri mana " Uncle Usman yafara neman wayarsa, Hajiya Anty ta Kalle shi cikin rawar murya tace" bazaka sameshi ba, yacemin kashe wayarsa zaiyi idan zasu fara wasan " tana fad'in hakan hawaye yazubo daga idonta, su yanbiyu ne suka janyo Waheeda, Sai girgiza kanta take tana hawaye Amma takasa magana, Sa'ad yatashi yakashe Kallan, Anty Maryam tariqe Waheeda tace" kiyi hakuri Waheeda, insha Allah zaiji sauqi " Cikin kuka tace"niku rabu dani, ku d'in shiru zakuyi idan mijinku ne?, Dan Allah Dan Annabi Daddy kabarni natafi, dama fishi yake Dani, qilama nice sila....." tafadi hakan tana fashewa da wani irin kuka Hajiya Anty ta rungume ta tana bubbuga Bayan ta, babu Wanda baiyi kuka ba acikinsu, saisu Daddy kawai, suna mutuqar qaunar d'an'uwan nasu, haka suka zauna shiru suna faman addu'ah, shide ba'a Nigeria yake ba bare sutafi koba visa, a wata qasa yake, Kuma yanzu dare ne dole zasu jira suga wanne mataki qungiyar tasu zasu dauka akan ciwon da yaji Babu Wanda yayi yunqurin kwanciya acikinsu, kowa wayace ahannunsa yana try number Babban Yaya ko zata shiga, Waheeda ce kawai babu waya Sai faman kuka take har numfashin ta yana sama kamar wadda take shirin suma, Sai wajan karfe biyu sannan cikin sa'a Daddy ya sameshi, cikin sauri ya miqe tsaye yace "Alhamdulillah tashiga, yabud'e wayar" Kowa Matsowa yayi kusa da Daddy duk suka taru suka yanyameshi, Daddy daya ga haka saiya saka wayar a hands-free, harta katse bai d'auka ba, saida yasake kira Akaro na biyu sannan yada'auka, kuka yafara ji yana tashi sama sama Kuma ba kukan mutum d'aya ba, cikin ransa yace sunga abinda yafaru kenan Daddy yace "Son, kana lafiya? Yaya jikin Naka?" Kafin Babban Yaya yayi magana Ummah ta qwace wayar, cikin kuka tace "kafadamin halinda kake ciki, Hankali na yakasa kwanciya, sonake nataho, bazan iya zama ba" Ahankali yace "Ummah...., ki kwantar da hankalinki, anduba min qafar, harma sun Bani injury, zan dawo gida insha Allah" Cikin kuka Ummah tace "karka dawo in kasan jikin babu sauqi, mu saimu biyo ka"β€οΈπŸ˜‚ Memakon yabata amsa saiyace "Ummah Ina Anty? Ina Waheeda?" Wayar tamiqawa Hajiya Anty, Anty ta share Hawayen idonta, sannan takar6i wayar tace "sannu Naufal, yajikin naka?" Ahankali yace"jiki da sauqi Anty, kikulamin da Waheeda nasan Hankalinta yatashi " Anty batayi magana ba, saita Bawa Waheeda wayar, saboda tasan yana jin nauyin ta bazai iya cewa tabawa waheedan waya ba, Waheeda kuwa tana kar6ar wayar Takoma Gefe, kuka take sosai takasa magana, cikin sanyin murya yace"kiyi shiru..., ba sosai bane ciwon" Cikin kuka tace "kayi hakuri nadena, daga yanzu nadena hanaka komai, naji tsoro sosai, jinake kamutu" Wani irin dad'i yaji ya ratsashi, yanzu Kam yagama tabbatar wa Waheeda tana sonsa, saboda haka wannan ciwon Koya warke bazai nuna mata hakan ba, yasamu mafaka ta yanda zai dinga zuba mata shagwa6a son ransa Ahankali yace "I luv you so much.......muahhhh,, muahhhh" πŸ’‹πŸ’‹ Yasakar mata kiss har biyu ta cikin wayar, sannan yaci gaba da fad'in "kimin addu'ah kinji, insha Allah zanji sauqi, jeki kaiwa su Daddy wayar Tace"to" sannan tatashi takai musu wayar, Sai a lokacin Hankalinta ya kwanta, Sai ajiyar zuciya take, jikin Hajiya Anty Takoma ta lafe kamar wata mage, bata Jima da kwanciya a jikin nataba bacci yasoma d'aukarta Yana gama wayar dakowa acikinsu harda junior, sukai sallama Bayan yagama kwantar musu da Hankali, Kiran mashkur ne yashigo wayar tasa, d'auka yayi tareda sallama, mashkur yace "friend mutanan nanfa sun hanamu shigowa Dakin, sunce har yanzu kana buqatar hutu, Sai lalla6a ka suke kamar qwai"πŸ˜‚ Murmushi yayi yace "rabu dasu mashkur, zamu hadu ai idan nafuto insha Allah, ciwon fa Bana kirki bane, kawai tsagewar qashi ne, da niyya na langwa6e musu, nagaji da ball d'in Dama hanyar guduwa wajan amarya ta nake nema, to Kuma Sai haka tafaru....." πŸ™Š Mashkur ya kwashe da dariya yace"wato me jiran kukane aka jefeshi da kashin awaki, banga laifin ka ba Abokina,Naga ma sun sanar katafi injury, Kasha Amarci lafiya...." Babban Yaya yayi murmushi yace "thanks Friend" Pls kuyi hakuri Dan Allah πŸ™πŸ»πŸ™πŸ»πŸ™πŸ»πŸ™πŸ» 1/28/22, 20:52 - Ummi TandamaπŸ˜‡: FQ Juyowa yayi ya kalli Waheeda, rage murya yayi yace "ya zanyi?" Cikin shagwa6a tace "ba saida tace katafi ba kaqi, yanzu gashinan zakasa naji kunyar ta, wallahi nide babu ruwana" Daga baqin kofa Hajiya Anty taji shirun yayi yawa tasake nocking tareda fadin "Daughter" Tashi yayi cikin sauri yabud'e kofar, yayi wuf yafad'a cikin toilet, Hajiya Anty tashigo Dakin fuskarta d'aukeda mamaki, ga Waheeda a kwance,Kuma taga Anja kofar toilet anrufe, to waye aciki?πŸ€” Zama tayi agefen gadon ta'ajiye mata, yanda qamshin turaren Babban Yaya ya cika Dakin shine ya tabbatar mata da cewa yana Nan betafi ba, cikin ranta tace wannan yaro da jaraba yake kamar ubansa πŸ™Š ta kalleta tace "tashi kici" Waheeda tatashi tad'auka tafara ci ahankali,tana tunanin Babban Yaya, gaskiya maza basuda kunya, yanzu Babban Yaya harya iya Kallan Anty, Bayan Antyn tasan abinda yamata, ta tuna yanda yashige toilet da gudu, Sai abun yabata dariya Tayi murmushi kawai, Hajiya Anty ta zauna a Dakin tana jiran taga ta inda Naufal zai futo, idan ba tsawatar masa tayi ba, yarinyar Nan saita shiga ukunta, shiru shiru har tsawon minti Goma bai futo ba, data gaji da jira saita daga murya tace "jiranka nake kafuto Naufal" Dariya takama Waheeda, bata iya 6oyewa ba saida ta Dara Ahankali yabude kofar toilet din yafuto Kansa aqasa yana Sosa qeyarsa,kunnansa takama ta riqe da qarfi, cikin jin zafi yad'ora hannun sa akai yace "Auchh!" Cikin rashin wasa tace "Naufal, meyasa bakajin magana ne? Nahana ka zuwa wajan yarinyar Nan daga Nan har tsawon kwana Goma" Cikin azaba yace "to Anty" Sakinsa tayi, cikin sauri yafice daga d'akin. tajuya ta kalli Waheeda tace "kekuma harda dariya ko?" Waheeda ta sunkuyar da kanta qasa, Hajiya Anty Kuma tajuya tafita falo ta zauna, tareda kunna kallo tana gadin Waheeda Baidawo gidan ba saida daddare, Bayan yagama rufe musu ko'ina na gidansu, falon yashigo zuciyar sa daya, yana d'ago Kansa tareda sallama sukai ido biyu da Ummah, cikin sauri ya sunkuyar da Kansa,yana tunanin meya kawo ta gidan itada bata zuwa? Anya kuwa ba Anty ce ta fada mata komai ba tazo ganin Waheeda? Zuciyar sa ce tabashi cewa Ummah tariga taji komai, lokaci daya ya tsinci Kansa da kunyar ta, ahankali yaqara so ya tsugunna agaban su yagaida Ummah Mamaki yakama Ummah, tace "yanaga kana sunkuyar dakai yayansu? Kuma ga jaka ko tafiya zakayi? Baka gajiya da yawo daga dawowarka zaka sake tafiya? Ko kewata bakayi ko? " Waheeda dake Gefe tayi murmushi, Kansa ya shafa yace"Ummah Ina Nan, Nan gidan muka dawo ne" Ummah ta Kalle shi, Kallan rashin fahimta, Hajiya Anty tace "kuka dawo Kota dawo?, itace tadawo Nan, Amma Kai ai kasan hanyar gidanku, konan gidanku ne?" Ummah tace "me yayi ne kike wannan fadan akan gida? Zamu bar miki gidan" tajuya ta Kalle shi tace "tashi mutafi" Kansa ya shafa yaqi tashi, Kuma yaqi d'ago Kansa ya kalleta, tunda yake da'ita, Bai taba tunanin akwai ranar da zaiji kunyar Ummah ba, Amma yau gashi shine yake kunyar ummah saboda Waheeda Hajiya Anty tace "wallahi danaji dadi, yabiki kutafi, dama ban gayyace Shiba, idan yazo nanma takura mata zaiyi da naci" Ummah tanajin haka tad'auki haske, Sai yanzu ne tasan dalilin kunyar, ashe shiyasa yaqi hada ido da ita, ashe dannata ya girma, murmushi tayi tamiqe tsaye tace "to saiki bashi matarsa tunda bakya son naci" Hajiya Anty tamiqe tabi Bayan ta zata mata rakiya, yana ganin fitarsu yamatsa kusa da Waheeda ya zauna aqasan kafet din, lips dinsa yad'ora akan Nata ya sakar mata kiss, sannan yakoma ya zauna yad'auki remote kamar bashine yayi ba, zaro ido tayi cikin mamaki, kafin tayi magana Anty tadawo falon, ganin Naufal a zaune aqasa kansa yana kan TV yasa ta share shi itama ta zauna, har qarfe goma suna zaune kowa yana kallo, goma da rabi nayi Uncle yashigo, dariya yayi, ganin Yanda Anty tasasu agaba takafa ta tsare, Sai yanzu ne tasan abinda yafaru kenan zata takurawa yaro, aishi tunda safe daya ga anshigo da'ita a hannu yasan akwai abinda yake faruwa, yasan dannasa ya angonce Zama yayi Shima, yanadan Jan Naufal din da zance harya sake suke zancen su kamar ba d'a da uba ba Sai dariya suke kamar ba dare ba, anty tana Gefe tana Kallan su, Waheeda kuwa bacci take akan kujera, Anty jira take taga Naufal yaje ya kwanta sannan tatafi da Waheeda daki, to taga alamun ba tafiya zaiyi ba, danhaka tatashi Waheeda suka tafi dakinta, babban Yaya yana kallonsu qasa qasa jiyake kamar ya kurma ihu, koba komai yakamata ace yaji dumin matarsa kafin taje ta kwanta, saida suka gama zancen su shida uncle sannan yayi masa saida safe yatafi dakinsa ya kwanta, Sai yau yake baqin cikin rashin wayar Waheeda, koda muryarta yaji yasan zaiji dadi, haka ya dinga juyi akan gadon, idan ya runtse Idonsa ma ita yake Gani, Sai tsaki yake saki shi kadai πŸ˜– Anty kuwa tare suka kwanta da Waheeda akan gadon ta, Sai wajan qarfe daya ta shirya tatafi wajan Uncle, yana zaune akan sallaya,addu'ah ya shafa yahau gadon tareda janyo ta jikinsa yace "yakamata kibar Yaron Nan yahuta da matarsa, Sai kallanta yake kin tafi da'ita daki, Ina masa magana Amma hankalin sa yana wajan matarsa" "Alhaji yarinyar Nan ta wahala, dazu saida doctor ladi tayi mata dinki wallahi,anbata hutun kwana goma, saiya Bari saita warke" Uncle yace "har kwana goma? Ke bakya tausayin Yaron ne? Shekararsa nawa babu aure? Kibawa yaro matarsa yaje yaci gaba daga inda ya tsaya, saiki ja masa kunne kawai" "ni nace karyayi auren dawuri? Ina barinsa zaije ya lalata mata dinki, yaje yakoyi haquri" "a a wallahi, idan yashiga wani Hali fa, ke bakyajin tausayin sane, mutum da matarsa, ai Shima yasan yanda zai lalla6ata ko" "Alhaji, bafa zan bashi yarinyar nanba, abarta ta warke, koma me zaiyi yaje yayi, daga lalla6awa ai zai zarce, yarinya duk tayi fari ta d'ashe rana d'aya saikace Mai ciki" "to shikkenan, Allah yabata lafiya" Hajiya Anty tace "Amin" Wasa wasa saida Waheeda tayi kwana Tara, Hajiya Anty takafa ta tsare babu abinda Babban Yaya yayi mata, duk wani motsinsa akan idonta yake yinsa, har so yake ta shirya ko zataje Asbiti Amma yaga shiru, ashe hutu ta dauka saboda kula da Waheeda, acikin kwanakin Nan hauka ne kawai baiyi ba, wata irin sha'awa yakeji tafitar Hankali, idan kayi masa magana ma jinka kawai yake, Amma ba fahimta yake baπŸ˜‚ Ranar data cika kwana goma yana idar da sallar asuba yabar uncle a masallaci ya dawo gida, yana kwanciya yaji mararsa ta riqe, tashi yayi ya dinga zagaye Dakin har gari yayi haske, futowa yayi daga d'akin yanufi Dakin Hajiya Anty Kansa tsaye, yana shiga yaga Waheeda tana bacci, Anty Kuma tana toilet, hannu yasaka ya d'auketa cimak, tana bacci taji anyi sama da ita, cikin sauri tabude idonta, tana ganinsa ta zaro ido, hannu yasa yarufe mata baki, Bai tsaya ko'ina ba Sai dakinsa, akan gadon ya dorata, cikin sauri tatashi zaune tace "Babban Yaya...." Kafin tayi wata maganar ya katseta, yace "nifa ba komai zan miki ba, kawai duminki zanji" Yana fadar haka yacire jallabiyar jikinsa, Waheeda tana ganin kyakykyawar qirar jikinsa, gabanta yafadi, saboda tasan zaiyi wahala yayi abinda yafada, idonta ne yaraina Fata, tayi tsilli tsilli akan gado, shi Kansa daya kalleta tabashi tausayi sosai, to Amma Yaya zaiyi? Gajeran wandonsa yacire, cikin sauri tasaki ihu tareda rufe idonta, qarasowa yayi kan gadon yakama hannun ta yabude fuskarta, cikin sigar rad'a yace "bazaki kalleni ba?" Hawaye ne yazubo daga idonta, ita Kuma qaddarar ta kenan, ta auren yayanta, gashi yana mata abubuwa masu wahalar Fassara, girgiza masa kanta tayi tareda runtse idonta, hannun sa yakai Bayan ta yacire mata Zip din rigarta, tareda cire rigar gaba daya yace "meyasa? Ni kike tsoro?" Girgiza masa Kai tasakeyi, yace "to bude idonki ki kalli abunda yasaki kuka rannan, niba nine nasaki kuka ba, shine, yakamata kiyi masa hukunci Mai tsauri" Cikin ranta tace nashiga uku na da wannan mutumin, ahankali tace "Babban Yaya Dan Allah kabari, Anty fa zata Iya shigowa, kabarni in tafi please, Allah tsoro nakeji" Cikin wata irin sha'awah yace "bazata shigo ba" Tace "Allah zata shig...." kafin ta qarasa yafada kanta, tareda hade bakinsu waje daya Wata irin soyaiya Mai tsayawa Arai yafara nuna mata, tunawa da tayi da ranar farko yasa taqi sakin jikinta, Amma dataji yanda yake wasanni da'ita batasan lokacin data bada Kai ba, kayanta yacire mata gaba daya, yaja bedsheet yarufe su, bakinsa yad'ora akan boobs dinta ya dinga tsotsarsu tamkar wani jariri sabuwar haihuwa Yadauki lokaci Mai tsawo yana abu daya kafin yafada cikin kogin ni'imar Waheeda, yayi mamakin yanda yaji wajan kamar ansake rufe shi, lokaci daya yasaki abinda yasaba, wato kuka πŸ˜‚ Ita kanta Waheeda bataji wani banbanci ba Dana farkon Hajiya Anty ta shirya tsaf cikin uniform dinta na Asbiti zata tafi wajan aiki, Sai a lokacin ta lura babu Waheeda a Dakin, tasan yanzu Naufal yana bacci, saboda haka may be ta zagaya gidan ne tunda kullum tana zaune adaki Jakarta ta dauka tafuto daga d'akin, but tana futowa falon taji wani irin kuka na tashi da gurnani, gabanta ne yafadi, cikin sauri ta nufi Dakin Naufal tayi tunanin ko wani abu ne yasame shi, tana zuwa bakin kofar Dakin taji yana kuka yana fadin "wayyo Allah naaaaa....Waheee ....daaaa,dadi" Cikin sauri tabar wajan, hamdala take cikin ranta da Allah yasa Uncle Usman baya Nan, ita kanta tasan yayi kokari a naci irinna Naufal, batabar gidan ba saida taja musu kofar falon tarufe, sannan tashiga mota ta wuce wajan aikinta Kwana biyar suka qara a gidan Hajiya anty, wayar Waheeda ta qaraso, irin wadda takeso din kamar yanda ta fada masa, cikin satin sukai sallama da kowa suka wuce Saudia shida ita dakuma Maya Satin su biyu a Saudia, Babban Yaya yahadawa Maya tsaraba sosai itada iyayenta, tadawo gida, shikuma ya wuce honeymoon shida amaryar sa zuwa Dubai Satinsu biyu a Dubai Babban Yaya yana shan amarcinsa son ransa, zuwa wannan lokacin harta saba, ita kanta tafara jin dadin abun kadan kadan Daga Dubai England suka wuce wajan aikinsa, suna zuwa gidan, jikin Waheeda yayi Sanyi, ta tuna lokacin da sukazo da ita, yanda take santin gidan alokacin yace mata idan taso zai iya zama gidanta, ganin yanda take tafiya ahankali jiki a sanyaye yayi tunanin gajiya tayi, Dan haka yasaka hannu ya sureta sukai cikin gidan, nanma suna shiga falo tatuna da Didat, wancen zuwan da tayi dashi ta dinga waya tana bashi haquri dakuma fahimtar dashi akan Babban Yaya yayanta ne,suna zuwa daki suka zube akan gadon, Waheeda tasake tunawa yanda sukai ta birgima akan gadon ita dashi wancen zuwan, alokacin Gani take babu ya Huzaifa, rayuwa kenan Dama hakane, zakayi samari kalakala ma banbanta, Amma bakasan dawa zakayi rayuwar aure ba, Babban Yaya ne ya katse mata tunanin ta, yace "Baby nagaji dayawa, wanka zakimin, dama yau baki minba, baki wanke abarki ba yau" ya qarasa maganar yana murmushi dimple dinsa na lotsawa Cikin shagwa6a tace "Naga takaina ni Waheeda Wai Dan Allah Babban Yaya waye yafada ma wannan maganar ne? Nide nasan dagani Sai Maya, dakuma Ummah mukadai mukasan maganar, Kuma nasan sude bazasu fadama ba" Murmushi yasake yi yace "Ina ruwanki da Wanda ya fadamin, Nima bazan fada ba, tunda alokacin ko gidan Nan zai zama shaida saida na tambaye ki laifin me ki kaiwa Ummah, Amma kikace min ba komai" Cikin shagwa6a tace "to Naga alokacin Kai Yaya nane, tayaya zan fadama" "yanzu Kuma fa? Ni menene?" Shiru tayi taqi bashi amsa, Sai wani kallo datake watsa masa na soyaiya Tashi yayi yacire kayansa, yashige toilet zaiyi wanka, yana shiga itama tacire kayanta ta daura wani Dan qaramin towel , taje wardrobe tasaka kayan, tana kokarin rufewa idonta ya sauka akan dairy din Babban Yaya, Wanda tafara karantawa kwanaki, dauka tayi, ta zauna abakin gadon tabude tafara karanta wa Gaba daya shafin farko Dana Gaba, tarihin rayuwar gidansu ne tun kafin ahaifeta, Sai kuma lokacin da aka haifeta da yanda ta sauya komai na rayuwar sa, yanda yake fuskantar matsala idan ya ganta da wasu mazan, da yanda ya baiyana tsananin yanda yake sonta acikin zuciyar sa, tausayi yabata, lokaci daya hawaye ya wanke mata fuska, tana karatu Amma hawaye yana d'isa akan paper, batasan yafuto daga toilet dinba, saijin maganar sa tayi akanta "idan kin gama karatun nafuto" Tana d'ago kanta data ganshi, tatashi da sauri ta rungume shi tareda fashewa da Kuka, Shima qwalla ce tafuto daga Idonsa, ahankali yace "menene abun kukan to?" Dagowa tayi daga jikinsa takai masa duka a qirjinsa, sannan tasake rungume shi cikin kuka tace "meyasa bazaka fadamin ba?" Murmushi yayi yace "idan nafada miki ma nasan bazaki Soni ba, lokacin danace zan aure ki cewa kikai bakya sona..." Tausayi yasake bata, tasake rungume shi sosai a qirjinta, saboda ita duk ya fuskanci matsi dakuma takura a wajan iyayen sa saboda aure, hannunta daya tacusa cikin lallausar sumar Kansa, cikin hawaye tace "I love you so much Babban Yaya, I can't life without you.... Ina qaunarka, please karka Barni" Wani irin dadi ne ya ratsashi, ahankali yace "I love you too Baby..., zakisa nasake wanka fa,Bayan Kuma bayimin zakiyi ba, qiri-qiri de kinqi ki wanke abarki" yaqara sa maganar cikin sigar tsokana, dariya ce ta kamata, tasaka bakinta awuyansa ta sumbace shi ❀️ 1/28/22, 20:52 - Ummi TandamaπŸ˜‡: XV Wani irin dadi yaji, ya Lumshe Idonsa, ahankali yace mata "karki Dena Dan Allah..." Murmushi tayi ta Kalle shi tareda dora harshanta akan lips dinsa tana lasa, daga qarshe tahade bakinsu tana nuna masa tsantsar yanda take sonsa, tsayuwar gagararsu tayi, suka fad'a kan gadon, yana kwance tana samansa itace ta dinga yin komai, babu bata lokaci yafara Hawayen dadi, Bai taba tunanin zata Iya masa irin wannan soyaiyar ba, Bayan komai yagama wakana kukan shagwa6a yasaka mata Sai tayi masa wanka, tunda yayi abinsa tazo ta 6ata masa, babu yanda ta'iya haka suka koma toilet din yau dai tayi masa wanka, haka yaqiyin komai Yabarta ta wanke shi tas, tana murmushi tana masa wanka Dan dolenta yau takama abarta ta wanke πŸ™ˆ Saida sukai kwana biyar a gidan, babu inda suke fita kullum suna gida suna manne da juna, Waheeda Kai yawaye, tadena kunyarsa ko kadan, ta haqura ta saduda ta riqeshi a matsayin mijinta, yanzu ko kwanciyar aure zasuyi baya yin komai, ita yabawa Dama ta dinga yimasa duk abinda takeso, kwanansu shida yakoma bakin aikinsa, wani lokacin agida yake barinta, wataran Kuma sufita tare, duk yanda takejin kishin mijin Nata, haka take kokarin danne zuciyar ta, ta tsani taga mata suna rububunsa, jitake kamar zuciyarta zata Fashe, Amma idan ta tuna dan'uwan Nata bamai yawan magana bane da biyebiyen mata Sai hankalin ta ya kwanta, shi Kansa miskilin Kansa ne, idan kikace Zaki soshi ma haushi ne zai kamaki, Amma Kuma suna dawowa gida saiyayi lallashi, Dan ta dinga kumburi kenan akan danme yanmata zasu dinga kulashi, shi Kansa babu yanda ya'iya saide yarage murya yabata hakuri kawai Yau agida Yabarta, tunda tatashi takejin zuciyarta tana tashi, duk abinda taci Sai amai, tun abun baya damunta har tazo tana damuwa, kitchen tashiga zata soya qwai taji kasala ta rufeta ga zazza6i, babu shiri tadawo falo ta takure akan kujera, wayarsa ta dinga kira zata fada masa, shikuma a lokacin suna training, saboda suna shiryen shiryen buga world cup ne, wayarsa bata hannun sa, lokaci daya taji wani baqin ciki ya kamata, ita kanta tarasa meyasa yanzu ko Yaya yayi mata laifi 6acin rai takeji marar misali, abu kad'an saiya 6ata mata rai Haka ta wuni a wajan sallah ce kawai take tashinta, yana dawowa ta daga Kai ta Kalle shi ta watsar😏 Zama yayi aqasan ta yazuba mata ido cikin murmushi yace "yau Kuma laifin menayi gimbiya? Babu oyoyo babu komai Sai fishi?" Cikin 6acin rai tace "bakasan ma mekayi ba? Inata Kiran wayar ka kaqi dauka, Kuma dakuka tashi baka kirani ba" Yanda yaga tana magana daqyar Kuma a hakan ita masifa take, Bai kulata ba yad'ora hannun sa akan wuyan ta yaji zafi zau, cikin damuwa yace "subhanallah.... Ai zazza6i nema ajikinki, Wallahi kinga wayar tana cikin jaka, a silent take, sannan damuka tashi sauri nake inaso nazo naganki, tashi muje Asbiti naji jikin naki da zafi" Shareshi tayi, tajuya masa baya, wayarsa yadauko a jakar yaduba anan yaga harda missed call din Hajiya Anty, kiranta yayi Bayan sun gaisa tace "Ina Waheeda" Tace "gatanan Anty, kinga fishi takema saboda takirani ban dauka ba, wallahi Anty training muke, nafada miki muna shirye shiryen buga world cup ne, Sai sauri nake nazo na ganta in mata albishir zamu tafi Nigeria, duk da yawan mu kowa qasar sa zai tafi, Nima Kuma wannan Karon Nigeria zan bugawa, to kinga tamaqi kulani ta juyamin baya, Kuma naji jikinta akwai zazza6i nace mata muje Asbiti tayi shiru, Allah Anty yanzu komai nayi mata saita dinga min fada" ya qarasa maganar kamar zaiyi kuka Anty tayi murmushi tace" bata wayar " Wayar yamiqa mata Shima ya kawar dakai alamun yayi fishi yace" ga waya inzaki karba, inbazaki karba ba inkashe wayata"πŸ˜‚ Cikin haushi tace "kakashe" "au haka kikace?" Yamaida wayar kunnansa yace "Anty ai kinji ko? Kinji de da kunnan ki ko? To tace na kashe bazata karba ba" Anty tayi murmushi tace "Naufal, banason shirme bata waya nace" Wayar yad'ora mata akan kunnan ta yakoma Gefe ya zauna yana girgiza qafa, Waheeda najin muryar Anty tatashi ta zauna tace "Anty Ina wuni" Hajiya Anty tace "Daughter, meyake damunki? Fadamin meyafaru?" Ahankali tace "Anty shine nakirashi yaqi dauka,tunda safe nake amai duk abinda naci sainayi amai, Kuma nakirashi ne dama infada masa, Kuma kullum Sai mata su dinga binsa suna liqe masa, kowacce mace saida dinga binsa tana masa Iyayi, Allah ni nagaji...." ta qarasa maganar tana fashewa da Kuka Babban Yaya ya Juyo da sauri ya kalleta, dama fishin duk saboda kishin sa ne? Wani irin dadi yaji, shida yake kuka saboda soyaiyar Waheeda itama gashi tana kuka saboda tasa soyaiyar, murmushi yake yana kallonta Tajuyo ta daka masa harara ta kawarda Kai Anty tace "Daughter kina Jina? Ki kwantar da hankalinki, na tabbatar Yayanku yana qaunarki, mata nawa yaqi saboda ke? Wanne irin 6acin raine bai sakamu aciki ba saboda ke? Kema da kanki cewa kikai mata ne suke bibiyarsa, ki godewa Allah tunda bashine yake bibiyarsu ba, ki watsar da wannan kishin naki ki ringumi mijinki, kar wasu mata su dameki, kanki kika Sani, ai yasan matan suna bibiyarsa Amma ya liqe miki, yaqi auren kowa saike, duk wadda kikaga tana son mijinki kitayata sonshi, kedai karki bashi kofar dazai dinga sauraransu, ki riqe mijinki dakyau ko kadan karkiyi sakaci, karki bada kofar da wata zata shigo, Nima kaina bazan Bari yayanku yakawo miki wata ba, Amma idan kin kwantar da hankalinki kinyi abinda nace " Tashi tayi daga wajan, ta matsa Gefe tace" to Anty zanyi, Kuma magungunan dakika Bani duk sun qare " "kiyi hakuri Daughter wasu suna Nan na ajiye miki, yacemin gida zaku taho, Kuna dawowa zan kawo miki, kinji dai abinda nafada miki, kidena wannan kishin kinutsu ki mallake mijinki" Ahankali tace "to Anty" "yawwa Daughter, bashi wayar ki shirya kuje asbitin" Zuwa tayi tabashi wayar, sannan ta wuce daki ta sauya Kaya tafuto Anty tace "Naufal, Ina tunanin yarinyar nanfa ciki gareta" Cikin sauri yace "Allah Anty?" Tace "qwarai kuwa, kadena damuwa da wannan 6acin ran Nata, ciki yana saka haka, Amma kuje asbitin aduba ta" Cikin murna yace "to Anty, Alhamdulillah" Yakashe wayar, ya kalleta yace "to madam Waheeda muje ko?" Cikin fishi tace "saide ka goyeni" Dariya ce ta qwace masa, yace "yarinyar Nan.... Kodan shikkenan zoki hau" Ya tsugunna agaban ta, tahau bayansa suka fita, saida yasaka ta amota sannan yashiga suka tafi Asbiti Suna zuwa kuwa, gwajin farko suka Gano tana d'aukeda ciki wata daya, tun a asbitin ya d'auketa yana juyi da'ita, mutane Sai dariya suke masa kasancewar sa sanannan mutum, wasu daga cikin doctor's har video suke musu, wasu Kuma picture Suna dawowa gida yad'ora ta akan cinyarsa yana shafa cikin, cikin murna yace "kamar yanda nake jefa qwalla araga, yanzu ma nayi nasarar jefa wata qwallon acikin ragar mata ta, kinsan nidin jarumi ne" Dariya tayi tace "Babban Yaya ai kaine kake yabon kanka da kanka, Kuma anfison ayabi mutum" Kafin yabata amsa wayar intisar tashigo, dauka yayi yace "intisar" Ummah tayi murmushi tace "ba intisar bace, nice, yanzu suka taho da gudu itada Ihsan suka nunamin photon ku a Asbiti Wai Waheeda tana da ciki, hakane?" Kunya ce ta kamashi, ya sunkuyar da Kansa kamar tana ganinsa yace "hakane Ummah" Tace "Alhamdulillah, to Allah yaraba lafiya" daga Nan ta kashe wayar, danta lura yanzu Naufal kunyar ta yakeji Waheeda ta zaro idonta tace "Wai har sunji?"😳 Hararar wasa yayi mata yace "mekika daukeni ne? Nafada miki ni jarumi ne, Sunana Naufal Umar Arabo a.k.a Big Brother, ni mashahurin mutum ne, inayin abu kad'an, zakijini ayanar gizo" Murmushi tayi tace "nayarda...." Fuskarta yakama da hannun sa yace "Ina sonki Waheeda, abinda nasani kenan, Bayan haka bazan iya fada miki komai ba saide kigani a aikace kawai, Allah yayi miki Albarka, Allah yarabaki da Baby na lafiya" Tace "Amin" tareda shigewa cikin jikinsa Cikin satin ya shirya musu tafiya Nigeria,dashi da mashkur da wasu Yan ball d'in Yan Nigeria suna sauka kuwa aka yanyamesu, daqyar yasamu suka qaraso gida, a gidan Ummah suka sauka, Ummah Sai Nan Nan take dasu kamar zata maida su ciki, Dafarko Babban Yaya kunya yakeji, daga baya Kuma yasake kamar kowa, Waheeda koda yaushe tana tareda yanbiyu, duk abinda takeso na kwadayi sune suke samo mata, bangare daya Kuma Ihsan tana shan soyaiya itada mashkur, intisar Kuma da Safwan yayan Maya Kullum Sai Maya tazo gidan wajan Waheeda, wataran ayi fada wataran arabu lafiya πŸ˜‚ Amma hakan baya hanata dawowa gobe, ko bata dawo ba Sai Waheeda ta kirata, haka zatazo ta zauna suna hira ayita musu kamar wasu Yara Babban Yaya yana wajan harkar Ball dinsu, acan yake wuni tareda su mashkur, da daddare kuwa ya lalla6a wajan matarsa su raba dare suna shan soyaiya, kullum Sai yayi, ko gajiya ba yayi, Waheeda har mamakin sa takeyi yanda yake rawar qafa akan abin, kuka kuwa babu fashi saide idan yanayin kukan tarufe masa baki karsu Ummah su jisu, shi kuwa baisan ma yana yi ba, abinda yasani shine matarsa tunda tasamu ciki taqara dadi, yariga yasan cewa Waheeda itace komai nasa a yanzu, tariga tagama mallakeshi Sun dade a Nigeria, ko hanyar gidansu basu nema ba, suna Nan a gidan Ummah, su Babban Yaya kuwa Bayan wani lokaci Kuwait suka wuce, inda acan ne Bana za'a buga gasar qwallon qafar tasu Saida aka gama qarqare wasa sannan suka dawo gida cikeda dumbin nasara, a ranar bai dawo gida dawuri ba saboda Kai tsaye Dama fadar shugaban qasa suka wuce, saida aka gama karramasu sannan kowa yatafi Gida A ranar Waheeda saida ta raina kanta, tun suna abu na marmari har tazo tana kuka tana bashi haquri, saida yayi sau uku ajere, sannan yarabu da'ita Washe gari shirya wa tayi suka tafi Asbiti, da'ita dashi dasu yanbiyu, harda su Sa'ad da Sa'eed, tallafin kudi sukaje suka Kai asbitoci, suna rabawa kowanne majinyaci Ba asbitin gwamnati kadai ba, harma da wasu daga cikin private hospital Suna zuwa wani private Hospital a lokacin har magrib tayi, suna sauri zasu koma gida sukaga Ana fada aharabar hospital din, wata mata da Miji ne sunata fada Sai rabasu ake Mijin yana cewa "kin cuceni, Allah ya'isa tsakanina dake Zuby, lafiya ta kalau na aureki, ashe yaudarata kikai kika Sakamin cutar qanjamau, bazan taba yafe miki ba kije nasake ki....." Waheeda ta dora hannunta akan bakinta cikin tsananin mamaki tace "Huzaifa!!!" Ihsan ta zumbura baki tace "Allah yaqara" Babban Yaya baice komai ba, yaja hannun Waheeda suka shige mota, huzaifa ya biyo su da gudu yana fadin "Waheeda ki yafemin" Hannu kawai ta daga masa, bata iya cewa komai ba, Dan taga gogan Nata akusa yake, ya daure fuska sosai babu alamar dariya, ya dawo mata Babban Yaya sak! 😎 Tanajin yanda su Sa'eed da Ihsan suke ta maganar huzaifa, itade bata tankaba, Amma har sukaje gida tana mamakin rayuwa, haqiqa Maya tamata gata data nuna mata mutumin dayake qaunarka tsakani da Allah, tabbas Maya Tawuce qawa awajanta, saide Yar'uwa Harsuka koma gida Rasa gane kan Babban Yaya tayi, Sai wani shan qamshi yake, a dakinsa ma sun futo daga wanka taga Sai wani abu yake yana dauke Kai, kamar bayason magana yace mata "kishirya kayan ki gobe zamu koma" Cikin sauri tace "gobe gobe Babban Yaya? Tafiya babu shiri? Mubari mana ko zuwa next week ne" Cikin daure fuska yajuyo ya kalleta yace "idan kin zauna a gidan me zakiyi? Ok nagane, kinfiso nabarki agida kina kallon wasu mahauka ta kina bude murya kina Kiran sunan su, miye hadinki dashi, kawai daga ganinsa Zaki wani kira sunan sa, to dake yake fadan ma kome? Shida matarsa ne, miye naki na magana? " Dariya ce ta kamata, Amma saita danne taqi yi, inda itace take kishin sa haka zai zauna yasa ta agaba yana mata murmushi, Amma shi kalla yanda ya sauya lokaci daya Ahankali tatashi ta qarasa wajan sa, ta rungume shi tabaya, tadora hannunta akan nipples dinsa tana shafawa tace "shine dalilin fishin?" Cikin 6acin rai yace "shine" Towel din jikinta tacire yafadi qasa, tafara goga masa boobs dinta ajikinsa, ta dora hannunta akan mararsa tace "to kayi hakuri nadena kaji Baby na? Bazan sake ba, kayi hakuri kaji?" Ajiyar zuciya yasauke yace "shikkenan" Cikin shagwa6a tace "to kayi murmushi mana" Yabude baki zai sake mata wani korafin Tayi sauri tadawo gabansa tasaka masa nononta a bakinsa, Sai yayi dif kamar bashiba, yakama yafara Sha, Dan dolensa haka ya haqura, awannan Daren sun Raya Sunnah yanda yakamata, ita kanta bataso ya daina ba, taji dadin abun sosai Kwanan su uku, suna shirin tafiya,daga baya sukai sallama da kowa, suka tafi, Bai Barta ta zauna haka ba a England, Addmissoin ya nema mata tafara karatu, inda Allah ya temaketa laulayin cikin Nata yazo mata da Dan sauqi, haka tafara karatu cikin kwanciyar Hankali, suna kula da Cikinta yanda ya kamata Amnah El Yaqoub ✍πŸ? 1/28/22, 20:53 - Ummi TandamaπŸ˜‡: MH Da shawarar Hajiya Anty tayi amfani, Kuma taga amfanin ta, domin kuwa Hankalinta yana kwance, duk abinda take buqata yanayi mata, Kuma mata da maza basu daina nemansa ba haka take danne wa, daga qarshe ma itace take daukan wayar ta fadamusu bayanan idan yabar wayar agida, wasu daga cikin fans dinsa idan ta daga wayar haka zasu dinga girmama ta, abinda tasani shine koda niyyar soyaiya suka kira mijinta kokuma da niyar zumunci itakam tariqe mijinta yanda ya kamata, duk wani haqqin sa tana kokarin bashi Watan cikinta shida Amma daqyar take wasu abubuwan, tabashi shawara su yanbiyu sutaho kodan su dinga rage mata wasu ayyukan, Amma qememe ya nuna bayaso saboda zasu takura masa idan sunzo, bazasu barshi yayi kukansa cikin dare yanda yakeso ba πŸ™ˆ Saide shine yake Hana Kansa wani aikin, ya zauna a gidan suyi komai tare, bikinsu Didat Sai qara matsowa yake,dama can shekara daya aka saka, yanzu Kuma saura wata biyu, Waheeda Kuma saura wata daya tagama second semester dinta,a lokacin Shima Babban Yaya wani club dinne suke shirin siyarsa, tana gama exam kuwa, suka dawo Nigeria, Anty tayi mamakin girman cikin Waheeda, wata bakwai Amma yarinya idan zata tashi saita runtse idonta Idan ta zauna kuwa wuni take a zaune, babu kunya Babban Yaya zaizo yasa ta agaba su zauna, duk abinda take buqata kawai fada masa zatayi, haka zai kama hannunta su dinga zagaya gidan suna tafe suna zancen su na masoya Ranar biki kuka kawai take, yanda taga yanbiyu sunyi shiga Mai kyau Kaya yayi musu cif cif ita kuwa Qin shigarta yayi, dole Sai Hajiya Anty ce tasa akayi mata sabon dinki a ranar, akayi mata doguwar Riga bubu, akasa Mai kwalliya itama tayi mata, duk wani party da aka shirya dasu walima Babban Yaya yana tare da ita, idan yaga tagaji Nan da Nan zai kawo hannu ya d'auketa, ko kadan bayason abinda zai taba lafiyar cikin Nan Anyi biki lafiya, ankai amare gidajan mazajensu Wanda Babban Yaya ya gwangwaje su dashi, gida iri daya Kuma kusa da juna Dayake yanbiyu ne matan nasu Nan da Nan Sai kansu yahadu da su yanbiyu, ko ranar bikin haka photonsu ya dinga yawo a yahar gizo, yanbiyu sun auri yanbiyu, ga Kuma wasu Yan biyun qannan mazajen Cikinta yana wata takwas, akasa bikin Maya wata daya Mai zuwa,Waheeda tayi farinciki tasan zuwa lokacin ta haihu Maya tana zuwa gyaran jiki Amma koda yaushe tana tareda Waheeda, idan suka zauna wani lokacin sai tayi tagumi tana kallon qawar Tata, kowa yaganta saita bashi tausayi, Shima Babban Yaya duk nacinsa saida ya haqura ya daga mata qafa, saide tayi masa wasu Yan dabaru harya gamsu Bikin Maya yarage sati daya, idon Waheeda yaraina Fata, haihuwa shiru shiru batazo ba, Hajiya Anty ta duba taga babu komai, Babyn ta yana cikin qoshin lafiya, haka Maya zatazo gidan sutafi tare dasu yanbiyu, duk wani abu sune kan gaba, wani zaiyi tunanin ma Yan gidansu Mayan ne, Amma duk Wanda yaji cewa yayun Waheeda ne, to saiya daina mamaki saboda kowa yasan tsakanin Maya da Waheeda akwai qaunaπŸ˜‚ Ranar Daurin aure tun safe Waheeda ta shirya, tayi kyau sosai cikin leshi hand bag dinta tana gefenta, tayafa mayafi Dan qarami taci magani tana jiran Babban Yaya, Dan tasan inde yaganta da mayafi zasuyi tashin Hankali Futowa yayi cikin shiri yayi kyau sosai cikin shadda kalar leshin jikinta, kallon ta yayi yace "kije ki shirya mana,tun safe kin tasheni, Kuma Naga baki shirya ba" Kallonsa tayi tace "aina shirya" "kije kinemi hijab, tayaya zakije da wannan mayafin, wallahi saide mufasa zuwa" Kallansa tayi duk ranta adagule, dama jitake kamar ta Fashe da Kuka, bikin maya guda, Amma babu ita Tace "Naga har kofar gida zaka kaini amota Kuma......" kafin ta qarasa magana taji mararta ta daure, ga bayanta da yayi wani irin amsawa, lokaci daya ta dora hannunta a mararta, ta runtse idonta tasaki wani irin ihu Cikin sauri Ummah tafuto aguje, Babban Yaya yarikice yarasa Yaya zaiyi mata, Ummah tana qaraso wa tace masa dauketa muje naquda ce,daukan ta yayi cikin tashin Hankali yanufi mota da'ita, Ummah takira Hajiya Anty tasanar da'ita, duk suka hadu a Asbitin Tun misalin shadaya sukazo, Amma har qarfe hudu Waheeda bata sauka ba, suna haka aka kawo wata yarinya itama haihuwar ce,Ana shiga da'ita Dakin haihuwa Wanda suka kawo ta suka qaraso wajan su Ummah suka zauna, mamaki ne ya kamashi ganinsu Ummah da Hajiya Anty , cikin mamaki yace "Anty ashe kune?" Babban Yaya yanajinsa bai d'ago ya Kalle shi ba, tunanin Waheeda kawai yake, ko awanne Hali take ciki? Anty tace "Didat? Ashe kaine, wallahi bamu lura ba" Babban Yaya yana jin ance Didat yadago Kansa, Hajiya kakar Didat kunya ta kamata, daqyar ta'iya gaisawa dasu Ummah Didat yace "wallahi nakawo matatane haihuwa, waye babu lafiya Ummah?" Ummah tace "Waheeda ce, itama haihuwar ce" Yayi shiru jikinsa yayi Sanyi, ahankali yace "Allah yasauke su lafiya" Ko awa daya basu qaraba, matar Didat ta haihu, Allah ya Albarka ceshi da samun ya mace, doctor tana bashi Babyn yakawo wa su Ummah ita yace "Ummah ga Waheeda, kusa mata Albarka" Ummah ta jijjiga Kai tana mamakin Didat, soyaiya kenan, addu'ah sukayi wa yarinyar, sannan ya karbeta yabawa Babban Yaya ita yace "ga takwarar Waheeda, kayi mata addu'ah" Babban Yaya ya karbi Babyn yana kallon ta, yasaka bakinsa a kunnan yarinyar yana mata addu'ah, doctor's suka futo hannun su d'aukeda Baby's suka Bawa su Hajiya Anty tareda fadin "tasauka lafiya, ansamu yanbiyu mace da namiji" Cikin farinciki Babban Yaya yace "doctor zan'iya ganinta?" "why not, bismillah" Fadawa yayi cikin Dakin datake, yana zuwa yakama hannunta yariqe, Hawayen farinciki suka zubo daga Idonsa, ahankali ya ajiye baby Waheeda agefenta, sannan ya rungume ta yafashe da Kuka, kukansa ne yatashe ta, tana bude idonta ta ganshi, sumar Kansa ta shafa ahankali tace "Babban Yaya nakusa mutuwa" Cikin sauri ya kalleta yace "bazaki mutu kibarni ba Waheeda, tare zamu mutu kinji? Sannu, Allah yayi miki Albarka, me kike so a duniyar Nan Waheeda?" Murmushi tayi tace "kainake so" "kinga ma samu na, babu wata Bayan ke" Babyn ta kalla tace "Mena Haifa Babban Yaya?" Babyn ya miqa mata yace "ga yarki Nan, itace babbar yarki, sunanta Waheeda Didat" Cikin mamaki tace "Waheeda Kuma?" "yes, Matar Didat ta haihu, yayi miki takwara, itace wannan, yaranmu suna wajan su Ummah, kin Haifa min mace da namiji masu kama dake" Rungume yarinyar tayi tace "Allah yaraya mana su gaba daya" Anty da Ummah dasuka shigo Dakin yanzu, suka hada baki sukace "Amin ya Allah" Cikin sauri Babban Yaya ya saketa, suka ajiye mata yaran a gabanta Kunya taji, taqi Kallan yaran, Yara har biyu duk Nata ne wai A lokacin Hajiya Anty takira Daddy da Uncle tasanar dasu, dakuma mama Haajara matar baba Habu, yanbiyu ne suketa Kiran wayar Babban Yaya, dauka yayi tareda sallama Ihsan tace "Babban Yaya Ana shirin tafiya da amarya fa saboda unguwar da Nisa, Kuma Maya taqi shirya wa tace Sai Waheeda tazo" Murmushi yayi yace "bata wayar" Wayar ta miqawa Maya, Babban Yaya yace "Maya qawar Taki ce naquda tatashi, gatanan kun samu yanbiyu" Cikin murna Maya tasaka ihu tana fadin "Dan Allah bata wayar Babban Yaya" Waheeda yabawa wayar, ahankali tayi magana tace "Maya" Wani irin hawaye yazubo daga idonta Itama anata bangaren kuka tasa tace "sannu Waheeda, Allah yayi babu ke za'a kaini, Allah yaraya mana su, insha Allah zanzo" Hawayen ta share takasa magana, Hajiya Anty ta qwace wayar tace "Maya yakuke kuka ne keda qawar Taki, ai murna yakamata kuyi tunda Allah ya sauketa lafiya, kiyi hakuri muma anjima zamu shigo insha Allah" Hajiyan Didat ce tashigo Dakin tareda Didat, Waheeda ta Kalle shi tace "Didat nagode, Allah yabar zumunci, ubangiji Allah yaraya Waheeda...." Yace "Amin" sannan suka dauki Babyn suka fita, Sai dare aka sallami Waheeda da sharadin Hajiya Anty zataci gaba da Kula da'ita agida Yanbiyu basu dawo gida ba saida suka Kai Maya, Sai wajan karfe goma driver yakawo su gida, aikuwa aguje suka shigo falon, a Dakin Ummah Waheeda take, Dan haka Nan suka hadu suka kwana gaba dayansu. Waheeda taga soyaiya tsantsa daga family dinta, a kwana shidan da tayi kafin suna ko kadan bata daukan yaran saide in nono zata basu, yanda yanbiyu suke dawainiya dasu saika rantse sune suka haifesu Ranar suna Yara sukaci sunan Ummah da Uncle Usman, Babban Yaya yahada mata kayan fitar suna a kwatuna biyar tareda dalleliyar mota qirar Benz, Sai kuma na baby's kowa a kwatuna uku uku manya, tareda kyautar filaye. baba Habu yazo shida tawagarsa, saida sukai kwana biyu sannan suka koma gida Bayan suna da sati biyu, yashigo gidan, kewar matarsa yakeji, Kuma kullum tana Dakin Ummah, Kuma yanzu nauyin Ummah yakeji kawai yashigo kai tsaye tana zaune afalo yashige Dakin, yana ganin babu kowa a falon Sai yanbiyu suna ta cacar baki akan wani film hamdala yayi cikin ransa, cikin sauri yashige Dakin Ummah tareda rufewa, ko lura da Wanda suke Dakin baiyi ba, yana Juyowa yaga Ummah da Waheeda a zaune, Ummah tana cirewa yaran Kaya zata musu wanka, ga ruwan wankan nasu Nan agefe Wata irin kunya ce takama shi, yayi sauri ya sunkuyar da Kansa, Ummah tatashi tsaye ta ranqwashe shi akansa tace "nide ba surukar ka bace, Gara ma kadena wannan kunyar" Tafice daga d'akin tareda janyo musu qofa, Naufal ya kalli Waheeda yace "wallahi jinake babu kowa saike, ashe tana ciki" Waheeda tayi dariya tace "wanka zata musu, tare muke da'ita tun dazu" Breast dinta ya kalla ya hadiye wani yawu yace "Sai qiba kike kullum, ko'ina yana qara cika, ni kin barni da kewarki" Tace "ai Anty ce tace nadena futowa ko falo ne, inyi zamana adaki cikin dumi" "ai gashinan na biyo ki, yanzu kinsan ni Dan gata ne tunda Ummah ta dakanta tajamin kofa inyi abinda raina yakeso" Harararsa tayi tace "kayi me? Nadena haihuwa nikam" Murmushi yayi yad'auki Me sunan Ummah yace "Ummah na Zona miki wanka kinji.." Waheeda tace "ka'iya ne?" "wallahi ban iyaba, saide kizo muyi musu tare" Tasowa tayi tana cewa "Nima ban iyaba, karmu basu ruwa fa" πŸ˜‚ Dariya yayi yace "ke bawani ruwa, tsaya kigani" Babyn suka saka a ruwan, Waheeda ta riqeta, shikuma yafara mata wankan, yana wanke mata Kai yarinya tafara miqewa tana tsandara kuka, cikin sauri yaqara zuba mata wani ruwan, Waheeda kuwa ta dage ta rirriqe yarinya kamar Wanda tariqe wata Babba πŸ˜‚ Ummah ce tashigo Dakin, cikin tashin Hankali tace "nashiga uku yarinyar zaku kashe?" Duk sukai shiru suka kasa bata amsa, Waheeda tace "Ummah shine yace zaiyi mata wankan, wallahi babu ruwana " Ummah tace "lalle, bakiji azabar naquda bane, kubani su ni, sakarkaru kawai"πŸ˜‚ Babban Yaya yamiqa mata yarinyar Sai kuka take, yasake miqa mata namijin, Tafice daga d'akin, Waheeda ta kinkimi ruwan wankan nasu takai mata, sannan tadawo Dakin Kallan gaban rigarta yayi yaga yadan jiqe kadan, yace "Zonan, menene yabata miki Riga?" Kalla tayi tace "ruwan nono ne, tun dazu bacci suke basu Shaba" Wata irin kasala yaji, cikin sarqewar murya yace "zomu Gani" Babu musu ta qarasa wajan sa, yajanye rigar tayi sama, ahankali yad'ora bakinsa akan nonon ta yafara tsotsa ahankali, cikin jin dadi tace "ahhh..." Yadade yanasha, Kuma bata hanashi ba, saboda dadi takeji, idan yaran ne suke Sha Kuma zafi take ji saboda da qarfi suke zuqowa Maganar Ummah suka Juyo abakin kofa tana cewa, "Waheed ga yaran Nan angama wankan basu nono susha " Cikin sauri yasake ta, yafada kan gadon da baya yana maida numfashi cikin kasala Waheeda tatashi taje ta karbo su, tadawo ta ajiye masa macen ajikinsa, tadora namijin a cinyarta zata fara bashi nonon Yarinyar ya ajiye yatashi zaune yace"waime kikeyi ne haka? " Tace "nono zan basu" "befa isheni ba, gaskiya kibasu madara, baga madarar su Nan nasiyo ba, menene amfanin ta?" Mamaki yakama Waheeda, ta tsaya tana kallonsa takasa yimasa magana, kuka yaran suka fara, yad'auki fidarsu datake cikeda madara yafara basu, shikuma yaja Waheeda jikinsa yaci gaba da shan nonon , Waheeda ta Kalle shi cikin mutuwar jiki tace"Babban Yaya kabarni nabasu abinsu Dan Allah, karka shanye basu shaba " Lumshe Idonsa yayi yace"Waheeda.... Ko a aljanna Allah yabarni tare dake, inason ki sosai" Dadi taji ya kamata, batasan lokacin data sake rungume Shiba, shi kuwa yaci gaba da shan nonon ahankali,jitayi yana neman tura hannun sa cikin pant dinta, cikin sauri tacire Mai hannun, ta d'ago Kansa daga qirjinta tace"Babban Yaya kabari, kar Ummah tashigo, kofar abude take " Kansa ya shafa yace"wallahi na manta, idan Ina tare dake manta komai nake Waheeda, kece kika sa nazama haka wallahi, Allah yayi muku Albarka keda yaranmu, bakina cewa kina sona ba saura Kuma idan na mutu ki auri wani, wallahi koda ace kin auri wani Bayan babu raina, to ban yarda kijiyar dashi irin dadin dakika Bani ba, kinji de nafada miki" Waheeda tasaka dariya, ta rungume shi,tace" Ina kaunarka mijina, Bana fatan abinda zai rabani dakai ma balle mutuwa, Ina fatan ace yaranmu suyi irin halinka, kakula damu yanda ya kamata Babban Yaya, musanman ni, banda bakin dazan gode Maka, saide inyi fatan inci gaba da kasan cewa dakai har qarshan rayuwa ta " Dariya yasaka, dimples dinsa suka futo, tasaka hannunta a wajan, batare daya janye hannunta ba yace"idan sukai irin halinki aina mutu"🀣 Kukan shagwa6a tasaka masa, cikin lallashi yace"toyi hakuri gimbiya ta, nadena fadar hakan, shikkenan? " Daga masa kanta tayi, Bai sake ce mata komai ba, yahade bakinsu waje daya, kissing dinta yake sosai cikin wani irin Salo, ita kanta abun yamata dadi, ahankali tafara maida masa da Martani, Nan da Nan ya susuce mata,yaja hannunta yad'ora akan marar sa, wani irin numfashi yasaki lokacin da yaji abinda take masa, yaran ne suka fara kuka, cikin sauri yasaka musu fida, sukaci gaba da abinda suke πŸ™Š TAMMAT BI HAMDULLAH ********************** ? ************************** ********** Ai Hausa Novels **************** *************************? ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ? ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ? ************************** Idan akwai Wanda na batawa sanadin wannan littafin yayi hakuri ya yayafe min, Dan Adam ajizi ne, nide nasan adan Zaman danayi daku ban shiga haqqin ku ba, Ina fatan Allah yasadamu da alkhairinsa Saikun jini a sabon Novel Dina SHAHAB..... Labarin SHAHAB gaba dayansa sadaukar wane ga masu suna AISHA, sannan labarin daban yake da sauran labaran Dana rubuta abaya, labari ne me tsayawa azuci, nikaina Dana tsarashi ya birgeni fiyeda Babban Yaya, zaizo muku Bayan nagama semester exam dina insha Allah akan farashi naira Dari uku kacal 300 πŸ‘ŒπŸ»babu VIP, group daya zan bude, zaku dinga samun posting safe da dare, idan Dame buqatar sa Sai iya ajiye number ta zuwa lokacin dazan fara insha Allah 08033300034 Har kullum karku manta da Amnah El Yaqoub marubuciyar ku ta : DANA SANI BURINAH WAZAN ZABA SHALELAN BABA NI DAKE DANGI DAYA INSAAF BABBAN YAYA SHAHAB Amina muhammad El Yaqoub jigawa State a.k.a Amnah El Yaqoub ✍πŸ?