********************** ? ************************** ********** Ai Hausa Novels **************** *************************? ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ? ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ? ************************** *Bismillahirrahamanirraheem* *LAYLERH MALEEK* *Written By* Phatymasardauna *Dedicated To My Blood Brother, My Happiness, My Sweetheart, nd My Heartbeat (AUWAL) I love you so so much my big bro, wish you quick recovery darling👏🏻.*                *FOLLOW ME ON*                            *Wattpad*                       @fatymasardauna #Firstlove. *Friday 31/October/2020*       *(📿Happy Jumma'at Mubarak To All Muslims Ummah, May Allah Bless You And Your Family.🕋)* *CHAPTER ONE* *(SOYAYYA wata irin ƙaddarace, da take ɗaure akan wuyan kowa, sannan kuma wata abace da ba'a iya ganin launinta da ido, hakanne ma yasa  ba'a iya sauyata, saidai idan taso takan tashi daga sunanta na SO ta koma ƘIYAYYA. Acikin  kowani rayuwar ɗan Adam akwai salon ƙaddarori masu tarin yawa, akowacce duniya akuma koda yaushe ƙaddara tana tafiya ne daidai da  rayuwa, haka kuma tana rayuwa da mu cikin  farinciki ko akasin haka, abu ɗayane yake tafiya acikin zuƙatanmu, shine MURADI, FATA, da kuma son samun ABUNDA ZUCIYA KESO. Sannan  kuma babu wani bawa wanda ke iya gujewa ƙaddaransa, Lallai ƙaddararmu tana gudana ajikinmu kamar jini, akowace rana abubuwa mabanbanta suna faruwa, to haka itama ƙaddara takan iya sauyawa ako da yaushe, wannan rayuwar daban take da saura, komai yana cikin zuciya da tunanin LAYLERH MALEEK.)*   ***       *** *** Cikin sauri take ƙoƙarin sanya uniform ɗin makarantar ta, sosai take sauri dan  tasan idan ta tsaya wasa zatayi latti, wanda zuwa yanzu  batasan da wani baki zata fara faɗan  excuse ɗinta ba, ga masu gadin makarantar, domin tasan zuwa yanzu suma sungaji da karɓan excuse ɗinta. Ɗan madaidaicin sket ɗin makarantar nata tasanya, wanda yake da ɗan tattara ajikinsa,  wanda idan kasanya sa, zaka jawosa har saman cikinka, dan iyan high waist ɗinnan ne, bayan ta saka sket ɗinne. Cikin sauri sauri ta zura wata farar rigan long sleeve ajikinta, ahanzarce ta tura rigar acikin sket ɗin, take ta zuge zip ɗin sket ɗin,  hakan da tayi ne kuma yasa ba'a ganin ƙasan rigar makarantar nata. Sauri sauri ta maƙala aninayen dake jere agaban rigar,  farin safa ta sanya aƙafafunta, tare da ɗaukan  wani toms ɗinta me kalan baƙi ta sanya. Dayake sket ɗin makarantar tata da kaɗan ya wuce guiwanta, hakan yasa safan da tasa aƙafanta yaɗan taimaka wajen suturta fatar ƙafanta. Kyawawan fararen idanunta  ta ɗago, tare da  sauƙesu  akan agogon bangon dake saƙale jikin bangon ɗakin.   8:15 am daidai ta gani, jitayi ƙirjinta yayi wani irin bugu, take taji zuciyarta ta karye, shikenan yau ma ta sakeyin latti kamar sauran ranakun,  by 8:00 am daidai ake kulle gate ɗin makarantar tasu,  da zaran an kulle kuwa babu me shiga, idan kazo late saidai ka koma gida,  duk da tasan cewar tana samun alfarmar shiga makarantar daga wajen masu gadi koda an kulle, saidai yau bata tunanin cewa zasu dubeta ma bare har su karɓi roƙonta. Cikin azama ta zura  ɗan madaidaicin hijabin makarantar ajikinta, wanda duka tsayinsa baiwuce guiwan hannunta ba,  kallon kanta tayi amadubi, tare da kafe madubin da ido, kyakkyawar fuskarta take kallo ta cikin madubin, sannu ahankali idanunta suka ciko da hawaye, lumshe idanun nata tayi, wanda hakan ya bawa hawayen dake ciki daman gangarowa. Da sauri ta share hawayen, ta  ɗauki ƙatuwar hand bag dinta ta goya.  Text book ɗin ta da tayi assigment acikinsa jiya, wanda ta ɗaurasa bisa kan mirror ta ɗauka,  da sauri tafice daga cikin ɗakin. Koda ta bude ƙofar ɗakin nata ta fito, nan cikin babban falon gidan, da kai tsaye za'a ƙirasa da aljannar duniya ta samu kanta, falo ne tankameme wanda tsarinsa da haɗuwarsa ya zarce misali, kallo ɗaya zakayiwa falon ka tabbatar da cewar mamallakansa ba ƙananan masu arziki bane,  saboda wasu irin haɗaɗɗun royal cushions masu uban kyau da tsada da aka ƙawata cikin falon dasu, adon jikin royal cushions ɗin ma kaɗai abun kallo ne,    tsakiyan falon kuwa wani irin haɗaɗɗen lallausan turkish carpet ne a malale, wanda kana takawa Ć´an yatsun ƙafanka na lumewa aciki, tsabar laushi, ta cikin falon acan gefe kuwa wani irin ƙawataccen dinning area ne me azabar kyau da tsaruwa, an kewaye gaba ɗaya wajen da haɗaɗɗen decoration me kyau, wasu irin haɗaɗɗun labule kewaye da kowani ƙofa da window dake cikin falon, ga kuma wasu irin flowers masu kyau da aka saka akowani kusurwan falon, wanda sai shinning suke suna ɗaukar ido, still daga cikin falon kuwa wani irin tangamemen tv plasma ne keta aikin ɓaɓatu shi kaɗai,  bayan plasman dake magana shi kaɗai babu wani halitta acikin falon, sai  sanyin A/C dake ta busawa. Kan dinning area' n ta kalla, wayam haka taga saman table ɗin  babu ko cokali, bare kuma  food flask, da dukkan alama dai yau ɗinma ba'a rage mata break fast agidan ba. Cikin rashin ƙarfin jiki ta murɗa handle din ƙofar falon ta fita zuwa babban compound ɗin gidan, wanda yayi matuƙar haɗuwa, kanta tsaye  ta nufi  hanyar babban gate ɗin gidan,  sunkuyar da kanta ƙasa tayi, tare da   sanya hannunta duka biyu ta riƙe jakar makarantar dake goye a bayanta. Ɗahiru me gadi dake tsaye abakin gate ɗin gidan, ganinta yasashi ɗan sakin murmushi cikin kulawa yace.     " *LAYLERH* Ć´an mata sarkin makara yau madai amakare za'aje makarantar kenan." Idanunta ta ɗan lumshe tare da jinjina masa kai alaman "Eh."   Murmushi ya kumayi tare da cewa.   "To Adawo lafiya Allah ya bada sa'a."   Cikin zazzaƙa kuma tattausan muryarta tace.   "Ameen Malam Ɗahiru nagode."       Buɗe Ć´ar ƙaramar ƙofar dake jikin gate din tayi ta fita. Malam Ɗahiru kuwa binta yayi da kallo yana girgiza kai, cike da matsanancin tausayinta, dan yasan babu makawa yanzu haka ko karyawa batayi ba, kuma haka zata tafi makarantar,   ga kuma motocin da suke ajiye agidan basa aikin komai sunkai guda 7, amma daga cikinsu babu wanda ake bawa umarni ko izinin kai Laylerh'n makaranta, kullum saidai ta fita bakin titi tahau taxi , ranan da bata da kuɗi kuwa saidai ta taka akan sawayenta, wannan dalili yana daga cikin abunda yasa yake matuƙar tausayin yarinyar. Cikin yanayi naɗan ɗaga ƙafa take tafiya, akan shumfufaɗaɗɗiyar hanyar da ta kewaye unguwar tasu, wanda kowani ƙofar gida akwai titi shumfuɗe agabansa, haka ƙa'idar unguwan tasu take, kasancewarta unguwar masu kuɗi shiyasa, saikayi tafiya me nisa aƙafa baka haɗu da wani ko wata ba, kowa na cikin gidansa akulle, idan ma zaka ga mutane tofa saidai acikin tsala tsalan motocinsu suna wucewa, musamman ma a irin wannan lokacin babu Ragowan ababen hawa akan titin unguwartasu, domin masu tafiya office da makaranta duk sun tafi. Tafiya take sosai, sai cira ƙafa take burinta baiwuce taganta abbaban gate ɗin da zai fitar da ita daga unguwar tasu ba, dan ananne kaɗai zata iya samun abun hawa. Sauri take sosai, duk da kasancewar ma babu wani abu na kirki da tasa acikinta tunjiya da dare, gashi yanzuma bata samu arzikin yin break fast ba ta fito. Saurin da takeyine yasa bata wani ɓata lokaci ba, ta iso ƙofar gate ɗin, me gadin gate ɗinne ya bita da kallo dan idan da sabo ya saba da ganinta kusan kullum, matuƙar akwai makaranta to fa sai yaga wucewanta. Ɗaga masa gaisuwa tayi sannan tabude ƙofar gate ɗin ta fice. Samun kanta tayi akan wata sabuwar titi, wanda take akwai ragowan ababen hawa akanta, saidai kuma duk ba motocin haya bane ke kai da kawowa awajen. Ahankali taɗan bubbuga ƙafafunta tare da ciza laɓɓanta, cikin wata irin murya me sanyi tace.      "Ya Allah Ka taimakeni katuromin abun hawa, yauma na makara, bansan yazanyi ba, nayi missing  lectures, gashi by 9:00 muna da test."    Yanayin yanda ta ƙare maganan tana ɗan rawar da idanunta ne yasa Ć´an guntun ƙwallan da suka maƙale acikin idanunta suka samu daman gangarowa. Daidai lokacin kuwa wata motar taxi tazo wucewa, da sauri ta sanya hannu tana taran taxi ɗin, cikin sa'a kuwa ya tsaya. Tana faɗa masa inda zai kaita, batare da tajira me zaice ba ta buɗe motar ta shiga, yayinda me taxi ɗin yaja motar sukayi gaba. Jakan dake goye abayanta ta ɗaura akan cinyarta, zage zip ɗin jakan nata tayi, ahankali ta sanya hannu acikin aljihun jakan ta zaro 1k wanda shine iya kuɗin da ya rage mata,  bayan shi kuwa bata da ko sisi. Ɗan jingina bayanta tayi da jikin kujeran motar, ahankali ta sauƙe ajiyar zuciya me nauyi, tabbas idan naira dubu ɗayan nan ta ƙare batasan ya zatayi ba, dole ne ta fara takawa da ƙafa. Ahankali taɗan lumshe kyawawan idanunta. Tunani ne kwance acikin zuciyarta har suka iso bakin katafaren school ɗin nasu batare da ta sani ba. Jin taxi ɗin ya tsaya ne yasa ta buɗe idanunta, ganin sun iso bakin gate ɗin makarantar ne yasata fitowa daga cikin taxi ɗin bayan ta miƙa wa me taxi ɗin, 1k ya bata canji. Ganin gate ɗin makarantar tasu a rufe ne yasa taji gabanta yaɗan faɗi, dan tabbas tasan cewa tayi latti. Ahankali ta ƙarasa jikin gate ɗin tare da ɗan  ƙwanƙwasawa. Ɗaya daga cikin securities ɗin dake gadin gate ɗinne ya buɗe Ć´ar ƙaramar ƙofar dake jikin gate ɗin,   ganinta ya sashi zuba mata ido, tare da ɗaure fuskarsa, duk da cewa shi sabo ne awajen amma  tabbas ya shaida fuskarta saboda tana yawan zuwa late, cikin gurɓatacciyar hausan sa da bai gama iyawa ba yace.  "Yarinya ki koma gida dan kinyi latti, kin san kuma bazan barki ki shiga ba, saboda yin hakan saɓawa aiki na ne."  Idanunta da suka ɗan ciko da ƙwalla ta ɗago ta kalleshi, cikin sassanyar murya tace. "Dan Allah kada ka hanani shiga, wallahi ban samu bus da wuri bane, please insha Allah zanna kiyayewa."    Kai ya girgiza  mata, tare da maida ƙofan ya soma ƙoƙarin rufewa, dan yasan idan har ya barta tashigo, muddin aka ganta akwai matsala, dan dokane na makarantar duk ɗalibin da baizoba har aka rufe gate to fa ko yazo saidai ya koma gida, idan kuwa aka kama ɗaya daga cikin  masu gadi da laifin buɗewa wani ɗalibi ko ɗaliba ƙofa to zai karɓi punishment me ƙarfi. Saurin riƙe ƙofar tayi cikin yanayin roƙo tace.   "Dan Allah Kamin alfarma koda sauɗaya ne, na yau kawai kabarni na shiga, 9 daidai muna da test kuma idan banyi ba zai iya kawomin nakasu please." Kallon yanda idanunta suka ciko da ƙwalla gate man ɗin yayi,  hakanan yaji wani abu adangane da ita,  duk da cewa shi ba musulmi bane, amma yakanji wani irin nauyi aransa idan aka haɗasa da ALLAH. Ɗan jinjina kansa yayi, cikin gurɓatacciyar hausan sa yace.  "Zan barki ki wuce, amma ki kula kada wasu su ga shigowarki, saboda idan aka kamaki nima hakan zai shafeni."   Dasauri ta jinjina kanta, cikin jin daɗi tace. "Nagode sosai."  da sauri ta shige cikin makarantar, shi kuma ya maida ƙofar ya rufe. Cikin hanzari take tafiya, har kafafunta suna harɗewa, tsoro ne fal zuciyarta, addu'a take tayi Allah Yasa kada aganta. Cikin ikon Allah kuwa har ta kawo bakin class ɗinsu bata taradda malami ko ɗaya awaje ba, duka suna cikin aji suna gudanar da lectures, haka ma securities ɗin da suke kula da makarantar basu taho ta wajen da take ba. Ɗan leƙa ajin nasu tayi ta window, gabanta ne ya faɗi ganin tuni Maths teacher ɗin da zaiyi musu text ya shiga, har ya fara rubuta musu questions akan  board. Jikinta ne ya soma rawa, dan sarai tasan  Teacher David baida mutunci ko kaɗan, yanzu sai yace bazata shiga ba. Ɗan danne siraran laɓɓanta masu kalan pink tayi, ahankali ta ƙaraso bakin ƙofar ajin nasu ta tsaya. Ƙarasowanta kuwa yayi daidai da ɗago da kansa, yakai duba zuwa bakin ƙofar. Ganinta ya sashi ƙanƙance ƙananan idanunsa, cikin halin baƙin hali yace. "you, from where?". Yatsun hannunta ta soma ɗan murzawa, samun kanta tayi da kasa cewa komai, dan tasan sa kamar maye yake, daka masa ƙarya zai gane. Kallonta yayi naɗan wasu daƙiƙu, wani yawu ya haɗiya tare da cewa.  "Oya come in."   Jin haka yasa taji wani sanyi aranta, ƙarasowa cikin class ɗin tayi, hakan yasa idanun gaba ɗaya Ć´an ajin ya dawo kanta, ɗan satan kallonta Teacher David yayi, can ƙasan maƙoshi yace.   "Oya Go and sit down."  ai kuwa kamar jira take da sauri, ta nufi wani benci wanda bakowa akansa ta zauna. Da sauri ta buɗe jakanta ta ciro paper da abun rubutu, sunanta ta rubuta ajikin papern sannan ta zubawa white board ɗin nasu ido, cikin ranta take karanta questions ɗin dake rubuce akan allon. Daga  bayanta yaji anja hijab ɗinta ta ƙasa ,ƙin juyawa tayi dan tasan Teemah ce kaɗai zata mata haka. Ɗan cije lips kyakkyawar matashiyar budurwan da ake ƙira da suna Teemah tayi, cike da takaicin rashin juyowan na LAYLERH,  ƙasa ƙasa tace. "Wallahi Laylerh ke Ć´ar air ce, kina sane da cewar ban iya maths ba, me makon ki zauna akusa dani shine zakije ki zauna awani sit daban ko hmmm." Ƙwafa tayi tare da hararan teacher david ƙasa ƙasa, cikin ranta tace.   "Banza tsohon maye, sai shegen son bada assigment da test, saikace an faɗa masa kowa ke gane darasin aljanu irin nasu, zaka gane wallahi kai da kunnuwan ƙwarangwal zan zana maka, sai injera maka sufuli aƙasansu."   Murmushi tayi tare da soma rubatawa takardan nata zero zero. Laylerh kam da gangan taƙi juyowa, dan tasan da ta juyo Teemah bazata barta ba, sai tayi duk yanda tayi teacher David ya ƙwace musu takardan su. Idanunta taɗan lumshe ahankali bayan tagama karanta questions ɗin, wani tunani ne yasoma shigowa ƙwaƙwalwarta, ahankali yanayinta ke sauyawa, zuciyarta ne ta fara bugawa da ƙarfi, yayinda numfashinta yasoma ƙoƙarin hautsunewa,  hannunta tasanya inda ta ƙanƙame jikinta, tare da sake rumtse idanunta,  gaba ɗaya jikinta ne ya ɗauki ɓari, wani irin zufa ne ya shiga keto mata. Sannu ahankali  hoton haɗaɗɗun cikin idanunsa masu masifar kyau suka soma yawo acikin idanunta, laɓɓan bakinta ne suka soma rawa. So take ta faɗi abun dake rai da kuma zuciyarta, kalma ɗaya tak, ita takeson furtawa ako da yaushe, amma har yanzu takasa samun dama. Tabbas tanason sa ni, tanason sanin wanene mamallakin wannan kyawawan idanun masu kyau da burgewa, meyasa yake shigowa cikin tunaninta akoda yaushe? batasan shi ba, batasan a ina zata ganshi ba, abu ɗaya kawai take iya fahimta amatsayinta na matashiyar budurwa, wanda ayanzune take ƙoƙarin mallakan hankalin kanta, wannan abu shine BUGUN ZUCIYA, tana da yaƙinin cewa lokuta da dama bada tunaninta take aiki ba, sannan kuma bugun zuciyarta na tafiya ne da abu guda. Farinciki, ko akasinsa, tsoro, ko fargaba, rauni da kuma tarin ƙaddara, tayaya zata iya ɗaukan hakan, bata fatan zuciyarta ta tarwatse akan wannan dalilin. (Kubiyoni, dan wannan labarin ba irin sauran bane, wannan daban yake da kowanne, kuyi comment da kuma votting  ɗina kamar yanda kuka saba, har ma fiye da haka, dan ta hakane kaɗai zan iya gane cewa lallai kuna enjoying labarina yanda ya kamata, sannan kuma karku manta ina alfahari daku akullum akuma koda yaushe, sannan ina neman Alfarma awajenku gaduk wani ko wata da ya karanta fejin nan, dan Allah kuyiwa YAYANA addu'a, akan  ALLAH yabasa lafiya😭. Then masoyana kuyi haƙuri da jinkirin dana samu na rashin kawo muku sabon labari da wuri, nagode sosai da nuna ƙaunarku agareni.🙏🏻)               *Vote* *and comment*                           *fatymasardauna* 1/19/21, 8:09 PM - Ummi Tandama: 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *LAYLERH MALEEK* *Writting by* Phatymasardauna *Wattpad* @fatymasardauna #Generalfiction *Chapter 2* Tunaninta ne ke neman juyewa, tamkar yanda taji duniyar na juya mata, idanunta ta kuma rumtsewa da ƙarfi, ƙoƙarin furta wani abu take amma takasa, saidai laɓɓanta dake motsawa ahankali, sannu ahankali bugun zuciya da fitan numfashinta suka soma daidaita, kyawawan idanun ne suka soma ƙauracewa ganinta, hakan yasa ta soma sakin ajiyar zuciya, idanunta ta buɗe asanyaye ta maida hankalinta ga takardan dake gabanta, duka questions ɗin da aka rubuta, babu wanda batasan answer'n saba, saboda tayi karatu sosai akan test ɗin, hakan ne yasa cikin mintuna ƙalilan ta gama amsa tambayoyin. Teemah dake ta faman rubuta masa shirme acikin paper'n ne ta kuma jawo Hijab ɗinta, cikin ƙasa da murya tace. "Laylerh wai bazaki juyo bane, kinataji ina miki magana tun ɗazu." Laylerh kam bata juyo ba, yima tayi kaman bataji Teemah'n ba, tasan Teemah sarai Ć´ar rigima ce, yanzu tana juyowa kuma shikenan bazata saketa ba har sai tasa malami ya gansu, maybe ace ma suje suyi kneel down awaje. Ganin Laylerh bata juyo bane yasa Teemah ta saki ƙwafa, abayyane tace "Wallahi zanyi maganinki Laylerh." Mumurmushi kawai Laylerh tayi, tasan halin mutumiyar tata sarai, fitinanniya ce, karatun ma bawai ya wani damunta bane. Mintuna 30 kacal teacher David yace suyi submit, nan yasoma bi line by line yana amsan papers ɗinsu. Yana ƙarasowa kan Laylerh ya miƙa mata hannu alaman ta bashi paper'n nata, miƙo masa tayi kaman yanda ya buƙata, saidai batare da ta yi aune ba taji ya shafo hannunta, da sauri ta ɗago idanunta ta kalleshi, gani tayi ya wani irin lumshe mata ido, harda lashe laɓɓansa. Da sauri ta janye hannunta, jin tacire hannunta daga nasa ne yasa shi wucewa sit ɗin Teemah, idanunsa da suka soma sanja kala ya watsawa Teemah harda ƙarin harara, cikin faɗa faɗa yace. "Ke bani takardanki." Miƙa masa takardan tayi, yana amsa ya juya ya tafi. Har yakai bakin ƙofar fita daga cikin ajin ya juyo cikin kakkausar murya yace. "LAYLERH MAHMOUD GWANI, by 10:00 am kizo office ɗina kisameni." Baijirayi me zata ceba ya fice daga cikin ajin. Yana fita Teemah tayi saurin dawowa sit ɗin da Laylerh ke zaune, wani duka ta kai mata tare da cewa. "Yamiki kyau uwa da uban Ć´an latti, wai ke kam Laylerh yaushe zaki daina latti ne?." Idanunta masu kyau taɗan lumshe, tare da shafa cikinta da taji yana murɗawa, cikin zazzaƙar muryarta tace. "Nibansan meke damunki ba Teemah, wallahi kina da takura, ɗazu da kike ta damuna mezan miki ne?." "Bansani ba ɗin Ć´ar rainin hankali." Teemah tafaɗa tana me gyara zamanta, idanu ta zubawa Laylerh'n, dan ganin wani bushashshen hawaye kwance akan fuskarta. Hannunta ta kai kan fuskar Laylerh'n ta shafa hawayen, asanyaye tace. "Kuka?." Shiru Laylerh tayi, tare da sunkuyar da kanta ƙasa. Kai Teemah ta girgiza, tare da ɗaura hannunta akan kafaɗan Laylerh'n, cikin kulawa tace. "Yau kuma meya sameki, harda kuka?." Kai Laylerh ta jijjiga alaman ba komai. Baki Teemah ta cije, tare da cewa "Hmmm kima daina ɓoyewa Laylerh damuwarki abune nayau da kullum, ya riga daya bi jikinki dole sai angane saboda haka kima daina wahalar da kanki wajen ɓoyewa, yauma bakiyi break fast ba kika fito ko?." Still idanunta taɗan lumshe tare da jinjina kai, alaman "Eh." Ajiyar zuciya Teemah ta sauƙe, cikin tausayin ƙawartata tace. "Ni narasa wace irin rayuwa akeyi agidanku Laylerh, bansan meyasa ake miki haka ba, babu wani mutum ɗaya da yake kulawa dake acikin gidannan, bakya taɓa jin daɗi sai Abbu na nan, suna kyararki suna miki abu kaman ke ba jininsu bace, always suna barinki kina yawo da yunwa, daidai da school wannan baza'a sa driver ya kawoki ba, sai idan Abbu na nanne ma watarana kike samun arzikin shiga mota, wallahi Laylerh Ć´an gidanku basu da kirki, more especially Momy." Saurin toshe mata baki Laylerh tayi, hawayen da suka cika idanunta ta goge, cikin raunin daya bayyana mata tace. "Kada kice haka Teemah, bansan meyasa ba raunina baya ɓuya, ako da yaushe ni me rauni ce akan damuwa ta,kada ki bari damuwata ta dameki Teemah, because damuwata ta yau da kullum ne." Baki Teemah ta taɓe sannan ta girgiza kai, komawa sit ɗinta tayi ta ɗauko wata food flask, wanda kuma tana zuwa da itane musamman dan Laylerh'n. Buɗe food flask ɗin tayi sannan ta tura mata gabanta, abinci ne me rai da lafiya acikin food flask ɗin, soyayyen doya da miyan egg sai pepper chicken soup akai, ayanda takejin yunwa sosai batajin zataƙi cin abincin, dayake time break ne hakan yasa acikin ajikin taci abincin, goran ruwan swan Teemah ta miƙo mata takarɓa tasha. Tuno da cewa Teacher David yace ta sameshi a office ɗinsa ne, yasa ta ce da Teemah tazo ta rakata. Akaf duk makarantar bata da wata ƙawa wanda ta wuce Teemah, kasancewar makarantar tasu ta Ć´aĆ´an masu faɗa aji ne, yasa kowa harkan gabansa yake, ba ruwan kowa da kowa, duk wanda ka gani yanaji da isa da kuma kuɗin babansa. Koda suka ƙarasa bakin office ɗin, tsayawa Teemah tayi, tace ita bazata shiga ba, saboda tasan me ta aikata akan pepern ta, duk yanda Laylerh taso Teemah taraka ta ciki ƙi tayi, dole haka ta nufi office ɗin ita ɗaya. Knocking ƙofan tayi daga ciki ya bata izinin shigowa, ahankali ta tura ƙofar ciki ta shiga. Tsayawa tayi daga ɗan nesa dashi, cikin sanyin murya tace. "Sir gani." Ɗago kai teacher David yayi ya tsura mata idanu, tsaida idanunsa akan ƙirjinta yayi, ƙuri ya mata baya ko ƙifta idanunsa. Ganin irin kallon da yake mata yasa ta maida hannunta cikin hijabinta, tare da ɓoye ƙirjinta. Tasowa yayi daga kan kujeran da yake zaune, kaitsaye ya nufo inda take sai faman ƙanƙance ƙananun idanunsa yake. Shikaɗai yake saƙa wani abu acikin zuciyarsa, tunani yake aɗazu iya hannunta kawai ya ɗan taɓa yaji wani iri ajikinsa, ina kuma ace idan ya rungumeta yasan abun da zaiji saiya kusa zautar dashi. Ganin yana matsota ne yasa ta soma ɗan jan jikinta baya, ahaka har takai jikin bango bai daina matsota ba, jinta ajikin bangone yasa ta rumtse idanunta, cikin muryarta dake rawa tace. "Sir...." Maganan natane ya maƙale sakamakon jin ya damƙo hannunta, yana ƙoƙarin jawota jikinsa, tsoro ne ya kamata take jikinta yasoma rawa, cikin sauri ta fusge hannunta tare da sake matsawa can gefe, hijab ɗinta ya riƙo, still ƙoƙarin jawota jikinsa yasoma yi, da sauri ta fusge hijab ɗinta tare da ficewa daga cikin office ɗin, hartana jin tuntuɓe saboda sauri. Cike da takaicin asarar daman da yayi akanta, ya cije laɓɓansa, tabbas yaso ace ya rungume ta yaji abun da yakeso yaji, batun yauba komai na yarinyar ke burgesa, musamman ma idan tana magana yanda laɓɓanta ke motsawa shiyake sawa yaji sha'awarta sosai. Laylerh kuwa tana fita daga office ɗin nasa, ta saki wata irin ƙatuwar ajiyar zuciya. Teemah dake tsaye ne ta riƙo hannunta tare da cewa. "Yadai Naga kina haki kamar wanda tayi wasan tsere." Atsorace ta kamo hannun Teemah suka bar bakin office ɗin, hankalinta aɗan tashe tace. "Teemah tsoro nakeji, Teacher David ɗan iskane koda na shiga wajensa ƙoƙarin kamani yayi." Idanu Teemah ta zaro, cikin yanayin mamaki tace. "Ɗan iska? No wonder shiyasa always zaki ga yana wuƙi wuƙi da ƙananun idanunsa, munafuki muwuce class kadama yaganmu." Suna riƙe da hannun juna haka suka nufi class ɗinsu. 5:00 pm daidai kamar yanda aka saba tashinsu akowacce rana, yau ɗin ma hakanne ya kasance ƙarfe biyar daidai aka tashesu. Gaba ɗaya compound ɗin makarantar tasu cike take da ɗalibai maza da mata, kowannensu kuwa kallo ɗaya zakayiwa fuskarsa ka nazarci halin da yake ciki, wato gajiya, da kuma yunwa, irin wanda ɗalibai suka saba dawowa dashi gida, haka take ma akan fuskar Laylerh Mahmoud Gwani, wanda itama amatuƙar gajiye take sosai, ga kuma wani irin stress dake damunta. Atare suka fito daga cikin class ɗinsu ita da Teemah. Kamar yanda yake a ƙa'idan makarantar tasu idan ankawo ɗalibi ko anzo ɗaukarsa daga bakin gate ake sauƙeshi ba ashigo da car cikin makarantar. Hakanne yasa gaba ɗaya wajen makarantar cike yake da motoci, ƙarasowan drivern gidan su Teemah ne yasa, Teemah ta matsawa Laylerh cewar lallai sai tashiga sun yi dropping ɗinta agida. Bazataƙi ba saboda itama tana da buƙatar hakan, kuma tsakaninta da Teemah babu ɓoye ɓoye. Kasancewar basu da wani nisa me yawa tsakanin gidan su Laylerh da makaranta, hakan yasa basu wani jima suna tafiya ba suka iso, aƙofar tangamemen gate ɗin gidan suka sauƙeta, bayan ta fito daga motanne ta ɗagawa Teemah hannu alaman sai gobe. Kai Teemah ta jinjina mata sannan driver yaja motar suka tafi. Ahankali ta tura ƙofar gate ɗin gidan nasu ta shiga, wannan karon kam ba Ɗahiru bane abakin gate, wani soldier man tagani sanye da kakinsa, fuskarnan tasa ko alaman murmushi babu, hakanan taji bugun zuciyarta ya tsananta, take wani tunani ya bijirowa ƙwaƙwalwarta, memories ɗin baya ne yasoma ƙoƙarin dawo mata, kallon soldier man ɗin takuma yi, asanyaye ta nufi katafaren ginin cikin gidan nasu. Wata haɗaɗɗiyar farar matace zaune acikin hamshaƙin falon, sanye take da awarwaro da kuma sarkan zinare awuyanta, kallo ɗaya zaka mata kasan taji yalwan arziki, dukiya kuma sun zauna mata, wata tsaleliyar wayace ƙiran iPhone 11 pro riƙe ahannunta, sai kuma laptop dake ɗaure bisa cinyarta tana latsawa, gefe da ita kuwa wata mata ce itama tasha kwalliya, saidai ita baza'a ƙirata da sunan babbar mace ba, dan da'alama bata da yawan shekaru jikine kawai da take dashi, wayane itama ahanunta tana ta faman latsawa. Da sallama ɗauke abakinta ta turo ƙofar falon ta shigo. Daga cikin mata biyun nan babu wacce ta ɗago kai ta kalleta balle tasa ran zasu amsa mata sallaman nata, ƙarasowa cikin falon tayi, tare da ɗan rusunawa, murya asanyaye tace. "Momy, Aunty, barka da gida." wacce aka ƙira da Momy ne ta ɗago kanta cike da tsananin isa, bata iya amsawa ba sai jinjina kai da tayi. Idan da sabo ta saba da hakan. Ta bayansu ta raɓa ta nufi hanyar da zai sadata da ɗakinta, daidai takawo tsakiyan tangamemen falon idanunta suka sauƙa akan wani ƙaton hoto dake cikin falon, wanda aka killacesa cikin wani haɗaɗɗen glass, idanu taɗan tsurawa hoton duk dama baka iya ganin fuskar wanda ke cikin hoton dan ya bada bayane aka ɗaukesa, kallo ɗaya zakayiwa bayan na cikin hoton ka fahimci cewa cikakken Namiji ne, kuma gwarzo, dan sanye yake da kakin sojoji ajikinsa, wanda sukayi masifar yi masa kyau, ahannunsa riƙe yake da wani kwalba, da alama unexpected pic ne akayi masa batare daya sani ba. "Laylerh." Momy taƙira sunanta. Jin momy taƙira sunanta ne yasata ɗauke idanunta daga kan hoton tare da juyowa, asanyaye tace. "Na'am Momy." Batare da Momy ta kalleta ba tace. "Kicire uniform ɗin kizo na aikeki." "To." tace sannan ta shige cikin ɗakinta. Aunty Aina'u dake zaune sai yanzu ta ɗago kai ta dubi Momy, cikin kulawa tace. "Yau naga kaman bakya cikin mood me daɗi meya faru?." Numfashi Momy ta fesar tare da gyara zamanta, cikin wani irin yanayi tace. "Next week CAPTAIN MALEEK Zai dawo." Idanu Aunty Aina'u taɗan zaro, cike da mamaki tace. "What Captain M.J GWANI zai dawo? mutumin daya share kusan 7 years a U.S bai waiwayo Nigeria ba, then yanzu kuma yace zai dawo, aikine zai kawosa kenan ko me?. " Baki Momy ta taɓe ataƙaice tace. "I don't know." Ɗan jim Aunty Aina'u tayi,lokaci ɗaya ta saki murmushin da ita kaɗai tasan ma'anarsa. Momy kam batasake cewa komai ba, saima ɗauƙan drinks tayi ta soma sha, zuciyarta duk ba daɗi, musamman akan dawowan CAPTAIN MALEEK. Laylerh kuwa tana shiga ɗaki Kayan jikinta ta soma cirewa, sannan ta wuce toilet, ruwan ɗumi ta haɗawa kanta sannan tayi wanka, koda ta fito wata doguwar riga me kalan ja ta sanya ajikinta, sannan ta saka hijab akai. Sauri sauri ta zura Flat shoe aƙafanta sannan ta wuce falo dan zuwa aikan Momy. Agaban Momyn ta durƙusa tare da cewa. "Momy nashirya." Wata Ć´ar ƙaramar jaka Momy ta miƙa mata, cikin magananta na isa tace. "Driver na jiranki awaje ki kaiwa Hajiya Asma'u." "To." kawai tace sanan ta miƙe tanufi ƙofar fita daga cikin falon, ɗaura hannunta akan Handle ɗin ƙofar yayi daidai da ɗaura nasa hannun akan handle ɗin ƙofar ta waje, tare da turo ƙofar ciki, hakanne yasa ta ɗanja baya, ɗago da kansa yayi daidai da haɗewan idanunsu waje ɗaya, hakan yasa ta tsaya tana kallonsa, shima manyan idanunsa ya zuba mata tare da tura duka hannunsa acikin aljihun wandonsa. U.S.A Adaidai wannan lokacin yasoma buɗe kyawawan idanunsa wanda sukayi masa nauyi, har yakai ga baya iya gani sosai. Hannunsa yakai ya shafi gefen cikinsa wanda aka ɗaure masa da bandage. Sake maida idanunsa yayi ya rufe, ahankali yake ganin tana masa yawo acikin idanunsa, akowacce rana akuma koda yaushe sai idanunsa sunyi masa gizo, yanda take ta wasan tsalle tsalle a compound ɗin gidan yake kallo acikin idanunsa. Rumtse idanunsa yayi sosai, saboda yanda yaji kansa nayi masa wani irin mummunan sarawa, take jijiyoyin jikinsa suka Mimmiƙe, da ƙarfi ya cire drip ɗin da aka saka masa tare da tashi zaune ya kama daidai saitin zuciyarsa da ke harbawa, idanunsa wanda sukayi jajur ya ware, inda ya sauƙesu akan agogon dake saƙale ajikin bangon ɗakin. *Vote nd Comment* (31/October/2020) am sorry Jiya nayi mistake ɗin date) *fatymasardauna* 1/19/21, 8:09 PM - Ummi Tandama: 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇      *LAYLERH MALEEK* *Writting By* Phatymasardauna                      *Wattpad*               @fatymasardauna #Destiny                    *Chapter 3* Idanunta taɗan lumshe tare da matsawa gefe ta bashi hanya, don ya wuce, murmushi ne ya bayyana akan laɓɓansa, cikin nutsuwa ya raɓa ta gefenta ya wuce har jikinsa na ɗan gogan nata, ƙamshin turaren dake tashi ajikinsa ne ya cika mata hanci.   Hakan yasa ta kau da kanta gefe, tare da ficewa daga cikin falon.                 Har ta fita daga cikin falon bai daina kallonta ba.      "Habeeb."   Daga cikin falon Momy taƙira sunansa.   Dawo da kallonsa wajen Momy'n yayi, tare da yi mata alama da idanunsa yanda zata fahimci me yake nufi.          Ɓata fuska tayi, cikin son nuna masa abun da yake son sani ba huruminsa bane tace.      "Zaka iya ƙarasowa muyi abun da ya kawo ka."    Murmushi Kawai Habeeb yayi dan dama yasan ko zaiyi yaya ne Momy bazata taɓa faɗa masa abun da yakeson ji ba, sau da dama yasha tambayarta agame da LAYLERH amma bata bashi amsa, saima tsumewa da takeyi, baisan me yasa hakan ba, saidai yasan dole akwai wani abu aran Momy, wanda zai iya yiwuwa tana da wani nufinne akan Laylerh na daban, da wannan tunanin ya ƙaraso cikin falon ya zauna.             Laylerh kuwa tana fita compound ɗin gidan, ta samu drivern Momy tsaye yana jiranta,  buɗe murfin motar tayi ta shiga sannan drivern ya tada motar,  maigadi ne ya wangale musu ƙofar gate ɗin gidan.   Koda suka kawo bakin gate ɗin, ɗan leƙa kanta tayi ta window'n motar, still har yanzu wannan soldier man ɗin na tsaye abakin gate, kamar dai yanda tabarsa ɗazu,  jingina bayanta da jikin kujeran motar tayi, tare da lumshe beautyful sexy eyes ɗinta.     "MR.SOLDIER."  tafaɗa abayyane tare da ɗan ciza ƙananan jajayen laɓɓan bakinta,   tabbas zuciyarta nason tuna mata wani abu daya wuce acan baya, saidai kuma ƙwaƙwalwarta taƙi amsa hakan, gudu take tare da ɗiban wasu ayyuka masu tarin yawa, wanda ayanda take da ƙarancin shekaru bai kamata ace hakan na kasancewa da ita ba,   dole haka ta watsar da wasu tunanin da suka kasance marassa amfani, ko da sauɗaya ne itama watarana tanaso ace takasance kamar kowa, tunanin abun da Teacher David yayi mata ne ya shiga dawowa kanta, ji tayi idanunta masu matsanancin rauni sun cika da ƙwalla, sannu ahankali hakan ke ƙoƙarin tuna mata wani abu daya faru da rayuwarta lokacin baya, cikin wani irin sanyin murya, me ɗauke da rauni tace.   *"YA M.J"*    hawayen da suka cika idanunta ne suka samu daman gangarowa, lokaci ɗaya taji gaba ɗaya jikinta yayi weak, tunanin abun daya faru abaya ne yasoma ƙoƙarin kutsowa cikin brain ɗinta, wani irin tsoro ne me tsanani ya lulluɓeta, hakan yasa gaba ɗaya jikinta ya soma rawa, cikin kunnuwanta tasoma jin wata irin murya naƙiran. *"AYSHNOOR!!"* in a slow tone, murya ce da bazata taɓa iya manta ta ba, acikin gaba ɗaya duniyarta da rayuwarta.   Da sauri ta buɗe idanunta, sakamakon jin yanda drivern ya caka burki, har sai da taɗan wantsalo gaba.           Idanunta taɗan zaro waje ganin saura kaɗan su buge wani ɗan dattijon mutumi da yazo tsallaka titi.   driver'n ne ya leƙa kansa waje inda ya bawa mutumin haƙuri, sannan yaja motar sukayi gaba. Sake lumshe idanunta tayi, akaro na sau ba adadi, hakan ɗabi'a ne, wanda yake gudana acikin jininta, lumshe ido da cije lips, sauda dama takan tambayi kanta meyasa takeyin hakan, saidai takan rasa amsan da zata bawa kanta, dole tabar hakan amatsayin ɗabi'arta. Ko mintuna 7 basu ƙara ba suka iso gaban makeken gate ɗin gidan Hajia Asma'u,   abakin gate ɗin drivern ya faka, hakanne yasa ta buɗe murfin motar ta fito, gaba ɗaya duk jikinta asanyaye yake, dole haka ta aro ƙwarin guiwa da jarumta ta sakawa kanta, dan bakowa takeso ya karanci damuwarta ba.    Ahankali ta tura ƙaramar ƙofar gate ɗin ta shiga cikin gidan,    maigadin dake zaune abakin ƙofar ɗakin da aka tanada musamman danshi, yana ganinta ya washe baki tare da tasowa ya ƙaraso gareta, baki har kunne ya shiga cewa.   "Fara me farar aniya, Farar Alkhairi,  kaga yarinya kyakkyawa son kowa, fara me zubin larabawa, wallahi ko acikin larabawa LAYLATU  kin fi wasu da yawa kyau, tauraruwa me haske abun son kowa."          Shiru Laylerh tayi tare da sakin murmushi, tabbas idan da sabo ta saba da halin mutumin, dan idan Momy zata aikota gidan sau dubu, to ba gajiyawa zai mata kirari sau dubu,   ɗan rusunawa tayi, saboda mutumin yana da ɗan yawan shekaru, cikin sanyin murya tace.   "Ina wuni Baba."      Baki ya sake washewa tare da cewa.    "Lafiya ƙalau Laylatul Khair, wato daren alkhairi kenan ko, inji larabawa, duk yanda akayi dai a daren Laylatul Ƙadari aka haifeki, wato daren Daraja kenan."   Dariya Laylerh tayi, sannan ta girgiza masa kai, sanin cewa idan ta tsaya zaita yi mata surutu ne yasa ta wuce cikin gidan.  Shima murmushin yayi sannan ya koma ya zauna.   Laylerh kuwa tsayawa tayi abakin babbar ƙofar da zai sadata da falon gidan, knocking tayi akazo aka buɗe mata ƙofar, Hajiya Asma'un ce da kanta ta buɗe kofar,  ganin Laylerh yasa ta saki ɗan murmushi, tare da cewa.     "Laylerh kece, sannunki da zuwa."    Tafaɗi maganan tana me bawa Laylerh hanya ta wuce.  Saida suka ƙaraso cikin falon Laylerh ta rusuna ta gaishe da Hajiya Asma'u'n, fuska asake Hajiya Asma'u ta amsa mata, tare da tambayanta su Momy.    "Lafiansu ƙalau."  Laylerh ta amsa mata, tare da miƙa mata Ć´ar jakan da Momy tace takawo mata, amsan jakan Hajiya Asma'u tayi tana murmushi, nan ta ƙwala ƙiran mai aikinta, ahanzarce kuwa mai aikin Hajiyan tazo, cikin isa Hajiya Asma'u tace.     "Kikawo wa Laylerh drinks da abinci."     "To" tace cikin sauri ta juya ta koma kitchine dan cika umarnin Hajiyan.                     Bawani jimawa ta kawowa Laylerh Jallop rice nd coslow sai kuma banana drinks,    cikin kulawa Hajia Asma'u tace. "Laylerh kici abinci."       Murmushi tayi, cikin yanayin nutsuwa tace.  "Hajiya na ƙoshi bana jin yunwa."  Kai Hajiya Asma'u ta girgiza tare da cewa.  "Aa Laylerh kinsan banason halin nan naki na fulaku."  Tana faɗan haka tatashi ta wuce ɗakinta.       Ɗan jim Laylerh tayi, bawai yunwan ne bataji ba, kawai dai bata da sakewa ne, sometimes takanji ɗar da kuma tsoron wasu mutanen na daban.  Ahankali take ɗiban abincin tana kaiwa bakinta, bata wani ci abincin sosai ba taji ta ƙoshi, kasancewar dama ita ba mutum bace me yawan cin abinci,  ruwa tasha sannan ta miƙe tsaye, daidai lokacin Hajiya Asma'u tafito daga ɗakinta.  Ganin Laylerh a tsaye yasa tace "Har kin kammala?."   Kai Laylerh ta jinjina, tare da ɗaukan tissue ta goge bakinta.         Wata Ć´ar ƙaramar jaka Hajiya Asmau ta bata, tare da cewa  "Gashi wannan  naki ne ki gaishemin da Momyn taku."   Ƙoƙarin girgiza kai Laylerh ta somayi, alaman bazata amsa ba, take Hajiya Asma'u ta ɓata fuska, ahanzarce tace.   "Banason musu Laylerh ki amsa kawai."    Karɓan Ć´ar ƙaramar jakan Laylerh tayi tare da yiwa Hajiya Asma'un godiya, daga haka tayi mata sallama sannan tafice daga cikin falon.          Saida ta shiga cikin mota, har suƙa fara tafiya, kafun ta buɗe Ć´ar jakan da Hajiya Asma'un ta bata, kayan meckup ne aciki sai kuma wani agogon silver me kyau, sai kuma kuɗi 5k, rufe jakan tayi tare da maida kallonta ga titi, abubuwa da yawa takeson saƙawa acikin rai da zuciyarta, amma duk yanda taso hakan abun ya kasa,  bata sani ba ko ƙwaƙwalwarta ne batayi ƙarfi ba wajen iya nazartan abubuwa.     isowansu gidane yasa ta ajiye duk wani tunani,   tana fita daga cikin motar kaitsaye babban falon gidan nasu ta nufa, bata taradda kowa ba,  ganin lokacin sallan Magrib ya gabato ne yasa  kaitsaye ta wuce ɗakinta.      Hijab ɗin dake jikinta ta cire sannan ta shiga toilet ta ɗauro alwala,      koda ta fito nan kan darduman dake shumfuɗe acikin ɗakin ta hau, ta gabatar da sallah, tana nan zaune akan sallayan har aka ƙira sallan Isha, bayan ta idar da sallan Isha ɗinne ta miƙe daga kan sallayan, gaban drawer ɗinta ta ƙarasa tare da buɗewa ta zaro wani riga da wando na bacci masu kalan blue,  doguwar rigan dake jikinta ta cire sannan ta maye gurbinsa da riga da wandon,   dunƙule dogon gashinta tayi waje ɗaya, sannan ta sanya wata hulan sanyi akanta, kasancewar ana ɗan busa sanyi kaɗan.     Kan ɗan madaidaicin gadon nata ta hau, tare da jawo blanket ta rufe jikinta dashi,  hannunta na dama ta ɗago tare da zubawa ɗaya daga cikin yatsunta dake sanye da wani haɗaɗɗen zobe idanu, wanda ajikinsa aka rubuta (L.M)  da manyan baƙi,  zobe ne na zallan zinare me tsananin kyau da tsada,  ɗan lumshe idanunta tayi ahankali take ɗan murza zoben da hannunta, tana matuƙar ƙaunar zoben sosai, wanda yana ahanunta ne sama da 7 years, tun yana ababban ɗan yatsarta har ya dawo ƙaramar yatsarta saboda yaɗan mawa babban yatsan nata kaɗan.             Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da tura kanta acikin pillow, ita da zuciyarta kawai suke faɗin wasu kalamai wanda ƙwayan sautinsa baya iya bayyana, saidai laɓɓanta dake motsawa ahankali.  Ahaka bacci ɓarawo ya ɗauketa.  Washe gari.   Da sassafe ta tashi, bayan tayi sallah ne ta wuce  kitchine,  ita da kanta ta haɗa break fast ɗin gidan, sannan ta gyara kitchine ɗin tare da duk wani abu da ta ɓata, acikin food flask tasa abincin wanda zata tafi makaranta dashi, ganin 7 yakusa ne yasa agurguje taje tayi wanka, ta shirya cikin  kayan uniform ɗinta me kalan navy blue nd milk,  sosai tayi kyau acikin shigar uniform ɗin, wanda yake ƙara bayyana zallan yarinta da kuma kyawunta, LAYLERH kyakkyawar yarinya ce wacce bata da yawan hayaniya, yarinyace da take tafiya daidai da shekarunta, bata da jiki haka kuma baza a ƙirata da sunan siririya ba, saidai tana da ɗan faɗi ta ƙasanta, duk da cewa ayanzu ne alamomin girma ke bayyana ajikinta, amma hakan bai hana hips ɗinta fitowa ba, tana da shape me kyau, wanda hakanne ke ƙarawa tsarin halittarta kyau,  kaitsaye ba za'a ƙirata da doguwa ba, saboda yanayin tsayinta yana tafiya ne da shekarunta. duk da kasancewar shekarun Laylerh basu ɗara 17 ba amma tana da structure me kyau, ayanayin fuskarta kuwa tana da ɗan madaidaicin baki da kuma dogon hanci, sannan tana da wasu irin rikitattun idanu masu ɗaukar hankali da yalwar eye lashes asaman su, kaitsaye idan kaga idanun nata bazaka ƙirasu da manya sosai ba, amma idan ta waresu suna da girma,  asaman forehead ɗinta kuwa wasu irin lausassun gargasane kwance lub, sunyi mata ƙawanya, wanda suka ƙara ƙawata kyawun fuskarta, kamar yanda komai nata yake me kyau hakama farar fatarta takasance natural.     Cikin sauri ta goya school bag ɗinta, sannan ta zura wasu sneaker shoe aƙafanta, yau kam sam bataso ta makara hakan yasa take komanta ahanzarce.    Tayi sa'a kuwa koda ta fito falo su Momy sun gama break fast ɗinsu,  food flask ɗinta ta ɗauka sannan ta fice daga cikin falon da sassarfa.      Koda ta fito daga cikin gidan nasu, kaitsaye hanyar da zata samu taxi ta nufa, da yake sauri take shiyasa bata wani ɓata lokaci ba ta iso babban titin, tana ƙarasowa kuwa ta samu taxi ta shiga.   Koda suka ƙarasa makarantar motar mai taxi ɗin na sauƙeta, motar gidan su Teemah na ƙarasowa,  hakanne yasa suka jera atare ita da Teemah suka shiga cikin makarantar, Teemah sai tsiya take mata, akan wai yau tayi ƙoƙari tazo da wuri.      Koda suka ƙarasa cikin class sanin cewa English shine firsf period ɗinsu yasa suka nutsu tare da bada hankalinsu ga Malamin English ɗin nasu.       Koda aka fita break anan cikin ajin suka zauna, dayake Laylerh bata wani damu dason yawo ba, shiyasa Teemah ke biye mata, sometimes acikin aji suke break ɗinsu.        5 daidai aka tashesu, Yauma Teemah ne tasa driver ɗinta yayi dropping Laylerh.           Tana shiga compound ɗin gidan, taga motar Momy na ƙoƙarin fita daga gidan,  yi tayi kaman bataga motar ba cikin sassarfa ta wuce cikin gidan,  kaitsaye ɗakinta ta wuce, wanka tayi sannan ta ɗauro alwala, riga da wandon fakistan tasa sannan tafito falon, kitchine ta shiga tare da zubawa kanta abinci,  sanin cewa Momy batanan yasa ta zauna acikin falon taci abincin, koda ta kammala tashar Zee world ta kalla, jin ana ƙiran sallah ne yasa taje ta ɗauro alwala, again bata tashi akan sallayan ba saida ta idar da sallan Isha, kasancewar gobe saturday, kuma ranan monday suna da Islamic test yasa ta ɗauki littafin Islamic ɗinta taɗan duba, sai 9 ta kwanta, take bacci ya ɗauketa, haka take bacci baya bata wuya, always da ta kwanta kawai zatayi bacci.  Washegari kuwa tun tashinta taji gidan nasu yaɗan cika da hayaniyan mutane,  kasancewar yau ɗin weekend ne yasa tayi tunanin ko Abbu ne zai dawo, jin yanda surutu ke tashi acikin compound ɗin gidan nasu ne yasa ta sauƙo daga kan gadonta, ahankali ta ƙarasa jikin window'n dake cikin ɗakinta, ɗan buɗe labulen windown tayi, soldiers ta gani da yawa, sunata zazzagaye compound ɗin gidan, saurin sake labulen tayi, tare da sa hannu taɗan dafe daidai saitin zuciyarta dake beating, sama da mintuna uku ta ɗauka ahaka, kafun daga bisani ta zura hijab ɗinta, ta fita zuwa falo, dan ko break batayi ba.  Momy ce zaune afalon ita da Aunty Aina'u,  sai kuma wasu wanda batasan ko su waye ba, saidai ayanda tagansu kowacce taji naira, da alama ƙawayen momy ne, ƙarasawa cikin falon tayi, tare dabin ko ina dake cikin falon da kallo, domin kuwa komai na falon an sauyashi, ga wani decoration da akayi me kyau, gefe guda kuwa masu aiki ne keta kai da kawowa acikin falon, hidima kawai sukeyi. Gaishe da ƙawayen Momyn tayi, haka suka amsa mata sama sama, dama ta saba da hakan, kitchine ta nufa saboda yunwa takeji sosai.             11:00 pm.    Wasu tsala tsalan motoci ne guda biyu ke gudu akan babban titin, motocine masu kyaun gaske, inda ɗaya daga cikin motocin takasance ƙirar Range Rover 2018, sai kuma wacce tafi Range Rover'n kyau, wanda take ƙirar G Waggon 2019, gudu sosai motocin keyi har suka kutso cikin, hamshaƙiyar unguwar, kan shumfuɗaɗɗiyar titin dake malale acikin unguwar suka ratso, inda suka tsaya  agaban makeken gate ɗin gidan, tare da danna horn, ko second 8 ba aƙaraba aka wangale musu makeken gate ɗin gidan, da gudu kuwa masu tuƙin cars ɗin suka shige cikin gidan.  Nan cikin tsakiyan compound ɗin gidan motocin suka faka,  cikin sauri  wasu soldiers guda huɗu suka fito daga cikin black range rover car, jikin G Waggon ɗin suka ƙaraso suka tsatstsaya, babu ko ɗigon fari'a  akan fuskar soldiers ɗin.     Sama da 5 minute aka ɗauka batare da wanda ke cikin G Waggon ɗin ya fito ba.        Ɗaya daga cikin sojojin nan ne ya kai hannunsa inda ya buɗe murfin motar, ta ɓangaren me zaman banza.      Ahankali ya zuro da ƙafafunsa waje wanda suke sanye da wasu tsadaddun takalma irin na sojoji, cikin nutsuwa ya gama fitowa daga cikin motar,  sanye yake da wando irin combat ɗinnan amma na kakin sojoji, sai kuma wata black t shirt me kauri daya saka ajikinsa, a kansa kuwa sanye yake da facing cap wanda take itama na soldiers ne, kallo ɗaya tak zaka masa, kabawa kanka amsar wanene shi, wato  jajirtacce kuma tsayayyen Namiji, wanda haɗuwarsa ya zarce duk wani misali, yana da wata irin murɗaɗɗiyar surar jiki abun burgewa,  fari ne irin tas ɗinnan, sannan kuma yana da wani irin kyau da ƙarin kwarjini, duk da cewa bazai haurawa 31 years ba, amma yana tafiya daidai da shekarunsa.   facing cap  ɗin daya sanya  akansa ne ya sanya fuskarsa, da asalin kamaninninsa suka ɗan ɓuya, amma duk da haka ana iya hango lallausan sajen dake kwance akan fuskarsa, wanda shi ya ƙara ƙawata kyawun fuskar tasa.   Cikin wani irin taku dake nuna zallan kwarjininsa ya nufi hanyar da zai sadasa da babban falon gidan.                Daidai lokacin Laylerh ta fito daga cikin kitchine hannunta ɗauke da flask da kuma cup.        Ahankali ya murɗa handle ɗin ƙofar falon ya shigo, shigowansa cikin falon yayi daidai da fitowan Laylerh daga cikin kitchine, haka zalika yayi daidai da kai dubanta zuwa ga ƙofar shigowa falon, adaidai lokacin ne kuma narkakkun idanunsa suka sauƙa akanta, ganinsa da kuma kallonta da yayi, yayi daidai da sarƙewan numfashinta, take tasaki flask ɗin dake hannunta, har da cup ɗin duk suka faɗi ƙasa. (Kuyi haƙuri duk bayan kwana ɗaya zankeyi muku update, saboda hakan na taimakawa wajen hutawan brain ɗina.) *2/Nov/2020* *Vote nd Comment please* *fatymasardauna* 1/19/21, 8:10 PM - Ummi Tandama: 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇              *LAYLERH MALEEK* *Writting* By phatymasardauna               *Wattpad*       @fatymasardauna #Crush               *Chapter 4* Ƙaran faɗuwan flask ɗin dake hannunta ne yasa, duk hankalin su Momy ya dawo kanta.       Cikin sauri ba tare da ta yarda ta sake ɗaura idanunta akansa ba, ta durƙusa awajen da flask ɗin ya faɗi, yayinda  gaba ɗaya jikinta rawa yake, hannayenta dake rawa tasanya ta  ɗauko flask ɗin, wanda da dukkan alamu glass ɗin dake  cikinsa ya fashe, ba kuma zai sake amfanuwa ba.                   Tun kallon farko da yayi mata wanda bai wuce na second 2 ba,  ya ɗauke idanunsa daga kanta, hannayensa ya cusa cikin aljihun wandon dake jikinsa tare da ƙarasowa cikin falon, Momy da ganinsa yasa ta miƙewa tsaye, fuskarta ɗauke da murmushi tace.   "Wellcome my son."       Kansa yaɗan jinjina mata,    tare da ɗam lumshe idanunsa alaman.              "Thanks."     Sannu da dawowa Aunty Aina'u da kuma sauran ƙawayen Momy'n sukayi masa, kamar yanda bai amsawa Momy ta magana ba, haka suɗin ma bai amsa musu ba, kansa  kawai ya gyaɗa musu. Hakanne yasa suka bisa da kallo. Kansa tsaye ya nufi wata haɗaɗɗiyar ƙofa dake cikin falon, key ya ciro daga cikin aljihunsa, tare da sawa ya buɗe ƙofar,  tura ƙofar ciki yayi, ahankali ya aje ƙafarsa akan lallausan carpet ɗin dake malale bakin ƙofar shigowa sashin nasa.  Maida ƙofar tasa yayi ya rufe tare da murza mata key ta ciki. Bayansa yaɗan jingina da jikin ƙofar tare da soma ƙarewa cikin haɗaɗɗen falon kallo, wanda yake mallakinsa ne, komai dake cikin falon so nead, babu wani alaman datti ako ina, sannu ahankali ƙamshin airfreshener ke tashi acikin falon, ga kuma daddaɗan sanyin A/C'n dake busawa, wanda hakanne ma yasa ɗakin gaba ɗaya ya ɗauki sanyi me daɗi.              Cikin takunsa na isa ya gama ƙaraso cikin falon,  zama yayi akan ɗaya daga cikin luntsuma luntsuman kujerun da suka ƙarawa falon kyau, sannan suka ƙara ƙawata shi,  facing cap ɗin dake kansa ya cire, hakanne ya bawa asalin kyakkyawar fuskarsa bayyana.   Wanda yake Kyakkyawane bana wasa ba, yayinda yake da wasu irin fitinannun eyes masu kyau, da ɗaukar hankali, duk da kasancewar idanun nasa basu da girma sosai, amma suna da yalwar lashes asamansu,  sannan ga kuma gashin eye brow ɗinsa dake ashirye tsab sai sheƙi suke,  yana da dogon hanci, da kuma small lips masu ɗauke da kalan pink, akan fuskarsa kuwa babu alaman wasa, ko murmushi, sam fuskar tasa bata ɗauke da yanayin dariya, bata kuma ɗauke da tsumewa, hakanan nature ɗinsa yake, yana da wani irin kwarjini naban mamaki, yayinda lafiyayyen sajen dake kwance akan kumatunsa ke ƙarawa fuskar sa kyau,  yana da wani irin lafiyayyen tulin gashi akansa,  wanda yasha gyara sai shining yake.       Ajiye facing cap ɗin nasa yayi tare da miƙewa tsaye, direct jikin wata ƙofa dake cikin falon ya nufa, ahankali ya murɗa handle ɗin ƙofar, sannan ya kutsa kansa ciki.                       Ɓangaren Laylerh kuwa, gaba ɗaya ganinsa ya so birkita mata lissafi, ɗaukan flask da kuma cup ɗin tayi ta mayar kitchine, anan gaban sink ta tsaya tare da kunna fanfo, ruwan dake gudunatasa hannu ta tara, tare da watsawa akan fuskarta, hakanan taji zuciyarta na tsananta bugawa,  idanunta da suka sanja launi ta lumshe, tare da sakin wata ƙakƙarfan ajiyar zuciya,   tabbas ganinsa da tayi ayanzu  yana neman tuna mata abubuwan da suka wuce tun tana Ć´ar ƙaramar yarinya,  ganinsa yasa memories ɗinta na baya na ƙoƙarin dawo mata,  duk da cewar ta kwashe shekaru masu yawa batare da ta sake sanyashi a idanunta ba, amma koda sau ɗaya ne zuciyarta bata taɓa bugawa batare da wani nau'i na tunaninsa ba, haka zalika sauyawan kamanni da jikinsa baisa ta kasa ganeshi ba, lallai shiɗin ne, koda ace idanunta zasu kasa tantance mata, to banda zuciyarta.    Jin kaman motsin za a shigo cikin kitchine ɗin ne, yasa  ahankali ta buɗe idanunta, tare da ƙoƙarin daidaita nutsuwarta,  anan cikin kitchine ɗin ta haɗa tea ɗin tasha. Samun kansa da yayi acikin makeken bedroom ɗin nasa ne, yasa shi soma ƙoƙarin cire rigar jikinsa,  hannunsa yakai ya shafi gefen cikinsa, wanda ke ɗaure da bandage,  ɗan rumtse idanunsa yayi, da alaman ciwon dake wajen nayi masa zafi,  ƙarasawa gaban madubin dake jikin bangon ɗakin yayi, take yayi ido biu da murɗaɗɗiyar surar jikinsa da kuma buɗɗaɗun muscles ɗinsa,  manya manyan 6 packs ne kwance acikinsa, wanda kallo ɗaya zaka masa ka tabbatar da cewa shiɗin ma'abocin motsa jiki ne, kusan ma ya maida hakan babbar ɗabi'arsa,  still sake kai hannunsa gefen  cikinsa  ta ɓangaren dama yayi, wanda akayi masa   zanen tattoo awajen, ɗan shafa zanen tattoo ɗin yayi, tare da lumshe idanunsa,   wanda yake har  hannayensa akwai zanen tattoo ajiki, saidai zanen tattoo ɗin nashi basu da yawa, wanda yake kuma kowanni zane da akwai abun da yake nufi, kamar zanen dake kwance akan cikinsa, azahirin gaskiya idan ka kalli zanen zaka ɗauka adone kawai akayi awajen, saidai ba hakan yake ba, dan idan mutum me fahimta ya ƙurawa zanen ido, zai iya fahimtar cewa suna ne aka rubuta, sai dai anjuya harufan sunan tayanda baza suyi sauƙin karantuwa har akai ga gane me aka rubuta ba, saidai idan mutum nada zurfin ƙwaƙwalwa, zaiyi saurin gane abun da aka rubuta da tattoo ɗin. Cikin nutsuwa ya zare dogon wandon dake jikinsa, ƙarasawa gaban makeken drawer glass ɗin dake cikin ɗakin nasa yayi, wanda komai dake cikin drawer'n ana iya gani daga waje, wani sabon towel ya ciro daga cikin drawer'n, tare da ɗaura towel ɗin akan waist dinsa, agogon dake hannunsa ya soma koƙarin cirewa, bayan ya kammala ne ya ƙarasa jikin wata ƙofa, wanda da dukkan alama ƙofar toilet ne, murɗa handle din ƙofar yayi ya shige kaitsaye. Tabbas kuwa nan ɗin toilet ne kaman yanda nayi hasashe, amma saidai ya banbanta da sauran toilet ɗin da kuka sani, domin komai dake cikin toilet ɗin na original royal glass ne, hatta bath ɗin wanka kewaye yake da royal glass me ɗaukan idanu,  ƙarasawa gaban shower yayi tare da sakarwa kansa ruwa.       Haka ya ɗauki sama da 30 minute yana wanke jikinsa, koda ya gama alwala yayi sannan ya ɗaura bathrobe ajikinsa. Koda ya fito daga toilet ɗin gaba ɗaya jikinsa ɗauke yake da danshin ruwa, musamman ma gashin kansa wanda har ɗigar da ruwa yake. Agaban dressing mirror ya zauna tare da ɗaukan wani ɗan ƙaramin towel ya shiga tsane gashin kansa,  yana kammalawa kuwa yasa handrayer ya busar da gashin kannasa, wani haɗaɗɗen body lotion ya murza ajikinsa, tare da shafe jikinsa da wani fitinnanen turare.  Ƙaran horn din motan dake tashi acikin compound ɗin gidan ne, ya shiga ratsa kunnuwansa, ɗan lumshe idanunsa yayi saboda sam shi bayason yawan hayaniya, agogon dake saƙale ajikin bangon ɗakin ya kalla, ganin cewa 12:30 pm daidai, ya sashi gane cewa Abbu ne ya dawo, dan dama yace masa yau zai dawo.   Cikin nutsuwa ya ƙarasa gaban drawer ɗinsa, wasu tsadaddun riga da wando ya ciro, kamar yanda ya saba dayin komansa cikin nutsuwa, haka yanzun ma anutse ya saka kayan, wanda suka matuƙar fito da kwarjini da kuma faffaɗan jikinsa, sosai kayan sukayi masa kyau kasancewar fatarsa na da haske sosai, black jeans ne da wata jar riga wacce take da adon baƙi da fari agabanta, sai kuma wata blue ɗin denim jacket daya ɗaura asaman rigar, tare da saka wasu tsadaddun white sneakers shoe aƙafansa, sosai shigar tasa tayi kyau, kwarjininsa kuwa ya sake bayyana,  wata farar facing cap me ratsin baby pink colour ya ɗaura akansa.  Masha Allah Yayi kyau sosai, dan babu wata macen da zata masa kallo ɗaya ta ɗauke kai, baga mace ba harma ga kowa, CAPTAIN MALEEK JAHEED GWANI kenan, matashin saurayin da aƙalla bazai ɗarawa 31 years ba, kyakkyawa ne shi na gasken gaske, sannan yana da abubuwan burgewa masu tarin yawa, duk da cewa bashi da tsawo sosai, amma tsarinsa da kuma murɗaɗɗiyar surar jikinsa, na matuƙar jan hankalin mata da dama, idan ka ganshi kai tsaye bazaka ƙirasa da sunan ɗan Nigeria ba, koda ga yanayin farin fatarsa, idan mutum ya kalla, zai gane cewar shiɗin ba asalin ɗan Nigeria bane, kana kuma shiɗin  yakasance wani irin   murɗaɗɗen mutum, wanda ba a iya gane gabansa da bayansa, miskiline  na ƙarshe, sannan bai fiye yawan  magana ba, saidai yana da zafin nama sosai akan komai musamman ma aɓangaren aikinsa, hakanne yasa sunansa ke yawo ako ina.             Wayarsa ƙirar iPhone 11 pro max ya ɗauka, cikin takunsa na isa kuwa ya nufi hanyar fita daga cikin ɗakin, murɗa handle ɗin ƙofar ɗakin yayi, tare dasa kai ya fice.         Kaitsaye babban falon gidan ya nufa.  Fitowarsa daga sashinsa yayi daidai da shigowar ALHAJI JAHEED GWANI  (Abbu )cikin falon,  ganin M.J ɗin ya saka Abbu sakin murmushi, cikin kulawa yace.    "Wellcome back Captain M.J"      Akaron farko kenan MALEEK ya ɗanyi murmushi, wanda iya kanta kan laɓɓan bakinsa, saidai kuma abun da baisani ba, murmushin ya matuƙar ƙarawa fuskarsa kyau, haka zalika akaron farko daga dawo wansa zuwa yanzu da sautin muryarsa ta bayyana, yace. "Thank you Abbu."    Hannu Abbu ya miƙa masa tare da cewa.   "Naji daɗin dawowanka Maleek, saboda kwata kwata hankalina baya kwanciya da zamanka a US ɗin nan, then 7 years fa kenan bakazo Nigeria ba."       Musabaha sukayi shida Abbu'n nasa, sannan ya zauna akan ɗaya daga cikin kujerun falon.       Momy da ganin Abbu yasa fuskarta ta faɗaɗa da fari'a tace.    "Your wellcome Alhajina."    Murmushi Abbu yayi tare da ɗan jinjina mata kai, cikin sakin fuska yace.  "Thank you."      Zama yayi akan kujeran dake facing ɗin ta Maleek,  take kuwa Momy tasa aka cika musu gabansu da kayan ciye ciye dasu drinks,   ƙawayen Momy dake zaune ne sukayi wa Abbu sannu da dawowa, wanda dama dan yi masa sannu da dawowan Momy ta tarasu, kasancewar yaune birthday ɗin Abbu'n shiyasa ta gayyacesu dan suzo sutaya ta murna.               Ko tsinke bai ɗauka daga cikin abun da aka ajiye masa ba, jin surutun ƙawayen Momy na neman Affecting ɗinsa ne, ya sashi miƙewa tsaye ya nufi hanyar fita daga cikin falon.  Da idanu Abbu da Momy suka rakashi, har ya fice daga cikin falon.    Miƙewa Abbu yayi shima ya nufi sama dan yanaso yaɗan huta, take kuwa Momy ta rufa masa baya.              Yana fita daga cikin falon,  kaitsaye compound ɗin gidan ya nufa, inda motarsa ke fake ya ƙarasa, soldiers ɗinsa da ke ta kai kawo acikin gidan nasu, suna ganinsa kowa ya shiga sense ɗinsa, duk suka ƙame awaje ɗaya, buɗe murfin motar yayi ya shiga,  shigansa cikin motar kuwa yayi daidai da tashin cute cat ɗinsa, wanda yake ƙira da sunan  cutie,  itaɗin tazama kamar wata baby ɗinsa ce, dan mafi yawancin lokuta yana tare da ita, yanason cat din tasa sosai, haka itama tayi matuƙar sabo dashi, hayewa saman jikinsa cat ɗin tayi, saman bayanta ya ɗan shafa,  tare da ɗaukan kwalin madararta dake cikin motar ya shiga bata abaki tana sha, time to time yake shafa screen ɗin wayar dake hannunsa, da'alama wani abu me mahimmanci yakeyi. Koda ya gama bawa cutie ɗin nasa madara, soldiers ɗinsa yayiwa alama akan su taho akwai inda zasuje, take kuwa duk suka shiga mota, drivers ɗinsa yaja suka fice daga cikin gidan.                     A Ɓangaren Laylerh kuwa tana barin kitchine ɗin kaitsaye ɗakinta ta wuce, kwanciya tayi akan ɗan gadonta tare da jawo wani text book ta soma karantawa,  ta jima tana karatun bayan tayi sallan azahar ne bacci ɓarawo ya ɗauketa ko tashi daga kan sallayan da tayi sallah batayi ba, ba ita kuwa ta farka ba sai ƙarfe 4. Toilet ta wuce ta sake ɗauro sabon alwala sannan tazo ta tada sallah, bayan ta idar da sallan la'asar ɗinne ta fita zuwa falo, dan ita kwata kwata bata masan Abbun nasu ya dawo ba.         Acikin falon kuwa Abbu ne da Momy zaune suna ɗan taɓa hira,   fitowarta daga cikin ɗakin kuwa, yayi daidai da kai duban Abbu ƙofar ɗakin nata,  ganin Abbu'n ne yasa ta ɗan waro manyan idanunta, cikin zumuɗi da kuma mamakin ganinsa tace.   "Abbu."   Murmushi Abbu Ya sakar mata tare da buɗe mata hannayensa, cikin  kulawa  yace.  "Oyoyo Mamana."   da ɗan sassarfa ta ƙaraso, durƙusawa agabansa tayi, tana murmushi, hannayenta Abbu ya kamo, cike da kulawa yace.  "Ćłan matana anata girma, ya school ɗin dai, hope kina karatu sosai?."         Murmushin daya bayyana zallan kyawunta tayi, cikin ƙaunar Abbu'n tace.   "Ina karatu sosai Abbu, next week ma insha Allah Zamu fara exam ɗin second term."   Kai Abbu ya jinjina tare da cewa.     "Masha Allah, Gaskiya naji daɗin hakan, fatan dai baki da wata matsala a school ɗin naku ko?."    Ɗan murmushi tayi tare da jinjina masa kai,  alaman "Eh." sai alokacin ta ɗago da kai ta kalli Momy wadda ta tsura mata ido,  sauƙe kanta ƙasa tayi tare da soma wasa da Ć´an yatsun hannunta.    Shafa kanta Abbu yayi, tare da cewa.   "Naga result ɗinki na firts time yayi kyau sosai, Allah Ya miki albarka."     da "Ameen" ta amsa, ganin irin kallon da Momy ke mata ne yasa ta miƙewa  tare da cewa.   "Abbu bari naje na haɗa maka apple drinks da jallop rice."    Murmushi Abbu Yayi tare da cewa.  "To Ć´ar gidan Abbu."   Kasancewar dama matuƙar yana gari, itace  meyi masa girki. Kaitsaye kitchine ta wuce, inda ta samu Larai me aikinsu nata aikin ɗaurawa da sauƙewa,    matsawa can gefe tayi, cikin nutsuwa ta shiga haɗa abubuwan da zata buƙata wajen haɗa apple drinks, tana kammala wa kuwa, ta ɗaura masa jallop rice me rai da lafiya.        haka tayita gudanar da aikinta cikin nutsuwa harta kammala, koda ta gama tuni an soma ƙiraye ƙirayen sallan Magriba,  akan dining table ta jera duka abincin da ta girka, har dama wanda Larai ta girka, saida ta gama komai sannan ta wuce ɗakinta, wanka tayi tare da ɗauro alwala,   koda ta fito daga toilet wata jar doguwar riga ƙiran turkish ta saka, wanda yake Abbu'n nata ne ya taɓa kawo mata tsarabar ta, sosai rigan tayi mata kyau, hijab tasanya sannan ta tada sallah.  Koda ta idar da sallahn bata tashi akan sallayan ba saida tayi sallan Isha.         Aɓangaren Maleek kuwa, tun fitansa sai yanzu yake shigowa cikin gidan.      Koda ya shigo kaitsaye part ɗinsa ya wuce, kasancewar yana da abubuwan da zaiyi masu yawa.                        Hijab ɗin dake jikinta ta cire, sannan ta saka wani jan hula akanta, wanda shi ya ƙara bayyana kyawun shigar tata, sanincewa Idan Abbu na gida, doka ne kuma ƙa'ida gaba ɗaya gidan atare suke cin abinci, hakanne yasa ta nufi falo kaitsaye, aikuwa tana zuwa ta samu Abbu da Momy akan dining,  Abbu na ganinta yace.   "Yauwa Laylerh zo maza kiyi serving ɗinmu, dama ke muke jira."    Ɗan murmushi tayi, tare da ƙarasowa, saida tayi serving ɗinsu, sannan taja kujera ta zauna. Abbune ya zaro wayarsa daga aljihu tare da dannawa lambar MALEEK ƙira, wanda fitowarsa daga wanka kenan, ganin ƙiran Abbu ne ya sashi ɗagawa.    "Kazo dining kayi dinner."  Abbu ya faɗa ataƙaice, tare da katse ƙiran.          Jin Abbu ya datse ƙiranne yasa shi cilla wayartasa kan gado, cikin nutsuwa ya cigaba da shirya kansa, wasu irin tarin tunani ne kwance aƙasan zuciyarsa.                          Acan falo kuwa gaba ɗaya Laylerh ta kasa sakewa taci abincin, saboda yanda Momy ke ta jifanta da wani kallo me ɗauke da ma'anoni guda biyu, idan taga Abbu na kallonsu kusa, saita ta ƙoƙari wajen ganin taja Layler'n da hira.                    Shigowansa cikin falon ne yasa gaba ɗaya ko ina na ya gauraye da daddaɗan ƙamshin dake tashi ajikinsa,  hakanne kuwa yasa tun kafun ƙarasowarsa dinning area'n ƙamshinsa yaje musu,     Laylerh da takai loman farko na abinci bakinta, samun kanta tayi da kasa haɗiye abincin, saboda yanda ni'imtaccen ƙamshinsa ya ratsa hancinta. Idanunta ta lumshe tare da jan dogon numfashi, sam bata kawo aranta cewar shi bane, hakan yasa ta ɗago kanta dan ganin daga ina ƙamshin ke fitowa, sauƙe idanunta akansa ne yasa batare da ta shirya ba ta soma ƙoƙatin haɗiye abincin dake bakinta batare da ta tauna ba,  wani irin mummunan ƙwarewa tayi, wanda yasa nan take ta fara tari , Abbu ne yaɗan sa hannu ya bubbuga bayanta, cike da kulawa yace.  "Sorry."  Cup ɗin ruwa ya miƙa mata, karɓa tayi hannunta na rawa takai cup ɗin bakinta, koda tasha ruwan kuwa ta ɗanji dama dama,     kasancewar babu yawan kujeru a dining arean ne yasa dole akujeran dake kusa da na Laylerh ya zauna,  zamansa yayi daidai da sakin ajiyar zuciyarta,    Abbu ne ya dubeta tare da cewa.  "Kiyi serving ɗinsa."    Jitayi kaman ta ruga da gudu, wani irin fitinannen tsoronsa takeji,  ga kuma zamansa akusa da ita, daya sa gaba ɗaya kwarjininsa ya lulluɓeta, hannunta na rawa haka tayi serving ɗinsa, komawa tayi ta zauna tare da ƙurawa plate ɗin abincin dake gabanta idanu.   Duk wannan abun da akeyi, koda sau ɗaya ne Maleek bai ɗago kansa ya kalli kowa ba, wayarsa ce a hannunsa yana dannawa. Har kusan sama da 4 minute. Ahankali ya ɗago kansa tare da jawo plate ɗin abincin gabansa,   cike da nutsuwa ya soma cin abincin nasa, time to time yakan ɗan lumshe sexy eyes ɗinsa. Laylerh kam gaba ɗaya ta kasa sake kai loman abinci bakinta, juya spoon ɗin hannunta kawai takeyi acikin abincin, ahankali bugun zuciyarta ke tsananta,  hakan yasa taji maƙoshinta na ƙoƙarin bushewa, hannunta takai da niyar ɗaukan cup ɗin juice, daidai lokacin kuwa yaɗaura hannunsa dake riƙe da wayarsa akan saman table ɗin, da niyar ajiye wayan nasa, batare da Laylerh ta sani ba ta sauƙe lallausan tafin hannunta akan nasa hannun, wani irin schock sukaji atare su dukansu, ahankali ya lumshe idanunsa,  Laylerh kuwa da sauri ta cire hannunta daga kan nasa, ƙirjinta na bugawa. Ɗan buɗe rikitattun idanunsa yayi, karon farko tun zamansa awajen daya ɗago idanunsa masu ɗaukar hankali ya kalleta, da sauri ta rumtse idanunta, tare da soma motsa laɓɓan bakinta, kalmar "Haƙuri." take ƙoƙarin haɗawa amma takasa. Yanayin yanda take yi da laɓɓanta ne ya sashi sake zuba mata narkakkun idanunsa, ahankali yakai hannunsa daidai saitin fuskarta.   *Vote nd Comment*     *fatymasardauna* 1/19/21, 8:10 PM - Ummi Tandama: 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇                *LAYLERH MALEEK*     *Writting by* Phatymasardauna                    *Wattpad*             @fatymasardauna #Arrogant                 *Chapter 5* Hannunsa ya kai daidai saitin fuskarta, kallon ƙwayar shinkafan dake manne agefen bakinta yayi, haka  yayi kaman zai cire mata  sai kuma ya fasa, tare da saurin ɗauke kansa daga gareta, lokaci ɗaya ya haɗe fuska kaman bai taɓa dariya ba arayuwarsa. Tuno wani abu da yayi ne, ya sashi rumtse idanunsa tare da ɗan cizan jajayen lips ɗinsa,  ahankali ya soma girgiza kansa,  haka yakejin zuciyarsa ba daɗi,  wani irin abune yaji yana yi masa yawo acikin jikinsa. Laylerh kuwa har zuwa yanzu bata buɗe idanunta ba, bugun zuciyarta ne ke ƙara tsananta, yayinda ƙirjinta ke   harbawa da sauri.      Ahankali taɗan buɗe idanunta wanda  cikinsu ya cika da ruwan hawaye, ɓoyayyar ajiyar zuciya ta saki, tare da ƙoƙarin shanye ruwan hawayen nata, dan batajin zata iya barinsu  sukai ga sauƙa akan fuskarta,  ɗan satan kallonsu tayi,  ganin cewa dukkaninsu hankalinsu ba'a wajenta yake ba ne  yasa ta ɗan matsar da kujeranta gefe, wanda hakan yasa ta ɗanyi nesa dashi,  spoon ɗin dake hannunta  tasa tare da ɗiban abincin ta kai bakinta, ahankali take  tauna abincin, dan hakanan taji duk batajin yunwa,  gefe guda kuwa  zuciyarta ne  ke saƙa mata abubuwa da yawa, azahirance  kuwa so take ta ɗan saci kallon gefen da yake, amma kuma kwata kwata tsoro da fargaban da takeji sun hanata.                       Ajiye spoon ɗin dake hannunsa yayi,  tare da miƙewa tsaye, baice da kowannensu ƙala ba, ya juya kai tsaye ya nufi bedroom ɗinsa. Da kallo  Abbu ya bisa  tare da girgiza kai, yasani dama har abada Maleek bazai taɓa sanjawa ba,  tuntuni ya riga daya bari miskilanci da zurfin ciki sun zame masa ɗabi'a,  gashi yanayin aikinsa ya ƙara sanja masa halayya, bazai taɓa faɗin damuwarsa ba komin girmanta, haka zalika koda yaushe fuskarsa babu wadataccen murmushi, then bakomai ke sashi dariya ba, koda kuwa abun yakai na dariya saidai kawai yayi murmushi.  Ajiyar zuciya Abbu ya sauƙe tare da ci gaba dacin abincinsa, dan baisan sai yaushe ne Maleek ɗin zai sanja ba. Tashin da yayi ne yasa Laylerh sakin ɓoyayyar ajiyar zuciya, tabbas yana da kwarjini mai tarin yawa, wanda shi yake sawa duk takejin kanta wata iri, bata da wani ƙwarin guiwa agabansa, ɗan lumshe idanunta tayi tare da haɗiye abincin dake maƙale amaƙoshinta, tashinsa shi ya sa taɗan saki jikinta, da kaɗan kaɗan ta dinga tsakuran abinci tana kaiwa bakinta. Abbu wanda ya kammala cin abincin sa ne ya ɗaura idanunsa akan wayan Maleek, wanda ke aje nan kan saman table ɗin,  sauƙe  idanunsa akan wayan kuwa, yayi  daidai da soma ƙiran wayar da akayi, kallon Laylerh da ke goge bakinta  da tissue Abbu yayi, cikin kulawa yace.    "Laylerh ɗauki wayarsa ki bisa da shi." Jin maganan da Abbun ya faɗa ne, yasa lokaci ɗaya ta fara tari  batare da ta shiryawa hakan ba,  da sauri ta ɗauki ruwa tasha, tare da soma mutsustsuka idanunta, kallon da Abbu yayi mata ne yasa asanyaye ta ɗauki wayar tasa dake ta faman ringing. Miƙewa tsaye tayi tare da barin dining area'n, koda ta ƙarasa cikin falon kaitsaye ta doshi ƙofar da zata sada ta da sashin sa.   Hakanan takejin ƙirjinta na bugawa da ƙarfi, gaba ɗaya jikinta rawa yake, ahanakali ta ɗaura hannunta akan handle ɗin ƙofar, tare da murɗawa ta tura ƙofar ciki,  asanyaye taɗan kutsa kai cikin falon,   takun farko ta jefa ƙafanta akan wani lallausan carpet me taushin gaske,  ga kuma wani irin daddaɗan sanyi me tafiya da ƙamshi daya daki kan fuskarta,  ɗan lumshe idanunta tayi, tare da  maida ƙofar  ta rufe, idanunta ta baza wajen ƙarewa falon nasa kallo,  komai na cikin falon atsare yake, da dukkan alama  mamallakin falon bayason yawan tarkace, domin daga yanayin tsarin falon nasa zaka fahimci haka,  inda aka zuba wasu haɗaɗɗun cushions masu kyaun gaske atsakiyar falon, sai kuma royal blue nd milk curtains da aka saka ajikin kowacce ƙofa da window dake cikin falon, kasancewar kujerun falon nada kalan royal blue shiyasa curtains ɗinma suka kasance royal blue nd milk,  gefe guda kuwa wani jibgegen tv plasma ne, wanda aka ɗaurasa akan wani glass table me kyaun gaske,  gefe da gefensa kuma wasu fararen flowers ne masu kyau,  kallon haɗaɗɗen turkish carfet ɗin dake malale atsakiyan falon tayi, wanda shima kalan royal blue da milk ne, tsarin falon yayi kyau sosai,  ahankali ta shiga takawa har ta ƙaraso tsakiyan falon, ganin bakowa afalon ne yasa ta ɗan ciji lips ɗinta, idanunta ta sauƙe akan wata haɗaɗɗiyar ƙofa dake cikin falon, wanda da dukkan alama kuma ƙofar bedroom ne. Kallon wayartasa dake riƙe ahanunta tana ta faman ringing tayi. Rasa yanda zatayi yasa ahankali ta ƙarasa jikin ƙofar zuciyarta cike da tsoro, ɗan murɗa handle ɗin ƙofar tayi, take kuwa ƙofar ta buɗe, kasancewar dama ba arufeta da kyau ba. Ganin ƙofar ta buɗe ne yasa ta ɗan zaro danunta waje, sam batayi tunanin ƙofar abuɗe take ba shiyasa ta tura, atsorace batare da ta ƙarasa shiga cikin ɗakin ba, da Ć´ar siririyar muryarta tayi sallama. Saidai shiru haka taji, ba ko motsin mutum bare tasa ran za'a amsa mata, sake kwaɗa wani sallaman tayi, still babu amsa. Jin shiru ne yasa tayi tunanin cewa ko baya cikin ɗakin, ajiyar zuciya ta sauƙe tare da ƙarasa shigowa cikin ɗakin. Wani daddaɗan ƙamshin da ya daki hancinta ne, yasa ta kuma  lumshe idanunta tare da jan wani dogon numfashi, tashin farko kenan da taji tana masifar son ƙamshin, dan ko tantama baza tayi ba, wannan ƙamshin shine ƙamshin da taji yana fita ajikinsa. Ɗan buɗe idanunta tayi ahankali,  inda ta sauƙe su akansa. Zaune yake agaban dressing mirror yayinda ya bawa ƙofar shigowa  ɗakin baya, sanye yake da white trouser yayinda ya cire rigar jikinsa ya ajiyeta agefe, yanayin yanda ya juya baya ne yasa gaba ɗaya surar bayansa ta bayyana,  wasu ƙananan hairs ne kwance lub akan white skin ɗinsa, yayinda fatar tasa ke wani irin shining, yanayin yanda ya juya baya ya kuma duƙar da kansa ƙasa shiya sanya ba'a iya ganin me yakeyi, kuma shima ba lallai yasan anshigo ɗakin ba. Idanunta masu kyau ta zubawa fatar bayansa bata ko ƙiftawa, bakomai ya ɗau hankalinta ba kuwa face wani ɗan zanen tattoo wanda akayisa kaman rubutu dake manne a tsakiyan bayansa. Ahankali taɗan lumshe idanunta, tare da budesu alokaci guda, gaba ɗaya ta shagala da kallon zanen dake kwance abayansa, hakanan taji shauƙin taɓa zanen na fusgarta, cikin nutsuwa ta soma takawa zuwa inda yake, wanda har zuwa yanzu bai ɗago kansa ba, baikuma yi wani ƙwaƙƙwaran motsi ba, da'alama dai baisan da shigowanta cikin ɗakin nasa ba. Taku huɗu kacal ya rage mata ta ƙarasa garesa, ƙiran wayansa da aka kumayi ya katseta, wani sabon tsoro ne ya lulluɓeta dan gaba ɗaya tamanta me ya kawota ɗakin nasa, Ɗagowa tayi ta kallesa, still har yanzu baiɗago kansa ba,  murza Ć´an yatsun hannunta ta soma yi ahankali dan batasan ta ina zata fara yi masa magana ba. Akaro na barkatai kenan daya closing very beautyful eyes ɗinsa,  ahankali ya ɗan juyo da kansa, batare daya ɗago ya kalleta ba, ya miƙo mata hannunsa alaman ta bashi wayan. Kamar dama jira take da sauri kuwa ta saka masa wayar atafin hannunsa, saidai tasha mamaki ƙwarai dan batayi tunanin yasan da zuwanta ɗakin ba. Ɗan satan kallon sa tayi, saidai bata iya hango full face ɗinsa, dan bawai ya juyo gareta bane, amma tana iya ganin rabin fuskarsa, da kuma gefen kumatu'nsa wanda ƙawataccen sajen dake wajen ya kwanta lub gwanin ban sha'awa. Juyawa tayi cikin sauri ta nufi hanyar fita daga ɗakin, wajen sauri kuwa har ƙafafunta na harɗewa. Tana fita daga cikin ɗakin ta saki wata ƙatuwar ajiyar zuciya,  ɗan kallon cikin falon nasa tayi, sannan da sauri ta fice. Koda ta fito daga sashin nasa, bata samu kowa anasu part ɗin ba, dan haka kai tsaye ɗakinta ta wuce. MALEEK kuwa yana amsan wayar, picking call ɗin yayi tare da kara wayar akan kunnensa,  har wanda ke kan wayan yagama bayanin da zaiyi baice ƙala ba, yana gama jin bayanin da akeyi masa acikin wayar ya kashe ƙiran tare da cilla wayartasa kan bed, ahankali ya ɗago da kansa tare da lumshe tsumammun idanunsa, numfashi yaɗan fesar sannan ya miƙe tsaye daga zaunen da yake. Tsadadden wrist watch ɗin dake ɗaure ahannunsa ya duba.   9:15 pm daidai, cikin takunsa na isa, da kuma yanayin da ya saba ya ƙarasa jikin haɗaɗɗen gadonsa, hannunsa yakai jikin bango, inda ya kashe hasken wutan ɗakin, bedside lamp Ya kunna, wanda yake bada blue nd pink light, hayewa saman gadon yayi tare da  lumshe idanunsa, gaba ɗaya jin kansa yake agajiye.    LAYLERH. Sake sakin wata sabuwar ajiyar zuciya tayi akaro na barkatai,  ahankali ta matse pillown dake hannunta tare da lumshe idanunta. "Yana da Kyau!."  tafaɗa abayyane batare da ta sani ba, naked skin ɗin bayansa da kuma kwantaccen sajen da ta gani agefen fuskarsa ne keta yiwa idanunta gizo. Sannu ahankali wani baƙon tunani ke shiga yana ratsa cikin ƙwaƙwalwarta, wanda asanadinsa ne zuciyarta ta shiga bugawa da ƙarfi,  saurin sanya hannayenta duka biyu tayi ta toshe kunnenta tare da rumtse idanunta. Ahankali ta shiga ambatan sunan Allah, dan sosai zuciyarta ke bugawa, wani abu ne keyi  mata yawo acikin kai da zuciyarta,  take wani irin masifaffen kewar iyayenta ya rufeta, duk da kasancewar bata gama sanin daɗinsu agareta ba, alokacin da ta rasasu, amma tabbas ayanzu tana da buƙatarsu acikin rayuwarta,  idanunta da suke alumshe ne suka ciko da ƙwalla, ahankali ta soma sakin shashsheƙan kuka. Tabbas har yanzu ita yarinyace, sannan  kuma tana da buƙatar me rarrashinta alokacin da take kuka,  rayuwarta cike take da kewa, akwai abubuwa da yawa wanda hankali da tunaninta bazasu iya ɗauka ba, haƙiƙa bakomai zata iya jurewa ba amatsayinta na mace me ƙananan shekaru, gaba ɗaya rayuwarta fata ce da kuma gurbi, wanda batasan yaushe ne zasu cika ba. Cusa kanta acikin pillow tayi tana me ci gaba da sakin shashsheƙan kuka ahaka har bacci ɓarawo ya ɗauketa. ASALIN LAYLERH MALEEK.                      Alhaji Uthman NAI'EB  dattijo ne me dattako da kuma kyawun hali, sannan mutum ne da sunansa ke yawo aciki da wajen Nigeria kasancewarsa babban ɗan kasuwa, kuma gwani awajen iya kasuwanci,  duk da kasancewarsa ba asalin ɗan Nigeria ba,  amma kuma yayi ƙaurin suna aƙasar, dama  kuma garuruwan dake cikin ƙasar, Alhaji Uthman Nai'eb cikekken balaraben EgĆ´pt ne, inda yakasance nanne ƙasarsa, kuma anan kowa da kowa nasa suke, saidai mahaifiyarsa Oum Khaltoum wacce  ta kasance ba cikakkiyar Ć´ar ƙasar Egypt ɗin ba,  wanda ita haifaffiyar Ć´ar Nigeria ce, Hakanne yasa da Allah Yayiwa mahaifinsa rasuwa ta tattaro ta dawo Nigeria, kasancewar shi kaɗaine ɗan da ta haifa aduniya, shiya sanya ya kasa zama anan Egypt ɗin ya biyo mahaifiyarsa Nigeria,  inda suka sauƙa acikin garin meduguri, wanda kuma nanne asalin garin mahaifiyartasa, kasancewarta shuwa arab, mace me kyaun gaske, shiyasa aure ya kaita har ƙasar Egypt.  Anan meduguri  suka ci gaba da rayuwarsu, inda ya kammala karatunsa anan cikin Nigeria, koda ya gama karatun nasa amaimakon ya fara aikin gomnati, sai ya fara kasuwancin saye da sayarwa,  wanda  dama tuncan hakan shine sana'an mahaifinsa, tasanadiyar hakan kuwa yabar masa tarin arziki me yawan gaske.    Cikin hukuncin Allah Kuwa sana'an kasuwanci ta karɓesa sosai, lokaci ɗaya ya fara zama wani hamshaƙin me arziki,  gashi yana da nasibi sosai, dukkan abun daya taɓa da yardan Allah Sai yayi albarka, hakanne yasa mutanen Nigeria wanda ya saba dasu suka saka masa suna GWANI, acewarsu bakomai ya sa shi haɓaka har haka ba illa Gwanancewa aharkan kasuwanci, uwa uba kuma yanda sunansa keta yawo acikin ƙasashe da dama, sannu sannu ya tara wata irin dukiya me tarin yawa, wanda shi kansa baisan iya adadinta ba, ganin bashi da niyar kawo zancen aure ne, yasa mahaifiyarsa wato Oum Khaltoum, ta kawo masa zancen aure, nuna cewar bashi da wacce yake so ne, yasa da kanta ta zaɓa masa wata galleliyar mace, wanda suke dangi da ita, itama shuwa arab ɗince, cikin lokaci ƙanƙani akayi bikin Alhaji Uthman NAI'EB  GWANI da matarsa Rauda. Alhamdulillahi ko da akayi biki Alhaji Uthsman Nai'eb zaman lafiya sukeyi sosai da matarsa Rauda, dan ta kasance mace me tsananin biyayya agareshi,  haka suke gudanar da rayuwarsu cikin jin daɗi da soyayya, saidai har zuwa yanzu Allah baibasu haihuwa ba, ahaka har suka shekara ɗaya, suna cika shekaransu da ɗan watanni kuwa Allah Yabawa Rauda ciki,  farin ciki da jin dadi ba'a magana awajen family'n, haka suka dinga tarairayan cikin har Allah Ya sauƙeta lafiya, inda ta haifo ɗanta Namiji me kama da babansa sak, sunyi murna sosai, ranan suna yaro yaci sunan Muhammad Jaheed,  haka rayuwa ta miƙa musu inda Jaheed nada shekara 2 Rauda tasake haihuwan Ɗa namiji, wanda aka sawa sunan AbdoulKareem. Shaƙuwane sosai atsakanin iyaye da Ć´aĆ´an nasu, AbdoulKareem nada shekara uku Rauda ta sake haihuwan ɗa Namiji wanda aka sawa suna Mahmoud Rai'eb.    Tun daga kan Mahmoud Rai'eb kuwa Rauda bata sake haihuwa ba, haka Ć´aĆ´an nata suka taso cikin so da ƙaunar juna da kuma haɗin kai. Haka Rayuwa taci gaba musu cikin jin daɗi,  sam basusan wani abu waishi talauci  ko ƙuncin rayuwa ba, saboda yanda mahaifinsu ke tashen kuɗi.   Lokacin da girma yazo musu ne kowa aka turasa karatu ƙasar daya fi so, Inda aka tura Muhammad Jaheed karatu ƙasar America, shi kuma AbdoulKareem Anan Nigeria yace yakeson yin karatunsa, yayinda Mahmoud Nai'eb ya tafi ƙasar Egypt, inda yake zaune da Ć´an uwansa kana kuma yana tafiyar da karatunsa yanda ya kamata. Akwana atashi rayuwa nata miƙawa haka ma shekaru, acikin kwanakin da suka shuɗe kuwa abubuwa da yawa sun faru, ciki kuwa harda rasuwan Oum Khaltoum, ƙwarai sunyi jimamin mutuwarta sosai.  Kasancewar Muhammad Jaheed shine babba acikin ĆłaĆ´an Rauda hakan yasa shiya fara kammala karatunsa, wanda zuwa yanzu kuma mahaifinsu girma ya kamashi, dole ya sakarwa ɗansa Muhammad Jaheed ragaman komai na kasuwancinsa, ya kuwa yi sa'a Muhammae Jaheed ɗin nada sha'awan kasuwanci, Alhamdulillahi kuwa dan komai natafiyawa Muhammad Jaheed yanda ya kamata, kasancewarsa ba mutum me sha'awar zaman Nigeria ba hakan yasa shi komawa ƙasar Dubai da kasuwancinsa, domin yana da costomers masu yawa acan,   ashe kuwa acan arzikinsa mafi yawa yake, dan dazuwansa Dubai bajimawa yatara wasu irin maƙudan dukiya me tarin yawa. Daga ɓangaren AbdoulKareem kuwa shima yagama karatunsa, dama ɓangaren Accounting yakaranta, yana gama karatunsa kuwa ya kama aikin banki. Mahmoud Nai'eb  kuwa gaba ɗaya rayuwarsa a Egypt yakeyinta, inda yamaida hankali akan karatunsa. Acan Dubai kuwa dukiya ta zaunawa Muhammad Jaheed sosai, sannan ya maida ƙasar tamkar nanne mahaifansa, dan har companies yake dasu aƙasar,  kasancewarsa jinin larabawa hakan yasa ya ɓata acikinsu, dan dukansu al'ada da ɗabi'arsu iri ɗaya ne.    Ahaka ne kuma watarana ya haɗu da wata mace ɗaya da ta sace zuciyarsa, wacce take itama Balarabiya ce Ć´ar asalin ƙasar Oman, bakomai ya ja hankalin Muhammad Jaheed zuwa gareta ba kuwa face baiwar kyau da Allah Ya mata, tabbas Abdiyya kyakkyawace sosai dan ko acikin larabawa kyawunta dabanne, ahaka dai ya isar da kansa gareta, dafari taso ƙin amincewa amma daya kai kansa wajen iyayenta sun amince dashi, take kuwa ya sanar da iyayensa, sunyi murna kwarai  saidai Oum Rauda bahaka taso ba, taso ace Ć´ar Nigeria ya aura, amma babu yanda ta iya ganin yanason Abdiyya yasa ta bari ya aureta. Anan cikin Dubai suka zauna shida matar tasa, inda suke gudanar da tsabtatacciyar soyayyarsu, gaba ɗaya duk wani son duniya Muhammad Jaheed ya ɗaura shine akan Abdiyya. Auren Jaheed nada wata 8 AbdoulKareem ma yayi aure,  inda ya auri wata cikakkiyar bafullatanan Yola me suna AISHA,  sosai kuwa Oum Rauda taji daɗin hakan, dan dama burinta ne ɗaya daga cikin Ć´aĆ´anta su auri Ć´ar Nigeria. Rayuwa me dadi ahalin suke gudanarwa,  Muhammad Jaheed da Abdiyya soyayyarsu sukeyi sosai, tun da sukayi aure kuwa sau ɗaya tak Abdiyya tazo Nigeria,  yanzu shekaransu 3 kenan da aure amma Allah baibasu haihuwa ba, aɓangaren AbdoulKareem ma hakane har zuwa yanzu matarsa Aisha bata da ciki. Cikin ikon Allah Kuwa shekarun Muhammad Jaheed huɗu da aure, Allah ya azurtasu da samun ciki, sosai sukayi murna da farinciki, haka Muhammad Jaheed ya dinga kashewa Abdiyya kuɗi masu tarin yawa dan kulawa da cikin nasu. Cikin ikon Allah Cikin nata nada wata 10 cib cib ta haifo zankaɗeɗen yaronta namiji, kyakkyawan gaske, wanda zuwansa duniya yazo musu da alkhairai masu tarin yawa,  yayinda duk wanda yazo kallon yaro sai ya tafi yana faɗin "Masha Allah."  saboda yanda Allah yayiwa yaron baiwar kyau, ranan suna yaro yaci sunan ABOUL MALEEK, tabbas kuwa anyi shagali sosai awannan rana. Wani irin tsantsar so Muhammad Jaheed da kuma Abdiyya ke nunawa ɗansu MALEEK duk wata soyayyar duniya sun ɗaurasa ne akansa, saidai yanayin tasowan Maleek da kuma hali da ɗabi'unsa yasauya musu tunani, dan tun yana da shekara 4 suka fuskanci cewa yana da halin miskilanci sosai, gashi babu ruwansa da kowa, ko irin wasan da yara keyi shi bayayi, lokacin daya fara magana ne kuma yasoma kiran mahaifiyarsa da Oum Abdiyya, mahaifinsa kuwa yake ƙiransa da Abbu Jaheed, haka zalika kama daga kan Abdoul Kareem har Mahmoud Nai'eb Abbu yake ce musu.  Ahaka dai rayuwa ta miƙa Maleek nada shakara 8 Abbu Mahmoud Nai'eb yayi aure anan ƙasar ta Egypt, inda ya auri Sofiyya kyakkyawar mace me tashen kyau da wayewa, wacce take kuma matsayin Ć´ar uwa agaresa,  bayan anyi bikin nasu, anan Egypt ɗin sukaci gaba da zama, dan anan yake aikinsa, kasancewar ya jima da zama babban doctor aƙasar Egypt ɗin. Ɓangaren Abbu Kareem kuwa har zuwa yanzu Allah Baibashi haihuwa ba, wanda kuma matsalan daga ɓangaren matarsa Aisha yake, sam kuma baidamu da hakan ba, dan yayi imani cewa haihuwa da rashinta duk na Allah Ne, dan kuma bata haihuba hakan bazai sashi ƙara aure ba. Abbu Jaheed kuwa tundaga kan Maleek basu sake haihuwa ba,  wani zuwa Dubai dasu Abbu Mahmoud da Sofiyya sukayi ne, shaƙuwa me ƙarfi ta shiga tsakanin Sofiyya da Maleek lokacin ma Sofiyya na ɗauke da ɗan ƙaramin ciki, koda suka zo tafiya maƙalewa Sofiyya Maleek yayi acewarsa zai bita harsai ta haifa masa ƙanwa kafun ya dawo. Kasancewar yana zuwa school shiyasa su Oum Abdiyya basu amince ba, dan alokacin ma exam sukeyi kuma suma basason yayi nesa dasu. Haka su Sofiyya suka dawo suka ci gaba da rainon cikinsu cikin ƙaunar juna. Lokacin da cikin Sofiyya yakai haihuwa,  Abbu Mahmoud ɗaukan ta yayi suka wuce Saudiya, cikin ikon Allah kuwa aƙarshen watan Ramadan ta haihu, daren wani jumma'a inda ta haifo kyakkyawar Ć´arta mace me tsananin kama da ita, duk da kasancewar Sofiyya kyakkyawar macece ta gaske, amma kuma duk kyawunta sai babyn nata da ta haifa tazo ta zarta ta kyau, ranan suna yarinya taci sunan AYSHA inda aka yanke za'ana ƙiranta da (Laylerh). Lokacin da aka haifi Laylerh kuwa Maleek nada 14 years dan har anturasa karatu U.S.A wato (United State Of America). Haka dai rayuwar tasu ta cigaba, Laylerh nada shekara 1, Oum Rauda wato mahaifiyarsu Abbu Jaheed, da kuma Abbu Uthman Nai'eb wato mahaifinsu sukayi accident wanda shine sanadi Allah Ya ɗauki rayuwarsu, al'amarin daya girgiza Abbu Jaheed da kuma Abbu Kareem da Mahmoud kenan, take suka tattara kan iyalinsu suka taho Nigeria, sunyi kuka sosai na rasuwar mahaifan nasu. Bayan kuma anyi sadakan bakwai ne suka tattara kowa ya koma ƙasar da yake. Haka suke ta gudanar da rayuwarsu, gaba ɗaya duk farincikinsu ya ragu, rashin iyayen nasu ya sanyaya musu jiki ƙwarai. Ɓangaren Maleek kuwa gaba ɗaya rayuwarsa ta koma America, karatu yakeyi sosai, game da halin miskilancinsa kuwa sai abun daya ƙaru. Laylerh kuwa yanzu shekarunta 7, daga kanta kuma Sofiyya bata sake haihuwa ba. Wata ranan jumma'a ranan da ahalin bazasu taɓa mantawa dashi ba, shine Sofiyya ta tashi da ciwon kai, kafun safiya zuwa yamma kuwa Allah ya ɗauki rayuwarta. Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un, tabbas Abbu Mahmoud ya shiga tashin hankali, dan yaji rasuwar Sofiyya fiye da duk tunanin me tunani, dan har saida yayi kaman ya zauce. Babu wanda yakejin tausayi kuwa aduniya face Ć´arsa Laylerh, duk kuwa da ƙanƙantan shekaru irin na Laylerh saida tayi kukan rashin mahaifiyarta. Ranan da akayi kwana 7 da rasuwan Sofiyya ne Oum Abdiyya tazo ta ɗauki Laylerh ta maida ita gabanta,   akuma lokacin ne Maleek yazo hutu Dubai. Haka rayuwar Laylerh ta ci gaba da tafiya agaban Oum Abdiyya. Hutun 2 weeks kawai Maleek yayi ya koma, inda Laylerh kuma taci gaba da rayuwarta anan Dubai. Shekarun Laylerh 9 Abbu Mahmoud  ya shirya musu tafiya Umra dukansu, har zuwa lokacin kuwa baisake wani aure ba, dan acewarsa bazai sake samun mace irin Sofiyya ba. Koda lokacin tafiyan nasu Umra yayi, Laylerh bata samu zuwa ba, saboda alokacinne suka fara exam na first time amakarantarsu, haka ɓangaren Abbu Jaheed ma baisamu zuwa ba, saboda wani uzuri daya tafi yi America, hakanne yasa Abbu Mahmoud da Oum Abdiyya ne kaɗai suka samu zuwa, Abbu Kareem kuwa dama yanacan Nigeria, danshi sam baya ganewa zaman ƙasashen waje. Koda sukaje sunyi Umra'n su lafiya, kuma suna saran dacewa,  ranan da suka ɗauko hanyan dawowa Dubai ne jirgin da suke ciki yayi hatsari, inda gaba ɗayansu suka rasa ransu sandiyan haɗarin. Mutuwarsu baƙaramin girgiza su Abbu Jaheed yayi ba, musamman Maleek, dan sosai yake son mahaifiyar sa fiye da komai, sunyi kuka sosai babu ma kaman Abbu Jaheed wanda rashin Sofiyya ya ɗaiɗaita tunaninsa, haka ma Laylerh duk da kasancewar tana da ƙarancin shekaru amma rasuwar Mahaifinta da kuma na Oum Abdiyya ya girgizata matuƙa, dan ayanzu tazamanto bata da kowa, dan gaba ɗaya dangin mahaifiyarta nacan ƙasar Egypt, kuma dama mahaifiyar tata bawasu dangi take dasu masu yawa ba, kasancewar mahaifiyar tata ita kaɗaice awajen iyayenta,  kuma ko a ɓangaren dangin uba ma family dinsu basu da yawa, dan basu wani cika yawan haihuwa ba shiyasa zuri'ar tasu basu da yawa. Bayan rasuwan Oum Abdiyya da Abbu Mahmoud, Abbu Jaheed yaji gaba ɗaya zaman ƙasashen waje ya ishesa, haka nan hankalinsa ya dawo Nigeria, haka ya ɗauko Laylerh suka dawo Nigeria, bayan yasa angina masa katafaren gida acikin garin Abuja,  Maleek kan dama yana can America. Dawowansu Nigeria ne kusan da shekara biyu Abbu Jaheed ya sakeyin aure, domin ya lura zaman Laylerh agabansa haka babu wata mace me riƙonta bazaiyi wuba. Hajiya Suwaiba, wato (Momy) itace matar da Abbu Jaheed ya aura, Hajiya Suwaiba irin wayayyun matan nan ne kuma Ć´ar boko, sannan babanta wani hamshaƙin me kuɗine anan Nigeria,  sannan tana da kyau daidai gwargwado, aɓangaren zamantakewa kuwa kwata kwata batason Laylerh, badon komai ba kuwa saidan kulawan da taga Abbu Jaheed na bawa Laylerh'n, atunaninta tunda Laylerh'n ba Ć´arsa bace, bai dace ace yana bata kulawa har haka ba, wannan dalilin yasa kwata kwata bata sakewa Laylerh, shiyasa gaba ɗaya rayuwar Laylerh tataso cikin kaɗaici, domin har acikin zuciyarta tsoron Momyn takeyi. Maleek kuwa tunda suka dawo Nigeria baizo ba, har saida sukayi shekara 3 sannan yazo. Duk yanda Momy taso yasake da ita yaƙi, dan babu abun dake shiga tsakaninta dashi idan ba gaisuwa ba, baya magana kwata kwata, miskiline na ƙarshe, wannan dalilin yasa Momy take jin shakkansa, saidai wani abu da ta lura dashi agame da Maleek ɗin shine, ko da wasa baya ƙaunar koda ƙuda me cutarwa ne ya sauƙa akan Laylerh, wannan dalili yasa tadaina tsawatarwa Laylerh idan yana nan. Gashi kuma tunda sukayi aure da Abbu Jaheed Allah baibasu haihuwa ba. Abbu Kareem kuwa ya koma England da zama acan yake gudanar da komai nasa har yanzu kuwa Allah bai bashi haihuwa ba. Tun dawowansu Nigeria kwata kwata sau biyu Maleek yazo, yamaida gaba ɗaya rayuwarsa America, acan yayi degree da kuma Masters nd PHD ɗinsa, bayan ya kammala ne ya dawo Nigeria, zama soldier shine babban burinsa, hakanne yasa koda ya kammala karatunsa America suka nemi da yayi aiki dasu inda suka nuna zasu basa babban matsayi saboda yanda yake da ƙwazo, saidai kasancewarsa me ra'ayi yasa shi ƙin amincewa, yana dawowa Nigeria kuwa dakansa ya nemi aiki'n soldier kuma ya samu, inda ayanzu yake matsayin Captain, saboda shiɗin ƙwararre ne sosai, dan ko lokacin dayake America shiyake horar da ɗalibai. Shekara 2 yayi a Nigeria yasake komawa U.S.A, haka ya share shekaru acan, still kuma yana gudanar da aikinsa na Nigeria duk da baya ƙasar, saidai yana da wakilan da sukeyi masa komai koda baya nan. Zuwa yanzu kuwa Laylerh nada shekara 17 inda take S.S 1,  ɓangaren rayuwarta da Momy kuwa ba abun  daya sauya, dan har yanzu Momy bata nuna mata ƙauna, saidai idan Abbu Jaheed nanan tana ɗan sakewa da ita. Wannan shine Asalin tarihin LAYLERH MALEEK. Cigaban Labari. 2:00 am Duk sanyin A/C'n dake tashi acikin ɗakin, bai hana murɗaɗɗiyar surar jikinsa fidda gumi ba,  ahankali yake ɗan jujjuya kansa,  dagani kasan baccin da yake bayayi masa dadi, acikin baccin nasa ne kuwa ya samu kansa cikin wata duniya ta daban, wanda ke neman juya masa tunani, duk da cewa hakan ba baƙon yanayi bane awajensa amma bayajin zai iya jurewa. Ahankali ya buɗe kyawawan idanunsa wanda suka sauya kala daga  farare zuwa ja. Hannunsa yakai daidai kan mararsa tare da ɗan lumshe idanunsa, wani irin fitinannen feeling yakeji na taso masa. Idan da sabo ya kamata ace ya saba da yanayinsa, shi kansa baisan wani irin mutum bane shi, saidai yayi imani cewa yawan jin feeling acikin jininsa yake.   *(Kuyi haƙuri kwana da yawa kunjini shiru, banajin daɗi ne shiyasa kuma phone ɗina ma batajin daɗi 😓, amma yanzu insha Allah Zakuna jina akai akai.)* *Vote nd Comment*     *fatymasardauna*  1/19/21, 8:10 PM - Ummi Tandama: 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇     *LAYLERH MALEEK*     *Writting By* Phatymasardauna                 *Wattpad*         @fatymasardauna #fanfiction                    *Chapter 6* Ahankali ya zuro da ƙafafunsa ƙasa daga kan gadon, ɗan cije red lips ɗinsa yayi, saboda yanda yakeji ajikinsa duk ba daɗi, bayajin idan baisha magani ba zai ji relief daga abun da yakeji, musamman ma ayanzu da yake jin mararsa nayi masa ciwo. Miƙewa tsaye yayi,  cikin nutsuwa ya ƙarasa gaban wata Ć´ar ƙaramar drawer dake cikin ɗakin, murfin drawer'n ya buɗe tare da  ciro wasu  tablets, hannunsa na rawa ya ɓalli maganin  tare da watsa su abakinsa,  ahankali ya ƙarasa gaban fridge ɗin dake cikin ɗakin, tare da  buɗewa ya ɗauko bootle water marar sanyi,  ɓalle murfin gorar yayi tare da kafa bakin goran akan soft lips ɗinsa,  sai alokacin ya haɗiye maganin dake bakinsa, asanyaye ya lumshe idanunsa tare da sakin ajiyar zuciya, shi kansa baisan wani irin mutum bane shi, always yana cikin feeling, abun tun baya damunsa har zuwa yanzu ya fara damunsa. Komawa saman bed  yayi ya kwanta, ahankali yake ta faman sauƙe ajiyar zuciya, sannu ahankali yakejin feeling ɗin na sauƙa, yayinda gaba ɗaya jikinsa ke samun relief,  shiru yayi tare da ƙurawa zanen dake saman ɗakin nasa ido, abubuwa da yawa yake saƙawa acikin zuciyarsa, ahaka  in 15 minute bacci ya ɗaukesa.  Ɓangaren Laylerh kuwa dama tajima dayin bacci, saidai acikin baccin nata ne ta dinga mafarkai iri iri, kamar yanda ta saba akowani dare saitayi mafarkin wani na musamman, wani wanda take ganin babu irinsa,  wanda kuma bai taɓa bata dama taga  cikakkiyar fuskarsa ba,, saidai ako da yaushe tana cikin aminta cewar  kyawawan idanun da keyi mata gizo mallakinsa ne, wani abun mamakin kuwa shine amafarkin nata na yau ba iya Mr.Beautyful eyes ɗin nata bane yazo kamar yanda ta saka masa suna,  abayansa wani take gani wanda shima bai bata daman ganin full face dinsa ba, wani ne ya kutso cikin mafarkin nata wanda yake neman shiga wani babi na rayuwarta,  zuwan sa ne kuma yasa mr.beautyful eyes ɗinta ke neman rufe mata kyawawan idanunsa. Aɗan razane ta farka daga nannauyan baccin daya ɗauketa, hakanan taji zuciyarta na bugawa, mafarkin nata ne yashiga dawowa cikin kanta filla filla, wani irin yanayi da tasamu kanta aciki me wuyar fassaruwa ne, yasa ta tashi ta nufi toilet alwala ta ɗauro sannan ta dawo ta sakeyin addu'a ta kwanta. Wani irin sabon fargaba ne ke neman lulluɓe zuciyarta, hakanan taji tasamu kanta cikin wani ƙaton rauni, pillow'n dake hannunta ta rungume, so take tayi kuka amma kukan yaƙi zuwa, yanda zuciyarta ke bugawa yasa sunan Ya M.Jay ke yawo acikin ƙwaƙwalwarta. Ahaka dai saida ta ɗauki sama da 20 minute kafun bacci ɓarawo ya kuma ɗaukarta. Washegari.             6am daidai ta tashi daga bacci, tana buɗe idanunta kuwa mafarkin ta na jiya ya shiga dawowa kanta,  kanta taɗan soma girgizawa tare da rumtse idanunta, sam batason sake tuna mafarkin, saboda tunasa yanasawa taji zuciyarta ta zama very weak sannan tanaji ajikinta cewa tanason yin kuka. Cikin sauri tatashi daga kan gadon, agurguje tawuce toilet alwala tayi sannan tazo ta gabatar da sallan asuba. Koda ta idar da sallan zama tayi tare da ɗaukan Alƙur'ani ta soma karantawa, sanin da tayi cewa idan Abbu Jaheed na gida tana da driver me kaita makaranta. Suratul Anbiya ta karanta sannan ta rufe Alƙur'anin. Miƙewa tsaye tayi, cikin nutsuwa tasoma gyara ɗakinta, tana kammalawa kuwa ta  shige toilet, wanka tayi sannan ta fito ɗaure  da towel ajikinta. Ƙarasawa gaban ɗan madaidaicin drawer'nta tayi, Ć´ar ƙaramar jakar da Hajiya Asma'u ta bata ta ɗauko, tare da ciro wani body lotion, wanda yake ɗaya daga cikin kayayyakin da Hajia Asma'un ta bata,  anan kan gado ta zauna cikin nutsuwa ta soma shafa lotion cream ɗin ajikinta, tana kammalawa kuwa ta ƙarasa gaban mirror, normal powder ta murza akan fuskar ta, sannan taɗan shafawa jajayen lips ɗinta white lip gloss,  daga haka kuwa ko kwalli batasa acikin idanunta ba ballantana kuma mascara, hakanan ta saba bata da yawan kwalliya, koda yaushe haka take zama fuskarta ba kwalliya, wasu lokutan kuwa haka take zuwa skull ɗin ma ko powder bata shafawa akan fuskar ta. Anutse ta sanya kayan uniform ɗin ta, yayinda ta haɗa dogon gashinta daya cunkushe waje ɗaya,  saboda rashin saloon ta ɗaure. Ɗan ƙaramin hijab ɗin skull ɗin nata tasa, tare da ɗaukan  jibgegiyar school bag ɗinta ta goya, kallon agogo tayi  7 am daidai, wanda hakan ke nuna mata cewa kenan tana da sauran 30 minute daya rage mata, ƙarasawa jikin ƙofar ɗakin tayi tare da murɗa handle ɗin  ƙofar ta fice.      Abbu Jaheed ne ke zaune acikin katafaren falo'n nasu, yayinda  Momy  ke zaune agefensa tana haɗa masa coffee, sosai Momyn  tasha ado cikin wani swiss yard me kyau,  tun tuni dama ita gwanar ado ce.   Ƙarasowanta cikin falon ne yasa Abbu Jaheed sakin murmushi cikin kulawa yace.    "Laylerh har lokacin tafiya school ɗin yayi ne?."           Murmushin daya bayyana asalin cute face ɗinta tayi, tare da jinjina masa kai cikin sanyi ta ce.  "Abbu barka da safiya."    Kansa ya ɗan  jinjina alaman "Yauwa."      Ɗan satan kallon Momy tayi haɗe da cewa.   "Barka da sapia Momy."     "Yauwa barka." Momy ta amsa mata ataƙaice.                Abbu Jaheed ne ya miƙe tsaye tare da kamo hannun Laylerh'n cikin kulawa yace.  "Zo muje kiyi break fast  kada ki makara."                  Ba musu ta miƙe tsaye, haka suka ƙarasa gaban dining area'n Abbu Jaheed na riƙe da hannunta.     Ɗaya daga cikin kujerun dining ɗin taja ta zauna, daidai lokacin  Larai ta fito daga kitchine hannayenta ɗauke da manyan food flask,  anan kan dining table ɗin ta jere food flask ɗin.  Zama Abbu Jaheed yayi tare da cewa Laylerh tayi seving ɗinsu.      Momy dake zaune afalo kuwa gaba ɗaya duk ranta ya ɓaci, sam batason irin kulawar da Abbu Jaheed ke bawa Laylerh, sanin cewa babu yanda zatayi ne yasa ta ɗauke kanta daga garesu.     Laylerh kuwa saida tayi seving ɗin Abbu, sannan itama tayi seving ɗin kanta. Agurguje taci chips da ƙwai ɗin, sannan ta ɗaura tea akai,  ganin zatayi latti ne yasa ta miƙe tsaye.  Abbu Jaheed dake cin abinci ne ya ɗago kai ya kalleta, cikin kulawa yace "Allah ya bada sa'a, kije Bala driver na jiranki awaje."    Kai ta jinjina  tare da cewa. "Ameen Abbu." cikin sauri ta ɗau school bag ɗinta ta fice daga cikin falon, kaman yanda Abbu ya faɗa mata  kuwa tana fita ta taradda Bala driver na jiranta. Wani irin sanyi taji acikin ranta, saboda kafun yanzun harta fara tausayin kanta na tafiyan da zatayi.   Cikin sauri sauri ta shiga motar Bala driver yaja suka fice daga cikin gidan.                             11:00am. Ahankali ya ke ware idanunsa wanda sukayi jajur dasu, hannu yasa yaɗan dafe kansa dake  sarawa kaɗan kaɗan, hakanan gaba ɗaya duk bayajin ƙarfi ajikinsa, wanda  hakan kuma  baya rasa nasaba da ƙarfin maganin daya sha daren jiya, wanda ko sallan asuba ma da ƙyar ya iya tashi yayi.        Cije jajayen laɓɓansa yayi, cikin ɗan kuzarin daya saura masa ya sauƙo daga kan gadon. Kaitsaye ya nufi toilet, tun daga bakin toilet ɗin ya soma rage kayan dake jikinsa, saida ya zama naked sannan ya  ƙarasa gaban shower,  hannunsa  yasa ya kunna makunnin shower'n, take ruwa ya soma sauƙa ajikinsa, ahankali yaɗan lumshe idanunsa yana mejin sanyin ruwan na ratsa duk jikinsa, wanda hakanne kuma yasa shi ɗan jin relief. Sama da 15 minute yana tsaye ruwa na dukan jikinsa, ahaka dai yayi wanka. Koda ya fito daga  toilet ɗin, towel ne ɗaure a waist ɗinsa,  gaba ɗaya jikinsa ɗauke yake da danshin ruwa, yayinda lafiyayyar suman kansa ta kwanta tayi lub, itama ahankali take ɗan ɗigar da ruwa. Wani mini towel ya ɗauka wanda dashi ya goge kai da kuma jikinsa,  kasancewar yana da yalwar gashi sosai akansa,  hakan ne yasa dole saida yayi amfani da handryer wajen sake busar da gashin kannasa.   Yana kammalawa ya shafa wani fitinannen body lotion me ƙamshin gaske ajikinsa, tare da feshe jikinsa da body spray.  Ƙarasawa gaban drawer ɗinsa wanda ke cike da kaya yayi,  ɓangaren ƙananan kayansa ya buɗe ya ciro riga da wandon track suit masu masifar kyau da tsada, koda ya sanya kayan ajikinsa ba ƙaramin kyau sukayi masa ba, haɗuwansa da kwarjininsa sun sake bayyana, gashin kansa kuwa sai shining yake domin yasha mayuka kala kala   Wasu white sneaker shoe ya sanya aƙafansa,  sannan ya ɗauki wayarsa da kuma wata black bag ya fice daga cikin ɗakin.                    Koda ya fito babban falon gidan nasu bakowa aciki,  kaitsaye compound ɗin gidan ya nufa.  Soldiers ɗinsa dake zazzaune acikin compound ɗin gidan, suna ganinsa gaba ɗayansu suka mimmiƙe, tare da ƙamewa awaje ɗaya,   ɗaya daga cikin soldiers ɗin nasa ne ya tafi cikin hanzari ya buɗewa Maleek ɗin murfin motar da zai shiga,  sauran soldiers ɗin ne suka soma ƙoƙarin rufa masa baya, hannu ya ɗaga musu batare daya kalli ɗaya daga cikinsu ba ya girgiza musu kai,  alaman baya buƙatar rakiyansu, gane abun da yake nufi ne yasa su komawa suka tsatstsaya. Bayan ya shiga cikin motar ya zauna ne,  ya ɗago kansa tare da duban  Abdul. (Abdul ɗaya daga cikin soldiers ɗinsa ne wanda  kuma shine driver'nsa.)   Cikin yanayin maganansa da baisaba yinta cikin walwala ba yace.     "Idan ka ajiyeni kabiya ta restaurant kayi muku takeaway."   Cikin girmamawa Abdul yace.  "Okay sir."        Baisake cewa komai ba ya maida hankalinsa kan wayarsa ƙiran iphone 12 pro dake riƙe ahannunsa.  Abdul kuwa shiga motar yayi tare da murza mata key,  gate man ne ya buɗe musu gate suka fice daga cikin gidan.                Kaitsaye  hotel ɗin transcop hilton  suka nufa. Koda suka ƙarasa wajen da ake parking cars, cikin isa ya buɗe murfin motar ya fito, batare da ya saurari Abdul daya fito dan buɗe masa motar ba,  kaitsaye ya nufi sashin da zai sadasa da babban ɗakin gym ɗin dake cikin hotel ɗin, kasancewar  privet section yayi register hakan yasa wajen babu yalwan hayaniya, hasali ma koda ya shiga ɗakin yin gym ɗin babu kowa.   Rigar dake jikinsa ya cire, cikin nutsuwa ya soma sana'ar tasa ta motsa jiki, wanda ya maidashi ɗabi'arsa, domin babu ranan da za'a wayi gari matuƙar da lafiyansa baiyi gym ba, hakanne yasa duk jikinsa ya mummurɗe.  Ganin ogan nasu yafara gym ne yasa   Abdul komawa mota,  tunowa da umarnin me gidan nasa ne ya sashi wucewa restaurant kaitsaye.          Ɓangaren Laylerh kuwa yau tun da taje skull bata samu nutsuwa ba saida suka kammala Biology test ɗin da zasuyi.              Teemah dake amatuƙar gajiye ne ta ɗan kwanto jikin Laylerh'n, akasalance tace.  "Wallahi Laylerh nagaji gashi yunwa nakeji  sosai."          Hararanta Laylerh tayi tare da cewa.   "Nima ae nagaji, bacci ma nakeji." Laylerh tayi  maganan tana ɗan lumshe idanunta.      Da sauri Teema ta ɗago daga jikinta, cikin zumuɗi tace. "Yauwa kin tunamin kinsan mafarkin me nayi  jiya kuwa?."      kai Laylerh ta girgiza alaman "A'a"       Murmushi Teemah tayi tare dayin fari da idanunta, cikin son nuna shauƙin abun da  takeji tace.   "Mafarkin Mr.Soldier nayi."          Idanu Laylerh taɗan zaro cike da mamaki tace.   "Mr.Soldier? wani Mr.Soldier?."           Hararan wasa Teemah ta watsa mata, cikin ƙaunar abun da takeson faɗi ta gyara zama, tare da ɗan rufe fuskarta tace.   "Mr. Soldier na wa kika sani?, idan nace Mr.Soldier kema kinsan Mr.Soldier ɗin gidanku nake nufi."        Idanu Laylerh ta zaro cike da matsanancin mamaki tace.   "Kina nufin YA M.J?."          kai teemah ta jinjina tare da cewa "Eh shi, duk da bantaɓa ganinsa ba amma inajin wani abu agame dashi Laylerh, sau ɗaya kawai dana ga pics ɗinsa afalon ku Allah Laylerh inasonshi, yana burgeni sosai, ban taɓa ganin wani mutum irinsa ba, ya haɗu Laylerh cute handsome ne bana wasa ba, please yaushe zai zo?"  Ta ƙare maganar tana me rolling idanunta.             Wahalallen saliva ɗin daya tsaya mata  amaƙoshi ta haɗiye, ahankali taɗan lumshe idanunta, akullum akuma ko da yaushe, Teemah na yawan yi mata sambatu akan Ya M.J, koda sau ɗaya ne kuwa bata taɓa jin hakan acikin jikinta ba sai yau.         Jin tayi shiru ne yasa Teemah dafa shoulder ɗinta, cike dason jin bayani akan Mr.Soldier man  ɗinta tace "Why kikayi shiru?."     Buɗe idanunta  tayi tare da sauƙesu akan Teemah, kallon cikin idanun Teemah'n tayi sannan ta sunkuyar da kanta ƙasa, tabbas yau ta hango wani abu acikin idanun Teemah, wanda yasanya taji wani abu me kama da  fargaba naneman kamata, wanda ita kanta batasan dalilin hakan ba.           Still ganin tayi shiru yasa  Teemah   kamo hannunta, batare da ta lura da yanayin da take ciki ba tace "Zo muje muyi sallan la'asar naga lokaci yayi, kuma anata fita no need mu zauna a class."   bata iya cewa komai ba sai bin bayan Teemah'n tayi suka fita daga cikin class ɗin.                Kaitsaye inda aka tanada donyin awala suka nufa, Ita tafarayin alwala sannan Teemah ma tayi.    Gefen masallaci suka nufa, wajen da aka tanadawa matan skull ɗin  musamman danyin sallah, atare sukayi sallan bayan sun idar da sallan ne suka koma class.    Ƙarfe 5 daidai aka tashesu, suna fitowa daga cikin school ɗin suka tarar da Bala driver har yazo ɗaukan Laylerh.  Murmushi Teemah tayi tare da cewa. "Lallai hakan alamace dake nuna cewa Abbu ya dawo."  Murmushi Laylerh tayi tare da jinjinawa Teemah kae, alaman "Eh" idanu Teemah taɗan kashe mata sannan sukayi murmushi,   saida Teemah taga tafiyarsu kafun driver ɗinta yazo itama ya ɗauketa.      Jin sunyi nisa da tafiyane yasa ta kwantar da jikinta ajikin kujeran motar, ahankali taɗan lumshe idanunta tare da sakin ajiyar zuciya.    Kalaman da Teemah ta faɗa mata ne suka shiga dawowa cikin kanta filla filla, hakanan taji gaba ɗaya duniyar ta daina yi mata daɗi, batasan me yasa ba sai tanajin kaman kalaman Teemah'n naneman ruguza mata wani abu daga cikin rayuwarta, wanda ita kanta batasan ko menene shi ba, zoben dake Ć´ar yatsar hannunta ta soma murzawa, ahankali takejin wani irin sanyi me dadi na ratsa jikinta,  sake lafewa ajikin kujeran motar tayi tana sakin numfashi ahankali,  idanunta da suke alumshe ne suka fara yi mata gizon kyawawan idanunsa wanda suka zamo wasu abu daga sashin zuciyarta, saboda ganinsu cikin yanayin gizo yana sama mata nutsuwa, wani irin baƙon yanayi wanda bata taɓa jin irinsa ba ne yasoma ziyartar ta, mafarkinta na jiya ne ke ƙoƙarin dawo mata, sam kuma batason hakan.  Jin an takawa motar tasu birki ne yasa tayi saurin buɗe idanunta, ga mamakinta sai gani tayi sun iso gida.   Jikinta asanyaye ta buɗe murfin motar ta fito,  idanunta ne suka sauƙa akan wasu sabin cars guda biyu dake fake atsakiyan gidan, ɗan kau da kanta gefe tayi tare da sake maƙala bag ɗinta akafaɗarta. Batakawo tunanin komai ba kaitsaye ta nufi babban falon  gidan...              Acan cikin falon kuwa  Abbu Jaheed ne zaune shida babban amininsa Alhaji Ahmad Rufa'e, wanda ya kawo masa ziyara tundaga garin Kaduna,  gefensu kuwa Momy ce ke ta faman ɗawainiya dasu sai kawo musu drinks da snacks take.     Zaune yake akusa da mahaifinsa, inda yake sanye cikin riga da wando na wani tsadadden yadi me kalan milk, duk da kasancewar yana da haske amma hakan bai hana yadin yi masa kyau ba, fari matashin saurayi ne wanda aƙalla bazai haurawa  shekaru 30 ba, da dukkan alama kuma jikinsa na tafiya daidai da shekarunsa, kaitsaye idan ka gansa zaka ƙirasa da  kyakkyawa, dan babu laifi shima yana da nasa salon kyau'n, sannan kuma kai tsaye ga wanda ya iya nazarin halayyan mutum idan ya gansa zai iyayi masa kallon me abubuwa guda uku, nafarko bashi da yawan sakewa, sannan kuma bashi da tsumewa, abu naƙarshe dayafi kowanne shine kallo ɗaya kawai zaka masa kafahimci cewa yana da nagarta. NAJEEB AHMAD RUFA'E kenan matashin saurayin dayakeji da ƙuruciyarsa, wayarsa ƙiran Samsung galaxy fold 2 ne ahannunsa yana ta faman latsawa, yayinda Abbu da Alhaji Ahmad Rufa'e keta faman tattaunawa akan harkan kasuwancinsu.          Cikin nutsuwa ta turo ƙofar falon ta shigo bakinta ɗauke da sallama, zaƙin muryarta da kuma sanyinta shiya sanya Najeeb ɗago kansa tare da sauƙe idanunsa akanta. (Sorry awajen sa matsayin ajin karatun Laylerh nasa SS 1, typing error ne SS 2 zansa, then my wattpadians gaskia kuna min rowan vote da comment, karku manta da comment da vote ɗinku kaɗai nakesamun confidence, my whatsapp people kuma fa kunamin rowan comment🙄) *Vote nd Comment*       *Fatymasardauna* 1/19/21, 8:10 PM - Ummi Tandama: 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇      *LAYLERH MALEEK*   *Writting By* Phatymasardauna                             *Wattpad*                    @fatymasardauna #Fantasy *Chapter 7* Sauƙe idanunsa da yayi akanta ne yasa duk tsikar jikinsa mimmiƙewa, take yaji wani sabon yanayi ya ziyarcesa, numfashi ya fesar tare da soma yawo da idanunsa akanta baya ko ƙiftawa. Ɗago ɗara ɗaran kyawawan Idanunta tayi, wanda hakanne ya bawa eye balls ɗinta daman sauƙa acikin nasa idanun. Wani irin faɗuwar gaba ne ya ziyarceta, cikin sauri ta janye idanunta tare dayin ƙasa da kanta, hakanan taji duk tazama wata iri. Ahankali tasake yin ƙasa da idanunta, tare da kawar da kanta gefe. Cikin yanayin sanyi ta ƙarasa shigowa cikin falon, tare daɗan durƙusawa cikin sassanyar muryarta tace. "Abbu barka da yamma." Murmushi Abbu yayi tare da cewa. "Yauwa Laylerh ya school ɗin?." ɗan murmushi tayi ahankali ta ce. "Alhamdulillah." Idanunta ta ɗaga tare da ɗan kallon Alhaji Ahmad Rufa'e wanda tun shigowanta fari'ar dake kwance akan fuskarsa ta ƙaru. Cikin yanayin ta na nutsuwa tace. "Ina yini." Sake faɗaɗa fari'ar dake kwance akan fuskarsa yayi, murya asake yace. "Lafiya ƙalau Laylerh ya karatu, ana nan anata fama ko?." Kai ta jinjina masa alaman "Eh." still har yanzu fuskarta ɗauke yake da murmushi. Kallon Abbu Alhaji Ahmad Rufa'e yayi cikin yanayin jin daɗi yace. "Masha Allah Alhaji Jaheed Laylerh ta girma, wancan zuwan nawa fa tana Ć´ar ƙarama da ita, dan in ban manta ba lokacin shekarunta 11 ko." Murmushi Abbu yayi, tare da jinjina masa kai, cikin dattako yace. "Ae kasan girman Ć´a mace babu wuya." Shiɗin ma Alhaji Ahmad Rufa'e'n murmushi yayi, dan tabbas ko maganan da Abbun ya faɗa haka ne. Laylerh da duk taji ta kura ɗan muskutawa kaɗan tayi, tare da sakeyin ƙasa da idanunta, hakanan takejin wani iri ajikinta, gashi jikinta na bata cewar ana kallonta. Najeeb ajiyar zuciya ya sauƙe tare da ɗan lumshe idanunsa, wanda tun shigowarta suke aikin kallonta basa ko lumshewa, hakanan yaji wani diffrent feeling akan yarinyar, duk da kasancewar tana da ƙananun shekaru, amma ya lura tana da abubuwan burgewa da yawa ajikinta, sosai kuma ya karanci yanayinta, cikin zuciyarsa yake maimaita sunan da yaji Abbu ya ƙirata dashi wato "LAYLERH". "Nice name." Ya faɗa batare daya bari sautin muryarsa ta fito fili ba, saidai laɓɓansa da suka ɗan motsa, baisan meya saba har yanzu ya kasa ɗauke idanunsa akanta. Bazata iya jure zaman wajen ba, musamman yanda taji tsikar jikinta na zubawa, miƙewa tsaye tayi domin ayanzu ba abun da takeso kaman ganinta aɗakinta, dan ko tantama batayi, kasancewar taji ajikinta cewa ana kallonta. Ganin Laylerh'n ta miƙe tsaye ne yasa Abbu cewa. "Laylerh baki ga Yayanki Najeeb bane? kigaishe sa mana." Jin Maganan da Abbu ya faɗa ne yasa akaro na biyu ta ɗago kyawawan idanunta ta kalleshi, kasancewar tun ɗazu idanunsa akanta yake, shiyasa idanunsu suka faɗa cikin na juna, saurin sadda kanta ƙasa tayi tare da kama Ć´an yatsun hannunta ta shiga murzawa, cikin muryarta dake cracking tace. "Ina yini." Akaron farko kenan daya janye idanunsa daga gareta, cikin son samawa kansa nutsuwa yace. "Lafiya." Jin sauƙar muryarsa acikin kunnuwanta ne yasanya ta sake ɗago kai ta kalleshi, wani abu da ta tuna ne yasa ta ɗauke idanunta daga kansa, tare da miƙewa tsaye cikin yanayin nutsuwarta ta nufi ɗakinta, kasancewar ta ɗebo gajiya amakaranta shiyasa takejin kanta nayi mata ciwo kaɗan kaɗan. Ta gefen idanunsa yabita da kallo,har ta shige wani ɗan corridor dake cikin falon, wanda anan cikin corridor ɗin ɗakinta yake, ganin ya daina ganinta ne yasa shi ɗauke kansa daga kallon hanyar da tabi. Alhaji Ahmad Rufa'e ne ya kalli Abbu cikin sakin fuska yace. "Tabbas Alhaji Jaheed nakusa samun suruka, masha Allah fatan dai baka manta da alƙwarin dake tsakanin mu ba." Cikin son ƙarfafawa aminin nasa guiwa Abbu Jaheed yace. "Tayaya zan manta da alƙwari me girma irin wannan, hakan ma bazata faru ba, kuma Insha Allah ina meyi maka albishir da cewa kafun ka koma Polland zan cika maka wannan alƙawarin naka dana ɗauka, dan ni kaina nafiso ayi komai agabanka." Murmushin jin daɗi Alhaji Ahmad yayi tare da cewa. "Alhamdulillah lallai zanji daɗin hakan kuwa." Murmushi Abbu Jaheed yayi, sannan suka ci gaba da hirarsu. Laylerh kuwa kaitsaye ɗakinta ta wuce, tana shiga ta turo ƙofar ɗakin nata tare da murza handle ɗin, school bag ɗin dake rataye akan kafaɗanta ta ajiye, tare da cire hijab ɗin dake jikinta. Anan kan ɗan madaidaicin gadonta ta zauna, tare da sakin ajiyar zuciya, ahankali ta ɗan lumshe idanunta, wanda suka ɗanyi ja saboda gajiya da kuma stress. Kallon da Najeeb keyi mata me ɗauke da ma'anoni kala kala ne ya dawo cikin mind ɗinta, da sauri ta buɗe idanunta tare da turo ɗan ƙaramin bakinta gaba, ashagwaɓe tace. "Ko waye shi ma oho, har da zaiyita wani kallona?." Ƙwafa tayi tare da soma ƙoƙarin watsar da tunaninsa acikin kanta, tashi tayi cikin nutsuwa ta soma ƙoƙarin cire uniform ɗin jikinta. Koda ta kammala cire uniform ɗin wani baby pink towel ta ɗaura ajikinta wanda ko cinyoyinta basu kai ga rufewa ba, kaitsaye ta wuce toilet dan sosai takejin kanta na sarawa, tun safe kuwa takejin mararta aɗan ɗaure, ruwan zafi ta haɗa dashi tayi wanka sannan ta ɗauro alwala. Koda ta fito daga cikin toilet ɗin, tsane jikinta tayi, tare da shafa wani body lotion ajikin ta, haka take bata dason yawan kwalliya, shi yasa ko powder bata shafa akan fuskarta ba, ƙarasawa gaban sif ɗin kayanta tayi tare da buɗewa, kayan cikin drawer'n ta zubawa ido kamar wacce ke na zartan wani abu, ɓangaren dogin rigunanta ta kalla, wanda kusan ma sune sukafi yawa acikin kayan nata, kasancewar tafison abayas, and kimono fiye da kowani kaya, wata blue ɗin abaya me adon manyan duwatsu wanda ke haɗe da ɗan gyalensa ta ciro, rigace me kyaun gaske dan ƙirar turkish abaya ce. Anutse ta zura rigar ajikinta, baƙaramin kyau kuwa rigar tayi mata ba, dan ta bayyana ɗan madaidaicin shape ɗin jikinta wanda kullum ƙara fitowa yake, bama kamar hips ɗinta wanda suke ta ƙara faɗi da kuma buɗewa, wanda kuma hakan na da nasaba da girma da take ƙarawa ako wacce rana, dogon gashinta daya nannaɗe ta tubke waje ɗaya, tare da ɗaura vail ɗin abayan akanta, jin yanda mararta ke ƙara murɗawa ne yasa ta zauna akan bedside drawer, ahankali taɗan rumtse idanunta tare da ɗaura hannunta akan mararta, wanda asannu sannu ciwon ke ƙaruwa, abubuwa da yawa take saƙawa azuciyarta, daga gefe guda kuwa zuciyarta na neman gangarawa wani sashi ne na daban, wanda hakan ne ke ƙara jefa tunaninta cikin rauni, batason ko menene ke shirin faruwa da ita ba, saidai wani lokaci tunaninta yakan tafiya ne da kowani ƙwayan bugun zuciyarta. Jin ciwon marar na sake nuƙurƙusanta ne yasa ta sake rumtse idanunta, tare da cije jajayen laɓɓanta, jin bazata iya jure zaman bane yasa ta tashi daga kan bedside ɗin, nan kan saman gadonta ta kwanta, tare da jawo blanket ta rufa ajikinta. 6:40 pm dai-dai. Baƙar motarsa ƙiran Toyota Avalon, bugun 2020 ta danno kai cikin farfajiyar gidan, awannan karon baya tare da soldiers ɗinsa, hasalima shi da kansa yake driving motar. Ganin motarsa ta kutso kai cikin gidan ne yasa soldiers din dake compound ɗin gidan shiga taitayinsu, inda duk suka ƙame awaje ɗaya. Daga yanayin yanda yake tuƙin motar kaɗai zaka gane irin yanda yake cike da isa, kuma komai nasa yana yinsa ne acikin nutsuwa, kasancewarsa bashi da yawan hayani ya. Atsakiyar compound ɗin gidan yayi parking motar, wanda ya ɗauki sama da 7 minute bai fito daga cikin motar ba. Sanin yagama daidaita parking ɗin motar ne ya sashi ɗauke hannunsa akan steering motar, ɗan jingina bayansa da jikin kujeran motar yayi, tare da fesar da iska ta bakinsa, cute cat ɗinsa me kalan milk dake kwance akan kujeran ɓangaren me zaman banza ne tayi saurin hayewa jikinsa, ɗagota yayi tare da ɗan soma shafa gashin bayanta, yanason cutie ɗin nasa, wanda sanadin haka ne tayi matuƙar sabo dashi. Madaranta ya ɗauko anutse ya soma bata abaki har sai da ta ƙoshi, gane ta ƙoshi ne yasa shi ɗaurata akan shoulder ɗinsa, anutse ya buɗe murfin motar ya fito. Ganin fitowarsa daga cikin motar ne yasa soldiers ɗinsa soma sara masa, kasancewar haka suka sabayi masa ako da yaushe. Abdul ne ya taho da sauri cikin takunsu na isassun maza wanda idan sunayi sai ƙasa ta amsa, da dukkan alama sun samu horo me tsanani awajen ogan nasu, dan duk wani soja dake cikin gidan daka kallesa, zaka san ba ragon namiji bane, da alama duka sojojin nasa horarru kuma ƙwararru ne, dan dukansu tsayayyu ne, kana kuma matasa masu jini ajika. "Well come back Sir." Abdul da ƙarasowarsa kenan yafaɗa cikin yanayin girmamawa. Kansa ya jinjina alaman "Yauwa." Tare da ɗan juyowa yayiwa Abbul ɗin kallo me alamar magana, shiɗin ma Abdul kallonsa yayi, gane abun da kallon Ogan nasa ke nufi yasa cikin sauri yace. "Yess Sir nayi mana takeaway ɗin lunch harma dana dinner." Jin haka yasa batare daya sake cewa komai ba, ya nufi babban ginin benen dake tsakiyar compound ɗin gidan, wanda kuma nanne zai sadashi da babban falon gidan har izuwa sashinsa da ƙofar shigansa ke cikin falon. Ahankali ya murɗa handle ɗin ƙofar falon ya shiga, zuwa lokacin babu kowa acikin falon dansu Abbu sun tafi masallaci yin sallah'n Magriba da ta Isha, Larai ce kaɗai ke tsaye akan dining area tana shirya dinner, yayinda ta kusan cike saman babban table ɗin cin abincin, dan girke girken da akayi yau ɗin na musamman ne, an girka abinci kala daban daban sunkai 7 banda drinks ɗin sha da aka haɗa kala daban daban, wanda kuma hakan duk aikin Larai da sauran kukus ɗin gidan ne, dan aƙalla suna da kukus sunkai 5 agidan, amma duk da hakan baya hana Laylerh aikatuwa, dan watarana Momy hana kukus din komai take, tace Laylerh ce zatayi, to yaudai Allah Ya samawa Laylerh lafiya daga yin aikin gidan. Kaitsaye ƙofar part ɗinsa ya nufa. Ćłan yatsun hannunsa yakai jikin wata na'ura dake jikin ƙofar tasa, na'urar na ɗaukan hoton Ć´an yatsunsa ƙofar ta buɗe, tura ƙofar yayi ya shiga ciki, yana shiga kuwa ƙofar da kanta ta kulle. Ƙarasawa tsakiyar falon yayi, tare da ɗaura hannunsa akan schoulder ɗinsa, kamo cutie ɗin nasa wanda ta fara bacci yayi, anan kan lallausan carpet ɗin dake malale atsakiyar falon ya ajiyeta, sannan ya nufi bedroom ɗinsa. Yana shiga cikin ɗakin kuwa ya soma ƙoƙarin rage kayan jikinsa, rigar t-shirt na Calvin Clain Jeans ɗin dake jikinsa ya cire, aɗan ƙagauce ya cire takalmin sopport ɗin dake ƙafansa. Zama yayi akan wata haɗaɗɗiyar cushion dake cikin ɗakin. Dan lumshe idanunsa yayi, yayinda ahankali yakejin kasala na sauƙar masa, jingina bayansa da jikin kujeran yayi, tare da sakin ajiyar zuciya, hakanan yau ɗin yakejin yanayinsa duk ba daɗi, hannunsa yasa ya dafe daidai saitin zuciyarsa dake beating, wanda cikinta ke cike da fata haɗi da muradi da kuma burin samun abun da takeso, tabbas zuciyarsa cike take da muradi, wanda yayi imani cewa ƙaddara na kewaye da wannan muradin nasa, mafarkin da yayi adaren jiya ne yasoma dawowa cikin kansa filla filla, hakan kuwa shiya sanyashi buɗe idanunsa, tare da tashi tsaye kaitsaye ya nufi toilet, sam bayason maimaita tunanin mafarkin nasa because mafarkin kaman abune marar tushe awajensa. Ruwan shower me sanyi ya sakarwa kansa, ba tare da ya bari ruwan ya jima yana dukansa ba yayi wanka haɗe da ɗauro alwalan sallan Isha. Koda ya fito daga wankan da wani farin towel ya tsane jikinsa, sama sama ya shafa men body lotion ajikinsa, wasu riga da wandon crazy jeans masu kyau yasaka, wanda suka sake bayyana hasken fatarsa, kasancewarsa mai son ƙamshi sosai, wannan yasa ako da yaushe baya barin jikinsa ba ƙamshi, hakan ne kuwa yasa koda bai shafa turare ba jikinsa ƙamshi yake. Wata haɗaɗɗiyar lallausan darduma ya ɗauka haɗi da wayarsa wanda keta faman ringing ganin ƙiran bawani me mahimmanci bane yasashi ƙin ɗagawa, darduman na riƙe ahannunsa haka ya fito daga part ɗinsa ya nufi masallaci. Ɓangaren Laylerh kuwa jin ciwon marar nata ya ɗan lafa ne yasa ta tashi tayi sallan magriba, koda ta sallame sallan bata tashi ba saida tayi sallan Isha, ɗan muskutawa gefe tayi tare da kwantar da kanta ajikin gado, azkar take amma gaba ɗaya tunani da hankalinta sun tafi zuwa wani waje daban, daga jiya zuwa yau wani irin fitinannen baƙon yanayi takesamun kanta aciki, babu wani minti da zai wuce batare da tayi tunaninsa ba, haka zalika ko wani bugun zuciyarta ɗaya da tunaninsa yake tafiya, haka takeji kaman ana zana mata tunaninsa acikin jininta, wani abu na musamman takeji akansa, wanda kuma hakanne kesawa taji zuciyarta na ƙoƙarin bayyanar da rauninta, batasani ba, bata kuma san meyasa tunaninsa ke sawa taji kaman tayi kuka ba, haka takeji ajikinta tanason kasancewa dashi, ayanzu ba abun da takeson shaƙa kaman ƙamshin sa, wani irin fitinannen feeling takeji akansa. Samun kanta da tayi cikin shauƙin tunaninsa ne yasa ta sake matse jikinta waje ɗaya, tare da lumshe kyawawan idanunta. Kusan atare suka shigo cikin gidan su dukansu, Najeeb wanda shiya fara ganin Maleek ɗin, murmushi ne ya faɗaɗa akan fuskarsa, cikin sakewa ya miƙawa Maleek hannu alaman su gaisa, akaron farko kenan tun wayewar gari zuwa yanzu da ya ɗan saki murmushi akan fuskarsa, wanda shima iya kansa kan laɓɓan bakinsa, hannu ya miƙawa Najeeb ɗin suka gaisa. Alhaji Ahmad Rufa'e ne ya fafaɗa fari'arsa tare da ɗan bubbuga kafaɗan Maleek ɗin cikin kulawa yace. "Wellcome back son, i hope kadawo nan Nigeria da zama?." Ɗan murmushi yayi wanda ya bayyana tsantsar kyaunsa, cikin husky voice ɗinsa yace. "Haka nake tunani." Murmushi dukansu sukayi, cikin jin dadi Abbu da Alhaji Ahmad Rufa'e sukace. "Allah yasa." Abbu ne ya dubi Maleek ɗin cikin kulawa yace. "M.J ga Najeeb ina fatan zamanka a America baisa kamantashi ba." Ɗan kallon Najeeb ɗin yayi, wanda shima kallonsa yake, batare da ya ce komai ba ya jinjina kai, alaman bai mantashi ba. Ɗauke kansa yayi gefe tare daɗan lumshe idanunsa, wanda hakan ya zame masa sabo kuma ɗabi'a. Najeeb kuwa ƙurawa M.J ɗin idanu yayi, hakanan yaji wani abu aransa game da Maleek ɗin, saidai atake yakau da tunanin dake ransa. Kusan atare duk suka shiga cikin falon, Momy dake zaune tana ganinsu ta saki murmushi, cikin kulawa da son karrama baƙin nasu tace. "Sannunku da dawowa, kusan mintuna 15 kenan da dinner ke jiranku a dinning." Murmushi Abbu yayi, tare da kai dubansa ga Maleek wanda ke ƙoƙarin nufar sashinsa. "Maleek." Abbu yaƙira sunansa. Tsayawa da tafiyan yayi tare da ɗan juyowa ya kalli Abbu'n nashi. Shima Abbun kallonsa yayi. Tabbas shi mutum ne me saurin fahimta, sometimes ma yafi fahimtar magana ta ido, fiye da yanda mutum zai furta, wannan yasa ko awajen horar da ɗalibai yakan sa su koyan yanda zasuyi magana da idanunsu, haka kuma idan aka musu magana da ido zasu fahimta, yakan gane abun dake zuciyar mutum daga yanayin kallon da mutum ɗin keyi masa, gane abun da Abbu ke nufi ne ya sashi fasa shiga side din nasa. Ƙarasawa dining area din sukayi, wanda tuni anriga da an ƙara yawan kujerun waje, sabanin da da kujeru 4 ne awajen. Zama sukayi dukansu, yayinda Momy ta shiga ƙoƙarin seving ɗinsu. Abbu ne ya ɗago kai tare da duban Momy cikin kulawa yace. "Kisa aƙiramin Laylerh?." Wani baƙin cikine ya tokare maƙoshin ta, sam batason kulawan da Abbu ke bawa Laylerh,Batare da ranta yaso ba ta ƙira ɗaya daga cikin masu aikin gidan, tace da ita taje ta ƙira Laylerh. Cikin sauri kuwa haka me aikin nasu ta tafi dan cika umarnin Momy'n. Laylerh da har yanzu ke zaune akan sallaya ta lumshe idanunta tare da dafe saman mararta dake murɗawa, jin ana knocking ƙofar ɗakin nata ne yasa ta bude idanunta, tare da juyawa ta zubawa ƙofar idanu, still knocking ƙofar da aka cigaba da yine, yasa ta miƙewa tsaye, duk da cewar tanajin ciwo amararta amma haka ta cije. Ƙarasawa jikin ƙofar ɗakin tayi tare da buɗewa. "Kizo in ji Hajiya." Me aikin tafaɗa tana me kafe Laylerh'n da idanu. Kai Laylerh ta jinjina alaman. "To." sanin halin Momy yasa batare da ta koma cikin ɗakin nata ba ta fito, yayinda ta ware ɗan kwalin dake kanta taɗan yafa zuwa wuyanta, duk dama dai vail ɗin dashi gwamma babu dan yana showing sosae. Tana ƙarasowa cikin falon, takai dubanta kan dining area'n, take kuwa idanunta suka sauƙa akan faffaɗan bayansa, kasancewar zaman da yayi ya bawa cikin falon baya ne, wani irin fitinannen sanyi ne taji na shiga jikinta, tare da ratsa tafin ƙafanta, yayinda hancinta ya shiga zuƙo mata daddaɗan ƙamshin turarensa. Ƙasa tayi da kanta tare da ƙarasowa dining area ɗin. Najeeb da tun shigowanta cikin falon ya zuba mata idanunsa, har zuwa yanzu kuwa bai ɗauke kallonsa daga gareta ba, baisan me yasa ba hakanan yake samun kansa dason kallonta, wani abu na musamman yakeji adangane da ita. Cikin sanyi taja kujera ta zauna, ɗan ɗago da kanta tayi, bisa tsautsayi idanunta suka faɗa cikin na Najeeb dake jifanta da kallo me ɗauke da ma'anoni daban daban, sauƙe idanunta ƙasa tayi, tare da sauƙesu akan yatsun hannun Maleek dake ɗaure bisa saman table ɗin cin abincin. Ƙurawa kyawawan fararen yatsun nasa idanu tayi wanda suke ɗauke da shining nails, yatsarsa ta tsakiya ta ƙurawa ido wanda ke sanye da wani haɗaɗɗen shining ring, ajikin ring ɗin an rubuta A.M da manyan baƙi. Kallon ring ɗin dake hannunta tayi da kyau, sam basu da maraba da wanda ke hannunsa saidai ita harufan da aka rubuta akan nata L.M ne nashi kuma A.M, ɗan jim tayi tare da murza zoben nata, duk da ita kanta batasan da ya akayi zoben ya shiga hannunta ba amma tanason zoben sosai, dan bata taɓa mantawa watarana tun tana ƙarama, ta kwanta bacci koda ta tashi sai gani tayi an sanya mata zobe aɗaya daga cikin yatsun hannunta, tun daga wannan lokacin kuwa bata taɓa cire zoben daga hannunta ba. So take taɗan saci kallonsa amma nauyin hakan takeji. Ganin duk sun fara cin abincinne yasa ta ɗauki plate tayi seving kanta. Duk yanda taso cin abincin nata ta kasa, domin hakanan takejin kallon da Najeeb keyi mata duk ya takurata, gefe guda kuma ga ciwon marar ta da ya tsananta, rumtse idanunta tayi tare da ɗan karyar da wuyanta gefe, ciwo mararta keyi sosae. Najeeb ne ya tsaida cin abincin da yakeyi tare da zuba mata ido, dan ya karanci cewa akwai abun dake damunta. "Laylerh!." Yaƙira sunanta cikin wata silent voice. Laylerh da ayanzu ciwon nata yakaita maƙura har ta kai ga idanunta sun kaɗa sunyi ja, ahankali ta ɗago da kanta ta kallesa. Idanunsa yaɗan zaro waje ganin yanda idanunta suka sauya launi ne yasa cikin kulawa yace. "Are you okay?." Samun kanta tayi da kasa tanka masa, lokaci ɗaya wasu hawaye suka kwaranyo daga cikin idanunta. Wanda Sauƙan hawayen nata yayi daidai da ɗago kai da Maleek yayi, wanda tun zuwanta bai ɗago kansa daga abun da yakeyi ba. Ganin hawaye a idanunta ne ya sashi janye idanunsa daga kanta, asanyaye ya ɗan lumshe idanunsa. *( Menene fata da burin dake cikin zuciyar Laylerh da Maleek? Idan ƙundin Ƙaddaransu ahaɗe take dana juna, me kuke tunanin zai faru anan gaba idan Najeeb ya shigo cikin rayuwar Laylerh? Tabbas akwai wata soyayya me tsananin zafi da taɓa zuciya agaba, kada ku manta tun afarko na faɗa muku cewa wannan salon na dabanne, haka zalika LAYLERH MALEEK daban yake da sauran labarai da kuka sani, kar ku manta yanzu akafara wasan. sannan kuyi haƙuri jia kunjini shiru nayi typing ne ya goge shiyasa, kuma typing akwai wahala sosai😪)* *Vote nd Comment* *fatymasardauna* 1/19/21, 8:10 PM - Ummi Tandama: 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇        *LAYLERH MALEEK*      *Writting By* Phatymasardauna                     *Wattpad*              @fatymasardauna #hausanovels                    *Chapter 8* Idanu Najeeb ya zuba mata ganin yanda take ta mutsu mutsu, ga kuma hawaye still na sauƙa akan fuskarta, ganin yanda take taune lips ɗinta ne yasa shi jin wani iri ajikinsa, asanyaye ya sake ƙiran sunanta, akaro na biyuk enan.                    Kasa amsa masa tayi saima rumtse idanunta da tayi, tare da cizan laɓɓanta, asanyaye ta sa hannu ta share hawayen dake kwance akan fuskarta, jin bazata iya jurewa bane yasa ta ɗaura kanta akan table ɗin cin abincin, sosai marar nata ke ci gaba da  murɗawa, ahankali ta soma sakin sheshsheƙan kuka, tare da dafe saman marar nata da hannunta.          Tashin sautin sheshsheƙan kukanta ne yasa hankalin su Abbu Jaheed dawowa kanta, cikin kulawa haɗe da nuna tsantsar damuwa Abbu Jaheed yace.  "Subahanallah Laylerh lafiya meke damunki?." Yayi maganar cikin yanayi na ɗan ruɗewa.                   Jin muryar Abbu ne yasa kukan nata ƙaruwa, cikin  sheshsheƙan kuka tace.  "Abbu mara na zai faɗo ƙasa, ciwo nakeji sosai."           Cikin tausayawa, Abbu da  Alhaji Ahmad suka haɗa baki wajen faɗin.  "Subahanallah!."       Ɗan jim Abbu Jaheed yayi, take kuma tunanin ƙiran Doctor ya zo masa, waya ya zaro daga cikin aljihunsa, cikin yanayin damuwa yace. "Bari naƙira Dr.Yazo ya dubaki."          Baisaurari komae ba yayi dialing number'n Dr.Ishaq. Bugu biyu kacal Dr. Ishaq  ɗin ya ɗaga, bayan sun gaisane Abbu  yayi masa bayanin abun dake faruwa,  kasancewar sa family doctor ɗinsu, yasa take yace gashinan zuwa.                 Jin hakanne yasa Abbu ya aje wayar, kallon Laylerh'n ya kuma yi wanda har yanzu ke aikin kuka, yayinda ta duƙunƙune jikinta waje ɗaya da dukkan alama ciwon marar ne ke wahalar da ita.        Cikin tausayinta Abbun yace.    "Sannu ko Laylerh, yanzu Dr. zai zo ya dubaki, am sorry jeki ɗaki ki kwanta kafun Dr. Ishaq ɗin yazo."                  Jin abun da Abbun ya faɗa ne yasa ta ɗan jan kujeran da take kai baya, cike da son daure ciwon da takeji ta miƙe tsaye,  tashin ta tsaye kuwa yayi daidai da wani irin murɗawa da mararta yayi, wanda hakan yasa ta rumtse idanunta da ƙarfi, tare da sakin wata Ć´ar ƙara, take jiri ya kwasheta, hakan yasa tatafi luuu zata faɗi, cikin azama Najeeb yasa hannu ya tarota ta faɗa jikinsa.  Daidai lokacin  kuwa Maleek ya ɗago kansa, wanda tun fara kukan nata ya sadda kansa ƙasa  baisake ɗagowa ba sai yanzun,  ɗago idanunsa da yayi yayi daidai da faɗawarta jikin Najeeb.     Wani irin abune yaji ya caki ƙahon zuciyarsa, wanda zafi da raɗaɗin sa ya ratsa cikin ƙwaƙwalwa da sassan jikinsa, rumtse idanunsa da suka kaɗa sukayi jajur yayi tare da buɗe bakinsa ya fesar da wani zazzafan numfashi.                Najeeb kuwa taro Laylerh'n da yayi ta faɗa jikinsa ne, ya sashi jin wani irin shock, take yaji gaba ɗaya tsikar jikinsa sun mimmiƙe, lokaci ɗaya wani irin yanayi ya soma ratsa ƙashi da bargonsa, hannayensa dake rawa yakai kan kyakkyawar fuskarta, cikin wata irin murya me sanyi yace.  "Laylerh! please wake up,  ki buɗe idanunki please."  Yafaɗi maganan aɗan ruɗe, dan yanda yaga idanunta na lumshewa, ya sanyashi jin faɗuwar gaba.           Duk da cewar tana jinsa amma bazata iya amsa masa ba, saboda hakanan takejin kamar tunani da hankalinta na ƙoƙarin barin jikinta, idanunta ne suka cigaba da  lumshewa, yayinda jikinta ya sake.          Ganin haka ne yasa Abbu tasowa hankalinsa amatuƙar tashe ya taho kan Laylerh'n, ɗago ta yayi daga jikin  Najeeb, ahankali Abbu ya shiga girgizata tare da soma ƙiran sunanta. Ganin kamar bata cikin hayyacinta ne yasa Abbu ɗago kai ya dubi Maleek wanda ya lumshe kyawawan  idanunsa, yayinda  yayi kamar baisan abun da ke faruwa ba.    Hankalin Abbu aɗan tashe yace.   "Please M.J sake ƙiran Dr.Ishaq, Laylerh ta fara fita hayyacinta banason wani abu ya sameta.."      Abbu bai ida maganar tasa ba Dr.Ishaq ya shigo cikin falon. Ganinsa ne yasa Abbu sauƙe ajiyar zuciya, da kansa ya ɗaga Laylerh'n inda ya kwantar da ita akan wata luntsumemiyar kujera dake nan side din dining area'n.       Ƙarasowa cikin falon Dr. Ishaq yayi, hannunsa riƙe da Ć´ar jakarsa wacce ya zuba kayan aikinsa da yasan zai ɓuƙata aciki.           Cikin kulawa Abbu da duk ciwon Laylerh'n yasa shi cikin damuwa yace.      "Please Dr. kayi checking ɗinta, naga kaman bata motsi."            Kai Dr.Ishaq ya jinjina alaman duk yanda Abbun keso haka za'ayi.  Ɗan ranƙwafawa yayi tare da buɗe Ć´ar jakarsa ya ciro abubuwan dayasan zai buƙata.    Cikin wasu Ć´an sakanni ya gama yi mata duk wasu gwaje gwajen da zaiyi mata.  Acikin Ć´an sakannin nan kuwa idan ka kalli fuskar Abbu da kuma Alhaji Ahmad, damuwa  kawai zaka hango akwance, yayinda Najeeb kuwa ya bada duk wani attention ɗinsa akan Laylerh'n, fararen kyawawan legs ɗinta wanda suka ɗan bayyana, sakamakon doguwar rigarta da ta ɗan ɗage ya zubawa ido baya ko ƙiftawa,daga cikin zuciyarsa kuwa abubuwa da yawa yake saƙawa.                Maleek.            Harzuwa yanzu idanunsa alumshe suke, ga wanda baisan meke faruwa ba, idan yazo zai iyi tunanin cewa  bacci yake, saidai kuma azahirance ba hakan bane,  shi kaɗai yasan abun da yakeji acikin zuciyarsa, ahankali yake fitar da numfashi, yayinda yakejin jikinsa duk ba daɗi, lokaci ɗaya yaji kansa nayi masa ciwo,  jingina bayansa da jikin kujeran da yake kai yayi, ajiyar zuciya yake saki akai akai, daga cikin ƙirjinsa kuwa zuciyarsa ce ke beating da sauri sauri.                        Daga ɓangaren Dr. Ishaq ma ajiyar zuciyan ya sauƙe, dan gane abun dake damun Laylerh'n yasa komai yazo masa cikin sauƙi, kuma ciwon nata ma ba sosai irin yanda zai tsoratar ɗinnan bane.              Wasu ruwan Injection guda biyu ya ciro acikin jakarsa tare kuma da Injection din, take yasoma haɗawa dan yasan idan yayiwa Laylerh'n su zata ɗan samu relief.            Ahankali taɗan soma ware shanyayyun idanunta wanda sukayi luhu luhu, da dukkan alama tanajin ciwon ajikinta sosai. Akan Dr. Ishaq ɗin ta sauƙe idanunta wanda ke tsaye yana haɗa ruwan alluran da zaiyi mata.          Ganin allura ahannunsa ne yasa ta ƙarasa ware idanunta, take jikinta ya soma ɓari saboda tsoro.    Ganin ta buɗe idanunta ne yasa Abbu ya ƙaraso kusa da ita, cikin kulawa yace.  "Laylerh sannu ko, ya jikin naki?."      Ashagwaɓe taɗan soma girgiza kanta, cikin muryarta da ta sanja amo tace.     "Please Abbu kafaɗa masa banason allura."         Murmushi Abbu yayi tare da shafa kanta, cikin matsanancin tausayinta yace.  "Sorry bazai miki da zafi ba, kuma ae alluran ita zata kashe miki pain din da kikeji, kiyi haƙuri amiki alluran kinji."  Abbu yafaɗi maganar cikin lallashi. Kai ta cigaba da girgizawa take hawaye suka cika idanunta, Allah Yasani arayuwarta tana matuƙar tsoron allura, saboda hakane ma ko ganinta batason yi.                Ganin da gaske alluran Dr.Ishaq ke ƙoƙarin yi mata ne yasa ta fashewa da kuka, amatuƙar tsorace ta soma jijjiga kanta tare da ɗan yarfa hanna yenta, cikin sheshsheƙan kuka tace.  "Please Ya M.Jay kace kada amin allura am scared,  pleaseeeeee .....!!" Taja maganan cikin wani irin yanayi dake nuna cewar bada iyaka bakinta takeyin maganna ba, har da zuciyarta.         Sauƙan maganganunta acikin kunnuwansa ne ya sashi rumtse Idanunsa da ƙarfi, lokaci ɗaya wasu abubuwa suka shiga yawo acikin tunani da ƙwaƙwalwarsa, tabbas irin hakan ya taɓa faruwa, wani lokaci da take buƙatar taimakonsa kamar yanda takeyi yanzu'n, kansa ya shiga girgizawa yayinda memories din baya ke ƙokarin dawo masa, lokaci ɗaya tunaninsa ya soma juyewa, abubuwa da yawa ne suka shiga bijiro masa. lokaci ɗaya jikinsa ya soma ɓari, take jijiyoyin jikinsa suka mimmiƙe, wanda hakan yasa gargasan jikinsa ma miƙewa, bazai iya jure yanayin da yake ciki ba, kukan Laylerh ne ke ƙoƙarin haukata masa tunani, ji yake kaman ana buga masa guduma acikin kansa, idanunsa ne suka soma yi masa gizon, abun da ya faru da Laylerh'n shekarun baya da suka wuce, kansa ya soma girgizawa take gaba ɗaya mood ɗinsa ya sauya, cikin wani irin matsanancin huci haɗi da nuna zallar yanayin da yake ciki da ƙarfi ya buga table din dake gabansa, wanda hakan yajawo plates da kuma glass cup's ɗin dake kan table din suka watse, tare da tarwatsewa aƙasa.   Ƙaaran buga table din da kuma fashewan cups ɗin da yacika falon ne yasa su Abbu atsorace suka maida hankalinsu garesa, hatta Dr. Ishaq da ke shirin yiwa Laylerh allura  tsaida komai yayi, ya zubawa M.Jay ɗin idanu.           Har yanzu jikinsa rawa yake, yayinda ya dunƙule hannayensa waje ɗaya, yana sakin wani irin zazzafan huci. Ganin yanda jikinsa keta faman ɓari ne yasa abun cikin yanayin sanyi yaƙira sunansa.          Jin muryar Abbu acikin kunnuwansa ne ya sa duk wani tunaninsa tsayawa, zuciyarsa tafasa take, yayinda yakejin zuciyarsa kamar zata faso ƙirjinsa ta fito waje, kansa ya girgiza dan bayajin zai iya jurewa yanayin da yake ciki, miƙewa tsaye yayi, cikin wani irin taku dake bayyana zallan izza da kuma ikonsa haɗi da nuna cewa shiɗin tsayayyen namiji ne ya nufi ƙofar da zata sadashi da falonsa, ko gani sosai bayayi saboda yanda idanunsa suka kaɗa sukayi ja.  Idanu su Abbu suka zuba masa har saida ya ɓacewa ganinsu, ajiyar zuciya Abbu ya sauƙe, tare da zama akan kujera yayi shiru, da yawan lokuta wani abu na haukata tunanin ɗan nasa wanda baisan ko menene ba, ba tun yauba ya fahimci cewa, Maleek ɗin nada wata damuwa acikin zuciyarsa, wanda ya kasa bayyanata ga kowa. Lumshe idanunsa yayi lokaci ɗaya yaji zuciyarsa ta karye, haƙiƙa rashin Oum Abdiyya shiya ruguza rayuwarsu, tabbas ya sani da tana nan duk wata matsala na Maleek zata sani amatsayinta na uwa.       Laylerh da ganin yanda Maleek ɗin ya rikide alokaci ɗaya ne yasa taji zuciyarta ta sake raunana, taso ayau din koda sau ɗaya ne ta kalli kyakkyawar fuskarsa, saidai hakan baiyi wuba, danko ayanzu bayansa kawai ta iya gani.              Kallonta Dr.Ishaq yayi cikin son lallaɓata yace.   "Kitsaya na miki alluran bazan miki da zafi ba."          Kanta ta girgiza take kuma ta sake sakin sabon kuka, cikin muryarta dake rawa tace.  "Tsoro nakeji, please Ya M.Jay tsoro nakeji."       "Ya M.Jay." Najeeb da ya zuba mata mayun idanunsa, ya maimaita sunan da take faɗi acikin zuciyarsa. Hakanan baisan me yasa ba yakejin wani iri idan ta ƙira sunan M.J ɗin. Ahankali ya taso daga inda yake tare da ɗan matsowa kusa da ita, anan kan hannun kujeran da take kwance ya zauna, cikin wani irin yanayin dake fusgarsa akanta yace.   "Oh sorry Laylerh, please stop crying."   Yafaɗi maganar tare da ɗaura hannunsa akan nata hannun, wanda hakan da yayi kuwa ba ƙaramin tayar masa da tsikar jikinsa yayi ba, taushi da kuma laushin hannunta ne suka soma ratsa shi, hakan ya sashi ɗan lumshe idanunsa.             Cikin shagwaɓar da ita kanta batasan ta iya taba tace.  "Da zafi sosai."    Idanunsa ya kuma zuba mata, ahankali ya jawota jikinsa, tare da sanya tafin hannunsa ya rufe idanunta.        Akaron farko kenan na rayuwarta da ta fara shiga jikin wani namiji wanda yake ba muharraminta ba, kuma har yayi hugging ɗinta haka, hakanan taji komai na duniyar ya daina yi mata daɗi, tunanin M.Jay ɗinta ne ya soma dawowa cikin brain ɗinta, asanyaye ta saki kuka, cikin shagwaɓa ta soma motsa laɓɓan bakinta, magana takeson yi amma takasa, wani abune acikin zuciyarta da takeson bayyana shi, amma harshenta yayi nauyi, dole haka ta rumtse idanunta.      Ganin haka ne yasa Dr. Ishaq soka mata alluran dake hannunsa.    Idanunta ta zazzaro tare da fasa ihu, take ta soma yunƙurin guduwa, riƙeta Najeeb yayi ƙam dan yasan idan yabarta alluran zai iya karyewa ajikinta.  Haka tanaji tana gani akayi mata alluran guda biyu, babu yanda ta iya.  Ana gamawa kuwa ta fashe da kuka, ahankali ta zame jikinta daga na Najeeb ɗin ta kwanta aƙasan carpet,  tsakani da Allah ta ke kukanta, wanda ita kanta batasan kukan meye takeyi ba, dan har acikin zuciyarta ba wai kukan alluran takeyi ba.              Ganin haka yasa Abbu yin murmushi, kasancewar yasan tun ada can ma Laylerh nada shagwaɓa sosai da kuma yawan koke koke musamman idan bata da lafiya.           Magunguna Dr.Ishaq ya rubuta wanda za'a sayo abata.  Kallon Abbu yayi cikin son kwantar masa da hankali yace. "Bawata matsala bace babba, insha Allah zata warke, wannan injection ɗin su zasu kashe mata pain ɗin, kuma za su sata bacci, idan ta tashi kuma insha Allah zata jita normal, sometimes dama ana samun irin haka,amma no problem zataji sauƙi Insha Allah." Cikin gamsuwa Abbu yace "Alhamdulillah." Hannu ya bawa Dr. Ishaq din sukayi musabaha, sannan ya amshi takardan    maganin da za a sayowa Laylerh'n.           Najeeb wanda gaba ɗaya ya zama very weak saboda riƙon da ya yiwa Laylerh'n, shiya karɓi takardan maganin daga wajen Abbu, inda yace zaije ya sayo.              Ganin haka yasa Abbu yace wa Momy ta kai Laylerh ɗaki, dan har tafara bacci anan kan carpet ɗin.    Babu yanda Momy ta iya dole haka takai Laylerh'n ɗaki, domin koda wasa batason nuna tsanar Laylerh agaban idanun Abbu, kasancewar ta jima da gane cewa Abbu na matuƙar son Laylerh'n sosai. Kusan atare Najeeb da Dr. Ishaq suka fita daga cikin falon, inda Dr.Ishaq ya wuce office ɗinsa, shi kuma Najeeb kaitsaye ya nufi pharmacy dan siyawa Laylerh magani. Duk da cewa tuƙi yake amma kwata kwata tunani da hankalinsa basa tare dashi, ba abun dake yawo acikin tunani da kuma brain ɗinsa, sai haɗuwar jikinsa da na Laylerh, idanunsa ya lumshe domin moment ɗin ya masifar ratsa shi, lallai yana da buri akan Laylerh wanda dole kuma saiya cikashi. Ɓangaren Maleek kuwa, koda ya ƙarasa bedroom ɗinsa, kaitsaye toilet ya wuce, har yanzu zuciyarsa zafi take masa, rigar dake jikinsa ya cire, tare da ƙarasawa gaban shower ya sakarwa kansa ruwa, kasancewar hakanne kaɗai zaisa shi yaji zuciyarsa tayi sanyi. Hannunsa yakai inda ya shafi tattoo ɗin dake kwance agefen cikinsa, wanda aka rubuta AYSHNOOR da manya baƙi tare kuma da juya harufan, ta yanda bakowane zai fahimci abun da aka rubuta awajen ba. Lumshe idanunsa yayi, ahankali yakejin wani irin sanyi na shiga jikinsa, duk yanda zuciyarsa takai ga tafasa sai yaji ta soma yin sanyi. Kansa ya kifa ajikin bango, yayinda ya zamana ruwan shower'n na dukan naked skin ɗin bayansa. Laɓɓan bakinsa dake ɗauke da danshin ruwa yaɗan motsa, asanyaye cikin wani irin yanayin da ke bayyana zallan abun dake cikin zuciyarsa yace. "I can't live without you!". *Please comment and vote.* 18/ November/2020 *fatymasardauna* 1/19/21, 8:10 PM - Ummi Tandama: 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *LAYLERH MALEEK* *Writting By* Phatymasardauna *Wattpad* @fatymasardauna #future *Chapter 9* Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da fesar da sassanyar iska ta bakinsa, jin yanda sanyin ruwan shower ɗin ke ratsa duk jikinsa ne ya sashi kashe shower'n, tare da jawo wani fari ƙal ɗin towel ya ɗaura akan waist ɗinsa, ƙarasawa gaban sink ɗin dake cikin toilet ɗin yayi tare da ɗauro alwala, hannunsa ya ɗaura akansa, cikin nutsuwa ya soma ɗan kaɗe gashinsa dake ajiƙe da ruwa, hannunsa yakai jikin wani hangers wanda anan jikin hangers ɗin yake rataye duk towels ɗinsa, ɗaya daga cikin towels ɗin ya ciro tare da soma goge jiƙaƙƙen gashin kansa, koda ya gama goge kannasa kuwa, nan cikin wani durstbin ya jefa towel ɗin, sannan kaitsaye ya fice daga cikin bathroom ɗin. Koda ya fito kuwa nan kan wata chair dake aje agaban mirror ɗinsa ya zauna, yayinda gaba ɗaya jikinsa ke ɗauke da danshin ruwa, yayinda gargasan jikinsa suka kwanta lub, daga gefe guda kuwa farar fatarsa har wani shining take, wani ɗan ƙaramin towel dake aje akan dressing mirror ɗin nasa ya ɗauka, wanda dashi yayi amfani wajen goge naked skin ɗinsa, wani lallausan body lotion ya shafa, haɗe kuma da shafa wani body spray me daɗin ƙamshi ajikinsa, wanda gaba ɗaya ƙamshin spray ɗin ya cika ɗakin. Cikin nutsuwa ya miƙe tsaye tare da ƙarasawa gaban sif glass ɗinsa, wanda ke cike da kayan sawansa, wani simple 3 quater jeans ya ciro tare da sawa ajikinsa. Haka Batare daya saka riga ba ya ƙarasa gaban bedside drawer ɗinsa, ɗan jan murfin drawer'n yayi tare da ciro wani ɗan ƙaramin box me kaman akwati. Ƙarasawa gaban wata lallausar kujeran dake gefen gadon yayi ya zauna. Ahankali ya kai hannunsa kan cikinsa daidai inda ya ɗaure da bandage, cikin nutsuwa ya soma warware bandage ɗin dake nannaɗe akan ciwon dake gefen cikin sa, ahankali yake ɗan cije jajayen laɓɓansa, tare da ɗan rumtse idanunsa, wanda da dukkan alama ciwon dake wajen na ɗan yi masa zafi. Koda ya gama cire bandage ɗin maida kansa yayi ya ajiye, tare da jingina bayansa da jikin kujera, ahankali yake ɗan sakin numfashi. Still lumshe idanunsa yayi yana mejin yanda ciwon nasa keyi masa zafi, duk da cewa kuwa yanzu kusan 3 weeks kenan dajin ciwon nasa, kasancewar sunje wani aiki ne cikin rashin sa'a bullet ya samesa agefen cikinsa. Akasalance ya buɗe ɗan ƙaramin farin box ɗin da ya ajiye agabansa, inda ya ɗauko wani sabon bandage da kuma wani magani. Sanin zafin maganin ya sashi rumtse idanunsa, ahankali yaɗan soma shafa maganin wani irin zafi da raɗaɗi ne suka shiga ratsa ƙwaƙwalwarsa, cije lips ɗinsa yayi, cikin ƙarfin hali haka ya naɗa sabon bandage akan ciwon, duk da kuwa cewar yanajin zugi da zafi ajikinsa amma dole haka ya daure. Bayan ya gama kintsa kansa ne ya tashi tsaye, inda kaitsaye ya nufi saman makeken gadonsa, light off ɗin wutan ɗakin yayi, sannan ahankali ya haye saman gadon, ɗan lumshe idanunsa yayi akaro na barkatai, tare da sakin bayyananniyar ajiyar zuciya, har yanzu yanajin ransa ba daɗi, ga kuma zuciyarsa da ke acunkushe, sam kuma baisan meyasa yakejin hakan ba. Tuno da mood ɗinta na ɗazu, da kuma sautin kukanta da yayi ne ya sashi sake maida idanunsa ya rufe, hannunsa ya ɗaura adaidai saitin zuciyarsa yana me sauraran, yanda zuciyar tasa ke bugawa, wani abu da ya tuna ne ya sanyashi ɗan cije lips ɗinsa, tare da sakin murmushi har saida laɓɓan bakinsa suka ɗan motsa, wayarsa dake yashe akan gadon ya ɗauka tare da kunnata, hoton wata kyakykyawar yarinya ne ya bayyana akan screen ɗin wayar, wanda duka dukanta bazata wuce 9 years ba, yayinda yarinyar ke sanye da riga da wando, fuskarta ɗauke yake da murmushi, wanda hakan ya ƙara ƙawata kyawun fuskarta. Idanunsa ya zubawa hoton dake mamaye akan screen ɗin wayar, ahankali yakejin wani irin shauƙi na ratsa duk illahirin jikinsa, matso da fuskar wayar tasa yayi, ahankali yaɗaura bakinsa akan screen ɗin wayar. Cikin wata irin sassanyar murya me ɗauke da daddaɗan amo yace. "My Baby Boo!!." manna wayar tasa yayi akan faffaɗan ƙirjinsa, tare da lumshe kyawawan idanunsa, yayi imani cewa wannan yarinyar itace bugun zuciyarsa, haka kuma ƙaddaransa natafiya ne dai dai da rayuwarta. Najeeb.. Da tunani kala kala acikin ransa, ya ƙaraso gaban babban pharmacy ɗin, cikin ɗan hanzari ya shiga ciki, magungunan da Dr. Ishaq ya rubuta wa Laylerh'n ya sayo, koda ya fito daga pharmacy'n kaitsaye wani supermarket ya wuce, kayan ciye ciye ya sayawa Laylerh'n dangin su choculate da dai sauransu. Daga supermarket din kuwa gida ya nufa. Koda ya shigo compound ɗin gidan, yana gama daidaita parking ɗin motarsa ya fito tare da nufar hanyar da zata sadashi da falon gidan kaitsaye. Yana ƙarasawa falon kuwa ya tarar da su Abbu Jaheed da kuma mahaifinsa suna hira. Ganin Najeeb ɗinne yasa Abbu sakin murmushi cikin kulawa yace. "Najeeb kadawo." Kai Najeeb din ya jinjina tare da ƙarasowa cikin falon. Wrist watch ɗin dake ɗaure a tsintsiyar hannunsa ya kalla, cikin yanayin nuna damuwarsa ga Laylerh'n yace. "Eh nadawo Abbu, ga magungunan, dan ya kamata ace tatashi tasha, saboda shima zai taimaka mata ƙwarai wajen rage raɗaɗin ciwon." Kai Abbu Ya jinjina cikin gamsuwa yace. "Ƙwarai hakan zai taimaka, amma yanzu nasan ana tashinta da kuka zata tashi." Jin abun da Abbun ya faɗa yasa, Najeeb lumshe idanunsa, ƙwarai yanason sake ganinta, saboda baya so ace ya kwana batare daya sake sanya idanunsa acikin nata ba. Ɗan sake duba agogon dake ɗaure a hannunsa yayi, cikin nutsuwa yace. "Bari naje nagwada lallaɓata ko zata tashi tasha maganin." Murmushi Abbu yayi tare dabin Najeeb ɗin da ido, wanda tuni ya kama hanyar dayake hasashen cewa lallai nanne ɗakin Laylerh'n. Kallon Alhaji Ahmad Rufa'e Abbu yayi, shiɗin ma Alhaji Ahmad ɗin da ya bi Najeeb da kallo, ajiyar zuciya ya sauƙe tare da dawo da kallonsa ga Abbu, murmushi kawai sukayi juna tare da jinjina kansu. Lokaci ɗaya kowannensu ya soma ancen zuci, yayinda kowannensu da abun da yake saƙawa acikin zuciyarsa. Laylerh. tun da Momy ta kaita ɗaki take bacci, har zuwa yanzu kuwa baccin take, sai dai kuma kallo ɗaya zaka mata kaji tausayinta, duba da yanayin yanda take baccin kasan cewa ba tanayinsa bane acikin daɗin rai, duba da irin yanda take ta faman sakin sheshsheƙan kuka duk da cewa baccin takeyi, kwance take akan ɗan gadonta yayinda gaba ɗaya fararen legs ɗinta suka bayyana. Tsayawa yayi agaban ƙofar da yake tunanin cewa itace ƙofar ɗakin nata, ɗaura hannunsa yayi akan handle ɗin ƙofar, tare da tura ƙofar ciki, ahankali ya kutsa kansa cikin ɗakin. Tashin farko idanunsa suka sauƙa akanta. Murmushi yayi sakamakon yanda yaga ta duƙunƙune jikinta waje ɗaya. Maida ƙofar ɗakin yayi ya rufe, tare da ƙarasowa cikin ɗakin, kaitsaye ya nufi jikin gadon da take kwance. Ledan magungunan dake hannunsa ya ajiye, ahankali yaɗan ranƙwafo inda ya zuba mata idanunsa, sannu ahankali yake ƙarewa kyakkyawar fuskarta kallo, sauƙe ganinsa yayi akan zara zaran eye lashes dinta wanda suke ɗauke da danshin ruwan hawaye, ƙasa yayi da idanunsa har zuwa kan Ć´an ƙananan jajayen shining lips ɗinta masu kyau, wani yawu ya haɗiya, wanda ya tsaya masa amaƙoshinsa, ahankali yaɗan lashi lips ɗinsa. Cikin wata silent voice yace. "Kina da kyau sosai." Yayi maganar tasa abayyane, still cikin yanayin shauƙin daya samu kansa aciki, hannunsa yakai kan fuskarta, ahankali cikin sanyin murya yaƙira sunanta. "Laylerh!." ko motsawa batayi ba balle yasa ran cewa zata buɗe idanunta. Hannunsa yakai yaɗan ja hancinta, cikin sanyi ya kuma ƙiran sunanta. Laylerh wanda acikin baccinta tasoma jiyo sautin bakuwar murya acikin kunnuwanta, ahankali ta soma bude sleeping eyes ɗinta, cikin zallan shagawaɓa ta soma ƙoƙarin yin kuka. Hannunsa ya ɗaura akan bakinsa, cikin kulawa yace. "Shii karkiyi kuka kinji, tashi kisha magani." Akasalance ta ƙarasa buɗe idanunta, ganinsa akanta yasa tayi saurin tashi zaune tare da sanya hannayenta duka biyu ta kare ƙirjinta, idanunta ta soma ɗan mutsutstsekewa, tare da turo bakinta gaba. Murmushi kawai Najeeb yayi tare da soma ɓare magungunan dake hannunsa. Ganin yana ɓare magunguna ne yasa ta ɓata fuska, cikin zallan shagwaɓa tace. "Ni dai Aa bazan sha ba." Ɗago idanunsa yayi ya watsa mata. Hakan yasa tayi saurin ɗauke idanunta akansa, dan batajin zata iya jurewa mayataccen kallonsa. Murmushi ya sakar mata again tare da tashi daga tsugunon da yayi. Kan bedside drawer ɗin dake gefen gadon ya zauna, magungunan dake cikin hannunsa ya miƙo mata haɗe da goran ruwan swan, cikin kulawa yace. "Karɓa kisha." Yi tayi kamar bazata karɓa ba, saidai ganin yanda ya kafeta da idanu yasa bisa dole ta sa hannu ta amshi maganin, wajen karɓan goran ruwan ne hannunta da nasa suka ɗan gogi juna, cikin sauri ta zame hannunta, tare dayin ƙasa da idanunta, magungunan ta saka abakinta tare da kai goran ruwan bakinta, jin ɗacin magungunan acikin maƙoshinta ne yasata rumtse idanu tare da ɓata fuska. Murmushi yayi, dan hakan da tayi ba ƙaramin ƙara fito da kyaun fuskarta yayi ba, hannu ya miƙa mata alaman tabasa goran ruwan, babu musu kuwa ta miƙa masa, ƙarɓa yayi tare da tashi tsaye, anan kan bedside drawer ɗin ya ajiye goran, Ć´ar madaidaiciyar ledan dake ɗauke da kayan choculate da ya saya ya ajiye mata anan kan bedside din, kallonta yayi, hakan yasa itama ta ɗago ta kalleshi, wanda hakan yasa idanunsu haɗewa waje ɗaya. murmushi yayi mata cikin kulawa yace. "Gut night." Yana faɗin hakan ya kashe mata hasken wutan da ya mamaye ɗakin, anutse yasa kai yafice daga cikin ɗakin. Idanu ta tsurawa bayansa har ya gama ficewa daga cikin ɗakin, ahankali ta saki ajiyar zuciya tare da komawa ta kwanta, lumshe idanunta tayi, cikin jiki da kuma zuciyarta takejin inama da ace Ya M.Jay ɗinta ne shi ɗin, inama da ace shi tagani acikin wannan yanayin nata, take lokaci ɗaya taji wani irin kasala haɗi da baƙon yanayi sun ziyarceta, ɗan ƙaramin pillown dake gefenta ta rungume, tare da ɗan karyar da kanta, batasan tayaya kuma ta ina zata fara siffanta haɗuwa da kuma matsayin kyawunsa ba, saidai koma yaya tayi imani cewa yana da wani baiwar kyau wanda dayawan maza basu dashi, M.J shidin na dabanne. Hannu tasa ta dafe kanta wanda takejin ya mata nauyi, ga kuma idanunta da suke ta faman lumshewa, da alama magungunan da Najeeb ɗin ya bata suna sa bacci, ji tayi gaba ɗaya jikinta yayi weak, shiru tayi tare da zurfafa tunaninta akan M.Jay ɗin, ko cikakken mintuna 20 kuwa batayi ba, bacci ya ɗauketa. Ɓangaren Najeeb kuwa yana fita daga cikin ɗakin nata, kai tsaye cikin falon ya koma, har zuwa yanzu kuwa Abbu da kuma Alhaji Ahmad suna zaune, ganinsa ne yasa Abbu cikin kulawa yace. "Bata tashi bako?." Murmushi yayi tare da girgiza kai, ɗan juyawa yayi ya kalli ƙofar ɗakin nata, anutse yace. "Ta tashi, kuma na bata maganin tasha." Ajiyar zuciya Abbu ya sauƙe tare da jinjina kansa. Alhaji Ahmad ne ya dubi ɗan nasa, cikin kulawa yace. "Dama kai nake jira naga dare ya somayi kasan gobe jirgin 6 zanbi zuwa Kaduna, ya kamata mu wuce masauƙin mu." Kai Najeeb ɗin ya jinjina tare da cewa. "Yeah nima bacci nakeji." Kasancewar ko wanni zuwa da Alhaji Ahmad ɗin keyi agidan na Abbu yake sauƙa, wanda musamman Abbu ya gina wani haɗaɗɗen part acikin gidan wanda yayisa ne musamman dan tarban amininsa Alhaji Ahmad idan ya shigo Nigeria, ko yazo garin na Abuja, hakanne yasa duk zuwan Alhaji Ahmad da yakeyi baya sauƙa a hotel anan cikin gidan yake sauƙa. Kusan atare suka miƙe dukansu, Abbu da kansa ya shiga taka musu har zuwa masauƙin nasu, wanda tuntuni Momy tasa an gyarasa. Ɗakuna uku ne acikin babban falon, wanda kuma kowannensu akwai furnitures masu kyau aciki. Ɗaya daga cikin ɗakin wanda shine na farko Najeeb ya sauƙa, yayinda Alhaji Ahmad kuwa ya sauƙa aɗayan ɗakin. Koda Najeeb ya shiga ɗakin murzawa ƙofar key yayi, cikin nutsuwa ya soma rage kayan jikinsa tare da ɗaura wani towel ya shiga wanka, baiwani jimaba ya fito daga wankan sanye da farar bathrobe ɗin wanka ajikinsa. Tabbas Najeeb kyakkyawane, duk da cewar bashi da yalwatacciyar murɗaɗɗiyar surar jiki, amma kuma yana da ɗan faffaɗan chest, sannan akan fuskarsa yana da dogon hanci tare kuma da manya manyan idanu, ga kuma wani haɗaɗɗen sajen daya kwanta luf agefen fuskarsa, sannan kuma yana da yalwar gashi asaman kansa, yayinda laɓɓan bakinsa keda kalan light pink, tabbas Najeeb yana da salon irin nasa kyau'n, kuma yana da abubuwan burgewa da dama ajikinsa, wanda dayawan mata ke buri da fatan samu, saidai kuma dama duk yanda mutum yakai ga abu, kyau, ilimi, ko wayewa akwae wanda yafishi, wannan yasa tsakanin MALEEK da Najeeb ya zama da banbanci, kama daga yanayi harma kuma da tsarin halitta, domin Maleek shi ɗayane babu na biyunsa, saidai kuma dukka ninsu gwanaye ne wajen kyau, sannan acikin dukansu babu me makusa ɗaya wanda zaisa mace ta ƙisu. Shirya kansa yayi cikin wasu fararen riga da wando, zuciyarsa cike da tarin tunanin Laylerh ya haye saman haɗaɗɗen gadon dake cikin ɗakin. Koda ya kwanta ya rufe idanunsa, fuskar Laylerh'nce keyi masa gizo, tuno da santala santalan legs ɗinta da yayi ne ya sashi sakin murmushi haɗi da ajiyar zuciya, tabbas duk da cewa Laylerh'n bata da wani girma sosai amma tana da tsarin halitta me kyau da kuma ban sha'awa, musamman yanda shape ɗinta yake, Allah yayi mata body structure me kyau, wannan yasa idan yana kallonta bayason ɗauke idanunsa daga gareta, tabbas yanaji ajikinsa cewa Laylerh zata zama wani yanki na rayuwarsa, domin yanaji ajikinsa cewa zai rayu da ita, har ma ya samu mafaka ajikinta. Da tunani iri iri haka bacci ɓarawo ya ɗaukesa. Washe gari. Kamar yanda ta saba tashi ƙarfe 6 daidai akowacce rana, to yau ɗinma hakan ne ya kasance, saidai tashin nata na yau ya banbanta dana ko yaushe, dan kuwa da wani irin tashin zuciya haɗi da amai ta tashi, hakanan duk takejin yanayin nata ba daɗi, kyawawan ƙafafunta tazuro ƙasa daga kan gadon, tare da miƙewa tsaye, duk da cewa tanajin jiri amma haka ta daure. ƙarasawa toilet tayi inda ta ɗauro alwala, bayan ta idar da alwalan ne ta ɗan ɗago tare da lumshe idanunta, sakamakon wani abu me ɗumi da taji ya na ƙoƙarin bin jikinta, ɗan shagwaɓe fuska tayi, dan bataso ace abun da take zargine, sake komawa tayi ta wanke jikinta, ganin cewa da gaske period ɗinta ne yazo yasa ta sake kwaɓe fuska take idanunta suka cika da hawaye,, duk da cewa wannan shine karo na biyu da farawanta amma sam batason abun, saboda yanda yake sawa takejin kanta atakure, tuno da cewa awancan karon Teemah ta bata kyautan Sanitary pads ne yasa ta sakin ajiyar zuciya, dan idan da ace Teemah bata taimaka ta bata ba, da yanzu batasan ya zatayi ba wanka tayi tare da kimtsa kanta. Kasancewar garin ana ɗan yanayin sanyi yasa koda ta sanya uniform ɗinta, wani kakkauran safa ta saka akafafunta wanda tsawonsa ya kawo har kan guiwowinta. Koda ta saka rigar makarantar ɗas ta mata, kasancewar idan tana period breast ɗinta na ƙara girma shiyasa rigar uniform ɗin nata ta zauna ajikinta sosai. Wani haɗaɗɗen combat shoe tasaka aƙafanta, wanda kuma zasu taimaka ƙwarai wajen rage mata sanyin da takeji. Kallon agogon dake saƙale ajikin bangon ɗakin tayi. 7:13 am daidai, school bag ɗinta ta goya, tare da zura ɗan ƙaramin hijab ɗin makarantar ajikinta, extra pad guda biyu ta ɗauka inda ta buɗe zip ɗin dake bayan school bag ɗinta ta saka pad ɗin aciki, ganin ta gama kimtsa kanta ne yasa kaitsaye ta nufi falo. (Am sorry yau ba editing, naso page ɗin yayi tsawo amma bani da time.) *Comment nd Vote.* *fatymasardauna* 1/19/21, 8:11 PM - Ummi Tandama: 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇     *LAYLERH MALEEK* *Writting By* Phatymasardauna                 *Wattpad*         @fatymasardauna #Destiny *(Alhamdulillah! Tabbas ina godiya agareku masoyana, musamman yanda kuke nunamin ƙauna kuma kuke nunawa labaraina, haƙiƙa inajin daɗin hakan, bani da abun ce muku sai godiya, sannan ayau inason sanar daku cewa littafin LAYLERH MALEEK ya tashi daga free book ya dawo na kuɗi, daga wannan pagen kuwa zan dakata da baku free pages, duk wacce takeson samun cigabansa tofa saita biya, inaso kusan banyi hakan dan na ɓata muku rai ko kuma kuga kaman nayi rashin adalci ba, no bahaka bane Laylerh Maleek mallakina ne kuma ina ƙaunar baku duk wani labarina amatsayin free, saidai tanadin danayiwa Laylerh Maleek yasa bazan iya ci gaba da sakinsa free ba, saboda haka am sorry to say, ga waĆ´anda suke buƙatar cigabansa 300 ne kacal, sannan zaku iya turamin kuɗin ta hanyar account number, ko kuma katin MTN na 300. Ga wacce ta turamin kuɗin ta account number saita min screenshot dan nagani na tabbatar zaku iya tuntuɓana ta Whatsapp Number na 07017879464. Ga kuma Account Number na kamar haka.  0002214625 Abubakar Muhammed Sardauna Ja'iz Bank Kada ku manta na faɗa muku cewa salon Laylerh Maleek daban yake, duk yanda kuke tunanin chakwakiyar cikin littafin ya wuce nan, haka zalika labarin ya shallakewa tunaninku. Nagode sosai duk wacce tabiya 300 ina tabbatar muku da cewa zata samu cigaban labarin Laylerh Maleek. Gare ku mutanen dake zaune a Niger zaku iya tura katinku ga wannan number'n. +227 90899076)*                  *CHAPTER 10* Sako da ƙafarta cikin falon yayi dae dae da buɗe ƙofar part ɗinsa da akayi.    Ganin haka ne yasa tayi saurin komawa baya, cikin hanzari ta lafe ajikin ɗan bangon da tasan wanda ke cikin falon bazae ganta ba. Cikin isa da kuma izza yake takunsa, sanye yake cikin full shigar uniform ɗinsa na soldiers, wanda sukayi matuƙar yi masa kyau, kana suka bayyana zallan kwarjini da cikar halittarsa, yanayin yanda kayan sukayi matuƙar yi masa kyau ne yasa Laylerh da ta ɗan ɗago kanta tana leƙensa ne ta kafeshi da idanunta, ganin shigar dake jikinsa ne yasata sakin baki da hanci tana kallonsa, tundaga kan ƙafarsa dake sanye cikin wasu haɗaɗɗun baƙaƙen takalma, sosai uniform ɗin suka zauna ajikinsa, yayinda ya ɗaura facing cap wanda yake shima na soldiers ɗinne akansa, sanadin hakanne kuwa yasa rumfar facing cap ɗin  ya ɗan rufe idanunsa, ƙawataccen sajen dake kwance akan fuskarsa ne ke wani irin shining, gefe guda kuwa red shining lips ɗinsa ne keta walwalali, wanda hakan shike ƙara ƙawata kyawun fuskarsa, tabbas Maleek kyakkyawane, kuma tsayayyen Namiji me ɗauke da tarin kwarjini da kuma abubuwan burgewa. Tabbas Batajin zata iya ɗauke kanta daga kallon kyakkyawan Namiji na musamman irinsa, wanda zata iya rantsuwa cewa babu wani namijin da uniform ɗin soldiers ya taɓa karɓansa kamar sa. Ɗan lumshe idanunta tayi tare da lasan siraran laɓɓanta,  duk da cewar basa kusa da juna amma gaba ɗaya ƙamshin daddaɗan turarensa ya cika falon, har takai ga ya ziyarci hancinta, numfashin dake ɗauke da daddaɗan ƙamshin turarensa ta shaƙa, tare da lumshe idanunta, acikin jiki da zuciyarta takejin wani abu nayi mata yawo, kamar yanda jini ke gudana ajikinta haka takejin wani abu na musamman adangane dashi, ganin ya nufi dining area ne yasa ta ɗauke idanunta akansa, har zuwa lokacin kuwa bata rufe bakinta dake a wangale ba, kwarjini da tsantsar haɗuwarsa ne suka mamaye zuciya da gangar jikinta, wanda hakan ya haifar mata da wani irin zazzafan shauƙi me ratsa gangar jiki. Sake sakin ajiyar zuciya tayi akaro na barkatai, yayinda tayi imani cewa ganinsa da tayi ne sanadiyar rugurgujewan nutsuwarta.  Ɗan ƙara leƙa dinning area'n ɗin tayi, wanda tuni har ya ƙarasa ya zauna, yayinda ya bawa cikin falon baya, gefe guda kuwa su Abbu ne zaune,ciki kuwa harda Alhaji Ahmad Rufa'e wanda saboda wani babban dalili ya kashe zuwansa Kaduna da zaiyi yau ɗin. Hannu tasa ta gyara hijab ɗin jikinta, tare da ƙoƙarin samawa kanta nutsuwa. Cikin yanayin sanyi ta fito daga inda ta ɓoye, tare da ƙarasowa cikin falon, kaitsaye dinning area ɗin ta nufa. Abbu na ganinta ya saki murmushi cikin kulawa yace. "Good Morning Laylatu."    (Laylatu shine sunan da Abbu ke ƙiranta idan yana cikin yanayin nishaɗi.)   Ɗan murmushin daya bayyana kyawawan haƙoranta tayi, cikin yanayin ta na sanyi tace.    "Am sorry Abbu Good Morning!."      Murmushi Abbu yayi tare da cewa.  "Morning my daughter, ya jikin naki?." "Da sauƙi sosai." Tafaɗa tana me gyara zaman school bag ɗin dake goye abayanta. Kallonta ta mayar ga Alhaji Ahmad Rufa'e, cikin girmamawa tace.  "Abba Ina kwana." Murmushi Alhaji Ahmad ɗin yayi, kasancewar tana kusa dashi yasashi ɗan dafa kanta, cike da kulawa yace. "Lafiya ƙalau Laylerh, ya jikin naki?." Murmushi tayi tare da cewa.  "Da sauƙi." Kai Alhaji Ahmad ɗin ya jinjina tare da cewa.   "Allah Yaƙara sauƙi!." Da "Ameen." Ta amsa tare da ɗago kanta, ɗan satan kallon inda Najeeb yake tayi, kasancewar kallonta yake yasa idanunsu faɗawa cikin na juna, da sauri tayi ƙasa da idanunta, hannayenta ta haɗe waje ɗaya tare da soma wasa da Ć´an yatsunta, samun kanta tayi cikin wani irin yanayi, bakinta taɗan turo gaba ashagwaɓe tace.   "Ina Kwana."   Bai amsa mata ba saima cigaba da kallonta da yayi, baƙaramin kyau ƙananan laɓɓanta sukayi masa ba, musamman ma da tana maganan,  wani irin hot feeling ɗinta yaji na ratsa duk jikinsa, lumshe idanunsa yayi tare da ɗan lashe lips ɗinsa, shikaɗai yasan me yakeji agame da Laylerh'n, lallai Laylerh macece wanda da kalma ɗaya kawai zata iya haukata nutsuwa da hankalin lafiyayyen ɗa Namiji. Jin bai amsata bane yasa taɗan murgaɗa baki, cikin ranta tace.  "Dan kasamu ma angaisheka, bazan sake gaisheka ba to." "Me yasa bazaki sake gaisheni ba to?."   Ya faɗa yana me yawo da idanunsa akanta. Kyawawan idanunta taɗan zaro waje, domin a iya saninta ita da zuciyarta ne kaɗai suke maganan, saboda haka bata tunanin cewa wani zaiji ta. Kansa ya jinjina tare da ɗage mata giransa ɗaya alaman "Kina mamaki ne?." Ƙasa tayi da kanta dan batasan me zata ce masa ba,  sauƙe idanunta tayi akan ƙafafun M.JAY wanda suke sanye cikin baƙaƙen takalma,  tabbas tana kwaɗayi da kuma son sake ɗaura idanunta akansa, ɗan ɗago kanta tayi tare da kai dubanta inda yake zaune, yayinda ya duƙar da kansa ƙasa yana me latsa wayarsa dake riƙe ahannunsa, saboda facing cap ɗin dake kansa ne yasa bata iya ganin full face ɗinsa. Yatsun hannunta ta cigaba da cakuɗawa waje ɗaya, ahankali ta soma mamul mamul da bakinta, abun dake cikin zuciyarta shi take ƙoƙarin furtawa amma gaba ɗaya laɓɓanta sunyi mata nauyi, ƙirji da kuma zuciyarta ne ke bugawa, hakanan ta samu kanta da rasa duk wani ƙwarin guiwarta. Ɗan rumtse idanunta tayi, tare da soma ƙoƙarin bawa zuciyarta confidence, kamar yanda bakinta ke rawa haka ma abun da takeson faɗi ɗin ke neman ƙwace mata. Cikin sassanyar muryarta dake cracking tace.   "Gud Morning Ya... M....JAY....!"  Tafaɗa cikin dauriya tare da fisgo maganan nata.      Sauƙan muryar ta acikin kunnuwansa ne yasa shi lumshe idanunsa dake abuɗe tare da tsaida dukkan abun da yakeyi, fararen teeth ɗinsa yasa tare da ɗan cizon laɓɓansa. Wani irin abune yaji ya tsaya a ƙirjinsa, wanda hakan yasashi kasa ɗago kansa, hakanan yaji komai na ƙoƙarin ƙwace masa. Jin shiru bai amsa ta bane, yasa taji gaba ɗaya jikinta yayi wani iri, lokaci ɗaya taji rauni na ƙoƙarin maye duk kan sassan jikinta, idanunta dake alumshe ne suka ciko da ƙwalla. Batare da ta yarda ta sake kai idanunta garesa ba, ta ja ɗaya daga cikin kujerun falon ta zauna. Najeeb ne ya ɗago kansa tare da kallon Maleek ɗin, na Ć´an wasu sakanni, dawo da kallonsa ga Laylerh yayi, wacce ta duƙar da kanta ƙasa, har yanzu wasa take da yatsun hannunta, yayinda idanunta ke cike da ƙwalla, duk da cewar bata yarda ta ɗago kanta kowa ya ga hakan ba. Tsura mata ido yayi, lokaci ɗaya yaji ba daɗi acikin ransa. Plate ɗin soyayyan dankali da ketchup ɗin dake gabansa ya tura mata, cikin wani irin yanayin dake bayyana zallar abun dake cikin zuciyarsa yace.  "7:30 am ya kusa, kiyi sauri idan bahaka ba zakiyi latti!." Jin abun daya faɗane yasa ta ɗan ɗago kai ta saci kallonsa, lokaci ɗaya ta soma ƙoƙarin shanye hawayen dake kwance acikin idonta, saidai duk yanda zata kai ga ɓoye hawayen nata dole idan mutum ya kalleta saiya gane. Sanin haka yasa bata yarda ta haɗa idanu da Najeeb ɗin ba, bakuma zata iya ƙauracewa tayin abincinsa da yayi mata ba, domin gaba ɗaya zuciyarta tayi rauni, haka zalika tunaninta na ƙoƙarin tafiya ne wani waje daban. A al'adarta bata fiye cin abinci da spoon ba hakan yasa ta sanya hannunta asanyaye ta soma cin abincin. Lumshe idanu Najeeb yayi haka yakejin kaman ya sata ajikinsa ya bata abincin abaki, wani irin shauƙinta yakeji. Maleek da haryanzu kansa ke ƙasa miƙewa tsaye yayi, batare daya sanya ko loman abincin dake gabansa abakinsa ba, ya soma ƙoƙarin barin dining area'n. Hakanne yasa Abbu dasu Najeeb ɗagowa duka suka kalleshi. Cikin yanayin mamaki Abbu Jaheed yace. "Aa Maleek ina zakaje kuma bayan bakaci abincin ba?." Tsayawa daga tafiyan da yakeyi yayi, batare daya juyo ya kalli kowannensu ba yace. "Naƙoshi." Baijira me Abbun zaice ba yasa kai ya bar wajen, kaitsaye ya nufi ɗakinsa. Da idanu duk su Abbun suka bishi, banda Laylerh wanda takasa ɗago kanta. Kai Kawai Abbu ya girgiza tare da cigaba da cin abincinsa. Tanajin motsin rufe ƙofarsa alaman ya shiga part ɗinsa ne, ta ture plate din abincin dake gabanta, tare da miƙewa tsaye school bag ɗinta ta ɗauka ta rataya. Abbu ne ya ɗago kai ya dubeta, cikin kulawa yace.  "Kema kin ƙoshi ko?."      Kai ta jinjina masa alaman "Eh."    Kallon plate ɗin abincin nata Abbu yayi wanda ko rabin rabi bataci ba. Kansa kawai ya girgiza tare daɗan sakin mumushi, dama yasan hakan zata faru, ya jima da fahimtar cewa LAYLERH da MALEEK abu ɗaya ne, zuciya da ruhinsu duk iri ɗaya ne. Gyara zamansa yayi kana yace.   "Kije driver ya kaiki." Kamar daman jiran hakan take cikin sauri  tace "To." ahanzarce ta juya ta nufi hanyar fita daga falon. Miƙewa Najeeb yayi cikin kulawa yace. "Nima fita zanyi zan sauƙeta amakarantar idan yaso sai driver ya ɗauko ta." Jinjina masa kai su Abbu sukayi tare da ci gaba da cin abincinsu. M.Jay Yana shiga part ɗin nasa kaitsaye bedroom ɗinsa ya wuce. Maida ƙofar yayi ya rufe, ahankali ya ƙarasa jikin window'n dake cikin ɗakin nasa, wanda daga nan wajen kana iya hango duk abun da ke faruwa a compound ɗin gidan. Idanunsa wanda suka sanja launi daga farare zuwa jajaye ya ware, tare da fesar da wani irin numfashi me zafi, duka hannayensa biyu ya zura acikin aljihun wandonsa, tare da maida ganinsa zuwa ga compound ɗin gidan, daidai lokacin ne kuma Laylerh ta fito. Najeeb na biye da ita abaya. Ganin Laylerh da Najeeb ne ya sashi dunƙule hannunsa dake cikin aljihun wandonsa. Idanu ya tsurawa Laylerh'n, yanajin abubuwa da yawa na yawo acikin jikinsa, tabbas LAYLERH ƙaddarar sa ce, wacce akullum akuma koda yaushe take yawo acikin jininsa, ako da yaushe akuma kowacce rana wani abu na SIRRI daya ɓoye ƙoƙarin bayyanar da kansa yake, tabbas yanaji ajikinsa cewa acikin BIYU za ayi ƊAYA. Laylerh da jin takun mutum abayanta  yasata juyawa,  ganin Najeeb agab da ita ne yasa ta ɗan  tsaya tare da matsawa gefe, kana ta sadda kanta ƙasa. Wucewa gaba yayi tare da cewa.  "Kibiyoni mota na sauƙeki a school." Bin bayansa tayi da ido har ya ƙarasa jikin motarsa. Sai alokocin ta lura da shigan dake jikinsa, na wani haɗaɗɗen yadi me kalan coffee wanda hakan yasa farar fatarsa bayayyana, duk da cewa ma bashi da haske sosai, saidai kuma white colour ɗinsa is a natural. Ayanayin da takejin kanta aciki yasa bata tunanin zata iya yi masa musu, asanyaye ta nufi wajen da motar tasa take. Murfin motar ta buɗe, nan gefen me zaman banza ta shiga tare da jawo murfin motar ta rufe. Ƙamshin turarensa daya cika motar ne yasata lumshe idanunta, tare da kwantar da kanta ajikin kujeran da take kai. Key Najeeb yayiwa motar yayinda me gadi ya wangale musu gate ɗin gidan suka fice. Ganin ficewarsu daga gidan ne ya sashi juya baya, dan yaga komai da ya faru. Wani irin abu me ɗacine yaji ya ziyarci maƙoshinsa, yayinda har yanzu hannayensa ke dunƙule. Hakanan yakejin zuciyarsa na tafasa, lokaci ɗaya mood ɗinsa ya sauya, idanunsa ne suka sakeyin ja. Cikin wani irin yanayi haka ya nufi hanyar fita daga ɗakin. Koda ya fito compound ɗin gidan ganinsa da full uniform yasa duk sojojinsa shiga hayyacinsu,  yana shiga mota kuwa suma suka shiga tasu motar. Yanayin yanda Abdoul yaga fuskar ogan nasu a murtuƙe ne yasashi jan motar a 360 suka fice daga cikin gidan, domin haka nan Abdul ya saba matuƙar yaga ran Captain ɗin aɓace to yasan abun zai iya shafansa matuƙar yayi tuƙi ahankali. Gudu suke shararawa sosai akan titin hakanne yasa cutie ɗinsa dake bacci ta tashi, ganinsa da tayi ne yasa ta hayewa saman jikinsa. Ɗago idanunsa da suka yi jajur yayi batare daya kalli cutie ɗin nasa ba ya hankaɗata gefe har saida ta buge da murfin motar, wani Ć´ar siririn ƙara ta saki tare da faɗuwa awajen. Jin kukan magen ne yasa Abdul ƙara gudun motar, saboda yasan ba abu me sauƙi bane zaisa Captain ya yi wurgi da magensa, yasan M.J ɗin sarai kwata kwata bai iya ɓacin rai da hasala ba. Ɓangaren Laylerh kuwa tun da suka kama hanyar makarantar koda sau ɗaya ne bata buɗe idanunta ba, gaba ɗaya zuciyarta tayi nisa awajen tunanin Maleek. Batasan meyasa take yawan jin rauni da kasala akan duk lamarin daya shafesa ba. Aɓangaren Najeeb ma kuwa hakanne ya kasance kamar yanda zuciyarta tayi nisa atunanin wani abu daban, haka shima tasa zuciyar, saidai tunanin nasu ya kasance mabanbantan juna, saboda izuwa yanzu tunaninsa ya fara karkata ga abun da zuciyarsa ke raya masa akan Laylerh'n. Ahaka suka ƙaraso bakin tamfatsetsen gate ɗin makarantar tasu. Jin motar ta tsaya ne yasa ta bude idanunta ganin sun iso bakin makarantar ne yasa ta buɗe murfin motar ta fita. Sam manta da cewar Najeeb ɗinne ya kawota shiyasa ko waiwayowa batayi ta masa godiya ba. Idanunsa ya zuba mata harta shige cikin makarantar. Wani murmushi me ɗauke da ma'anoni daban daban yayi, tabbas ya hango abubuwa da yawa acikin idanun Laylerh, abu mafi girma daya gani acikin idanun nata kuwa shine RAUNI lallai dole da wannan raunin nata zaiyi amfani wajen biyan buƙata da kuma isar da shawarar zuciyarsa. Cike da yiwa kansa fatan samun nasara yayiwa motarsa key kaitsaye yabar arean makarantar. Laylerh. Gaba ɗaya yau haka ta ƙare wuninta acikin school ɗin cikin rashin jin daɗin yanayin, abun da yafi damunta ma shine yanda take yawan jin faɗuwar gaba. Duk yanda Teemah taso jan Laylerh'n ajiki hakan baisamu ba, dole ta ƙyaleta, dan yanayin damuwa ya bayyana ƙarara akan fuskarta. Haka Teemah taje tayiyo tsokanar ta aka biyota har cikin aji aka dinga dambe da ita, yayinda ta kafe kai da fata cewar itace me gaskiya bayan kuma itace da tsokana, Laylerh kam kallonsu kawai takeyi, dan idan da sabo ta saba da neman faɗan Teemah kuma bata taro daidai da ita Ć´an SS 3 take tsokanowa suzo ayitayi da ita gashi sam bakinta baya taɓa mutuwa koda kuwa za a dakata, to awannan karan ɗin ma dai Teemah taji ajikinta, saida waĆ´anda ta tsokano ɗin suka gaji da faɗan dan kansu suka tafi, kasancewar bakin Teemah'n kwata kwata yaƙi mutuwa. Koda aka tashesu daga makarantar atare suka jero su dukansu suka fito bakin makarantar, Teemah sai masifa takewa Laylerh wae ae tana gani akazo har aji akaci zalinta bata kula ba, ita dai batace mata komai ba, dan tasan koda ma tafaɗa Teemah bazata taɓa sanja halinta ba. Driver'n Abbu ne yafara zuwa ɗaukar Laylerh, kafun itama Teemah daga baya akazo aka ɗauketa. Har sukayi nisa a tafiyar tasu ta kasa daidaita nutsuwarta, still haka takejin heart ɗinta na bugawa da sauri. kwantar da bayanta tayi ajikin kujeran motar tare da ɗan lumshe idanunta, yayinda take saƙa abubuwa da yawa acikin ranta. Ahaka har suka iso gida. Tana fita a motar kaitsaye ɗakinta ta wuce, yanayin yanda ake ɗan busa sassanyar isaka agarin ne yasa koda ta cire uniform ɗinta, wani kakkauran doguwar riga ta saka, yunwa takeji sosai shiyasa kaitsaye ta nufi kitchine dan samawa kanta abun da zataci. Momy. Zaune take abakin gado yayinda gaba ɗaya fari'a da kuma annurin fuskarta suka kau, gefenta kuwa Aunty Aina'u ce dake ta faman taunar cheewing gum, tana me karkaɗa ƙafanta. Cikin yanayin fushi Momy tace.   "Banason Laylerh Aina'u, banason yarinyar nan, ban kuma taɓa jin tsanarta me tsanani acikin raina ba kamar yau danaji ƙudirin Alhaji akanta, ki bani mafita Aina'u dan narantse bazan taɓa bari abun dake zuciyar Alhaji ya bayyana har ya aiwatar da abun da yake so ba." Murmushi Aunty Aina'u tayi tare da gyara zamanta cikin halin ko in kula da kuma bayyanar da zallan abun dake cikin zuciyarta tace.   "Dole saikin kashe Laylerh kafun ki samu ainihin haƙiƙanin abun da kikeso, saboda haka ki kasheta kawai!." Murmushi Momy tayi tare da miƙewa tsaye, cike dajin daɗin shawarar da Aina'un ta bata tace. "Tabbas zan kashe Laylerh Aina'u amma bada hannu na ba, Zan kashe Laylerh ne ta hanyar Captain M.J, najima da wani buri araina wanda nake buri da fatan cimmasa, tabbas Captain da kansa zai ruguza rayuwar Laylerh." Murmushi sukayi su dukansu domin kowacce da abun da take saƙawa acikin ranta. Acan falon Abbu kuwa Alhaji Ahmad ne da Abbu zaune, akan lallausan darduman da ya ƙawata tsakiyan falon. Cikin nutsuwa Abbu ya ɗago kai ya dubi Alhaji Ahmad dake ta faman aikin duba wasu files dake gabansa. Gyara zama Abbu yayi tare da sakin ajiyar zuciya. Cikin  muryarsa da tayi sanyi yace.  "Nasa ka auren Laylerh nan da 1 month." Ɗago kai Alhaji Ahmad yayi tare da ɗan sakin murmushi,cikin halin dattako yace. "Tabbas nasan da hakan Alhaji Jaheed, saidai bansan meyasa kaketa yawan maimaita hakan ba tun ɗazu." Ajiyar zuciya Abbu ya sauƙe tare da cewa. "Bansan Ya Laylerh zata ɗauki abun ba, saboda har yanzu ita ɗin yarinyace, tabbas nasan ba zataƙi zaɓina ba, saidai kuma bansan me yasa nakejin faɗuwar gaba agame da hakan ba inajin kamar akwai wani gurbi daban cike ba." Murmushi Alhaji Ahmad Rufa'e yayi tare da ɗan bubbuga kafaɗan Abokin nasa cikin kulawa tare dason basa ƙarfin guiwa yace. "Insha Allah bakayiwa Laylerh zaɓen tumun dare ba, ina me tabbatar maka da cewar kamiƙa Laylerh a inda za'a kula da ita namaka alƙawari cewa Laylerh bazatayi kuka ba, kai Uba ne nagari kuma kayi abun daya dace." Murmushi Abbu yayi tare da miƙewa tsaye yaɗan soma zagaye falon, cikin son ƙarfafawa kansa guiwa da kuma cika alƙawarin daya ɗauka yace. "Insha Allah nima haka nake fata." Maleek. Shigowarsa cikin falon kenan, kaitsaye ya nufi dining area, kujera yaja ya zauna tare da cire facing cap din dake kansa, murfin bootle water'n dake hannunsa ya buɗe tare da juye ruwan dake cikin goran akansa, sanyin ruwan daya ratsa sa ne ya sashi kifa kansa akan table tare da sakin ajiyar zuciya. Laylerh fitowarta daga kitchine ɗin kenan hannunta ɗauke da plate ɗin indomie'n da ta dafa. Kaitsaye danning area ta nufa, idanunta akan indomie'n nata har ta ƙaraso dinning ɗin. Ƙamshin turarensa da tajine yasata ɗaga idanunta, take kuwa ta sauƙe ganinta akansa. Kallonsa da tayi kuwa yayi daidai da ɗago kansa da yayi. Akaron farko kenan da tafara sa idanunta acikin nasa kusa da kusa. Wani irin matsanancin shock ne ya shigeta asakamakon hakan, lokaci ɗaya gaba ɗaya jikinta ya fara kakkarwa, kanta ta shiga girgizawa yayinda laɓɓan bakinta suka soma vibrating, ɗan jan jikinta baya tashiga yi, aruɗe ta saki plate ɗin dake hannunta, tare da sakin wani razanannen ƙara. *(Menene buƙatar Najeeb akan  Laylerh? sannan kuma me yakeso awajenta? wani buri yakeson cimmawa akanta? Aurenta yakeson ko kuwa wani abu yakeso awajenta na daban? WANENE MIJIN DA ABBU ya zaɓawa Laylerh? Me kuma Momy zata aikata akan Laylerh? Miye Laylerh ta gani akan fuskar Maleek daya ke ƙoƙarin fitar da ita a hayyacinta?  Lallai Tabbas akwai wani abu, BURI ƊAYA ne ke yawo da kuma gudana acikin zuciyar Laylerh da kuma Maleek. Shin Laylerh Mallakin Wayene acikin MALEEK da NAJEEB? Kada ku manta tun da farko nafaɗa muku cewa ba irin yanda kuke tunani bane, cos ba amayi komai ba, ko wasan ma ba a fara ba.)* *Karku manta game buƙata zata turo katin MTN na 300 ko kuma ta turo 300 ta account number.* *Whatsapp number 07017879464* *Account number 0002214625 Abubakar Muhammed Sardauna Ja'iz Bank.* *Thank You*       *fatymasardauna* 1/19/21, 8:11 PM - Ummi Tandama:   🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇        *LAYLERH MALEEK*      *Writing By* *fatymasardauna* *(Wannan littafin na kuɗi ne, kada ki karanta idan kinsan baki biya ba, zaki iya turo kuɗinki 300 ta account number 0002214625 Abubakar Muhammed Sardauna. Whatsapp nomber 07017879464)*        *Chapter 11* Hannayenta ta sanya tare da toshe kunnuwanta, wanda hakan yasa indomie'n dake cikin plate ɗin zubewa akan ƙafanta. razanannen ƙaran da ta saki ne yayi daidai da shigowar Abbu cikin falon.     Yanayin yanda jikinta ke ta faman karkarwa ne yasa ƙafafunta ƙoƙarin kasa ɗaukanta, take tatafi luu zata faɗi.   Cikin hanzari ya sanya hannunsa ya tallafota ta faɗa jikinsa, take wani irin shock ya shiga yawo ajikinsa,  kyawawan idanunsa ya sauƙe akan cute face ɗinta, tare da kai dubansa ga lips ɗinta daketa faman ɓari.      "Hey!."  Ya faɗa cikin wata irin haɗaɗɗiyar lion voice ɗinsa, wanda dadin sauti da amonta ya ratsa cikin kunnuwanta. Wani irin sassanyar iska ne ya shiga ratsa dukkan illahirin jikinta, sannu ahankali ta soma sakin numfashi, tare da ɗan bude kyawawan idanunta wanda lokaci daya suka bayyana asali da kuma zallar kalansu na sexy eyes. Adisashe ta soma ganin kyakkyawar fuskarsa, tare da jefa idanunta acikin nasa,  lokaci daya taji kwakwalwarta na kokarin birkicewa, tabbas wayannan idanun da take gani ayanzu sune idanun da tajima tanaso da kuma burin gani agaba daya rayuwarta, wayannan idanun sune idanun da suka zama kaman abincin ruhinta, mafarkinta da kuma dukkan fatan ta. Wani irin zubawa tsikar jikinta ya shiga yi, hakan yasa sexy eyes dinta soma lumshewa, take kuwa hawaye suka soma gangarowa daga cikin idanun nata. Tabbas bazata iya jurewa yanayin da takejin kanta aciki ba, haka nan takejin duniyar na juya mata. Narkakkun idanunsa masu oily ya zuba mata, domin ya lura da tana kokarin fita cikin hayyacinta ne.     Fuskarsa dake dauke da danshin ruwa ya hade, cikin husky voice dinsa yace. "Ke what's wrong?". Shiru tayi tare da sake sakar masa jikinta, ganin da yayi cewar batayi motsi bane ya sashi zare hannunsa dake bayanta,  wanda dama hannun nasa ne ke riƙe da ita. Sakinta da yayine yasa tatafi luu zata faɗi. "MALEEK!".  Abbou da tun ɗazu yake tsaye yana kallonsu ya kira sunansa, jin muryar Abbou'n acikin kunnensa ne ya sashi saurin sake riƙota, hakanne yasa bata kae ga faɗuwa ƙasa ba.        Ƙarasowa dining area ɗin Abbou Jaheed yayi, gaba daya fuskarsa babu alaman walwala. Kallon Maleek ɗin yayi tare da kau da kansa gefe  "Me kayi mata?" Ya tambayi Maleek ɗin yana me kallon Laylerh'n. Kyawawan fararen idanunsa yadan zaro, tare da rolling dinsu alaman "Me nayi mata kuma?." Fuska Abbou ya haɗe tare da cewa.  "Tabbas ruwa baya tsami banza, ni nasan cewa Laylerh bazata taɓa faɗuwa haka kawai ba, dole saidai wani abu tagani daga gareka.".             Jin hakane ya sashi sakin murmushin da shi kaɗai ya baiwa kansa sanin ma'arsa, ahankali ya ɗago ya kalli Abbou'n, kaman zaice wani Abu kuma sai ya kuma maida kansa kasa. Laylerh da gaba daya ta Shiga shock din ganin idanunsa, jin muryan Abbou Jaheed akunnenta ne yasa ta fashewa da kuka, lokaci daya taji gaba daya zuciyarta tayi rauni.       Ganin yanda ta fashe da kuka ne ya sashi lumshe idanunsa, lokaci daya yasa tafukan hannunsa ya rufe fuskarsa. Hannun Laylerh'n Abbou ya kama tare da dagota tsaye cikin kulawa yace. " Stop crying Laylerh, faɗamin me ya miki kike kuka?." Kanta ta Dan shiga girgizawa tare da kokarin shanye hawayen dake idanun nata. Hannunta Abbou ya kama tare da zaunar da ita akan daya daga cikin kujerun falon. Kallon ƙafarta yayi wanda tuni fatar wajen ya somayin ja, saboda yanda zafin indomie'n ya kama fatar ta. Ɗago kai Abbou yayi ya kalli Maleek ɗin, wanda har yanzu fuskarsa ke cikin tafin hanunsa.               Kansa kawai ya girgiza, da kansa ya ɗauko ƙanƙara acikin fridge tare da  ɗaurawa Laylerh'n asaman ƙafarta inda indomie din ya ƙona ta. Dubanta Abbou yayi cikin kulawa yace."Kije ɗaki ki kwanta kinji, nasan zuwa anjima ciwon zai daina miki zafi." Kanta ta jinjina tare da ɗan jan sheshshekan kuka. Mikewa tsaye tayi haɗe da ɗan ɗaga ƙafarta ta soma takawa ahankali, taku biyu kadai tayi ta tsaya da tafiyan tare da sakin yar siririyar kara, zafin da ta ji sosae ne yasata rumtse idanu, tare da cije laɓɓanta.        Cikin zafi da kuma radadin da takeji tace "Abbu kafana zafi, bazan iya tafiya ba." Yanayin yanda tayi maganan tana me yarfa yan yatsun hannunta ne yasa Abbou jin tausayinta. Kallon Maleek Abboun yayi cikin yanayin bada umarni  yace. "M.J ka mata ka kaita ɗaki please bari zan kira Dr." Jin abun da Abbou'n ya fada ne yasashi saurin dago kansa. Kai Abbu dake kallonsa ya jinjina masa tare da haɗe fuska. Bottle watern dake aje a gabansa ya zubawa ido, yayinda zuciyarsa ta Shiga saka masa abubuwa da yawa.    Ajiyar zuciya ya sauke tare da dagowa ya kalli inda Laylerh ke tsaye, wanda tsawon one minute kenan da take tsaye ta kasa tafiya. Kujeran da yake zaune akai ya ɗan baya tare da mikewa tsaye, ya nufi inda Laylerh'n ke tsaye, yayinda gaba ɗaya idanunta suka kaɗa sukayi ja.      Hannunsa ya ɗaura akan kafaɗarta, wanda hakan bisa dole ya tilasta mata juyowa, ɗan ranƙwafawa yayi     batare da tunani ko tsammani ba kawai taji ya ɗaga ta caɗak.      wani irin abu me kama da shocking ne ya shiga yawo ajikinta. Idanunta ta rumtse da ƙarfi, domin hakan ya zama wani baƙon yanayi  na musamman agareta, akaron farko kenan da ta samu kusanci dashi har haka, daddaɗan ƙamshin turarensa ne ya soma ratsa hancinta, tare da  cakuɗewa da numfashinta.       Samun kanta ajikinsa da tayi, yasa bata da wani zaɓi daya wuce maƙale wuyansa da hannayenta, Cikin nutsuwa ya nufi hanyar da zai sadashi da ɗakinta,  daga gefe guda kuwa irin yanayin riƙon da yayi mata ne yasa tsikar jikinsa mimmiƙewa, lokaci ɗaya brain ɗinsa ta soma  ƙoƙarin juya  tunaninsa zuwa wani waje daban.   Ƙarasowarsu bakin ƙofar ɗakin nata ne yasa shi tura ƙofar da ƙafarsa, wanda hakan yasa ƙofar  buɗewa da kanta.    Yana kutsa kansa cikin ɗakin sassanyan ƙamshin cool perfumed ɗinta ne ya ratsa cikin hancinsa, hakanne ya sashi ɗan lumshe idanunsa,  shi mutum ne me tsananin son ƙamshi  wannan ne yasa hancinsa baya raina ƙanshi aduk inda yake.         Ƙarasowa cikin ɗakin yayi,  sai kuma alokacin ne ya kai dubansa kan kyakkyawar fuskarta.                 Wanda har yanzu idanunta alumshe suke, yayinda zara zaran eye lashes ɗinta ke jiƙe da danshin ruwan hawaye, dawo da kallonsa kan ƙananan  lips ɗinta yayi, wanda duk ta tattaune su da teeth ɗinta hakan yasa sukayi ja, take yaji wani irin abu na mamaye duk ilahirin jikinsa, wanda hakan ya sashi saurin ɗauke idanunsa akanta. ƙarasawa kan ɗan madaidaicin gadon nata yayi, ahankali ya soma ƙoƙarin zareta daga jikinsa, tare da kwantar da ita akan gadon.    Jin ya kwantar da ita akan gado ne yasa ta saurin juya masa baya tare da cusa kanta acikin pillow, tabbas da ace zai ga yanda ƙirji da zuciyarta ke bugawa sanadin ɗaukarta da yayi, to da bai ɗauketa a daddaɗan jikinsa kamar yanda yayi ayanzun ba.     Ɗan lumshe idanunsa yayi tare kuma da buɗesu alokaci guda. Akaro na biyu kenan da tun dawowansa ya tsura mata idanunsa masu rikitata.       Kallon dogon dunƙulallen gashin kanta wanda ya baje akan pillown da ta ɗaura kanta sanadin juya masa bayan da tayi yayi, ahankali ya soma yawo da idanunsa akanta, har zuwa kan hips ɗinta da suka sake cikowa, ƙasa yayi da kansa ahankali ya ɗan soma jan jikinsa baya, tare da zuba hannayensa acikin aljihun wandon jeans ɗin dake jikinsa. Abu ɗaya ne ke yawo acikin zuciyarsa, wanda akullum kuma ako da yaushe ke sukan zuciyarsa, wanda hakan kuwa shi ya haifar masa da rauni me girma acikin rayuwarsa, bayajin zai iya jure kallonta,domin yayi imani cewa itace raunin zuciya da kuma rayuwarsa, sannan kuma ya jima da sanin cewa itace  ƙaddara mafi girma agaresa, tabbas akwai wani abu dake kwance acikin ƙirjinsa, wanda yake azabtar da zuciyarsa akowacce rana.  Baisan meyasa yazama haka ba, baisan kuma dalilin dayasa raunin zuciyarsa ke ƙara fallasa kansa akowacce rana ba, baya fatan wani lokaci yazo masa da zai kasa jure abun da yake ji. Kansa ya soma  girgizawa, sakamakon yanda yaji kasala na ƙoƙarin sauƙar masa, cikin sauri ya juya ya fice daga cikin ɗakin.                   Jin alaman ficewarsa daga ɗakin ne yasa Laylerh dake kwance  buɗe idanunta, tare da juyowa tabi ƙofar ɗaƙin da kallo, wani irin sanyi ne ke ratsa duk jikinta, yayinda daddaɗan ƙamshinsa ya kama numfashinta.     Idanunta ta lumshe wanda hakan ya bawa hawayen dake cikin idanun nata daman gangarowa.     Tabbas yau ranace ta musamman agareni, mutumin da nake gani acikin mafarkina ya bayyana,  "Ya. M.Jay" tafaɗa cikin tsananin shauƙin da takejin kanta aciki. Sam bata taɓa kawo cewa M.JAY shine mamallakin waĆ´annan kyawawan idanun da take gani acikin mafarkinta ba. Hannu tasa tare da dafe daidai saitin zuciyarta dake ta faman bugawa da ƙarfi.           Tuno da yanayin da kuma zalla. kyawun eye balls dinsa da tayi ne,  yasa ta ƙanƙame jikinta waje ɗaya, pillown dake gefenta tayi rungume tare da ɗan sakin murmushi.     "Jikin ka akwai daɗi ya M.Jay, haka ma ƙamshin ka komai naka akwai daɗi na tabbatar da hakan!."        Tafaɗi hakan cikin yanayin dake bayyana zallar abun dake zuciyarta, take taji ta nemi duk wani zafin da ƙafartata keyi mata ta rasa.           Ɓangaren Maleek kuwa yana fita daga cikin ɗakin nata kai tsaye part ɗinsa ya wuce.     Yana shiga cikin bedroom ya turo ƙofar dakin nasa ya rufe, tare da murzawa ƙofar key. Ahankali ya ɗan jingina bayansa da jikin ƙofar, tare da lumshe gajiyayyun idanunsa.    Bai tabbatar da abun da yakeji ba sai ayau ɗin, Lallai ne  akan Laylerh komai na musamman ne agareshi.  Buɗe idanunsa yayi haɗe da ƙarasowa cikin ɗakin, kan wata haɗaɗɗiyar kujera ya zauna tare da sanya hannu ya dafe kansa, still ajiyar zuciya ya sauƙe, tare da ɗan dafe ƙirjinsa.       Abubuwa da yawa ne ke yawo acikin tunaninsa, ahankali ya soma ɗan murza gold ring ɗin dake hannunsa,  daga gefe guda kuwa idanunsa ne suka kaɗa sukayi ja, tabbas tausayi da rauni sun riga da sunyi tasiri acikin rayuwarsa, wanda sanadin haka ako da yaushe yakanjin cewa ba akan daidai yake ba, ako da yaushe LAYLERH ce, kaman yanda jini ke gudana acikin jikinsa haka zanen ƙaddaranta ke bibiyan rayuwarsa.       Ƙaran wayarsa ne ya katsesa daga duniyar tunanin daya ke ƙoƙarin faɗawa.      Kallon wayar tasa yayi, ganin sunan Abbou Jaheed  na yawo akan screen ɗin wayar ne ya sashi ɗagawa tare da kara wayar akan kunnensa.       Abbou Jaheed dake zaune jin Maleek  ya ɗaga wayarne yasa shi cewa.   "Idan kayi sallan Isha kazo dinning area inason ganinka."        "To."  ya amsa  cikin wata irin murya, dan lokaci ɗaya yaji ƙirjinsa na bugawa.     Take Abbou Jaheed na gama jawabinsa ya kashe wayar.   Jin Abboun ya katse ƙiran ne ya sashi aje tasa wayar shima, tare da miƙewa tsaye ya shige bathroom.          Ruwa ya sakarwa kansa saboda hakanne kaɗai zai sama masa relief daga abun da yake ji a zuciyarsa.          Najeeb.. tsawon mintuna 20 kenan da ya keta juyi akan makeken gadonsa, gaba ɗaya tunanin Laylerh ya hanawa ƙwaƙwalwarsa sukuni, wani irin hot feeling yakeji adangane da ita na ratsa duk ilahirin jikinsa, hakanne yasa yafara tunanin cewa abun daya ɗauka da wasa zai iya fin ƙarfin tunaninsa.   Jin ana ƙiran sallan Isha ne ya sashi miƙewa, ya shige  toilet tare da ɗauro alwala.  Yana fitowa kaitsaye ya wuce masallaci.    7:30 pm  daidai Abbou Jaheed da Alhaji Ahamad Rufae suka shigo cikin gidan, yayinda Najeeb ke biye dasu abaya, ahaka har suka ƙaraso cikin falon.  Yayinda yau Momy da kanta ta shirya musu diner, bayan tasa Larai ta girka musu foods kala kala haɗi da drinks.        Kujera Abbou Jaheed yaja ya zauna tare da duban  Larai dake ta aikin mopping tiles ɗin falon,  yace ta kira masa Laylerh. Cikin girmamawa kuwa  tace "To ranka shi dade."   Ahanzarce ta nufi ɗakin Laylerhn.      Laylerh dake kwance tayi hugging pillow,yayinda zuciyarta tayi nisa cikin tunanin Maleek wanda hakan yasa ita kaɗai take ta sakin murmushi.   Jin ana knocking ƙofar ɗakin tane yasa ta miƙewa, ahankali take ɗan taka kafarta wanda tuni ta ware ta daina yi mata zafi sosai.  Ƙarasawa jikin ƙofar tayi tare da buɗewa.         Ganin Larai tsaye abakin ƙofarne yasata sakin murmushi, cikin son bawa Larai'n girmanta tace.  "Inna Larai ki shigo mana."   Murmushi Larai tayi tare da cewa.  "Aa ai bama sai na shigo ba, dama Alhaji ne yace na ƙirawoki."   murmushi Laylerh tayi tare da cewa to gani nan zuwa.     Komawa cikin ɗakin tayi, kaitsaye drawer ɗinta ta buɗe wani farin ɗan ƙaramin mayafi ta ɗauka tare da yane kanta dashi, cikin nutsuwa ta nufi falon dan amsa ƙiran da Abboun ke mata.        Tana shigowa cikin falon tayi ido huɗu da Najeeb wanda dama tun zamansa awajen jiran fitowarta yake.     Kasa tayi da kanta tare da ƙarasowa dining area ɗin. Kujera taja ta zauna, cikin salon shagwaɓan da sometimes bata sanin tanayi tace "Abbou gani."   Murmushi Abbou yayi sannan cikin kulawa yace.    "Ya ƙafan naki ta daina zafi ko?."    kai ta gyaɗa masa alaman.    "Eh."      Kanta yaɗan shafa cikin tausayi haɗi da ƙaunarta yace.  "Good girl tashi kiyi seving ɗinmu to."      Murmushi ita ɗinma tayi, wanda har acikin ranta tanajin daɗin kulawan da Abbou Jaheed ke bata, tabbas tarasa uwa uba amma Abbou na iyaka ƙoƙarinsa wajen ganin batayi kukan maraici ba. Cikin nutsuwa ta soma ƙoƙarin seving ɗinsu.  Daidai lokacin M.Jay ya shigo cikin falon.  Ɗan Lumshe idanunta tayi tare da shaƙan daddaɗan ƙamshin turarensa da ya kawowa hancinta ziyara,  jin motsin ƙarasowansa dining area dinne yasa tajin wani irin sanyi na ratsa jikinta, take ta kwaɗaitu da son ɗaura idanunta akansa.   Jan kujera tayi ta zauna tare da ɗan satan kallon gefen da yake, sosai yayi kyau cikin shigar white shirt, da kuma white trouser ɗin dake jikinsa.      Maida kanta ƙasa tayi tare da jawo plate ɗin abincinta gabanta, kasancewar yunwa takeji sosai yasanya bata jira komai ba ta fara cin abincin.      Maleek kuwa tun isowarsa wajen bai ɗaga kai ya kalli kowannen su ba, wani haɗaɗɗen cup ya ɗauka tare da haɗawa kansa tea, komawa yayi ya zauna ahankali ya ke ɗan sipping tea ɗin yayinda rabin nutsuwarsa ke kan wayar dake hannun sa.        Ɗagowa Abbou Jaheed dake cin abinci yayi ya dubi kowannensu.    Tsaida cin abincin nasa yayi tare dayin ɗan gyaran murya.   Cikin kulawa haɗi da nuna musu amfanin abun da yakeson faɗa yace.  "Tabbas duk wani buri da kuma fatan uba nagari shine farinciki da kuma samun nasaran ĆłaĆ´ansa."  Ɗan jim yayi tare da sauƙe ajiyar zuciya, kallon Laylerh dake cin abinci yayi cikin kulawa haɗi da tsananin tausayinta yaƙira sunanta.      "LAYLERH!."         akaron farko kenan da taji ƙiran sunanta da Abbou'n yayi ya tsinkar mata da zuciya, tsaida cin abincin nata tayi tare da ɗago kai ta kalli Abou'n.       Hannunta ya kamo cikin kulawa yace.   "Laylerh ke Ć´ata ce da nakejin soyayyarki acikin raina, duk da nasan cewar banine na haifeki ba,amma koda sau ɗaya ban taɓa kallonki amatsayin wacce ba jinina ba, haka zalika ako da yaushe matsayin Uba nake agareki, kuma nasan ina da haƙƙin da zanyi miki zaɓi  na gari arayuwa, nayi imani cewa kamar yanda bazan iya cutar da yayanki Maleek ba haka kema bazan iya cutar dake ba, tabbas kina da matsayi me girma awajena Laylerh,  wanda hakan yasa na yanke wani hukunci  batare da nayi shawara da kowa ba, fatana da kuma burina ako da yaushe shine ki karɓi zaɓin da nayi miki hannu bibbiyu!."   Ɗan numfasawa yayi tare da sake riƙe hannunta ƙam, idanunsa ne suka ciko da ƙwalla, saboda lokaci ɗaya yaji Rasuwar ƙaninsa Abbou Mahmoud ya dawo masa sabuwa, dan tabbas da ace yana nan ayau shine zaiyiwa Laylerh'n haka.       Ganin Hawaye a idanun Abboun ne yasa Laylerh zaro idanunta, cikin tsananin mamaki haɗi da kaɗuwa ta soma girgiza kai, cikin muryarta dake ckracking tace.  "Please Abbou dan Allah, Ka umarceni akan komai bazan taɓa saɓa maka ba, please Abbou dan Allah karka bari hawaye sufita daga cikin idanunka saboda ni!."   tayi maganar ƙwalla na saukowa daga cikin idanunta.        Ganin hawaye akan fuskarta ne yasa Abbou shima ya girgiza kai, cikin sassanyar murya yace.  "Kada ki sake barin hawaye su fita daga cikin idanunki Laylerh, burina ako da yaushe shine nafaranta miki, har abada ina fatan hakan da nayi bazai zamo cutarwa agareki ba."    tsagaitawa da maganan nasa yayi tare da ɗan gyara zamansa cikeda  kulawa yace.   "Nasan ke Ć´ace me biyayya agareni ako da yaushe, kamar kuma yanda yake alhakin kowani Uba ne ya zaɓawa Ć´arsa miji nagari, nayi ƙoƙarin kamanta hakan, dan na zaɓa miki NAJEEB amatsayin mijin da zaki Aura.!!!." *(Hmmm chab chakwakiya kenan Abbou ya zaɓawa Laylerh Miji, lallai akwai gurmi.)* 1/19/21, 8:11 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *This book is mainly for those that pay, if you know you did'nt pay please don't read it. Here is the account number for people that are willing to pay- 0002214625 Abubakar muhammed Sardauna Jaiz bank. Whatsapp Number 07017879464.* *Chapter 12* Idanunsa ya rumtse lokaci ɗaya yaji duniyar na neman juya masa, bugun zuciya da numfashinsa ne suka nemi tsayawa sakamakon jin kalaman Abbu'n, yayinda shock ɗin daya shiga yasa shi kasa motsa koda Ć´ar yatsar sa. Wanda hakan yasa yanayinsa da nata suka kasance alokaci ɗaya, tamkar diran aradu haka taji sauƙan kalaman Abbu'n acikin kunnuwanta, manya manyan idanunta wanda alokaci ɗaya suka sauya launi ta zazzaro waje, jin maganganun Abbu Jaheed ɗin yasa zuciyarta yin nauyi, take wasu irin abubuwa suka shiga haukata mata tunani da nutsuwarta, ahankali ta soma girgiza kanta, yayinda sabin zafafan hawayen da suka cika idanunta suka samu daman gangarowa kan fuskarta, gaba ɗaya jikinta ya ɗauki rawa, cikin wata irin sarƙaƙƙiyar murya wanda take dauke da cracking tace. "A...b..b.u..." Katseta daga maganan da take ƙoƙarin yi ɗin Abbou yayi cikin tsananin tausayinta da kuma tausayin maraicinta da yakeyi yace. "Ki yarda dani Laylerh bazan taɓa zaɓa miki mijin da zai cutar dake ba, haka kuma amatsayina na Uba dole ne na zaɓa miki Mijin da zai zamo *GARKUWA* agareki, wanda zai share miki dukkan kukanki, ya kuma hanaki tuna cewar ke marainiya ce, Farincikin ki akullum shi nake burin gani Laylerh, burina ki samu miji nagari ki kumayi zaman aure nagartacce, domin burin kowani Uba aduniya shine ya aurar da Ć´arsa ga Namiji mafi nagarta da halin ƙwarai, wanda ko bayan ransa zai kula masa da ɗiyarsa!." Ɗan numfasawa Abbun yayi tare da sauƙe ajiyar zuciya. Cikin sanyi ya cigaba da cewa. "Alƙawari na ɗauka Laylerh, alkawarin bawa Najeeb aurenki tun kina da shekaru 11 aduniya, ayanzu kin kawo girma saboda haka nake fatan cika wannan alƙawarin dana ɗauka." Damƙe hannunta yayi ƙam cikin kulawa yace. "Kada kicemin a'a Laylerh, kada ki watsamin ƙasa ta hanyar ƙin karɓan zaɓin da nayi miki, duk da cewar bana fatan yi miki dole arayuwa, saboda haka kina da zaɓi, idan har baki aminta da Najeeb ba, kada ki ɓoyemin ki faɗa agabana kuma agaban kowa da kowa, ina me tabbatar miki da ashirye nake na bawa Aminina Alhaji Ahmad da kuma ɗansa Najeeb haƙuri, domin alƙawari ne dana ɗaukawa kaina cewar bazan taɓa miki dole ba, koda kuwa umarni nabaki kika shallake, kada ki ɓoye abun dake cikin rai da zuciyarki Laylerh, lallai kema kina da zaɓi!." Abbu Jaheed ya faɗi maganar cikin bayyana zallan abun dake cikin zuciyarsa. Hawayen dake gudu akan fuskarta kaman an kunna famfo ne suka kasa tsayawa, lokaci ɗaya duk wani tunani da nutsuwarta suka kau, yayinda bugun zuciyarta ya tsananta, har takai ga ƙirjinta gaba ɗaya na amsawa, wani irin shuuuu haka takeji acikin kunnenta kaman wanda aka watsa mata ruwa, laɓɓa da harshenta ne sukayi nauyin da har takai ga ta kasa motsa su. Najeeb da tunda aka fara maganan ya shiga shock zuba mata idanunsa yayi, lokaci ɗaya yaji komai na kansa na warwarewa, ko da wasa bai taɓa tunanin samun auren Laylerh'n zaizo masa asauƙi har haka ba, shi kaɗai yasan abun da yakeji akan Laylerh, wanda bai gama tabbatar da cewar zuciyarsa ta kamu da son Laylerh'n ba saida Abbu yayi wannan maganan, wanda shima a iyaka tsawon rayuwarsa baisan da ita ba. *"LAYLERH"* Abbou Jaheed yaƙira sunanta, domin gaba ɗaya ya lura da yanayin yanda jikinta ke rawa, ga kuma ruwan hawayen da yake ta sauƙa akan kyakkyawar fuskarta, hakanne yasa lokaci ɗaya yaji zuciyarsa ta karye, yayinda yanayin damuwa ta maye gurbin fuskarsa, zallan fargaba ya bayyana acikin idanunsa. Ɗaga idanunnata dake cike da ƙwalla tayi ta kalli Abbou'n, wanda hakan ke nuna cewar batajin zata iya furta wata kalma daga bakinta. Maleek Tamkar yanda bugun zuciyarsa da numfashinsa ke ƙoƙarin tsayawa haka ma tunaninsa, akaron farko kenan daya samu kansa cikin irin wannan condition ɗin, the first time kenan dayaji zuciyarsa na barazanar tarwatsewa, yayinda kuma ƙirjinsa yayi masa nauyi, akaron farko kenan dayaji yana son jin wani abu daga bakinta, wanda yayi imani cewa jin hakan daidai yake da ruguza gaba ɗaya shafin rayuwarsa, wanda ananne kuma littafin sabuwar ƙaddararsa zai buɗe, wanda baya tunanin acikinsa akwai wani sassauci, idanunsa wanda sukayi jajur kaman jan garwashi ya buɗe, akaron farko kenan da tun zamansa awajen ya ɗago idanunsa ya kalleta, haƙiƙa da ace wani daga cikinsu zai kallesa, to da yagano haƙiƙanin abun dake cikin rai da zuciyarsa. wanda ya jima yana ɓoyewa, tabbas yaji ajikinsa cewa ayau wani babi nadaga cikin littafin Ƙaddaran rayuwarsa ƙoƙarin buɗewa, wanda ya tabbatar cewa babine na Ƙaddara mafi girma me matuƙar wahalarwa da kuma tsuma zuciya. Kamar yanda ya zuba mata ido kuwa haka dukanninsu suka zuba mata nasu idanun, harda Momy kuwa wacce gaba ɗaya akalan tunaninta ƙoƙarin soma sanjawa. Ajiyar zuciya Abbou Jaheed ya sauƙe, tabbas ya karanci wani yanayi daga kan fuskar Laylerh'n, wanda kusan shi kaɗai ma ya isa nusar dashi abun dake cikin zuciyarta, gaba ɗaya jikinsa ne yayi sanyi, hakanne kuwa ya sashi ɗan lumshe idanunsa. Cikin sanyi haɗi da raunin daya samu nadaga ƙwarin guiwarsa ya ɗan shafa kan Laylerh'n, atausashe yace "Kinsan banason kukanki ko kaɗan, saboda haka ki share hawayenki, domin ni bazan taɓa yi miki dole akan abun da ba kya so ba, saidai kuma inason kisani, bazan taɓa miki zaɓin danasan zai cutar da rayuwarki ba, nafahimci dukkan yanayinki Laylerh saboda haka kibar kuka!." Asanyaye ya ƙarasa maganar, haɗe da ɗan jan kujeran dayake kai baya, ya miƙe tsaye, lokaci ɗaya yasoma ƙoƙarin barin dining area'n. Ganin hakane yasa ta sadda kanta ƙasa, sosai zuciyarta ke bugawa, yayinda gaba ɗaya duk wani kafar sadarwa na jikinta yayi sanyi, abubuwa da yawa ne ke yawo acikin zuciya da tunaninta wanda tayi imani cewa nan gaba kaɗan suna iya jikkata mata zuciya. Amatuƙar sanyaye ta juyo ta kalli Abbou wanda yake gab da barin dining area'n, bazata iya jurewa ba, domin gaba ɗaya rauni ya cika zuciyarta, cikin wani irin matsanancin kuka daya ciwota, ta miƙe tsaye da wani irin gudu taje ta faɗa jikin Abbun, tare da rungumesa ta baya, wani irin fitinannen kuka ta saki me ratsa zuciya, cikin kukan haɗi da muryarta da bata fita da kyau tace. "NA AMINCE Abbou, Na amince, bana fatan na kasance me butulci agareka ba, da nayi hakan kuwa Abbou gwara na rasa raina, Na amince da duk wani zaɓinka agareni zan rayu aduk yanda kaso......" Kukane ya sarƙe mata numfashi hakan yasa ta sake rungume Abbou Jaheed ɗin ƙaƙam. Tabbas maganganunta daidai suke da zuban wuta ajikinsa, haka kuma daidai suke da soyewa haɗi da ƙuntatar zuciyarsa, idanunsa ya rumtse da ƙarfi, take kuma jikinsa ya soma wani irin ɓari, wani irin mahaukacin yanayi ya samu kansa aciki me wuyar fassaruwa, wanda da ace yasan zai samu kansa acikin irin yanayin, to da koda wasa bazai sake ƙafarsa tatako cikin Nigeria ba, wanda hakan gashi ya zamanto silar rugujewar ƘUNDIN RAYUWARSA. Hawayen dake cikin idanun Abbou Jaheed ne suka samu daman zubowa kan fuskarsa wanda shi kansa bai ankara da hakan ba saida suka samu daman zubowa, da sauri yasa hannunsa ya goge hawayen, tare da ɗan juyowa ya shiga shafa kan Laylerh'n, yayinda yakejin wani irin farinciki na ratsa zuciyarsa, cikin son bayyana zallan farincikin da yake ciki yace. "Masha Allah! Allah Yayiwa rayuwarki albarka, yasaki acikin farinciki kamar yanda kika sani ayanzu, ina me miki fatan nasara da kuma cigaban rayuwa, insha Allah Bazakiyi danasanin zaɓin dana miki ba, domin Najeeb ma ɗan uwa kuma Yaya yake awajenki, Nagode Laylerh Allah ya miki albarka!." Ya faɗi maganar yana me shafa bayanta, dan har yanzu kuka take me tsuma zuciya. kukan da duk wanda ya jisa saiya tausaya mata, kukan da ya zamanto tamkar sauƙan yayyafin ruwan zafi acikin kunnuwan Maleek, kukan dake motsa masa zuciyarsa wanda ke cike da zogi haɗi da zallar ƙuna, kukan da raɗaɗi da kuma zafinsa ke ƙona zuciyar Maleek, kukan da yake neman zautar dashi haɗi da fitar dashi hayyacinsa, kukan dayafi komai hautsuna tunaninsa, bayajin zai iya jurewa domin hawayenta azabtar dashi suke, wanda hakanne yasa take wani zazzafan ciwon kai ya rufesa, hakanne ya sashi miƙewa tsaye batare da yana iya kallon gabansa ba ya nufi hanyar barin dining, gaba ɗaya jikinsa ya sake, yayinda zallan damuwa ya bayyana atattare da duk wani yanayinsa, idanunsa ne suka kaɗa sukai jajur kaman wuta, duk da kuwa cewar dishi dishi yake gani haka ya nufi side ɗinsa. Najeeb kuwa da kwata kwata yakasa ɗauke idanunsa akan Laylerh dake kuka, ajiyar zuciya ya sauƙe tare da lumshe idanunsa, wani haɗaɗɗen yanayi yakejin kansa aciki wanda hakan yasa murmushi bayyana akan fuskarsa, take yasoma hasashen wata duniya ta daban, wanda yake da tabbacin zai samu kansa aciki matuƙar yakasance tare da Laylerh, tabbas ya jima da sanin cewa Laylerh'n tana da wani irin sirrin kyau nata na musamman, musamman yanayin tsarin halittar jikinta wanda babu wani ɗa namiji da zai iya kallo ya kau da kansa, Laylerh tayi daidai da choice of mind ɗinsa, komai nata is natural, still murmushi ya sake tare da soma ɗan jujjuya kujeran daya ke kai, hakanan yakejin wani irin fitinannen ƙaunarta na ratsa duk jikinsa, haƙiƙa shi kansa bai gamsar da kansa cewar Laylerh zaɓinsa bane sai yau, da yakejin ƙaunarta na huda dukkan sassan jikinsa yana shiga jininsa. Jin taƙi daina kukan nata ne yasa Abbou Jaheed ɗan ɗagota daga jikinsa, cikin lallashi haɗi da ƙaunarta yace. "Kukan namiye ne haka Laylerh? badai kin aminta da zaɓin dana miki ba?." Cikin sheshsheƙan kukan ta jinjina masa kai alaman "Eh." Murmushi Abboun yayi mata, tare da sanya hannu ya shiga goge mata hawayen da gaba ɗaya ya ɓata fuskarta, again cikin son ƙarfafa mata guiwa yace. "Kuka bai kamaci fuskarki ba Laylerh, farinciki ya kamata kiyi domin dayawan ĆłaĆ´a mata burin ganin aurensu suke, to ke kinsamu zakiyi aure meye kuma na kuka, ko kinason kisani hawaye ne?." Saurin girgizawa Abboun kai tayi alaman "A'a." Kanta yaɗan shafa tare da cewa. "Yauwa Laylatuna, to muje kici abincinki kinji!." Hannunta ya kamo ya nufo da ita kan dining ɗin, kujera yaja tare da zaunar da ita, plate ɗin abinci ya turo mata gabanta tare da spoon yace "Taci." Kasa koda kyakkyawan motsi tayi, domin har yanzu jikinta rawa yake, hawayen dake fita a idanunta kuwa ta kasa yi musu controll domin haka nan suke ta zuba sha kaman ankunna famfo, kafun kuwa ta gama goge wasu, wasu sun kwaranyo. hannunta na rawa ta ɗauki spoon ɗin tare da soma juya abincin, kwata kwata batajin zata iya sanya wani abu acikinta, bakinta ma bata tunanin iya buɗesa. *Ya M.Jay.* shine kawai keta yawo acikin mind ɗinta, ahankali taɗan saci kallon gefen da tasan yana zaune, ganin kujeransa wayam ba kowane yasa taji zuciyarta tayi wani irin dokawa, yayinda wani sabon kuka me sauti marar controll ya kuma ƙwace mata, hakan yasa ta kifa kanta akan table ta shiga rera kuka. *Note Editing* *(am sorry na muku late update wallahi bani da charge ne, kuyi manage da wannan insha Allah Gobe da safe zan muku sabon update yanzu wayana saura 10 percent😪.)* 1/19/21, 8:11 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* Fatymasardauna *(This book is mainly for those that pay, if you know you did'nt pay please don't read it. Here is the account number for people that are willing to pay-0002214625 Abubakar Muhammad Sardauna Jaiz bank, Whatsapp number 07017879464.)* *Chapter 13* Hannu Abbou Jaheed yasa ya dafa kafaɗanta, cikin kulawa haɗi da muryarsa da tayi sanyi yaƙira sunanta, saboda kukan nata ya farayin yawa, wanda hakan kuma zai iya haifar mata da ciwon kai me tsanani. Jin yanda Abbou yaƙira sunanta asanyaye ne yasa ta soma ƙoƙarin daidaita nutsuwarta, tare kuma da ƙoƙarin shanye kukan da takeyi ɗin, saidai duk yanda taso tsaida kukan nata hakan yaci tura, domin kuwa kukan ya riga da yaci ƙarfinta,wanda har hakan ke ƙoƙarin fallasa sirrin dake cikin zuciyarta. sheshsheƙan kukan da take sakewa ne yasa Abbou Jaheed ɗin miƙo mata bottle water me sanyi, ayanda takejin ƙirjinta nayi mata ƙuna, yasa batajin zata iya ƙin amsan ruwan, hannunta dake rawa tasa ta karɓi goran ruwan, yayinda shi dakansa ya buɗe mata murfin goran, takai ruwan bakinta. Sosai ta shiga tuttulawa cikinta ruwa, har saida tasha fiye da rabin goran, ganin yawan shan ruwan zai iya kawo mata wani abu na daban, ko ma ta iya ƙwarewa ne yasa Abbou Jaheed ya karɓi bottle water'n daga hannunta. Ajiyar zuciya ta shiga sauƙewa akai akai yayinda takejin zuciyarta ta sakeyi mata nauyi, gaba ɗaya haka taji komai na duniyar ya daina yi mata daɗi, yayinda taji wani abu me nauyi ya tokare mata aƙirjinta, still ga kuma wani irin ciwon kai da takeji, wanda har ta kai ga tanajin kannata na sarawa, miƙewa tsaye tayi tare da lumshe kyawawan idanunta wanda sukayi jajur, suka kuma bayyanar da zallan abun dake cikin zuciyarta, wato haƙiƙanin gaskiyar da ita kanta batasan da cewar tana kwance acikin zuciyarta ba. Kallonta Abbou Jaheed yayi cikin tausasa murya haɗi da tausayinta yace. "Ina zakije, bayan kuma bakici abinci ba?." Ɗan buɗe runannun idanunta da suka soma lumshewa tayi, cikin sanyi da kuma muryarta daya soma dashewa tace. "Bacci nakeji Abbou, zanje ɗaki ne na kwanta." Ɗan jim yayi, kana cikin yarda da abun da tafaɗa ɗin ya jinjina mata kai alaman "Taje ta kwanta." Batajin zata iya sake ɗaga idanu ta kalli wani daga cikinsu, saboda haka asanyaye ta juya ta nufi hanyar sauƙa daga step na dining area'n. Da kallo Abbou Jaheed ya bita yana mejin wani abu na yawo acikin ransa, hakanan yakejin kamar kukan da ta keyi, bana haka kawai bane yana ɗauke ne da ma'anoni guda biyu, wanda kuma yakasa fahimtar haƙiƙanin ma'anar hakan, saidai wata zuciyar tana nusar dashi cewar bawai tana kukane saboda batason zaɓin da yayi mata ba, tana kukane saboda al'amarin yazo mata abazata, kasancewar har yanzu ita yarinyace. Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da ɗan yin shiru, kana ya daina cin abincin da yakeyi. Aɗaya daga cikin ɓari na zuciyarsa sam bayajin cewa zaɓawa Laylerh miji da yayi, kawo nakasu ne acikin rayuwarta, domin yayi imani cewa Najeeb zai kula da Laylerh sosai. haka zalika bazai taɓa barinta tayi kukan maraici ba, saidai kuma ya rasa me yasa wata zuciyar tasa ke so da ƙoƙarin kawo masa wani tunani na daban adangane da hakan, wanda kuma ya tabbatar cewa tunanin hakan bazai amfanar dashi da komai ba, ganin da yayi damuwa na ƙoƙarin shiga zuciyarsa ne ya sashi share duk wani tunani ya cigaba da cin abincinsa, aransa yana me fatan hakan da yayi ya zamanto Alkhairi agaba ɗaya rayuwarsu. Maleek. Dake tafiya yana gauraya hanya, kamar yanda ya baro cikin falon baya iya ganin gabansa sosai, haka ma har yanzu dishi dishi yake gani a idanunsa, ahaka ya ƙaraso cikin tamfatsetsen bedroom ɗinsa wanda ke cike da kayan alfarma. Hannunsa dake rawa ya ɗaura akan handle ɗin ƙofar, tare da maida ita ya rufe, ahankali ya jingina bayansa da jikin ƙofar tare da rumtse jajayen idanunsa masu kama da garwashin wuta, zuciya da ƙirjinsa ne keyi masa wani irin zafi da suka, yayinda wani irin ɗaci ke mamaye maƙoshinsa, ƙwaƙwalwarsa ce ke ƙoƙarin zautar dashi, ta hanyar dawo masa da maganganun Laylerh'n cikin kunnensa. *"NA AMINCE"* wannan kalmar da ta faɗa tafi komai haukata tunaninsa,domin jin sauƙarta yayi acikin kunnensa tamkar diran aradu, kwata kwata bayajin zai iya jurewa, wani abu me kama da fargaba ne ke neman daƙushe tunaninsa, hakanne kuma ke sa zuciyarsa tsananta bugawa, har takai ga yana iya jin faɗuwar gaba da kuma wani yanayi na daban, sam bai saba da irin wannan yanayin da yakejin kansa aciki ba, wanda hakanne yasa bayajin zai iya jurewa. Asanyaye ya buɗe idanunsa wanda suka sake runewa, yayinda kansa ke masa wani irin ciwo, irin wanda bai taɓa jiba, ahankali ya shiga taka ƙafafunsa da suke gab da kasa ɗaukar nauyinsa, saboda yanda gaba ɗaya jikinsa yayi weak, ƙarasawa gaban tsayayye kuma babban mirror'n dake manne agefen drawer'nsa yayi. Jajayen Idanunsa ya sauƙe akan madubin, wanda hakan yabashi daman kallon hoton bayyananniyar surar jikinsa, tun daga kan ƙafarsa har zuwa kansa, akaro na farko kenan daya taɓa zubawa kansa idanu ta cikin madubi, hakanan yaji gaba ɗaya zuciyarsa tayi rauni, wanda har hakan ya bayyana acikin idanunsa. "RAUNI!" Ya faɗa cikin wata irin murya, tare da rumtse idanunsa ƙam, domin itace kalmar daya fi tsana arayuwarsa, sanin cewa itace take ta wasa da zuciya haɗi da Ƙaddaransa. Hannunsa dake adunƙule yasa ya bugi daidai saitin zuciyarsa, still cikin wata murya me ɗauke da wani irin amo dake son bayyana jajircewarsa yace. *"I am not a LOSER, and i will never be LOSER."* Ɓuɗe idanunsa da suke a rumtse yayi tare da jingina bayansa da jikin bango, tabbas ayanzu shi kaɗai yasan me yakeji acikin zuciyarsa, duk da cewar yanajin zafi da raɗaɗi azuciyarsa, amma bayaso ya zamanto RAGO, aƙidarsa ce kuma fatansa ne, akullum yasan cewar shiba Rago bane, har yanzu kuwa yanaji ajikinsa cewa har abada bazai taɓa zama rago ba, duk da kuwa yasan cewar Ƙaddaransa nada rauni, amma hakan bazai sashi zama me kasawa ba, yanaji ajikinsa cewar kalmar LOSER bazata ci gaba da yawo acikin jininsu shida abokinsa SOORAJ ba, duk da kuwa cewar yasan SOORAJ yayi nasara na samun abun da yakeso, amma shi wata zuciyar bata gaya masa cewar zaiyi nasara. Acan falo kuwa Najeeb da gaba ɗaya kukan Laylerh'n ya gama ɗaga masa hankali, ɗan jingina bayansa da jikin kujeran da yake kai yayi tare da lumshe idanunsa. Tabbas yasan cewa yana cikin farinciki ayau, domin samun Laylerh ba ƙaramar sa'a bace ga kowanni Ɗa Namiji, saidai kuma kukan dayaga tanayi ya matuƙar taɓa masa zuciya, duk kuwa da yanda ya zurfafa tunaninsa ya kasa tantance wa da kuma gano kukan nata na miyene, saboda zuciyarsa bata kawo masa cewar akan aurensa take wannan kukan ba, domin ya yarda cewa shi namiji ne da kowacce mace zatayi fatan samu, why Laylerh zatayi kuka akan maganar aurensa da ita?. Wani irin killer smile ya sake tare da ɗan soma jujjuya kujeran da yake kai, bayajin zai damu da koma meye, saboda yaji ajikinsa cewa Laylerh mallakinsa ce. Momy kuwa da jin batun auren Laylerh da Najeeb, yasa ta aikin saƙawa da kuncewa acikin zuciyarta, samun mafita da tayi yasa ta saki murmushi me ɗauke da ma'anoni daban daban, cikin nuna kulawa da kuma son auren tace. "Masha Allah Najeeb angon Laylerh, gaskiya wannan bikin na Ć´an gata ne, saboda haka ya kamata mu fara shiri tunda wuri, congratulation na ta yaka murna." Murmushi Najeeb ɗin yayi tare da yin ƙasa da kansa, Abbou Jaheed da Alhaji Ahmad Rufae ma murmushin sukayi, domin sun riga da sunsan me suka shirya, Abbou Jaheed ne ya dubeta, cikin kulawa yace. "Karki damu very soon za'ayi biki Insha Allah, maybe ma nanda 3 to 4 weeks." Cike da mamakin kusancin abun Momy taɗan zaro idanunta, wani abu kuma da ta tunane ya sata sakin murmushi. Tare da cewa. "Allah Ya kaimu." "Ameen." suka faɗa atare daga haka kuma babu wanda yasake cewa komai acikinsu suka ci gaba da cin abinci, zuciyar Abbou Jaheed fari tas, domin gashi da yardar Allah Zai cika alƙawarin daya ɗaukarwa Amininsa, saidai kuma har yanzu idan ya tuna wani abu sai yanajin fargaba da kuma faɗuwar gaba na ziyartarsa, sanin cewa sharrin shaiɗan nada yawa ne ya sashi soma faɗin "A'uzubillahi!." acikin zuciyarsa, dan yasan da hakane kaɗai zai samu tsira daga abun da yakeji, wanda har yake zargin kansa da rashin aikata daidai. Laylerh da tun barin dining ɗin, ta nufi ɗakinta ahankali take iya taka ƙafafunta, komai bayayi mata dadi, duniyar kanta dama abubuwan dake cikinta, jin zuciyarta takeyi acunkushe, yayinda tunani da nutsuwarta ke ƙoƙarin yin rauni, kamar yanda bugun zuciyarta ayanzu ta raunana. Ahankali ta maida ƙofar ɗakin nata ta rufe, duk jikinta rawa yake har ta ƙafafunta kuwa, ƙarasawa gaban gadonta tayi, tare da zuba guiwowinta aƙasa, wasu irin hawaye masu zafin gaske ne suka silalo daga cikin idanun nata wanda hakan yasa ta lumshe su, akaron farko kenan da ta fara samun kanta cikin irin wannan yanayin, yanayin daya zamanto barazana ga bugawar zuciyarta, ita kanta batasan me takeji ba, bata kuma san me takeyiwa kuka ba, hasalima amsa take nema domin tana da buƙatar sanin me takeyiwa kuka, kukan zaɓin da Abbou Jaheed yayi mata ne kokuma me?, hannu tasa ta share hawayen da suka zubo mata, tare da sadda kanta ƙasa, tasani tabbas Abbou Jaheed Ubane agareta, kuma koda sau ɗaya bata taɓa masa kallon wani na daban agareta ba, Abbou shine gaba ɗaya duk wani gatan ta, ya riƙeta alokacin da tafi kowa buƙatar hakan, ya bata gata alokacin da duk wasu masu bata gata su ka bar duniya, saboda ita kawai ya bar kasuwancinsa na Dubai ya dawo Nigeria, ko yaushe burinsa shine ya sama mata farinciki, wannan kaɗai yasa bai cancanci butulci awajenta ba, domin bai kasance me musguna mata ba, ta yaya zata ƙi amincewa da zaɓinsa? tayaya zata watsa masa ƙasa a idanunsa? tayaya zata dubi mutum me girma kamarsa tace bata amince da zaɓinsa ba? tsawon shekaru da dama kenan da yake riƙonta bai kuma taɓa neman wata alfarma awajenta ba sai akan wannan, shi me iya bata umarni ne ako da yaushe, amma ayanzu sai yabata zaɓi, me yasa zata ƙi amsan zaɓi da kuma umarninsa na farko? ba zata iya ba, saboda ta yarda cewa aduniya babu wani Namiji bayan UBA haka kuma babu wata mace bayan UWA mahaifiya, tayi imani kuma cewa ita me karɓan zaɓin Abbou ne koda kuwa wani daban zai kawo yace ta aura zata amince masa. Ɗan zamewa tayi tare da jingina kanta ajikin gado, kuka ne me sauti ya ƙwace mata, hakan yasa ta ƙanƙame jikinta waje ɗaya, tare da soma rera kukan, gaba ɗaya zuciyarta tayi rauni, wani irin matsanancin tausayi haɗi da wani abu me kama da bege takeji na mamaye duk zuciyarta, yayinda bugun zuciyarta ke harbawa da wani abu na musamman adangane dashi, wanda hakanne kuma yake daɗa sata kuka, tabbas ita me matsanancin Rauni ce akansa. *M.Jay* shi kaɗaine ke yawo acikin jiki da jininta, shi kaɗaine ke yawo acikin tunaninta, haka zalika kuma shi kaɗaine ke yawo acikin gaba ɗaya Rayuwarta, batasan da me zata ƙira abun da takeji akansa ba, saidai koma meyene tayi imani mai tsananin zafi da suka ne agareta, sake ƙanƙame jikinta tayi waje ɗaya, tare da sanya hannu ta dafe kanta dake masifar sarawa, wanda har hakan yasa jiri me ƙarfi ke ɗibanta, ganin duniyar na juya mata ne yasa ta haurawa saman gadon ta kwanta, blanket taja ta rufe jikinta dake ta faman ɓari, saboda yanda zazzaɓi me zafi ya sauƙar mata lokaci ɗaya. Duk yanda taso ta tsaida zuciyarta waje ɗaya ta kasa yin hakan, domin kuwa hoton fuskarsa da kuma idanunsa ne ke yawo acikin nata idanun, lokaci ɗaya duk wata nutsuwa tata tasoma ƙaura daga jikinta, batasan me ta aikata ba, wanda har yasa takejin ba daidai azuciyarta ba, ba abun da take fata da buri awannan lokacin kamar bacci, saidai kuma duk yanda taso da yin hakan batajin zata iya. Haƙiƙa idan zuciyoyi biyu suka kasance manne da juna, kuma akan abu ɗaya lallai ne kuma tilas yanayinsu ya kasance iri ɗaya, ba iya buri da fatan Laylerh Maleek bane ke cikin rauni, har ma da zallan Ƙaddaransu dake neman juya rayuwar su zuwa cikin wata sabuwar shafi mai ɗauke da manyan darussa. *M.Jay* Sama da 30 minute kenan daya ɗauka atsaye ruwan shower'n daya kunna na dukan jikinsa, wanda amatsayinsa na cikakken Namiji me motsa jiki haka kuma soldier yasa sam baiji ajikinsa cewa ya gaji da tsayuwan ba, yanayin yanda ruwan ke dukan jiki da kuma kansa kaɗai ya isa bayyana maka cewar lallai ba'a cikin tunaninsa yake ba, domin duk yanda yaso da yayi zeroying mind ɗinsa abun yaci tura, ahankali yakai hannunsa ya kashe shower'n, tare da ɗaukan wata kakkauran bathrobe din dake gefensa ya sanya ajikinsa, ba tare kuma daya tsaya tsane gashin kansa ba ya nufi ƙofar fita daga cikin bathroom ɗin, hannunsa ya ɗaura akan handle ɗin ƙofar ya buɗe, yayinda yakejin ƙirjinsa na amsawa aduk wani taku ɗaya da zaiyi. A irin yanayin da yake ciki yasa sam bayajin zai iya tsane gashin kansa dake ɗigar ruwa, wani dogon trouser kaɗai ya saka batare da ya sanya riga ajikinsa ba, duk da kuwa cewar ana busa sanyi sosai agarin ga kuma sanyin A/C'n daya cika ɗakin. Ƙarasawa gaban windown ɗakin nasa yayi, wanda daganan inda yake yana iya hango compound ɗin gidan. Har yanzu zuciyarsa zafi takeyi masa, yayinda wani irin ɗaci yake daɗa mamaye maƙoshinsa, idanunsa da suke alumshe ya ware, saboda bayajin zai iya jurewa gizon da sukeyi masa, ayanzu baya buƙatar komai domin brain ɗinsa gab take da juyewa, wanda hakanne kuma yayi sanadiyar hautsunewar tunaninsa, yayinda har yanzu maganganunta ke masa yawo acikin kunnensa, kalamar "Na'amince!" da ta faɗa itace mafari acikin sabuwar shafin ƙaddaransu da ta buɗe ayau ɗin. haka kuma yakejin kalmar na neman tarwatsa masa ƙwaƙwalwa da zuciyars, kallonsa ya maida ga wata Ć´ar ƙaramar drawer dake cikin ɗakin nasa wanda aka rufeta da pin cord, ahankali ya soma takawa har ya ƙarasa gaban Ć´ar drawer'n. Tare da ɗan durƙusawa agaban drawer'n. L73M75 shine pin ɗin buɗe drawer'n, wanda anan ciki yake aje duk wani abu me mahimmanci daya shafi sirrinsa, yana gama sa pin ɗin kuwa take drawer'n ta buɗe da kanta, yayinda murfin farko na drawer'n ke ɗauke da wasu manya manyan Diary's guda biyu, sai kuma wani farin abu kaman gari da aka killacesa acikin wani haɗaɗɗen leda. Idanu ya zubawa garin da ajikin ledan aka rubuta Cocaine da manyan baƙi, duk kuwa da cewar yanajin zuciyarsa na bugawa akai akai, amma bashi da wani zaɓi wanda ya wuce hakan. Ledan cocaine ɗin ya ɗauƙo tare da maida drawer ɗin ya kuma sanya pin ɗin ya rufe. Idanunsa akan ledan dake hannunsa haka ya ƙarasa gaban kujeran dake gefen gadonsa ya zauna, ahankali ya jawo wani ɗan ƙaramin table ya ajiye agabansa, bayajin zai tsaya sauraran shawaran da zuciyarsa ke ƙoƙarin basa, domin brain ɗinsa ta ɗauki cajin da idan ya bata cikakkun 20 minute zata iya samun matsala, zuciyarsa kuwa ko tantama bayayi zata iya bugawa. Hannayensa na rawa haka ya fasa ledan cocaine din tare da juye garin akan haɗaɗɗen glass table ɗin dake gabansa. Kamar yanda hannunsa ke rawa haka ma duk jikinsa, cikin zaucewa ya matso da fuskarsa kan table ɗin, tare da yiwa Cocaine ɗin wani irin shaƙa, wanda hakan yasa tatafi har zuwa cikin kansa. Haka ya ɗauki sama da 13 minute yana shaƙan cocaine ɗin, ahankali ya ɗago da kansa yana me jan wani irin numfashi, tare da ɗan soma jujjuyawa kansa, domin cikin abun da bai wuce 18 minute ba har ya fara samun kansa acikin wata duniya ta daban, duniyar da bakomai acikinta sai gushewar hankali, kafun 10 minute tuni ya fara ganin abubuwa na zame masa bibbiyu, yayinda yake ganin komai adisashe. *30/November/2020* 1/19/21, 8:11 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna *(This book is mainly for those that pay, if you know you did'nt pay please do'nt read it. Here is the account number for people that are willing to pay 0002214625 Abubakar Muhammed Sardauna Jaiz Bank. Whatsapp number 07017879464)* *Chapter 14* Lumshe idanunsa yayi tare da shaƙan wani dogon numfashi, ahankali yakejin mood ɗinsa na sanjawa, yayinda mayen cocaine ɗin ke ƙara ratsa cikin brain ɗinsa, sake maida kansa ƙasa yayi tare da ci gaba da shaƙan cocaine ɗin son ransa, wanda hakan yasa zuga ɗaya kwata kwata yayi mata ta ƙare, ɗan ɗgowa yayi tare da jingina bayansa da jikin kujeran da yake kai, ahankali yakejin kansa na juyawa, yayinda yakejin ita kanta duniyar nayi masa wata iri, kasancewar ya shaƙi cocaine ɗin sosai ne yasa take tasoma yi masa aiki, domin kuwa cocaine din nada ƙarfi sosai, sannu sannu hankalinsa ke ƙoƙarin gushewa. Ganin yana shirin manta duniyar da yake ne ya sashi miƙewa tsaye daga zaunen da yake, wani irin hajijiyan daya ɗaukesa ne ya sashi saurin dafe bango, tare da soma ɗan girgiza kansa, dan ko gani sosai bayayi, adaddafe haka ya ƙarasa jikin makeken gadonsa wanda yaji farin bedsheet na alfarma, faɗawa saman gadon yayi, batare kuma daya kula ba dan ya fara fita hayyacinsa ya kwanta akan ciwon nasa, take kuwa ciwon ya fame, wanda hakan kuma yasa jini ya ɗan soma fita daga jikinsa. Kasancewar baya cikin hayyacinsa yasa bai wani ji zafin fame ciwon nasa sosai ba. Idanunsa dake abude ya mayar ya rufe, saboda yanda yaga gaba ɗaya duniyar na juya mai, ahankali yaji nauyin da zuciyarsa tayi yana raguwa, yayinda mind ɗinsa ke ƙoƙarin yin zeroying, take duniyar ta soma ƙoƙarin zame masa sabuwa wanda babu ɗigon damuwa acikinta, duk da kasancewar shi ba ma'abocin shaye shayen ƙwayoyi da kuma alcoholic bane, amma time to time yakan shan cocaine dan tana rage masa damuwar dake ransa, musamman ma idan kansa ya ɗau tension, duk da kuwa yasan hakan ba abu bane me kyau, saidai kuma watarana yakan kasa controlling kansa akan shan cocaine ɗin. Ahankali samun nutsuwa da kuma sanyin zuciyar da ya samu yasa shi, faɗawa cikin wani baƙon yanayi, yayinda yakejin wani irin hot feeling na ratsa duk jikinsa, cikin yanayin fitar hayyacin daya samu kansa aciki ne, ya sashi soma ganin kyakkyawar fuskarta nayi masa gizo, wanda sanadin hakanne kuma ke ƙara hura masa wutar zallan feeling din da yakeji, har takai ga kowacce gashi dake jikinsa mimmiƙewa,, yawancin lokuta baisan meyasa yake yawan jin hot feelings akan ta ba, yanayin da yake ji akanta me ƙarfi ne sosai, sometimes yakanji kamar bazai iya controlling kansa ba, wanda izuwa yanzu kuwa har hakan ya riga daya zame masa sabo, dan ayanzu feeling ɗinta ya zama kamar jini ne da yake gudana acikin jikinsa. pillow'n dake gefensa ya ɗauka tare da yin hugging pillow'n nasa tight, sannu ahankali zuciyarsa ke saƙa masa abubuwa da yawa, yayinda kuma gaba ɗaya tunanin nasa ba acikin hankalinsa yakeyinsu ba, idanunsa dake a lumshe ya buɗe, tare da jawo wayarsa da ke aje saman wani ɗan madaidaicin stool ɗin dake gefen gadon. Kunna wayar tasa yayi tare da ƙurawa hoton dake mamaye kan saman screen ɗin wayar idanu, ɗan ƙaramin bakin yarinyar da hoton ta ke jikin screen ɗin wayar ya ƙurawa idanu, sama da 14 minute ya ɗauka yana kallon hoton kyakkyawar yarinyar, kafun daga bisani ya ɗan lumshe idanunsa dake ɗauke da zallan maye, da kuma yanayin bacci, cikin wata irin kasalalliyar muryar sa dake ɗauke da wani irin amo yace. "No one like you AYSH! I love your smile, your voice and your eyes, I love your ......" shiru yayi tare da kasa ƙarasa maganar dake cikin rai da kuma zuciyarsa, ɗaura wayar tasa yayi akan ƙirjinsa, tare da ƙurawa zanen pop'n dake cikin ɗakin idanu, yanayin yanda mood ɗinsa ya sanja lokaci ɗaya ne yasa ƙarara zaka iya fahimtar cewa, akwai wani abu dake kwance acikin zuciyarsa, wanda yake jin tsoron furtawa, tabbas yayarda cewa akwai wani abu dake sukan zuciyarsa, wanda kuma asannu hakan ke neman haukata tunani da nutsuwarsa, jin tunani na neman fasa masa ƙwaƙwalwarsa ne, ya sashi ɗan soma jujjuya kansa, baiwani ɗau lokaci ahaka ba kuwa, bacci ɓarawo ya ɗaukesa. Laylerh. Juyi kawae take tayi akan ɗan madaidaicin gadonta, duk kuwa ga yanda taso bacci ya ɗauketa hakan ya ci tura, domin kuwa da zaran ta lumshe idanunta, hoton fuskar Maleek ne keyi mata gizo, wanda hakan ke ƙara narkar mata da zuciya, yayinda wani irin sassanyar ƙauna haɗi da shauƙinsa ke mamaye gaba ɗaya illahirin jikinta, lallai ta yarda da cewar akwai wani abu adangane dashi, dake shumfuɗe acikin zuciyarta, wanda take da fata da kuma burin sanin ko menene shi, sake gyara kwanciyarta tayi tare da yin hugging ɗin pillow'n da take kai.duk yanda kuwa taso ta saki zuciyarta hakan ya faskara, kasancewar damuwa da kuma fargaba sun riga da sunyi tasiri acikin tunaninta, dalilin haka kuwa yasa taji komai na duniyar baya yi mata dadi, lumshe idanunta da suka ɗan kumbura tayi tare da sakin ajiyar zuciya me ƙarfi, ƙoƙarin tsaida duk wani tunani dake cikin ƙwaƙwalwarta tayi, duk da cewar yin hakan abune me wuya, amma dole ne tayi hakan matuƙar tanaso ta rumtsa. har yanzu ita yarinyace, dalilin haka yasa brain ɗinta bazata iya ɗaukar wata damuwa me nauyi ba. Haka ta dinga juyi akan gadon, dicikin sa'a kuwa ko 15 minute bata ɗauka ba bacci me nauyi ya ɗauketa. Washe gari. 7:00 am daidai ta farka daga nannauyan baccin daya ɗauketa daren jiya, Kasancewar kuma bata samu baccin da wuri ba, shiyasa ta ɗan makara yau ɗin. Ahankali ta buɗe idanunta wanda suka yi luhu luhu saboda kukan da tasha jiya, duk da cewar bata wani jin kuzari me ƙarfi ajikinta amma ahaka ta daure ta nufi toilet, koda ta ƙarasa toilet ɗin kayan jikinta ta rage tare da haɗa ruwan ɗumi tayi wanka, tana gama wankan kuwa ta zura wata Ć´ar baby pink bathrobe ajikinta tare dayin brush kana kuma ta ɗauro alwala, ganin tagama gudanar da abun da zatayi acikin toilet ɗinne, yasa batare da ta jira komae ba ta fice daga cikin bathroom ɗin. Cikin yanayin hanzari da kuma gudun kada ta makara zuwa makaranta, ta shumfuɗa sallaya tare da tada sallah'n asuba, duk da cewar ma tasan ta makara, koda ta idar da sallan kuwa bata tsaya yin wani ƙyale ƙyale ba, versiline kawai ta shafa ajikinta sai kuma wata haɗɗɗiyar powder silk da ta shafa akan fuskarta, sai kuma peach colour lip stick da ta shafa sama sama akan laɓɓanta, wanda hakan ya ƙara fitar da asalin kalan shape da kuma kyawun bakinta. Ƙarasawa gaban drawer'nta tayi aɗan hanzarce ta ciro kayan uniform ɗin ta, ɗan madaidaicin sket na uniform din ta fara sawa, kafun ta saka rigar uniform ɗin, ko da yaushe uniform ɗin nata ƙara yi mata kyau suke, yayinda komai nata ke sake bayyana gwanin ban sha'awa, dan sosai uniform ɗin nata ke bayyana zallan ƙuruciyarta, saboda zamowarta me kyaun jiki dana sura ne, yasa ko cikin shigar uniform ɗin shape ɗinta kasa ɓoye kansa yake, wanda kuma hakanne kejan hankalin maza dayawa zuwa gareta. Ahanzarce ta saka white socks aƙafanta tare da goya ƙatuwar school bag ɗinta akan shoulder nta, duk da cewar simple meckup tayi, amma hakan bai hana cute face ɗinta bayyana ba, musamman ma shining lips ɗinta da yasha oil lipstick, mathematical text book ɗinta ta ɗauka cikin ɗan hanzari ta nufi hanyar fita daga ɗakin, kasancewar 20 minute kaɗai ya rage mata. Acan Falo kuwa Abbou Jaheed ne zaune kan ɗaya daga cikin haɗaɗɗun kujerun falon, hannunsa riƙe da jaridan Daily Trust. Gefensa kaɗan kuwa Momy ce ke tsugune tana haɗa masa black coffee, sanin cewar bata da wata dama na sanya kokwanto acikin zuciyar Abbou'n sama da wannan lokacin ne yasa, ta ɗan ɗago da kanta ta kallesa, cikin son nusar da manufarta da kuma sauya salon magana tace. "Alhajina inason magana dakai." Jin abun da ta faɗa ne yasa Abbou Jaheed ɗagowa ya dubeta, cikin kulawa yace. "Inajinki." Ganin daman da take buri da fatan samu na shirin samuwa alokaci ɗaya ne yasata gyara zama, tare da duban Abbou Jaheed ɗin, cikin ƙasa da murya tace. "Akan maganan auren Laylerh da Najeeb ne, duk da nasan cewa bani ce na haifeta ba, amma sai nake ganin yana da kyau nasan duk wani plan da kake shiryawa akanta, saboda kamar Ć´a haka na ɗauke ta, sannan kuma ina ganin kamar babu dacewa acikin haɗin auren Laylerh da kuma Najeeb da kake ƙoƙarin yi, baka tunanin cewa ko akwai wani wanda Laylerh keso ba Najeeb ba daya kasance zaɓinka." Da katawa da karatun jaridan Abbou Jaheed yayi, tare da zubawa Momy idanu, mamaki da kuma shayin kalamanta ne suka shiga yi masa yawo acikin ƙwaƙwalwarsa, lokaci ɗaya yaji yanaso ya fahimci wani abu daga cikin kalaman ta, hakanne kuwa ya sashi ɗan gyara zama tare da numfasawa, cikin yanayin sa na dattako yace. "Bana tunanin na aikata ba daidai ba akan maganar auren Laylerh da Najeeb, kuma har abada banajin zanyi dana sanin haɗa wannan auratayyan danayi, kuma alƙawari ne na ɗaukawa kaina cewar matuƙar ina darai da numfashi Laylerh bata da wani miji sai Najeeb." Ɗan numfasawa yayi tare da gyara zamansa. Daidai lokacin ne kuma Laylerh ta ƙaraso cikin falon, wanda shigowarta cikin falon ne yasa Abbou Jaheed dakatawa daga abun da yakeson faɗa, tare da zuba mata idanu, har ta ƙaraso inda yake, ɗan durƙusawa tayi, cikin yanayin girmamawa tace. "Barka da sapia Abbou." Murmushi Abbou Jaheed ɗin yayi mata tare da jinjina mata kai, cikin kulawa yace. "Yauwa Laylerh barka, fatan kin tashi lapia?." Murmushin daya bayyana kyawawan fararen haƙoranta tayi, cikin sanyi tace. "Lapia ƙalau." Murmushi Abbou Jaheed ɗin ma yayi, saboda ganin murmushin ta da yayi a yanzu yasa shi jin wani irin ƙwarin guiwa, wanda acikin Ć´an sakannin da suka wuce yanzun ya soma ƙoƙarin rasa su, saidai ganin yanda fuskarta ke asake ya sashi jin dadi acikin zuciyarsa, tare da sake tabbatar wa aransa cewa Laylerh bata da wani miji sai Najeeb. Laylerh kuwa maida kallonta wajen da Momy ke zaune tayi, cikin sanyin da ya zame mata sabo tace. "Good morning Momy!." ɗan ɓata fuska Momy'n tayi, cikin rashin kulawa tace. "Morning!." Bata damu da yanda momyn ta amsa mata gaisuwan nata ba, because idan da sabo ta saba da irin halayyan Momyn. miƙewa tsaye tayi tare da ɗan gyara zaman jakar dake rataye akan kafaɗanta, kallonta Abbou Jaheed yayi tare da ƙiran sunanta. Wanda hakan yasata ɗan juyowa ta kalleshi, tare da cewa "Na'am Abbou." jaridar sa dake aje agefe ya ɗauka, cikin kulawa yace. "Je ki ƙiramin Yayanki Maleek!." Ambatan sunan Maleek ɗin da yayi ne yasanya taji ƙirjinta ya buga, yayinda hakanan taji zuciyarta ta tsinke, ɗan lumshe idanunta tayi tare da haɗiyan wani wahalallen yawu da lokaci ɗaya ya tsaya mata amaƙoshi. Jakar makarantar nata ta ajiye anan kan kujera, cikin takunta na nutsuwa ta nufi sashin M.Jay ɗin. Ahankali ta ɗan murda handle ɗin ƙofar da zai sada ta da babban falonsa, cikin sa'a kuwa tana tura ƙofar ciki ta buɗe, wanda hakan ke nuna cewa dama bai rufe ƙofar da kyau ba. Ƙamshi da kuma daddaɗan sanyin A/C ne suka daki hancinta, wanda hakan yasa ta shaƙi wani dogon numfashi me dadi, yayinda ta ɗaura ƙafanta akan lallausan carpet ɗin dake malale nan bakin ƙofar, aje ƙafarta akan carpet ɗin yasa take Ć´an yatsun ƙafarta suka soma nutsewa acikin carpet ɗin, idanunta da ta lumshe taɗan ware tare da soma bin ko'ina dake cikin falon da kallo, komai akimtse yake yayinda sassanyan ƙamshi ke tashi, wanda sanadin hakan yasa duk wanda ya samu kansa acikin falon bazai so ya fita ba. Ganin babu alamarsa acikin falon ne yasa ta ɗan sauƙe ajiyar zuciya, karo na biyu kenan da ta shigo cikin ɗakin tun dawowarsa, soma takawa tayi ahankali ta ƙaraso cikin falon, idanunta ta tsayar akan ƙofar bedroom ɗinsa, hakanan take ɗanjin zuciyarta na tsananta bugawa, yayinda wani abu me kama da tsoro yake ƙoƙarin mamaye duk wani kuzarinta. Cikin dauriya haka ta ƙarasa jikin ƙofar, ahankali takai hannunta ta ɗanyi knocking ƙofar, shirun da taji ne ya sata sake yin knocking door ɗin, still nan ma bataji alaman za'a buɗe ƙofar ba, rumtse idanunta tayi tare da ɗaura hannunta akan handle ɗin ƙofar, duk da kuwa yanda zuciyarta ke bugawa amma bata da wani zaɓi wanda ya wuce shigarta cikin ɗakin. Tura ƙofar tayi tare da ɗan kutsa kanta ciki, again wani fitinannen ƙamshi ne ya kawowa hancinta ziyara, ƙamshin da tafi so, yafi kuma kowanne ƙamshi yi mata daɗi adunia, wannan ƙamshin nasa na dabanne, domin shaƙansa kaɗai acikin hancinta yana sama mata nutsuwa. Hangosa da tayi akan gado ne yasa ta maida ƙofar ahankali ta rufe, kyawawan idanunta ta ƙura masa, musamman ganin irin kwanciyan da yayi, gaba ɗaya ƙafafunsa aƙasa suke, kuma da dukkan alama bacci yake da gasken gaske, irin kuma baccin nan da ke nuna mutum baya cikin nutsuwarsa. Ƙarasawa jikin gadon nasa tayi, tare da sauƙe idanunta akan naked skin ɗin bayansa wanda yaji zanen tattoo, haka nan taji wani iri ajikinta, lokaci ɗaya kuma taji zuciyarta ta karye, ƙasa tayi da idanunta tare da kama Ć´an yatsun hannunta ta shiga murzawa, take kuwa ƙwalla ya cika idanunta. wani dogon numfashi taja tare da soma ƙoƙarin shanye hawayen ta, cikin sassanyar muryarta dake cracked taƙira sunansa. Jin shiru bai amsa mata bane yasa ta ɗan ɗago kanta ta kalleshi, still har yanzu yana nan ayanda yake ko motsawa baiyi ba. *"Ya M.jay"* ta ƙara ƙiran sunansa ashagwaɓe tare da ɗan taɓa ƙafarsa, har yanzu baiyi motsi ba, balle tasa ran zai buɗe idanunsa, hannunta dake rawa tasa ta ɗanja yatsar ƙafarsa, ɗagowan da zatayi ne kuwa idanunta suka sauƙa akan white bedsheet ɗin daya ke kai wanda ke ɗauke da jini, daidai inda ya kwantar da cikinsa, amatuƙar ruɗe ta zaro idanunta waje lokaci ɗaya jikinta ya soma ɓari, sam tama manta da me yakawo ta ɗakin, cikin sauri ta haye saman gadon tare da ƙarasawa ta tallafo kansa, gaba ɗaya ƙarfinta ta tarrara ta shiga ƙoƙarin juyasa ta yanda zataga daga ina jinin ke fitowa ajikinsa, wani abun mamaki kuwa ko motsawa baiyi ba duk kuwa ga yanda ta saka gaba ɗaya ƙarfinta wajen juyasa, wani irin nauyi yake dashi wanda hakan yasa ƙarfinta bazai taɓa iya matsar dashi daga inda yake ba, ganin ta kasa matsar dashi gefe ne yasa taja wani irin dogon numfashi, tare da sakin wani wahalallen nishi, zama tayi akan gadon tare da tanƙwashe ƙafafunta, ahankali ta ɗago kansa ta ɗaura akan cinyarta, wanda hakanne ya bawa kyakkyawar fuskarsa daman bayyana, idanunta da suka ciko da ƙwalla ta sauƙe akansa, tare da ɗaukan hannunta dake ta faman ɓari ta ɗaura adaidai kan kumatunsa, cikin muryar kuka tace. "Please Ya M.Jay ka buɗe idanunka kaji! Katashi please!!..." Daidai lokacin kuwa aka turo ƙofar ɗakin aka shigo. *fatymasardauna* 1/19/21, 8:11 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting by* fatymasardauna *(This book is mainly for those that pay, if you know you did'nt pay please don't read it. Here is the account number for people that are willing to pay-0002214625 Abubakar Muhammed Sardauna Jaiz Bank. Whatsapp number 07017879464)* *Chapter 15* Gaba ɗaya hankalinta akan M.Jay ɗin yake, wanda hakanne kuma yasa ko kaɗan bataji motsin buɗe ƙofar ɗakin nasa da akayi ba. Kyawawan idanunta dake cike da ruwan hawaye ta zuba masa, hakanan taji duk gaba ɗaya jikinta yayi sanyi, yayinda lokaci ɗaya taji wani irin matsanancin tausayinsa ya rufe mata zucia. Idanunta taɗan lumshe, cikin wata irin sassanyar murya me ɗauke da sanyin amo tace. "Please Yah M.Jay katashi, ka buɗe idanunka kaga yanda jini ya ɓata maka bedsheet, please dan Allah ka bude idanunka kaji!." Kamar amafarki, kana kuma cikin nannauyan yanayin daya samu kansa aciki, yaji sauti da kuma amon muryarta na ratsa kunnuwansa, hakan yasa duk da bai gama sanin awace duniya yake ba, ahankali ya ɗan soma motsa kyawawan sexy eyes ɗinsa wanda suka masa nauyi, cikin dauriya haɗe da wani fitinannen baccin da bai gama sake shi ba, yaɗan soma buɗe kyawawan idanun nasa kaɗan kaɗan, anan kan kyakkyawar fuskarta ya tsaida idanun nasa, yayinda ahankali yake ɗan buɗewa da kuma lumshe su, duk kuwa da cewar baya iya ganin fuskar nata da kyau, amma hakan bai hanasa shaida cewar itace agabansa ba. Mayun idanunta masu ɗauke da ruwan hawaye ta zuba mai bata ko ƙyaftawa, ganin da tayi ya ɗan buɗe idanunsa ne, ya sata waro nata idanun. Take taji wani irin sanyi na ratsa duk ilahirin jikinta, wanda hakanne ya tilasta mata ƙiran sunansa. "Yah M.Jay!." Ta faɗa cikin wata irin unique voice ɗinta me daɗin sauraro. Wanda sanadin zaƙi da kuma daɗinta yasa idanunsa dake amarairaice ƙara buɗewa, sanadin hakanne kuma yasa shi soma ganin fuskarta da kyau. Da idanunsa masu ɗauke da zallan yanayin bacci, wato really sexy eyes yake kallonta, yayinda yake mata wani kallo, irin kallon nan mai kama dana mayen sha'awa, tare kuma da kashe jiki. Akaron farko kenan itama da ta kasa ɗauke idanunta akansa, duk da kuwa da irin kallon da yake mata, wanda yasa takejin kaman an jona mata shocking ajikinta, lokaci ɗaya tsikar jikinta suka mimmiƙe, wani irin yaaaarr yaarrr haka takeji ajikinta, yayinda takejin wani abu na musamman na ratsa cikin ƙashi da ɓargonta. Bata taɓa ba, haka kuma bata saba ba, bakuma tajin zata iya jurewa kallon da yake mata, saboda hakan baƙon yanayi ne awajenta, wanda kuma sanadinsa ya sa takejin kaman zata shiɗe, kyawawan idanunta dake cike da ƙwalla ta lumshe. hakanne kuma ya bawa hawayen dake cikin idanunta daman sauƙawo kan fuskarta, batare kuma da ta shiryawa hakan ba. Ganin hawaye na sauƙa akan fuskarta ne yasa akasalance ya lumshe idanunsa, ahankali yakejin wani sassanyan yanayi na shiga jikinsa. akaron farko kenan kusan sama da 7 years da zuciyarsa ta fara kwaɗaita masa riƙe hannunta, wanda kuma tunanin nasa yayi daidai da abun da ke cikin zuciyarsa. Ahankali cikin yanayin sanyi ya ɗaura hannunsa akan nata hannun da ta ɗaura bisa saman kyakkyawar fuskarsa. Haɗewar hannun nasu waje ɗaya kuwa, shi ya sanya shi lumshe idanunsa tare da jan wani dogon numfashi. Itama Laylerh jin sauƙan hannunsa akan nata ne yasa ta lumshe idanunta, wanda eye lashes ɗin samansu ke ɗauke da danshin hawaye. Take kuwa lokaci ɗaya wani irin zazzafan yanayi ya soma fusgarta, tabbas shi ɗin kawai takeji yana yawo acikin jikinta. Haƙiƙa hakan ya zame musu yanayi na musamman, kuma yanayin farko da ya fi komai daɗi acikin yanayin rayuwarsu. Kamar kuma yanda sassanyar iska me dadi ke hura duk wani ƙofar gashi na jikinsa, haka itama ya kasance takeji acikin jikinta, sanadin hakan yasa yanayinta yaso fin nasa yanayin ƙarfi, dan wani irin diffrent feeling takeji akansa, wanda cikin mintuna kaɗan yake neman fitar da ita daga duniyar tunaninta. *LAYLERH!!.* Abbou Jaheed da kusan mintunansa 10 da shigowarsa cikin ɗakin ya ƙira sunanta da wata irin kakkausar murya, kasancewar tun shigowarsa ya zubawa gaba ɗayansu idanu yana kallonsu. Tamkar sauƙan guduma atsakar kanta, haka taji sautin muryar Abbou Acikin kunnenta, lokaci ɗaya gabanta yayi wani irin faɗuwa, yayinda ƙirjinta ya soma dukan uku uku, cikin hanzari haɗi da zallan tsoro ta ture kan M.jay ɗin wanda ta ɗaura bisa kan cinyarta, ahankali taɗan soma ja da baya, tare da zubawa Abbou Jaheed dake tsaye abakin ƙofar shigowa ɗakin idanunta wanda suka firfito waje saboda tsoro. Shiɗinma Abbou Jaheed ɗin kallonta yake, saidai wani abun mamaki babu alaman wasa ko murmushi akan fuskarsa. Ganin hakan kuwa shiya ƙara tsorata zuciyarta, cikin hanzari ta diro daga kan gadon tare dayin ƙasa da kanta, dan batasan me zata cewa Abbou Jaheed ɗin ba. Lura da hakan da Abbou Jaheed din yayi ne, yasa shi sake haɗe fuska cikin muryarsa da bata ɗauke da alaman wasa yace. "Da nace ki ƙirashi, hakan na nufin kizo ki zauna ne?." Cikin tsoro ta soma girgiza kanta, take duk jikinta ya ɗau rawa, cikin sanyin murya tace. " Kayi haƙuri Abbou ƙin tashi yayi shine na tashe shi, kuma ma jini na gani ajikinsa shi yasa na hau, amma bazan sake ba......." "Ya isa!." Abbou ya faɗi haka ta hanyar katseta daga maganan nata, fuskarsa kwata kwata babu alaman walwala. "Zoki wuce!." Ya faɗi hakan cikin kaurara murya tare dayi mata nuni da ƙofar fita daga cikin ɗakin. Ganin yanda Abbou ya tsume ne yasa taji gabanta ya faɗi, saboda akaron farko kenan da taga Abbou Jaheed ɗin yayi mata magana cikin tsawa, domin kuwa tasan hakan ba al'adarsa bace, ji tayi gaba ɗaya jikinta yayi sanyi, hakanne yasa hawaye taruwa acikin idanunta, kasancewar dama ita gwanace wajen saurin kuka. Cikin hanzari tazo ta raɓa ta gefen Abbou Jaheed din ta wuce, duk kuwa da yanda zuciyarta ke ƙara kwaɗaita mata son sake kallon M.jay ɗin, amma tsoro da fargaba sun hanata haka ta fice daga ɗakin. Jin alaman fitanta daga cikin ɗakinne yasa Maleek dake kwance maida idanunsa ya lumshe. *"Maleek"* Abbou Jaheed dake tsaye ya ƙira sunansa. Batare da ya buɗe idanu ko motsa jikinsa ba yace. "Na'am!!." Idanu Abbou Jaheed ya zuba masa, tare da ƙarasowa cikin ɗakin, kallon tattoo ɗin dake jikin Maleek ɗin yayi, tare da girgiza kansa, kana ya maida dubansa zuwa ga bedsheet ɗin da Maleek ɗin ke kwance akai, wanda ke ɗauke da ɗan ɗigo ɗigon jini, cikin yanayin dake ɗauke da ɗan mamaki yace. "Jinin meye wannan ajikin bedsheet ɗinka?" Jin tambayan da Abbou Jaheed ɗin yayi masane ya sashi ɗan buɗe idanunsa, tare da kallon gefensa inda ɗigo ɗigon jini ya ɓata, hannunsa yakai kan cikinsa tare da ɗan shafa saman ciwonsa, wanda yakejin yana ɗanyi masa zafi kaɗan kaɗan, koda ya ɗago hannun nasa jini ya gani anan jikin tafin hannunsa, wanda hakan ke nuna masa cewa jinin daga ciwonsa yake fitowa, ahankali ya maida idanunsa ya rufe, saboda baisan dame zai amsa tambayar da Abbou'n yayi masa ba. Ganin yayi shiru ne yasa Abbou Jaheed zuba masa ido, aransa yana me mamakin hali irin nasa, sam baidamu da kansa ba bare kuma lafiyar jikinsa, wata irin rayuwa yake ta ko oho, banda taurin zuciya da miskilancin tsiya ba abun da ya iya, kullum sai yayi ta abu kaman Jarumi, bayan kuma azahirance ba hakan yake ba. Sake dubansa Abbou Jaheed ɗin yayi da kyau, domin hakanan jikinsa ya basa cewa kamar Maleek ɗin ba adaidai yake ba, kasancewar bai taɓa ganinsa acikin irin wannan yanayin ba. Take wani sabon tunani yaso ɗarsuwa acikin ran Abbou Jaheed ɗin, amma sanin da yayi cewa ɗan nasa baya shaye shaye yasa shi kawar da wannan tunanin acikin ransa, domin ayanzu sam bayason abun da zai kawowa zuciyarsa, da tunaninsa kokwanto. Ɗan gĆ´ara tsayuwarsa yayi, cikin kulawa ya dubi Maleek din agajarce yace. "Kasameni a falo by 8:00 am." Kansa kawai ya iya jinjinawa Abbou'n, saboda har zuwa yanzu bai fara jin kansa adaidai ba, duk da cewar baya cikin maye, amma haka yakejin kansa yayi masa nauyi. Juyawa Abbou Jaheed yayi ya fice daga cikin ɗakin batare da ya sake cewa Maleek din komae ba. Jin motsin fitan Abbou Jaheed daga ɗakin ne ya sashi buɗe idanunsa, ahankali ya ɗan ɗago da kansa tare da tashi zaune ya jingina bayansa da jikin saman gadon da yake kai, amatuƙar kasalance yakai dubansa ga haɗaɗɗen agogon dake saƙale jikin bangon ɗakin. 7:40 am daidai da ya gani ne yasashi sanya hannu ya ɗan murza idanunsa, dan yana ganin kaman gizo ne idanunsa keyi masa, sake duban agogon yayi inda yaga 7:41 am, wato har minti ɗaya ya ƙaru akan ganinsa na ɗazu. Cikin hanzari ya tashi daga kwancen da yake, duk da cewar ba shi da wani kuzari ajikinsa kaitsaye haka ya nufi toilet, zuciyarsa cike da takaici, domin kuwa ko sallan asuba baiyi ba, abun da tunda yake a iyaka tsawon rayuwarsa bai taɓa bari yayi missing ba, matuƙar kuwa da lafiyansa. amma wani abun takaici sanadin cocaine ɗin daya shaƙa sai gashi yau har 7:41 am bai yi sallan asuba ba, treating ɗin ciwonsa yayi tare da ɗauro alwala, yazo ya gabatar da sallah. Aɓangaren Laylerh kuwa tana fita daga part ɗin M.jay ɗin kaitsaye compound ɗin gidan ta nufa, ba kaɗan ba kuwa tsawan da Abbou Jaheed ɗin ya yi mata ya tsorata ta, kasancewar tunda take da Abboun bai taɓa yi mata magana cikin irin wannan sigar ba, ako yaushe yana yi mata magana ne cikin yanayin lallaɓawa da kuma tausayi. Da tunani kala kala acikin ranta haka ta ƙarasa wajen da driver ke tsaye yana jiranta, koda drivern ya ganta buɗe mata murfin motar yayi ta shiga, cikin sauri shima yashiga tare dayiwa motar key, maigadi ne ya wangale musu makeken gate ɗin gidan, wanda hakan yabawa drivern daman cilla motar kan titi. Jin motar tasu ta hau titi ne yasata kwantar da bayanta ajikin kujeran da take kai tare da lumshe idanunta, har zuwa yanzu zuciyarta bata daina bugawa ba, kyakkyawar fuskarsa da kuma haɗaɗɗun idanunsa ne suka soma yi mata yawo acikin idanunta, wanda hakan yasa lokaci ɗaya tsikar jikinta suka mimmiƙe. Tabbas ganinsa da tayi yau ɗin yasa ta samu kanta cikin wani irin sabon yanayi me wuyar fassaruwa, yanayin daya zamar mata me daɗi kuma na musamman, tunawa da yanda sexy eyes ɗinsa keyi mata wani irin kallo ne yasa ta rungume hannayenta akan ƙirjinta, tare da sakin wani lallausan murmushi, sosai yanayin ya mata daɗi, dan taji moment ɗin har acikin jikinta, lallai ta sake yardarwa kanta cewa Yah M.Jay ɗin na musamman ne, haka kuma komai nasa me kyau ne, tuna yanayin yanda ya ɗaura hannunsa akan nata ne yasa ta saurin ware idanunta, saboda wani irin sabon shock da taji ya shigeta. Daidai lokacin kuwa suka kawo ƙofar shiga makarantar tasu. Anutse ta buɗe murfin motar ta fito, kaitsaye da ɗan sassarfa ta nufi hanyar shiga makarantar, dan kuwa baifi saura 5 minute ba ne ya rage arufe gate ɗin shiga makarantar nasu gaba ɗaya. Koda ta shiga cikin makarantar kai tsaye class dinsu ta nufa. Tana ƙarasawa cikin ajin Teemah da tun ɗazu take jiran zuwanta, tana hangota ta saki murmushi tare da ƙarasowa da gudu ta faɗa jikinta. Idanunta taɗan lumshe tare da ɗan jan jikinta baya, cikin salo da kuma yanayinta na shagwaɓan da ya zame mata jiki tace. "Auchh Teemah zaki karyani." Murmushi Teemah tayi, tare da ɗanyin fari da idanunta, cikin son bayyana abun dake cikin ranta tace. "Dole ae tunda anyimin Surprise!." Da ɗan mamaki Laylerh ta kalleta, cikin rashin fahimta tace "Surprise kuma?." "Yeah." Teemah tafaɗa tana me kamo hannun Laylerh'n suka ƙaraso kan parmanent sit ɗinsu. Bayan sun zauna ne cike da zumuɗi Teemah ta zuge zip ɗin jakarta tare da sa hannu ta ciro wata waya ƙiran iphone 8+ ta miƙawa Laylerh. Idanu Laylerh taɗan zaro cikin mamaki tace. "What?." Murmushi Teemah tayi, cike da murna tace. "Ya Mu'azamz ne ya sayamin, jiya kusan kwana nayi banyi bacci ba saboda murna." Murmushi Laylerh tayi tare da ɗan rungume Teemah'n, cikin son tayata farinciki tace. "Congrat my headache saura kuma ki bari ya hanaki karatu." Kai Teemah ta girgiza tare da cewa. "Bazan taɓa bari hakan ya kasance ba kuwa Insha Allah." Murmushi sukayi su dukansu. Shigowan malami cikin ajin nasu ne kuma yayi sanadiyar katsewar hiran nasu, inda suka maida gaba ɗaya hankalinsu kan darasin da ake koya musu. M.Jay koda ya idar da sallah ganin bashi da wadataccen lokaci ne yasa anan cikin ɗaki ya gudanar da gym ɗinsa, wanda yin hakan kuma ya ɗaukesa kusan sama da 1hour, lokaci ɗaya duk gaba ɗaya jikinsa ya jiƙe da gumi, duk da kasancewar sanyin A/C' na busawa acikin ɗakin kuwa, hakan bai hanasa fitar da gumi ba, kasancewar ya motsa jikinsa sosai, lokaci ɗaya yaji duk wani kasala da kuma bad mood ɗin da yakejin kansa aciki sun kau. Track suit ɗin dake jikinsa ya cire tare da ɗaura towel akan waist dinsa, kaitsaye ya wuce toilet dan yanaso yayi wanka. Bai wani jim acikin toilet ɗin ba ya fito, bayan ya sake treating ciwonsa inda ya naɗe wajen da sabon bandage. koda ya fito kuwa bai wani ɓata lokaci wajen kimtsa kansa ba, hakanan yau ɗin yaji yana buƙatar saka kayan da suka kasance na al'adar hausawa wato riga da wandon jumper, domin kuwa yana dasu saidai bai fiye sawa bane kawae. Kasancewar zaman da yayi a USA gaba ɗaya kullum cikin uniform yake, hakan yasa bai fiye saka wasu tarkacen kayayyaki ba. Ƙarasawa gaban drawer'n sa yayi tare da buɗe ɓangaren da yake ajiye manyan kayansa, wani haɗaɗɗen yadin getzner ya ciro wanda aka masa ɗinkin half jumper da kuma wandon pencil. koda yasa kayan kuwa sosai suka zauna ajikinsa, yayinda suka sake bayyana zallan kyau da kuma kwarjininsa. wasu black toms ya saka aƙafansa, tare da feshe jikinsa da wani fitinannen turaren Dolce & Gabbana me daɗin ƙamshi, Koda ya kalli madubi, kallo ɗaya yayiwa kansa ya ɗauke kai, domin ya riga daya sani tunda daɗewa cewa shi kyakkyawane, haka zalika komai nasa me kyau ne, don haka baya buƙatar duba madubi. Sanin cewa Abbou Jaheed na jiransa a falo ne yasa bai wani tsaya bata lokaci ba kaitsaye ya nufi falon. Koda ya ƙarasa cikin falon kuwa zaune suke dukansu ciki kuwa harda Alhaji Ahmad Rufae da kuma Najeeb, sai Momy dake zaune agefensu. Ganinsu a zazzaune ne yasashi ƙarasowa cikin falon, cikin girmamawa ya gaishe da Alhaji Ahmad Rufae, fuska asake Alhaji Ahmad din ya amsa masa. Ɗan haɗe fuskarsa yayi, tare da maida asalin mood dinsa na Soldier ya miƙawa Najeeb dake zaune hannu sukayi musabaha, yayinda zuciyar ko wannensu da abun da take saƙawa. kan kujeran dake facing na Abbou Jaheed ya zauna, batare daya kalli Momy ba yace mata. "Good Morning!." Momy da tasan cewa da ita yake ne yasa ta washe baki, fuska asake ta amsa masa gaisuwar tasa, dan har acikin ranta so take tasamu karɓuwa awajensa, domin ta hakanne kaɗai zata iya cimma buri da kuma ƙudurin dake ranta, wanda alƙawari ne ta ɗaukar wa kanta, cewar dashi zata yi amfani wajen ruguza rayuwar Laylerh. Abbou Jaheed wanda dama tuntuni zuwan Maleek ɗin yake jira ne ya ɗago kansa, tare da ɗanyin gyaran murya, cikin yanayin dattako irin nasa yace. "Alhamdulillah ban taraku anan dan na sanar daku wani abu na daban ba, saidan sanin cewa dukanku kuna da haƙƙi akan maganar da zanyi." Ɗan numfasawa Abbou Jaheed ɗin yayi tare dayin gyaran murya, kana yace. "Na tsaida lokacin auren Laylerh da Najeeb nan da makonni uku masu zuwa. ina fatan kuma dukanku zakuyi farinciki da hakan." Tamkar Sukan kifiya akan ƙahon zuciyarsa haka yaji sauƙan kalaman Abbou Jaheed ɗin acikin kunnuwansa. Idanunsa ya rumtse domin ko kaɗan bayason sake jin wani batu daya danganci auren Laylerh'n, wanda yayi imani hakan zai iya fasa masa zuciya. (Wayyo Bacci😪😓😭😴) *3/December/2020. time 9:50 pm* 1/19/21, 8:12 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna *(This book is mainly for those that pay, if you know you did'nt pay please don't read it. Here is the account number for people that are willing to pay-0002214625 Abubakar Muhammed Sardauna Jaiz Bank. Whatsapp Number 07017879464)*                    *Chapter 16* Zaune suke ita da Teemah aƙasan wata bishiyar flower, wanda kuma da yawan lokuta sukan zauna awajen ne,  idan suka fito break. Sassanyar iskan bishiyan dake hura duk ilahirin jikinta ne yasa ta lumshe idanunta,  tare da sakin ajiyar zuciya me ƙarfi, wani irin daddaɗan yanayi ta samun kanta aciki, wanda kuma hakanne ya taimaka wajen gusar mata da kaso 40 acikin 100 na damuwar dake kwance acikin ranta.   kallonta ta mayar ga Teemah dake ta  aikin latsa wayarta, time to time take sakin murmushi, wanda hakan ke bayyana cewar tana jin dadin abun da takeyi acikin wayar tata, zubawa Teemah'n idanu tayi, yayinda lokaci ɗaya kuma maganar auren ta da Najeeb ya dawo cikin tunaninta, wanda hakan yasa ta lumshe kyawawan idanunta, take kuwa wani irin faɗuwar gaba da tsoro suka sauƙar mata, in one second duk wani yanayin nishaɗin da takejin kanta aciki ya kau,  wanda hakan yasa  damuwa ta maye gurbin farincikin dake kan fuskarta.        Teemah kuwa da take buga game din zombie high way awayanta  ba tare da ta ɗago kai ta kalli Laylerh'n  ba tace.   "Babe  kinsan yanda game ɗinnan keda daɗi kuwa?."         Laylerh da tun ɗazu idanunta ke alumshe, yayinda ta faɗa wata duniya ta daban, hakan yasa sam bata ji abun da Teemah'n ta faɗa ba, hasalima gaba ɗaya hankali da nutsuwarta ba'ajikinta suke ba.    Jin shiru Laylerh'n bata amsa  bane yasa  Teemah ta cire kai daga kallon  wayarta ta, tare da ɗagowa ta kai dubanta  zuwa ga inda Laylerh'n ke zaune.          Ganin Laylerh'n tayi shiru ne yasa ta ƙira sunanta, cikin yanayin mamakin sauyawan mood ɗinta lokaci ɗaya.       Laylerh kuwa kasancewar har  zuwa yanzu bata cikin nutsuwarta, hakan yasa still bataji ƙiran sunan ta da Teemah'n tayi ba.          Idanu Teemah ta zuba mata, domin bata taɓa ganin Laylerh'n acikin matsananciyar damuwa irin wannan ba, gane cewa da gaske Laylerh'n ta tafi duniyar tunani ne yasa Teemah ɗan buga kafaɗarta, cikin kulawa tace.  "Wai meye haka Laylerh?.".  Jin Teemah ta taɓata ne yasa ta buɗe idanunta wanda sukayi jajur dasu.                "Tunanin me kikeyi?." Teemah ta tambaya tana me tsareta da idanu.          Ƙasa tayi da kanta haɗe da fesar da wani irin numfashi me zafi, tabbas tasan cewa agaba ɗaya rayuwarta bata da wata ƙawa ko Ć´ar uwa sama da Teemah, duk da kasancewar tasan ƙwaƙwalwa da kaifin hankalinsu iri ɗaya ne da na Teemah'n, amma tanaji ajikinta cewa Teemah zata iya warware mata wani  abu daga cikin matsalarta, hakanne kuwa yasa taji zuciyarta ta aminta da ta faɗawa Teemah'n damuwarta.          Ganin yanda idanun Laylerh'n suka ciko da ƙwalla ne yasa Teemah cewa.  "Ganin hawaye a idanunki, da kuma shirun da kikayi, hakan alamace dake nuna cewar lallai akwai damuwa atattare dake,  meyake damunki Laylerh,  ko Abbou Jaheed ne zai koma Polland?."          Idanunta ta lumshe tare da girgida kai alaman "Aa."      Ajiyar zuciya Teemah ta sauƙe, cikin halin nuna kulawa tace.  "Okay tell me whats wrong? ba kuma naso ki ɓoyemin komai dan Allah!."      Jin abun da Teemah'n  ta faɗane yasa idanunta sake cikowa da ƙwalla, kanta dake ƙasa ta ɗago tare da duban Teemah wanda ta tsura mata ido.    Ganin ruwan hawayen dake cikin  idanun Laylerh'n sun ƙaru ne, yasa Teemah zaro idanu, cikin yanayin mamaki tace. "Laylerh kuka kuma? Please  ki faɗamin meke damunki da har ya saki kuka!."            Ayanda takejin zuciyarta, yasa  batajin zata iya ɓoyewa Teemah komai,  kuma ya zama dole ta faɗawa Teemah'n  koda hakan zaisa taji sanyi acikin ranta, ƙoƙarin shanye hawayen nata tayi, cikin sanyi da kuma muryar dake bayyana rauninta tace.  "Teemah Aure Abbou Jaheed zai yimin, zai aurar dani ga wani daban, wanda bansan cewa yana sona ko baya sona ba, tsoro nakeji Teemah bansan ya ake zaman aure ba, bansan ta ina zan fara ba, zuciya ta da ƙirjina bugawa suke, inajin gaba ɗaya duniyar bata min daɗi, haka nakejin tamkar zan rasa wani abu ne da yafi komai mahimmanci arayuwata!."  Ta faɗi maganar hawayen dake cikin idanunta suna me sauƙa akan fuskarta.   Idanu Teemah ta ɗan zaro cikin yanayin mamaki tace.   "Aure kuma Laylerh? wai kina nufin Abbou Jaheed da kansa yace zai aurar dake? waye zai aura miki to?."    Teemah tayi mata duka waĆ´annan tambayoyin alokaci ɗaya, domin ba kaɗan ba maganar auren Laylerh'n  ya shigeta.          Guntun hawayen da suka ɗan gangaro daga cikin idanunta ta share, araunane tace.  "Ki taɓa saitin zuciyata kiji Teemah, gaba ɗaya fargaba ne ya cika cikinta,  sannan inajin wani abu me zafi na sukana."      Tsagaitawa da maganan tayi tare da kamo hannun Teemah ta ɗaura adaidai saitin zuciyarta, cikin wani irin yanayi tace.  "Tabbas inada buƙatar sanin haƙiƙanin abun da nakeji acikin zuciyata Teemah, ki taɓa zuciyata da kyau kiji, sam bata da nutsuwa, haka zalika tunani da komai na akansa ne, yanzu na, anjima na, da ma ko yaushe na,  inajinsa yana gudana ajikina tamkar yanda  jini ke gudana, haƙiƙa nayi imani cewa matuƙar na cigaba da rayuwa ahaka wannan yanayin zai illatamin zuciya da kuma gangar jiki, please Teemah ki faɗamin  me yasa nakejinsa ako yaushe? ko acikin baccina shi nake gani, ko wani bugun zuciyata da tunani haɗe da komai nasa yake tafiya, shin me hakan yake nufi ki faɗamin dan Allah tun kafun narasa hankali na!."          Idanu Teemah ta zuba mata akaron farko kenan da taji ajikinta cewa, ƙawartata  ta samu zaucewar ƙwaƙwalwa.  Riƙo hannun Laylerh'n tayi da kyau cikin rashin fahimtar inda kalaman Laylerh'n suka dosa tace.   "Ki dawo cikin hayyacinki Laylerh, kada ki bari ki zautar da kanki akan abun da gaskiyarsa yake abayyane, bansan akan wa kike magana ba, ki faiyyace min komai ta yanda zan fahimta, sannan kidaina waĆ´annan kalaman masu wuyar fahimta please!."              Jin abun da Teemah'n ta faɗa yasa ta lumshe idanunta, tare da ɗan soma girgiza kai, akaron farko kenan da ta riga ta fahimci cewa Teemah, bazata iya warware mata tsalarta ba, haka zalika kuma ba zata taɓa fahimtar abun dake cikin rai da zuciyarta ba, "Why ƙaddara zata zo mata da nauyi me girma irin haka?, nauyin da har takai ga tanajinsa kaman zai fasa mata ƙwaƙwalwa." Lallai bata da mafita wanda kuma hakan yasa taji duk gaba ɗaya zaman makarantar ya isheta,  miƙewa tsaye tayi, tare da sa hannu ta dafe kanta da lokaci ɗaya taji yana sara mata.  Kallonta Teemah tayi tare da cewa.  "Ina kuma zakije?."    "Class!." ta bata amsa asanyaye batare kuma da ta jirayi komai ba ta fara tafiya.   Ɗan jim Teemah tayi na wasu lokuta tare da binta da idanu, itakam sam bata fahimci komai akan lamarin Laylerh'n ba, hasali ma gani tayi kaman Aljanu ne ke damunta. Ganin cewar da gaske tafiya class Laylerh'n zatayi ta barta yasa cikin hanzari ta rufa mata baya.                     MALEEK.   Duk yanda yaso daidaita nutsuwarsa ya kasa, baisan meyasa  jin duk wata magana da ta shafi auren Laylerh'n ke matuƙar haukata masa tunani ba,   idanunsa da sukayi ja ya lumshe tare da sa tafukan hannunsa ya rufe kyakkyawar fuskarsa,  lokaci ɗaya duk wasu maganganun da Abbou Jaheed  da kuma Alhaji Ahmad ɗin keyi, suka daina shiga cikin kunnuwansa, domin gaba ɗaya zuciyarsa tatafi izuwa wani waje na daban.              Abbou Jaheed wanda suka gama tattaunawa da Alhaji Ahmad Rufae, akan maganar auren Laylerh'n ne ya ɗago da kansa, tare da dawo da kallonsa ga Maleek wanda har yanzu bai buɗe fuskarsa dake arufe da tafukan hannunsa ba.           "Maleek!." Abbou Jaheed ya ƙira sunansa cikin nutsuwa.               Jin sautin muryar Abbou Jaheed ɗin acikin kunnensa ne ya sashi ɗan janye tafin hannunsa daga kan fuskarsa, idanunsa da suka kaɗa sukayi jajur ya buɗe haɗi da yin ƙasa dasu, kasancewar sam bayaso ayanzun kowa ya fahimci irin situation ɗin da yake ciki, cikin wata irin murya dake son ɓoye damuwarsa yace.  "Na'am."     Ɗan zuba masa idanu Abbou Jaheed ɗin yayi, ahankali ya sauƙe ajiyar zuciya tare da cewa. "Sama da shekara 2 kenan yanzu dana zuba maka ido inason naga gudun ruwanka, saidai kuma na lura da cewa kwata kwata babu tunanin aure acikin ƙwaƙwalwarka, saboda haka kasa aranka cewar, kamar yanda na zaɓawa Laylerh Miji, na kuma sa aurenta lokacin ɗaya,  haka kaima zanyi maka, saboda haka ya rage naka a iya lokacin daya ragema ka nemo matar aure, idan kuma ba haka ba dakaina zan nemo maka wacce zata dace dakai."            Jin abun da Abboun ya faɗane yasashi ɗago kansa, hakanan yaji kalaman Abbou Jaheed ɗin kaman tatsuniya, duk da kuwa yasan cewa duk abun da Abbou Jaheed ɗin yafaɗa tabbas zai iya aikatawa, amma kwata kwata bayaji ajikinsa cewar zai rayu da wata mace.         Idanunsa ya ɗan lumshe tare kuma da sakin wani murmushi, wanda iya kansa laɓɓan bakinsa, tabbas ya yarda da cewar, muradi da kuma fata ɗaya ne acikin zuciyarsa, wanda kuma rashin samun cikar burinsa daidai yake da ƙin yin aurensa har abada. Sama da 10 years kenan daya ɗauka yana dakon abubuwa da yawa acikin rai da zuciyarsa,  tun baisan me yakeyi ba, tun kuma baigane me yake ji ba, har hakan ya cakuɗa da numfashinsa, ya zamanto bugun zuciyarsa, duk wani zafi da yakeji ya jure, ako yaushe akuma ko wacce rana buri ɗaya ne ke yawo acikin zuciyarsa, wanda kuma ayanzu wannan fata da burin suka cika da tarin ƙaddarori masu wuyar ɗauka.    Ahankali ya miƙe tsaye dan bayajin zai iya cigaba da zama acikin falon.     Batare daya cewa kowannensu ƙala ba, kansa tsaye ya nufi hanyar ƙofar fita daga cikin falon. Hakanne kuwa yasa duk suka bisa da kallo.      Saidai kuma banda Najeeb wanda ayanzu yake ƙoƙarin gaskata zargin dake cikin zuciyarsa, saidai kuma koma meye bayajin zai iya barin abun da ayanzu ya gamsu cewar lallai yanaso.              Koda ya fita daga cikin falon kaitsaye compound ɗin gidan ya nufa, inda ma aikata kota ina keta hidimomi, masu bawa flowers ruwa, da masu wanke cars duk suna aikinsu. Direct babban parking space ɗin gidan ya nufa, wanda kuma ananne tarin motocinsa ke fake. Abdoul dake zaune ganin Ogan nasa ya fito, yasa cikin sauri ya taso tare da ƙarasowa inda yake, cikin girmamawa yace.  "Good Morning Sir."   Kansa kawai ya iya jinjina wa Abdoul ɗin, wanda hakan ke nuna cewa ya amsa.  ƙarasawa jikin wata haɗaɗɗiyar sabuwar motarsa ƙiran Mercedesbenz CLA 35 yayi, ganin hakanne yasa Abdoul gane cewa yau ogan nasa mercedes ɗin yake son hawa. Cikin hanzari kuwa ya ciro key ɗin motar, tare da buɗewa M.Jay ɗin murfin motar ya shiga,  shikuwa Abdoul kamar yanda ya saba, nan wajen zamansa na driver ya shiga tare da murzawa motar key, cikin ƙwarewa ya fitar da ita daga parking space ɗin, maigadi dake tsaye kuwa  yana ganinsu ya wangale masu gaba ɗaya gate ɗin gidan,  cikin ƙwarewa Abdoul ya cilla hancin motar waje, sanin inda ogan nasa yafi zuwa idan yana cikin garin na Abuja ne,  yasa batare daya tsaya wani ɓata lokoci ba ya miƙi hanyar da zata kaisu Maitama Estate.    Ɓangaren Laylerh kuwa tun komawarsu class ta samu kanta da kasa iya aiwatar da komai, hakanan ta zama wata so silently, yayinda gaba ɗaya tunani da nutsuwarta suka ƙaura izuwa wani waje na daban, sanadin hakan kuwa yasa duk wani malamin da zai shigo yi musu lecture bata taɓa fahimtar komai akan hakan, saboda hakanan takeji kaman anshafe mata ƙwaƙwalwa.         Yayinda acikin ranta kuwa fata da kuma burin son sanin haƙiƙanin abun dake cikin zuciyarta ne, duk ya hanata sukuni, haka kuma duk yanda Teemah taso Laylerhn ta saki jikinta kasawa tayi, duk kuwa yanda taso ta ɓoye damuwarta ta kasa. Ahaka har aka tashe su daga makarantar, kamar kullum kuma kamar koda yaushe tare suka jero suna tafiya, ahaka har suka fito daga cikin makarantar, suna fitowa kuwa kowaccensu tasamu driver na jiranta.  Laylerh da tatafi zata shiga mota ne, Teemah ta riƙo hannunta, wanda hakan yasa tafasa shiga motar ta juyo ta fuskanci Teemah'n.   Idanu Teemah ta ɗan lumshe cikin sanyin muryar dake bayyana tausayin ƙawarta ta tace.   "Please Laylerh ki daina damuwa kinji, kisa aranki cewa auren da Abbou Jaheed zai miki shine mafi alkhairi agareki, kuma nasan Abbou Jaheed bazai taɓa zaɓa miki mijin daya san zai cutar dake ba, dan Allah ki daina sa damuwa aranki kinji please!!."   Teemah'n ta ƙare maganan tana me haɗe hannuwanta biyu waje ɗaya, wanda hakan ke nuna alaman roƙo.     Ayanayin da take ciki yasa batajin zata iya cewa Teemah'n komai, domin yanzu babu abun da takeson gani da ji, kamar M.Jay. ɗan lumshe idanunta tayi tare da jinjinawa Teemah'n kai alaman  "To."  Murmushi Teemah tayi mata, sannan ta juya ta nufi wajen da motar gidansu ke fake.    Asanyaye ta shige motar tare da ɗan kwantar da kanta asaman kujera tana maida numfashi, ahaka drivern yaja suka bar harabar makarantar. Maitama Estate. Tsaye yake agaban wani  haɗaɗɗen glass frizer, yayinda hannunsa ke riƙe da zungureriyar kwalban wine, sai kuma wani ɗan ƙaramin glass cup da ya riƙe a hannun damansa, ahankali yake ɗan jujjuya cup ɗin, wanda ya riga daya zuba wine ɗin aciki, yayinda gaba ɗaya tunaninsa ya tafi izuwa wani waje daban.     Idanu wani haɗaɗɗɗen gayen dake zaune akan ɗaya daga cikin kujerun falon ya zuba masa, *Fou'ad* kenan tabbas yana mamakin hali irin na abokin nasa, ajiyar zuciya ya sauƙe akaro na barkatai, ɗan gyara zamansa yayi cike kuma da ƙaunar abokin nasa yace.   "Meyasa kake ɓoye sirrin dake cikin zuciyarka Maleek? batun yauba nasan kana ɗauke da damuwa, wanda ko da ace baka faɗa ba, gaba ɗaya yanayinka ya nuna hakan, meyasa kake ɓoye abunda ke cikin zuciya da ƙirjinka?, meyasa kake ƙoƙarin haramtawa kanka abun da Allah Ya halatta ma? ya kamata ka farka daga wannan nannauyan baccin da kake, because yanzu rayuwa ta sanja, then zurfin ciki baya kawo komai sai dana sani, meyasa ako da yaushe kake tauyewa zuciyarka haƙƙinta bayan kuma kasan ta kamu da SO matsananci?."           Idanunsa ya ɗan lumshe  tare kuma da buɗesu alokaci guda, Ajiye kwalban wine ɗin dake hannunsa yayi, ahankali cikin nuna halin ko in kula ya ƙaraso cikin falon, kan wata kujera dake facing na Fou'ad din ya zauna, ba tare kuma da ya kalli Fou'ad ɗinba, cikin husky voice ɗinsa  yace.  "So? menene kuma SO?... its in possible, because i dont have any feeling in my mind."                 Murmushi Fou'ad yayi domin shi yariga daya san waye Maleek, ya kuma san komai agame dashi, taurin rai dana zuciya tamkar aminai suke awajensa, kwata kwata baya taɓa ɗaukan kuskurensa, always gani yake shi akan daidai yake.      Miƙewa tsaye Fou'ad ɗin yayi tare da ƙarasawa wajen da Maleek ɗin ke zaune, hannunsa ya ɗaura akan shoulder ɗinsa, cikin kulawa yace.  "SO ne Maleek, ni nayi imani cewa akwai so acikin zuciyarka, meyasa kake ɓoyewa? meyasa bazaka iya faɗa ba? Meyasa....."         "Enough Fou'ad, Enough is Enough please!!."  Maleek din  yafaɗi haka ta hanyar katse Fou'ad daga maganan da yakeyi.  Bayajin zai iya jurewa jin kalaman da yawancin lokuta Fou'ad ɗin ke faɗa masa, wannan dalili yasa sometimes bayason zuwa wajen Aboki kuma Aminin nasa, saboda ako yaushe so yake saiya ƙuresa.   Wayayoyinsa dake aje kan table ya ɗauka, batare da ya kalli Fou'ad ɗin ba ya juya ya nufi hanyar fita daga falon.    Da kallo Fou'ad ya bisa har ya fice daga cikin falon. Murmushi yayi tare da komawa kan kujera ya zauna, daman ya sani ako da yaushe Maleek ɗin baya karɓan gaskiya aduk yanda tazo masa.               Abdoul dage zaune aharabar gidan Fou'ad ɗin kuwa, ganin yanda Ogan nasa ya fito kaman afusace ne yasashi saurin tashi tsaye, cikin hanzari ya ƙarasa jikin mota, tare da buɗewa Maleek ɗi murfin motar yashiga.  Shiɗin ma shiga yayi, yayinda tun kafun yaja motar yayiwa gateman alaman ya buɗe Musu gate ɗin zasu fita, ba ɓata lokaci kuwa gateman ɗin ya wangale musu gate ɗin gidan suka fice.      Koda suka fara tafiya lumshe idanunsa yayi, yanamejin yanda sanyin A/C ke ratsa dum jikinsa. kalmar "SO" da Fou'ad ya faɗa ita keta yi masa yawo acikin ƙwaƙwalwarsa,  hakanan yaji ya tsani kalmar domin yayi imani cewa abun da yakeji acikin zuciyarsa ya fi karfin aƙirasa da sunan SO, tabbas kalmar SO tayi kaɗan ta ɗauki nauyin abun daya jima yana sukar zuciyarsa. Ɓangaren Laylerh kuwa tunda suka ɗauki hanyar dawowa gida bata buɗe idanunta da suke alumshe ba, ahankali kala kalan tunani ke cika zuciyarta, yayinda wani irin maganaɗisun son ganinsa ke yawo ajikinta. Jin tsayuwar motar tasu ne yasa ta gane cewar sun iso gida. Ahankali ta buɗe idanunta tare da ɗaukan school bag ɗinta dake gefenta, anutse ta buɗe murfin motar ta fito, batare da ta tsaya sauraran komai ba kuwa ta nufi haɗaɗɗiyar ƙofar da zata sada ta da babban falon gidan, koda ta ƙarasa jikin ƙofar ahankali ta murɗa handle din ƙofar ta shiga falon bakinta ɗauke da sallama, babu kowa acikin falon sai tv plasma dake ta faman ɓaɓatu shi kaɗai. Kasancewar agajiye take jin kanta yasa kaitsaye ta nufi hanyar da zai sadata da ɗakinta. Yanayin yanda ta sadda kanta ƙasa ne yasa sam bata ma lura dashi ba. Najeeb dake tsaye idanunsa yaɗan lumshe tare da sakin ajiyar zuciya, tsawon 10 minute kenan daya ɗauka atsaye yana jiran dawowarta. Ganin zata wuce batare da ta ganshi bane yasashi kamo hannunta. Wanda hakan yasa ta juyo amatuƙar razane, tare kuma da ƙoƙarin fasa ihu saboda ta tsorata sosai, cikin sauri yasa hannunsa ya toshe mata baki, tare da ɗan soma girgiza mata kai, alaman kada tayi ihu. Faɗawar idanunta cikin nasa ne yasata sauƙe wata ƙatuwar ajiyar zuciya tare da lumshe idanunta, murmushin daya bayyana asalin kyawun fuskarsa yayi, cikin silently voice yace. "Matsoraciya kawai!." Jin yace mata matsoraciya ne yasata buɗe idanunta, tare kuma da daidaita nutsuwarta, cikin yanayin shagwaɓan daya zame mata jiki tace. "To meyasa zaka tsoratani?." "Saboda inason sanin wace irin mata zan aura!." Yafaɗa yana me bin duk jikinta da idanu. Jin da tayi ya ambaci aure ne yasa ta ɗago manya manyan idanunta ta kallesa. Wani irin yaaarrr yaji ajikinsa sakamakon kallon da tayi masa, hakanne kuma yasashi kamo hannunta duka biyu ya riƙe ƙam acikin nasa, ahankali ya matso gab da ita wanda har hakan yasa numfashinsu gauraya dana juna. ahankali idanunsa suka ɗan fara lullumshewa, cikin muryarsa da ta sanja amo yace. "INASONKI Laylerh, Inasonki sosai da sosai!!." Yanayin yanda ya ƙare maganar cikin wani irin tone ne yasata lumshe idanunta, wanda sanadin hakan yabasu daman sake kusanci da juna sosai, still kuma har yanzu hannayenta na cikin nasa. Daga waje kuwa ahankali Maleek ya ɗaura hannunsa akan handle din ƙofar shigowa falon, kasancewar ƙofar ba akulle take bane yasa take ta buɗe, sako kansa cikin falon da yayi ne, ya sashi sauƙe idanunsa akansu. *5/December/2020* 1/19/21, 8:12 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna *(This book is mainly for those that pay, if you know you did'nt pay please don't read it. Here is the account number for people that are willing to pay-0002214625 Abubakar Muhammed Sardauna Jaiz Bank. Whatsapp number 07017879464.)* *Chapter 17* Mummunan ganin da idanunsa sukayi ne yasa lokaci ɗaya yaji wani irin abu me nauyi ya daki ƙirjinsa, wanda hakan ya tilastawa zuciyarsa bugawa da ƙarfi, idanunsa da suka zama jajaye ya rumtse tare kuma da dunƙule Ć´an yatsun hannunsa, wani irin tafasa yakejin zuciyarsa nayi, ga kuma wani ɗaci da ya mamaye maƙoshinsa. haƙiƙa wannan yanayin baƙone awajenta, irin wanda bata taɓa samun kanta acikinsa ba, tabbas a iyaka tsawon rayuwarta bata taɓa kusanci da wani namijin da ba muharraminta ba kamar yanda Najeeb ya tilasta mata yi ayau ɗin. Yanayin yanda hucin numfashinsa ke dukan beauty face ɗinta ne yasa gaba ɗaya tsikar jikinta mimmiƙewa, ahankali ta ɗan soma jan jikinta baya, domin bazata iya jurewa kusancin nasu ba, wanda sanadin hakanne yasa taji jiri na ƙoƙarin ɗibanta. Samun kansa cikin wata sabuwar duniya ta daban da yayi ne, yasa wani irin zazzafan shauƙi ya soma ɗibansa, sosai yanayin ya masa daɗi, kasancewar bai taɓa samun kusanci da ita har haka ba, Jin da yayi tana ƙoƙarin nisanta kanta da shine yasa shi sake damƙe hannunta dake cikin nasa, cikin wani irin yanayin da yakejin kansa aciki yace. "Please Laylerh faɗamin kina sona?" Jin tambayan da yayi mata ne yasata buɗe tsumammun idanunta, tare da sauƙesu akansa, wani irin kallo takeyi masa wanda ke nuna kamar bata fahimci abun da yake faɗa ba, hasalima ayanayin da take ciki kamar bata gane komai. Shi ɗinma idanunsa wanda suka juye izuwa kalan bacci ya zuba mata baya ko ƙiftawa,ahankali yakejin ƙaunarta na mamaye duk wani sassa na jikinsa. kwata kwata batajin zata iya ci gaba da kallon cikin idanunsa, wanda yanayinsu ya riga da ya sauya, har takai ga tana hango wani abu na daban acikinsu, ahankali tayi ƙasa da kanta tare da ɗan lumshe idanunta, hakanan taji kirjinta na bugawa, yayinda wani irin abu me kama da fargaba haɗi da tsoro suka nemi mamaye dukkan sassan jikinta, sanyi da kuma iskan da taji na ratsa cikin tafin ƙafanta ne yasa zuciyarta fara yi mata wani tunani na daban. Har zuwa yanzu idanunsa akulle suke, domin azahirance bayajin zai iya jurewa kallonsu a irin yanayin da suke ciki, har zuwa yanzu ƙuna da raɗaɗi yake ji acikin zuciyarsa, haka yakeji kamar ana caka masa mashi aƙirjinsa, haƙiƙa da ace yasan shigowarsa cikin falon zai gusar masa da Ć´ar nutsuwar da tayi masa saura, to tabbas da ya hana kansa ahigowa falon. Idanunsa da sukayi jajur ya ware, yayinda tuni gashin jikinsa suka soma mimmiƙewa, lokaci ɗaya kuma fuskar sa tayi ja, kasancewar yaji tambayar da Najeeb din yayi mata ne, yasa zuciyarsa soma tafarfasa, domin jin amsar da Laylerh'n zata bashi daidai yake da hargitsewan tunani da ƙwaƙwalwansa. Amatuƙar fusace ya saki handle ɗin ƙofar falon, wanda sanadin hakan yasa ƙofar falon rufewa da wani irin ƙarfi. Jin ƙaran ƙofar ne yasa Laylerh da ta bawa ƙofar shigowa falon baya tayi saurin juyowa. Ganin M.Jay dinne yasa zuciya da ƙirjinta yin wani irin tsalle kamar zasu faɗo ƙasa, cikin wani irin masifaffen tsoron daya shigeta tayi saurin janye hannunta daga cikin na Najeeb ɗin tare da ɗan matsawa gefe. Ɗauke kansa yayi daga kallonsu tare da kawar da idanunsa da suka soma ganin dishi dishi zuwa wani waje na daban, cikin wani irin taku dake nuna zallan isa da taƙama irin na cikakkun soldiers, ya nufi hanyar part ɗinsa, sam bai yarda ya sake kallonsu ba, hasalima yi yayi kamar baisan dasu acikin falon ba. Idanunta da sukayi raurau kana suka ciko da hawaye ta lumshe, ji tayi gaba ɗaya zuciyarta ta karye, yayinda taji wani irin haushin kanta ya kamata, hakanan taji ajikinta cewa kamar bata aikata daidai ba. " Shin meyasa tabari Najeeb ya riƙeta? Meyasa?." tayiwa kanta tambayar da babu wani me amsa mata ita. Najeeb wanda ya zura hannayensa cikin aljihun wandon jumper'n dake jikinsa ne ya sauƙe ajiyar zuciya tare da ɗan lumshe idanunsa, sahirtaccen murmushi ne ya bayyana akan fuskarsa wanda har hakan yasa fararen haƙwaransa bayyana, idanunsa ya zubawa Laylerh'n wanda ta riga da ta basa baya. Hannunsa ya ciro ahankali ya dafa shoulder ɗinta, cikin yin ƙasa da murya yace. "Meyasa kika juyamin baya?." Idanunta dake cike da tarin ƙwalla ta lumshe akaro na barkatai, kaman kuwa jira hawayen nata suke ta lumshe idanun nata, ahankali suka ɗan gangaro kan fuskarta, jin hawayen nata sun zubo ne yasa cikin sauri ta kai hannun ta share, tare da ɗan jan jikinta gefe, ahankali kuma ta soma ƙoƙarin zame hannunsa daga kan kafaɗanta, dan hakanan taji duk komai ya daina yi mata daɗi. Ganin yanda take ƙoƙarin zame jikinta ne yasa Najeeb sanya hannayensa duka biyu ya juyo da ita, suka zamana suna fuskantar juna. Cikin sauri ta rufe idanunta dan kuwa kwata kwata batason sake haɗa idanu dashi, duk da kuwa kasancewar bata gama sanin menene ainihin haƙiƙan abun dake cikin zuciyarta ba, saidai batajin zata iya bari ya fuskanci rauninta, sanin da tayi cewa ayanzu babu komai acikin ƙwayoyin idanunta face rauni. Sauƙe idanunsa akan zara zaran eye lashes ɗinta dake ɗauke da danshin hawaye yayi. "Laylerh!!." Yaƙira sunanta cikin wata irin murya me ratsa jiki da zuciya. Sanyin muryan nasa da ya ratsa kunnuwanta ne yasa ta buɗe idanunta ahankali, saidai bata yarda ta sauƙe ganinta akansa ba. Kyakkyawan fuskanta da kuma kyawawan laɓɓanta yake kallo, ahankali yakejin wani irin shauƙi na sauƙar masa, hakanne kuma yasashi ɗan lumshe idanunsa tare da jan wani dogon numfashi, ahankali ya janye hannayensa dake kan kafaɗunta tare kuma da ɗan shafa gefen fuskarta, cikin wata irin silent voice me ɗauke da sassanyan amo yace. "Ke kyakkyawace Laylerh, salon kyaun ki na daban ne, haka zalika duk wani sirrin kyau akwaishi atattare dake, please ki kulamin da kanki kinji, sannan kuma kimin kwalliya me kyau anjima zanzo zance wajenki, kamar yanda kowani saurayi yake zuwa wajen budurwarsa!." Idanunsa ya lumshe tare kuma da buɗesu alokaci ɗaya, hancinta ya ɗan ja cikin kulawa yace. "Take care!." Raɓawa yayi ta gefenta ya wuce, wanda sanadin hakan yasa jikinsu gogan na juna. Idanunta ta lumshe tare da jingina bayanta ajikin bango, sam ko ɗaya kalamansa basu shigeta ba, hasalima kwata kwata bata fahimci inda kalaman nasa suka dosa ba, abu ɗaya kawai tasani shine yanayin da taga M.Jay ɗin aciki, domin yanayin nasa, ya nuna cewar akwai zallan damuwa atattare dashi. Jin zuciyarta na ƙara raunana ne yasa ta jan ƙafafunta da takejin sun mata nauyi ta ƙarasa bakin ƙofar shiga ɗakinta, ahankali ta murɗa handle ɗin ƙofar ta shige ciki. M.Jay Ahankali ya maida ƙofar bedroom ɗin nasa ya rufe, cikin wani irin huci da yakejin zuciyarsa nayi ya tura duka hannayensa biyu cikin aljihun wandonsa, idanunsa dake alumshe ya ware, sakamakon yanda suka ɗauko masa hotunan Laylerh'n da kuma Najeeb riƙe da hannun juna. "Ki na sona?" maganan da Najeeb ɗin ya faɗa kenan, dake ta yimasa yawo acikin ƙwaƙwalwa da zuciyarsa, sanadin haka kuwa ƙirjinsa ke ƙara yi masa zafi, kwata kwata yakasa fahimtar me hakan yake nufi, tunowa da wani abu da yayi ne yasa shi ɗan soma girgiza kansa, lallai ya yarda cewa gaba ɗayan rayuwa ƙaddara ce, dake iya sanjawa ako da yaushe, kana kuma yayi imani cewa shima tasa rayuwar ƙaddarace, saidai kuma tasa ƙaddaran ta banbanta dana kowa, domin sosai take hurting mind ɗinsa, akaron farko kenan da yaji yayiwa Najeeb wani irin mugun tsana, tsana mafi tsanani, kuma irin tsanar da bai taɓa yiwa kowa irinta ba. Iska me zafi ya fesar daga bakinsa tare da ɗan lumshe jajayen idanunsa, sam baya jin daɗin mood ɗin daya samu kansa aciki. Nan kan saman gadonsa ya faɗa tare da sanya hannu ya dafe daidai saitin zuciyarsa dake harbawa da ƙarfi. Koda ta ƙarasa cikin ɗakin nata, asanyaye tasoma cire kayan uniform ɗin dake jikinta, haka takejin gaba ɗaya komai ba yayi mata daɗi, gefe guda kuma ga wani abu da takeji na sukan zuciyarta, sanadin hakanne kuma yasa takejin kamar ta aikata wani abun da yake ba daidai ba, tabbas har yanzu tana da buƙatar sanin meyasa takejin feeling na musamman akan M.Jay din, meyasa idan ta gansa take rasa duk wata nutsuwarta?, haka kuma takan kasa controll ɗin kanta, musamman akan abun da takeji azuciarta dangane dashi, lallai tana da buƙatar sanin haƙiƙanin menene SO da kuma yanda akeji idan ankamu dashi, lumshe idanunta tayi asakamakon tunawa da yanda zuciyarta ke matsanancin bugawa matuƙar M.Jay ɗin nakusa da ita. "Idan wannan abun da takeji shine SO, kenan gaskiya da kuma haƙiƙanin abun da takeji acikin ranta yana nufin soyayya ne?." Tambayar da zuciyarta tayi mata kenan, wanda hakan yasa taɗan zaro idanunta waje, kasancewar sam bata shiryawa tambayar ba, kanta taɗan girgiza kana abayyane tace. "Idan kuma da gaske hakan shine SO, na kamu da son Yaya M.Jay kenan?" tayiwa kanta tambayar da bata da mafarin samun amsarta.. Still girgiza kanta tayi domin hakanan taji bata gamsu da tunanin nata ba, sanin cewa zuciyarta zatayi ta saƙa mata abubuwa da yawa ne yasa cikin sauri ta ƙarasa cire uniform ɗin dake jikinta, tare da ɗaura wani farin towel ajikinta wanda tsawonsa ya tsaya iyaka cinyoyinta. Ganin da tayi cewa ankusa ƙiran sallan Magriba ne yasa kaitsaye ta wuce toilet, kasancewar yanayin garin na yau akwai ɗan zafi ne yasanya ta haɗawa kanta ruwa acikin bathtube tare da shiga ciki ta kwanta, sanyi da kuma daɗin ruwan daya ratsata ne ya sata ɗan lumshe idanunta tare kuma da sakin ajiyar zuciya, lokaci ɗaya taji duk wani damuwan dake ranta ya soma gushewa. Samun kanta da tayi acikin wani sabon yanayi ne, yasa tayi wankan ta cikin nutsuwa, bayan kuma ta gama wankanne ta ɗauro alwala. Koda ta fito daga toilet ɗin tsane jikinta tayi da wani ɗan ƙaramin towel, wani haɗaɗɗen body lotion me daɗin ƙamshi ta shafa ajikinta, bayan lotion ɗin kuwa bata sake shafa komai ajikinta ba, domin dama yawan kwalliya ba ɗabi'arta bane, wannan yasa bata wani damu dayinsa ba. Ƙarasawa gaban sif ɗin kayanta tayi tare da buɗewa, kayannata dake jere acikin sif ta zubawa ido, tana tunanin wanda zata saka, kasancewar idan ana yanayin zafi kwata kwata bata saka kaya me nauyi ajikinta. Wani dogon wandon skin tight ta ciro haɗe da wata haɗaɗɗiyar farar armless, koda ta saka kuwa ba ƙaramin kyau kayan sukayi mata ba, musamman ma wandon daya kama jikinta sosai, har yakai ga ya bayyana tsararren hips ɗinta. Koda ta gama saka kayan kuwa har anshiga sallan magriba, aɗan gurguje ta zura ƙaton hijab ajikinta, tare da shumfuɗa wani lallausan darduma ta tada sallah. Anutse tayi sallan nata koda ta idar kuwa bata tashi akan sallayan ba, tana nan zaune har aka ƙira sallan Isha, bayan ta idar da sallan isha ɗinne tayi azkhar ɗinta haɗi da addu'o'i sannan ta miƙe tsaye, sanin cewa lokacin cin abincinsu yayi ne yasa ta cire hijab din dake jikinta, tare da ƙarasawa gaban drawer'nta, wata black kimono da aka ƙawata gaba ɗaya jikinta da adon fararen duwatsu ta ciro haɗe da sanyawa ajikinta, kasancewar kuma rigar na ɗan showing ne yasa, duk wanda ya kalleta zai hango ainihin shigar dake jikinta, ɗan kwalin rigar ta naɗa akanta, wanda kuma ya sauƙo har zuwa kan ƙirjinta. Ɗan kallon kanta tayi amadubi, ganin da tayi cewa shape ɗin jikinta bai bayyana sosai bane, yasa anutse ta fice daga ɗakin. Acan falon kuwa Abbou Jaheed da Momy ne kaɗai ke zaune akan dining table ɗin, kasancewar Alhaji Ahmad Rufae ya wuce Kaduna, M.Jay kuwa tunda ya shiga ɗakinsa ba wanda yasakejin motsinsa, sai kuma Najeeb da gabaki ɗaya ma shi baya gidan. Anutse ta shigo cikin falon, ganin Abbou Jaheed da kuma momy zaune dining area ne yasa duk taji jikinta yayi sanyi, tunowa da yanda taga mood ɗin Abbou Jaheed ɗin yauda safe ne yasa ta ɗanji fargaba ya ɗarsu acikin ranta, ganin cewa basu ganta bane yasa ta juyawa cikin sauri ta soma ƙoƙarin komawa ɗakinta. "Laylerh." Abbou Jaheed ya ƙira sunanta, wanda tun shigowarta cikin falon ya ganta. Jin Abbou Jaheed ya ƙira sunanta ne yasa ta tsayawa, ahankali cikin yanayi na ɗan fargaban da takeji acikin ranta ta juyo, ƙasa tayi da kanta tare da soma wasa da Ć´an yatsun hannunta, cikin sanyin murya tace. "Na'am." "Kizo!." Abbou Jaheed ya faɗa yana me karantar yanayinta, tabbas yasan cewa ɓacin ran daya gwada mata ayau da safe yayi mata tsauri sosai, amma ta hakane kawai zai gujewa faruwan abun da yajima yanajin tsoron afkuwansa. Asanyaye ta ƙaraso kan dining area ɗin, wanda har zuwa yanzu bata yarda ta ɗago kai ta kalleshi ba, saboda wani irin nauyi da kunyansa takeji. Gane abun dake zuciyarta ne yasa Abbou Jaheed ɗin sakin murmushi, cikin kulawa ya kamo hannunta, tare da cewa. "Zauna kici abinci!." bazata iya musa masa ba domin dama yunwa takeji, kan ɗaya daga cikin kujerun dining area din ta zauna, tare da ɗaukan plate tayi seving ɗin kanta, kasancewar tanajin yunwa sosai ne yasa ta maida hankali wajen cin abincin. Idanu Abbou Jaheed ya zuba mata cike da matsanancin tausayinta, hakanan yakeji ajikinsa cewar yanayin dayayi mata magana ɗazu da safe bai kyauta ba, wanda kuma har yanzu yanayin daya gansu aciki ita da Maleek din ya kasa barin cikin idanunsa, baisan meyasa ba yake yawan jin fargaba, akan duk wani lamari daya shefesu su biyun, duk da kuwa yasan cewar jinin Maleek ne ke gudana ajikin Laylerh'n amma yana tsoron faruwar wani abu. Ajiyar zuciya ya sauƙe tare kuma da lumshe idanunsa, tabbas akwai wata rana acikin rayuwar Laylerh Maleek din wanda baya fatan zuwanta garesa, sama da shekara 7 kenan da ya ɗauka yana nisanta tsakanin Laylerh da Maleek ɗin, ba kuma ya fatan waĆ´annan shekarun daya ɓata su tafi abanza, wanda kuma sanadin ganinsu da yayi tare ayau ɗin, yasa zuciyarsa ta raunana, yayinda yake ganin abun da yake gudu da kuma ɓoyewa yana neman tunkarosa nan kusa batare daya shiryawa hakan ba. Jin taƙoshi ne yasa ahankali taɗan ture plate ɗin abincin daga gabanta, duk da cewar bata wani ci abincin sosai ba amma haka take jin kanta aƙoshe, cup ɗin exotic ɗin dake gabanta ta ɗauka ahankali ta ke ɗan sipping drink ɗin, duk da ma kasancewar cikin zuciyarta ɗauke take da tarin damuwa na rashin ganin M.Jay ɗin da tayi awajen cin abincin, hakanan yasa duk taji ba daɗi aranta. Baƙon Ƙamshin turaren daya ziyarci hancinta ne yasa ta ɗago da ɗara ɗaran idanunta, wanda kuma hakan yayi daidai da shigowarsa cikin falon, sanye yake cikin shigar tsadaddun riga da wandon da sukayi matuƙar amsar jikinsa, kana kuma suka bayyana kyawunsa, akaron farko kenan da taji ta kasa ɗauke idanunta akansa, tabbas shi ɗinma kyakkyawane, kuma yana da abubuwan burgewa da yawa ajikinsa, kallon yanda ƙawataccen sajen dake kwance akan fuskarsa ke sheƙi tayi, wanda kuma hakan yasa suka haɗa idanu dashi, da sauri tayi ƙasa da kanta, domin sam bataso ya kamata tana kallonsa ba. Ƙarasowa dining area ɗin yayi tare da ɗan jan kujera ya zauna, fuskarsa ɗauke da murmushi yace. "Abbou barka da dare." Murmushi Abbou Jaheed ɗin yayi, fuskarsa asake cike kuma da nuna jin daɗi yace. "Yauwa Najeeb barka dai, yau kai da ɗan uwanka Maleek kun mana yajin aikin cin abinci ko." Murmushi Najeeb ɗin yayi har saida fararen haƙwaransa suka bayyana, kallonsa ya mayar gefen da Momy ke zaune, cikin nutsuwa haɗi da girmamawa yace. "Please Momy alfarma nazo nema awajenki!." Jin abun daya faɗa ne yasa Momy sakin Murmushi, kana ta faɗaɗa fari'ar dake kwance akan fuskarta, sannan cikin kulawa tace. "Faɗi koma wace irin alfarma ce ka samu." Murmushin jin daɗi yayi tare da tsaida idanunsa akan Laylerh wacce har yanzu taƙi ɗago kanta dake ƙasa. Kansa yaɗan shafa ataƙaice yace. "Dama inasone Laylerh ta min rakiya zuwa mall." Jin abun daya faɗa ne yasa Laylerh'n tayi saurin ɗago kai ta kalleshi, idanunsa ɗaya ya kashe mata, wanda hakan yasa ta turo ɗan ƙaramin bakinta gaba. Murmushin me ɗauke da ma'anoni daban daban Momy tayi, cike dason cimma manufarta akansu tace. "Laylerh ae ƙanwarka ce Najeeb, saboda haka kana da iko da ita ako da yaushe, bakomai kuje Allah Yadawo daku lafiya." Abbou Jaheed dake jin duk abun da suke faɗa ne ya saki murmushi, cinin kulawa yace. "Ni babu wanda zai tambayi izinina kenan wato nagama nawa dana ba da aure ko?." Murmushi Momy da Najeeb din sukayi, ahankali ya miƙe tsaye cikin yin ƙasa da murya yanda Laylerh'n zataji sa yace "Kisameni amota please." Baijira amsawarta ba ya juya, kaitsaye ya nufi hanyar fita daga falon. Laylerh da ta bisa da kallo ƙasa ƙasa taɗan murguɗa masa baki. "AYSHA!." Abbou Jaheed ya ƙira asalin sunanta murya asanyaye. Yanayin yanda taji muryan Abbou Jaheed din asanyaye, da kuma yanda yaƙira asalin sunanta ne yasata ɗago kai ta kalleshi, saidai tunkan yakai ga cewa komai taji zuciyarta ta tsananta bugawa, domin kuwa Abbou Jaheed ɗin bai taɓa ƙiranta da sunanta na asali ba. Abbou Jaheed kuwa hannunsa yasa acikin aljihunsa tare da soma ciro wasu bandir bandir ɗin kudi wanda aƙalla yawansu yasa zasu kai dubu ɗari biyar, anan kan saman table ɗin dake gabansu ya ɗaura kuɗaɗɗen tare da kamo hannunta ya ɗaura akan kuɗaɗen, idanunta ta zubawa Abbou Jaheed ɗin sakamakon rashin sanin abun da hakan da yayi ke nufi. Ajiyar zuciya ya sauƙe, ganin irin kallon da Laylerh'n keyi masane ya sashi gyara zama, ahankali cikin kulawa haɗe da tausayinta da yakeji yace. "Haƙƙin kowani ubane ya damƙawa Ć´arsa sadakinta atafin hannunta, saboda haka ganaki sadakin, haƙƙin ƙine kina kuma da damar da zakiyi duk abun da kikeso dashi matuƙar abun bai kaucewa ƙa'idan addini ba." Wani irin ruftawa taji zuciya da ƙirjinta sunyi, yayinda kalman "SADAKI" da taji Abbou Jaheed din yafaɗa, ya sanya lokaci ɗaya taji duk wani tunaninta ya tsaya cak, lokaci ɗaya kuma zuciyarta ta tsananta bugawa, take taji wani abu na sukan tsoka da kuma jinin jikinta, samun kanta tayi da kasa ɗauke idanunta akan Abbou'n nata, sanadin haka kuwa yasa hawaye suka cika idanunta, jikinta ne ya ɗauki rawa, wanda hakan ya bawa hawayen dake cikin idanunta daman gangarowa kan kyakkyawar fuskarta. Wani irin shu'umin murmushi Momy ta sake, tare da ɗan cije laɓɓanta, cikin zuciyarta tace. "Kin fara kuka kenan Laylerh daga yanzu har ƙarshen rayuwarki, tabbas daga kan wannan daren mummunan ƙaddaranki zata fara bibiyanki, ayau akuma cikin wannan daren zaki rasa duk wani farinciki, tabbas zakiyi kuka Laylerh kuka irin na fitar hayyaci, kukan kuwa da babu me rarrashinki." Still wani shu'umin murmushin tayi, domin kuwa ta hangowa kanta zallan nasara, wannan dama ce da ta jima tana fata da burin samu, daman kisan duk wani farinciki dake cikin zuciyar su, daman kawar wa da Laylerh budurcinta, haka kuma daman nesanta ƙauna me tsananin ƙarfi. *(Kuyi haƙuri two days bana baku update kullum kuma akan kari, wallahi bani da lapia seriously, dan Allah kuyi haƙuri dani zanna baku update duk bayan kwana ɗaya please! Kumin wannan uzurin dan Allah🙏🏻)* 1/19/21, 8:12 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna *(This book is mainly for those that pay, if you know you did'nt pay please don't read it. Here is the account number for people that are willing to pay-0002214625 Abubakar Muhammed Sardauna Jaiz bank, whatsapp number 07017879464.)* *Chapter 18* Idanu Abbou Jaheed ya zuba mata sakamakon ganin yanda hawaye ke sauƙa akan fuskarta. "Laylerh!." ya kira sunanta cikin sanyayyar murya, dake bayyana zallar damuwarsa. Haƙika zuciyarta ta riga da tayi rauni sosai, wanda sanadin hakan yasa batajin zata iya controling hawayen ta, kasa amsa ƙiran da Abbou Jaheed din ke mata tayi, saima ƙasa da tayi da kanta, saboda sam batajin akwai wani abu da zata iya faɗawa Abbou Jaheed ɗin da bakinta. Ganin yanda tayi shiru kana kuma ta sunkuyar dakai ne yasa Abbou daya zuba mata ido sauƙe ajiyar zuciya, cikin yanayin sanyi haɗi da fargaba da kuma faɗuwar gaban da yakeji ya kamo hannunta, ɗan numfasawa yayi kana kuma cike da kulawa me ɗauke da tsananin tausayinta ya ce. "Ya isa haka kidaina kuka, haƙiƙa wannan hawayen dana gani akan fuskarki, na tabbatar da cewa bawai hawaye ne na haka kawai ba, lallai akwai wani abu dake kwance aƙasan zuciyarki da kike ɓoyewa, saboda haka kamar yanda na tambayeki afarko, zan kuma sake tambayarki yanzu akaro na biyu, inaso ki faɗamin aurenki da Najeeb ne ba kyaso?." Yayi mata tambayar cikin nutsuwa me ɗauke da kulawa. Jin tambayar da Abbou Jaheed ɗin yayi mata ne yasata ɗan lumshe idanunta wanda ke cike da ƙwalla, tabbas da ace tana da dama da ta bayyana zallan abun dake ɓoye acikin zuciyarta, da ace kuma Abbou jaheed zai gane halin da take ciki, to da baiyi mata tambaya akan kukan da take ba, domin kuwa ita kanta batasan kukan me takeyi ba, kwata kwata batajin tsana da haushin Najeeb acikin ranta ko kaɗan, sannan haka kuma batajin ƙin aurensa, saboda shiɗin tsayayyen Namiji ne, kuma haɗaɗɗe da kowace mace zatayi fatan samu amatsayin mijin aurenta, saidai kuma awani ɓigere na zuciyarta auren ta da Najeeb ɗin fargaba da kuma tsoro yake haifar mata, sam batasan meyasa take samun kanta cikin matsanancin rauni akan maganar da ya shafi auren nata ba, haka take jin cewa wani abu me girmane yake ƙoƙarin tunkaro rayuwarta. Again ganin tayi shiru takasa amsa tambayar da Abbou Jaheed ɗin yayi mata ne, yasa lokaci ɗaya fargaba ya ziyarci zuciyar Abbou Jaheed, wanda kuma hakan ya tilasta masa sauƙe ajiyar zuciya tare da ɗan numfasawa cikin sanyi yace. "Ke nake sauraro Laylerh, domin nasan duk da cewar Najeeb zaɓina ne dana miki, wanda kuma nake fatan cika alƙawarin dana ɗauka,hakan bazai sa nakasa baki zaɓi ba, saboda haka inason ki amsa min tambayata, me kikeji game da aurenki da Najeeb? idan har ba kyason Najeeb ki sanar dani Laylerh, insha Allah bazan miki dole ba, zan kuma bawa Amini na Alhaji Ahmad Rufa'e haƙuri, duk da kuwa nasan fasa batun aurenki da Najeeb zai maidani mutum mafi ƙaranta awajensa, amma zan jure domin farincikin ki yafiye min komai." Wasu sabin hawaye ne suka sake gangarowa daga cikin idanunta, tabbas soyayyan Ć´a da mahaifi wata abace me tsananin girma tare kuma da zallan shaƙuwa, haƙiƙa Abbou Jaheed mahaifine agareta, duk da kasancewar kuwa bashine ya haifeta ba, amma tayi imani cewa bazai taɓa cutar da rayuwarta ba, tabbas idan Abbou Jaheed zai iya yarda ya ɗau kunya da kuma zubewar girma da ƙimarsa awajen jama'a da kuma abokansa, saboda ya sama mata farinciki ita me yasa bazata iya jure komai dan ta sama masa nasa farinciki da cikar buri ba? ako da yaushe idan tana cikin ƙunci Abbou Jaheed ɗinne ke ƙoƙarin yaye mata, duk da cewar bashi ya haifeta ba amma tayi imani cewa yana mata soyayyar da iya kanta zaiyiwa Ć´ar cikinsa. Lallai Abbou Jaheed ubane daya cancanci dukkan sadaukarwan ta, ta yarda cewa saboda shi zata iyayin komai, domin koda ace bai bata zaɓi ba, dama yana da haƙƙin da zai bata umarni ta bi, ya kuma kawo mata kowani irin mijine ta karɓa. Hannunta tasa ta share hawayen dake kwance akan fuskarta, ahankali ta ɗago jajayen idanunta wanda suka cika da ruwan hawaye, cikin sanyi haɗe da murya dake rawa tace. "Kai Uba ne agareni Abbou, haka kuma kana da daman da zakayimin zaɓi na karɓeshi hannu bibbiyu, bana tunanin bijirewa umarninka koda na second ɗaya ne, ba kuma na tunanin saɓawa maganarka ako da yaushe, kai mahaifina ne kuma kana da iko me ƙarfi akaina, na'amince da zaɓinka Abbou har cikin zuciyata, kuma bana tunanin akai wani abu dazai kawarmin da hankali akan zaɓin da ka min....." Ɗan tsagaitawa da maganar tayi sakamakon yanda kuka yake neman ƙwace mata, ahankali cikin muryarta da ta soma cracking tace. "Bawai ina kuka saboda zaɓinka bane,ina kukane kawai saboda aure zai nesantani dakai dama duk wata kulawa taka, zanyi nesa na barka Abbou, zanyi nesa nabar Ya M........" kasa ƙarasa maganar nata tayi, sakamakon kuka me ƙarfi daya ƙwace mata, saboda tunawa da M.Jay ɗin kaɗai da tayi ya ƙara ruguza mata duk wani ƙwarin guiwarta. Wani irin sabon tausayinta ne ya lulluɓe zuciyar Abbou Jaheed, wanda har hakan yasa idanunsa cikowa da ƙwalla, hannunsa ya ɗaura akanta cikin kulawa haɗi da tsantsar ƙauna yace. "Tabbas ke Ć´ace ta musamman awajena Laylerh, kana kuma ke kyautar Allah ce me tsananin daraja, ina alfahari dake ako da yaushe, sannan kuma kada ki taɓa tunanin cewa kulawan da nake baki zata iya sauyawa ako da yaushe, kafun iyanzu ke Ć´a tace haka ma kuma yanzu still amatsayin Ć´a kike awajena, saboda haka aurar dake da zanyi bashi zaisa ki tashi daga matsayin Ć´ata ba, har gaban abada ke Ć´ata ce Laylerh, sannan kuma kulawa ta zai tabbata akanki har zuwa ranan da zan daina numfashi, kuma nasan ko bayan babu raina zan kasance me alfahari domin na bada aurenki a inda ya dace, inda nasan bazaki taɓa wulaƙanta ba, kuma kamar yanda kikamin biyayya insha Allah kema watarana Ć´aĆ´an da zaki haifa zasuyi miki biyayya." Hannayenta ya kama cikin muryarsa da tayi sanyi sosai yace. "Ki share hawayenki, sannan ki tashi kije Yayanki Najeeb yana jiranki amota." Ya faɗi hakan yana me miƙa mata tissue, duk da kuwa cewar shima zuciyarsa tayi rauni amma ƙarfin hali kawae yakeyi. Cikin macewa da kuma sanyin jiki ta karɓi tissue ɗin tare da ɗan soma goge hawayen dake kwance akan fuskarta, gaba ɗaya jikinta yayi sanyi dajin maganganun Abboun, duk da kuwa azuciyarta tanajin cewa tana da zaɓi, amma dole haka zata daure saboda ƙaddara ta riga fata. Ƙoƙarin daidaita nutsuwarta ta soma yi, kana kuma ahankali ta miƙe tsaye. Kallon Abbou Jaheed ɗin tayi cikin sanyi da kuma son gusar da damuwar dake cin zuciyarta tace. "Nagode Abbou Saina dawo." Murmushi ya sakar mata tare da jinjina mata kai alaman "Adawo lafiya." Juyawa tayi cikin sanyi da kuma yanayin nutsuwarta ta nufi hanyar fita daga falon, gaba ɗaya zuciyarta acunkushe take da tunani kala kala, wani irin baƙon yanayi takeji ajikinta, wanda yake tafiya da duk bugun zuciyarta, karyewar zuciya da kuma fargaba sune abun da suka mamaye gaba ɗaya ƙwanyarta, yayinda takejin wani irin abu me kama da duhu da kuma zallan ruɗu na neman mamaye gaba ɗaya rayuwarta. Isowa bakin ƙofar falon da tayi ne, ya sa ta sake daidaita nutsuwarta, cikin nutsuwa ta murɗa handle din ƙofar falon ta fice. Zaune yake acikin babbar motar tasa ƙiran Prado LandCruiser, yayinda ya sanja shigar jikinsa zuwa wani tsadadden yadi me kyau, time to time yake ɗan duba agogon dake ɗaure atsintsiyar hannunsa, ɗago kansa da yayi ne ya bashi daman hangota, wanda fitowarta daga falon kenan, lokaci ɗaya ya zuba mata mayun idanunsa baya ko ƙyaftawa, kasancewar kuma garin yaɗan ɗau sanyi ne yasa shuke shuken bishiyoyin da ke compound ɗin gidan soma kaɗawa, hakanne kuma yabawa doguwar rigar dake jikinta daman buɗewa, sanadin hakanne yasa kayan jikinta fitowa fili, tare kuma da bayyana shape ɗinta. Idanunsa da suka sauƙa akan shape ɗin cikinta da kuma hips ɗinta ya ɗan lumshe, tare da jan wani dogon numfashi, dan kuwa har cikin ransa ya yaba da kyau da kuma tsarin halittar ta, lokaci guda kuwa yaji wani irin hot feeling na jansa zuwa gareta, numfashi me zafi ya fesar tare kuma da sake kafeta da ido, ko acikin ransa yasan cewa haƙiƙa samun ta amatsayin mata babbar nasarace ga kowani Ɗa Namiji, haka kuma rashinta daidai yake da duk wani ƙuncin rashin samun nasara. Samun kanta acikin compound ɗin gidanne yasa ta cigaba da daidaita nutsuwarta, kyawawan idanunta ta zubawa gaba ɗaya cars din dake cikin compound ɗin gidan, kasancewar akwai tarin motoci agidanne yasa ta kasa tantancewa kanta wace mota ce Najeeb din ke ciki. Murmushi yayi domin daga ganin yanda take ta kalle kalle ya fahimci cewar bata gane wace mota yake ciki ba, kasancewar baya son wahalar da'ita ya sashi danna horn ɗin motar. Jin horn ɗin mota agefenta ne yasa ta dawo da kallonta inda taji ƙaran, hangosa tayi zaune agaban motar ɓangaren driver ya tsura mata idanu baya ko ƙyaftawa, ganin irin kallon da yake matane yasa ta sadda kanta ƙasa, tare da soma takawa cikin nutsuwa ta ƙarasa wajen da motar nasa ke fake. Daga ciki yasa hannunsa ya buɗe mata murfin motar wanda hakan ya bata daman shiga ciki ta zauna, ahankali ta maida murfin motar ta rufe tare da ɗan lumshe idanunta. "Kin shanyani da yawa." Yafaɗayana me kai dubansa gareta. Jin abun daya faɗa ɗinne yasa ta ɗago ɗara ɗaran idanunta ta kalleshi, kana lokaci ɗaya kuma ta sadda kanta ƙasa. Ganin hakane ya sashi zuba mata idanunsa cike da son karantar yanayinta, saboda yaga gaba ɗaya mood ɗinta ya sanja. "Laylerh!." Yaƙira sunanta cikin yin ƙasa da murya. Samun kanta tayi da kasa amsa masa haɗe kuma da kasa ɗago kai ta kalleshi, kwata kwata batason ya fahimci rauni haɗi da damuwarta, wanda tasan ko daga cikin muryarta zai iya fahimtar hakan, domin ayanzu idan tace zata tsananta magana tabbas kuka zai iya ƙwace mata. "Laylerh!!." Ya kuma ƙiran sunanta akaro na biyu. Yanayin yanda taji muryarsa tayi sanyi sosae ne yasa ta ɗago kai ta kalleshi. Idanunsa acikin nata ya sakar mata murmushi, tare da soma yi mata wani irin shu'umin kallo, cikin son ƙarfafa mata guiwa haɗe da gusar da duk wata damuwa dake kan fuskarta yace. "Ba yau ba, ba kuma kullum ba sam damuwa bata kamaci kyakkyawar fuskarki ba, zai fi kyau ako da yaushe ki faɗi abun dake cikin zuciyarki akan ki ɓoyeshi, kisani ita damuwa tana gushewane kawai idan kasamu ka fitar da abun dake cikin ranka, sannan kuma barinta azuciya kwata kwata baya kawo mafita, sometimes saidai ya sake jefaka acikin wani hali, inaso ki gusar da damuwar dake kan fuskarki ta hanyar faɗaɗa murmushinki, kina da kyau saboda haka murmushi yafi dacewa dake ako da yaushe, ko wani bai taɓa faɗa miki cewar kina da kyau ba ne?." Idanu ta tsura masa saboda har acikin zuciyarta so take ta fahimci inda kalamansa suka dosa, kasancewar ayanzu komin ƙanƙantar hanyar da zaisa ta fahimci abun dake cikin zuciyarta nemansa take. Ganin yanda take kallonsa ne yasashi sakin murmushi tare da ɗauke kansa daga gareta, domin yasan idan ya cigaba da kallonta to bazai iya controlling ɗin kansa ba, anutse yayiwa motar key tare da ɗanyin reverse, ganin hakane yasa maigadi wangale masa wawakeken gate ɗin gidan ya cilla hancin motar tasa waje. Idanunsa da sukayi matuƙar ja ya rumtse, tare da sakin curtain ɗin window'n dake riƙe ahannunsa, ahankali ya juyawa window'n baya, yayinda yakejin wani irin raɗaɗi da kuna na sukar zuciyarsa, wani irin abu me kama da zallan kishi ne ya tokare masa ƙoshi, har zuwa yanzu abu ɗaya ne ke yawo acikin idanunsa, wato ganin da yayiwa Laylerh'n tare da Najeeb riƙe da hannun juna, wanda yanzu ma again akan idanunsa yaga ficewarsu daga cikin gidan, kansa da yakejin ya masa nauyi ya riƙe, tare da ware idanunsa wanda suka ƙara zama jajur kaman wanda aka watsa musu jan barkono, tafasan da zuciyarsa keyi ne yasa hatta sautin fitan numfashinsa ma saida ya sauya. Lallai ba ƙaramin asara bane rasa abun da yakasance kamar fata da buri agareshi, tabbas arayuwa akwai ƙaddarori masu tarin yawa acikinta, saidai wata Ƙaddaran tafi gaban kwatance, domin zafi da kuma ƙunarta takan iya raunata gaba ɗaya rayuwa. Hannayensa ya zuba acikin aljihun wandonsa, tare da fesar da wani zazzafan numfashi, ɗan jingina bayansa da jikin window'n yayi, saboda bayajin zai iya barin wajen batare da yaga dawowan Laylerh'n cikin gidan ba, domin yaune karon farko daya fara jin cewa yayi mistake na ɓoye gaskiyar abun dake cikin zuciyarsa, wanda sanadin haka gashi yana neman rasa duk wani muradi da kuma ƙwarin guiwarsa, tabbas bazai iya jurewa ba matuƙar Ƙaunar daya jima yana kiwonta acikin zuciyarsa ta watse alokaci guda. Ɓangaren Laylerh kuwa jin sun hau tsakiyar titi ne yasata jingina bayanta da jikin kujeran motar, tare da maida gaba ɗaya kallonta zuwa kan titi tana kallon yanda ababen hawa keta zirga zirga, wanda azahirin gaskia kuwa hankalinta ba akan ababen hawan yake ba, tunani da nutsuwarta ne kawai ke ƙoƙarin tafiya zuwa wani waje na daban. Tabbas tasan babu wani abun ƙi atattare da Najeeb, kama daga kan halayya ɗabi'unsa dama yanayin tsarin halittarsa,saidai kuma koma yaya zuciyarta ta karkata ne izuwa wani waje na daban. "Inasonki!." Maganar da Najeeb din ya faɗa ɗazu kenan da ke ta yi mata yawo cikin ƙwaƙwalwarta, ahankali taɗan lumshe idanunta, kana kuma acikin rai da zuciyarta yanda babu me iya ji ko karantar yanayinta tace. "Tayaya Najeeb ya fahimci cewar yana sona kuma har ya iya gayamin? hakan na nufin cewa yasan alamomin so da kuma wanda ba so ba kenan? haka kuma furta kalman SO ga wanda kake so, bai zamanto abu me wahala ba kamar yanda ta ɗauka, lallai tabbas tana da buƙatar wanda zai gaya mata ya kalan nata SO ɗin yake." Ɗan nisawa tayi tare da sauƙe ajiyar zuciya akaro na barkatai, tabbas tana da buƙatar sanin amsan duka waĆ´annan tambayoyin dake cikin ranta, nan ta yanke shawarar cewa zata tambayi Najeeb, kuma bata damu ba koda kuwa zai gane cewa bashi take so ba. Momy Safa da marwa take tayi atsakiyan katafaren ɗakinta, babu komai acikin zuciyarta kuwa face son ganin cikar burinta. Wayarta dake aje kan bedside ne ta soma ƙara, alaman shigowar ƙira, hakanne kuma yasata tsayawa daga tafiyan da take tare da kai dubanta inda ta ajiye wayar tata, ɗan jim tayi tana tunanin wanda zai ƙirata adaidai lokacin, jin ƙiran wayar na neman katsewa ne yasa da ɗan sassarfa ta ƙarasa wajen da wayar take, ganin sunan Aina'u akan screen ɗin wayar ne yasa cikin sauri tayi picking call ɗin, batare kuma da ta jira Aunty Aina'un tayi magana ba tace. "Bani da wadataccen lokaci Aina'u, ayau nakeson ruguza rayuwar Laylerh dama duk wani farincikin daya rage mata ta hanyar amfani da babban Rauninta wato Maleek!." Jin Abun da Momyn tafaɗa ne yasa Aunty Aina'u sakin murmushi, cikin son fahimtar da Ć´ar uwartata tace. "Rusa ƙauna me tsanani kamar wacce ke tsakanin Maleek da Laylerh ba abu bane me sauƙi kamar yanda kika ɗauka Hajiya Suwaeba, lallai dole muna buƙatar nutsuwa kafun aiwatar da komai, domin yin abu cikin gaggawa zai iya jawo mana tonon asiri, kuma kinsan dukanmu bazamu so hakan ba." Ɗan jim Momy tayi cikin rashin fahimtar kalaman Aina'un tace. "Me kike nufi, ban fahimci kalamanki sam." Murmushi Aunty Aina'u tayi cike kuma da son bayyana abun dake ranta tace. "Baikamata plan ɗinmu ya faraci daga yanzu ba, tabbas ada munyi tunanin cewa Alhaji Jaheed, Maleek zai aurawa Laylerh, sai kuma yazo ya ɓata mana tunani, ta hanyar bawa Najeeb aurenta, kuma hakan da yayi damace ya bamu me kyau, wanda zamu ɓata rayuwar Laylerh ta hanyar ɗansa Maleek, sanadin hakan kuma zai jawo tsana me tsanani tsakanin Maleek da Laylerh har ma kuma dashi Alhaji Jaheed ɗin kansa, domin nayi imani cewa matuƙar yafahimci cewa Maleek na bibiyan Laylerh bayan kuma tana da aure abun bazai taɓayin kyau ba, ba kuma mu da yanda zamuyi wanda ya wuce mu bari Maleek ya nemi Laylerh da aurenta." Jin abun da Aina'un tafaɗa ne yasa Momy lumshe idanu, tare da sakin wani shu'umin murmushi, lallai tayarda ƙanwarta Aina'u tafita kaifin hankali da kuma tunani haɗi da iya shirya mugunta, gashi yanzu take ta samu kanta acikin farinciki da kuma zallan nishaɗi. fashewa da wata irin dariya me ɗauke da tunanin samun nasara tayi, sai kuma da tayi dariyan sosai kafun taɗan tsagaita cikin yarda da shawarar ƙanwartata tace. "Tabbas kinyi magana me ma'ana Aina'u, zan kuma bita ayanda ta dace, saidai kada ki manta aƙwarine na ɗaukarwa kaina cewar sai Maleek ya zamanto silar lalacewar rayuwar Laylerh, bansan meyasa ba nakejin wani abu adangane dasu, lallai barinsu su biyun zai iya kawomin matsala ako da yaushe, tabbas zan bari Laylerh ta auri Najeeb domin hakan ma wata damace dazan samu, wanda kuma nasan abu mafi munin baƙin ciki shine Maleek ya kusanci Laylerh da aure akanta, tabbas zanso hakan domin mafari ne na hargitsewar rayuwarsu!." Dariya suka saka su dukansu, daga bisani kuma suka yi sallama. Ajiye wayar Momy tayi tare da yin murmushi, tabbas burinta ne ta ƙuntatawa rayuwar Laylerh da kuma ta Maleek, cikin isa da kuma bayyanar da abun dake cikin zuciyarta tace. "Dole saina tono sirrrin dake ɓoye, sannan kuma kuskure ɗaya kayi arayuwarka Maleek, da ka bari nasan cewa Laylerh itace Rauninka." *(ku tsumayeni gobe akwai update insha Allah😘)* 1/19/21, 8:12 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna *(This book is mainly for those that pay, if you know you did'nt pay please don't read it. Here is the account number for people that are willing to pay-0002214625 Abubakar Muhammed Sardauna Jaiz bank, whatsapp number 07017879464.)* *Chapter 19* Tunda suka ɗau hanyan super market ɗin yake satan kallonta lokaci zuwa lokaci, yayinda kuma ya maida gaba ɗaya hankali da nutsuwarsa zuwa gareta, wanda asanadiyar hakanne ya fahimci cewa akwai damuwa me tarin yawa dake kwance acikin zuciyarta wanda ta kasa furtashi ga kowa, duk kuwa da yanda zuciyarsa ke cike da son sanin damuwar tata haka ya share, domin kwata kwata bayason abun da zai hargitsa tunaninsa. Isowarsu bakin babban katafaren shoprite ɗinne ya sashi kashe motar, ahankali ya ɗan jingina bayansa da jikin kujeran motar, cikin yanayin kasalan daya sauƙar masa lokaci ɗaya yaƙira sunanta. Duk da cewar idanunta alumshe suke kana kuma tayi nisa cikin duniyar tunanin da take, hakan baisa ta kasa jiyo sautin muryarsa da ya ƙira sunanta da ita ba. Ahankali ta kallesa da idanunta wanda suka sanja launi zuwa yanayin bacci. Shi din ma kallonta yake saidai kuma yanayin nasa nasa kallon ya banbanta da irin wanda take masa, domin kuwa shi irin kallon nan me matuƙar kashe jiki yakeyi mata. Kasancewar kwata kwata bata saba da jefa idanunta acikin idanun wani namiji ba, hakan yasa bazata iya jure yanayin kallon nasa da yakeyi mata ba, ahankali ta ɗauke kanta daga gareshi, tare da kai dubanta zuwa babban ƙofar shiga katafaren Shoprite ɗin, gaba ɗaya har acikin zuciyarta batason irin kallon da Najeeb din keyi mata, saboda yanayin kallon nasa yakansa taji wani iri ajikinta. Shi kuwa ganin ta ɗauke kai daga garesa ne, yasashi sauƙe ajiyar zuciya, ahankali kuma ya buɗe murfin motar, ta ɓangaren da yake, kana kuma cikin tone ɗin muryarsa data sanja amo saboda kasalan daya sauƙar masa lokaci ɗaya yace. "Muje ko." Jin abun daya faɗane yasata buɗe murfin motar, ahankali ta zuro da kyawawan fararen ƙafafunta waje, wanda suke sanye cikin wasu haɗaɗɗun baƙaƙen flat shoe masu kyaun gaske, koda ta gama fitowa daga cikin motar, ahankali ta gyara zaman ɗan siririn mayafin dake jikinta, saboda kwata kwata bata fiye son tafiya ana kallon jikinta. Najeeb kuwa ganin ta fito ne yasashi ɗan soma takawa, wanda hakan yasa ta rufa masa baya. Ahaka suka shiga cikin shoprite din yana gaba tana biye dashi abaya, yayinda kuma atsakaninsu ya kasance babu wani tazara sosai. Kaitsaye sashin womens clothing ya nufa yayinda take biye dashi abaya, wasu manyan super market trolley ya ɗauka tare da ɗan juyowa ya kalleta. murmushi ɗauke akan fuskarsa yace. "Muje ki tayani sayyayya, then duk abun da kikaga ya miki ki ɗauka." Ya faɗi maganar yana me tura mata trolley ɗaya gabanta, Kai taɗan jinjina tare da mai da dubanta ga wata haɗaɗɗiyar abaya wanda tun shigowarsu wajen ita tafara ɗaukar hankalinta, domin kuwa rigar ta haɗu sosai saidai sanin cewa rigar zatayi tsada ne yasa ko kusa bata kawo tunanin ɗaukarta ba, idanu ta soma bazawa tana me ƙarewa haɗaɗɗun kayayyakin dake wajen kallo, domin kuwa kayane masu kyau haɗi da burgewa aka zuba awajen. Kasancewar kwata kwata bata saba da irin hakan bane yasa ta kasa ɗaukan komai dake wajen, domin kuwa wannan shine zuwanta shooping na farko da wani daban wanda ba Abbou Jaheed ba, saboda sometimes idan zata zo shooping da Abbou Jaheed ɗin suke zuwa, yanayin rashin sabon da tayi da hakanne kuwa yasa takasa ɗaukan komai dake wajen, sanin cewa bazata iya ɗaukan komai dake wajen bane yasa ta tsayawa tare da juyowa zuwa ɓangaren da Najeeb din yake, ganin yanda yake ta kwasan kaya, dangin su abayas da kuma straight gown, haɗi da boubou ne yasa ta zuba masa ido, tana me mamakin yanda yaketa jidan kaya masu uban yawa kaman bada kudi zai biya ba. Najeb kuwa ganin basket ɗin nasa ya kusa cikane, yasa shi ɗan dakatawa haɗe da juyowa ya fuskanci Laylerhn, wanda har zuwa yanzu ba abun da ta ɗauka. Ganin da tayi yana kallonta ne yasa ta sauƙe idanunta ƙasa, tare da kama ƙasan vail ɗinta ta soma wasa dashi. Ɗan lumshe idanunsa dake cike da mayen ƙaunarta yayi, domin yanayin yanda tayi acting ɗin ne yasa yaji wani irin sanyin ƙaunarta ya ratsa sa, ahankali ya ɗan tura keken hannunsa wanda ke cike da kaya, kaitsaye ya nufo inda take. Koda ya ƙaraso tsaida idanunsa akanta yayi cikin kulawa yace. "Meyasa baki ɗauki komai ba, ko babu abun daya miki ne?." Kai ta girgiza masa alaman "babu" "Why?." Yafaɗa cikin yin ƙasa da murya tare kuma da sanya hannunsa ya ɗan ɗago haɓarta, wanda hakan ya bawa kyakkyawar fuskarta daman bayyana. Idanunsa ɗaya ya kashe mata tare da cewa. "Biyoni muje." Yanayin yanda yayi maganar yana ɗan tafiyane yasa bata jira komai ba ta rufa masa baya, kaitsaye ɓangaren takalma suka nufa, nan ma kamar yanda sukayi aɓangaren abayas haka sukayi anan ɗin ma, dan shikaɗai ya dinga jidan takalma masu kyau da tsada. Ita dai duk inda yayi da idanu kawai take binsa, gaba ɗaya ta kasa ganin makusa ajikinsa, ganin kuma yanda yake mata wani irin kallo na alaman bazaki ɗauki komai ba ko, yasa ta ɗauki wani pink sneakers shoe me kyau. Haka dai ya dinga janta suna kutsawa duk inda wani kyan ƙyale ƙyalen mata suke, ita dai idanu kawai ta zuba masa. Saida yayi sayayya sosai kafun suka ƙarasa wajen da ake biyan kudi, ganin da yayi kamar tagaji ne yasashi ɗauko wata kujera ya ajiye mata batare daya kalleta ba yace. "Please zauna ki jirani anan inazuwa yanzu." Baijirayi me zatace masa ba ya juya, ya nufi part ɗin da ake saida su chocolate da kuma kayan sweets. Binsa tayi da kallo har saida ya ɓacewa ganinta, kafun ta sauƙe ajiyar zuciya, haɗe da dawo da kallonta ga mutanen dake ta hada hada awajen, yayinda kuma duk wanda yazo wucewa sai ya kalleta, musamman ma maza da suke mata ƙuri da ido kaman zasu cinyeta, wanda kuma hakanne yasa duk taji ta ƙosa da zaman wajen, saboda irin yanayin kallon da suke mata ne yasa taji ta kamar wata baƙuwar halitta wanda mutane basu saba gani ba. Najeeb kuwa aƙalla saida ya share sama da 15 minute kafun ya dawo wajen, again trolley ne ahannunsa wanda ya sake cikasa da kaya. Ƙin kallonsa tayi, domin kusan karo na uku kenan da yake kamata tana kallonsa, wannan yasa ayanzu taƙi ɗago kanta ta kallesa. Gane manufarta ne yasashi sakin murmushin, domin kome take yana lure da ita, yasan sarai taƙi kallonsa ne saboda batason ya kamata akaro na hudu. Yana tsaye kuwa aka gama yi masa lissafin kuɗinsa ya biya, tabbas ba ƙaramin kuɗi ya kashe a sayayyan nasa ba, saidai kuma ko ajikinsa baiji cewar ya kashe kuɗi ba,, saboda kuɗin akwaisu har ma ba asan iyaka adidinsu ba. Nan cikin wasu ƙattin ledodi aka zuba musu kayayyakin tare kuma dasa wasu daga cikin ma'aikatan wajen suka kai musu mota. Koda suka fito daga cikin shoprite ɗin, bayan motar Najeeb ya buɗe wa ma'aikatan suka zuba musu kayayyakin aciki, kasancewar shi me yawan kyauta ne yasashi zaro kuɗi a aljihunsa wanda shi kansa baisan ko nawa bane, ya bawa waĆ´anda suka kawo masa kayan, batare kuma daya saurari godiyarsu ba ya buɗe murfin motar ya shiga, Laylerh dake tsaye ganin ya shiga cikin motar ne yasa itama ta buɗe murfin motar ta shiga, akaron farko kenan da taji Najeeb din ya burgeta saboda kyautan da yayi, tabbas arayuwarta tanason mutum mai tausayin na ƙasa dashi, haɗe da mutum mai taimakon mutane masu rauni. Tana gama daidaita zamanta ta jawo murfin motar ta rufe, ahankali ta maida idanunta ta rufe, tare da sauƙe ajiyar zuciya, haka takejin wani irin daddaɗan sanyi na ratsa duk jikinta, yayinda sabon shauƙin sa ke ratsa zuciya da ƙwaƙwalwarta, sanadin hakanne kuma yasa duk taji kasala ya sauƙar mata. Sanin cewa baya kusa da ita ne yasa idanunta suka cika da tsumayin ganinsa. Sanyi da kuma tsananin shauƙin dake ratsata ne yasa taji ajikinta cewa, "Inama da ace shine azaune akusa da ita ba Najeeba ba, inama da ace shine ke buɗe baki yana mata magana kamar yanda Najeeb ke mata, ina ma da ace shine keyi mata irin kallon da Najeeb ke mata." tabbas da ace zai zamanto gaba ɗaya duniyarta da har abada ta kasance acikin farinciki, kyawawan idanunsa ne suka shiga yi mata gizo aciki na idanun, lokaci ɗaya ta saki sahirtaccen murmushin daya ƙarawa fuskarta kyau, tabbas tanason komai nasa, musamman ma yanayin cikin kyawawan idanunsa, jajayen laɓɓansa, da kuma lafiyayyen sajen dake kwance akan ƙuncinsa, tabbas yana da tsari me matuƙar burgewa, wanda ako da yaushe yakesawa taji tana matuƙar son kallonsa, saidai kuma awani sashi na zuciyarta, shiɗin ya kasance kamar wani abun tsorone agareta. Najeeb dake ƙoƙarin murza steering motar ne, ya zuba mata idanu cike da mamakin yanda yaga murmushi bayyane akan fuskarta, kasancewarsa mai saurin fahimtar yanayi da kuma halayyar ɗan adam ne yasa shi gane cewar tanajin daɗin tunanin da takeyi, duk da cewar baisan tunanin me take ba, amma kwata kwata bayason katseta daga yanayin nata, saboda murmushin da tayi ya matuƙar ƙarawa fuskarta kyau. Ahankali ya murzawa motar key haɗe dayin reverse, kaitsaye ya fice daga farfajiyan shoprite ɗin, cike da ƙwarewa ya cilla motar tashi kan titi. wanda kuma sanadin hakanne ya sa Laylerh dawowa cikin hankalinta. Ganin da yayi ta bude idanunta ne yasa shi cewa. "Tunanin mekikeyi haka da ya miki dadi har kike murmushi?" Idanunta ta ɗan lumshe, saboda kwata kwata bata taɓa tunanin cewa zai tambayeta game da tunanin da takeyi ɗin ba, mekenan zata ce masa? tace masa tunanin Ya M.jay ɗinta take, ko kuwa ta faɗa masa cewa tafara zargin kanta da cewar idan abun da takeji acikin zuciarta, shi ake ƙira So, to ta fara son Ya.M.jay.? kanta taɗan girgiza, domin ita kanta bata yarda da cewar son Ya M.Jay din take ba, saboda kwata kwata ma batasan ya ake gane haƙiƙanin so na gaskiya ba. Ganin tayi shiru ne yasa shi share maganar, saboda bayason matsa mata akan abun da take ɓoyewa acikin zuciyarta, kansa ya ɗan girgiza tare da sakin wani murmushi me ɗauke da ma'anoni daban daban, kana kuma cikin nutsuwa yaci gaba da tuƙinsa, yayinda kuma kusan rabin hankalinsa ya maidashi zuwa gareta. Ganin tana hammane yasashi gane cewar bacci takeji, hakanne yasa shi ƙara gudun motar tasa, sai gashi kuwa cikin mintuna ƙalilan sun iso gida. Laylerh da bacci ya soma ɗaukarta jin tsayuwar motar da kuma ƙaran horn ne yasa ta buɗe idanunta, ganin su a ƙofar gida ne yasata sauƙe ajiyar zuciya, domin dama duk jin kanta take atakure. Ƙaran horn din motar nasu ne kuwa yasa maigadi tahowa cikin hanzari ya wangale musu gate din, anutse ya tura hancin motar nasa ciki, sai kuma da ya ƙarasa babban parking space ɗin gidan sannan ya daidaita parking ɗin motar. Ɗagowa yayi ya kalleta cikin sigar tsokana yace. "Miss sleep wakeup mun iso gida." Jin abun daya faɗane yasa ta ɗan sake ware idanunta, tare da turo ɗan ƙaramin bakinta gaba, cikin yanayin shagwaɓan da batasan tanayi ba tace. "Nifa ba bacci nakeyi ba." Murmushin daya bayyana fararen haƙwaransa yayi, cikin yin ƙasa da murya yace. "Really?." Kai ta jinjina masa alaman ''Eh." Idanunsa ya ɗan lumshe saboda sosai yanayin shagwaɓan nata ya burgesa. Ganin yanda ya zuba mata idone yasa ahankali ta soma ƙoƙarin buɗe murfin motar. Akasalance yaƙira sunanta cikin wani irin murya, wanda jin amo da kuma sautin fitar muryar tasa ne yasata dakatawa, daga fitan da take ƙoƙarin yi tare da juyowa ta kalleshi. Ganin ta juyo garesa ne yasa shi tura hannunsa acikin aljihun wandonsa, inda ya ciro wani haɗaɗɗen ɗan ƙaramin box me masifar kyau, irin dai box ɗinnan da ake sanya zobe ko sarƙa aciki, sosai aka ƙawata jikinsa, wanda kuma hakan alama ne dake nuna cewar zobe ko sarkan dake cikinsa me tsadane sosai, ahankali ya buɗe murfin box ɗin wanda hakan yabawa haɗaɗɗen diamond ring ɗin dake ciki daman bayyana, ring ne me kyaun gaske wanda aƙalla kuɗinsa zai iya kaiwa 500k, yanayin tsadan zoben da kuma kyaunsa ne, yasa yake wani irin shining, musamman ma duwatsun da akayi masa ado dashi, dan sunfi komai dake jikinsa ɗaukar hankali, ciro zoben daga ma'ajiyinsa yayi tare da ɗagowa ya kalleta, ganin ta zubawa zoben idanu ne yasa shi ɗan lumshe nasa idanun tare da sauƙe ajiyar zuciya, hannunsa ɗaya ya miƙa mata tare dayi mata alama akan tabashi hannunta. Gane abun dayake nufi ne yasa tayi ƙasa da kanta, tare da soma wasa da Ć´an yatsun hannunta, haka takejin kamar bazata iya sa hannunta acikin nasa ba. Ganin tayi ƙasa da kanta ne yasa cikin wata irin kasallaliyar murya ya sake ƙiran sunanta. Awannan karon kam bazata iya jurewa yanda amon muryarsa ke fita ba, gashi kuma duk ta ƙosa ta tafi, hakanne yasa ta miƙa masa hannun nata, kamar yanda ya buƙata. Sauƙan lallausan fatar hannunta akan nasa ne, yayi sanadiyar miƙewar tsikar jikinsa, take yaji ƙofofin sadarwar tunaninsa sun tsaya, yayinda taushi da kuma laushin hannunta suka birkita masa tunani lokaci ɗaya suka kuma sauƙar masa da nannauyan kasala, idanunsa da suka ɗan soma marairaicewa ya zubawa kyawawan Ć´an yatsun hannunta, wanda suke ɗauke da shining nails masu kyau, ahankali ya sauƙe ganinsa akan hafaɗɗen zoben dake sanye cikin ƙaramar Ć´ar yatsan hannunta wanda aka rubuta, *L.M* asamansa da manyan baƙi. *L.M* ya maimaita kalman da aka rubuta ajikin zoben, wanda kuma haruffan da aka rubuta ɗinne suka ƙara ƙawata zoben, ƙurawa zoben idanu yayi, domin kuwa ya tabbatar cewa zoben ba gama gari bane, bakuma irin zoben nanne da ake zuwa super market asaya ba, zobe ne da idan mutum yanaso musamman ake haɗa masa a company, kuma ba ƙaramin kuɗi zoben ke dashi ba, musamman duba da irin yanayi da kuma tsarin zoben, wanda aƙalla kuɗinsa zai iya kaiwa 1.5 million. Ɗago shanyayyun idanunsa yayi, cikin sanyin murya yace. "Waya saya miki wannan zoben?." Jin tambayar tasa ne yasa ta ɗan ɗago ta kalleshi, sanin cewa bata da amsar da zata bashi shiyasa tayi shiru, domin azahirance itama batasan waya siya ko ya bata zoben ba, saboda itama kawai ganin ring ɗin tayi ahannunta, wanda kuma har yau takasa ciresa daga yatsanta duk da kuwa cewar ayanzu ring ɗin yaɗan matse hannunta. Ganin tayi shiru ne yasashi sauƙe ajiyar zuciya, lokaci ɗaya yasoma ƙoƙarin yaƙi da mummunan tunanin dake son shiga zuciyarsa, Ć´ar yatsan hannunta na tsakiya ya kama, ahankali ya zura mata haɗaɗɗen zoben dake hannunsa. "Happy Engagement!" yafaɗa adaidai lokacin da yagama zura mata zoben a yatsarta, wanda ya zauna ɗas kana ya kuma ƙarawa hannun nata kyau. "Engagement!." Ta maimaita kalmar acikin zuciyarta, dan kuwa hakanan taji kalmar tayi mata ban baraƙwai abakinta, gefe guda kuwa yanayin yanda ya riƙe hannunta ne yasa duk taji ta takura, ƙoƙarin janye hannuta daga cikin nasa tayi, saidai yanayin irin riƙon da yayi mata ne yasa bazata iya ƙwace hannun nata ba, har sai in dan kanshi ya sake mata, kwaɓe fuska tayi haɗe da ɗan karyar da wuyanta gefe, cikin muryarta dake ɗauke da zallan shagwaɓa tace. "Please ni zanje nayi bacci." Sassauta riƙon hannun nata yayi, cikin kasalalliyar murya yace. "Okay please ki kulamin da kanki sosai, sannan kiyi bacci me daɗi kinji, good night and sweet dreams my beautyful girl!." ya ƙare maganar yana me kissing ɗin soft hand skin ɗinta. Cikin sauri ta janye hannunta tare da buɗe murfin motar ta fice, batare kuma da ta tsaya sauraran wani abu da zaice ba kaitsaye ta nufi ƙofar babban falon gidan. Idanunsa da sukayi matuƙar ƙaɗawa kana sukayi ja ya rumtse, cikin wani irin zafin zuciya da kuma raɗaɗin daya keji ya dunƙule hannayensa tare da naushin glsss ɗin window'n, wanda hakan yasa gaba ɗaya glass ɗin amsawa, saidai kasancewar glass ɗin me ƙarfin gaskene yasa bai wani fashe wa sosai ba, akaro na farko kenan da tun tsayuwarsa awajen ya zame, inda ya zauna akan guiwowinsa, wanda kusan sama da 40 minute ya ɗauka a tsaye yana jiran dawowarsu, yanayin yanda yakejin ƙuna acikin ransa ne yasashi dafe ƙirjinsa daidai saitin zuciyarsa dake bugawa, komai kuwa daya faru atsakanin Laylerh da Najeeb din akan idanunsa, amatuƙar zafafe yakejin ƙirjinsa nayi masa suka, yayinda yakejin wani irin fushi ya cika zuciyarsa, haka yakeji kaman ya tashi yaje ya kakkarya Laylerh'n gida biyu, domin kuwa wani irin haushi da takaicin sune ya cika ƙirjinsa, babbar abun dayake sukan zuciyarsa kuwa shine, yanda yaga Laylerh'n ta miƙawa Najeeb hannunta, tabbas ganin da yayi musu yasa gaba ɗaya duniyar ta daina yi masa daɗi, yayinda baƙin ciki da ƙuna suka maye gurbin nutsuwarsa, bakomai yafi ƙona masa zuciya ba kuwa face kissing hannun Laylerh'n da yaga Najeeb ɗin yayi, wanda hakan ya zamanto tamkar sauƙan mashi ne akan ƙahon zuciyarsa, idanunsa ya kuma rumtsewa da ƙarfi, yayinda yakejin kansa na wani irin juyawa, sanadin hakanne kuwa yasa take memories din baya suka soma dawowa cikin ƙwaƙwalwarsa, wanda hakan ya sashi ƙara birkicewa, kunnuwansa ne suka soma dawo masa da gunjin kukanta, inda yakejin siririyar muryarta dake cikin matsanancin neman taimako na dukan zuciya da kuma hautsuna masa ƙwaƙwalwa, ahankali yanayin daya wuce ya soma wanzuwa acikin idanunsa, hakan yasa shi jin tamkar alokacinne abun ke faruwa. Lokaci ɗaya gaba ɗaya jijiyoyin kansa suka amsa da wani irin azababben ciwo, yayinda kuma gashin jikinsa suka mimmiƙe, still kuka da sautin muryarta yakeji suna tashi acikin kunnuwan sa, wanda hakan yasa amatuƙar zauce ya soma buga kansa da jikin bango, kwata kwata bayason jin ihun nata dake ƙoƙarin mai dashi mahaukaci, kana kuma bayason ganin moment ɗin daya riga ya wuce acikin idanunsa. Cikin 10 minute gaba ɗaya ya fita hayyacinsa tare da zaucewa, da ƙyar ya iya tashi ya ƙarasa gaban drawer'n da anan ciki yake ajiye cocaine ɗinsa, ɗeɓo cocaine ɗin yayi ya zuba akan tiles din dake malale ƙasan ɗakin, kwanciya yayi aƙasan wajen kana cikin yanayin zaucewa ya shiga shaƙan cocaine din azafafe, yanayin yanda yake zuƙanta kaman mahaukaci ne yasa take hankalinsa ya soma gushewa, sanadin hakanne kuma yasa duk wani tunani dake cikin ransa ya kau, lokaci ɗaya ya samu kansa cikin wata sabuwar duniya. Ahankali ya buɗe idanunsa wanda suka rikiɗe suka sake yin ja, saman ɗakin nasa dayake ganin yana juya masa ya ƙurawa ido, saboda haka yake gani kamar ba acikin duniya yake ba, cikin abun da bai wuce 14 minute ba ya sake samun kansa cikin wata duniyar, wanda take kama da bacci, suma, da kuma fitar hankali. Idanunsa ne suka rufe yayinda gaba ɗaya jikinsa ya daina motsi. Ɓangaren Laylerh kuwa koda ta ƙasara cikin falon, bata iske kowa ba hakan yasa kaitsaye ta wuce ɗakinta, kasancewar amatuƙar gajiye take hakan yasa doguwar rigar dake jikinta kawai ta cire, kana ta wuce toilet ta ɗauro alwala, baccine sosai ya cika idanunta hakan yasa tana fitowa daga toilet ɗin ta faɗa saman gadonta, cike da mayen bacci tayi addu'a, cikin abun da baiwuce mintuna 15 ba kuwa bacci ya ɗauketa. Najeeb kuwa zuciyarsa cike da tarin tunani haɗi da saƙe saƙe kala kala ya wuce masauƙinsa, babu abun daya tsaya masa arai kamar kalmomi biyun da yagani ajikin zoben dake hannun Laylerh'n, gaba ɗaya zuciyarsa taƙi nutsuwa masa da hakan, baisan meyasa akaron farko yaji faɗuwar gaba ta ziyarcesa ba. haka dai yayita juyi akan gadon, zuciyarsa cike da tunani kala kala bacci ɓarawo ya ɗaukesa. Washegari. Kasancewar ranan yau takasance ranan weekend, hakan yasa Laylerh koda ta tashi tayi sallan asuba wani sabon bacci ta sake komawa, ba ita ta farka ba kuwa sai kusan 9 am, tun tashinta taji gaba ɗaya gidan nasu ya cika da hayaniyar mutane, kaitsaye toilet ta wuce tayi wanka, koda ta fito mai kawai ta shafa ajikinta sai normal tpowder da taɗan murza akan fuskarta, wata doguwar rigan abaya me kyau tasaka ajikinta, tare da yane kanta da ɗan kwalin kayan, kasancewar tun tashinta takejin cikinta na kukan yunwa ne yasa ta zura takalmin flat shoe aƙafanta, kaitsaye ta nufi falo duk da kuwa kasancewar yau din tun tashinta takejin faɗuwar gaba haɗe kuma da tsinkewar zuciya na ziyartarta, sanin cewa bata da makama sai addu'a ne, yasa ta shiga karanro addu'a haɗi da ambaton sunan Allah azuciyarta, tunkaro falon da tayine yasa tasoma jiyo ɗan surutan mutane wanda kuma da dukkan alamu Momy ce da ƙawayenta, ƙarasowanta cikin falonne yasa idanunta suka sauƙa akan wasu haɗaɗɗun akwatunan da suka cike tsakiyan falon, wanda aƙalla yawansu zasu kai goma sha huɗu, akwatuna ne different colours masu kyau da kuma burgewa, hakanne yasa ma ta zubawa akwatunan ido. "Gaskiya Hajiya Suwaeba kayan aure sunyi kyau Laylerh tayi goshi, saura kuma afara yi mata gyaran amarya, tun da dai biki ya matso kusa." Ɗaya daga cikin ƙawayen Momy tafaɗa, tana me ɗaga wani tsadadden lace ɗin dake hannunta, wanda yake ɗaya ne daga cikin kayan auren. Maganganun da ƙawar Momyn ke faɗa ne yasa zuciyar Laylerh tayi wani irin bugawa. (note edit) 1/19/21, 8:13 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting by* fatymasardauna *(This book is mainly for those that pay, if you know you did'nt pay please don't read it. Here is the account number for people that are willing to pay-0002214625 Abubakar Muhammed Sardauna Jaiz bank. Whatsapp number 07017879464. )* *Chapter 20* Da idanunta da suka cika da ƙwalla take kallon kayan lefen, lokaci ɗaya taji bugun zuciyarta ya tsananta, yayinda duk wani kuzarin da ya rage mata yayi ƙaura, tabbas tasan da cewar Abbou Jaheed zaiyi mata aure kana kuma abun yana damunta, amma kwata kwata aranta bataji ta gamsu da hakan ba sae yanzu, haka kuma tsoron hakan bai ɗarsu acikin rae da zuciyarta ba sae yanzu da taga kayan lefen da suke amatsayin nata, tabbas ganin kayan lefen ya sake karyar mata da zuciya, domin hakan alamace dake nuna cewa aurenta da Najeeb ba makawa sae anyisa. Idanunta da suka ciko da ƙwalla ta lumshe, tare kuma da sauƙe kanta ƙasa, jitayi komae ya fita daga ranta, yayinda lokaci ɗaya taji yunwan da takeji dinma ya tafi, zallan yanayin damuwa ne ya bayyana ƙarara akan fuskar ta, cikin sanyin jikin daya ziyarceta lokaci ɗaya ta juya cikin hanzari ta nufi ɗakinta, kwata kwata batama yarda kowa yaganta ba. Ahankali ta maida ƙofar ta rufe tare da sulalewa ta zauna a bakin ƙofar, idanunta dake cike fal da ƙwalla ta lumshe, wanda hakanne kuma ya bawa hawayen dake cikin idanun nata daman gangarowa bisa kan kuncinta, akaro na barkatae kenan da takejin zuciyarta na karyewa, Rauni da kuma matsanancin damuwa su suka maye duk wani gurbin nutsuwarta, haka takejin wani sabon shauƙi haɗi da zallar begensa na game zuciyarta, haƙiƙa wannan shine karona farko da takeji ajikinta cewa lallai aure zai rabata dashi, za kuma tayi nesa dashi, zata daina ganinsa, zata daena ganin kyawawan idanunsa, kyawawan lips ɗinsa, dama yanayin tsarin tafiyarsa, kwarjini da kuma zallar ƙamshinsa dake narkar mata da zuciya. wanda kuma tayi imani cewa masifaffen kewarsa zai iya daƙushe duk wani farincikin rayuwarta, tabbas rashin M.Jay ɗin wata babbar nakasa ce dake ƙoƙarin kutso kae cikin rayuwarta. Ahankali ta buɗe idanunta dake alumshe, wanda sanadin hakanne kuwa yasa wasu sabin hawaye suka silalo daga cikin idanun nata, so take tayi kuka sosai, so take ta faɗi sirri da kuma gaskiar abun dake ɓoye acikin rai da zuciyarta, tabbas ayau akuma yanzu ta gamsarwa kanta cewar lallai abun da takeji dangane dashi So ne, irin kuma soyayyar nan mai matuƙar ƙuna dakuma azabtar da zuciya, lokaci ɗaya taji gaba ɗaya hankali da nutsuwarta sun tafi izuwa garesa, yayinda idanunta kuma suka cika da so haɗi da tsumayin ganinsa. Jin yanda hawaye ke sauƙa akan ƙuncinta ne yasa asanyaye tayi ƙasa da idanunta, hakanne kuma ya bata damar sauƙe ganinta akan Ć´ar yatsarta dake sanye da zoben da Najeeb ɗin ya saka mata adaren jiya, ɗauke kai daga kallon zoben tayi, saboda akaron farko kenan da taji wani abu dangane da zoben ya daki zuciyarta, batajin zata iya barin zoben ahannunta, hakan yasa ahankali ta zareshi daga cikin Ć´atsarta, wata irin sassanyar ajiyar zuciya ta sauƙe, tare da ɗan kwantar da kanta ajikin bango, haƙiƙa so take tasamu nutsuwa daga abun dake sukar zuciyarta, so take ta sashi acikin idanunta domin sosai ta riga da ta kwaɗaitu dason ganinsa, wanda har hakan yasa takejin kaman tayi tsuntsuwa zuwa ɗakinsa, dan tayi imani cewa ganinsa ne kaɗai zai iya sama mata nutsuwa. Maleek. Ahankali yake buɗe sleeping eyes dinsa da sukayi masa nauyi kana kuma suka ƙanƙance, dishi dishin da yake gani acikin su ne ya sashi maida idanun nasa ya rufe, domin haka yake ganin kamar ginin ɗakin zai faɗo masa, kasancewar har zuwa yanzu mayen cocaine ɗin bai sakeshi ba, dan haka yakejin gaba ɗaya jikinsa yayi weak, ga kuma wani irin fitinannen kasala haɗi da ciwon kai da suka dirar masa lokaci ɗaya. Hannu yasa ya ɗan dafe kansa dake yi masa ciwo kaman zai rabe biyu. still idanunsa dake amarairaice ya buɗe tare da sauƙe ganinsa akan babban agogon bangon dake rataye aɗakin. 9:30 am daidai agogon dake saƙale ya nuna masa, ɗan cije laɓɓansa yayi saboda sam baiso cocaine din ya wahalar dashi har haka ba. Ahankali ya ɗan motsa jikinsa tare da soma ƙoƙarin ɗaga kansa da yakejin yayi masa nauyi sosai, wanda kuma yasan hakan bai rasa na saba da overdose na cocaine din da yayi, ɗan jingina bayansa da jikin gadon yayi tare da sakin ajiyar zuciya, har yanzu ganin duniyar yake tana ɗan jujjuya masa, wanda ko sallan asuba ma da ƙyar ya iya tashi yayi, tun da yayi sallan kuwa ya koma bacci me kama da zallar maye bai tashi ba kuma sai yanzu. Lumshe fitinannun idanunsa yayi, domin kuwa har zuwa yanzu itace acikin tunani da kuma zuciyarsa, baisan meyasa ba lokuta da dama haka yakejin kamar ana hura masa wuta acikin zuciyarsa, wanda har hakan yasa shi fara tunanin cewa abun da yakeji din naneman fin ƙarfin tunaninsa, yanayin yanda zuciyarsa ke harbawa, haka dukkan gaɓɓan jikinsa ke azabtuwa da sauyayyar ƙaddaran dake neman kutso kai cikin rayuwarsa, laɓɓansa yaɗan cija da ƙarfi, domin har yanzu yakasa mantawa da moment ɗin da ya gansu aciki ita da Najeeb din, kunan da yakeji azuciyarsa ne ya sashi ware idanunsa da sukayi ja, tare dasa hannu ya dafe daidai saitin ƙirjinsa dake yi masa ƙuna. Haƙiƙa "Ƙaddara" itace abu mafi girma da suka taso suka samu kansu suna rayuwa acikinta, tun daga kan yarinta kuwa har zuwa girmansu, tabbas kowani bawa tare da ƙaddaransa yake tafiya me kyau ko akasinta, saidai ako yaushe wasu zuciyoyin sukan zama masu rauni wajen gaza ɗaukar ƙaddaransu, abune da yake abayyane cewar wata ƙaddaran takanzo da sauyaye kala kala, wani lokaci takan zo da farinciki, wani lokaci kuwa ta kanzo da saɓanin haka, tabbas yayarda cewa acikin ƙaddaransa aka sako masa Laylerh, wanda tazama itace damuwa da kuma dukkan rauninsa, tabbas yau ce rana ta farko da yaji cewar da yana da dama da kuma iko, to da ya sauya ƙaddaransa daga mummuna izuwa kyakkyawa, ya kuma goge sunan Laylerh dake rubuce acikin ƙirjinsa. Sake rumtse idanunsa yayi ƙam sakamakon yanda yaji zuciyarsa na bugawa akai akai. Sanin da yayi cewa yawan tunani bazai amfanesa da komai bane yasa, ahankali ya zuro da fararen ƙafafunsa ƙasa, tare da soma yunƙurin miƙewa tsaye, jin da yayi ƙafafun nasa na neman gaza ɗaukarsa ne ya sashi dafe bango, tare da sanya hannayensa ya murza sexy eyes dinsa da har yanzu suke ganin komai dishi dishi. Cije red lips ɗinsa yayi kana cikin dauriya ya tsaya akan ƙafafunsa da suke ɗanyi masa zafi, ƙoƙarin shanye duk wani abu da yakeji yayi, kaitsaye ya wuce toilet, saboda so yake yaɗan watsa ruwa ajikinsa. Koda ya ƙarasa cikin bathroom ɗin da kansa ya haɗawa kansa ruwan wanka acikin babban jakuzzie. Kayan dake jikinsa ya cire haɗe da shiga cikin jakuzzie'n ya kwanta, akasalance ya ɗanyi rolling eyes ɗinsa tare da sakin sassanyar ajiyar zuciya. Wata irin nutsuwa ya samu saboda yanda daddaɗan ɗumin ruwan dake cikin jakuzzie'n ke ratsa shi, gefe guda kuma wani irin daddaɗan ƙamshi ne ke tashi acikin ruwan, domin kuwa sosai ya cika turaren wanka acikin ruwan, sake gyara kwanciyarsa yayi, tare da ɗan ware idanunsa wanda gaba ɗaya yanayinsu ya sauya daga normal zuwa sexy emotion, Ɗan ɗago hannunsa yayi, wanda hakan ya bashi daman sauƙe idanunsa akan kyakkyawan zoben dake sanye a yatsar hannunsa. Harrufa biyu dake jikin zoben ya ƙurawa ido, aransa yanajin abubuwa da yawa na yawo ajikinsa dangane da harafin *A* wanda takasance kamar itace ado ga zoben. Shiru yayi yana sauƙe ajiyar zuciya akai kai, tamkar wanda zuciyarsa tayi nisa cikin tunani, haƙiƙa babu wani second ko minute da zai shuɗe batare da tunaninta acikin rai da zuciyarsa ba, baisan dame zai kwatanta abun da Ć´akeji adangane da ita ba, akullum akuma ko da yaushe matsanancin shauƙinta ne ke matsawa gangar jikinsa, wanda sanadin hakan yasa ya zamo mutum me matsanancin feeling, lallai baya tunanin cewa zai iya jurewa baƙon yanayin dake shirin kutsowa cikin rayuwarsa, wanda yasan jure hakan abu ne me matuƙar wahala. Tamkar dole ya zame masa ɗaukar shawarar da zuciyarsa ta bashi,, duk da kuwa cewar yasan yin hakan zai iya zama tamkar cutarwa ne ga rayuwa da ma duk wani farincikin sa, saidai bayaso ya cigaba da zama mutum me kasa ɗaukan rauni da damuwarsa ako yaushe. Tabbas bashida wata makama da ya wuce masa yarda da shawaran da zuciyarsa ta basa, domin yayi imani cewa hakanne kaɗai zai kare zuciyarsa daga ƙoƙarin bugawa, lallai ya yarda cewa, acikin dukkan rayuwa akwai ƙalubale, kana kuma hanya ɗaya ce ako da yaushe shine Nasara ko ko Faɗuwa. Yariga da ya gamsu da abun da zuciyarsa ta shirya mai, hakanne ya sashi nutsar da zuciyarsa waje ɗaya ahanzarce kuma yayi wanka. Koda ya fito daga bathroom ɗin kuwa wani farin towel ne ɗaure akan waist ɗinsa, yayinda gaba ɗaya gargasan jikinsa suka kwanta lub akan fatarsa, cikin nutsuwa ya ƙarasa gaban dressing mirror domin ba laifi wankan da yayi, yasa yaji ɗan ƙarfi ajikinsa. Ɗan ƙaramin towel ya ɗauka ya shiga goge jikinsa, bayan ya gama ne kuma ya shafa haɗaɗɗen body lotion me daɗin ƙamshi ajikinsa, kasancewar al'adarsa ne son ƙamshi, hakan yasa shi feshe gaba ɗaya jikinsa da fitinannen body spray me ƙamshin gaske. Take kuwa gaba ɗaya ɗakin nasa ya gauraye da sassanyan ƙamshin turaren, wani comb ya ɗauka anutse ya shiga taje cikakken suman kansa da ya sake kwanciya lub saboda gyaran da yake yawan samu akai akai, hannu yasa ya ɗan shafi lallausan baƙin sajen dake kwance akan beauty face ɗinsa, wanda kuma ita take ƙarawa fuskarsa kyau, gefe guda kuwa jajayen laɓɓansa da akullum suke ƙara turuwa ne ke ta faman sheƙi, wanda hakan ke ƙara bayyana hasken fuskarsa. Anutse ya ƙarasa gaban makeken drawer'nsa, inda ya buɗe murfin side ɗin da yake ajiye kayan gym ɗinsa. Wani navy blue track suit mai kyau da tsada ya ciro tare sa sanya kayan ajikinsa, wanda ƙafan wandon track suit din nasa ya kasance kaman pencil. Sosai kayan suka amshi jikinsa, suka kuma ƙara bayyana haske da kyaun fuskarsa. Kaitsaye wajen shoesrug ɗinsa dake cike da takalma kala kala ya nufa, wani haɗaɗɗen white sneakers shoe ya ciro haɗe da sanyawa aƙafansa. Anutse ya ƙarasa inda ya ajiye wayarsa ƙirar iPhone 12 pro max, koda ya duba screen na wayar 2 missed calls ya gani, wanda kuma da number'n Fou'ad ne akayi masa missed call ɗin, sanin da yayi cewar ba lallai ƙiran ya zama serious issue ba ne, yasa batare da ya bi ƙiran ba ya tura wayar cikin aljihun wandonsa, sannan kaitsaye ya fice daga cikin ɗakin. Direct babban falon gidan nasu ya nufa, koda yaƙarasa cikin falon kuwa Momy da Aunty Aina'u ya samu azaune, yayinda Aunty Aina'u keta jujjuya tsala tsalan atamfofin dake cikin kayan lefen Laylerh'n dake zube agabansu. Duk da cewar idanunsa sun sauƙa akan akwatunan dake tsakiyan falon, saidai baiko kalli inda suɗin suke ba kaitsaye ya nufi dining table. hakanne kuwa yasa dukansu suka bisa da kallo. Ɗaya daga cikin kujerun dake dining table ɗin yaja ya zauna. Tare da jawo ƙaton flask ɗin dake aje kan babban table ɗin, batare kuma da ya tsaya sauraran komae ba ya haɗawa kansa tea. Ahankali yake sipping tea ɗin cike da nutsuwa, tun da ya zauna awajen kuwa bai ɗago kansa ba, saidai time to time yakan dafe daidai saitin zuciyarsa. Sama da 15 minute ya ɗauka zaune awajen, kafun daga bisani ya miƙe kaitsaye ya fice daga cikin falon. Ganin fitansa ne yasa Momy da ta bisa da idanu, ta saki wani irin shu'umin murmushi abayyane tace. "Lokaci nazuwa Maleek, lokacin da zakayi dana sani marar iyaka, lokacin da zaka samu kanka da ɓata rayuwar Laylerh, lokacin da gabaki ɗayanku zakuyi kuka marar iyaka." Cikin takunsa me ɗauke da isa da kuma zallar ƙasaita ya ƙaraso zuwa compound ɗin gidan. Abdoul dake zaune yana bawa sniffer dog abinci, ganin ogan nasa ya fito ne yasa shi miƙewa tsaye da sauri, cikin girmamawa yace. "Good morning sir" Kai ya jinjinawa Abdoul ɗin saboda a yanayin da yake ciki bayajin zai iya motsa laɓɓan bakinsa, har ya kae ga amsa gaisuwar Abdoul ɗin. Abdoul kuwa ganin yanayin fuskar ogan nasa babu alaman wasa ne ya sashi daidaita nutsuwarsa, tare da rufawa Captain din baya. Ƙarasawa jikin mota sukayi, inda cikin hanzari Abdoul ya buɗe masa murfin motar wanda take ƙiran benz 2019, shiga cikin motar yayi ya zauna tare da ɗan lumshe idanunsa, cikin silently voice ɗinsa yace. "Kabawa cutie abinci?." Kai Abdoul din ya jinjina cikin nuna masa respect yace. "Eh ranka shi daɗe na bata." Maida idanunsa yayi ya lumshe, wanda kuma hakan alamace dake nuna cewar ya gamsu da abun da Abdoul din yafaɗa. Ahanzarce Abdoul ya shiga cikin motar tare dayi mata key, wanda already dama maigadi ya wangale musu gate din gidan, hakanne kuwa yasa cikin sauƙi Abdoul ya cilla motar kan shumfuɗaɗɗen titin dake malale daga ƙofar gidan har zuwa babban gate ɗin da zai fitar dakae daga unguwar tasu. Suna fita daga gidan kuwa motar Najeeb na shigowa. *(Kuyi haƙuri rashin caji ne ya ɓoyeni, yanzu ma sauri sauri haka na muku typing... ..... Insha Allah Next chapter zaku sha biki💃 Laylerh dae tame rabo ce, daga aurenta kuma wasan zai fara.)* *Sunday.* *9:00 pm* 1/19/21, 8:13 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *writting by* fatymasardauna *(This book is mainly for those that pay, if you know you did'nt pay please don't read it. Here is the account number for people that are willing to pay-0002214625 Abubakar Muhammed Sardauna Jaiz bank. Whatsapp number 07017879464. )*             *Chapter Tweenty one* Najeeb da shigowarsa cikin gidan kenan, ganin ficewar motar Maleek ɗinne ya sashi bin motar da kallo, aransa yana jin wani irin abu me kama da tsananin kishi na mamaye zuciyarsa, tabbas kusan kullum sae zuciyarsa ta saƙa masa abubuwa da yawa adangane da Maleek ɗin, baisan kuma meyasa ba akoda yaushe yakanji nutsuwar zuciyarsa na gushewa matuƙar ya tuna da Maleek din, kana ako da yaushe akwae wani abu dayake hangowa kwance acikin idanu da kuma fuskar Maleek ɗin, wanda kuma har zuwa yanzu ya kasa fahimtar gaskiyar abun da zuciyarsa ke raya masa. Sanin cewa duk wani tunani da zaiyi ayanzu ba lallai ya zamo mai tasiri ba ne, ya sashi share duk wani abu dake cikin rai da zuciyarsa. Ƙarasa shigewa cikin gidan yayi, yayinda yake murza kan streering motar tasa cikin nutsuwa, sanin da yayi cewar idan ya shiga cikin gidan bazae wani jima sosae bane, yasashi yin parking ɗin motar anan tsakiyar compound ɗin gidan.  Cikin nutsuwa ya gama daedaeta parking din, tare da buɗe murfin motar ya fito, sanye yake cikin wasu ƙananan kayan da suka matuƙar amsar jikinsa, kana kuma suka ƙara bayyana kyawu da ƙwarjininsa, daga gefe guda kuwa gashin kansa ne keta sheƙi, saboda yanayin yanda yasha gyara da mayuka iri iri, duk dama shi ba mae yawan barin tarin suma akansa ba ne, saboda gashin dake kansa ko rabin nakan M.Jay baiyi ba,  still kyakkyawar sajen dake kwance akan fuskarsa ne ke shining, yayinda kuma sajen ya kwanta lub akan ƙuncinsa, kana kuma akan kyakkyawar fuskartasa yana ɗauke da Ć´an madaidaitan lips masu kalan light pink. Cikin nutsuwa yake tafiya yayinda sassanyan ƙamshin turaren oud ke tashi ajikinsa. Kaitsaye ya nufi ƙofar da zata sadasa da babban parlourn gidan. Koda ya isa bakin ƙofar ahankali ya ɗaura hannunsa akan handle din tare da ɗan tura ƙofar ciki, kasancewar ƙofar ba arufe take da key ba ne, yasa take ta buɗe, cikin nutsuwa ya kutsa kansa cikin falon, yayinda bakinsa ke ɗauke da sallama. ƙaran tv da na A/C ne kawai ke tashi acikin parlour'n, kasancewar babu kowa acikin falon, dan tuni Momy da Aunty Aina'u sun tashi daga falon sun koma ɗaki. Gama ƙarewa falon kallo da yayine ya sashi sakin ajiyar zuciya, ahankali ya ƙarasawo tsakiyar falon, anan akan ɗaya daga cikin haɗaɗɗun kujerun dake cikin parlourn ya zauna, tare da zaro wayarsa ƙiran company'n iphone ya soma dannawa. Larae Ć´ar matashiyar me aikinsu wanda fitowarta daga kitchine kenan, ganinsa da tayi ne yasa ta ɗan rusuna, kana cikin girmamawa tace.  "Sannu da zuwa ranka ya daɗe." Jin muryan Larae'n acikin kunnensa ne ya sashi ɗago da kansa, cikin sakin fuska yace.  "Yauwa sannu, naji gidan shiru ko bakowa ne?" Yayi mata tambayar yana mai sake maeda kansa ga wayarsa.     "Akwai mutane yanzu Hajiyan ma suka haura sama, aƙirawo maka ita ne?" Larai ta faɗa. Kai ya girgiza alaman "A'a."  Ganin hakanne kuwa yasa Larae miƙewa tsaye ta koma kitchine, ɗan madaidaicin tray ta ɗauko wanda yake ɗauke da ɗan ƙaramin cup asamansa, da kuma bottle water me sanyi, sai kuma kwalin juice ɗin exotic.     Ƙarasowa gabansa tayi tare da ɗaura ɗan ƙaramin tray ɗin anan kan saman table ɗin dake gabansa. koda ta kammala zuba masa juice ɗin acikin cup, juyawa tayi tare da soma ƙoƙarin barin falon, ganin hakane yasashi ɗanyin gyaran murya, cikin nutsuwa yace. "Please kimin magana da Laylerh mana." Jin Abun daya  faɗa ne yasata jinjina kai kana kuma cikin sauri tace.  "To." Juyawa tayi kaitsaye ta nufi hanyar ɗakin Laylerh'n. Kwance take akan ɗan madaidaicin gadon daya kasance mallakinta, yayinda kyawawan idanunta wanda sukayi ja kana suka disashe saboda kukan da tayi suke alumshe, hakan yasa yanayinta yayi kamar na me bacci. Ajiyar zucia take sauƙewa akai kai, yayinda kuma har yanzu numfashi da kuma bugun zuciarta suka kasa daidaita, ita kanta batasan dame zata fassara yanayin da takejin kanta aciki ba, saboda kwata kwata bata cikin mood me daɗi. Duk kuwa da irin yanayin da takejin kanta aciki, hakan bai hanata wasa haɗi da murza zoben dake sanye a yatsar hannunta ba, saboda hakan ya zame mata kamar ɗabi'a, matuƙar ta samu kanta acikin yanayi na damuwa ko farinciki, sometimes takan samun kanta tana wasa da zoben nata, sanadin hakan kuwa yana sawa taji sanyi aranta.  Kasancewar batayi nisa acikin tunanin nata bane yasa ta jiyo knocking ƙofar ɗakin nata da akeyi. Idanunta wanda sukayi luhu luhu ta bude tare da zubawa ƙofar shigowa ɗakin idanu,  saboda bata tsammanin ƙiran kowa adaidai wannan lokacin.. "Laylerh!."  Larae dake tsaye abakin ƙofar, tana knocking ta ƙira sunan Laylerh'n tana me sake ƙonƙwasa ƙofar. Jin muryar Larae ne yasata sauƙe ajiyar zuciya, ahankali cikin amon sautin Muryarta da baya fita sosai tace.  "Yes come in." Larae dake waje kuwa kwata kwata batama ji abun da Laylerhn ta faɗa ba, azatonta ma bacci Laylerhn take, tunanin hakanne kuwa yasa ta cigaba da ƙonƙwasa ƙofar. Ganin Larae'n bata daina knocking ƙofar bane yasa ta ɗan lumshe idanunta, ahankali ta tatashi zaune, tare da zuro da kyawawan ƙafafunta ƙasa daga kan gadon. Miƙewa tsaye tayi tare da nufar jikin ƙofar ɗakin, dan tasan idan bata buɗe ƙofar ba larae ba zata taɓa daina knocking door ɗin ba. Ahankali ta murda handle ɗin ƙofar, wanda yasa take ƙofar ta buɗe. Ƙoƙarin daidaita nutsuwarta tayi, kana cikin yanayin sanyi tace. "Inna Larae ashe kece kike bugun ƙofa." Murmushi Larae tayi tare da cewa.  "Eh wallahi nice, dama baƙo kikayi afalo shine yace na ƙiraki." Jin ance wae tayi baƙone yasa ta ɗan zaro idanunta waje, cikin yanayin mamaki tace. "Ni! Baƙo kuma?" "Eh"  Larae tabata amsa ataƙaice tare da juyawa tabar wajen. Ganin larai'n tatafi ne yasata ɗan lumshe idanunta, tare da juyawa ta koma cikin ɗakin, direct gaban dressing mirror ta ƙarasa tare da ɗan tsayawa ta shiga duba kanta. Riga da sket ɗin atamfa ne ajikinta, wanda akayi masa ɗinkin 8 pieces, yanayin yanda akayi tsarin ɗinkin ne kuma yasa hips ɗinta wanda akullum suke ƙara fasowa suka bayyana, rigar atamfar kuwa da ta kasance fitted sosai ta kama jikinta, yanayin yanda rigartata ta kamata ne yasa shape ɗin lafeffen cikinta bayyana, baƙaramin kyau kuwa kayan yayi mata ba, kasancewar tana da body structure me kyau. Rashin sanin baƙon dake ƙiran nata ne yasata ƙarasawa gaban drawer'nta, ta ciro wani ɗan madaidaicin chiffon vail wanda aka ƙawata jikinsa da adon manyan duwatsun stones. Yafa gyalen tayi akanta, wanda hakan yasa tsawon gyalen ya sauƙo zuwa iyaka guiwar hannunta.  batare da ta tsaya sa takalmi ba, kaitsaye ta nufi falon, zuciyarta ɗauke da mamakin saƙon ƙiran daya sameta, dan kwata kwata batakawo cewar adae dae wannan lokacin wani zaezo nemanta ba. Takun farko na shigarta cikin falon idanunta suka sauƙa akansa. Zaune yake akan kujeran dake facing part ɗinta, yayinda wayarsa ke riƙe ahannunsa yana dannawa, gefe guda kuwa cup ɗin juice ne ke riƙe ahannunsa yana sipping kaɗan kaɗan. Ganin Najeeb ɗinne yasata tsayawa cak daga tafiyan da take, tare dayin ƙasa sa kanta, lokaci ɗaya ta soma wasa sa yatsun hannunta. Najeeb kuwa jin alamun shigowar mutum cikin falonne ya sashi ɗago da kansa, take ya sauƙe idanunsa akan kyakkyawar fuskarta. Lokaci ɗaya yaji wani iska me sanyi ya shigesa, wanda ya sashi lumshe idanunsa tare kuma da buɗesu alokaci guda, sake dubanta yayi haɗe da soma yawo da idanunsa akanta, yana me kallonta tun daga ƙasa har zuwa kan fuskarta. Sosai yaga shigar atamfar jikin nata ya mata kyau, wanda hakan yasashi kasa ɗauke idanunsa akanta. "You look so beautyful!." Yafaɗa in a slowly voice batare da ya bayyana sautin muryarsa ba. Laylerh kuwa da kanta ke ƙasa, ahankali ta ɗan buɗe idanunta, yayinda ta samu kanta da kasa ɗago kae ta kalleshi, dan hakanan taji wani irin nauyin sa ya cika idanunta, sau dayawa takanyi mamakin yanda take samun kanta dajin nauyinsa, bayan haka kuwa batajin komae adangane dashi, domin gabaki ɗaya feelings ɗinta akan mutum ɗaya ne, wato *M.Jay* domin tasa aranta cewa shiɗin na musamman ne, saboda ako da yaushe brain ɗinta jigila take wajen kai da kawowan tunaninsa. Sakeyin ƙasa da kanta tayi, dan taji ajikinta cewar Najeeb din kallonta yake, duk da kuwa cewar bata ganinsa, amma taji ajikinta cewa idanunsa na yawo akanta. Sanin halinsa na kallon ƙurulla ne yasa cikin yanayin sanyi ta ƙaraso cikin falon. Kusa da kujeran da yake kai ta ƙarasa, ahankali taɗan durƙusa akan guiwowinta, batare da ta yarda ta ɗago kanta ba tace. "In kwana.!" Jin amon sautin muryarta ne yasa shi lumshe idanunsa, lokaci ɗaya yaji wani irin nutsuwa ya sauƙar masa, haɗe da zazzafan shauƙinta. Cikin son daidaita nutsuwa da kuma muryarsa yace. "Kafun gaisuwa kyakkyar fuskarki nakeson gani, saboda nayi kewarta sosai, please ki ɗago ki kalleni!." Yanayin yanda ya kai ƙarshen maganan nasa da wata irin tone ne yasa Laylerh ta sake ƙasa da kanta, domin har acikin zuciyarta batason irin kashe murya da kuma kallon da Najeeb ɗin keyi mata. Ganin taƙi ɗago da kan nata ne yasa shi tashi tsaye, tare da ƙarasowa inda take, ahankali ya durƙusa akan guiwowinsa kamar yanda tayi, hakanne da yayine kuwa yasa suka ƙara samun kusanci da juna. Ganinsa da tayi haka agabanta batare dayin zato ko tsammani ba ne yasata ɗan waro manya manyan idanunta waje, cikin yanayin mamaki, da kuma muryarta dake ɗauke da shagwaɓa tace.   "Meye haka, ae bance bazan ɗago da kaena ɗin ba." tafaɗi maganar asangarce. Murmushin daya bayyana fararen haƙwaransa yayi, cikin son kwaikwayon salo irin nata yace. "Basai kin ɗago ba ma ae tunda dai gani nazo kusa dake."  Jin amon muryartasa, da kuma yanda yayi maganar ne yasata ɗagowa ta kalleshi, hakan kuwa shiya bawa idanunta daman faɗawa cikin nasa, ganin irin kallon da yake mata yasa, cikin sauri tayi ƙasa da kanta, tare kuma da sake turo ɗan ƙaramin bakinta gaba. "Why bazaki iya jurewa kallona ba? ko kunyana kike ji?." Ya faɗi maganar yana me kallon yanda take wasa da Ć´an yatsun hannunta. Shiru tayi ta kasa amsa masa, domin ahaƙiƙanin gaskia bata da amsar da zata bashi. Rashin ganin ring ɗin da ya bata da yayi ne, ya sashi zubawa Ć´an yatsun hannunta ido. ahankali ya sauƙe idanunsa akan ring ɗin da ya zame mata tamkar rai da rayuwa. *"L.M"* ya maimaita sunna haruffan dake jikin zoben, wanda har yau kalmomi biyun sun tsaya masa arai, aduk sanda ko yaso yin tunani dangane da kalmomi biyun sai yaji kansa ya kulle. Rumtse idanunsa yayi, sakamakon yansa yaji wani zafi zuciyarsa. Baisan meyasa zuciyarsa ta kasa yarda da zoben dake hannunta'n ba, saboda aduk sanda ya kalli zoben ahannunta sai yaji wani abu na daban azuciyarsa, domin yayi imani cewar zoben bawae nahaka kawai ko kuma na ado bane, tabbas zoben alƙawari ne, alƙawari me matuƙar girma, wanda kuma iya asalin mamallakin zoben ne yasan asalin alƙawarin, wanda aka ɓoye ba ason bayyanarwa. Jin zuciyarsa na ƙoƙarin gaya masa wani abu na dabanne yasa, ahankali yakai hannunsa kan fuskarta tare da ɗan ɗago haɓarta. Take kuwa full face dinta ya bayyana. Ćłan ƙananan laɓɓan bakinta masu launin ja ya zubawa ido, lokaci ɗaya ya haɗiyi wani yawu mai ɗauke da matsanancin sha'awa. Hucin numfashinta daya daki kan fuskarsa ne yasashi lumshe idanunsa, take kuma yaji wani irin feeling ɗinta na shiga jikinsa, yanayin yanda suka samu kusanci sosai ne, ya sashi ji ajikinsa ba abun dayake kwaɗayi kamar kissing kyawawan laɓɓanta, sauƙe mata idanunsa yayi yana me ƙarewa beauty face ɗinta kallo, yayinda yakejin wani irin hot feeling ajikinsa. Laylerh kuwa da gaba ɗaya yanayin ya zame mata baƙo, ganin ya zubawa lips ɗinta ido ne yasa tayi ƙasa da idanunta. Lokaci ɗaya taji zuciyarta ta karye, sanyi haɗi da zazzafar shauƙin Maleek dake kwance acikin zuciyarta ne suka motsa. Tabbas zata so ace ayanzu shine agabanta haka ba Najeeb ba, zataso ace shine akusa da ita, tana shaƙan daddaɗan ƙamshin turarensa dake matuƙar narkar mata da zuciya, zataso ace ta acikin fitinannun kyawawan idanunsa ta jefa nata idanun, yayinda idanunta zasuyi yawo acikin beautyful eye balls dinsa, wanda ganinsu ke haifar mata da matsanancin kasala. Lokaci ɗaya taji gaba ɗaya jikinta ya sake, sanadin hakan kuwa yasa ta lumshe idanunta, wandake cike da masifaffen shauƙin Maleek. Najeeb kuwa har yanzu ya kasa ɗauke idanunsa akanta. feelings dinta yakeji sosai, wanda hakan yasa yake jin kamar yayi hugging dinta, ayanayin yanda yakejin kansa yasan cewa idan suka ci gaba da kasancewa ahaka, lallai zai iya hugging ɗinta kowani lokaci, hakanne ko ya sashi miƙewa tsaye, anutse ya zauna akan kujeran dake gefenta. Ahankali ya ɗaura hannayensa akan kafaɗunta tare da ɗagota ya zaunar da ita akusa da shi, sanadin hakan har arms ɗinsu na gogan juna.  "Laylerh.!" Yaƙira sunanta da muryarsa wanda ta koma can ƙasan maƙoshi. Ƙiran sunan nata ne yasata bude idanunta ahankali, kana cikin sanyin murya ta, amsa masa. Ɗan gyaran zamansa yayi tare da juyowa ya fuskanceta. Tabbas so yake ta fahimci kalamansa, ayanzu so yake ta gane manufa da kuma hujjarsa, duk da cewar bayason bayyana mata irin faɗuwar gaban da yakeji. Ahankali ya kamo hannunta ya riƙe acikin nasa, cikin sanyin murya yace. "Inasonki Laylerh, bansan da yaushe soyayyarki ta shigeni da yawa har haka ba, duk da kasancewar tun aganin farko da nayi miki naji ajikina cewa lallai zamu rayu tare, har yanzu kuwa inaji ajikina cewar lallai zaki rayu aƙarƙashin inuwata." Ajiyar zuciya ya sauƙe, wanda yasa ya ɗan tsagaita da maganar, hannunta dake cikin nasa ya kuma riƙewa. Cikin son gamsar da kansa haɗe da kawar da tunanin dake cikin zuciyarsa yace. "Nasan cewa aurena dake haɗin Allah ne, amma daga wani ɓangare na zuciyata, ina yawanjin faɗuwar gaba, tare kuma da fargaba, inaji ajikina tamkar wani abu zaimin shamaƙi, wanda zai hana zuciyata samun nutsuwa, lallai ina hango wani ƙalubale wanda nasan zuciyata bazata iya jurewa ba, saboda haka nayiwa Abbou Jaheed magana ya kuma dawo da lokacin auren mu kusa, Insha Allah nanda sati 1 zaki zama mallakina tawa halak malak, matata ta har abada, dan hakan ne kaɗai zai gusar min da fargaban dake sukan zuciyata akowacce rana, ina da kishi Laylerh, kishi kuma matsanancin, saboda haka bana fata wani ya shigo cikin rayuwarki." Wani irin dummm da taji acikin kunnenta ne yasa ta ɗago kai ta kalleshi. "Nanda sati ɗaya zaki zama mallakina, matata ta har abada.!" Sune kalmomin da taji sun daki zuciya da kuma dodon kunnenta, haƙiƙa har yanzu takasa yarda da kuma tantancewar wai zata zamo mata ga Najeeb, saboda har yanzu bata samu wani ƙwaƙƙwaran gamsuwa azuciyarta dangane da hakan ba, bugun zuciya da shigar numfashinta duk batare dashi suke tafiya ba, haka zalika babu ko ɗigon dangar takarsa dake yawo acikin jininta, bazata ce tanasonshi ba, haka zalika kuma baza tace tana ƙinsa ba, tabbas ta yarda cewa koda ace shidin yana daga cikin littafin ƙaddaranta, to baikasance ababi me tasiri ba, domin zuciya da tunaninta kwata kwata ba'akansa suke ba. Idanunta dake neman kawo ƙwalla ta lumshe tare da zare hannayenta dake cikin nasa, ahankali ta kawar da kanta gefe, dan karon farko kenan da taji wani abu me kama da ƙuna na yawo acikin ƙirjinta. Najeeb kuwa ganin ta zare hannunta daga cikin nasa ne yasashi jin zuciyarsa tayi wani iri, the first time kenan daya fara tunanin cewa Soyayyar sa bata shiga zuciyar ta ba. "Idan kuwa har dagaske ne babu soyayyar sa azuciyar Laylerh, to waye kenan take so?. "  Yayiwa kansa tambayar da bashi da amsarta. Saurin girgiza kansa yayi domin bashi da  lokacin da zaiyi wani dogon tunani, yanayin yanda yaga canjawar mood ɗinta lokaci ɗaya ne yasashi jin duk wani confidence ɗinsa na zama very low. Ahankali ya tura hannayensa cikin aljihun wandonsa, bandir din fararen Ć´an dubu dubu ɗauri biyu ya ciro daga cikin aljihun nasa, wanda aƙalla zasu kai 100k, kasancewar kowani bandir ɗaya na kudin 50k ne. Sake kamo hannayenta yayi akaro na biyu, ya ɗaura mata kuɗin akan tafukan hannunta. Cikin muryarsa da tayi sanyi yace.  "Gashi kiyi amfani dasu, idan kuma kina da buƙatar ƙari ko wani abu na daban ki sanar dani." Ɗan tsagaitawa da maganar tasa yayi, tare da sake sanya hannunsa acikin aljihun wandonsa, waya ƙiran iphone 11 ya ciro, tare da ɗaura mata wayar akan cinyarta, ahankali ya sanya hannayensa ya juyo da fuskarta, ɗan ranƙwafowa yayi, tare da kissing forehead ɗinta, cikin sanyin murya da haɗe da mood ɗinsa daya sanja lokaci ɗaya yace.  "Please ki kulamin da kanki."  Miƙewa tsaye yayi batare da ya sake duban yanayin fuskarta ba kaitsaye ya juya ya nufi hanyar fita daga cikin falon. da idanunta wanda suka ciko da ƙwalla ta bisa da kallo har ya fice daga cikin falon. Maida idanun nata tayi ta lumshe tare da sauƙe wata irin ajiyar zuciya. Duk yanda taso ga tsaida hawayen dake cikin idanunta kasawa tayi, dole saida suka sauƙa akan fuskarta. Kuɗi da kuma wayar daya ajiye mata takalla,  hakanne yasa taji zuciyarta ta ƙara karyewa,  haƙiƙa so take tayi kuka sosai ko zataji sukunin abun dake addabar zuciyarta. Kudi da kuma wayan daya bata ta ɗauka asanyaye ta wuce ɗakinta. Tana shiga cikin ɗakin nata kuwa anan kan gado ta zube tare da watsar da kudin harma da wayar. Fashewa tayi da wani irin marayan kuka, kukan da ita kanta batasan dalilinsa ba, kukan da tarasa madogara da kuma dalilin yinsa, kana kuma kukan dake fallasa asiri dakuma sirrin zuciyarta, kukane me ɗauke da yanayin yarinta, damuwa, haɗe kuma da ƙunan zuciya. Haka kuwa tasha kukanta ta ƙoshi har bacci ɓarawo ya ɗauketa, wanda kuma ko acikin baccin nata sheshsheƙan kuka ta dinga sakewa. 3:30 pm. Daidai jirginsu ya sauƙa anan cikin airport din Nnamdi azikwe international airport. Abbou Jaheed dake tsaye ajikin motarsa hango ɗan uwan nasa wato Abbou Kareem da kuma matarsa Oum Aisha da yayine yasashi faɗaɗa fari'ar dake kwance akan fuskarsa, cikin matsanancin farinciki ya ƙarasa garesu. Rungume Abbou Kareem din yayi cike da tsananin murna shima Abbou Kareem ɗin ya rungeme ɗan uwan nasa, domin kuwa yanzu kusan shakararsu 1 kenan basu haɗu ba, duk da kasancewar ma Abbou Jaheed ɗin na kaiwa ɗan uwan nasa ziyara lokaci zuwa lokaci. Bayan sun gama murnar ganin junane cikin farinciki Abbou Jaheed ya dubi Oum Aysha dake ta faman sakin murmushi, dan zuciyarta acike take da nishaɗin zuwa ƙasarta da tayi. A mutunce suka gaisa da Abbou Jaheed din. Cikin farinciki Abbou Jaheed yace.  "Bayan lokaci mai tsawo da kuka ɗauka bakwa ƙasar yau gashi kun dawo saboda auren Ć´arku."  Murmushi Oum Aysha tayi cikin zaƙuwa tace.  "Ƙwarai kuwa, bana ma tunanin sake komawa wata ƙasar yanzu gaskia, dan ayanzu naji shauƙin ƙasata sosai, yayinda kuma na ƙosa naga tilon Ć´ata." Murmushi Abbou Jaheed yayi cikin nuna jin daɗin zuwan nasu yace.  "Tabbas nasan Laylerh zatafi kowa farinciki da zuwanku, dan gaba ɗaya rayuwarta acike take da kewa, yanzu kuwa kunzo adaidai lokacin da tafi ko yaushe buƙatarku." Murmushi sukayi su dukansu, kafun Abbou Jaheed ya musu jagora zuwa mota. Kaitsaye suka kama hanyar unguwar ta Asokoro. Koda suka iso gidan cikin kulawa Momy ta tarbesu, duk da kuwa har cikin zuciyarta bataso zuwan nasu ba, musamman ma zuwan Oum Aysha, saboda kwata kwata batason matar. Anan cikin falon suka zauna, inda Momy tasa Larai ta cika musu gabansu da kayan ciye ciye. Basu wani ci abincin sosai ba Oum Aysha da idanunta suka matsu dason ganin Laylerh, ta ture plate ɗin abincin dake gabanta, tare da ɗago kai ta dubi Abbou Jaheed, cikin yanayin ƙosawa tace.  "Nifa idanuna sun matsu dason ganin Laylerh, har yanzu kuma naji ta shiru, kodai bata nan ne?." Murmushi Abbou Jaheed yayi tare dayi mata nuni da hanyar ɗakin Laylerh'n, alaman cewa tana ɗaki. Gane abun da yake nufine yasata miƙewa tsaye kaitsaye ta nufi ɗakin Laylerh'n. Ahankali ta tura ƙofar ɗakin ta shiga bakinta ɗauke da sallama. Tana shiga kuwa idanunta suka sauƙa akan Laylerh'n dake kwance tana bacci, duk da cewar bacci take amma sai sakin sheshsheƙan kuka take, kana cikin sangartacciyar muryarta take ƙiran sunan Maleek. Murmushi Oum Aysha tayi tare da ɗan girgiza kanta, sam batayi mamakin jin da tayi Laylerh'n na ambatan sunan Maleek ba, domin abune da yake tilas, kuma hakan dama baikamata ya zama abun mamaki ba, dan kusan rabin jinin dake gudana ajikin Laylerh'n na Maleek ne, zuciya da kuma ruhinsu ɗaya, haka ma tunaninsu ɗaya. Sake sakin wani murmushi tayi domin tabbas tana ƙaunar ɗiyar ƙanin mijin nata sosai, bawai kuma dan bata taɓa haihuwa bane yasa takeson laylerh'n ba, tana matuƙar kaunar Laylerh'n ne saboda maraicinta. Ƙarasawa jikin gadon tayi ta zauna tare da sanya hannu taɗan dafa goshin Laylerh'n, cikin kulawa taƙira sunanta. Kasancewar bata da nauyin bacci ne yasa ta jin sautin muryar Oum Ayshan acikin kunnuwanta, hakan yasa ahankali ta ɗan buɗe idanunta, cikin sa'a kuwa ta sauƙesu akan Oum Aysha. Ganin kaman gizo idanun nata ke matane yasata tashi da sauri tare da ƙara ware idanunta. Murmushi Oum Aysha tayi cikin kulawa tace. "Buɗe idanunki da kyau Laylerh, niɗince dai Oum Ayush ɗinki bawata daban ba." Cikin wani irin matsanancin farinciki tafaɗa jikin Oum Aysha'n tare da wani irin maƙalƙaleta, zuciyarta cike da tsananin farinciki tace.   "Oyoyo Oum Ayush ɗina, oyoyo nayi kewarku sosai, meyasa kuka daina zuwa wajena keda Abbou Kareem?, meyasa kuka manta dani? bayan kuma kunsan zanyi kewarku sosae?."  Tayiwa Oum Ayshan duka tambayoyin cike da zallan shagwaɓa. Murmushi Oum Ayush ɗin tayi tare da ɗan soma shafa kan Laylerh'n, cikin kulawa tace.  "Am so sorry my daughter bamunki zuwa bane, kinsan yanayin aikin Abbou Kareem din naki babu zama shiasa bamu samu isashshen lokaci munzo ba, kiyi haƙuri ki yafe mana kinji!." Murmushi tayi tare da ƙara shigewa jikin Oum Ayush din, cikin son bayyana farincikinta tace. "Naji dadi sosai Oum Ayush, naji dadin zuwanku ina Abbou Kareem ɗina?." Murmushi Oum Ayush tayi tare da cewa. "Abbou Kareem dinki yana falo."  Tana matuƙar son Ćłan uwan baban nata, domin kuwa suna iyaka ƙoƙarinsu wajen nuna mata ƙauna, hakama Oum Ayush data kasance mata ga yayan baban nata tana nuna mata soyayya sosae kamar uwar da ta haifeta. Cikin yanayin zumudi ta sauƙa daga jikin Oum Ayush din, da sauri ta nufi falon zuciyarta cike da son ganin Abbou Kareem. Da gudu ta faɗa jikinsa haɗe da rungumesa ƙam, cikin yanayin zallar shagwaɓa tace.  "Oyoyo Abbou na."   Murmushi jin dadi Abbou Kareem yayi, cikin jin daɗin ganinta yace.  "Oyoyo Laylerh nayi kewarki sosai."   Jin ya ambaci kewa ne yasata ɗagowa daga jikinsa asangarce tace.  "To ba kune kuka ƙi zuwa ba.!" Murmushi sukayi daga shi har Abbou Jaheed. Kanta yaɗan shafa tare da haɗe hannuwansa biyu waje ɗaya, cike da ƙaunarta yace.  "Tuba muke munsan munyi laifi, hakanne ma yasa muka taho da tsarabar jaka guda na chocolate" Dariya tayi harsaida fararen haƙwaranta suka bayyana.   Cikin jin dadi tace. "Wow thank you Abbou nah.!" Murmushi sukayi dukansu zuciarsu cike da farinciki, saidai banda Momy wanda take murmushin nata abisa dole. Sosai Laylerh tasake acikin iyayen nata, wanda zuwansu ya gusar mata da kaso 70 acikin 100 na damuwarta, suna tare har aka ƙira sallan Magriba, atare su Abbou Jaheed suka wuce masallaci, yayinda Oum Aysha kuwa suka wuce masauƙinsu ita da Laylerh, kasancewar part guda ake ware musu agidan idan sun zo Nigeria. 12:30 am. Amatuƙar razane ta farka daga nannauyan baccin daya ɗauketa, lokaci ɗaya taji duk jikinta ya soma bari, hannayenta dake rawa tasa ta dafe daidai saitin zuciyarta dake bugawa da ƙarfi. Yanayin yanda jikinta ke rawane yasata cije laɓɓanta, tare da rumtse idanunta ƙam, tabbas ta matuƙar tsorata da mafarkin da tayi akansa, ahankali taɗan soma jujjuya kanta da taji yayi mata nauyi sosae, sosai mafarkin da tayin ya ɗata mata hankali, ya kuma hautsuna duk wani tunaninta. Yayinda wani irin tsoro me ɗauke da zallan fargaba ya lulluɓeta, batajin zata iya jurewa, domin zuciyarta ta karye sosai, tsoro takeji kada mafarkin nata ya zamanto gaskiya, hakan yasa ahankali ta zuro da ƙafafunta ƙasa tare da sauƙowa daga kan gadon. Kallon agogon dake saƙale ajikin bangon ɗakin tayi, duk da cewar dare ya raba sosai bata tunanin akwae wani abu dazai hanata zuwa garesa. (Gobe akwae update insha Allah, saboda ba'anan naso tsayawa ba, rashin time ne kawae.) *Wednesday, 16 December.2020* *12:28 pm* 1/19/21, 8:14 PM - Ummi Tandama: *Laylerh Maleek* *Writting By* fatymasardauna *22* Ahankali take tafiya, yayinda kuma zuciarta ke cike da tarin tsoro, domin kuwa babu wani abu dake motsi acikin gidan ko ina ya ɗau shiru, kasancewar awannan lokacin dayawan mutane sunyi nisa acikin baccinsu.  Sam bata damu da duhun da ya mamaye falon ba, haka kaitsaye ta nufi ƙofar da zata sada ta da part ɗinsa. Duk da cewar ayanzu zuciyarta ta fara kawo mata wani abu me kama da tsoro,  saidai sam batajin akwai abun da zai hanata zuwa garesa awannan daren, domin kuwa zuciyarta cike take da son ganinsa, saboda ba kaɗan ba mafarkin da tayi akansa ya ɗaga mata ahankali. Ɗaura hannunta akan handle din kofar tayi tare da tura ƙofar ciki ahankali. Sassanyan ƙamshi da kuma sanyin A/C ne suka daki kan fuskarta, wanda hakan ya tilasta mata lumshe kyawawan idanunta, tare kuma da buɗesu alokaci guda, ayanzu kam tafahimci cewa shi mutum ne me son ƙamshi, wannan yasa ako da yaushe ɗakin nasa baya rabo da ƙamshi. Ahankali ta shiga ƙarewa falon nasa kallo, wanda komai dake cikinsa yake need babu alaman datti ko akasin hakan, duk da cewar babu yalwataccen haske acikin falon, dan blue light ne kaɗai ke kunne, amma hakan baisa ta daina ganin tsarin falon ba. Gaba ɗaya zuciyarta ta riga da ta karye da tunaninsa, hakan yasa kaitsaye ta nufi ɗaya daga cikin ƙofar dake cikin falon, wanda kuma anan bedroom ɗinsa yake. Bata ko tashi jin fargaba da matsanancin faɗuwar gaba ba, saida ta ƙarasa jikin ƙofar ɗakin nasa ta tsaya. Ɗan lumshe idanunta tayi tana me sauraran yanda heart dinta ke beating, take wani irin tsoro ya lulluɓeta, abu biyune aranta wanda na farkon shike ƙara karya mata zuciya, domin kwata kwata batason ace mafarkin da tayi akansa ya tabbata, dan koda da second ɗaya ne batajin zata iya jurewa cutuwarsa, idanunta da suka cika da ƙwalla ta lumshe, lokaci ɗaya mafarkin da tayi ya shiga dawowa cikin kanta, wanda hakan yasa ta riƙe kannata da sauri, yayinda idanunta keyi mata imagine ɗinsa kwance acikin jini kamar yanda tagani amafarkin nata,  cikin sauri ta murɗa handle ɗin ƙofar, tare da tura ƙofar ciki take kuwa ƙofar ta buɗe. Ahankali ta ɗan tura kanta cikin ɗakin, take kuwa taga duhu ya mamaye ganinta, kasancewar ko ɗigon haske babu acikin ɗakin. Ganin duhun ne yasa ta jin wani irin faɗuwar gaba, tare kuma da tsinkewar zuciya, domin kuwa hakan alamace dake nuna mata cewar babu kowa acikin ɗakin, dan da akwae mutum to da dole zai bar haske komin ƙanƙantansa. Kanta taɗan soma girgizawa cike da fargaban abun da zuciyarta ke ƙoƙarin raya mata,  bazata iya jurewa ba domin kuwa taji zuciyarta ta kasa samun nutsuwa, duk kuwa da yanda zuciyarta ke sanar da ita cewar baya cikin ɗakin bata amince da hakan ba. Ahankali ta soma ɗan bin jikin bangon ɗakin, tare da soma laluɓe ko zataji makunnin wuta. Sanin da tayi cewar duka ɗakunan gidan makunnan wutansu kusa da ƙofa ake saka su ne yasa ta bin jikin bangon ƙofar ahankali. Cikin sa'a kuwa taji ta ɗaura hannunta akan makunnin wutan. Idanunta ta rumtse da ƙarfi, sakamakon yanda zuciyarta ke cike da fargaba, haɗi da kuma tsoron abun da zata gani bayan ta kunna hasken, tabbas tana matuƙar jin tsoro, domin tasan acikin biyu dole ne ɗaya saiya faru, maybe kunna hasken da zatayi yasa mafarkinta tabbata, wata kila kuma akasin haka shine baya cikin ɗakin nasa. Ɗanjim tayi tare da sake rumtse idanunta, lallai tabbas tasan cewa acikin biyu za'ayi ɗaya, zuciyarta cike da tsoro da kuma fargaba ta danna makunnin wutan ɗakin, take kuwa gaba ɗaya ɗakin ya gauraye da haske. Atsorace tasoma ɗan ware idanunta dake akulle, inda ta sauƙe ganinta akan haɗaɗɗen gadon dake cikin ɗakin,  gani da kuma nutsuwarta ne suka sauƙa akansa, inda yake kwance anan kan tsakiyar bed din yayi kwanciyar nan irin ta rub da ciki, yayinda kuma yake sanye yake da dogon wando ajikinsa, kasancewar bashi da riga ne yasa faffaɗar surar bayansa dake ɗauke da Ć´an tsirarun tattoo ya bayyana. Sauƙe idanunta akansa da tayi ne yasanya ta sakin wata ƙatuwar ajiyar zuciya, wanda ƙarfi da kuma sautinta ya bayyana, wani irin matsanancin farinciki ne ya shiga zuciyarta, yayinda takejin wani irin daddaɗan sanyi na ratsa har tafin ƙafarta, jingina bayanta da jikin bangon ɗakin tayi, tare da lumshe idanunta, wanda hakan yasa ahankali wasu sirararan hawaye suka silalo daga cikin idanunta. "Alhamdulillah Allah!." tafaɗa cikin wata sassanyar murya dake bayyana zallan abun dake cikin zuciyarta. Ahankali ta kuma buɗe kyawawan idanunta, tare da sauƙesu akansa, wani irin matsanancin farinciki takeji na ratsata, sanadin hakan kuwa yasa bugun zuciya da fitan numfashinta daidai ta. Sauƙe idanunta akansa da ta yine yasata jin wani irin matsanancin shauƙinsa na bin jiki da jininta, ahankali cikin nutsuwa ta shiga takawa zuwa jikin gadon nasa. Ayanayin yanda takejin zuciyarta ta tsumu da matsanancin shauƙinsa, batajin akwae wani abu na daban da zai kawar mata da tunaninsa. Samun kanta da tayi abakin gadon nasa ne yasa ahankali ta zauna abakin gadon, still idanunta akansa yake, yayinda takejin wani irin matsanancin tausayinsa ya rufe mata zuciya, sanadin hakan ko yasa duk wani rauninta ya bayyana. Idanunta wanda ke cike da ruwan hawaye ta sauƙe akan zanen tattoo ɗin dake bayansa, tsaida ganinta tayi akan wani zane da akayi masa me kaman butter flay, sosai zanen yayi mata kyau hakan yasa taji gaba ɗaya ta kwaɗaitu dason taɓa zanen. Batare da tunanin komae ba ahankali ta kai hannunta dake rawa kan fatar bayansa, daidai inda zanen butter flay ɗin yake. Sauƙar hannunta akan fatar bayansa ne yasa tajin wani irin abu me ƙarfi ya shiga jikinta, yayinda lokaci ɗaya tsikar jikinta suka mimmiƙe, saidai kuma taushin skin ɗinsa da taji ya shigeta ne yasa ta kasa ɗauke hannunta daga jikin nasa. Ahankali taɗan lumshe idanunta tare da sauƙe ajiyar zuciya. Cikin muryar dake bayyana tsananin rauninta tace.  "Alhamdulillah Allah Nagode maka, da baka bari mafarkina ya zama gaskiya ba, Allah Na godema daka tsare shi ayanzu, Ya Allah Na Ina roƙonka daka tsareminshi ako da yaushe!." Yanayin yanda takai ƙarshen maganan nata, cike da son bayyana abun dake cikin zuciyarta ne yasa wasu hawaye masu sanyi suka zubo daga cikin idanunta, take kuwa suka ɗiga akan fatar bayansa. Sauƙan hawayen nata akan fatarsa ne yasa taga gargasan jikinsa sun mimmiƙe, yayinda kowani ƙofar gashi dake jikinsa suka bubbuɗe. "Ya Maleek.!!"  Akaron farko ta ƙira full sunansa, cikin wata irin kasallaliyar murya, tun bayan wani lokaci me tsawo daya shuɗe. Sanin cewar bacci yake hakan yasa batasa aranta cewar zae amsa mata ba. Jin bai amsa mata ba ne yasa ahankali ta soma wasa da Ć´ar yatsarta akan fatar bayansa, kana kuma cikin wani sabon  yanayi ta soma zagaye zanen tatto ɗin dake jikinsa. Gaba ɗaya ta shagala kan abun da takeyi masa din, wanda har hakan yasa ta soma sakin murmushi batare da ta sani ba. Ahankali taɗan lumshe idanunta, yayinda takejin wani irin daddaɗan sanyi na ratsa ta, sassanyar ajiar zucia take sauƙewa tare kuma da shaƙan nunfashi me ɗauke da daddaɗan ƙamshin turarensa, wanda daɗinsa ke ƙara kashe mata jiki. Akasalance ta soma yawo da yatsar hannun ta har zuwa tsakiyan bayansa. Zubawa shining skin ɗinsa idanu tayi, dan har acikin ranta tana mamakin yanda skin ɗinsa keda kyau da kuma laushi, ganin yanda gargasan jikinsa ke mimmiƙewa da kuma tsikar jikinsa dake tashi ne yasa taji ƙirjinta ya buga, domin bata fata ace ya farka ya sameta haka, kuma akan gadonsa, sannan tana taɓa masa jiki batare da izininsa ba. Kallon kanta tayi dan sai alokacinne ma ta tuna da rigan dake jikinta, wanda take na bacci ce kuma iyakanta guiwa, gashi gaba ɗaya saman wuyar rigar net ne, wanda hakan yasa kusan gaba ɗaya rabin breast ɗinta suka bayyana kansu ta cikin net ɗin. Da sauri ta sanya hannu ta kare ƙirjinta, dan sai alokacin gaba ɗaya hankalinta ya dawo jikinta,  kasancewar kansa na facing ɗin door ne yasa ahankali taɗan ranƙwafo kansa, dan so take ta duba bacci yake ko kuwa idonsa biyu. Ranƙwafowan da tayin ne kuwa yasa jikinta gogan nasa jikin, yayinda tausasan breast ɗinta suka gogi bayansa. Ɗan leƙa fuskarsa tayi, ganin kyawawan idanunsa arufe ne ya sata sauƙe ajiyar zuciya,  idanu ta zubawa fuskar tasa tana kallon yanda zara zaran eye lashes dinsa suka kwanta lub aƙasan idanunsa, kana kuma ga eyebrow ɗinsa wanda suma suka kwanta lub, yayinda  gashin  nasa ya kasance baƙi siɗik dan har wani shining yake. Ahankali ta sauƙo da idanunta zuwa kan dogon hancinsa, da kuma ɗan ƙaramin bakinsa, wanda ke ɗauke da jajayen laɓɓa masu sheƙi. Ƙurawa lips ɗin nasa idanu tayi bata ko ƙyaftawa, domin ba ka ɗanba suka mata kyau, kana kuma sukayi matuƙar burgeta. Hakanan taji wani irin abu na tsirga mata, lokaci ɗaya kuma taji wani irin abu na yawo acikin tafukan ƙafarta, hakanne ko ya tilasta mata lumshe ido tare da sakin numfashi, lokaci ɗaya taji duk jikinta yayi weak, yayinda kasala ya sauƙar mata. Sake lumshe idanunta tayi akaro na barkatai cikin muryarta daya zama very silent tace.  "Kana da kyau Yah M.Jay, ban taɓa ganin wani irinka ba, your so so beautyful.!!" tafaɗi hakan tana me sake ninƙaya acikin wani sabon shauƙin da ta samu kanta. Ƙaran bugawan agogon dake aje kan bedside din gadonne yasata bude idanunta da sauri ta kalli agogon 1:00 am daidai agogon ya nuna, ganin hakane yasa ta ɗan zaro idanunta waje dan gaba ɗaya ta shagala. Cikin sauri ta matsa daga jikinsa tare da zuro da ƙafafunta ƙasa. Tana sauƙa daga kan gadon nasa kuwa ta soma ƙoƙarin gyara rigar jikinta. Ɗagowa tayi ta kallesa, ganin yanda yake fitar da numfashi ahankali ne yasata ɗan lumshe ido, cikin sanyi da kuma daɗin murya tace.   "Have a sweet dreama Yah M.Jay!." Ahankali ta juya cikin takunta me ɗauke da nutsuwa ta nufi hanyar fita daga ɗakin. Sam tama manta da batun kashe wuta haka tayi ficewarta. Jin alamar fitanta daga cikin ɗakinne yasa ahankali ya buɗe idanunsa wanda suka sauya launi daga kalan fari zuwa ja, yayinda kuma suka rikiɗe suka koma zallar sexy eyes wanda suke ɗauke da zallar wutar sha'awa acikinsu, kana kuma suka bayyana da kuma fallasa asirin dake cikin zuciyarsa. Hanyar da tabi ya zubawa ido, haka yakejin tsikar jikinsa na ci gaba da tashi, yayinda kuma gargasan jikinsa ke ƙara miƙewa, the first time kenan da yaji wata irin mahaukaciyar sha'awarta na neman fasa masa mara. Domin kuwa tun shigowarta falonsa yaji motsin mutum, kana kuma har ta shigo cikin ɗakin idanunsa biyu, duk wani abu da ta aikata ta kuma faɗa yana jinta, saidai rufe idanunsa da yayi yasa ta ga kamar bacci yakeyi, tabbas baƙaramin juriya yayi ba, domin alokacin da ta ɗaura hannunta akan tsakiyar bayansa, wani irin masifaffen shock ne ya shiga jikinsa, take kuma jarababbiyar feelings dinsa ta motsa, lallai ya daurewa hakan, domin yanayin yanda take wasa da Ć´an Ć´atsun hannunta akan bayansa baƙaramin ruguza masa lissafi yayi ba,  saidai kuma azuciyarsa cike yake da mamakin abun da zai kawota ɗakinsa acikin daren,  tabbas ayau lallai ya yarda cewa da So da kuma sha'awa mataki mataki ne, saboda ya fahimci cewa aso da kuma sha'awar Laylerh ya tafi zuwa wani mataki na daban, babban mataki wanda bakowa ke iya hawansa ba. Sannan Ayau ya sake tabbatarwa da kansa cewa shi me matuƙar Rauni ne akanta, sannan kuma duk wani fata da burinsa akanta ne, ayayinda jini ke guda ajikin kowa shi ƙaddararsa da ta Laylerh ce ke gudana acikin jikinsa. A karon farko na gaba ɗaya tarihin rayuwarsa kenan dayaji zuciyarsa ta karye da gasken gaske. Idanunsa dake neman fallasa zallan ɗaci da kuma raɗaɗin dake kwance acikin zuciyarsa ya rumtse da ƙarfi, tare kuma da haɗiye wani yawu me ɗaci da ya tsaya amaƙoshinsa. Tunowa dayayi cewar Abbou Jaheed ya hanasa komawa USA ne yasa shi jin wani sabon abu ya tokare masa maƙoshi, haƙiƙa ƙaddarori sun kewaye rayuwarsa, saidai ako da yaushe yana fata da kuma burin cimma nasara, domin kuwa har yanzu yana nan akan bakansa cewar bazai taɓa zama Me kasawa ba akullum akuma koda yaushe. Akaron farko kenan daya fara ƙokarin saka kansa baccin dole, duk da kuwa cewar baccin ya ƙauracewa idanunsa tuntuni, saidai ya zame masa dole ya ƙaƙalo baccin matuƙar yana son tseratar da rayuwarsa daga bugawar zuciya. Laylerh. Kanta tsaye tafita daga falon nasa, koda ra fito kuwa anan cikin babban falon gidan ta samu kanta, batare da ta damu da dubun da ya mamaye falon ba ta nufi ɗakinta. Ganinsa yasata jin zuciyarta ta mata sanyi, yayinda duk wani damuwa dake kwance acikin zuciyarta ya yaye. Tabbas tayi imani cewa. M.Jay ɗin daban yake da kowa. Locking ƙofar ɗakin nata tayi sannan ta koma ta kwanta. Kasancewar zuciyarta cike take da farinciki hakan yasa bata wani jima ba bacci ya sake ɗaukanta. *(Note editing)* 1/19/21, 8:14 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna *(This book is mainly for those that pay, if you know you did'nt pay please don't read it. Here is the account number for people that are willing to pay-0002214625 Abubakar Muhammed Sardauna Jaiz bank. Whatsapp number 07017879464. )*                  *Chapter 23* Maleek. Sama da 20 minute ya ɗauka yana ta faman juyi akan gado, duk yanda ko yaso bacci ya ɗaukesa ya kasa, haƙiƙa  shigowarta cikin ɗakin nasa yasa yayi losing duk wata nutsuwarsa, yayinda ahankali yakejin wani nannauyan kasala na sauƙar masa, again ga kuma  wani sabon hot feelings ɗinta dake sukar duk wata kafar sadarwa na jikinsa, wanda kuma sanadin hakanne ya sashi kasa rumtsawa. "Yah Maleek." Sautin amon sassanyar muryar da taƙira sunansa da shi ne ya shiga dawowa cikin kunnensa,   ahankali ya soma tuna yanda take zagaye Ć´ar yatsar hannunta akan  fatar bayansa, wannan yasa batare daya sani, ko shiryawa hakan ba ya saki wani ƙawataccen murmushin daya bayyana zallar kyawunsa, ahankali ya ɗan lumshe idanunsa, dan so yake bacci ya ɗaukesa tunkan tunaninsa ya koma ga wani fanni na daban. Duk da cewar zuciyarsa na ƙoƙarin raya masa wani abu na daban, ƙin bata daman hakan yayi saboda ayanzun yafi buƙatar bacci fiye da komae.  Cikin abun da bai wuce 15 minute ba kuwa yayi sa'a  bacci ya ɗaukesa. Washegari. 9:00 am Daidai ahankali ta buɗe idanunta wanda suka cika da yanayin bacci, miƙa tayi tare dayin hamma, kana  cikin nutsuwa ta zuro da kyawawan ƙafafunta ƙasa. Idanunta dake ɗan gane mata dishi dishi ta murza, ahankali ta sauƙo daga kan gadon tare da miƙewa tsaye. Yanayin yanda taji jikinta ya zama very weak sosai ne ya sa ta ɗan lumshe idanu, tare dasa hannu ta dafe kanta dake ɗan sarawa kaɗan kaɗan, wanda  kuma tuni hakan ya zame mata sabo, dan kusan ko wacce rana idan ta kwanta da ciwon kai take tashi. Kaitsaye bathroom ta nufa, dan tasan idan tayi wanka zata daina jin ciwon kan. Ahankali ta murɗa handle din ƙofar bathroom ɗin ta shiga, cikin nutsuwa ta cire rigar baccin dake jikinta, tare da ƙarasawa gaban shower, akasalance ta sakarwa kanta ruwa. Jin sauƙan ruwan shower'n ajikinta ne yasata sauƙe ajiyar zuciya, take kuwa moment ɗinta na daren jiya ya shiga dawo mata, tunawa da kyakkyawar fuskarsa da tayi ne yasa ta sakin murmushi har saida fararen haƙwaranta suka bayyana, tabbas yanayin na jiya yayi mata dadi sosai, domin sanadinsa ne yasa takejin zuciyarta wasai, haka kuma acikin kaso ɗari na damuwarta tayi loosing kaso hamsin. Yanayin yanda ɗumin ruwan shower'n ke sauƙa ajikinta ne yasata lumshe idanunta akaro na barkatai takuma sauƙe ajiyar zuciya. Yayinda takejin wani ɓangare na zuciyarta, na ƙoƙarin aikawa ƙwaƙwalwarta wasu tunani ma ban banta. Sanin da tayi cewar idan ta biyewa tunanin zata matuƙar ɓata lokacinta ne, yasa take ta soma ƙoƙarin zeroying mind ɗinta. Wanda hakan yasa tayi wankanta cikin nutsuwa. Koda ta kammala wankan wani light peach colour ɗin bathrobe tasa ajikinta, saboda  yanayin weather'n garin yasa ana ɗan busa sanyi kaɗan, wani ɗan ƙaramin farin towel ta ɗauka tare da naɗe dogon gashin kanta wanda ke jiƙe da ruwa, anutse ta ƙarasa gaban sink din dake cikin bathroom ɗin, brush tayi haɗe da sake wanke fuskarta, kana cikin nutsuwa ta fice daga cikin toilet ɗin. Koda ta fito daga cikin bathroom ɗin akan Agogon dake saƙale jikin bangon ɗakin ta sauƙe idanunta 9:30 am daidai da ta gani ne yasa taɗan zaro idanunta waje, don kwata kwata bata kawo aranta cewar ta ɓata lokaci abaccin nata har haka ba, saboda tunda ta tashi tayi sallan asuba ta sake komawa wani sabon bacci, bata tashi ba sae yanzu. Ganin babu wani wadataccen lokaci ne yasata ɗaukan towel cikin nutsuwa ta shiga goge jikinta, tana gama goge jikin nata kuwa ta ƙarasa gaban dressing mirror. Wani body lotion me sauƙin ƙamshi ta shafa ajikinta, tare kuma da feshe jikinta da body spray ɗinta me daɗin ƙamshi, wanda ƙamshinsa ke matuƙar samar da nutsuwa, dan irin ƙamshin nan da baifiye tashi bane dashi, dan sometimes ba me jin ƙamshin har sai idan mutum ya samu kusanci da ita sosai ne zai iya jiyo ƙamshin. Dama kwallia ba aikinta bane, hakan ne kuma yasa bata wani tsaya shafa powder da jambaki ba direcɗ ta nufi wajen drawer'nta. Koda ta bude drawer'n wani riga da sket ɗin material me kalan baƙi ta ciro, wanda aka ƙawata gaba ɗaya jikinsa da adon fararen duwatsun white stones. Anutse ta sanya kayan da yayi matuƙar amsar jikinta, dan kuwa baƙaramin kyau material ɗin yayi mata ba, yanayin yanda kayan ya lafe ajikinta ne yasa cikakkun hips ɗinta bayyana. Dogon gashinta dake bin bayanta ta tubke da wani babban ribbom, sake komawa gaban dressing mirrorn  tayi tare da zubawa kanta idanu. Ita kanta tasan tayi kyau sosai, hakanne ko yasata sakin murmushi,  ita kanta tana mamakin yanda kowani kaya tasa saiya mata kyau, ɗan kwalin material ɗin nata ta yafa akanta, kasancewar kuma yana da ɗan girmane yasa shi sauƙowa har bayanta. Tun tashinta takejin cikinta na kukan yunwa,  wannan yasa tana gama kimtsa kanta bata tsaya wasa ba ta zura wasu flat shoe masu kalan fari aƙafanta, zuciyarta cike da ɗokin ganin Mr. Beautyful Eyes ɗinta, ta murɗa handle ɗin ƙofar ta fita. Zaune suke dukansu akan dining table ɗin cikinsu kuwa harda Najeeb. Wanda shigowarta cikin falon yayi daidai da ɗago kansa da yayi, take kuwa ya sauƙe idanunsa akanta. Wani irin kyau'n da yaga tayi masa ne ya sashi dan lumshe idanunsa tare da sauƙe ajiyar zuciya. Laylerh kuwa ganinsa da tayi ne yasa ta sauƙar da kanta ƙasa, tare da ƙarasowa kan dining table ɗin. Ganin Laylerh'n ne yasa Oum Ayush sakin murmushi, cikin kulawa tace.  "Laylerh kin tashi?." Murmushine ya bayyana akan fuskarta, ahankali taɗan jinjina kai alaman "Eh" ɗago kanta tayi tare dakai dubanta zuwaga su Abbou Jaheed dake zaune, cikin nutsuwa ta gaishesu, inda suka amsa mata fuska asake, Abbou Kareem ne ya ɗago kai ya dubeta, cikin yanayin tsokana yace. "Sarkin shagwaɓa har antashi?." Murmushi me kama da dariya tayi  cikin nutsuwa da kuma bayyana  farincikin dake ranta tace.  "Eh Abbou nah na tashi, saidai kuma kwana nayi ina mafarkin chocolate ɗin dakace kakawomin.."    Dariya sukayi dukansu, cikin kulawa Abbou Kareem ɗin yace.  "To bari mugama cin abinci saina ɗauko miki."  "To." tafaɗa cikin jin daɗi, dan tasan chocolate ɗin dayake kawo matan daɗinsu na musammne  Juyowa tayi tare da gaishe da Oum Ayush, fuska ɗauke da murmushi Oum Ayush ta amsa mata, tare da tambayarta yanda ta kwana, da "Lapia." ta amsa mata kana ta juya ta gaishe da Momy,  ganin su Abbou Kareem ɗinne yasa Momyn ta amsa mata cikin sakin fuska. Ɗaya daga cikin kujerun dining ɗin taja ta zauna, kasancewar kujeran nata na facing ɗinsa ne yasa batare da ta ɗago kai ta kalleshi ba, cikin tura baki tace  "Ina kwana." Murmushin daya bayyana haƙwaransa yayi batare kuma daya amsa mata ba ya ci gaba da zuba mata idanu, dan yau ɗin sosae tayi masa kyau. Jin bai amsata bane yasa ta murguɗa baki, cikin zuciyarta tace.   "Dama ni banaso ka amsa mayen kallo kawae." Yanayin yanda tayi maganan tana mamul mamul da bakinta ne yasashi karantar abun da take faɗi. Wani irin dariya ne ya kamasa amma sanin cewa su Abbou Jaheed na wajen yasa shi shanye dariyar tasa, laɓɓan bakinsa yaɗan ciza cikin zuciyarsa yace.  "Daga yau kwana huɗu ne kawae ya rage na mallakeki, saboda haka ki tabbatar daga wannan lokacin bazaki tsira ahannuna ba, dan sai na cinye wannan bakin tsiwan naki."  Ya ƙare zancen zucin nasa yana me sakin wani shu'umin murmushi. Laylerh kuwa plate ɗin abincin da Oum Ayush ta ajiye agabanta wanda yake ɗauke da chips and ketchup da kuma soyayyen ƙwai ta kalla, ahankali ta fito da tongue dinta tare da ɗan lashe lips ɗinta, sosai abincin ya shiga ranta, dan tanason chips saboda yana ɗaya daga cikin favorite foods ɗinta. Spoon ta ɗauka tare da soma cin abincin cikin nutsuwa. Gaba ɗaya dining table din ya ɗauki shiru yayinda kowa ke cin abincinsa anutse. Ɗan lumshe idanunta tayi haɗe da sauƙe ajiyar zuciya, kwata kwata bataji dadin rashin ganinsa a dining table ɗin ba, saboda sosai zuciyarta ta azalzaleta da son ganinsa. "Miss you so much.!" ta faɗa acikin zuciyarta tare da sakin wani gauron numfashi. Tabbas idanunta cike suke dason ganinsa, saboda har yanzu mood ɗin jiya na mata yawo acikin jiki da jininta, wanda kuma tayi imani cewa har abada bazata taɓa iya manta moment ɗinba, domin shine moment na farko daya tsaya acikin mind ɗinta. Tuna yanda take wasa da yatsarta akan zanen butterflay ɗin dake bayansa ne yasata sakin murmushi, cikin matsanancin shauƙin daya ɗebeta tace. "he is beautyful." yanayin yanda ta motsa laɓɓan bakinta ne yasa sautin maganar nata fitowa batare da ta shiryawa hakan ba, jin sautin muryar na ta ya bayyana ne yasa cikin sauri ta sanya hannu ta toshe bakinta, tare da ɗago kanta da sauri tasoma rarraba idanu, dan dan bata fatan ace wani yaji abun da ta faɗa. Idanunsu ne suka sarƙe acikin na juna, kasancewar tuntuni ita yake kallo. Yanayin kallon da yakeyi mata me ɗauke da alamar tambaya ne yasata yi ƙasa da kanta, tare da sa teeth ɗinta ta ciji beautyful lips dinta. Ganin ta sunkuyar da kanta ƙasa ne yasashi gane cewar lallai akwae abun da zuciyarta ke saƙa mata na daban. "he is beautyful." ya maimaita kalmar dayaji ta faɗa. "Wa kenan?."  yayiwa kansa tambayar da bashi da amsarta. Tabbas yasan cewa so da kuma burin aurenta azuciyarsa suke, saidai baisan meyasa ako da yaushe yake ƙara jinta acikin jikinsa ba, haƙiƙa yanaji ajikinsa cewa kamar idanunsa na ƙoƙarin rufewa, ta yanda zasu kasa gane masa abun dake kwance acikin zuciyar ta, saboda lokuta da dama idan yaso nazartar zuciyarta fargaba da kuma tsoro ne ke lulluɓeshi, dan ko da da second ɗaya ne baya so ya fahimci cewa akwae wani azuciyar Laylerh'n, saboda ya riga daya kai maƙura ta yanda bayaji ajikinsa cewar zai iya sadaukar da ita ga wani. Wani irin gauron numfashi yaja tare da aje spoon din dake hannunsa, ahankali ya soma ƙoƙarin miƙewa tsaye. Ganin Najeeb ɗin ya tashi tsaye ne yasa Abbou Jaheed ɗago kai ya dubesa cikin kulawa yace.  "Najeeb ya akayi?."  Murmushin dole ya ƙaƙalo ya ɗaura akan fuskarsa, tare da ɗan soma shafa sumar kansa, cikin yanayin girmamawa yace.  "Naƙoshi Abbou kuma banaso na makara dan akwae wani project da zanje na duba." Cike da gamsuwa Abbou Jaheed ya jinjina kai tare dayi masa fatan nasara da kuma dawowa lapia. Da "Ameen" ya amsa sannan kaitsaye ya fice daga cikin falon. Laylerh dake binsa da kallo ƙasa ƙasa   ganin ya fita ne yasata sauƙe ajiyar zuciya, dan dama ta ƙosa ya tafi din, saboda irin yanayin kallon da yake mata takurata yake. Cikin nutsuwa ta kammala cin abincin nata, tare da ɗaukan tissue ta goge bakinta. Ƙoƙarin miƙewa tsaye ta soma yi, saidai ƙiran sunanta da Abbou Jaheed yayi yasata dakatawa tare da ɗago kai ta kalleshi, cikin sanyin muryarta tace. "Na'am Abbou." Abbou Jaheed dake zaune yana cin abinci batare daya ɗago kai ya kalleta ba yace.  "Yaushe ne zaku fara exam?." Jin tambayar nasa ne yasa ta sauƙe ajiar zuciya, dan batayi tunanin cewa hakan zai tambayeta ba.  "Monday!." ta basa amsa tana me wasa da yatsun hannunta. Kai Abbou Jaheed ɗin ya jinjina cikin kulawa yace.  "Yayi kyau, amma kinsan yanzu babu maganar zuwanki makaranta ko." Jin maganartasa tayi mata zuwan bazata ne yasa ta ɗan zaro idanunta waje, cikin yanayin mamaki haɗi da ɗaure kae tace. "Abbou Exam fa zamu fara..." Katseta daga maganan nata Abbou Jaheed yayi tare da cewa. "Nasan exam zaku fara saboda haka already nasamu principal na makarantar taku munyi magana dashi, so rashin zuwanki bazai zamo wata matsala ba insha Allah, saboda nayi masa maganar cewa inaso kiɗau hutu na 2month ya kuma amince." Idanunta ne suka ciko da hawaye, yayinda taji gaba ɗaya zuciyarta ta karye, koda wasa bata taɓa kawo aranta cewa wae saboda auren nata Abbou Jaheed zai hanata zuwa makaranta ba, shikenan yanzu duk karatun da tayiwa exam ɗin ya tashi abanza? Jin hawaye na ƙoƙarin sauƙa akan fuskarta ne yasa tayi saurin juyawa tabar dining table ɗin. Da kallo Oum Ayush ta bita sakamakon ganin yanda gaba ɗaya mood dinta ya sanja, ahankali ta miƙe tsaye tare da rufawa Laylerh'n baya. Tana shiga cikin ɗakin nata ta saki kuka me sauti, tare da faɗawa saman gado ta shiga rera kuka, gaba ɗaya bataji daɗin hukuncin da Abbou Jaheed din ya yanke mata ba. Ahankali Oum Ayush taturo ƙofar ɗakin ta shigo,ganin Laylerh'n na kukane yasata tsayawa ajikin ƙofar ta zuba mata ido. Laylerh dake kuka jin an buɗe ƙofar ɗakin nata ne yasata ɗago kanta da sauri, wanda hakan yasa ta sauƙe idanunta akan Oum Ayush ɗin. ganin Oum Ayush ɗin nata ne yasata sauƙowa daga kan gadon cikin sauri taje ta faɗa jikinta tare da rungumeta ƙaƙam, ta sake sakin sabon kuka. Ajiyar zuciya Oum Ayush ta sauƙe, yayinda ahankali ta shiga shafa bayan Laylerh'n. Kanta ta ɗan soma girgizawa, cikin yanayin sheshsheƙan kuka tace.  "Shikenan yanzu Oum Ayush bazan sake zuwa makaranta ba?" Kai Oum Ayush ɗin ta girgiza tare da kamo kafaɗunta ta ɗagota hakan yasa suka zama suna fuskantar juna, murmushi Oum Ayush ɗin tayi kana cikin kulawa tace.  "Waya faɗa miki cewa bazaki sake zuwa makaranta ba, zakije makaranta mana Laylerh, bakiji me Abbou Jaheed ya faɗa ba, hutu kawai ya ne mamiki na wata biyu, bayan kuma lokacin ya cika zaki cigaba da zuwa makarantarki kamar yanda kika saba, ki share hawayenki kinji, saboda na tabbata Abbou Jaheed bazai taɓa yi miki abun da zai cutar da rayuwarki ba,  duk da cewar bansan me kikeji akan aurenki da Najeeb ba, amma nayi imani cewa Abbou Jaheed bazai miki mummunan zaɓi ba, sannan kuma inaso kisa aranki cewar kamar yanda kowani bawa yake tafiya da ƙaddaransa, haka kema kike tafiya da taki ƙaddaran, ki kuma sa aranki cewa Auren ki da Najeeb shima wata ƙaddara ce ta daban, sannan kuma inaso kisani ba ko da yaushe ne kuka ke maganin damuwa ba, wani lokaci jajircewa da kuma addu'a sune abu mafi tabbas wajen kawar da duk wata damuwa, kisa hakan aranki kinji!." Ta kai ƙarshen maganar nata cikin lallami, haɗi da yiwa Laylerh'n nuni akan yanda zata fuskanci rayuwa. Duk da cewar ƙwaƙwalwa da kuma tunaninta basu gama fahimtar abun da kalaman Oum Ayush ɗin ke nufi ba, saidai taji a zuciyarta ta samu gamsuwa, wanda hakan yasa ahankali ta sa hannu ta goge hawayen  dake kwance akan fuskarta.. Ganin ta goge hawayen nata ne yasa Oum Ayush sakin murmushi cikin kulawa tace.  "Yauwa ko kefa, kidaina yawan sa damuwa aranki kinji."  Kai ta jinjina tare da sake shigewa jikin Oum Ayush ɗin ta rungumeta, tabbas tanayiwa Oum Ayush ɗin kallon uwa kuma mahaifiya, wanda hakan yake sawa taji cewar har yanzu tana da garkuwa, kana kuma mahaifiya me sharewa Ć´arta hawaye ako da yaushe. Hannunta Oum Ayush ɗin ta kama cikin kulawa tace. "Muje part ɗina saboda yau ya kamata afara miki gyaran amarya na musamman, da tunjia naso mu fara amma ganin ba lokaci yasa na bari sai yau." Ayanda jikinta gaba ɗaya yayi sanyi ne yasa ba musu tabi bayan Oum Ayush ɗin. Kaitsaye sashin Oum Ayush ɗin suka nufa. koda suka ƙarasa cikin falon, kallonta Oum Ayush tayi tare dayi mata nuni da ɗaya daga cikin kujerun falon,  gane abun da Oum Ayush ɗin ke nufi ne yasata zauna akan kujeran. Ita kuwa Oum Ayush kaitsaye ɗaki ta wuce. Bata wani jima sosai ba ta fito hannunta ɗauke da wani ɗan ƙaramin towel, da kuma wani ɗan madaidaicin bowl wanda aka zuba wani abu me kaman kwaɓaɓɓen madara aciki. Miƙa mata towel ɗin Oum Ayush tayi tare da cewa "Tashi kije ki cire kayanki." "To" tace haɗe da karɓan towel din, kaitsaye ta wuce ɗakin Oum Ayush ɗin. Cikin nutsuwa ta cire riga da sket ɗin dake jikinta tare da ɗaura towel ɗin, wanda tsawonsa ya tsaya iyaka cinyarta. Babban madubin dake kafe ajikin bangon ɗakin ta kalla, ganin yanda gaba ɗaya surar jikinta ya bayyana ne yasa duk taji kunya ya rufeta, saidai babu yanda zatayi dole ahaka ta bude ƙofar ta fita. Anan kan wani darduma Oum Ayush ta zaunar da'ita tare da sawa ta miƙe ƙafafunta. Cikin nutsuwa Oum Ayush ta shiga shafa mata wannan kwaɓaɓɓen abu me kaman madaran ajikinta, ƙamshi da kuma sanyin abunne ya sata lumshe idanunta, tare da ɗan jingina kanta da jikin kujera. Cikin abun dabai wuce 20 minute ba kuwa Oum Ayush ta gama shafe mata duka abun ajikinta, wanda yasa gaba ɗaya falon ya cika da ƙamshi,  wani ruwa me kaman oil Oum Ayush ɗin ta shafa mata akan fuskarta. Tsawon 30 minute ta ɗauka zaune awajen, ganin abu ya bushe ne yasa Oum Ayush soma mummurza jikin Laylerh'n, ɗan rumtse idanunta tayi saboda yanda Oum Ayush ɗin ke murje mata fata yasa tana ɗanjin zafi kaɗan. Hannunta Oum Ayush ɗin ta kamo suka ƙarasa bedroom, kasancewar tuni ta haɗa mata ruwan ƙamshi ne yasa kaitsaye ta jata zuwa toilet. Nuna mata bathrobe ɗin dake cike da wani brown ɗin ruwa me tsananin ƙamshi Oum ɗin tayi,  kana cikin kulawa tace. "Kishiga ki kwanta, kuma ki tabbatar kin buɗe jikinki yanda ruwan zai ratsaki da kyau, 30 minute zakiyi, idan time ya cika zan miki knocking door saiki fito." Da to kawae ta amsawa Oum ɗin dan gaba ɗaya jikinta yayi luƙus. Ganin Oum Ayush ɗin tafita daga cikin toilet ɗinne yasata zare towel din dake jikinta,  anutse ta ƙarasa jikin bathtube ɗin tare da shiga ciki ta kwanta. Daddaɗan ɗumin ruwan da kuma ƙamshin daya ratsata ne yasata lumshe idanunta, tare kuma da sake nutsa jikinta cikin ruwan, ahankali ta shiga sauƙe ajiyar zuciya, yayinda kuma lokaci ɗaya taji wani irin daddaɗan bacci na neman ɗaukarta. Kanta ta ɗaura akan saman bathtube ɗin, hakan yasa ko mintuna biyu ba ayi ba bacci ɓarawo ya ɗauketa. Cikin baccin nata ne taji ana knocking ƙofar toilet ɗin. Da sauri ta buɗe idanunta, sanin cewa Oum Ayush ne ke knocking ɗin, yasa ta fitowa daga cikin bathtube ɗin. Wani sabon towel  ta ɗaura ajikinta. Gama ɗaura towel ɗinnata kuwa yayi daidai da shigowar Oum Ayush cikin toilet din. Jin yanda lokaci ɗaya jikin Laylerh'n ya game da ƙamshi ne yasa Oum Ayush ɗin  sakin murmushi, hannun Laylerh'n ta kamo tare da buɗe tafukan hannun nata, ta fesa mata wani abu dake riƙe ahannunta me kaman turare, sanyin abun da kuma ƙamshinsa me masifar daɗi ne yasa Laylerh ta lumshe idanunta, lokaci ɗaya tunanin Ya M.Jay ɗin ya fado cikin brain ɗinta, domin tasan cewa  shine mutum me tsananin son ƙamshi, sanyin da taji aranta ne yasa ta saki murmushi. Oum Ayush dake kallonta itama murmushin tayi cikin salon tsokana tace. "Murmushin me kike kodae kin tuna da angon naki ne?." Jin an ambaci angonta ne yasata shagwabe fuska tare da turo ɗan ƙaramin bakinta gaba, cikin yanayin shagwaɓan daya zame mata sabo tace.  "Ni wallahi ban tuna dashi ba." Dariya maganar tata ta bawa Oum Ayush, saidai bata bari dariyar tata ta bayyana ba, madadin haka sai ta kamo hannun Laylerh'n suka fito daga cikin toilet ɗin. Tabbas har acikin ranta ta gano cewar  akwae wani abu da Laylerh ke ɓoyewa acikin zuciyarta, wanda kuma ita tasan ko meye ke cikin zuciyar Laylerh'n, domin ga mutum ne fahimta da kuma saurin nazarta,  kallo ɗaya kawai zaiyiwa cikin idanun Laylerh'n ya karanto duk wani abu dake kwance acikin zuciyarta, fahimtar hakan da tayi ne kuma yasa tun zuwansu jiya da taga Laylerh'n taji gaba ɗaya zuciyarta ta karye, saidai lokaci ya riga daya ƙure saboda  bata da yanda zatayi akan hakan,  amma  kuma abu ɗaya tasa aranta shine INDA RAI DA RABO, saboda babu wanda ya isa ya hana hukuncin Allah Faruwa, lallai ne kuma tilas abun daya tsara shi zai faru babu wanda ya isa ya hana, domin kuwa ƙaddara na iya sauyawa ako da yaushe. Sake hannun Laylerh'n tayi tare da ƙarasawa Inda da ta ajiye burner wanda ta zuba masa turaren ƙamshi da game jiki acikinsa, kunna burner'n tayi tare dayiwa Laylerh alaman cewa ta zo ta tsugunna agaban burner'n, Laylerh da gaba ɗaya son ƙamshi ya shigeta, cikin hanzari tazo ta tsugunna agaban burner'n. lulluɓeta Oum Ayush ɗin tayi da wani babban mayafi, wanda hakan yabawa turaren daman game gaba ɗaya jikinta. 15 minute ta ɗauka turaren na bin jikinta, kafun Oum Ayush tace mata ta tashi hakanan. Wani cup dake ɗauke da maganin da aka dama shi da madara Oum Ayush ɗin ta miƙo mata tare da cewa ta shanye sa tas. Aɗan tsorace takai cup ɗin bakinta, dan duk atunaninta maganin zaiyi ɗaci, harshenta tasa taɗan lasa maganin, jin babu ɗaci ne yasaka ta sakin murmushi, kasancewarta gwanan shan zaƙi take ta shanye gaba ɗaya maganin, harda su sucking lips ɗinta. Again wani magani me kaman zuma Oum Ayush ɗin ta miƙo mata, babu Musu kuwa ta karɓa ta shanye, tana shanyewa kuwa ta soma suɗe bakinta, saboda wanda tasha yanzun yafi na farkon zaƙi. Ajiye cup ɗin tayi tare da zama akan ɗan madaidaicin bedside carbinet ɗin dake cikin ɗakin. Wata doguwar riga marar nauyi Oum ayush ta miƙo mata tare da cewa tasa. Babu musu kuwa ta amshi rigar tasa, wanda gaba ɗaya jikinta ke fitar da daddaɗan ƙamshin humra. Hijab da kuma takalmi Oum Ayush din ta bata tasa, sannan itama ta shirya kanta, duban Laylerh'n tayi cikin kulawa tace. "Taso muje unguwa." Jin cewar fita zasuyi ne yasata miƙewa cikin sauri ta bi bayan Oum Ayush wanda tuni tayi gaba. Koda suka fito compound ɗin gidan, kaitsaye wajen da tarin motocin gidan ke fake suka nufa, wata baƙar benz Oum ayush ɗin tasa driver ya fito mata dashi, kasancewar da kanta takesonyin driving ne yasa ta buɗe murfin motar tare da shiga ɓangaren driver. Ganin hakanne kuwa yasa Laylerh shiga gefen me zaman banza ta zauna. Cikin ƙwarewa Oum Ayush ta murzawa motar key, yayinda me gadi ya wangale musu gate suka fice daga cikin gidan. Kaitsaye wani babban saloon lounge suka nufa, wanda kuma wajene da bakowa ke zuwansa ba. Koda suka ƙarasa cikin babban lounge ɗin amutumce aka tarbesu. Ɗaya daga cikin manyan ma aikatan wajen Oum Ayush ta samu, tare dayi mata bayani akan irin gyaran da takeso ayiwa Laylerh'n, saboda daga gobene za'a fara gudanar da events ɗin bikinta, yayinda wasu event ɗin kuwa sai bayan an ɗaura auren ne za'ayi su. Cikin girnamawa matar tace za ayi duk yanda oum Ayush din keso, za kuma suyiwa Layler'n gyara yanda ya kamata. Ganin yanda Oum Ayush ɗin ta zuba musu kuɗi sosai ne yasa nan take matar ta shiga gyara Laylerh. Ita dai Laylerh kallonsu kawai take, yayinda aranta take mamakin gyaran da ake mata, wanda kuma tasan anayi mata hakanne dan zatayi aure, auren da har yanzu bataji ajikinta cewar Eh dagaske za'a ɗaura shi ko a'a ba. *(Shin wa kuke tunanin cewa Laylerh zata aura acikin mazaje biyun nan? MALEEK ko NAJEEB? nasan dukan ku kun matsu dajin hakan, to koma dae wanene zai bayyana gobe a next page wajen ɗaurin aure. Lallai duk wanda yafi ƙuri'a kuma wanda yafi sa'a shi zaiyi wuf da ita😅 yaseen nagaji da typing hannuna zogi anan zan tsaya.🏃🏻‍♀ď¸?)* 1/19/21, 8:14 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna *(This book is mainly for those that pay, if you know you did'nt pay please don't read it. Here is the account number for people that are willing to pay-0002214625 Abubakar Muhammed Sardauna Jaiz bank. Whatsapp number 07017879464. )* *(Hey guys wannan page ɗin na haɗa muku dana yau da kuma na gobe ne, so ku karanta rabi yau, sai gobe ku ƙarasa sauran😂, nidae na faɗa muku kada wata tace ban faɗa ba tam😆.)* *Chapter 24* Kusan awa ɗaya aka kwashe anayi mata gyaran gashin, wanda hakan yasa cikin ɗan ƙanƙanin lokaci gashin nata yayi kyau, tare kuma da ƙara tsawo, yanayin yanda aka gyara kannata ne kuma yasa shining face ɗinta ƙara fitowa. Kasancewar idan suka sake mata dogon gashin nata zai na taɓo tsakian bayanta ne, yasa koda suka kammala gyaran suka ɗaure mata gashin atsakiar kanta, tare da fesa mata wani turaren gashi me matuƙar ƙamshi. Oum Ayush kuwa dake zaune ganin yanda gashin Laylerh'n yayi kyau sosae ne, yasa ta ƙara musu kuɗi. Sosae kuwa ma'aikatan shagon sukayi mata godia kafun suka baro saloon lounge ɗin. Daga shagon saloon ɗin kuwa kaitsaye wani babban lounge na tailoring fashions styles suka nufa, aƙofar katafaren lounge ɗin Oum Ayush tayi parking motar tare da ɗagowa ta kai dubanta ga Laylerh wacce gaba ɗaya hankalinta ke ga motocin dake ta faman zirga zirga akan titi. Cikin nutsuwa Oum Ayush ɗin tace "Sarkin kalle kalle, fito muje ko." Jin abun da Oum Ayush ɗin tace ne, yasa ta yin murmushi tare da buɗe murfin motar ta fito. Atare suka ƙarasa cikin babban lounge din wanda ke cike da tailors kala kala. Ganinsu ne yasa Ogan shagon da kansa ya tarbesu cikin girmamawa, dan kamar yanda aka tarbesu a shagon saloon ɗin cikin mutum tawa haka ma aka karɓesu anan shagon ɗinkin, bayan sun gaisane kuma aka shiga jido kayayyakin da Oum Ayush ɗin ta bada ɗinki, saboda tun kafun zuwansu Oum Ayush ta yiwa shugaban lounge ɗin waya, wannan yasa tun kafun ƙarasowansu kayan nasu ya zama ready. Ganin kuma kamar suna sauri ne yasa shugaban lounge ɗin da kansa yasa aka kai musu kayan mota, godiya Oum Ayush ta mishi sannan suka baro lounge ɗin. daga tailoring lounge ɗin direct gida suka nufo, yayinda tun ahanya gaba ɗaya bacci ya cika idanun Laylerh. Koda suka dawo gidan kuwa anan part ɗin Oum Ayush ta zauna, kasancewar tafi jin dadin zama anan din fiye da ko ina. Anan kan sofa ta zauna tare da ɗan jingina bayanta da jikin kujera, ahankali ta lumshe idanunta wanda suke cike da bacci, cikin abun da baiwuce mintuna goma ba kuwa baccin ya soma ƙoƙarin fusgarta, saidai kuma zuwan Oum Ayush da bowl ɗin dulka yasa dole ta buɗe idanunta. Duk da kasancewar ta gaji sosai, saidai bazata iya musawa Oum Ayush dinba, haka ta zauna Oum Ayush ɗin ta gurje mata gaba ɗaya jikinta da dulka, saboda yanda tasha gurza kuwa har saida farar fatarta tayi ja. Sama da awa ɗaya kwaɓaɓɓen dulkan ya ɗauka ajikinta, kafun daga bisani Oum Ayush ta sata taje tayi wanka, bayan tafito daga wankan ne kuma Oum Ayush ta sake bata wasu haɗaɗɗun magunguna, hannunta na rawa kuwa ta karɓi kofin maganin tare da kaiwa bakinta, saboda atunaninta maganin zai zamo me zaƙi kamar irin wanda aka bata afarko, saidai kuma ɗaura harshenta akan maganin da tayi ne, yasa tayi narai narai da ido, tare da taɓe bakinta, saboda haka taji ɗanɗanon maganin kwata kwata ba daɗi. Ƙoƙarin furzar da maganin ta somayi, saidai ganin yanda Oum Ayush ke kallonta ne, yasa bisa dole ta shanye maganin badan taso ba. Tana aje kofin maganin kuwa Oum Ayush ta sake turarata da wani turare me kamshin gaske, ita dai Laylerh sakin jiki kawae tayi, dan gaba ɗaya ta gaji da shafe shafe da kuma murje murjen da Oum Ayush ɗin ke mata. Ahaka dai suka ƙare gaba ɗaya wunin na yau, yayinda Oum Ayush ta zage wajen gyara Laylerh'n sosai, wannan yasa acikin wuni ɗaya kacal taushin jiki da kuma ƙamshi suka matuƙar kama jikinta, koda dare yayi kuwa bayan ta idar da sallan Isha wani shafe shafen Oum Ayush ta sake yi mata, tare da bata wasu kalan magunguna na daban tasha, kasancewar agajiye take sosai ne yasa kafun ƙarfe 9 bacci ya ɗauketa, inda kuma anan sashin Oum Ayush ɗin ta kwana. Dream!. Lokaci ɗaya ya soma ƙoƙarin janye jikinsa daga nata, yayinda ahankali yake ɗan yin nesa da ita, tare da soma ƙoƙarin sakin hannunta dake cikin nasa. Wani irin fitinannen yanayin da take gani acikin idanunsa ne, ya sata soma girgiza kainta, wanda hakan yasa hawayen da suka cika idanunta suka samu daman gangarowa kan fuskarta, lokaci ɗaya kuma wani irin matsanancin kuka ya ƙwace mata, tabbas so take ta rungumesa ko zataji sanyi aranta, saidai yaƙi bata daman hakan, ganin cewar dagaske sakin hannunta dake cikin nasa zaiyi, yasa ta tsananta kukanta, kana cikin wata irin muryarta da bata fita da kyau tace. "Kada ka sake hannuna Yah Maleek, dan Allah Kada kayi nesa dani! katsaya atare dani pleaseee...!!!" Ta ƙare maganar cikin matsanancin kukan daya riga yaci ƙarfinta.. Sosae kukanta ke taɓa masa zucia, saidai kuma abun dayakeji aƙirjinsa ya wuce duk wani gaban kwantance. Kansa ya shiga girgizawa haɗe dayi mata nuni da daidai saitin zuciyarsa, kana ahankali ya zare hannunsa dake cikin nata, tare da juya mata baya. Ganin ya juya mata baya ne yasa cikin matsanancin kuka tatafi da gudu dan ta faɗa jikinsa, saidai kuma kafun ƙiftawar ido tuni ya ɓacewa ganinta, hakanne yasa ta sulale ƙasa tare da fashewa da wani irin kuka, cikin karyayyar muryarta ta ƙwala ƙiran sunansa da ƙarfi. Yanayin yanda taƙira sunansa da babban murya ne, yasa sautin muryar ta ta bayyana afili. Jin amo da kuma sautin muryar nata ne yasa ta dawowa daga cikin duniyar mafarkin da ta faɗa. Ahankali ta soma buɗe idanunta wanda suka ɗan ƙanƙance saboda bacci. Wani irin juyawa taji kanta nayi, yayinda zuciyarta ke bugawa da sauri. Jin sautin surutun mutane acikin gidanne yasa ta ɗanyi shiru, domin tana son tabbatar da abun da kunnuwan nata ke jiye mata. Jin da tayi cewar da gaske hayaniyan mutane ne ke tashi acikin gidan, bawai ƙarya kunnuwanta ke mata ba, yasa ahankali ta tashi zaune, tare da jingina bayanta da saman gadon da take kai. Mafarkin da tayi akan Maleek ɗinne ya shiga dawowa cikin brain ɗinta filla filla, take kuwa taji ƙirjinta yayi mata nauyi, yayinda wani abu me kama da faɗuwar gaba ya shiga ziyartar duk wani kafar sadarwa na jikinta. Yanayin yanda taji zuciyarta na bugawa ne yasa ta maeda idanunta ta lumshe. Dai-dai lokacin kuwa Oum ayush ta turo ƙofar ɗakin ta shigo. Ganin Laylerhn azaune ne yasa ta sauƙe ajiar zucia haɗe da cewa. "Tun da kin tashi sai ki hanzarta yin wanka, dan masu lallen dana ƙira, sunzo tuntuni ke kawae suke jira." Jin an ambaci masu lalle ne yasa ta kalli Oum Ayush ɗin, cikin sassanyar muryar tace. "Oum Ayush masu lalle kuma?." "Eh mana masu lalle, ko kin taɓa ganin inda aka bar amarya haka ba lalle ajikinta?." Oum Ayush tafaɗa tana me nufar ƙofar bathroom dan so take ta haɗawa Laylerh'n ruwan wanka. "Amarya.!" Ta maimaita kalmar da Oum Ayush ɗin tafaɗa, dan hakanan taji kalmar abakinta kamar sabuwar kalma, ganin bata da lokacin tunani ne yasa ta sanya hannayenta ta mutsutstsuke idanunta, da suke gane mata dishi dishi, ahankali kuma ta zuro da kyawawan ƙafafunta ƙasa daga kan gadon. Daidai nan Oum Ayush ta fito daga cikin toilet ɗin, towel ɗin dake hannunta ta miƙawa Laylerh'n, tare da ce mata ta karɓa tasa. Babu musu kuwa ta karɓi towel ɗin ta ɗaura ajikinta. Ganin haka ne yasa Oum Ayush fita daga ɗakin, kana kuma cikin minti biyu ta dawo hannunta ɗauke da wani cup wanda cikinsa ke ɗauke da madarar shanu. "Kitabbatar kin shanyesa tas kafun kishiga wankan." Oum Ayush ta faɗa tana me miƙawa Laylerh'n kofin madarar. Ganin madara ne acikin kofin yasa ta karɓa, tare da kafa kanta ta shanyesa nan take ta ajiye cup din. Juyawa Oum Ayush din tayi ta fita, wanda hakanne kuma ya bata daman shigewa toilet ɗin kaitsaye. Yau ma kamar jia ruwan wankan da Oum Ayush ɗin ta haɗa mata acikin bathtube din wankan, sai tashin daddaɗan ƙamshi yake, cikin marari ta shiga cikin ruwan ta kwanta, tare da lumshe idanunta. Tunawa da mafarkin nata na yau da tayi ne yasa taji gaba ɗaya jikinta yayi sanyi, take kuma taji zuciyarta ta karye, duk da cewa bata da yaƙini akan mafarki, amma tanaji ajikinta cewa lallai wani abu zai shigo cikin rayuwarta, wanda zai mata shamaki da duk wani muradin zuciyarta, tabbas taji ajikinta cewa wata sabuwar ƙaddara na neman kutso kai cikin rayuwarta, wanda kuma hakan daidai yake da salwantar farincikin ta. Cikin rashi kuzari da kuma ƙarfin jiki tayi wankan. koda ta fito daga cikin toilet ɗin, zaune ta taradda Oum ayush akan gado, gefenta kuwa Aunty Zee ce, wanda takasance ƙanwa ga Oum Ayush ɗin. Ganin Aunty Zee ɗinne yasa ta ɗan doka tsalle, cikin sauri ta ƙaraso ta faɗa jikin Aunty Zee ɗin, cikin farinciki tace. "Oyoyo Aunty Zee." Murmushi matashiyar matar da aƙalla bazata haura 31 years ba tayi, tare da shafa kan Laylerh'n cikin kulawa tace. "Oyoyo Laylerh amarya." Jin Aunty Zee ɗin ta ƙirata da amarya ne yasa ta ɗan turo ƙaramin bakinta gaba ashagwaɓe tace. "Nifa ba amarya bace." Dariya Oum Ayush da kuma Aunty Zee din sukayi, saboda dukansu sunsan cewa akwai ƙurucia acikin sha'anin Laylerh'n. Wasu ɗinkin riga da sket na atamfa, wanda yana ɗaya daga cikin kayan da suka karɓo jiya awajen tailor Oum Ayush ta bata tace ta saka. Koda ta sa kayan kuwa sosai ɗinkin ya amshi jikinta yayinda hips ɗinta suka bayyana kaman zasu fasa sket ɗin, kasancewar kuma Oum Ayush ta turawa telan da yayi ɗinkin hoton Laylerh'n ne yasa shi yi mata ɗinkin daidai da jikinta, wanda kuma tasaya kayayyakin ne a Dubai musamman saboda Laylerh'n tasa alokacin bikin ta, saboda tafi kowa sanin irin ƙiyyayar da Momy ke nunawa Laylerh'n, wannan yasa lokacin da Aunty Zee takai musu ziyara ta bata wasu daga cikin kayan tace takawo nan Nigeria aɗinka. Kasancewar Aunty Zee ƙwararriyar me meckup ne yasa ta zaunar da Laylerh'n tayi mata light meckup akan fuskarta. Masha Allah kuwa sosai fuskar Laylerh'n tayi raɗau da ita, yayinda wani fitinannen kyau ya bayyana akan fuskar Laylerh'n, take kuwa ta fito a siffanta na amarya. Oum Ayush da kanta ta kama hannunta zuwa falo, wanda yake cike da jama'ar Oum Ayush, dan acewarta auren gata za'ayi Laylerh'n saboda hakane ma ta gayyato ƙawayenta da kuma danginta na kusa dan tundaga yau takeson bikin ya soma, inda yau za'ayi sakun lalle, gobe kuma shine za'ayi walima, sannan kuma zasuyi mothers night da dare, yayinda jibi insha Allah Za'a shafa Fatiha. Ganin taron jama'a acikin falonne yasa Laylerh taji duk ta takura,yayinda gaba ɗaya jikinta yayi sanyi, saboda ayanzu ne ta sake tabbatarwa da kanta cewar lallai Aurenta da Najeeb ba fashi. Kilisa aka mata na musamman ta zauna, take wacce zatayi mata zanen Lallen ta fara aikinta. Haka ma dae yauɗin Kusan wuni sukayi suna abu ɗaya, yayinda akayiwa Laylerh'n zanen jan lalle me matuƙar kyau, kasancewar kuma tana da hasken fata ne yasa zanen lallen fitowa raɗau ajikinta, yayi mata kyau. 6:00 pm daidai ta wanke lallen tare da yin wanka tayi sallah, tana nan zaune akan sallayan har aka kira sallan isha, bayan ta idar da sallan ne ta haye saman gadon Oum Ayush, saboda yanda taji lokaci ɗaya zazzaɓi na ƙoƙarin sauƙar mata, da kwanciyan nata kuwa ko minti 20 ba tayi ba bacci ɓarawo ya ɗauketa. Washegari. Da wani irin zazzafan zazzaɓi ta farka wanda har yakai ga da ƙyar ma take iya mota gaɓɓan jikinta. Ganin yanda jikin nata yayi tsanani sosae ne yasa Hankalin Oum Ayush ya tashi, take tayiwa Abbou Jaheed waya ta sanar dashi cewar Laylerh'n bata da lafiya, hankalin Abbou Jaheed atashe ya ƙira family Doctor ɗinsu. Cikin abun da baiwuce 30 minute ba kuwa Dr. din yazo. Zuwa lokacin kuwa zafin jikin Laylerh'n ya ƙara tsananta, allurai biyu dr ɗin ya mata, tare da bata magani, duk da kuwa cewar tanajin ciwon ajikinta bata sha maganin ba saida Oum Ayush ta lallaɓata sannan tasha maganin, kasancewar kwata kwata batason magani. Kasancewar alluran da dr. Ɗin ya mata nada ƙarfi sosae ne yasa take bacci ya ɗauketa. Ganin kuwa ta samu bacci ne yasa Oum Ayush komawa cikin jama'arta suka ci gaba da hidimominsu. Ƙarfe uku daedae ta farka daga baccin nata sakamakon hayaniyan daya cika gidan. Ahankali ta buɗe idanunta da sukayi mata nauyi, jin motsi da kuma ƙaran danna waya agefenta ne yasa ta ɗan juyo da kanta. Ganin Teemah zaune agefen gadon ne yasa ta ɗan waro idanunta, cikin yanayin mamaki haɗi da muryarta da bata fita da kyau ta ƙira sunan Teemah. Jin muryar ta ne yasa Teemah dake danna wayarta ta ɗago da sauri, ganin Laylerh'n ta buɗe idanunta ne yasa cikin sauri ta hawo saman gadon tare da kamo hannun Laylerh'n ta riƙe, cikin kulawa tace. "Sannu Amarya ya jikin naki, nayi mamaki sosai da Oum Ayush ta tura driver har gida ya ɗauko ni, ashe kin fara jinyan amarcin ne tun yanzu, tun kan akashe boss!." Yanayin yanda ta ƙare maganar cikin tsokana ne yasa Laylerh da taɗan yunƙura ta tashi, ta watsawa Teemah'n harara. Dariya Teemah tayi tare da matsawa kusa da Laylerh'n, cikin yin ƙasa da murya tace. "Gaskia Angon nan naki zai kwashi garaɓasa, ji yanda kike ƙamshi kaman anmiki wanka da turare, bayan haka kuma kalli yanda skin ɗinke keta sheƙi like diamond, awwn sunan wani abu wae so sweet!." Teemah tafaɗi haka tana me ɗan rungume Laylerh'n. Ayanayin yanda takejin kanta yasa bata tunanin biyewa shirmen Teemah'n, dan har yanzu bawae zazzaɓin ya gama sauƙa ajikinta bane. Shigowar Oum Ayush cikin ɗakinne yasa Teemah ta saki Laylerh'n, cikin salon tsokana tace. "Yauwa Oum Ayush amaryar tamu ta farka." Murmushi kawae Oum Ayush tayi, kasancewar tasan halin Teemah'n da tsokana. Ruwan wanka Oum Ayush ɗin ta haɗawa Laylerh, tare da zuwa ta kamo hannunta, da kanta ta kaita har cikin toilet, ganin jikin Laylerh'n babu ƙarfi sosae ne yasa Oum Ayush din da kanta tayi mata wanka, bayan ta fito daga wankanne kuma aka turare mata jikinta da turaren wuta me dadin ƙamshi. Aunty Zee ne ta shiryata cikin wani haɗaɗɗen yadi me kalan blue da kuma golding, wanda aka masa ɗinkin riga da sket, sosai kayan suka amshi jikinta sannan suka bayyana hasken fatarta, meckup me kyau Aunty Zee ɗin ta mata, saidai sanin cewa laylerh'n bata da ishashshen lapia ne yasa bata tsawaita meckup ɗin ba. Dogon gashinta Aunty Zee ɗin ta kama inda ta nannaɗe mata shi da wani blue ɗin ribbom, da babban ɗan kwalin kayan tayi mata ɗaurin turban. Haɗaɗɗen sarƙan gwal da kuma awarwaro Aunty zee ɗin tasa mata, wanda hakan ya ƙara ƙawata adon nata, wani golding colour laffaya me tsananin kyau da tsada Aunty Zee din ta naɗa mata, tare da bata wasu haɗaɗɗun takalma masu kalan golding ta saka aƙafafunta, bakaɗan ba Laylerh'n tayi kyau, duk dama yanayin rama ya bayyana akan fuskarta saidai hakan baihana kyawunta bayyana ba. Ganin yanda Laylerh'n tayi kyaune yasa Teemah ta shiga yi mata pics masu kyau. Kasancewar tuntuni jama'a sun hallara a hall ɗin da za'ayi waliman ne yasa Aunty Zee kamo hannun Laylerh'n dake ta faman baza ƙamshi suka fice daga cikin ɗakin, yayinda Teemah ke biye dasu abaya saiyi wa Laylerh'n vedio take, duk da kasancewar yanayin yanda aka ɗan sa mata laffaya ya rufe rabin fuskarta. Koda suka fito compound ɗin gidan, cikin wata haɗaɗɗiyar Range Rover Aunty Zee ta saka Laylerh'n tare da zama akusa da ita, Teemah kuwa gaban motar ta shiga, kasancewar dama tuntuni su drivern ke jira, suna shiga kuwa yaja motar suka bar compound ɗin gidan. 4:30 pm daidai suka isa katafaren hall din da aka ƙawatasa da decoration, yayinda tuni mutanen da Oum Ayush da kuma wanda momy ta gayyata sun cika wajen. Zuwan su Laylerh'n ne yasa malamar da aka gayyato ta fara wa'azi akan yanda mace zatayi rayuwa me kyau da tsabta acikin gidan aurenta. Babu laifi kuma sosai Malamar tayi wa'azi me ratsa zuciya. Ƙarfe 6 daidai aka tashi daga walimar, nan fa aka soma ciye ciye, bayan kuma anci ansha ne Oum Ayush ta raba kyaututtuka na burgewa ga duk wacce ta halarci waliman. Ɓangaren Laylerh kuwa gaba ɗaya ta kasa sake jikinta, kasancewar bata saba da yawan shiga jama'a ba, hakanne kuma yasa hayaniyar mutanen ya ƙara mata ciwon kai, wannan yasa jikinta ya sake ɗaukan zafi. 7 daidai suka dawo gida, kasancewar akwai gajiya da kuma ciwo ajikinta ne yasa tana idar da sallan isha ta kwanta anan kan sallayan bacci ya ɗauketa. Shigowar Oum Ayush cikin ɗakinne ta sauƙe idanunta akan Laylerh'n dake kwance akan sallaya. Ajiyar zuciya Oum Ayush ɗin ta sauƙe tare da kafe Laylerh'n da idanu, wani irin matsanancin tausayin Laylerh'n ne ya cika mata zuciya, wanda hakan yasa take taji idanunta sun ciko da ƙwalla, cikin dauriya ta shanye ƙwallan dake idanun nata, ahankali ta ƙaraso inda Laylerh'n ke kwance, ɗan durkusawa tayi tare da shafa kan Laylerh'n, cikin sanyi da kuma matsanancin tausayin Laylerh'n tace. "Nasan matsalan dake damun zuciarki Laylerh, kuma insha Allah Idan da rai da rabo watarana zaki rayu da Maleek, zaki zauna a ƙarƙashin inuwarsa zama na har abada, saboda ku ɗin fata da buri ne haɗe awaje ɗaya, insha Allah zaku kasance atare da juna." Hannu tasa ta share ɗan guntun hawayen daya sauƙa akan fuskarta, tare da ɗaga Laylerh'n caɗak ta kwantar da ita akan gado, jin jikin nata da zafi sosai ne yasa Oum Ayush ɗin ta rufa mata blanket, tare da rage mata gudun A/C kaitsaye ta fice daga cikin ɗakin. Washegari. Tabbas Rana bata ƙarya, duk kuma abun da Allah Ya tsara faruwarsa sae ya faru, kamar yanda ranar yau ɗin ta kasance asabar kuma acikinta ne za'a ɗaura auren Laylerh'n. Kallon Agogon dake saƙale ajikin bangon ɗakin Fou'ad yayi, wanda ya nuna masa ƙarfe 9:30 am daidai. Ajiyar zuciya ya sauƙe, kana akaro na bartakai yakai dubansa ga Maleek wanda ke zaune akan kujera, yayinda idanunsa ke alumshe. Gefe dashi kuwa wani haɗaɗɗen yadin getzner ne wanda akayiwa ɗinkin riga da wando da kuma babban gare. "Maleek.!" Fou'ad ya ƙira sunansa cikin yanayin dake bayyana zallar damuwar dake kwance acikin zuciyarsa. Samun kansa yayi da kasa amsawa Fou'ad ɗin duk da cewar kuwa yaji ƙiran da yayi masa. Yanayin yanda yakejin zuciyarsa na harbawa akai akai ne ya sashi sanya hannu ya dafe daidai saitin zuciyar tasa, wanda yakejin tanayi masa ƙuna da kuna suka, yayinda yakejin wani abu me tsananin ɗaci na game maƙoshinsa. Kwana uku kenan daya kasa rumtsa idanunsa da sunan bacci, sanadin hakan kuwa yasa gaba ɗaya yafita hayyacinsa, yayinda kallo ɗaya zaka masa ka karanto zallan damuwa kwance akan fuskarsa. Tabbas atsakanin jiya da yau shi kaɗae yasan me yakeji azuciyarsa, domin kuwa zafi da raɗaɗin dayake bazai taɓa misaltuwa ba, dukkuwa ga yanda yaso daurewa sai yaji abun na neman fin ƙarfinsa, wannan yasa ya barwa kansa komai domin zuwa yanzu zuciarsa ma bazata iya ɗaukar ƙunan da yakeji ba, ada yayi tunanin cewa har abada bazai taba bari rauninsa ya bayyana ba, saidai ayanzu ya riga daya fahimci cewa, RAUNINsa bame ɓuya bane, saboda duk wani sirrin zuciyarsa yanzu rubuce yake akan fuskarsa. Fou'ad daya tsura masa ido ganin bae amsa ƙiran da yayi masa din bane yasashi miƙewa tsaye tare da ƙarasowa inda Maleek ɗin ke zaune. Tabbas ya fahimci irin yanda Maleek ɗin keji azuciyarsa, saboda gaba ɗaya fuskarsa ta bayyana matsanancin Rauninsa, haƙiƙa koda yaushe azuciyarsa yake ɓoye duk wani sirrinsa, saidai kuma ayau zuciyar tasa takasa juran cigaba da ɓoye abun dake cikinta. Tabbas wannan shine karo na farko da Fou'ad ɗin ya fara ganin Maleek ɗin acikin irin wannan halin, ahankali ya sanya hannunsa ya dafa kafaɗan Maleek ɗin cikin son ƙarfafa masa guiwa yace. "Shiru da zurfin ciki basa taɓa kawar da damuwa M.Jay, tabbas na fahimci irin yanda kakeji azuciyarka, saidai kuma kasani ako da yaushe muna tafiya ne da Ƙaddaran mu, ƙaddaran mu da bamu da ikon sanjata daga mummuna izuwa kyakkyawa, sau dayawa ba komae da kake so kake samu ba, haka kuma ba kowani buri ne ke cika ba, sau da dama mukan rasa hope ɗinmu, kuma amma hakan baya nufin cewa har abada zamu ta rasa hope ɗin mu bane, lallai watarana burin mu zai cika, saboda idan mun rasa anan zamu samu acan, Allah Shi yake duk wani tsarinsa babu kuma wanda ya isa ya wargaza, saboda haka ka sawa zuciarka jarumta, dan Allah Na roƙeka akaro na uku katashi kasa kaya mutafi wajen ɗaurin auren nan, kada fa kamanta Laylerh ƙanwar kace, kuma ako da yaushe burinka shine rayuwarta tayi kyau, meyasa bazaka kwaɗaitawa kanka halartar ɗaurin aurenta ba? ka tuna koba komai itaɗin ƙanwace agareka, kuma ita ɗin wani ɓangare ne na zuciyarka, saboda idan akace ayau Abbou Jaheed ya kwanta dama kaine komae nata, sannan kayi tunanin rashin zuwanka wajen ɗaurin auren nata me zai haifar? baza'a fasa abun da Allah Ya tsara ba, haka kuma Abbou Jaheed bazaiji daɗin bakan ba, idan ya tambayeka dalili wace amsa zaka bashi?, nasan baka da ita, saboda haka ka manta baya Maleek ka fuskanci gaba please!." Idanunsa wanda suka kaɗa sukai jajur ya buɗe tare da tsaida kallonsa akan Fou'ad ɗin, tabbas kalaman fou'ad ɗin na ƙarshe sun tabbatar masa da cewar Fou'ad baisan zafi da rafaɗin da yakeji acikin zuciyarsa ba, domin da ace yasan koda kwatankwacin hakan bazai taɓa ce masa ya manta da baya ya fuskanci gaba ba, domin kuwa abune da har abada bazai taɓa yiyuwa ba, domin manta baya agareshi tamkar mantawa da rayuwarsa ne. Laɓɓan ɓakinsa ya cija tare da dunƙule hannunsa, haƙiƙa dama yasan babu wanda zai fahimci haƙiƙanin abun dake cikin zuciyarsa, babu wanda zai gane me yakeji acikin ransa, zafi, ƙuna, da kuma zogi da raɗaɗin da yakeji azuciarsa duk babu wanda zai fahimta. Ahankali ya miƙe tsaye tare da ɗaukan kayan da Fou'ad din ya ajiye masa agefensa, cikin yanayin sanyi ya nufi bedroom ɗin dake cikin falon. Duk da yanda yakejin wani irin jiri na ɗibansa, haka ya shirya kansa cikin riga da wandon getzner'n, tare da ɗaura gare akan rigar jikinsa, wata haɗaɗɗiyar hula me kalan blue ya saka akansa, kasancewar aikin dake jikin babbar rigar tasa blue ne, tunda yake wannan shine karo na farko daya fara saka manyan kaya, bakuma ƙaramin kyau suka masa ba, yayinda suka bayyana cikar kamalansa, duk da cewar yana ɗauke da damuwa amma hakan baisa murɗaɗɗiyar surar jikinsa sauyawa ba, kyau ajininsa yake wannan yasa ako wani condition ya samu kansa kyawunsa baya tawaya. Haɗaɗɗen black blue ɗin takalmi ƙiran company'n Italy ya sanya aƙafansa, tare da ɗaura agogon diamond ahannunsa. Ƙwarai yayi kyau sosai, dan da ace wata mace zata ɗaura idanunta akansa cikin shigar tasa, to babu yanda za'ayi ta ɗauke kanta. Sam baya buƙatar duba madubi wajen ganin kyawunsa, hakan yasa ahankali ya murɗa handle ɗin kofar ya fice. Fou'ad dake zaune ganin Maleek din ya fito ne yasashi sakin baki yana kallonsa, tabbas duk da cewar shi ma Namiji ne kuma kyakkyawa, yasan cewa Maleek ajin ƙarshe ne ahaɗuwa, dan yana da tabbacin cewa irin yanayin kyawun Maleek ɗin daban yake dana kowa. Sanin da yayi cewar idan ya tsaya yin wata magana, abune me sauƙi Maleek ɗin yace ya fasa zuwa ne yasashi gimtse bakinsa, haka suka jera atare suka fice daga cikin falon. Koda suka fito compound ɗin gidan motar Maleek ɗin ƙirar G waggon suka shiga, yanayin yanda yake jin jiri ne yasa shi miƙawa Fou'ad makullin motar saboda bayajin ayanda yake zai iyayin driving dan ko gani sosae bayayi. 9:55 am daidai suka iso ƙofar gidan su Maleek ɗin dake cike da tarin jama'a, manya manyan malamai, Ć´an kasuwa, da kuma Ć´an siyasa ne cike awajen. Yayinda Abbou Jaheed da kuma Abbou Kareem suka sha adonsu cikin shigar manyan kaya. Najeeb na hango atsakiyarsu wanda yayi matuƙar kyau cikin shigar milk colour getzner dake jikinsa, yasha ado sosai ta yanda kallo ɗaya zakayi masa ka fahimci cewa shine angon. Yanayin yanda mutane suka cika wajen ne yasa Fou'ad yayi parking motar daga nesa. Duk da cewar bayason yawan hayaniya haka ya buɗe murfin motar ya fito. Taku ɗaya zuwa biyu yayi yaji wani ƙaƙƙarfan jiri na neman kadashi, yayinda wani irin duhu ke ƙoƙarin mamaye ganinsa. Kasancewarsa soldier kuma Namiji me iya shanye duk wata wahala, hakan yasashi daurewa, ya ƙarasa cikin taron jama'an, yayinda Fou'ad ke binsa abaya. Wajen zaman da aka tanada musamman dan suɗin suka ƙarasa suka zauna. Ganinsa awajen ɗaurin aurenne Abbou da gaba ɗaya zuciarsa ke cike da fargaba ya saki murmushi, saboda sae ayanzu yaji sanyi aransa. Kamar yanda aka rubuta ajikin katin auren ƙarfe 10:00 am daedae dubban jama'a suka shaida ɗaurin auren. *LAYLERH MAHMOUD NAI'EB da kuma angonta NAJEEB AHMAD RUFA'E* akan sadaki naira dubu ɗari biyar (500k). Jin an ɗaura aurenne kuwa yasa me shela ɗaga muryarsa inda ya shiga nanatawa jama'a cewar lallai aurefa ya ɗauro, Laylerh ta zamo matar Najeeb. Ɗaura auren da akayi yayi daidai da bugawar zuciyarsa da ƙarfi, yayinda gaba ɗaya jijiyoyin jikinsa suka mimmiƙe, take wani irin matsanancin ciwon kae ya kawo masa ziyara, wanda hakan yasashi sanya hannu ya kama kansa haɗe kuma da miƙewa tsaye, duk jikinsa rawa yake, cikin dauriya haɗe da cijewa ya soma taka ƙafarsa, domin kwata kwata bayajin zai iya jurewa zaman wajen, taku ɗaya kacal yayi wani irin jiri haɗi da duhu me tsanani suka mamaye ganinsa take kuwa ya tafi luuu ya faɗi ƙasa awajen. *(Kuyi haƙuri two days ba editing bana gama typing da wuri shiasa.)* *Sunday 20/December/2020* 1/19/21, 8:14 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna *(This book is mainly for those that pay, if you know you did'nt pay please don't read it. Here is the account number for people that are willing to pay-0002214625 Abubakar Muhammed Sardauna Jaiz bank. Whatsapp number 07017879464. )* *Chapter twenty five* Ahankali take taka ƙafafunta dake matsanancin karkarwa, sanadin hakan ne kuma yasa suke neman gaza ɗaukar nauyinta. Yayinda kuma wani irin matsanancin ciwon kae da jiri me ƙarfi keneman rinjayarta. Haƙiƙa abun da takeji acikin azuciyarta yau din, ya wuce duk wani tunanin me tunani, kasancewar haka takejin zuciyar tata kaman zata fasa ƙirjinta ta fito waje. Yanzu kusan sama da 15 minute kenan da gama wankan ta, amma takasa fitowa daga cikin bathroom ɗin saboda yanda kanta ke bala'in sarawa, da kuma jirin dake neman kada'ita. Ƙarasowarta bakin ƙofar bathroom ɗinne, yasa ahankali ta ɗaura hannunta akan handle ɗin ƙofar, tare da buɗeta asanyaye ta fito. Wani ɗan ƙaramin towel ne ɗaure ajikinta, wanda tsawonsa ya tsaya a iyaka cinyarta, sannan kallo ɗaya zaka mata ka ga zallan raman da tayi, wanda ya bayyana kansa ɓaro ɓaro. Yayinda dagon gashin kanta dake jiƙe da ruwa ya kwanta lub akan baya da kuma wuyanta. Lumshe idanunta wanda ke cike da ƙwalla tayi, ahankali tasa hannu ta dafe daidai saitin zuciyarta dake bugawa da sauri sauri. Hawayen dake cikin idanunta ne suka gangaro kan fuskarta, haƙiƙa rana irin ta yau takasance ɗaya daga cikin ranakun da bazata taɓa mantawa dasu ba acikin rayuwarta, dan ayau tarasa duk wani fata da burinta, sannan farinciki da kuma nutsuwar zuciya, a yau duk wani tunaninta ya tsaya cak, haka takejin zuciarta na mata wani irin matsanancin ciwo, tabbas ayau ta yarda cewa samun abun da kakeso aduniar nan yafi komae daɗi, haka kuma rasashi yafi komai ciwo, kana kuma samun abun da kakeso abune me matuƙar wuya, tabbas ayau ta sake yardarwa kanta cewar tana matsanancin SON SA, sannan taji ajikinta cewar lallai tarasa Yaya, farinciki kuma jigonta, hakan yasa takejin wani irin suka da kuma raɗaɗi me zafi acikin zuciyarta, haƙiƙa bazata iya jure rashinsa da kuma yanayin da take ciki ba, domin zuciyarta bata da wannan ƙarfin. Turo ƙofar ɗakin da akayi ne yasa ahankali ta buɗe idanunta. Teemah da shigowarta ɗakin kenan ganin hawaye kwance akan fuskar Laylerh'n ne yasa ta ɗan zaro idanunta waje, cikin yanayin mamaki tace. "Kuka kuma Laylerh? meke damunki?." Ayanayin da take ciki yasa batajin zata iya amsawa Teemah'n, tabbas so take tayi kuka sosae ko hakan zaisa taji sauƙin abun dake sukar zuciyarta, so take tayi kukan da shi kaɗai ne zai iya rarrashinta. Ahankali ta soma ƙoƙarin sulalewa ƙasa tare da sakin wani irin kuka me tsananin taɓa zuciya. Ganin haka yasa Teemah tayi saurin ƙarasowa gareta, tare da sa hannayenta ta ɗago Laylerh'n. Jin Teemah'n akusa da ita ne yasa ta faɗa jikinta tare da rungumeta ƙam, kuka take sosai irin kukan nan dake bayyana zallar damuwar dake zuciyar me yinsa, yanayin yanda take kukan ne yasa tsoro da kuma fargaba suka shiga zuciar Teemah, domin kuwa a iyaka saninta da Laylerh bata taɓa ganinta tana irin wannan kukan ba, ga kuma yanda lokaci ɗaya duk jikinta ya ɗauki ɓari. Cikin sanyin jiki ta rungume Laylerh'n, kana cikin karyayyar muryarta tace. "Please Laylerh ki daina kuka, ki faɗamin meyake damunki, ko zazzaɓin ne ya saki kuka haka? dan Allah Kifaɗamin saboda kinsa gaba ɗaya zuciyata ta karye, stop crying please......"  Yanayin yanda Teemah taƙare maganar cikin sanyin murya da kuma karyewar zuciya ne yasa idanunta cikowa da ƙwalla, kwarai tausayin ƙawarta ta ya kamata. Laylerh kuwa yanayin yanda take rusa kuka sosai ne, yasa numfashinta soma sarƙewa, hakanne kuma yasa lokaci ɗaya jikinta ya saki, take kuwa  numfashinta ya ɗauke, wanda hakan yasa ta sulale daga jikin Teemah ta faɗi ƙasa. Ganin da Teemah tayi Laylerh'n ta zube aƙasa bata numfashi ne yasa ta fasa wani irin ƙara, amatuƙar razane ta juya da gudu ta fita daga cikin ɗakin dan ƙiran Oum Ayush, akan tazo taga halin da Laylerh'n ke ciki. Cikin yanayin damuwa haɗi da zallar rashin hankali Fou'ad dama sauran jama'an dake cike awajen sukayi kansa, durƙusawa agabansa Fou'ad yayi tare da kamo kafaɗunsa ya soma jijjigawa, amatuƙar ruɗe kuma cikin tsoro haɗi da zallar fargaban daya rufesa ya soma ƙiran sunansa. Cikin sauri da tashin hankali su Abbou Jaheed suka ƙaraso wajen da Maleek ɗin ke yashe. Durƙusawa Abbou Jaheed yayi, hankalinsa amatuƙar tashe ya soma ƙiran sunan Maleek ɗin, tare da girgiza shi. Ko motsi Maleek ɗin baiyi ba, kasancewar tuni ya jima da fita a hayyacinsa, yayinda gaba ɗaya numfashinsa ya bar gangar jikinsa. Fou'ad da idanunsa suka ciko da ƙwalla ne yasa hannunsa adaidai hancin Maleek ɗin, shirun da yaji ba alamar fitar numfashi ne yasashi zaro idanunsa waje, da sauri yakai hannunsa ya dafa ƙirjin Maleek ɗin daidai saitin zuciyarsa. Jin zuciyar Maleek ɗin na harbawa kaɗan kaɗan ne yasashi sauƙe wata nannuyar ajiyar zuciya, cikin sanyin da jikinsa yayi ya ɗago kae, ya kalli Abbou Jaheed wanda yake cikin tashin hankali, cikin muryarsa dake ɗan rawa yace. "Taɓa zuciyarsa kaji Abbou bata beating da kyau, komae nata yana zama low, please Abbou aƙira doctor kada mu rasa shi.!" Abbou Jaheed da gaba ɗaya ya ruɗe kasa koda motsa jikinsa yayi, domin idan yace zai nemo wayartasa ma baisan ta inda zai fara ba. Abbou Kareem ne yayi saurin ciro wayarsa, cikin tashin hankali ya dannawa abokinsa Dr.Hafeez ƙira, bugu uku kuwa Dr.Hafeez ɗin ya ɗaga. Cike da tashin hankali Abbou Kareem ya labartawa Dr.Hafeez ɗin abun dake faruwa. Yanayin yanda Dr.Hafeez yaji muryar Abbou Kareem ɗin aɗan ruɗe ne yasashi cewa gashinan zuwa. Ahankali Fou'ad yasoma ƙoƙarin ɗaga Maleek ɗin, saidai kuma yanayin yanda jikin Maleek din ke asake ne yasa Fou'ad ɗin kasa ɗaga sa shi kaɗai, ganin hakane yasa Najeeb wanda isowarsa wajen kenan cikin matsanancin damuwa ya sa hannu suka ɗaga Maleek ɗin. Direct cikin gida suka nufa dashi, saidai kasancewar farfajian gidan cike yake da mutane Ć´an biki dake ta hada hada, yasa suka bi ta ƙofar baya, wanda direct ya kaisu har zuwa  sashinsa. Kaitsaye bedroom ɗinsa suka wuce dashi, tare da kwantar dashi akan makeken gadonsa, wanda yaji bedsheet na alfarma. Su Abbou Jaheed da suka biyosu ne suka tsaya sukayi jigum jigum, kallo ɗaya zakayiwa fuskar Abbou Jaheed ka fahinci cewa yana cikin tashin hankali da kuma tsananin damuwa. Abbou Kareem daya cire hulan kansa ya soma fifita dashi ne ya ɗago kai ya kai dubansa ga Fou'ad wanda ke tsugune agaban gadon, cikin muryarsa data bayyana tsananin damuwarsa yace.     "Fou'ad meke damun Maleek ne, dama tun can bashi da lafiya har haka, amma ba wanda ya sani?." Fou'ad ko jin tambayar da Abbou Kareem ɗin yayi masa ne yasashi fesar da wani gauron numfashi, cikin yanayin damuwa yace.  "Bani da masania akan wannan rashin lapiyan nasa Abbou Kareem, hasalima lafiya ƙalau muka fito daga gida, bansan meyake faruwa dashi ba, aĆ´an kwanakin nan gaba ɗaya bana gane masa, domin yau kwana biyu kenan da muke tare dashi, amma ko abinci bayaci, abun dana lura dashi kawai shine baya cikin farinciki, lallai akwae abun dake damunsa."  Yafaɗi hakan yana me ƙoƙarin danne zuciyarsa, domin ahaƙiƙanin gaskia ingiza sa take akan yafaɗi haƙiƙanin abun dake damun Maleek ɗin, saidai kuma sanin da yayi cewar faɗan gaskiyar lamarin bazai haifar da komae ba ne yasashi rufe bakinsa, domin tuntuni aikin gama ya riga daya gama, bayyana sirrin zuciyar Maleek ɗin ba abun dazai haifar sai rugujewar mutumta ka, da kuma ɓata alaƙa, dan Allah Yariga dayayi tsarinsa. Jin abun da Fou'ad din ya faɗane yasasu yin shiru, tare da zubawa Maleek ɗin dake kwance idanu, wanda kuma sai alokacinne suka lura da yanda ya rame, amma kuma fatarsa ta ƙara haske sosae. Abbou Jaheed dake tsaye jin idanunsa sun ciko da ƙwalla ne yasashi lumshe su, tare da jingina bayansa da jikin bango, ahankali yake sauƙe ajiyar zuciya, yayinda aransa yake addu'a da fatan samun lafiyar ɗannasa, tabbas yasan idan wani abu ya samu Maleek to sakacinsa ne, kuma Allah Sae ya kamashi saboda hakan, dan shi kansa yasan baya bawa ɗannasa kulawa yanda ya kamata. Wayar Abbou Kareem da ta soma ƙara ne yasa kowannensu dawowa daga duniyar tunanin da suka faɗa. Ganin sunan Oum Ayush na yawo akan screen ɗin wayarne yasa Abbou Kareem ya ɗauki wayar cikin sauri. Jin abun da take faɗa ne yasashi rumtse idanunsa, lokaci ɗaya kuma ya buɗesu tare da kai dubansa ga Najeeb dake tsaye. Ajiyar zuciya ya sauƙe batare daya ce komae ba ya kashe wayan. Kallonsa ya mayar ga Abbou Jaheed dake tsaye. Ganin yanayin Abbou Kareem ɗin ya sauya ne yasa Abbou Jaheed yace. "Lafiya meke faruwa?." Ajiyar zuciya Abbou Kareem ɗin ya sauƙe, kana cikin sanyin muryar dake bayyana sabuwar damuwar da ya samu kansa aciki yace.  "Laylerh ce  ba lafiya, wai tafaɗi bata ko numfashi." Idanu dukansu suka zazzaro waje, cikin yanayin tashin hankali haɗi da damuwa.  Abbou Jaheed yace.  "Subahanallahi yanzu ina Laylerh'n take, sannan wani hali take ciki?." Abbou ya haɗewa Abbou Kareem duka tambayoyin awaje ɗaya. Ɗan jim Abbou Kareem yayi, kana cokin sanyi yace "Tana sashin Aysha, sannan akwae buƙatar likita ya dubata cikin gaggawa, wannan wani irin tashin hankaline haka? ace atake yara dukansu biyu basu da lafiya, sannan kowannensu baya cikin hayyacinsa, Ya Allah Kabamu ikon jurewa hukuncinka." cewar Abbou Kareem daya ƙare maganar yana me ɗaga hannayensa sama alaman roƙon Allah. Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da lumshe idanunsa wanda suka ɗanyi ja, haƙiƙa jin cewar Laylerh'n bata da lafiya ya sanyaya masa guiwa sosai, tunawa da cewar yau kwanansa huɗu kenan baisanyata a idanunsa ba, yasa yaji ya kwaɗaita dason ganinta, domin dama bai nisanta kansa daga gareta da wata manufa ba, kawai dai yanaso sai ta zamo mallakinsa ne, saboda ako yaushe yasa ta acikin idanunsa, ji yake kaman ya jawota ya rungumeta, dan sosai yake da feeling me ƙarfi akanta. Ahankali ya ware idanunsa tare da ɗan soma jan jikinsa baya, batare daya sani ba ya buge wani ɗan ƙaramin table dake bayansa, sanadin hakanne ko yasa wani abu me kaman box dake ɗaure asaman table ɗin an lulluɓesa da wani farin yadi me kyau ya faɗo ƙasa. "Oh My God!." Yafaɗa alokacin dayake juyawa dan ɗaga abun daya ture ɗin ba tare da saninsa ba. ɗaukan box ɗin wanda afaɗuwar da yayi yasa abun dake cikinsa suka zubo ƙasa, hannunsa yakai kan wani ɗan madaidaicin abun saka hoto wanda aƙa ƙawatasa da ado me kyau, ahankali ya ɗago abun tare da juyawa dan hakanan yaji kwaɗayin ganin hoton wanda aka saka acikin abun, sauƙe ganinsa akan hoton dake liƙe ajikin abunne yasashi ɗan zaro idanunsa, lokaci ɗaya kuma ya ƙurawa hoton idanu. Sanye take cikin wani riga da sket na atamfa me kalan blue, yayinda tasanya hannayenta biyu ta kama waist ɗinta, saidai kuma yanayin yanda idanunta ke kallon gefe ne yasa da ka gani zaka fahimci cewa unexpected pic ne aka mata batare ma da saninta ba. *"LAYLERH..!!"* yaƙira sunanta acikin zuciyarsa wanda take cike da mamakin yanda akayi hoton Laylerh'n yazo ga Maleek, har yayi masa irin wannan karramawar tahanyar sashi a glass me matuƙar tsada da kyau. "Me hakan yake nufi?." Zuciyarsa tayi masa tambayar da sam bashi da amsarta. Jin wani tunani na ƙoƙarin ɗarsuwa acikin ransa ne, ya sa yayi saurin girgiza kansa, cikin son watsar da duk wani tunani dake ransa yace.   "Ita Ć´ar uwarsa ce, saboda haka bai kamata na damu kaina dan naga hotonta aɗakinsa ba, sam ma babu ƙatar hakan." Da wannan tunanin yayi saurin tattare wajen, tare da gyarasa ya maidashi yanda yake. Turo ƙofar ɗakin da akayine yasa su maida hankalinsu wajen, ganin Dr.Hafeez ne yasa suka sauƙe ajiyar zuciya, Abbou Kareem ne yayi masa jagora harzuwa inda Maleek ɗin ke kwance. Wasu Ć´an gwaje gwaje Dr.Hafeez ɗin yayiwa Maleek, ganin abun na buƙatar nutsuwa sosai ne yasashi ɗago kai haɗi da cewa.   "Please ko zaku ɗan jira a falo, because hayaniyan ku zai iya ɗan disturbing ɗina wajen yi masa kyakkyawan checking." Jin abun daya faɗane yasa dukansu suka fita daga ɗakin, dan su dama burinsu shine suga ya buɗe koda idanunsa ne. Koda suka fito daga cikin ɗakin, Abbou Jaheed, da kuma Abbou Kareem ne suka nufi cikin gidan, dan dama sun matsu suje su duba jikin Laylerh'n, kasancewar tuni Abbou Jaheed ya tura Dr. Ishaq wato family doctor'nsu saƙo akan yazo ya duba jikin Laylerh'n. Alhaji Ahmad da Najeeb kuwa waje suka koma dan sallaman baƙin da suka tara, yayinda aka bar Fou'ad shi kaɗai zaune acikin falon Maleek ɗin. Oum Ayush ce zaune abakin gadon, saikuma Aunty Zee da Teemah wanda suke tsaye agefen Dr. Ishaq wanda yake ƙoƙarin daidaita tafiyar drip ɗin daya ɗaurawa Laylerh'n. Buɗe ƙofar ɗakin da akayine yasa duk suka juya, ganin su Abbou Jaheed yasa Oum Ayush sauƙe ajiyar zuciya. Ƙarasowa cikin ɗakin sukayi fuskarsu ɗauke da matsananciyar damuwa, hannu Abbou Jaheed ya sa ya ɗan taɓa goshin Laylerh'n wanda ya ɗau zafi zau kamar wuta, hakanan yaji wani irin matsanancin tausayin Laylerh'n ya kamashi, cikin karyewar zuciyar da ta sameshi ya dubi Dr.Ishaq, asanyaye yace. "Dr. meyake damun ta ne? dan naji jikinta ya ɗauki zafi sosai." Ajiyar zuciya Dr.Ishaq ya sauƙe, tare da duban Abbou Jaheed din ganin yanda gaba ɗaya hankalinsu ya tashi ne yasa shi ɗanyin guntun murmushi, cikin kulawa yace. "No karku damu bawani serious problem ba ne, kawae dai tana fama ne da matsanancin zazzaɓi, sai kuma yanayin damuwan da tasa aranta yasa jininta hawa, ƙwarai nayi mamaki danaga hakan, domin ƙaramar yarinya kamar Laylerh bana tunanin akwae wata damuwa da har zai iya sawa ta kamu da ciwon hawanjini, agaskiya Alhaji Jaheed ina tunanin ya kamata ace ku bincike ta, domin sanin damuwar dake damunta, dan akasin hakan, zaisa damuwar ta ta ƙara faɗaɗa, wanda kuma hakan zai iyasa ciwon nata yayi worst, idan kuwa haka tafaru gaskia za'a iya samun matsala, saboda ita yarinyace, sometimes ma batasan yanda zata kula da kanta ba." "Innalillahi Wa'inna Ilaihirraju'oun..!!" Gaba ɗaya suka haɗa baki wajen faɗan haka, saboda ko kusa basu taɓa kawo aransu cewar wai Laylerh zata iya kamuwa da cutar hawan jini ta sanadin damuwa ba, domin kuwa itaɗin yarinyace ƙarama, wanda suke ganin cewa babu wata damuwa da zai kawo naƙasu arayuwarta, musamman ma da ayanzu ne take ƙoƙarin cika 18 years, kuma ayanzu ne suke tsammatawa rayuwarta ƙarin jin daɗi, saboda auren da akayi mata. Ahankali Abbou Jaheed ya cire hulan dake kansa, tare da zama anan bakin gadon, tuni kuwa zufa ya keto masa, haƙiƙa yau rana ce ta farinciki agaresa, amma kuma gashi tana ƙoƙarin juyewa izuwa ranar riskar damuwarsa, sosai ya kaɗu dajin cewa wae Laylerh'nsa na ɗauke da hawan jini, wannan na nuna alamar cewa kenan bai riƙe amanar da ɗan'uwa da kuma mahaifiyarta suka bashi ba, saboda idan har damuwa zata iya sawa Laylerh ciwon hawan jini, to haƙiƙa hakan na nuna cewar ya gaza bata kulawarsa hundred percent. Shiru yayi tare dasa hannayensa ya rufe fuskarsa, lallai abun da yakejin tsoro tuntuni shine ke ƙoƙarin faruwa. Ahankali Abbou Kareem da jin maganar hawanjini'n Laylerh'n yasa shi a shock ya sauƙe ajiar zucia, cikin sanyin da guiwowinsa sukayi yace. "Yanzu Dr.Ishaq menene mafita? sannan kuma ya ake ciki da maganar farfaɗowanta?" "Tariga da ta farfaɗo tuntuni, kuma kamar yanda na faɗa muku matuƙar za'a kiyaye, akuma bata kyakkyawan kulawa, to hakan bazai zama wani abun damuwa ba, saboda yanzu nayi mata allurai, sannan kuma akwae magunguna da za'a sayo idan ta farka sai abata tasha, kada kuma ayi nesa da ita dan zata iya farkawa kowani lokaci, duk dama alluran dana mata suna da ƙarfi sosai, sannan idan ta farka ya kamata abata abinci taci kafun magani." Cike da gamsuwa da bayanansa Abbou Kareem ya jinjina kae haɗe da cewa. "Insha Allah.!" Dr.Ishaq kuwa ɗaukar jakarsa yayi, saboda dama ya gama mata duk wani abu daya kamata, ganin zai fita daga ɗakinne kuma yasa Abbou Kareem ya rufa masa baya. Ɓangaren Maleek kuwa sama da 30 minute Dr.Hafeez ya ɗauka yana checking ɗinsa. Gano matsalar Maleek ɗinne yasa take zufa ya ketowa Dr.Hafeez. Hannu yasa ya share zufan haɗe da ɗago kansa, kana ya sauƙe wata ƙatuwar ajiyar zuciya, lallai akwai aiki ja agabansa, kallon agogon dake ɗaure atsintsiyar hannunsa yayi. "10:40 am" Yafaɗa abayyane yana me ɗan zaro idanunsa. Cikin sauri da kuma hanzari ya juya yafice daga cikin ɗakin. Fou'ad dake zaune afalo yayi jigum, ganin Dr.Hafeez ɗin yafito afujajan ne yasashi saurin miƙewa tsaye, cikin bayyana tashin hankalinsa yace. "Dr. Lafiya?." Kai Dr.Hafeez ya girgiza, cikin yanayin tashin hankalin da yake ciki yace. "Ba lafiya ba, saboda akwai babban matsala mintuna 20 kawai muke dashi wanda ya rage mana da zamu iya ceto rayuwar Maleek, maza maza yanzu ka ƙira emergency, mu wuce dashi hospital." Amatuƙar razane Fou'ad yace. "20 minute fa kacal kace Doctor, bangane me kake nufi ba, please kafaɗamin meke damun Maleek.?!!!" yanayin yanda yayi maganar cikin matsanancin tashin hankali ne yasa. Dr.Hafeez soma girgiza kansa, ƙwarai shima ya tsorata da al'amarin. cikin muryarsa da tayi sanyi sosai yace. "Zuciyarsa ce take gab da bugawa!." Tamkar shock haka Fou'ad yaji sauƙan kalaman Dr.Hafeez cikin matsanancin tashin hankali yace. "Bugawar zuciya?." "Eh, irin bugawan da bazata sake amfani ba, wanda kuma za tasa ya rasa gaba ɗaya Rayuwarsa.!!!" *(No charge woo🥴. team Maleek how market? najiku shiru, kuyi haƙuri kowa da irin tasa ƙaddaran, then ƙaddara ba agogon hannu bace bare mu juyasa yanda mukeso, ahaka Labarin Laylerh Maleek yazo, amma idan zaku taushi zuciyarku asannu zakuji dadin karatu.)* 1/19/21, 8:15 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna. *(This book is mainly for those that pay, if you know you did'nt pay please don't read it. Here is the account number for people that are willing to pay-0002214625 Abubakar Muhammed Sardauna Jaiz bank. Whatsapp number 07017879464. )*                        *Chapter twenty sixth* Ahankali Fou'ad ya rumtse idanunsa wanda suka cika da ƙwalla, saboda sosai yaji  wani irin matsanancin tausayin abokin nasa ya sake lulluɓe sa, yayinda kuma yaji take zuciarsa ta karye. Tabbas ya yarda cewa kowani bawa da irin tasa ƙaddaransa arayuwa, yayinda shi kuma Maleek wannan itace ƙaddaransa, Ƙaddarar So me tsananin zafi, raɗaɗi, haɗi da kuma cutarwa, haƙiƙa sae ayau ya sake tabbatarwa da kansa cewar, ba ako da yaushe bane zurfin ciki ke haifar da riba, hasalima sometimes baya kowo komai sai danasani, da kuma ƙunan zuciya, dan asanadin hakanne kanaji kana gani zaka rasa dama da kuma zaɓin zuciyarka. Hannu yasa yaɗan dafe kansa, tuna cewar basu da wadataccen lokacine yasa shi buɗe idanunsa cikin sauri yace. "Yanzu Dr.Hafeez meye abunyi? Dan Allah kayi duk yanda zakayi wajen ganin ka ceto rayuwar Maleek, kada Mu rasashi please....!" Dr.Hafeez dake ƙoƙarin cire handglobe ɗin dake hannunsa ne, cikin sauri sauri yace.  "Babu wani wadataccen lokaci Fou'ad, domin ni kaina na tsorata da lamarin, amma yanzu na tura saƙo wa asibitin mu, nanda mintuna 5 za'azo da ambulance aɗaukeshi, rashin lokaci yasa tafiya amotar gida bazai yiwu ba." Jin hakane yasa Fou'ad sauƙe wata wahalalliyar ajiyar zuciya, hakanan gaba ɗaya komai ya daina masa dadi, zuciyarsa cike da fargaba haɗi da zallan tashin hankali ya laluɓo wayarsa dake cikin aljihu, tare da dannawa number'n Abbou Jaheed ƙira. Abbou Jaheed dake zaune abakin gadon da Laylerh ke kwance, wanda tuni ya riga daya faɗa duniyar tunani, jin ƙaran wayarsa ne yasa shi dawowa hayyacinsa, tare da zaro wayar daga aljihunsa, ganin sunan Fou'ad na yawo akan screen ɗin wayar ne yasashi saurin picking call ɗin. Saidai kuma jin abun da Fou'ad ɗin ke faɗa ne, yasa matsanancin tashin hankali ya bayyana ƙarara akan fuskarsa, hakanne ko ya sashi miƙewa tsaye cikin sauri yana faɗin kalmar. "Innalillahi Wa'inna Ilaihirraju'un!." Jin Abbou Jaheed ɗin na salati ne yasa su Oum Ayush da kuma Abbou Kareem zuba masa ido, ganin ya cire wayar akan kunnensa ne kuma, yasa Abbou Kareem cikin tashin hankali, da faɗuwar gaba yace.  "Wani abune kuma ya sake samun Maleek ɗin?." Jin Abbou Kareem ya ambaci sunan Maleek ne yasa Oum Ayush dafe ƙirjinta, tare kuma da rumtse idanunta, domin tasan ƙwarai dama hakan zai iya faruwa. Abbou Jaheed ko ganin yanda suka kafesa da ido ne, yasa ya ɗan soma girgiza kansa, cikin muryarsa da tayi matuƙar rauni yace.  "Maleek yana cikin wani hali, domin Dr.Hafeez yace mintuna 20 ne kacal suka rage na iya ceto rayuwar sa, domin zuciyarsa tana gab da bugawa." Idanu suka zazzaro su dukansu domin baƙaramin kiɗima su maganganun Abbou Jaheed ɗin sukayi ba, cikin matsanancin tashin hankali Oum Ayush da ga ba ɗaya jikinta yayi sanyi tace.  "Inna lillahi wa'inna ilaihirraju'oun, meya samu Maleek? dama bashi da lafiya ne?." Duk acikinsu babu wanda zai iya amsa mata tambayoyin nata, saboda gaba ɗaya basa hayyacinsu, damuwa ne zalla kwance akan fuskokinsu. Cikin hanzari ba tare da waninsu yace ƙala ba, suka juya suka fice daga cikin ɗakin, Abbou Jaheed har yana jin tuntuɓe. Oum Ayush da hankalinta yakai ƙololuwa wajen tashi, ganin babu wanda ya amsa ta acikinsu ne yasa ta rufa musu baya da sauri. Ahargitse suka fito compound ɗin gidan, wanda hakan yayi daidai da shigowar ambulance farfajiar gidan. Cikin gaggawa ma'aikatan ambulance ɗin suka firfito. Ahargitse kuwa su Abbou Jaheed sukayi wa ma'aikatan ambulance ɗin jagora har zuwa sashin Maleek. Koda suka shiga cikin sashin nasa kuwa, kaitsaye bedroom ɗinsa suka wuce, inda suka ɗaurasa akan wani bed me ƙafafun taya, irin dai gadon nan da ake ɗaukan marassa lafiya akai. Koda suka gama daidaita masa kwanciarsa akan gadon, cikin yanayin sassarfa suka shiga tura gadon zuwa inda motarsu take, cikin sauri su Abbou Jaheed da duk sun ruɗe, suka rufa musu baya. Ƙaran ambulance ɗin da ya cika gidan ne, yasa gaba ɗaya jama'ar dake cikin gidan suka san cewa ba lafiya, hakanne ko wasu daga cikinsu suka firfito dan ganewa idanunsu abun dake faruwa. Zuwa lokacin kuwa, har an saka Maleek din acikin motar ambulance ɗin, yayinda driver'n motar ya jata da wani irin speed ya fice daga cikin gidan. Hakan yasa take su Abbou Jaheed suka shiga moto tare da rufa musu baya. Yanayin yanda motar Ambulance ɗin ke gudu sosai akan titi batare da wani shamaki ya tsaida ta bane yasa cikin mintuna kaɗan suka iso babban katafaren asibitin da Dr.Hafeez ɗin ke aiki. Ambulance ɗin na tsayawa kuwa aka soma ƙoƙarin fito dashi daga cikin motar, koda suka fito dashi direct Emergency aka wuce dashi, nan take batare da jiran wani abu ba kuwa ƙwararrun likitotin dake cikin asibitin suka duƙufa akansa dan ganin sun ceto rayuwarsa. Acan gida kuwa hankalin su Oum Ayush amatuƙar tashe yake, saboda bata samu daman binsu asibitin ba kasancewar idan tatafi Laylerh zata iya farkawa kowani lokaci. Wanda take kuma labarin ciwon Maleek ɗin ya cika gidan. Har ya isa kunnen Momy da kuma ƙanwarta Aunty Aina'u. Wata irin dariya  me ɗauke da farinciki Momy tayi, cikin bayyana jin daɗinta tace.  "Nasamu hanya mafi sauƙi na tarwatsa akwalan zuciyar ka Maleek, domin yanzu  ne baƙin cikin rayuwarka zai soma, sannan kuma ta sanadiyar Laylerh wata rana sai ka rasa zuciya aƙirjinka." Dariya Aunty Aina'u ta fashe dashi, dan itama kanta taji daɗin hakan, cikin son zuga Ć´ar uwartata tace. "Ya kamata ace daga yanzu wasan ya soma, tunda dai aure ne an riga da an ɗaura, so ina tunanin ba amfanin tsaya wani ɓata lokaci." Murmushi Momy tayi haɗe da jinjina kanta cikin son cimma manufarta tace. "Tabbas sai abun da nakeso ya faru, sai kuma na cimma burina." Dariya sukayi su dukansu ita da Aunty Aina'un, tare da cigaba da kitsa yanda munafurcin nasu zai kasance. Ɓangaren Oum Ayush kuwa jikinta amatuƙar sanyaye ta baro compound ɗin gidan, kaitsaye ɗakinta ta koma wajen Laylerh'n da ke kwance. Teemah ce zaune agefenta, wanda gaba ɗaya yanayin damuwa ya bayyana akan fuskarta, saboda jin ance Mr.Soldier ɗinta babu lafiya, yasa duk taji jikinta ya mutu. Shigowar Oum Ayush cikin ɗakinne yasa ta ɗago kanta cikin sauri tace.  "Ya jikin Yah M.Jay ɗin?." Oum Ayush da gaba ɗaya yanayin idanunta sun sauya, sun kuma cika da ƙwalla, ajiar zucia ta sauƙe tare da ƙarasowa cikin ɗakin, cikin sanyin murya tace.  "Da sauƙi, saidai an wuce dashi asibiti." "Asibiti!." Teemah tafaɗa tana ɗan zaro idanunta wanda suka cika da tsananin tausayin Ya M.Jay ɗin da kuma ƙawarta Laylerh. Kai Oum Ayush ta jinjina mata, tare da ƙarasowa jikin gadon ta zauna, ahankali ta ɗago kan Laylerh ta ɗaura acinyarta, baƙaramin tausayin Laylerh da Maleek ɗin takeji ba, wanda hakan yasa gaba ɗaya rauninta ya bayyana, har ta kai ga idanunta na neman zubar musu da ƙwalla. Hospital. Gaba ɗaya likitotin da suka duƙufa akansa gumine ke feso musu, saboda sosai suka tsorata da ciwon Maleek ɗin, don wani irin kamu ciwon yayi masa, wanda shi kansa baisan da hakan ba, duk da cewar ciwon baici jikinsa sosai ba, amma wani abun mamakin shine zuciyarsa dake neman bugawa lokaci ɗaya. Ɗaya daga cikin doctors ɗinne ya kalli agogon dake ɗaure a tsintsiyar hannunsa, wanda ke nuna 3 minute kacal ya rage musu, akasin haka kuwa zasu iyayin losing ɗinsa. Duk wani iya ƙoƙari da basirarsu sunyi amma shiru, saidai kuma ganin da sukayi cewa, da gaske zasu iya rasashi ne yasa suka ƙara dagewa wajen ganin dawowan numfashinsa, dan ta hakane kaɗai bugun zuciyar tasa zata daidaita. Wani na'ura da suka ɗaura masa akan aƙirjinsa ne yasa shi jan wani dogon numfashi me ɗauke da yanayin nishi. Amamakance jin yanda yaja dogon numfashin ne yasa su maida idanunsu ga wata Ć´ar ƙaramar abu me kaman computer dake gabansu. Ahankali suka ga numfashin nasa na ƙoƙarin dawowa, yayinda take zuciyarsa fara ɗan motsi da harbawa. Ajiyar zuciya suka sauƙe su dukansu, domin hakan alamace dake nuna zallan nasara, dan ba kaɗan ba shawo kan matsalar tasa ya basu wuya. Handglobes ɗinsu suka soma cirewa yayinda wasu daga cikinsu suka turo gadon da Maleek din ke kwance zuwa wani special room. Acan waje kuwa hankalin su Abbou Kareem amatuƙar tashe yake, kasancewar dukansu basu san awani hali Maleek din ke ciki ba. Aɓangaren Abbou Jaheed kuwa ko zama ya kasayi, kallo ɗaya zaka masa kafahimci cewa yafi kowannensu shiga tashin hankali, yayinda aransa yake ta fata da kuma addu'an samun sauƙin ɗannasa, kasancewar shi kaɗai ne ɗan daya ke dashi guda ɗaya aduk faɗin duniya, saboda haka bazai taɓa son wani abu da zai cutar dashi ba. Dr.Hafeez da kuma Dr.Al-bashir wanda fitowarsu daga emergency room ɗin kenan, ganin su Abbou Jaheed atsaytsaye cikin tashin hankali ne yasa suka ƙaraso garesu. Ganin Doctors ɗinne yasa su Abbou Jaheed zuba musu ido, kowannen su zuciyarsa cike da tarin fargaban abun da kunnuwansa zasu jiyemai. Ganin yanda tashin hankali ya bayyana ƙarara akan fuskokinsu ne yasa. Dr.Hafeez sakin murmushi, cikin son ƙarfafa musu guiwa yace.   "Alhamdulillah ku kwantar da hankalinku, domin da izinin Allah Nida abokan aikina munyi nasarar ceto rayuwar Maleek." Tamkar sauƙan ruwan sanyi haka su Abbou Jaheed sukaji kalaman Dr.Hafeez, sanadin hakan kuwa yasa suka sauƙe wani irin ƙatuwar ajiyar zuciya, da ke bayyana tsananin jin daɗinsu. Take kuwa cikin tsananin zumuɗi da zallar farinciki Abbou Jaheed yace. "Alhamdulillah Allah, Yanzu Dr.Hafeez ina Maleek ɗin yake? ya buɗe idanunsa kuwa?." Ɗan girgiza kai Dr.Hafeez yayi, inda Dr.Al-Bashir ya gyara tsayuwarsa, kana cikin kulawa yace. "Munkaisa ɗakin hutu na musamman, saidai har yanzu bai buɗe idanunsa ba, amma hakan bazai zamo wani abun damuwa ba, insha Allah koda yaushe zai iya buɗe idanunsa, ya kuma dawo cikin hayyacinsa." "Alhamdulillah!!." Dukansu suka haɗa baki wajen faɗan hakan, domin ba kaɗan ba sukaji dadin kyakkyawan labarin da su Dr.Hafeez ɗin suka kawo musu, wanda hakan yasa zuciyoyinsu yin sanyi. "Amma kana ga zamu iya ganinsa yanzu kuwa Doctor? " Abbou Kareem ya tambaya. Kai Dr.Hafeez ya girgiza cikin kulawa yace. "Agaskia yanzu yana buƙatar hutu sosai, duk dama bai gama dawowa hayyacinsa ba, so inaga zaifi kyau ku bari sai nan da cikakken 1 hour, kafun nan brain ɗinsa ta sake hutawa, saboda sai brain ɗinsa ta samu nutsuwa sosai, kafun bugun zuciyarsa zai cigaba da tafia daidai." Jin hakanne yasa su jinjina kae, cike da gamsuwa da kalaman Dr.Hafeez ɗin. Duban Abbou Jaheed Dr.Hafeez yayi, anutse yace.   "Please Alhaji ina son ganinka a office." Da "To" Abbou Jaheed ya amsa, nan kuwa su Dr.Hafeez ɗin sukayi gaba shi kuma ya rufa musu baya. Yayinda Abbou Kareem da Alhaji Ahmad da kuma Fou'ad suka samu guri suka zauna, anan kan wasu bench zuciyoyinsu cike da nutsuwa. Abbou Jaheed kuwa kaitsaye Office ɗiɓ Dr.Hafeez suka wuce. Koda suka ƙarasa cikin office ɗin kujeran da aka tana da musaman dan zaman baƙi, Dr.Hafeez ya nunawa Abbou Jaheed, alaman ya zauuna. Gane abun da Dr.Hafeez ɗin ke nufi ne yasa Abbou Jaheed jawo kujeran ya zauna, tare da maida dubasan ga Dr.Hafeez. Gyara zama Dr.Hafeez yayi haɗe da sauƙe ajiyar zuciya. Wani file ya ɗauko yayu rubutu aciki, bayan ya gama ne kuma ya ɗago ya kalli Abbou Jaheed cikin nutsuwa yace.  "Please Alhaji dama Maleek yana ɗauke da wata damuwa ne, wanda ta jima tana damunsa?." Kai Abbou Jaheed ya girgiza, kana cikin sanyin jiki yace.   "Agaskiya Dr. Bana tunanin haka, saboda a iya sanina da shi, baya sakewa da jama'a bare kuma har damuwarsu ta dameshi." Ajiyar zuciya Dr.Hafeez yayi, kana yace. "Babu wata damuwa Insha Allah Zai samu sauƙi, saidai kuma agaskiya yana da buƙatar kulawa sosai, dan akwai buƙatar hanasa yawan tunani, domin matuƙar yana sa damuwa aransa da kuma yawan tunani to fa wani abunne na daban zai iya kamasa, wanda magancesa bazai zo mana da sauki ba, sannan ya kamata aguji ɓata masa rai, domin samun kansa acikin bacin rai shima abune da zai iya jawo masa babbar matsala." Kai Abbou Jaheed ya jinjina tare da faɗin.  "Insha Allah zamu kiyaye." Hannu Dr.Hafeez ya miƙa masa sukayi musabaha, tare da tabbatar musu da cewar akowani lokaci Maleek ɗin zai iya dawowa hayyacinsa, duk dama sunyi masa allurai masu ƙarfi, saidai ganin yana da ƙarfin jini yasa suka sa tsammanin cewa zai iya dawowa hayyacinsa anan kusa. Koda Abbou Jaheed ya fito daga office ɗin Dr.Hafeez, direct wajen daya bar su Abbou Kareem ya nufa. Kallon Abbou Kareem da kuma Alhaji Ahmad, harma da Najeeb wanda ya iso wajen bada jimawa ba yayi, ganin kaman akwai damuwa akan fuskarsu ne ya sashi nemo ƙwarin guiwa ya azawa kansa, cikin kulawa ya dubi Fou'ad dake zaune wanda ya zuba tagumi.  "Fou'ad."  Yaƙira sunansa, hakanne yasa Fou'ad din ɗago kai ya kalli Abbou Jaheed ɗin. "Ka zauna dashi, mu zamu koma gida kasan munbar mutanen gidan cikin tashin hankali, ga kuma Laylerh itama ba lafiya ne da ita ba." Cike da gansuwa Fou'ad ya jinjina kai alaman "To." Abbou Kareem kam har acikin ransa baiso tafiya ba, saidai ganin Abbou Jaheed din dakansa ne yace su tafi yasashi amincewa, nan suka shiga motarsu suka kama hanyar dawowa gida. Gida. Ahankali ta soma ɗan buɗe idanunta wanda sukayi luhu luhu, kana kuma suka ƙanƙance, jin kaman an ɗaɗɗaure mata jijiyoyin jikinta ne yasa ahankali ta soma ƙoƙarin motsa hannunta. Oum Ayush dake zaune agefenta ganin ta fara motsi ne yasa ta zuba mata ido, ahankali cikin sanyin murya ta ƙira sunanta. Jin muryar Oum Ayush acikin kunnenta ne yasa ta ƙarasa buɗe idanunta, ƙoƙarin amsa ƙiran da Oum Ayush ɗin tayi mata take, saidai kuma ta kasa, saboda yanda taji laɓɓan bakinta sunyi mata nauyi. Ahankali ta soma ɗan jan jikinta, kasancewar so take ta tashi zaune, duk da kuwa batajin wada taccen ƙarfi ajikinta. Ganin tana yunƙurin tashi ne yasa Oum Ayush kamo kafaɗunta tare da taimaka mata ta ɗan jingina bayanta ajikin gadon. Cikin kulawa Oum Ayush ɗin tace.  "Sannu ko ya jikin naki?." Kanta ta jinjina alaman da sauƙi, gefen fuskarta Oum Ayush ta shafa, cike da tausayinta tace.   "Yanzu ina ne ke miki ciwo?." Kai ta ɗangirgiza ahankali takai hannunta daidai saitin ƙirjinta, wanda da dukkan alamu nan ɗinne ke mata zafi. Fahimtar cewa ƙirjin nata ne kaɗai ke mata ciwo yasa Oum Ayush duban Aunty Zee cikin kulawa tace.  "Zee haɗo mata tea yanzu tasha please." "to" Aunty Zee ta faɗa take kuwa cikin gaggawa ta fice daga cikin ɗakin. Mintuna 5 tsakani ta dawo cikin ɗakin hannunta ɗauke da mug wanda ta haɗa tea din aciki. Ƙarasowa jikin gadon tayi tare da miƙawa Oum Ayush mug ɗin. Karɓan mug ɗin Oum Ayush tayi tare da kamo hannun Laylerh, cikin kulawa tace.  "Tashi kisha tea kinji, nasan zaki ɗan samu ƙarfi ajikinki." Jin abun da Oum Ayush ɗin tafaɗa ne yasa ta shagwaɓe fuska, saboda kwata kwata bata sha'awar komai, "Naƙoshi." Tafaɗa akasalance, tare da jan blanket ta rufe jikinta, dan bawani rigar kirki bane ajikinra, nan ma Oum Ayush ɗinne tasa mata rigar. "Kiyi hakuri ki sha kinji, saboda likita yace sai kinci abinci kafun kisha magani, dan akwai yunwa ajikinki, karbi kishi kinji Laylerh na." Oum Ayush ta faɗa cikin rarrashi. Haƙiƙa acikin yanayin da takejin kanta batajin zata iya ɗaukan rarrashi, saboda ayanzu ma zuciyarta bugawa take da sauri sauri, yayinda tarin tambayoyi ke kwance acikin ƙirjinta, kallon Oum Ayush ɗin tayi, cikin karyayyar muryarta me ɗauke da matsanancin rauni tace.   "Nasan zuwa yanzu Abbou Jaheed ya ɗauramin aure ko Oum Ayush?." Jin tambayar nata ne yasa matsanancin tausayinta ya rufe zuciar Oum Ayush,  hannunta takai ta dafa kafaɗun Laylerh'n, cikin sigar lallashi haɗe da sanyin murya tace.  "Haka Allah Ya tsarawa rayuwarki Laylerh, kuma inaso kisani kowa baya wuce ranarsa, domin aure kaman Mutuwa ne, ranar da Allah ya tsayarwa mutum ko za'ayi yaya bazai wuce saba, kisawa zuciyarki salama, domin fatan mu ako da yaushe shine Allah Yabaku zaman lafiya da kwanciyar hankali azaman aurenki da Najeeb, domin ayanzu ya riga daya zamo mijinki, wanda kuma nan da anjima kaɗan zamu miƙa mishi ke amatsayin mata." Jin abun da Oum Ayush ɗin ta faɗa ne, yasa ta lumshe idanunta wanda suka ciko da ƙwalla, ahankali taji bugun zuciyarta na ci gaba da tsananta, yayinda wani irin abu me kama da maɗaci ya tsaya amaƙoshinta. "Shikenan yanzu ta zama matar aure?" tayiwa kanta tambayar, take kuwa hawayen da suka cika idanunta suka samu daman gangarowa kan fuskarta. Daidai lokacin ne kuma aka turo ƙofar ɗakin, wanda hakan yasa su Oum Ayush suka maida kallonsu ga ƙofar. Ganin Abbou Jaheed da kuma Najeeb dake biye dashi abayan ne yasa Oum Ayush sauƙe ajiyar zuciya. Ƙarasowa cikin ɗakin Abbou Jaheed yayi, wanda ganin Laylerh'n a ɗan kishingiɗe yasa shi jin sanyi aransa. Da ɗan sauri ya yaraso jikin gadon yana me ƙiran sunanta. Jin muryar Abbou Jaheed akunnenta ne yasa tayi saurin buɗe idanunta, take kuwa wasu sabin hawaye suka shiga sauƙa akan kumatunta. Ganin hawaye afuskarta ne yasa Abbou Jaheed shafa kanta, cikin kulawa yace.  "Sannu ko Laylerhtun Abbou Jajeed ya jikin naki?." Shagwaɓe sick face ɗinta tayi, cikin muryarta dake ɗauke da rauni tace "Da sauƙi." Kai Abbou Jaheed ɗin yanjinjina, tare da duban Oum Ayush cikin kulawa yace.  "Taci abinci kuwa?." Kai Oum Ayush ta girgiza alaman "A'a"  tare da nuna masa mug ɗin tea ɗin dake hannunta.  Karɓan mug ɗin yayi haɗe da miƙawa Laylerh'n, cikin kulawa yace.  "Karɓi kisha kinji." kai ta girgiza alaman "A'a." domin har acikin zuciyarta yanzu babu wanda takeson gani sama da Maleek. Najeeb. Ahankali ya sauƙe ajiyar zuciya tare da tura duka hannayensa cikin aljihun rigar jumper'n dake jikinsa, duk da cewar kwana huɗu kawai yayi baisata a idanunsa ba, amma hakan bai hanashi ganin kyau da kuma hasken da ta ƙara ba,  ba abun daya fi ɗaukar hankalinsa atattare da ita kuwa, kaman cute innocent face ɗinta, da kuma jajayen lips ɗinta. Idanunsa dake cike da mayen soyayyarta ya lumshe, ahankali ya fesar da wani numfashi, yayinda yakejin kamar yaje ya rungumeta acikin jikinsa.musamman ma yanda yaga tana zuba zallar shagwaɓa, wannan yasa shi jin gaba ɗaya tsikar jikinsa sun mimmiƙe. Abbou Jaheed kuwa ganin da gaske Laylerh'n taƙi karɓan tea dinne yasa shi ajiye mug din haɗe da miƙewa tsaye, kallon Oum Ayush da kuma Aunty Zee yayi, cikin nutsuwa yace. "Mutafi wata ƙila idan Najeeb ya mata magana zata sha."  Jin hakanne kuwa yasa Oum Ayush da Aunty Zee harma da Teemah suka miƙe, jin an anbaci Najeeb ne kuma yasa Teemah sake kallon haɗaɗɗen gayen dake tsaye cikin milk colour ɗin shadda, wanda dama tun shigowarsa take kallonsa. Murmushi ne ya bayyana akan fuskarta, acikin zuciyarta tace. "Gaskiya Najeeb handsome guy ne, shine wannan Ć´ar rainin hankalin zata wani ce bata sonshi." ƙwafa tayi tare da ƙudurtawa aranta cewar sai tayiwa Laylerh'n tsiya, da zaran tasamu sauƙi saita tsokane ta. Kasancewar kuma Teemah'nce ta zamo ta ƙarshen fita daga ɗakin, hakan yasa ta jawo ƙofar ɗakin ta rufeta gam. Laylerh kuwa ganin su Abbou Jaheed sun fita daga cikin ɗakinne yasata maida idanunta ta rumtse su ƙam, lokaci ɗaya kuwa ƙirjinta ya soma bugawa, akaron farko cike da tsoron Najeeb ɗin ta ƙanƙame jikinta waje ɗaya. Najeeb kuwa da bai motsa daga tsayuwan nasa ba, har yanzu idanunsa akanta suke, saboda yanda yaji idanun nasa basu ƙoshi da kallonta ba, ganin kuma yanda take ta kakkame jikinta ne yasashi takowa ahankali ya ƙaraso jikin gadon. Ƙamshin turarensa da ya shiga ratsa cikin hancinta ne ya sata gane cewar ya iso kusa da ita. "Laylerh.!!" Yaƙira sunanta cikin wata irin murya, me ɗauke da wata irin amo. Hakanan ta samu kanta da kasa amsa masa, tare kuma da kasa buɗe idanunta ta kalleshi, saboda abu ɗaya ne ke yawo acikin zuciyarta, kuma shi kaɗai take so, shi take son gani da ji, shi kaɗai ne kuma zai iya rarrashinta har zuciyarta ta samu nutsuwa, haƙiƙa MALEEK shine saɓin zuciarta. *(Sorry guys jia banyi update ba, saboda naga dayawanku fushi kuke da auren Laylerh shiasa nima nace bari na huta.😃)* *24 December 2020* 1/19/21, 8:25 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna *(This book is mainly for those that pay, if you know you did'nt pay please don't read it. Here is the account number for people that are willing to pay-0002214625 Abubakar Muhammed Sardauna Jaiz bank. Whatsapp number 07017879464. )* *Chapter twenty eighth* Sauƙan harshensa acikin bakinta ne yasa bugun zuciya, da nunfashinsu soma ƙoƙarin ɗaukewa, musamman saboda yanda sukaji wani irin abu me tsananin ƙarfi ya shiga cikin jikinsu, wanda hakan yasa suka samu kansu acikin wani irin yanayi me matuƙar wahalar fassaruwa, irin yanayin kuwa da dukkaninsu basu taɓa sanin cewar akwaishi acikin duniya ba, yanayin daya gusar musu da hankali haɗi da nutsuwarsu, kana yanayin da yasa gaba ɗaya rauninsu bayyana, tabbas ayau dukansu sun shaida cewar su ɗin muradi da kuma BURI ƊAYA ne, domin haɗewar su waje ɗaya yasa wani irin matsanancin shauƙi da kuma zazzafan ƙauna ya shiga yawo acikin jininsu, tare da haukata duk wani nau'in tunanin dake yawo acikin ƙwaƙwalwarsu, wanda sanadin haka yasa gaba ɗaya jikinsu ya soma ɓari. Tabbas ayau bashi da ikon control ɗin kai da kuma zuciyarsa, kasancewar ayau ne duk wata soyayyar dake ɓoye acikin zuciyarsa ta bayyana kanata afili, haƙiƙa rasa Laylerh awajensa tamkar rasa rayuwarsa ne, domin kuwa ayau ya sake tabbatarwa da kansa cewar itace bugun zuciya da numfashinsa. Tabbas wannan yanayi ne da ya zamo baƙo agaresu, saboda haɗuwar saliva ɗinsu waje ɗaya ba ƙaramin gigita musu tunani yayi ba, musamman Laylerh wanda ɗanɗanon yawun bakin Maleek ɗin yasa ta fara ƙoƙarin manta kae da kuma duniyar da take, kasancewar a iyaka tsawon rayuwarta, wannan shine karo na farko da wani namiji ya fara sanya bakinsa acikin nata, kuma wannan shine karo na farko da ta fara jin ɗanɗano da kuma launin saliva ɗin sa. Maleek kuwa da gaba ɗaya jikinsa ya ɗauki rawa, ahankali cikin matsanancin shauƙin dake ɗibansa, ahankali ya sake tura harshensa acikin bakinta, amatuƙar sanyaye yasa laɓɓansa ya kamo Ć´an ƙananan lips ɗinta, da aka shafawa sweat lipgloss, hannayensa yasa ya sake matseta ajikinsa, adaidai lokacin da yayiwa lips ɗinta wani fitinannen sucking ɗin daya sa lokaci ɗaya numfashinta ya soma ƙoƙarin ɗaukewa, haƙiƙa kasantuwar hakan shine karo na farko agaba ɗaya tarihin rayuwarsu, shin tayaya zasu misalta yanayin, da kuma faɗarsa?. Tabbas ba zata iya jurewa yanda yake tsotsan bakinta da jajayen laɓɓansa masu masifar taushi ba, domin har aƙasan ƙafarta takejin wani abu na yi mata yawo, yayinda gaba ɗaya tsikar jikinta suka mimmiƙe, jin yanayin nasu take kamar amafarki, kasancewar ko da wasa bata taɓa kawo tunanin hakan aranta ba. Yanayin yanda yake juya harshensa acikin bakinta ne, yasa harshensu haɗewa waje ɗaya. Wanda hakan yasa cikin fitinnannen yanayin da ta samu kanta aciki ta sake shigewa jikinsa, haɗe da manna ƙirjinta da nasa, wanda kuma tayi hakanne saboda bata cikin hayyacinta, kasancewar garɗi da kuma daɗin saliva ɗinsa, yasa tuni ta manta matsayita, da kuma sanin wacece ita. Aɓangaren Maleek ma hakan take, dan kuwa kamar yanda Layler'n ta zauce haka shima ya fita hayyacinsa, yayinda gaba ɗaya ya manta wacece ita awajensa, zazzafan soyayyar da yake mata yasa shi manta cewar ita ɗin matar wani ce, kana halaliyar wani, kuma mallakin wani. Saboda ayanzu gaba ɗaya zuciyarsa ta cika da matsanancin son nunawa Laylerh'n irin yanda yajima yana muradin ta. Yanayin yanda yake shan bakinta amatuƙar zauce ne yasa shi mata wani irin runguma, wanda har sai da ƙashin jikinta yayi ƙara, saboda yanda ya matseta sosai ajikinsa, haka yakejin kansa kamar mayunwacin zaki, yayinda kuma yakejin kamar ya ciro zuciyarsa ya damƙa mata atafin hannunta, ko hakan zai sa ya samu sassauci na daga abun da yakeji, saboda ayanzu yakai ƙololuwar zautuwa akan soyayyarta, haƙiƙa son da yake mata ya wuce duk wani tunanin me tunani. Laylerh kuwa ahankali wasu zafafan hawaye suka kwaranyo daga cikin idanunta, yayinda tuni tsayuwa ya soma ƙoƙarin gagararta, duba da irin yanda ta samu kanta acikin wani fitinannen baƙon yanayi, wanda kuma tunda take adunia bata taɓa shiga makamancinsa ba, tabbas ayanzu Maleek ya kawota wata gaɓa, wanda yasa bazata ko iya tsayawa da kafafunta ba, kasancewar kuma takai maƙura ne yasa, ahankali gaba ɗaya jikinta ya sake, take kuwa ta narke ajikinsa, tare da soma yunƙurin zube guiwowinta aƙasa. Saidai kuma kasancewar Maleek ɗin na riƙe da ita, hakan yasa bai bari ta kai ƙasa ba, ya sake mannata da jikinsa. Ahankali cikin yanayin sanyi ya zare bakinsa daga cikin nata, tare da haɗe goshinsu waje ɗaya. Idanunsa wanda sukayi jajur, suke kuma ɗauke da danshin hawaye ya buɗe, tare da sauƙe ganinsa akan kyawawan idanunta, wanda har zuwa yanzu basu daina zubar da ƙwalla ba. Ahankali ya soma fitar da wani irin numfashi. Cikin yanayin sanyi da kuma son daidaita nutsuwarsa, yakai hannunsa kan fuskarta, ahankali ya soma ƙoƙarin share mata hawayen dake kwance kan fuskar nata. Jin hannunsa akan fuskarta ne, yasa ta ɗaura nata hannun akan nasa, tare da kama hannun nasa ta riƙe. Cikin yanayin sanyin dake bayyana matuƙar rauninta, ahankali ta soma ɗan grgiza kanta, yayinda laɓɓan bakinta suka soma ɗan motsawa, da alama wani abu takeson faɗa, amma kuma ta kasa. Ganin hakan da yayi ne kuma ya sashi ƙura mata tsumammun idanunsa, dake matuƙar rikitata. Ƙwarai yasan akwae wani abu acikin zuciarta, wanda kuma hakanne kuma ya sashi, jafa idanunsa acikin nata baya ko ƙyaftawa, kasancewar so yake ya karanci abun dake cikin zuciarta ta hanyar kallon ƙwayar idanunta, saidai kuma yanayin yanda zuciarsa ke bugawa da matsanancin sonta, ya riga daya sashi rasa duk wata nutsuwarsa, yayinda daga wani sashe na ɓangaren tunaninsa kuwa, gani yake kamar duk abun dake faruwa bai zamanto gaskia ba, haka yake ganin komai kamar amafarki, saboda kasantuwarsa da Laylerh'n ya sashi jin wani abu na daban, kana kuma na musamman, haƙiƙa ayau zuciarsa ta riga da ta gama karyewa, domin yasan cewar ya rasa fata da duk wani muradin sa, tayaya zai iya rayuwa batare da ita ba? tayaya zuciyarsa zata iya jurewa? sama da shekaru sha ya ɗauka yana dakon wani abu azuciarsa wanda baisan ko menene ba, duk kuwa da cewar akowacce rana zafi da kuma ɗaɗaɗin abun na sukan zuciarsa amma haka yake daurewa, akullum burinsa kuma shine yasan gaskiyar abun dake zuciarsa, baisan kowa ba, bai saba da kowa ba, shi kaɗai yake rayuwarsa, idan zafi yaji shi kaɗai yake shanyewa, haka kuma idan yaji damuwa zuciarsa yake barmawa, saboda bashi da wanda zai faɗawa, sama da shekaru bakwae kenan yanzu da sanin haƙiƙanin matsalar dake damun zuciarsa, amma haka ya daure, ya kuma bawa kansa ƙarfin guiwa, akullum ji yake ajikinsa cewa bazai taɓa zama me gazawa ba, wannan yasa komae tsananin abu yakan iya jurewa, haƙiƙa amatsayinsa na Namiji kuma soldier ya shanye abubuwa da yawa, amma ayau rana ɗaya kawai komai ya ruguje, yazama Loser. Tabbas bazai taɓa mantawa da wannan ranar ba, domin acikinta ya fara sanin meye gazawa, haka kuma acikinta ne yafara sanin haƙiƙanin ƙunci, da kuma ɗacin rayuwa, kana kuma acikinta ne kalmar Gazawa ta mamaye gaba ɗaya rayuwarsa, ya zama me RAUNI, me tsananin RAUNI. Lallai ako da yaushe mutum yana rayuwa cikin lafiya ne idan jini yana gudana yanda ya kamata acikin jikinsa, idan akasin hakan ta faru kuma saɓanin farinciki ne yake biyowa baya, kasancewar Laylerh itace ginshiƙin numfashi, kuma jininsa me zai faru dashi kenan alokacin da tabar jikinsa? amsa guda ɗaya ce itace Mutuwa. Haƙiƙa ya aminta cewar gaba ɗaya rayuwa cike take da ƙaddara, kuma ako yaushe sanjawa take, kamar yanda ayau wata sabuwar shafin ƙaddara ta buɗe masa, wanda kuma sanadin hakan yasa, ya zamo mutum me matuƙar rauni. Tabbas akullum kuma ako yaushe yakan tambayan kansa, akan meyasa ƙaddara take wujijjiga rayuwarsa?. Yau ga Laylerh tsaye agabansa amatsayin matar wani, Laylerh'n da ya rayu da sonta acikin kirjinsa sama da shekaru, Laylerh'n da kowani bugun zucia da numfashinsa ke tafiya da matsanancin sonta, Laylerh'n da yakejin ta ajikinsa kamar jini, Laylerh'n da ta kasance. AYSHNOOR ɗinsa, mafarkinsa, burinsa, kana kuma bugun zuciyarsa, Laylerh'n da tazamo gaba ɗaya duniyarsa. Tabbas abune me matuƙar wahala jure rayuwa babu masoyi, saidai har yanzu bazai cire rae ba, haƙiƙa zai jira, kuma ko yaushe zai zamana cikin jiranta, tabbas zai jirata har zuwa lokacin da zuciarsa zata daina bugawa, lokacin da numfashinsa zaibar gangar jikinsa, son LAYLERH ajininsa yake, daina sa abune da har abada bazae taɓa yiwuwa ba. Idanunsa da suka cika da ƙwalla ya lumshe, tare da cije laɓɓansa da ƙarfi. "Zanjiraki Ayshnoor, haƙiƙa zan jiraki har zuwa lokacin da numfashi zae bar jikina!..." Yafaɗa cikin wata irin raunanniyar muryar dake bayyana karyewar zuciarsa, wanda kuma ga dukkan alama baisan maganar tasa ta fito fili ba, dan atunaninsa azuciya yayi ta. Ahankali ya sassauta riƙon da yayi mata, cikin sanyi ya ɗaura bakinsa adaidai tsakiar forehead ɗinta, tare da sakar mata wani irin hot kiss, wanda yasa gaba ɗaya tsikar jikinta mimmiƙewa. Ahankali ya ɗan soma janye jikinsa baya daga gareta. Laylerh da wani sabon kuka ke shirin cimmata, da sauri ta riƙo hannunsa, kanta tasoma girgizawa, kana cikin wata irin muryar da ta taho tare da matsanancin kuka tace. "Dan Allah Yah Maleek! Dan Allah!!!" Yanayin yanda tayi maganar cikin kukane yasa shi soma girgiza mata kai, tare kuma da ƙoƙarin zare hannunsa dake cikin nata, saboda bayajin zai iya jurewa yanayin da yakejin kansa aciki, domin idan yaci gaba da kasancewa ahaka zuciarsa zata iya tarwatsewa. Laylerh kuwa da gaba ɗaya kukan da take yakusa shiɗar da'ita, ganin da gaske zai zare hannunsa daga cikin nata ne yasa ta fashewa da wani sabon kuka me tada hankali, wanda yasa gaba ɗaya jikinta ya soma rawa, hakanne kuwa ya bashi daman zare hannunsa daga cikin nata, ahankali ya ɗan soma jan jikinsa baya, tare da soma girgiza mata kai, yayinda kuma ya kasa ɗauke idanunsa akanta, wanda suka cika da ƙwalla. Ganin hakane kuma yasa itama ta soma girgiza masa kae, saboda kuka yaci ƙarfinta sosai, hakan yasa bazata iya magana ba, duk da cewar kuma ƙafafunta sun kasa tsayuwa waje ɗaya, haka tashiga takawo ahankali, dan so take ta kusanta kanta dashi, domin har yanzu bai daina jan jikinsa baya daga gareta ba. Hannunta dake rawa ta miƙo masa, cike da burin son ya kama hannun nata, cikin muryarta da ta zama over cracking tace.. "Pl....e.a...s.ee BOO don't leave me! Please!!!" Tamkar narkakkiyar dalma haka zuciarsa ta narke, alokacin da taƙirasa da sunan BOO, sunan da yajima yana so yaji daga bakinta, sunan da yayi matuƙar kewar jinsa daga bakinta. Take hawayen dake cikin idanunsa suka soma ƙoƙarin sauƙowa kan kumatunsa, wanda hakan yasa cikin sauri ya juya, tare da murɗa handle ɗin ƙofar bathroom ɗin dake bayansa ya shige, kafun Laylerh'n ta ƙaraso kuwa tuni ya murzawa ƙofar key. Hakanne kuwa yasa Laylerh da ta iso da sauri, ta faɗa jikin ƙofar tare da sakin wani irin kuka me matuƙar taɓa zucia da kuma ta da hankalin me sauraro. Jin kukan tane kuma yasa ahankali ya sulale ƙasa inda ya zauna daɓas, tare da jingina bayansa da jikin ƙofar, idanunsa ya rumtse ƙam saboda kokaɗan bayason jin kukan Laylerh'n, dan ko ayanzu haka jin zuciarsa yake na ƙuna kaman zata faso ƙirjinsa. Laylerh kuwa zuwa yanzu, mafarkin da tayi daren shekaran jia ne ya shiga dawowa ƙwaƙwalarta filla filla, wanda hakan yasa sautin kukanta ƙaruwa, har ya kai ga numfashinta ya soma ƙoƙarin ɗauƙewa, hakanne kuwa yasa ta ta durƙusa guiwowinta aƙasa tare da jingina kanta da jikin ƙofar, ahankali cikin sheshsheƙa ta soma ƙiran sunansa. Maleek kuwa duk yanda yaso daurewa hakan ya kasa, dan haka yakejin kaman kansa zai tarwatse, haƙiƙa kukanta shine abu na farko dake saurin karyar masa da zucia, kana kuma shike sawa yaji kaman ana sukan zuciarsa da mashi, saboda matuƙar yaji sautin kukanta, zuciarsa ɗumi take ɗauka. Ahankali ya tashi daga jikin ƙofar, tare da arowa kansa juriya ya ƙarasa gaban jakuzzien dake cikin toilet ɗin, haƙiƙa ayanda yakejin kai da zuciarsa, yasa shi jin zai iyayin komai matuƙar zaiji salama da kuma sassauci. wannan yasa batare da tunanin komai ba ya shiga cikin jakuzzie'n dake cike da ruwa ya kwanta, tare kuma da nutsa kansa acikin ruwan, hakanne ko yasa gaba ɗaya jikinsa ya lume, take kuma ruwan ya soma shiga cikin hanci da bakinsa. Yanayin yanda ya kwanta acikin ruwanne kuma yasa ga wanda baisani ba idan ya shigo cikin bathroom ɗin bazai taɓa tunanin cewa akwai mutum acikin jakuzzie'n ba, saboda yanda gaba ɗaya ruwan dake cikin jakuzzie'n ya haɗiyesa. Sunday 27 december 2020 7:36 pm. 1/19/21, 8:25 PM - Ummi Tandama: *L.M* *Chapter 30* Oum Ayush na riƙe da hannunta suka nufi babban falon gidan, wanda yake mallakin Abbou Jaheed ne, da yawan lokuta anan yake sauƙe muhimman baƙinsa. Koda suka ƙarasa cikin falon kuwa, zaune suka samu su Abbou Jaheed ɗin akan luntsuma luntsuman kujerun dake cikin falon . Kaitsaye wajen Abbou Jaheed Oum Ayush ɗin ta nufa, wanda kuma har yanzu riƙe take da hannun Laylerh, akan lallausan carpet ɗin dake malale atsakiyar falon, Oum Ayush ta zaunar da ita, daidai gaban Abbou Jaheed. Abbou Jaheed kuwa da ke riƙe da jarida ahanunnunsa, ganin shigowar Oum Ayush da Laylerh'n ne yasashi ajiye jaridan daily trust ɗin dake hannunsa. Ɗan gyara zamansa yayi, kana cike da kulawa ya kalli Laylerh'n wanda ta duƙar da kanta ƙasa, murmushi ne ya ɗan bayyana akan fuskarsa, wannan yasa cikin farincikin da yakejin kansa aciki yace. "Laylerh'n Abbou Jaheed matso kusa da Abbou'nki mana." Laylerh da gaba ɗaya jikinta ke asanyaye, jin abun da Abbou Jaheed ɗin ya faɗa ne yasa ta ɗan muskutowa tare da matsowa kusa dashi. Hannu Abbou Jaheed yasa ya ɗan shafa kanta, cikin kulawa da kuma bayyana farincikinsa yace. "Alhamdulillahi Allah ya bani dama da kuma iko, yau na cika alƙawarin dana ɗauka, kana kuma na sauƙe nauyin dake rataye a wuyana, ayanzu Laylerh, babu abun da zance saidai yi miki fatan nasara agidan aurenki da kuma kyakkyawar rayuwa, sannan ahar kullum kuma ina me godewa Allah da yasa kika zamo Ć´a me biyayya agareni, Allah Ya Miki albarka Laylerh, ya kuma baki Ć´aĆ´a masu biyayya kamar yanda kika zama me biyayya agaremu." "Ameen." Abbou Kareem da kuma Oum Ayush suka amsa, yayinda kowannensu fuskarsa ke ɗauke da murmushi. Wanda Abbou Jaheed ɗinma Murmushi ne bayyane akan fuskarsa, cikin ɗan sigar tsokana yace. "To ni ma yau ɓoyemin fuskar ɗiyar tawa akeyi, baza'a bari nagani ba." yayi maganar yana me ƙoƙarin ɗaga mayafin da ya rufe fuskar Laylerh'n. Murmushi Oum Ayush tayi tare da cewa. "Eh mana Alhaji, ai kasan amarya, fuskarta tsada yake dashi awajen kowa." Murmushi Abbou Jaheed ɗin yayi, adaidai lokacin daya ɗan ɗage mayafin, wanda take fuskar Laylerh'n ta bayyana, ganin hawayen da yayi kwance akan fuskarta ne kuma, yasa take yanayin fuskarsa ta sanja, lokaci ɗaya jikinsa ya ƙarayin sanyi, domin dama ƙarfin hali kawai yake, take kuma wani sabon tausayin ta ya lulluɓesa, hakanne ko ya sashi ƙiran sunanta murya asanyaye. Laylerh wanda ganin Abbou Jaheed ɗin yasa zuciyarta ta ƙara karyewa, kasa amsa ƙiran nasa tayi, take kuma wasu sabbin hawaye suka cika idanunta, hakan ko yasa ahankali tayi ƙasa da kanta, tare da haɗe yatsunta waje ɗaya ta ɗan soma murzawa, lokaci ɗaya kuma batare da ta ankara ba hawayen dake cikin idanunta suka shiga gangarowa kan fuskarta. Ganin hakane yasa Abbou Jaheed sauƙe ajiyar zuciya, tare da kai hannunsa ya dafa kafaɗan ta, cikin yanayin sigar lalallashi yace. "Kuka kuma Laylerh? please ki share hawayenki kinji, yau ranace ta Musamman agareki bai kamata ace kina ɓarnatar da hawayenki ba, domin babu wani mutumci da daraja ha Ć´a mace, wanda ya wuce mata zaman gidan mijinta, kiyi farinciki domin dayawan mata suna da burin ganin irin wannan ranar, da za akaisu ɗakin mijinsu, saboda haka ki daina kuka, addu'ar mu kuma ako da yaushe shine Allah Ya baku zaman lafiya da zuriya ta gari, sannan inaso ki ɗauka cewar ba wai zallan jin daɗi ne kawae acikin rayuwar aure ba, haƙiƙa akwai ƙalubale da yawa, hakan yasa watarana zaki samu kanki cikin farinciki, watarana kuma akasin haka, saidai ina me umartarki da ako yaushe ki riƙe mijinki hannu bibbiyu, sannan kiyi masa biyayya iya iyawarki, domin ta hanyar hakanne kaɗai zaki samu aljannar da kowa ke fatan samu, tare kuma da tarin nasarorin rayuwa, ina fata kuma zaki ci gaba da zama me biyayya agaresa kamar yanda kike yanzu dama ko yaushe." Ɗan tsagaitawa da maganan nasa yayi, kana ahankali ya riƙo hannunta, cikin ɗan muryarsa da tayi sanyi yace. "Haƙiƙa zamuyi kewarki sosae Laylerh, saidai kuma babu yanda muka iya, domin haka rayuwa take, duk yanda aka kai ga sabo watarana dole sai anyi nesa da juna, ina miki fatan nasara agaba ɗaya rayuwarki, daga ƙarshe kuma ina me miki albishir da cewa, zaku zauna acikin gidannan keda Najeeb na ɗan wani ƙalilan ɗin lokaci, saboda bai gama kammala ginin gidan da zaku zauna ba, sannan kuma ganin da nayi cewar baki da ishashsen lafiya, yasa nayi amfani da wannan damar, ta hanyar bada umarni aka gyara muku ɗaya daga cikin extra part ɗin dake cikin gidannan, nayi hakanne kuma saboda naga rashin lafiyarki yana buƙatar kulawa sosai, bai kamata kuma ace kinyi nesa damu batare da kinji sauƙi ba, kuma kema nasan hankalinki zaifi kwanciya idan kina tare damu, saboda haka bana so na sake ganin hawaye a idanunki." Ya ƙare maganar yana me ƙoƙarin share mata hawayen dake kan fuskarta. Wanda kuma agaba ɗaya amaganganunsa babu wanda yasa taji zuciyarta ta samu nutsuwa, saima ƙara karyewa da tayi. Hakanne ko yasa ta kasa control ɗin hawayen dake cikin idanunta, yanayin yanda taji zuciyarta ta sake raunana sosae ne yasa, lokaci ɗaya taji wani irin kuka me ƙarfi yazo mata, da sauri tasa hannu ta toshe bakinta, saboda ko kaɗan batason Abbou Jaheed yaga gazawarta, kasancewar tasan kukan nata na yau, ya banbanta da na kowacce rana, domin kuka ne da sautinsa, zai iya fallasa asirin zuciyarta. Hakan yasa ta soma ƙoƙarin maida kukan ta hanyar sakin shashsheƙa. Oum Ayush da ta lura da yanayin Laylerh'n, cikin sanyin jiki ta miƙe tsaye, tare da ƙarasowa inda Laylerh'n ke zaune, ɗago ta tayi tare da miƙar da ita tsaye ta mannata ajikinta. Kamar kuwa dama jira Laylerh'n take, domin Oum Ayush na mannata da jikinta ta fashe da kuka. Ahankali Oum Ayush ta soma shafa bayanta, dan awannan karan bata da bakin da zata cewa Laylerh'n tayi shiru. Abbou Jaheed dake kallonsu, jin ƙwalla ta cika masa ido ne yasashi sauƙe kansa aƙasa, hannunsa ya tura acikin aljihun rigarsa, tare da ciro wasu ɗaurin kuɗaɗe masu yawa da kuma ɗan makullin mota. Cikin dauriya da kuma son danne zuciyarsa daga raunin da take ƙoƙarin yi, ya miƙawa Oum Ayush kuɗi da kuma key ɗin motar, cikin muryarsa da tayi sanyi sosae yace. "Sadaki da kuma makullin motar dana saya mata ne, idan kun kaita ɗakinta sai ki bata, sannan dan Allah kuyi mata duk wani abun daya dace, domin addu'ar mu ako yaushe shine, Allah Ubangiji ya basu zaman lafiya." Da "Ameen" Abbou Kareem ya amsa, wanda shima tuni idanunsa sun ciko da ƙwallan tausayin Laylerh'n, kasancewar shi tuntuni yake ganin kamar Laylerh'n bata kae ace har sun aurar da ita ba, saidai kuma akan hakan bashi da ta cewa, domin duk abun da Ɗan uwa kuma Yayansa Abbou Jaheed ya aiwatar awajensa daidai ne. Ahankali kuma cikin nutsuwa Oum Ayush ta kama hannun Laylerh'n suka fice daga cikin falon. Kaitsaye sashin Oum Ayush ɗin suka koma, inda suka samu Aunty Zee da kuma Teemah azaune. Zaunar da Laylerh'n akan gado Oum Ayush tayi, tare da ƙarasawa gaban sif ɗinta fa ciro wani tsadaddiyar atamfar vlisco wanda akayiwa ɗinkin fitted gown, miƙawa Aunty Zee atamfar tayi, cikin ɗan yanayin hanzari tace. "in 20 minute ki sake shirya Laylerh, saboda ba lokaci dare na ƙarayi." "To." Kawae Aunty Zee tace, tare da karɓan kayan, ƙarasawa wajen da Laylerh'n ke zaune tayi, anutse ta warware mayafin dake jikin Laylerh'n, miƙa mata doguwar rigar atamfar Aunty Zee tayi, babu musu kuwa ta karɓa ta saka, domin zuwa yanzu gaba ɗaya jikinta ya gamayin sanyi. Koda tasa kayan kuwa sosai rigar ta zauna ajikinta, kasancewar kuma rigar nada faɗin wuya ne yasa kusan gaba ɗaya rabin breast ɗinta bayyana. Ɗan taɓa jikinta Aunty Zee tayi, jin jikin nata akwai zafi sosai ne kuma yasa bata wani damu kanta wajen yi mata sabon meckup ba, tayi mata simple ɗaurin ɗan kwali, tare da ɗaukan wani sabon vail me kyaun gaske ta rufa mata ajikinta, har zuwa kan fuskarta, wasu turare masu daɗin ƙamshi ta turara Laylerh'n dasu, tare da ɗaukan body spray again ta shafa mata, take kuwa gaba ɗaya ɗakin ya gauraye da ƙamshi. Wasu haɗaɗɗun takalma Oum Ayush ta sa mata aƙafanta, tare da kamo hannunta ta miƙar da ita tsaye. Yanayin yanda Oum Ayush ɗin ta riƙeta ne yasa ta lafe ajikinta, anutse Oum Ayush ta soma takawa da Laylerh'n suka fice daga cikin ɗakin, yayinda Aunty Zee da kuma Teemah ke take musu baya, ahaka suka fito daga part ɗin Oum Ayush ɗin. Kaitsaye ɗaya daga cikin part ɗin dake cikin gidan suka nufa. Aunty Zee ne ta buɗe ƙofar, yayinda Oum Ayush ta cewa Laylerh'n tayi Bismillah ta shiga da ƙafar dama. Jin abun da Oum Ayush ɗin tafaɗa ne yasa Laylerh yin bismillah tare da jefa ƙafarta na dama, acikin katafaren falon da aka matuƙar ƙawatasa, duk da cewar fuskarta arufe yake da tattausan mayafi, hakan bai hana daddaɗan ƙamshin turaren dake tashi acikin falon ratsa hancinta ba. Kaitsaye Ouum Ayush dake riƙe da hannunta, ta nufi ɗakin daya kasance nanne bedroom ɗin Laylerh'n wanda aka zuba masa asalin royal bed me masifar kyau, wanda musamman akayi order'nsa daga Dubai. Akan lallausan gadon da yaji bedsheet na alfarma Oum Ayush ta zaunar da ita, tare da ƙara gyara mata rufin mayafinta. Ɗan ɗagowa Oum Ayush tayi, tare da yiwa Aunty Zee da kuma Teemah alama da idanu akan su fita daga ɗakin. Take kuwa babu musu suka fita, domin dama sun san plant ɗin da suka shirya. Ganin sun fita aɗakinne yasa Oum Ayush, dafa kafaɗan Laylerh'n wanda har yanzu fuskarta ke lulluɓe, cikin kulawa tace. "Yau Allah Yayi munkawo ki ɗakin aurenki, ina fata kuma ba zaki manta da maganganun dana faɗa miki ba, saboda ita rayuwar aure daban take." Kanta taɗan jinjina alaman "Eh." Murmushi Oum Ayush ɗin tayi, cikin kuma son tayi mata wayo tace. "Na ajiye miki saƙo akan bedside drawer, bari naje na duba yanayin tsarin falon, zan turo miki Teemah ta tayaki kwana." Batare da ta saurari abun da Laylerh'n zata faɗa ba, ta juya ta fice daga cikin ɗakin. Samun su Teemah afalo da tayi ne yasa cikin sauri tace musu "Kuzo muje, nan bada jimawa ba Najeeb zai zo." Miƙewa sukayi dukansu suka bi bayan Oum Ayush, yayinda suka bar Laylerh ita kaɗai acikin part ɗin, tana zaman jiran dawowansu. *(Am sorry yau ina cikin bad mood😡 shiasa banyi typing ɗin da tsawo ba, maybe typing errors yayi yawa.)* 11:30. am 1/19/21, 8:25 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna *Chapter 31* Ahankali ta sake gyara zama, tare da ɗan matse jikinta waje ɗaya, domin haka takejin wani irin sanyi na ratsa duk ilahirin jikinta. Kasancewar tana zaune ne atsakiyan gadon hakan yasa ta ɗan jingina bayanta, tare da lumshe gajiyayyun idanunta, hakanan takejin wani irin faɗuwar gaba tare kuma da tsinkewar zuciya na ziyartar ta, wanda kuma hakanne yasa ta ƙara takure kanta waje ɗaya, duk da cewar yanzu an kwashe sama da 20 minute da fitan Oum Ayush daga cikin ɗakin amma har yanzu bata fidda rai da zuwan Teemah ba, kamar yanda Oum Ayush ɗin ta faɗa mata cewar.  "Teemah zata zo ta tayata kwana." Idanunta wanda takejin sunyi mata nauyi ta lumshe, ahankali kuwa zanen hoton fuksarsa ya soma yi mata gizo, sanadin hakanne ko yasa take moment ɗinsu ya shiga dawowa cikin ƙwaƙwalwar ta, wanda yasa  lokaci ɗaya tasamu kanta acikin wani irin yanayi me wahalar fassaruwa, yanayin da bata taɓa jin irinsa ba, yanayin da yasa taji wani abu na musamman na yawo acikin jikinta, ba tare da ta ankara ba wani irin sahirtaccen murmushi ya bayyana akan fuskarta, hakan kuma ya faru ne saboda tuna yanda ya ɗaura bakinsa akan nata da tayi, domin kuwa sai ayanzu ne abubuwan ke dawo mata, cike da wani zazzafan shauƙi, tuna yanda sweat lips ɗinsa ke tsotsan tongue ɗinta ne, yasa komai ya sake ƙwace mata, akaron farko taji wani irin fitinannen shauƙinsa na fusgarta,  haƙiƙa moment ɗin ya kasance me matuƙar daɗi agareta, wanda za taso maimaituwarsa ako yaushe, saboda arayuwarta bata taɓajin wani abu da yakai mata saliva ɗinsa dadi da kuma garɗi ba, yanayin yanda yake goga harshensa akan nata da ta tuno ne yasa take taji gaba ɗaya tsikar jikinta ya tashi,  wanda hakan yasa taja wani irin numfashi me kama da sexual erection sound, ahankali tajawo pillown dake gefen gadon ta rungumesa ƙam. Lokaci ɗaya yanayin fuskarta ya sanja daga yanayin tausayi zuwa na zallan shagwaɓa. "Still I'am waiting for you.!"  ta faɗa cikin wata irin kasalalliar muryar dake bayyana zallan shagwaɓa, da kuma gaskiar abun dake zuciarta, duk da cewar kuwa batasan maganan nata ya fito fili ba. Sake duƙunƙune jikinta waje ɗaya tayi tare da lumshe kasalallun idanunta, wanda suka soma ɗanyi mata nauyi saboda ta ɗan fara jin bacci. Kasancewar kuma kafun yanzun taci kuka sosae ta ƙoshi ne yasa ko 10 minute bata ƙara ba bacci ɓarawo ya ɗauketa. 9:00 pm daidai haɗaɗɗiyar mota ƙiran Range Rover Maroon colour ta shigo cikin gidan, adaidai ƙaron parking space ɗin gidan motar ta faka. Almost 6 minute kafun matuƙin motar ya ya buɗe murfin motar ya fito, Sanye yake cikin wani haɗaɗɗen shadda me kyau da tsada, wanda akayi masa ɗinkin riga da wando da kuma babbar riga, kasancewar kuma kayan nada kalan shuɗi wato blue ne yasa kayan ya amshi jikinsa sosae, musamman ma haɗaɗɗiyar hulan daya kafa akansa, wanda ta ƙara ƙawata kyaun fuskarsa, yayinda kallo ɗaya zakayiwa fuskarsa, ka fahimci cewa yau ɗin yana cikin farinciki, maida murfin motar yayi ya rufe, ahankali kana kuma cikin nutsuwa ya nufi hanyar part ɗin da yasan an ajiye masa amaryarsa aciki. Koda ya ƙarasa ahankali ya tura ƙofar falon tare da tura kansa ciki, wani irin daddaɗan ƙamshin da ya daki hancinsa ne ya sashi lumshe idanunsa tare da sakin ƙaƙƙarfan ajiar zuciya, domin kuwa sosai ƙamshin turaren ya masa daɗi, buɗe idanunsa yayi tare da ƙarasowa cikin falon, ahankali ya shiga ƙarewa falon kallo, domin ba kaɗan ba yanayin yanda aka tsara falon, da kuma tsadaddun kayan da aka zuba acikinsa suka matuƙar burgesa. Bayan ya gama ƙarewa falon kallone kuma, kaitsaye ya nufi ɗaya daga cikin ƙofofin dake falon. Ahankali ya ɗaura hannunsa akan handle ɗin ƙofar tare da murɗawa ya tura ƙofar ciki. Kaman yanda daddaɗan ƙamshi ya daki hancinsa alokacin da ya shigo falon haka yanzun ma, sanyin A/C da kuma sassanyan ƙamshin turaren dake tashi acikin ɗakin ne suka shiga ratsa shi, ahankali ya maida ƙofar bedroom ɗin ya rufe, tare da juyowa ya sauƙe idanunsa akan Laylerh wanda take kwance ta duƙunƙune jikinta waje ɗaya, kallo ɗaya kuma zaka mata kafahimci cewa bawani jin daɗin kwanciyan nata take ba, kuma daga yanayin yanda ta lulluɓe kanta da mayafin dake jikinta, zaka gane cewar sosai sanyin A/C'n ke ratsa ta. Wata iriyar ajiyar zuciya me ƙarfi ya sauƙe tare da ɗan jingina bayansa ajikin ƙofa, idanunsa ya zuba mata, yayinda aransa yakejin wani irin matsanancin SO da kuma shauƙinta na ɗibansa, tabbas yasan cewa samun Laylerh amatsayin mata ga kowani ɗa Namiji babban nasara ce, wannan yasa shi yake ƙara jin wani irin sanyi na ratsa zuciyarsa, yayinda kuma agefe guda yake ƙara godewa Allah Da ya mallaka masa Laylerh alokacin da yake tsananin buƙatar ta. Ɗan nunfasawa yayi ahankali ya ƙaraso cikin ɗakin, ƙatuwar ledan dake hannunsa ya ajiye akan wani ɗan ƙaramin stool na glass wanda akayi masa surki da ado me yanayin zinare. Remote ya ɗauka ya rage gudun A/C'n ɗakin, ahankali ya ƙaraso jikin gadon, rashin sanin cewa Laylerh'n bacci takeyi ne yasa ya ƙira sunanta cikin wata sassanyar murya. Ganin shiru bata motsa bane yasa shi zama abakin gadon, ahankali ya ɗan ranƙwafa tare dasa hannunsa yaɗan buɗe mayafin da ta rufe fuskarta dashi. Tozalin da yayi da kyakkyawar innocent face ɗinta wanda ke ɗauke da bushashshen hawaye ne ya sashi sauƙe ajiyar zuciya, tare da sakin wani murmushi me ɗauke da ma'anoni daban daban, ahankali ya kai hannunsa ya shafi gefen fuskarta, cikin muryarsa da tayi sanyi sosai yace. "Laylerh rigima, ko yaushe cikin kuka." Ahankali yaɗan soma warware mayafin dake jikinta, har ya cire mata shi gaba ɗaya, idanu ya zubawa haɗaɗɗen zanen jan lallen daya ƙara ƙawata farar fatar hannunta, kana kuma ahankali ya shiga ƙarewa gaba ɗaya shigar jikinta kallo, duk da kuwa cewar akwance take amma hakan bai hanashi ganin kyawun da doguwar rigar jikin nata tayi mata ba, gajerar ajiyar zuciya ya sauƙe tare da ɗaga kansa ya kalli agogon dake manne ajikin bangon ɗakin, 9:20 pm daidai daya gani ne yasa shi ɗan matsawa kusa da Laylerh'n, ahankali yasa hannunsa ya shiga ɗan jijjigata. Laylerh kuwa tuni baccinta yayi nisa, hakanne ma yasa ko kaɗan bataji tashinta da yakeyi ba, domin tuni tayi nisa acikin mafarkin da takeyi, kasancewar kuma mafarkin Maleek takeyi ne yasa gaba ɗaya ta saki jiki, dan ba kaɗan ba mafarkin yayi mata daɗi, musamman da ta samu kanta acikin mafarkin kwance ajikin Maleek. Najeeb kuwa ganin baccin nata yayi nesa ne yasa ahankali ya kama kafaɗunta tare da ɗan juyo da ita ya zamana suna fuskantar juna. Idanunsa ne suka sauƙa akan ƙirjinta, wanda kusan rabin breast ɗinta suka bayyana ta saman rigar dake jikinta, take kuwa yaji tsikar jikinsa ya zuba, yayinda tashin farko yaji wani irin abu na yawo acikin jikinsa, domin wannan shine karo na farko daya fara ganinta ahaka, saurin ɗauke idanunsa daga kan ƙirjin nata yayi inda ya maida kallonsa ga fuskarta, idanu ya tsurawa Ć´an ƙananan jajayen laɓɓanta da yaga suna ɗan matsawa ahankali, wanda kuma da alama magana take, saidai kuma sautin maganan nata baya fitowa fili. Ahankali ya matso jikinta tare da sa kunnensa adaidai saitin bakinta tayanda zaiji abun da take cewa, sa kunnensa da yayi kuwa yayi daidai da ambatan sunan M.JAY da tayi, wanda sanadin hakan kuwa yasa take yaji ƙirjinsa ya yi wani irin bugawa, da sauri ya janye jikinsa tare da komawa ya zauna. "M.JAY." ya maimaita abun da kunnuwansa suka jiye masa, cikin wata irin murya me ɗauke da matsanancin kishi, take kuwa yaji wani abu me kama da maɗaci ya mamaye maƙoshinsa, yayinda wani yanki na zuciyarsa ke tambayarsa, kan cewar meyasa Laylerh'n ke ambatam sunan Maleek acikin baccinta? "Kenan hakan na nufin akwae wani abu azuciyarta dangane da Maleek?." Aflili yayiwa kansa tambayar da bashi da amsarta, jin zuciyarsa na neman azalzalansa da wani tunani na dabanne yasa shi rumtse idanunsa, tare da soma ambaton sunan Allah, Domin wannan ranan ta dabance awajensa, saboda haka bayaso wani abu na rashin jin daɗi ya wanzu acikin zuciyarsa. Miƙewa tsaye yayi tare da cire babbar rigar dake jikinsa, kana ahankali ya ƙarasa gaban fridge ɗin dake cikin ɗakin, goran ruwa me sanyi ya ɗauka tare da ɓalle murfin ya kafa goran abakinsa, saida yasha ruwan sosai kafun ya soma sauƙe ajiyar zuciya akai akai. Jin ya samu nutsuwa azuciyarsa ne yasa shi tuna cewar duk wunin yau ɗin Laylerh'n bataci abinci ba, kuma koda ya taɓa fuskarta yaji jikinta da zafi. Sake komawa yayi ya zauna akan gadon. Ɗan jijjigata ya somayi tare da ƙiran sunanta yanda yasan za taji sa. Kamar amafarki haka takejin tashin muryarsa acikin kunnenta, hakanne ko yasa ahankali tasoma ɗan buɗe idanunta, sauƙe idanunta akansa da tayi ne yasa azabure ta tashi zaune tare dasa hannayenta ta kare ƙirjinta. Murmushin daya bayyana haƙwaransa yayi, cikin salon tsokana yace. "Meye kike wani kakkare jiki bayan kuma tuntuni na riga da naga komai." Jin abun daya faɗa ne yasata ɗan zaro idanunta waje, cikin yanayin kasala da kuma shagwaɓan daya sauƙar mata lokaci guda ta turo ɗan ƙaramin bakinta gaba, sake matse jikinta waje ɗaya tayi, take kuwa saiga hawaye sun cika mata ido. Ganin ruwan hawaye a idanunta ne yasashi sake matsowa kusa da ita, har ya zamana jikinsu na gogan juna, ahankali yasa hannu ya dafa kafaɗanta, cikin yanayin kulawa yace. "Am sorry nabarki ke kaɗai ko ya jikin naki?." Idanunta wanda ke cike da ƙwalla ta ɗago ta kalleshi, ganin kuma shi ɗinma kallonta yake ne yasa da sauri tayi ƙasa da kanta. Sam bai damu da rashin amsawar nata ba, domin dama yasan ba lallaine ta amsa masa ba. Hannayenta wanda ta kare ƙirjinta dasu ya kalla. Hannunsa yasa daniyan kamo hannayen nata, hakan yasa da sauri ta rumtse idanunta, murmushin daya fitar da kyawun fuskarsa yayi cikin yin ƙasa da murya yace. "Kinci abinci?." Kai ta jinjina masa alaman "Eh." Saidai kuma tunowa da nasihar da Oum Ayush tayi mata ne yasa ahankali cikin muryarta da tayi sanyi sosai tace. "Naƙoshi." "Okay to tashi ki sanja kaya." Yafaɗa yana me ƙoƙarin miƙar da ita tsaye. Jin yace ta sanja kaya ne yasata ta ɗan zazzaro idanunta waje, cikin yanayin mamaki tace. "Kaya kuma?." "Eh, bakisan kwanciya da irin wannan kayan yanasa ciwon jiki ba?." Yafaɗa yana me nuna kayan jikinta, wanda ya kamata kana kuma ya bayyana shape ɗin jikinta. Baki ta buɗe daniyar cewa wani abu, amma kuma saidai tunawa da maganan Oum Ayush yasa tayi shiru, domin tace mata koda wasa kada yasata abu taƙiyi, sannan kuma kar tanayi masa musu, saboda yin hakan zai rage mata ƙima da mutumci a idanunsa. Ganin kuma bata ce masa komai bane yasashi kama hannunta, suka ƙarasa gaban makeken drawer'n dake cikin ɗakin. Buɗe murfin drawer'n yayi, take kuwa jerin sababbin kayan da Oum Ayush ta ɗinka mata suka bayyana, kayane masu yawan gaske, wanda aka jere su tsab acikin drawer'n, ɓangaren atamfofi da laces daban, haka ma ɓangaren english wears, dama dogin riguna dangin su abayas daban. Wanda wasu su Abbou Jaheed ne suka saya mata wasu kuwa daga cikin kayan aurenta suke. Kan wani sleeping dress maroon colour me adon net hannunsa ya sauƙa, hakan yasa batare da tunanin komae ba ya ciro rigar, kallon Laylerh'n yayi tare da miƙa mata rigar, da idanunsa yayi mata alama akan tasa. Gane abun da yake nufine yasa ta turo ɗan ƙaramin bakinta gaba, batare da ta sani ba abun da take faɗa azucitarta ya fito fili, inda tace. "To agabanka ne zansa!" Jin abun da ta faɗa ne ya sashi sakin murmushi, tare da kura mata idanunsa, domin ba kaɗan ba salon shagawaɓan ta ke tafiya da imaninsa, wanda idan tanayi har bayaso ta daina, saboda yanda yakejin wani irin feelings ɗinta. Laylerh kuwa ganin yana kallonta ne yasa tayi saurin juya masa baya, saboda har acikin ranta ba tason irin kallon da Najeeb ɗin keyi mata, duba da irin yanda gaba ɗaya mood ɗinsa ke sanjawa lokaci ɗaya idan yana kallon nata. 1/19/21, 8:25 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna. *(This book is mainly for that, if you know you did'nt pay, please don't read it. Here is the account number for people that are willing to pay-0002214625 Abubakar Muhammed Sardauna Jaiz Bank. Whatsapp number 07017879464.)*                            *Chapter Thirty Two* Ahankali ya sauƙe ajiyar zuciya tare da ɗan lumshe idanunsa, ganin kuma da yayi alamar cewa idan yana tsaye agabanta ba saka kayan zatayi bane ya sa shi juya mata baya, haɗe da buɗe ɗaya daga cikin site ɗin drawer'n ya ciro wani towel. Batare kuma da ya juyo ya sake kallonta ba kaitsaye ya nufi ƙofar bathroom ɗin dake cikin ɗakin. Jin alaman shigewarsa cikin toilet ne yasa ta sauƙe wani irin ajiyar zuciya, tare da ɗago rigar baccin da ya bata ta warware. Ganin rigar nada tsawo ne yasa ta ɗanji sanyi aranta, dan dama gaba ɗaya a tsorace take dashi, wannan yasa batajin zata iya zama haka agabansa daga ita sai ɗan rigar bacci. Ahankali ta soma kiciniyar zare doguwar rigar dake jikinta, bayan ta cire rigar jikin nata ne kuma ta zura rigar baccin, wanda tayi matuƙar amsar jikinta, saidai kuma yanayin yanda rigar ta lafe ajikinta ne yasa haɗaɗɗen shape ɗin jikinta bayyana, musamman ma tsararren hips ɗinta da ya ƙara cikowa, kasancewar kuma rigar nada guntun hanune yasa duk taji ta takura, sannan gefe guda kuma ga saman rigar dake a buɗe, wanda hakan yasa duk rabin breast ɗinta suka bayyana. Ganin yanda rigar yayi mata ne yasa ta shiga ƙarewa kanta kallo, don  batajin cewar zata iya zama agaban wani namiji ahaka bama Najeeb ɗinba, koda kuwa zama hakan ya kamata dole to bazata taɓa sakewa ba, buɗe murfin drawer'n tayi tare da soma baza idanunta ko zata hango Hijab ta saka, cikin sa'a kuwa idanunta suka sauƙa akan wani hijab, duk da cewar kuwa hijab ɗin bashi da girma sosae haka ta zurasa ajikinta, domin ko ba komae zai rufe mata shape ɗin jikinta da ya bayyana. Bayan ta gama sa hijab ɗinne, ta ɗago kanta ahankali ta shiga ƙarewa ɗakin kallo, wanda kallo ɗaya zakayiwa furnitures ɗin dake cikinsa, kasan ba ƙananan kuɗi aka kashe wajen sayansu ba. Sauƙe idanunta da tayi akan ɗan ƙaramin abun saka hoton da cikinsa ke ɗauke da hotonta ne yasa ta ɗan lumshe idanunta,wani abu da yazo zuciarta ne kuma yasa ta sakin murmushi, tabbas akullum akuma  koda yaushe idanunta kan yi mata gizo da kyakkyawar fuskarsa, wanda hakan yasa komai yayi take ganinsa  daban dana kowa, saboda tasa aranta cewa shiɗin na dabanne, yayinda abu mafi ɗaukar hankalinta agaresa kuwa sune kyawawan tsumammun idanunsa masu matuƙar rikita mata lissafi, uwa uba kuma daddaɗan ƙamshinsa dake bawa zuciyarta nutsuwa, tunawa kuma da yanda yau ɗin ta shaƙi ƙamshin nasa sosai ne, yasa duk taji tsikar jikinta sun soma zubawa, yayinda kuma take jikinta ya soma zama very weak. Abayyane kana kuma cikin matsanancin shauƙin daya ɗebeta tace. "No one like you Yah Maleek, saboda komae naka na dabanne, sannan kuma babu wani irinka!"  Yanayin yanda ta kare maganar cikin sanyin murya ne kuma yasa, take idanunta suka ciko da ƙwalla, domin faɗan hakan da tayi, kamar ta tsokalo  tunanin dake kwance acikin zuciyarta ne. Sau dayawan lokuta ayanzu takan tambayi kanta cewa.  "Wai dama haka so yake, ko kuwa irin nata salon son ne yazo ahaka?." Saboda yanayin yanda takejin Soyayyar Maleek ɗin acikin zuciyarta ya banbanta da komae, haƙiƙa soyayyarsa ta zamo kamar numfashi  kana kuma bugun zuciya agareta, tayi imani kuma cewa, zata iya cigaba da rayuwa ne kawae idan akwai soyayyarsa acikin ƙirjinta, akasin hakan kuwa barazana ne ga lafiya da ma rayuwarta gaba ɗaya. Najeeb kuwa ahankali ya murɗa handle ɗin ƙofar bathroom ɗin ya fito, yana fitowa kuwa idanunsa suka sauƙa akanta. Yanayin yanda ta tsaya ajikin drawer'n da kuma yanda ta lumshe idanunta ne yasashi ɗan tsayawa yana kallonta from head to toe, ganin kuma ta lulluɓe jikinta da hijab ne ya sakashi sakin ɗan guntun murmushi, ahankali ya saki ƙofar bathroom din tare da takowa zuwa gareta. Ganin da yayi har ya iso gareta bata buɗe idanunta bane, yasa ahankali yaɗan yarfa mata ruwan dake hannunsa, domin shigarsa toilet ɗin Alwala yayi. Jin sauƙan ruwa akan fuskarta ne yasata buɗe idanunta da sauri, wanda hakanne yasa ta dawowa hayyacinta, kasancewar kuma hawaye sun cika idanunta ne yasa ta kasa ɗago kae ta kalleshi, saboda awannan karon sam bataso yaga hawayenta. Saidai kuma shiɗin ma ayanzu baiwani damu da son ganin cikin idanun nata ba, ƙatuwar sallaya ya ɗauka, kana cikin yin ƙasa da murya yace. "Kije kiyi alwala kizo muyi sallah." Jin abun daya faɗa ne yasa ta ɗan saci kallonsa ta ƙasan idanunta, ba tare da ta musa masa ba kuwa ta nufi hanyar bathroom ɗin. Da kallo ya bita harta shige ciki ta turo ƙofar, wani tunani dayazo zuciyarsa ne yasashi jin wani irin tausayinta ya cika masa zuciya, take kuwa maganganun da Abbou Jaheed yayi masa suka shiga dawowa cikin kunnensa, inda yake ce masa.   "Laylerh Marainiyace bata da uwa bata da uba, ayanzu shi da yake amatsayin mijinta shi ya kamata ya zama komae nata, haƙƙinsa ne ɗauke mata duk wani damuwarta, haka kuma haƙƙinsa ne ya bata farinciki."  Murmushin daya sa kumatunsa ɗan loɓawa yayi, ahankali ya zura hannayensa acikin aljihun rigar dake jikinsa, tare da zubawa ƙofar bathroom ɗin ido yana jiran fitowarta. Ɓangaren Laylerh kuwa tana shiga cikin bathroom ɗin, hijab din dake jikinta ta cire tare da ƙarasawa gaban sink ta soma alwala, koda tazo shafar kai haka gaba ɗaya dogon gashin kanta ya baje akan fatar wuyanta, bayan ta gama alwalanne kuma ta sake maida Hijab ɗin jikinta, ahankali ta murɗa handle ɗin ƙofar bathroom ɗin ta fito. Fitowan nata kuwa yayi daidai da sauƙe idanunta akansa da tayi, cikin sauri tayi ƙasa da kanta, tare da tsayawa ta kasa ƙarasowa wajen da yake. Murmushi yayi kana ahankali ya shiga takawa zuwa gareta,  ƙamshin turarensa da taji ne yasa ta gane cewar ya iso kusa da ita.  "Nayi alwala'n." tafaɗa cikin sassanyar muryarta dake ɗauke da craking. Kansa ya jinjina tare da cewa. "To muje muyi sallah."  baijirayi komai ba ya kama hannunta suka nufi inda ya shumfuɗa musu sallaya. Saida ya daidaita tsayuwarsa akan sallayan kafun ya saki hannunta, itama ta gyara nata tsayuwar. Yanayin tsayuwar da sukayi ne yasa ya zama yana gaba ita kuma tana ɗan bayansa kaɗan. Kamar yanda yake ashari'ance shiya jasu sallah raka'a biyu. Koda suka idar da sallan juyowa yayi ya fuskanceta, ahankali yakai hannunsa ya dafa kanta, tare da karanta mata addu'o'i ya shafa mata. Tare da ɗan matsowa kusa da ita, hakanne kuma yasa suka zama suna kusa da juna sosae. Hannunsa ya ɗaura akan hannayenta da tun ɗazu take ta faman wasa dasu. "Laylerh!' Yaƙira sunanta cikin wata irin sassanyar murya, kasancewar gaba ɗaya jikinsa ya fara zama weak. Samun kanta tayi da kasa amsa masa, dan haka takejin laɓɓan bakinta sun mata nauyi. Jin kuma bata amsa masa bane yasa asanyaye ya jawota jikinsa. Hannayensa yasa ya zagayeta dasu tare da yi mata wani irin runguma, ahankali ya lumshe idanunsa, tare da sauƙe wata irin katuwar ajiyar zuciya. Laylerh kuwa kasancewar batayi tsammanin hakan daga garesa bane yasa taji ƙirjinta na wani irin bugawa,  ahankali ta soma ƙoƙarin zame jikinta daga nasa, amma saidai riƙon da yayi mata ya kasa bata daman hakan. Shikuwa Najeeb sake matseta yayi ajikinsa, anutse ya soma kokarin cire hijab ɗin dake jikinta. Ganin hakanne kuma yasa ta ƙanƙame jikinta waje ɗaya, lura da tayi cewar da gaske cire mata hijab ɗin yakeson yi ne, yasa ashagwaɓe tace. "Ni dai kabarmin hijab ɗina please!" Sauƙan sautin kasalalliyar muryarta acikin kunnuwansa ne, yasashi sake jin wani irin feeling ɗinta na sake shiga jikinsa, yatsarsa ya ɗaura akan bakinta tare da yi mata alama akan  tayi shiru. Batare kuma da ya saurari komae ba ya cire mata hijab ɗin, wanda hakan yasa take dogon gashin kanta da yasha gyara, ya samu daman sake bajewa akan wuyanta, da kuma gefen fuskarta. Jin ya cire mata hijab ɗinne yasa ta rumtse Idanunta da ƙarfi tare da ƙanƙame jikinta. Najeeb kuwa daddaɗan ƙamshin jiki da kuma na gashinta da suka bugesa ne, ya sashi lumshe idanu, tare da shaƙan wani dogon numfashi, inda take kuma daddaɗan ƙamshin nata ya ƙara masa yawan feeling ɗinta, saboda wani irin ƙamshi ne me matuƙar daɗi jikin nata ke fitarwa. Cikin kasalar da yake jin kansa aciki, yakai hannunsa ya ɗago haɓarta, idanunsa ya zubawa smalls lips ɗinta, yana mejin wani irin abu na yawo acikin jikinsa. Ahankali ya shiga matso da fuskarsa dab da nata, batare da zato ko tsammani ba ya sauƙe mata wani irin kiss adaidai kusa da bakinta, wanda yasa duk taji tsikar jikinta ya tashi, da sauri tasa hannayenta ta rufe fuskarta. Shikuwa Najeeb ganin ta rufe fuskarta ne yasashi miƙa hannunsa ya ɗauko ƙatuwar ledan daya shigo da ita ɗazu. Buɗe ledan yayi, wanda ke cike da kayan ciye ciye, ledan chocolate ɗaya ya ɗauko tare da ɓarewa, sake gyara mata zamanta ajikinsa yayi, haɗe da ɗago fuskarta yakai ɓararren chocolate ɗin bakinta, yanayin yanda taga ya tsareta da idanun sa ne, yasa cikin yanayin sanyi ta buɗe bakinta ya samata chocolate ɗin, anutse ta soma tauna choco ɗin tana ɗan lumshe idanunta, kasancewar dama ita gwanace wajen son zaƙi, ganin tana cin chocolate ɗinne yasa shi soma warware wani poil paper wanda aka zuba pepper chicken acikinsa,  again kuma wani poil paper'n ya ƙara buɗewa, wanda shi kuma cikinsa ke ɗauke da roasted fish, wanda akayiwa haɗaɗɗen sauce. "Chicken or roasted fish, wanne zakici acikinsu?."  yayi mata tambayar yana me Kallon yanda take ta mamul mamul da bakinta. "Ni chocolate kawae nakeso." Ta bashi amsa tana me kallon tarin chocolates ɗin dake zube agabansa. Kai yaɗan girgiza, dan sanin halinta ne dama yasashi sayo chocolate ɗin da yawa. "Saikinci abinci kafun na sake baki wani chocolate." Yafaɗa yana me saka hannunsa acikin pepper chicken ɗin dake gabansa, ɗauko naman kazan yayi daidai wanda zai iya shiga bakinta, ya miƙa mata, sam batajin sha'awan pepper chicken ɗin, amma jin yace bazai bata chocolate ba saitaci abinci yasa ahankali ta buɗe bakinta ya samata, tana cinyewa kuwa ya sake ƙara mata. Cikin son yi mata wayo haka ya shiga bata pepper chicken ɗin abaki, bataci wani sosae ba ta kawar da kanta gefe. Ganin ta kawar da kanta gefe ne yasashi cewa "Ƙin ƙoshi." Ya ƙare tambayan yana me juyo da fuskarta, zuwa gareshi, kai ta jinjina masa alaman "Eh." Juice ɗin exotic ya miƙo mata, babu musu kuwa ta karɓa tasha. Still ƙoƙarin sauƙa daga jikinsa ta somayi, saidai kuma yanayin riƙon da yayi mata yasa ta kasa samun daman hakan, ganin da tayi cewar bashi da alaman saketa ne yasa, ashagwaɓe tace. "Bacci nakeji." Kansa ya jinjina mata alaman yaji, ahankali ya ɗan sassauta riƙon da yayi mata, tare da ɗaukan chocolate guda ɗaya ya miƙa mata. Tana karɓan chocolate ɗin kuwa cikin sauri ta tashi daga jikinsa. Murmushi kawai yayi batare da yace da ita komai ba, ya soma cin roasted fish ɗin dake gabansa. Ita kuwa Laylerh ganin tasamu ta ƙwace kanta daga garesa ne yasa ta shiga sauƙe ajiyar zuciya, tare da ƙarasawa kan gado, aɗan baki bakin gadon ta kwanta tare da lumshe idanunta, wani irin bugawa takejin ƙirjinta nayi, yayinda wani abu me kama da faɗuwar gaba ke ƙoƙarin ruskarta, batasan me yasa ba ayanzun takejin gaba ɗaya mood dinta na sanjawa. Kana lokaci ɗaya taji bata ko ƙaunar chocolate ɗin daya bata, ƙanƙame jikinta waje ɗaya tayi tare da jan lallausan blanket ɗin dake aje kan gadon ta lulluɓe jikinta, yanayin kuma yanda ta kwanta shiru ne yasa wasu irin tunani suka shiga yawo acikin ƙwaƙwalwarta. Almost 20 minute ya ɗauka yana cin abincin, bayan yagama ne kuma ya ɗauki tissue ya goge bakinsa. Tattare wajen yayi tare da faka sauran abincin agefe. Ahankali ya miƙe tsaye tare da ɗan juyowa ya kalli, inda Laylerh'n ke kwance, yayinda ta lumshe idanunta kamar me bacci. Murmushi kawae yayi, kaitsaye kuma ya nufi toilet. Koda ya ƙarasa cikin toilet ɗin kayan jikinsa ya rage tare da sakarwa kansa ruwa. Bayan ya gama wankanne ya saka wani bathrobe ajikinsa, tare dayin brush, saida kuma ya kammala duk wani abun da zaiyi kafun ya fito daga toilet ɗin, hannunsa riƙe da towel yana goge jikinsa, kaitsaye ɓangaren sif ɗin kayansa ya nufa. Wani dogon wando da kuma button shirt marar nauyi yasa ajikinsa, kasancewar kuma dare ne yasa bai saka aninayen gaban rigar duka ba. Cool perfumed me daɗin ƙamshi ya shafa ajikinsa, tare da ƙarasawa ya rage hasken wutan dake cikin ɗakin. Ahankali ya ƙaraso ya kwanta akan gadon. Kwanciyar tasa kuwa yayi daidai da bugawar zuciyar Laylerh wanda dama duk wani motsinsa akan kunnenta yake, domin duk yanda taso bacci ya ɗauketa abun yaci tura, saima faɗuwar gaba da tsinkewar zuciyar dake ƙara ziyartarta. Najeeb kuwa ahankali ya gyara kwanciyarsa, tare da juyowa ya zamana yana fuskantar Laylerh'n wanda ta riga da ta bashi baya. Sam shikam ya kasa gane wani irin fitinannen ƙamshi Laylerh'n keyi, wanda gaba ɗaya yake sashi rasa duk wata nutsuwarsa, kasancewar har yanzu ƙamshin nata bai daina ratsa hancinsa ba, duk da kuwa cewar akwae ɗan rata atsakaninsu, amma hakan bai hanashi jiyo daddaɗan ƙamshin dake tashi ajikinta ba. Sanadin hakanne kuma yasa yakejin wani irin hot feelings dinta na damunshi. "Laylerh." Yakira sunanta cikin wata irin sillent voice ɗinsa dake bayyana irin zallar feelings ɗinta da yakeji. Laylerh kuwa Jin sauƙar muryarsa acikin kunnuwanta ne, yasa ta rumtse idanunta da ƙarfi, yayinda zuciyarta ta cigaba da wani irin bugawa, tsoron dake kwance acikin zuciyarta ne kuma ya bayyana kansa afili, wanda hakan yasa take jikinta ya soma karkarwa, kamar mejin sanyi. Sosae abun ke damun zuciarta, dan koda wasa bata taɓa kwana ɗaki ɗaya da wani namiji ba, wannan shine karonta na farko, shi yasa duk takejin kanta afirgice. Najeeb da yakai ƙololuwa wajen sha'awarta ganin bata amsa masa bane, yasa shi matsowa kusa da ita, harta kai ga ƙirjinsa na gogan bayanta, ɗan rankwafowa kanta yayi tare da sa hannu ya juyo da ita, ya zamana suna fuskantar juna. "Laylerh!!"  Akaro na biyu ya sake kiran sunanta, saidai kuma yanayin yanda taji amon muryar tasa ayanzunne yasa ahankali ta soma buɗe idanunta, take kuwa ta sauƙe ganinta acikin idanunsa wanda sukayi ja, wannan yasa ta kasa ɗauke idanunta akansa, ganin yanda gaba ɗaya mood ɗinsa ya sanja. Ahankali ya ɗan hura mata iskan dake bakinsa akan fuskarta, cikin matsanancin shauƙin daya samu kansa aciki, yasa hannunsa ya shiga shafa gefen fuskarta, ganin yanda jikinta ke rawa ne, yasashi ɗan lumshe idanunsa akasalance yace.  "Tsoro na kikeji?." Kasa amsa masa tayi, saima wasu irin sabin hawaye ne suka fito daga cikin idanunta. Yanayin yanda yayi kusa da ita ne kuma yasa numfashinsu gauraya dana juna. Ahankali bugun zuciyarta ke cigaba da tsananta, take kuwa ta soma ɗan motsa laɓɓan bakinta dake rawa, da'alama so take ta faɗi wani abu dake zuciyarta, amma yanayin yanda bakin nata ke rawa, yasa sirrin dake zuciar nata kasa bayyana. Tamkar sauƙan ruwa da ɗaukewa, haka gaba ɗaya duk wani tunaninta ya tsaya, alokacin da taji sauƙan bakin Najeeb ɗin akan wuyanta, sanadin hakan kuwa ne yasa duk wani motsi na jikinta dakatawa, harta kuwa numfashinta saida ya tafi hutun wucin gadi. Ɓangaren Najeeb kuwa daddaɗan ƙamshin dake tashi ajikinta ne yasashi ƙara shigewa jikinta, tare dayi mata wani irin hugging, cikin mahaukacin feelings ɗin daya samu kansa, ya shiga sakar mata wasu irin mahaukatan kisses awuyanta. Wanda kuma hakan yasa da ƙyar ta iya ƙwato nunfashinta dake ƙoƙarin ɗaukewa gaba ɗaya, samun kanta acikin baƙon yanayin da tayi ne yasa jikinta ya tsananta ɓari, yayinda taji kaman ana buga mata guduma atsakiyar kanta, hannayenta tasa duka biyu ta riƙe kanta da lokaci ɗaya yasoma yi mata wani irin ciwo. Najeeb kam gaba ɗaya ya soma fita hayyacinsa, saboda lokaci ɗaya ya soma ƙoƙarin manta komae, cikin kuma yanayin daya samu kansa aciki ne, ya ɓalle Ć´an ƙananan button ɗin dake jere agaban rigar baccin nata, take kuwa kyawawan breast ɗinta suka bayyana. Ganin breast ɗin nata afili ne kuma ya ƙara ruɗashi, azafafe yaci gaba da kissing ɗin wuyanta. Yanayin yanda kanta ke juyawa ne yasa ta runtse idanunta da ƙarfi, wani abune ke ƙoƙarin kutsowa cikin tunaninta, take mummunan yanayin daya rusketa abaya yashiga dawo mata, wanda har yasa taji ajikinta cewar watarana irin haka ya taɓa faruwa da ita. Ji tayi gaba ɗaya duniyar na juya mata, yayinda lokaci ɗaya idanunta suka shiga dawo mata da abubuwan da suka faru da ita ashekarun baya da suka wuce. jikintane ya cigaba da ɓari hartakai ga haƙwaranta na haɗewa waje ɗaya, take wani irin fitinannen tsoro ya shigeta, ahankali ta soma jujjuya kanta da takejin yayi mata nauyi sosae. Komae da ya wuce ne yashiga dawo mata tamkar alokacinne abubuwan ke faruwa. Bazata iya jurewa yanayin ba, domin abun yasake dawo mata, yayinda idanunta suka rikide, ba abun da suke gane mata sai lokacin da yake ƙoƙarin keta mata rigar jikinta, hakan yasa ta ƙanƙame jikinta waje ɗaya, tare da sakin wani irin kara, lokaci ɗaya ta soma kiciniyar kwace jikinta daga na Najeeb din. ƙaran da tayi ne ya dawo da Najeeb hayyacinsa cikin yanayin mamaki ya ɗago kansa ya kalleta, ganin kuma yanda jikinta ke ta ɓari ga kuma gumin dake feso mata ne yasa shi riƙeta da kyau, cikin yanayin mamakin daya shiga yashiga kiran sunanta, saboda ya lura kaman bata cikin hayyacinta. Kuka me tsanani ta fashe masa dashi tare da soma jijjiga kanta da'alama so take ta ƙwace daga riƙon da yayi mata. "Laylerh!!" Yaƙira sunanta da ƙarfi, atunaninsa ko hakan zaisa ta shiga hayyacinta, dan abu takeyi kamar wanda aljanu suka kama. Sam tayi nisan da bata jin ƙira, kasancewar gaba ɗaya ta fara fita hayyacinta, amatuƙar zauce take haɗe jikinta waje ɗaya, yayinda ta shiga rera masa kuka, tare da soma yaƙushinsa tamkar wanda ta samu gushewar hankali. Najeeb kuwa ganin yanda take yaƙushin fatarsa da kuma yanda take ƙara jan jikinta bayane yasa shi sakinta, aikuwa dama kamar jira take cikin sauri ta diro daga kan gadon, ganin haka yasa cikin sauri ya cafko hannunta. Razanannen ƙara ta saka masa tare da soma ƙoƙarin ƙwace hannunta dake cikin nasa, yanayin ruɗewan da yayi ne kuma ya sashi sakin hannun nata batare da ya shiryawa hakan ba,  baya baya ta somayi tare da haɗe hannuwanta biyu waje ɗaya alaman roƙo, matsota da yakeyi ne yasa ta soma girgiza masa kai, cikin wani irin muryar da baisanta da shiba take faɗin.  "Dan Allah ka ƙyaleni, karka cutar dani dan Allah!!!" Jin hakane yasa da sauri yakae hannu zae taɓa ta, rumtse idanunta tayi tare da soma ƙiran sunan Maleek, kafun yayi wani yunƙuri kuwa tuni ta buɗe ƙofar ɗakin ta fice aguje. Matsanancin mamaki da kuma shock ɗinta ne yasa Najeeb tsayawa kamar statue ya kasa koda motsa ƙafarsa, domin yanayin da yaga Laylerh'n ya matuƙar tsoratar dashi. Ita kuwa Laylerh cikin matsanancin kuka ta fito daga part ɗin nasu, kaitsaye babban falon gidan ta nufa, yanayin yanda take gudu tana kuka ne yasa duk wani wanda baccinsa baiyi nisa sosae ba zai iya jiyo gunjin kukan nata. Kasancewar kuma ta taho aguje ne yasa tana buga ƙofar falon, ta buɗe nan take. Atsorace take sosae, hakan yasa gaba ɗaya sautin kukanta ya cika ko ina dake cikin falon, haƙika tashiga tsoron da yasa ko ganin gabanta bata iyawa, duba da irin yanda take ganin abubuwan da suka faru da ita suna dawo mata sabi, wannan yasa ta shiga ruɗu sosae. Yanayin yanda ta shigo falon aguje ne yasa ta faɗa jikin MALEEK wanda shi kuma alokacin yake koƙarin fita daga cikin falon. Jin da tayi ta faɗa jikin mutum ne yasa ta ɗago idanunta wanda suka soma dishewa, sauƙe ganinta da tayi akansa ne kuma yasa ta rungumesa ƙam tamkar zata shige cikin jikinsa, kuka ta fashe masa dashi, ahaukace ta soma jijjigasa, bakinta ta buɗe daniyar yin magana, amma gaba ɗaya takasa, saima numfashinta dake ƙoƙarin ɗaukewa. Ganin hakane yasa shi rungumeta ƙam ajikinsa, kansa ya ɗan soma girgiza mata, kana ahankali ya tura mata Ć´ar yatsarsa cikin bakinta. Daidai lokacin kuwa Su Abbou Jaheed  wanda kukan Laylerh'n ya taso su suka karaso cikin falon, wanda kuma hakan yayi daidai da shigowar Najeeb cikin falon. *4/January/2021* 1/19/21, 8:27 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna *Note Edit* *Chapter 33* Ƙanƙame jikinsa tayi ƙam yayinda gaba ɗaya jikinta ke rawa , wanda kuma hakan yasa numfashinta soma ɗan carkewa, matsanancin kukan da takeyi ɗinne kuma ya ɗan tsagaita alokacin da ya sanya mata Ć´ar yatsarsa acikin bakinta. Maleek kuwa ganin da yayi cewa da gaske ta fita hayyacinta ne yasa shi matseta ajikinsa sosae, duk da cewar hannayenta dake kan ƙirjinsa na yaƙushin fatarsa amma sam baidamu da hakan ba, hasalima ko zafin abun da take masa ɗin baijiba. Rumtse idanunsa wanda suka kaɗa sukayi jajur yayi, wani irin tafasa yakejin zuciyarsa nayi, yayinda matsanancin tausayin Laylerh'n ke ƙara mamaye zuciyarsa, tabbas yasan me take gujewa, kana kuma me takejin tsoro, saboda ya jima yana gujewa zuwan wannan ranar, ranar da zatasa abun da ya wuce shekarun baya ya kuma dawowa cikin tunanin ta, meyasa Najeeb zai taɓa masa Laylerh'nsa har haka? idan ƙaddara batayi musu adalci ba, Najeeb baikamata yace zai kusanci masa Laylerh'n sa ba, ƙwarai ya tuna abun daya jefa Laylerh'n acikin wannan rikitaccen halin, yanayi da kuma acting ɗinta na yanzu, daidai yake da wanda tayi lokacin baya, lokacin da kwata kwata bayason tunoshi acikin gaba ɗaya tarihin rayuwarsa, domin tuna abun kansawa yaji kaman kansa zai fashe, kasancewar tuna hakan baƙinciki ɓacinrai da kuma ƙunan zuciya ne ke kewayesa. Shin meye amfaninsa idan har za'a samu wani wanda zai ɗimautar masa da Laylerh akaro na biyu, batare daya ɗau mataki ba, akaron farko wani yaso ketawa Laylerh'n tasa mutumci, gashi kuma ayanzu ma hakan naƙoƙarin faruwa, Kansa da yayi masa wani irin nauyi ya ɗan soma girgizawa, yayinda kuma idanunsa wanda sukayi jajur suka nemi ƙoƙarin tara masa ruwan hawaye acikinsu. Jin yanda numfashin Laylerh'n ke fusga da sauri sauri ne, yasa ahankali yasa hannunsa ya shiga shafa bayanta, tare da ɗan soma jijjigata ajikinsa tamkar wata ƙaramar yarinya Ć´ar shekara 3. Haƙiƙa tun tana ƙaramarta ajikin mutum ɗaya take samun nutsuwa, komin kukan da take kuwa daya ɗauketa zatayi shiru, wannan mutumin kuwa ba kowa bane face shi, daya zama tamkar shine ma rayuwarta gaba ɗaya. Aduk kuma sanda tagansa ji take kaman ta tsira daga dukkan wani abun cutarwa, ahankali tasake shigewa jikinsa, tare dasa harshenta ta kanannaɗe yatsarsa dake cikin bakinta, har zuwa yanzu jikinta ɓari yake, yayinda still kuma numfashinta ya kasa daidaita. Maleek da yaji komae na duniyar ya daina masa daɗi, baƙinciki da ƙunci sun cika zuciyarsa, jin yanda ta ƙara shige masa sosae ne yasashi ɗaura haɓarsa akan watsatstsen gashin kanta dake ta fitar da ƙamshi, tare kuma da sake rungumeta ƙam, domin ayanda yakejin zuciarsa na wani irin tafasa, da ace itadin bata jikinsa to tabbas da zai iya aikata komae, ciki kuwa harda illata Najeeb, wanda sanadinsa ne Laylerh'n ta dawo tamkar wata zautacciya. Su Abbou Jaheed da Momy haɗi da Oum Ayush kuwa da suka fito falon tuntuni, haka suka tsaya suna kallonsu tamkar wasu statue. Ciki kuwa harda Najeeb wanda shiɗinma tsayawa yayi yana kallon ikon Allah, ba abun da ya bashi mamaki kuwa kamar yanda yaga Laylerh da Maleek ɗin naƙara shigewa jikin juna. Abbou Jaheed ne yayi ƙarfin halin sauƙe ajiyar zuciya, wanda take kuma maganar da Dr.Menk ya faɗa masa shekarun baya ya shiga dawo masa, musamman cewar da Dr.Menk din  yayi. "atarana abun daya faru da ita zai iya dawowa cikin tunaninta, musamman alokacin da wani namiji ke ƙoƙarin romancing ko kuma yin sex da'ita, saboda ta tsorata sosae kuma abun ya shiga jikinta." Wani irin gauron numfashi Abbou Jaheed ɗin ya fesar, domin kuwa bama sai anyi mishi ƙarin bayani ba ya riga daya fahimci komae, saidai kuma yanayin yanda yaga Laylerh da Maleek ɗinne yasa yaji wani iri acikin zuciyarsa, duk da kuwa cewar suɗin Ć´an uwane, amma irin wannan kusancin nasu ayanzu ɗauke yake da matsala babba, domin kuwa ko ba komae ayanzu akwae aure akan Laylerh'n, wani tunani kuma dayazo zuciyarsa ne, yasa shi cikin ɗan kausasa murya yaƙira sunan Maleek ɗin da haryanzu yake riƙe da Laylerh'n. Maleek kuwa jin muryar Abbou Jaheed acikin kunnuwansa ne, yasa shi buɗe idanunsa wanda sukayi ja, yanayin yanda yaji muryar Abbou Jaheed ɗin kaɗai yasan me yake nufi, hakan yasa ahankali yasoma ƙoƙarin ɓanɓare Laylerh'n daga jikinsa, saidai kuma irin yanayin riƙon da tayi masa da ƙarfi ne yasa yakasa cireta ajikin nasa, hannayensa yasa ahankali ya tallafo fuskarta, tare da ɗan ƙura mata idanu, saboda har yanzu gata gama dawowa cikin hayyacinta ba, domin idanunta har yanzu akulle suke, still kuma lips ɗinta basu daena karkarwa ba. Da idanunsa wanda cikinsu ke ɗauke da saƙonni kala kala yake kallonta, batare da yayi tsammani ko shiryawa ba kuwa, idanun nasa suka faɗa kan ƙirjinta, da kudan gaba ɗaya rabin breast ɗinta suka bayyana tasaman wuyan rigarta da buttun ɗinta ke watse. Wani irin abu da yaji ne yasashi runtse idanunsa da karfi, tare da sa hannu ya dafe daidai saitin zuciyarsa, wanda lokaci ɗaya ta shiga wani irin dokawa, da ƙyar ya fusgo numfashinsa dake ƙoƙarin ƙwacewa, haƙiƙa ganin breast ɗinnata da yayi ya matuƙar sashi a shock saidai kuma, tuno da cewar Najeeb ya kalleta ahaka kamar yanda shima ya kalleta ne yasa shi jin wani ɗaci tare da ƙuna aransa, saboda sosae yake matuƙar kishin Laylerh'n. Idanunsa yaɗan lumshe tare da soma kokuwa da zuciarsa wanda ke ƙara hasalasa, domin tabbas yasan idan ya biyewa fushin da zuciarsa ke ciki, to duk abunda zaiyi bazai zamo me kyau ba. Yanayin kuma yanda yaji ƙuna acikin zuciarsa ne yasa take yaji har ita Laylerh'n ya soma jin haushinta, hakanan idanunsa suka rufe yake ganin kamar komae ma dake faruwa da saninta. Ayanayin yanda yakejin ƙuna acikin zuciarsa ne yasa shi, sanya hannayensa duka biyu ya tureta daga jikinsa, tare kuma da saurin miƙewa tsaye. Laylerh kuwa da jikinsa ya zame mata mafaka, jin ya tureta gefe ne yasa, ta riƙo ƙafafunsa ta rungume, tare da sakin sabon kuka, saboda sam batason yayi nesa da ita, dan zamansa akusa da ita ɗin, yasa taji cewar ta samu mafaka, domin tayi imani cewa matuƙar yana kusa da ita, bazai taɓa bari wani abu ya cutar da ita ba, kamar yana kuwa ya ceceta alokacin baya, haka take saran cewa ayanzuma zai taimaketa, dan gani take kamar Najeeb cutar da rayuwarta zaiyi. Tabbas aduniyar nan zai iya jurewa komae amma kuma banda sauƙan sautin kukanta acikin kunnuwansa, domin sukan karyar masa da zuciya, sannan sukansa ka rauninsa bayyana, wannan yasa ko kaɗan bayason kukanta, domin yakanji kaman narkakken dalma ne ake ɗiga masa akan zuciyarsa. Kowa ya sani har akullum baya iya jurewa jin sautin kukanta, to hakama ayanzun bayajin zai iya jurewa, rumtse jajayen idanunsa yayi, cikin dauriya da son karfafawa kansa guiwa ya janye ƙafansa daga riƙon da tayi masa, batare daya tsaya sauraran komae ya nufi ƙofar fita daga cikin falon. Najeeb kuwa ganin yanda Maleek ɗin ya taho tamkar wanda baya hayyacinsa ne yasashi ɗan matsa masa daga bakin ƙofar, amma kuma duk da haka da Maleek ɗin yazo wucewa saida shoulders ɗinsu suka gogi juna. Jin irin karfin bugun da shoulder ɗin Maleek ɗin yayiwa kafaɗansa ne yasashi juyawa yabi bayan Maleek din da kallo. Ahankali ya zura hannayensa acikn aljihun wandon dake jikinsa, tare da fesar da wani irin numfashi. Ƙwarae yaji zafin abun da Maleek din yayi masa, saidai kuma amma yabarsa amatsayin bashi wanda zai rama anan kusa, wani irin murmushi yayi tare da jingina bayansa da jikin bango, ahankali ya dawo da kallonsa ga Laylerh wacce ke durƙushe jikinta sai faman ɓari yake, tamkar wanda aka watsawa ruwan sanyi. Oum Ayush da gaba ɗaya lamarin ya rikitata sai ayanzu ta samu bakin ƙiran sunan Laylerh'n, tare da ƙarasowa ta dafa kafaɗanta. "Lafiyanki ƙalau kuwa Laylerh me yake damunki ne, kibar kuka, ki natsu kiyi mana bayani." Oum Ayush tafaɗa tana me ɗan jijjiga Laylerh'n. Faɗawa jikin Oum Ayush ɗin tayi ta rungumeta ƙam, tare da ɗan soma girgiza kanta, cikin muryarta me ɗauke da yanayin kuka, kana kuma yake bayyana zallan abun dake cikin zuciyarta tace. "Help me Oum Ayush tsoro nakeji sosae, dan Allah Kice masa ya ƙyaleni, kada ya cutarmin da rayuwata please!!!" alokacin da ta kai ƙarshen maganan nata kuka take sosae, tare da haɗe hannuwanta biyu waje ɗaya alaman roko. Gane abun da take nufi ne yasa cike da tsauyawa Oum Ayush ta rungumeta, ahankali taɗan soma shafa mata bayanta, cikin kulawa da kuma son sama mata nutsuwa tace. "Please Laylerh kidaina kuka kinji, Najeeb Mijinki ne bakuma zai taɓa cutar dake ba, sannan gani akusa dake, ga kuma su Abbou Jaheed duk bazamu bari wani abu ya taɓaki ba, please control your self!" Duk da kuwa cewar bata cikin nutsuwarta sosae, amma taɗanji zuciarta ta samu nutsuwa dajin kalaman Oum Ayush ɗin. Ganin ta ɗan sassauta kukan da takeyi dinne kuma yasa Oum Ayush kamo hannunta ta zaunar da ita akan ɗaya daga cikin kujerun falon, ɗago da kanta Oum Ayush ɗin tayi tare dayiwa Najeeb dake tsaye alama akan ya bata ruwa. Gane abun da take nufine yasa anutse Najeeb ya ƙarasa wajen fridgen dake cikin ɗakin, buɗewa murfin fridge ɗin yayi tare da ɗauko bottle water me ɗan sanyi kaɗan. Zagayowa ta bayan Laylerh'n yayi yanda bazata gansa ba, ya miƙawa Oum Ayush bottle water'n. Karɓan goran ruwan tayi tare da buɗe murfin, addu'a ta karanta abakinta tare da ɗan tofawa acikin ruwan, miƙawa Laylerh'n goran ruwan tayi, cike da kulawa tace. "Karɓa ruwa kisha." Kamar kuwa dama jira take, har hannunta na rawa wajen karɓan goran ruwan takae bakinta. Alokacin da ruwan ya shiga maƙoshinta kuwa idanunta ta lumshe tare da sauƙe ajiyar zuciya, sosae tasha ruwan har fiye da rabin goran, kafun ahankali ta janye goran daga bakinta, idanunta ta lumshe ahankali ta maida kanta jikin Oum Ayush. Cikin abun da bae wuce mintuna kaɗan ba kuwa taji wani irin nutsuwa da kuma bacci na zuwar mata, hakanne kuma yasa tasake lafewa ajikin Oum Ayush ɗin. Abbou Jaheed da gaba ɗaya tausayinta ya cika masa zuciya, ƙarasowa wajen yayi tare dasa hannu ya shafa kanta, cikin kulawa yace. "Laylerh are you okay?." Jin muryar Abbou Jaheed ɗinne yasata buɗe idanunta, ahankali cikin muryarta da tayi sanyi sosae tace. "Am okay." Murmushi Abbou Jaheed din yayi, tare da dafa kafaɗanta, cike da jin daɗin dawowa hayyacinta da tayi yace. "Good girl, kije ki kwanta kiyi bacci kinji, namiki alƙawarin babu abun da zae sameki." Kanta ta jinjinawa Abbou Jaheed ɗin alaman to, domin dama ko bai faɗa ba, bacci ya fara zuwar mata. Ganin kuma ta samu nutsuwa ne yasa Abbou Jaheed din juyawa ya koma ɗakinsa, domin sanin haƙiƙanin abun dake faruwa da Laylerh'n yasa samma babu amfanin tsayawa wani dogon magana. Kallon babban agogon dake cikin falon Oum Ayush tayi, ganin ƙarfe shabiu harda rabi da tayi ne yasa ta miƙewa tsaye, shafa kan Laylerh'n tayi, cikin kulawa tace. "Kije ki kwanta kinji." Batare da ta jira me Laylerh'n zatace ba kuwa ta juya ta shiga ɗaya daga cikin ɗakunan dake cikin falon. Ganin kuma duk sun watse ne yasa ahankali ta miƙe tsaye, juyowan da zatayi ne kuma idanunta suka sauƙa akan Najeeb dake tsaye ya harɗe hannayensa akan ƙirjinsa, wanda kuma shiɗin ma kallonta yake, haɗa idanun da sukayi ne yasashi sakar mata murmushi, tare da buɗe mata hannayensa alaman tazo garesa. Babu musu ko tunanin wani abu ahankali kuwa ta shiga takowa inda yake. *5/January/2021* 1/19/21, 8:28 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Chapter 34* Ahankali ta shiga takawa zuwa inda yake, yayinda takejin zuciyarta nayi mata wani iri, domin kuwa duk da cewar bata wani cikin nutsuwarta sosae, abun da Maleek ɗin yayi mata, yasa duk taji jikinta yayi sanyi, yayinda kuma gaba ɗaya rauni ya lulluɓe ta, domin zuwanta garesa da farko yasa taji cewar ta samu mafaka, saidai kuma turetan da yayi daga jikinnasa, ya ɓata Duk wani tunaninta, yayinda ya haifarmata da karyewar zuciya. Hakanne kuma ya ƙara sa mata tausayin kanta sosae. Isowarta kusa da Najeeb ɗinne yasa ta lumshe idanunta, dake cike da ruwan hawaye, yayinda ƙiris take jira da za taga Maleek ɗin to da ta fashe masa da kuka, ta yanda zai fahimci abun dake cikin zuciarta. Sannan duk da cewar har yanzu tanajin tsoro da kuma fargaba acikin rai da zuciarta, saedae ba tajin cewa ayanxu akwae wani wanda zai rarrasheta sama da Najeeb din, domin shi kaɗai ne yake tare da ita ayanzu. Ganin ta iso kusa dashi ne, yasa ahankali ta tsaya da tafiyan da takeyi ɗin, saboda batajin zata iya shiga jikinsa kai tsaye, kamar yanda ya buƙata. Najeeb kuwa murmushi ya kuma sakewa akaro na barkatai, saboda sam baidamu da rashin shigowa jikin nasa da Laylerh'n batayi ba, domin dama yasan cewa ba lallaine tazo gareshi ba. Ahankali yaɗan matso kusa da ita, haɗe da miƙa mata hannunsa, cikin muryarsa da tayi sanyi sosae yace. "Trust to me Laylerh bazan cutar dake ba, i promise you, idan bakyaso na taɓaki, bazan sake taɓa ki ba, am sorry nasaki kuka." yakare maganar yana me haɗe hannayensa alaman ban haƙuri. Jin abun daya faɗane yasa ta buɗe idanunta dake alumshe, ahankali ta sauƙe ganinta akan fuskarsa, murmushin da ta gani, kwance akan fuskar nasa ne kuma yasa duk taji zuciyarta ta karye, take duk saitaji tausayinsa ya kamata, musamman yanayin yanda taga fuskarsa awadace da murmushi, yayi kaman baidamu da abun daya faru ɗin ba, wanda kuma tasan dole ne zaiji ba daɗi acikin ransa. Haƙiƙa dayawan lukuta takan tambayan kanta, dangane da soyayyar da Najeeb ɗin keyi mata, saboda tun bata fahimtar kalan soyayyar tasa, harta fara fahimta, wanda kuma saudayawa takanji ajikinta cewa badon soyayyar Maleek da ya cika zuciyarta ba, tabbas da ta amincewa rayuwa da Najeeb, saboda ko kaɗan bashi da makusa, daga kan tsarin halittarsa har zuwa kyawun fuskarsa, komae nasa me kyaune daidai da tsarin da Allah Yayi masa. Tabbas tausayinsa yayi tasiri acikin zuciarta, hakanne kuma yasa taji cewa ayanzu'n bazata iya ƙin amsa tayinsa ba. Asanyaye ta ɗaura hannunta akan tafin hannunsa da yake miƙo mata. Sauƙan taushi da kuma lallausar fatar hannunta acikin nasane ya sashi lumshe idanunsa, tare da riƙe hannun nata ƙam. Murmushi ya ɗanyi, tare da juyawa yana me riƙe da hannunta, suka nufi hanyar fita daga cikin falon. Ganin kuma yanda gaba ɗaya jikinta ke asanyaye ne yasa shi tafiya ahankali, saboda har yanzu hannunta na cikin nashi. Kaitsaye part ɗin da aka ware musu na musamman suka nufa, isarsu ƙofar dazai sadasu da falon nasu ne yasa shi sake mata hannu, tare da buɗe musu ƙofar falon suka shiga, maida ƙofar yayi ya rufe haɗe da murza mata key. Lura kuma da rofe ƙofar da yayinne kuwa yasa ƙirjin Laylerh soma wani irin bugawa, aɗan tsorace ta ɗago kai ta kalleshi. Shiɗinma kallonta yayi, saidai kuma gane ta tsorata ne yasashi ɗan girgiza mata kai, tare da kamo hannunta, batare daya ce da ita ƙalaba, ya nufi hanyar bedroom ɗin dake cikin falon, yayinda ahankali yake ɗan murza hannunta dake cikin nasa. Acan ɓangaren Maleek kuwa tun barinsa falon, ransa amatuƙar ɓace ya fito compound ɗin gidan, saboda tsabar ƙunan da zuciyarsa keyi masa ne, yasa ko iya ganin gabansa da kyau bayayi, kaitsaye wajen da yake parking cars ɗinsa ya nufa. Kasancewar kuma lokacin dare yayi ne yasa kosu Abdoul babu awajen duk suntafi sun kwanta. Hannunsa yasa acikin aljihun wandonsa ya laluɓo key ɗin wata baƙar mota benz, batare da tunanin komae ba ya buɗe murfin motar ya shiga, cikin sauri yayi mata key, haɗe dayin reverse ya fito daga cikin parking space din, ƙarasowansa bakin makeken gate ɗin gidan dake akulle ne, yasa shi soma danna wani irin mahaukacin horn, wanda yasa gateman ɗin dake onduty wanda tuni ya fara bacci, ya taso ahanzarce, ɗan leƙowa gateman ɗin yayi, ganin Oga Maleek ne da kansa, yasa ahanzarce megadin ya wangale masa gate ɗin, kamar kuwa wanda zai tashi sama haka ya cilla hancin motar tasa waje. Gudu sosae yake shararawa akan titi, yayinda yakejin kansa nayi masa wani irin sarawa, zuciyarsa kuwa tamkar wanda aka kunna wuta acikinta haka yakeji. Komae bayayi masa daɗi, hoton surar ƙirjin Laylerh'n ne ya faɗo cikin idanunsa, sanadin hakan kuwa yasa saura kaɗan steering motar ta ƙwace masa, saboda yanda yaji wani irin abu ya ratsa har cikin tafin ƙafarsa. Tabbas akowacce rana idan ya tuna da yanda ya iske wani banzan bature na shirin yiwa Laylerh nasa fyaɗe yakanji kaman kansa zai tarwatse, yayinda baƙinciki da ɓacin rai ke cika masa zuciya, tabbas har yanzu baya iya manta wannan banzan moment ɗin, idanunsa kan yawan yi masa imagine lokacin da Laylerh'n ke kuka tana ƙiran sunansa, sautin kukanta da har yau yakasa gogewa daga cikin kunnuwansa, kamar yanda tunanin abun ya kasa fita daga cikin mind ɗinsa, tuno wa da yanda idanunsa suka haska masa, lokacin da baturen ke ƙoƙarin yagawa Laylerh'n rigar jikinta da yayi ne yasa shi, kaiwa steering motar tasa wani irin bugu, wanda hakan yajawo har saeda motar tasa ta karkace daga hanya, ganin hakane kuma ya sashi taka wani irin birki, haɗe da kashe motar ma baki ɗaya. Hannayensa duka biyu yasanya ya dafe kansa dake ciwo, kana cikin wata irin muryarsa dake fidda gurɓataccen amo asanyaye yace. "Why Lyalerh? Why zaki bari wani nadaban ya taɓa jikinki? sure da ace irin haka bai taɓa faruwa dake ba, da shikenan Najeeb zaiyi duk abun da yakeso dake, sannan da ya samu chance ɗin da any how zaiyita yunƙurin taɓaki, hakan kuma damace agaresa da zai lalataki dason sanin Namiji." Shiru yayi tare da rumtse Idanunsa da ƙarfi, still cikin ƙunan da zuciyarsa keyi yace. "Bazae taɓa yiwuwa ba, naji na amince akaron farko na zama loser, saboda rashin sa'a na kinyi nesa dani, Nayarda cewa Najeeb shine Mijinki, amma hakan bawae yana nufin cewar, shine mamallakin jiki da kuma virgin ɗinki ba, tabbas bazan taɓa bari haka takasance ba, sam bazan taɓa bari wani Namiji na daban ya shiga jikinki har yasan testing ɗinki ba, domin haƙiƙa zan iya jure komae amma banda hakan, bazan juri hakan ba Ayshnoor bazan iya jurewa ba sam......" Yafaɗa cikin ƙaraji, tare kuma da da katawa da maganan nasa da yakeyi da kansa shi kaɗai, ahankali yazaro wayarsa dake cikin aljihun wandonsa. madannin kunna wayar ya danna, take kuwa screen ɗin wayar ya kawo haske, bawani ɓata lokaci ya shiga gurin saka password ɗin wayar, tare da rubuta haruffan L.A.Y.L.E.R.H, yana gama rubutawa kuwa wayartasa ta buɗe. Direct image ɗinsa ya shiga, hoton farko da idanunsa suka fara sauƙa akansa kuwa bana kowa bane face, hoton Laylerh'n daya ɗauka batare da saninta ba. Wanda take zaune akan dining table taɗan ɗaga kanta kaɗan, inda ya kuma ɗauki hoton ne daidai lokacin da ake ta shirye shiryen bikin nata. Idanu ya zubawa hoton tare dakai hannunsa daidai saitin ɗan ƙaramin bakinta. Akankali ya shiga yawo da Ć´ar yatsarsa adaidai saitin bakin nata, cikin muryarsa wacce ta zama slowly lokaci ɗaya yace. "Am sorry Ayshnoor, am really sorry, . I don't mean to hurt you, is just that i can't control my self, so am very sorry Mah Noor...." Yafaɗa yana me shafa fuskarta dake mamaye akan screen ɗin wayar, saboda haka yakejin tamkar Laylerh'nce akusa dashi. Ahankali ya ɗaura wayartasa akan ƙirjinsa, tare da sa hannunsa ɗaya ya tada motar tasa dake fake agefen titi, cikin yanayin sanyin daya samu kansa aciki, ya cilla motar tasa kan titi, zuciyarsa cike da saƙe saƙe kala kala haka yake tuƙa motar, yayinda kuma tafiya kawaw yake batare dayasan inda zaije ba. Ɓangaren Laylerh kuwa duk yanda ƙirjinta ke bugawa, da kuma yanayin yanda bugun zuciarta ke tafiya da sauri sauri, haka ta daure, duk da kasancewar tanajin tsoro, saidai kuma taɗanji sauƙi ba kaman mood ɗin da tasamu kanta ɗazu aciki ba. Shigowarsu cikin bedroom ɗinne kuma yasa ta rumtse idanunta. Najeeb kuwa dake riƙe da ita, jin yanda hannunta dake cikin nasa ke rawa ne yasashi tsayawa tare da juyowa ya kalleta, yanayinta kaɗai ya kalla kafahimci cewa amatuƙar tsorace take, hakan kuwa yasa ahankali yaɗan saussauta riƙon da yayiwa hannun nata, anutse yakai hannunsa ɗaya ya shafi gefen fuskarta, cikin yin ƙasa da murya yace. "Again har yanzu, duk da na miki promise tsorona kikeji?." Shiru tayi tare da kasa amsa masa tambayar nasa, domin aganinta babu amfanin mayar masa da amsan abun daya riga ya sani, saboda tsoron nasa abune dake bayyane akan fuskarta, wannan kuwa yasa, koda zata faɗi wani abu, to baiwuce ƙarya zatayi masa ba, ahaƙiƙanin gaskia kuma sam ayanzu batason yi masa ƙarya shiyasa kawae tayi shiru. Ganin da yayi tayi shiru ne yasa shi jan hannunta suka ƙarasa bakin gadon dake cikin ɗakin, da kansa yasa hannayensa ya riƙe shoulder'nta, tare dayi mata nuni da hannunsa alaman cewa ta kwanta. Gane abun da yake nufi ne kuma yasa ahankali ta ɗago ɗaraɗaran idanunta tare dayi masa wani irin kallo me ɗauke da ma'anoni daban daban. Sarae yasan abun da take rayawa azuciyarta, hakan yasa ya jinjina mata kai. Asanyaye ta zare hannunta dake cikin nasa, cikin yanayin sanyi ta haye saman gadon, anan baki baki ta kwanta, kamar dae yanda tayi ɗazu. Najeeb kuwa ganin ta kwanta ɗin ne yasashi ɗan numfasawa tare da komawa kan wata haɗaɗɗiyar kujeran dake cikin ɗakin ya zauna, hannayensa yasa ya tallafi haɓansa, tare da tsurawa Laylerh'n dake kwance idanu, abubuwa da yawane ke yawo aransa dangane da ita, yayinda kuma har yanzu jarababben feelings ɗinta ya kasa sakeshi, saboda tsabar bala'ima har ji yake mararsa na murɗawa, shikansa baesan cewa ƙarfin sha'awar da yakeyiwa Laylerh'n takai haka ba sae yau, da yaga samu ya ga rashi nan take, abun da yake tambayar kansa ayanzu kuwa shine. "Shin haka zai zauna da Laylerh'n batare da ya shayar da ita dadi, da kuma ɗanɗanon dake cikin aure ba?." Tabbas abun ya tsaya masa arai, saboda Allah Yasani amatuƙar buƙace yake da Laylerh'n, dan ko ada duk lokacin da ya kalleta, sai yaji wani irin hot feelings ɗinta na sukarsa, burinsa ako da yaushe shine ta zamo mallakinsa, tayanda zai kashe duk wani sha'awarta da yakeji, wanda akusan kullum take hanasa sukuni, amma kuma sai gashi ya kasa samun daman hakan. Ahankali ya fesar da wani irin numfashi me zafi, tare da sa duka tafukan hannayensa ya rufe fuskarsa, da kuma idanunsa wanda sukayi jajur. Laylerh kuwa da tun ɗazun take kallonsa, ganin ya rufe fuskarsa ne yasa ta lumshe idanunta, wanda suke fitar da hawaye. Ƙaƙƙarfan numfashi taja, yayinda awani sashe na zuciyarta, takejin tausayin Najeeb ɗin ya lulluɓeta, domin duk da kasancewarta yarinya, hakan bai hanata sanin cewar ga kowanni Ango da Amarya ranar farkonsu, ranar farinciki ce agaresu ba, amma awajensu su ba hakan bane. Sannan tambaya ɗaya da ta fara yiwa kanta shi ne. "Meyasa Ƙaddara ke wujijjiga rayuwarsu?." Haƙiƙa dukansu suna buƙatar canjin rayuwa, ba itaba ba Maleek ba har ma Najeeb ɗin kansa, domin kwata kwata ita tasan bata dace dashi ba, dan ba irinta wanda zuciyarta tayi nisa acikin son wani ya kamata ya samu amatsayin mata ba, me ƙaunarsa ya kamata ya samu. Ɗanjim tayi kana kuma acikin ranta take faɗin. Inama da ace kowa zai gane cewa Maleek shine zaɓin zuciyarta, mafarkinta, da kuma muradinta, inama da ace agogon ƙaddaranta zai juya ta hanyar kusanta ta da MALEEK, saboda shine ya kasance mafarkinta akullum. Babban abun dake damunta kuwa shine, tayaya zata fara koyawa zuciyarta zama batare da shi ba? Tayaya zata koyawa kanta soyayyar Najeeb, wanda acikin kaso ɗari na zuciyarta, batajinsa acikin kashi biyar, kana tausayi da kuma feeling ɗin da takeji akan Maleek sam batajinsa akan Najeeb, ƙwarai tasan akwae banbanci atsakaninsu. Idan tace banbanci kuma, to tana nufin tazara me nisa. *6/January/2021* 1/19/21, 8:28 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna *(This book is mainly for that, if you know you did'nt pay, please don't read it. Here is the account number for people that are willing to pay-0002214625 Abubakar Muhammed Sardauna Jaiz Bank. Whatsapp number 07017879464.)* *(Note Edit)* *Chapter 35* Ajiyar zuciya ta kuma sauƙe akaro na barkatae, tare da sake matse jikinta waje ɗaya, haƙiƙa awani ɓangare na sashin zuciyarta tausayin Najeeb ɗinne yayi kwance, wanda har hakan yasa takejin kamar akwai wani abu na rashin kyautawa da tayi masa, saidai kuma bata da wani zaɓi wanda ya wuce ta ƙyalesa, duk da kuwa ta lura da cewar yana cikin damuwa. Ahankali kuma cikin yanayin sanyi takae hannu ta share hawayen dake tsiyaya ta gefen fuskarta, jin brain ɗinta na ƙoƙarin tuna mata kalaman da Oum Ayush ta faɗa mata ne yasa ahankali takai hannayenta ta toshe kunnuwanta, saboda tuna maganganun Oum Ayush ɗin zai ci gaba da sawa taji kaman bata aekata daedae ba, wannan yasa ta soma ƙoƙarin nutsar da kanta yanda bacci zai ɗauketa, kasancewar tun ɗazu takejin baccin, amma kwata kwata rashin samun gamsashshiyar nutsuwa ya hanata. Najeeb, Kusan mintuna 15 ya ɗauka yana zaune akan kujeran, yayinda kuma har yanzu tafukan hannunsa ke kan fuskarsa, tunani daban daban ne ke yawo acikin ƙwaƙwalwarsa,yayinda wani tunanin yake kasancewa me daɗi, wani kuma akasin haka. Ahankali ya fesar da wani numfashi me zafi ta bakinsa, haɗe da janye hannayensa dake kan fuskarsa, wata gauruwar ajiyar zuciya ya sauƙe, kana ya kuma sauƙe ganinsa akan Laylerh'n. Kallon agogon dake maƙale aɗakin yayi. Ƙarfe ɗaya 1:00 am dai dai ya gani, aransa da kuma zuciyarsa yace. "Sabuwar ƙaddara da kuma sabuwar rayuwa." Sake dawo da kallonsa ga inda Laylerh'n ke kwance yayi, wanda zuwa yanzu yasan ta riga da tayi bacci, sannna kuma har yanzu sosae yakejin feelings ɗinta na ratsashi, musamman ma idan ya tuna da yanda ɗazun ya sauƙe lips ɗinsa akan soft skin ɗinta, me tsananin taushi da ƙamshi, haka yakejin tsikar jikinsa na zubawa, gefe guda kuwa ga mararsa dake ta faman murɗawa, saidai kuma sanin kansane babu yanda zaiyi dole haka zaiyi haƙuri ya ƙyaleta, saboda baisan me zai faru anan gaba, idan ya sake taɓata ba. Ahankali ya miƙe tsaye daga zaunen da yake, cikin yanayin dake bayyana cewar gaba ɗaya jikinsa ya gamayin sanyi, ya ƙarasa gaban gadon da Laylerh'n ke kwance. Ɗan sunkuyawa yayi ya leƙa fuskar Laylerh'n wanda ke ɗauke da danshin hawaye. Murmushin daya ɗan bayyana ɓoyyayen dimples dinsa yayi, ahankali yakai hannunsa kan fuskarta, tare dasa Ć´ar yatsarsa ya lakato hawayen dake maƙale agefen idanunta. "Wataƙila kuka baya bata wahala." Yafaɗi hakan azuciyarsa yana me shafa gefen fuskarta, wanda sili silin dogon gashinta suka kwanta awajen. Jawo blanket ɗin yayi ya rufa mata da kyau, tare da zagayawa ahankali ya hau kan gadon, gudun kuma kada ya tasheta abaccin da takeyi ɗinne yasa shi yin komansa ahankali, inda yaja blanket ɗin shima ya rufe rabin jikinsa, yanayin yanda ya kwanta ɗinne yasa yana iya kallon bayanta, da kuma dogon gashinta da ya watse akan pillow. Idanunsa wanda sukayi ja ya lumshe tare da shaƙan wani sassanyan numfashi, me ɗauke da fitinannen ƙamshin dake fita ajikin Laylerh'n, jin ƙamshin na ratsa hancinsa ne yasashi buɗe idanunsa ya tsurawa bayanta ido, take kuwa yaji wani irin sabon sha'awarta na sake shiga jikinsa, yayinda yake jin kamar ya juyo da ita ya haɗe bakinsu waje ɗaya, ko hakan zaisa yaji sassauci na daga abun da yakeji. Ahankali yaɗan matso da jikinsa kusa da ita, saidai kuma hakan baisa ya zama suna kusanci da juna ba, saboda tsakaninsu akwae ɗan tazara kaɗan, alokacin da ƙamshin nata ya ci gaba da shiga hancinsa kuwa, lumshe idanunsa yayi tare da sakin wani irin numfashi me kama da nishi, asanyaye yasa hannunsa ya dafe mararsa da yakejin tanayi masa ciwo, haƙiƙa shi kansa baisan cewa ƙarfin sha'awan Laylerh'n da yakeyi yakai haka ba sae yau, dayake ganinta gashi gata, aɗaki ɗaya, kuma agado ɗaya, saidai kuma babu yanda za'ayi ya kawar da duk wata damuwar da ta dameshi ayau ɗin, duba da irin halin da Laylerh'n ke ciki, idan kuma har bazai tauyawa mata ayau ɗin ba, to haƙiƙa baicika masoyin gaskiya ba, duk da kuwa cewar yana matuƙar buƙatarta, akuma yanda yakejin kansa ayanzu, nutsuwa kawae yakeson samu daga gareta, tabbas da ace taɓata bazai zamo masa wani sabon case ba, to daya shiga jikinta yayi romancing ɗinta ko zaiji nutsuwar da zata sa ya iyayin bacci, saboda Allah Ma ya gani amatuƙar matse yake, ayanzu kuwa sosae yake buƙatar mace akusa dashi. Sake dafe mararsa yayi da ƙarfi, saboda yanda yaji ta murɗa masa, tare kuma da rumtse idanunsa, ahankali ya sake matso da jikinsa kusa da Laylerh'n, tare da cusa fuskarsa acikin bajajjen gashin kanta dake fitar da ƙamshi, kasancewar turarukan gashi na musamman Oum Ayush ke bata tana shafawa. Ahankali ya sake gyara kwanciyarsa, tare da ƙara kusanta gansa da ita, saidai kuma duk da haka baiyi yunƙurin taɓa jikinta ba, saboda yasan abu kiris ne zai iya tada ta daga baccin da takeyi. Idanunsa ya lumshe, tare da sake dafe mararsa, ahankali yake fitar da wani irin numfashi, domin tabbas awannan lokacin shi kaɗai yasan me yakeji. Duk abun da yakeyi ɗin tanajinsa, saboda dama baccin nata bawae yayi wani nisa bane, tun hawansa kan gadon kuwa ta ɗan buɗe idanunta, saidai kasancewar bataso yagane cewar ta farka ɗinne yasa ta maeda idanunta ta rufe, tare da ƙinyin kyakykyawan motsi, duk da cewar kuwa hawansa kan gadon yasa taji faɗuwar gaba, saedae bisa dole ta daurewa duk wani fargaba da tsoronta, dan tayi imani awannan karon idan wancan mood ɗin ya dawo mata babu wani me cetonta,, jin kuma yanda ya matso bayanta ne yasa ta, soma ambaton sunan Allah acikin rae da zuciyarta, tare dayin fatan Allah Yasa bacci yakuma sake ɗaukarta, cikin ikon Allah kuwa ko 5 minute ba'ayi bacci me ɗan ƙarfi ya ɗauketa. Ɓangaren Najeeb ɗinma dae rufe idanunsa yayi, tare da yiwa kansa fatan bacci, saboda ya tabbatar cewa nan da mintuna kaɗan idan bacci bae ɗaukesa ba komae zai iya faruwa, domin feelings ɗin nasa ƙara hawa yake, wanda kuma zuwa nanda Ć´an mintuna kaɗan yasan bazae taɓa iya control ɗin kansa ba. Jin kuma yanda sautin numfashin Laylerh'n ke fita ne ya sashi gane cewar baccinta ya ɗan soma nisa, wannan dalilin ya sashi sake matsowa jikinta, wanda kuma hakanne ya bashi daman jin feelings ɗin nasa naɗan sauƙa, take kuwa bacci ɓarawo ya ɗaukesa. Maleek. Yanayin yanda yake tuƙar motar tasa cikin yanayin sanyi ne yasa saida ya share wasu mintunoni kafun ya iso babban katafaren wajen da yake kamar night club, domin wajene dake ɗauke da yalwar mutane, duk kuwa da cewar dare ne amma wadataccen haske da kuma yawan mutanen dake wajen zaka ɗauka cewar rana ne, duba da irin yanda dayawan mutanen wajen keta hada hadansu, wanda kuma da yawansu samarine da Ć´an mata, sannan kuma daga yanayin shigar jikinsu kaɗae zaka gane ko suɗin suwaye ne, domin babu wata mace ko ɗaya awajen da take sanye da shigar mutumci. Yayinda da yawan mutanen dake wajen ke enjoying cool music ɗin dake tashi awajen ta hanyar romancin junansu. Haƙiƙa daga yanayin tsarin wajen kaɗai zai tabbatar maka da cewa bawajen zuwan kowa da kowa bane, saedae waĆ´anda suka jiƙe acikin nairori, musamman duba da irin tsala tsalan haɗaɗɗun maza da kuma Ć´an matan dake wajen, saboda suɗin ba irin gama garin samari da Ć´an matan nan bane. Tun shigowarsa farfajiyan wajen, da idanunsa suka sauƙa akan tsirarun Ć´an matan dake ta shawagi awajen, da kuma wasu dake cikin tabkeken swimming pool ɗin dake tsakiyar compound ɗin, ya yi ƙasa da idanunsa tare da kawar da kansa gefe. Irin yanayin takun da yakeyi ne, cikin ƙasaitar da tabi jininsa, ya jawo hankalin Mutane da yawa dake wajen ya dawo kansa. Kasancewar tun shigowarsa wajen hasken fata da kuma kyawun fuska, haɗi da murɗaɗɗiyar surar jikinsa ya ɗauki hankalin mutane da yawa. Shikuwa duk da yasan dayawan mutanen dake wajen kallonsa sukeyi amma sam baidamu ba, saboda idan da sabo yasaba da irin haka, wannan dalilin nema yasa baicika yawan shiga wajen taron jama'a ba. Direct gurin da ya zama kamar nanne cikin glub ɗin ya nufa. Ɗaya daga cikin haɗaɗɗun kujerun dake wajen yaja ya zauna, tare da zaro wayarsa dake aljihunsa ya ajiye anan kan ɗan table ɗin dake gabansa. Ɗaya daga cikin masu aikin wajenne ya ƙaraso inda Maleek ɗin ke zaune, cikin rusunawa haɗi da girmamawa yace. "Barka da zuwa ranka ya daɗe me za'a kawo ma?." Maleek kuwa daya sunkuyar da kansa ƙasa jin muryar mutum akansa ne yasashi ɗagowa ya kalli mutumin, yanayin fuskarsa ne ta sanja, duk da kuwa bae taɓa zuwa wajen ba, wannanne karo na farko, amma yaga alaman cewa bazae samu abun da yake so ba, wani abun mamakin ma shine kwata kwata baisan dalilin daya kawosa wajen ba, hakanan dae ya samu kansa da shigowa wajen, duk da kuwa yasan cewa wajen holewa ne da yake tara isassun Ć´an iska da yawa. "kabani drinks." yafaɗa ataƙaice, domin bayaso ya tsawaita dogon magana. Mutumin dake tsaye kuwa jin Maleek ɗin ya ambaci drinks ne, yasashi gane cewar kwata kwata Maleek din bae taɓa shigowa wajenba, ɗan rusunawa yayi tare da cewa. "I'am sorry sir, bamu da normal drinks saedae wanda akayi mix ɗinsa, sae kuma alcohol and wine non alcoholic." Jin mutumin ya ambata masa alcohol ne yasashi saurin ɗago kae ya kalleshi, saboda tun da yake adunia bae taɓa shan giya ba, kuma bayajin akwae watarana da zae sha. Kansa yaɗan girgiza, tare da kama Laɓɓan bakinsa yaɗan ciza, cikin muryarsa da bata fita sosae yace. "Kabani wine amma non alcoholic." "Okay sir" mutumin ya faɗa tare da juyawa cikin sauri ya tafi dan kawowa Maleek ɗin wine kamar yanda ya buƙata. Bajimawa kuwa mutumin ya dawo hannunsa ɗauke da kwalbar wine da kuma wani glass cup me yanayin zinare. Ajiye kwalban yayi agaban Maleek ɗin, tare da juyawa ya tafi. Maleek kuwa ɗaukan kwalban wine ɗin yayi batare kuma daya duba, ko wine ɗin non alcoholic bane, ya ɓalle murfin ya zuba wine ɗin acikin cup. baikuma damu da yawan wine ɗin da ya zuba acikin cup ɗinba, ya kafa kofin abakinsa, bai kuma cire daga bakinsa ba har saida yaga ya shanye gaba ɗaya wine ɗin dake ciki, Ahankali ya ɗauki wayarsa dake aje, tare da kunnata, kifa kansa akan table ɗin dake gabansa yayi, haɗe da tsurawa hoton Laylerh dake mamaye akan screen ɗin wayar idanu, wanda da ace zae tabbata yana kallo, to har abada bazae taɓa gajiyawa ba, domin sosae kallon hoton yake bawa zucia da ƙwaƙwalwarsa nutsuwa, idanunsa da suka sauƙa akan kyawawan lips ɗinta yaɗan lumshe, tare da fesar da wani irin numfashi me sanyi. "I LOVE YOU!!!" ahankali ya faɗa ta hanyar motsa jajayen laɓɓansa, da suke ɗauke da danshin wine ɗin da yasha. Kwantar da kansa akan table ɗin yayi, saedae kuma ko mintuna 16 ba acika da shan wine din nasa ba, yaji kansa naɗan juyawa, yayinda idanunsa ke sake marairaicewa, tamkar wanda yakejin bacci haka yanayinsa ya dawo, musamman ma idanunsa da suka soma juyewa, haɗi da sanja launi. Take kuma cikin mintuna kaɗan yaji duniyar na neman juya masa, ganin da yayi cewar da gaske yana neman fita acikin hayyacinsa ne yasashi miƙewa tsaye, tare da ɗaukan wayarsa, wallet ɗin dake cikin aljihunsa ya ciro tare da buɗewa batare kuma daya duba ba ya ciro fararen Ć´an dubu dubu ya ajiye musu akan table ɗin. Ahankali cikin yanayin da yakejin kansa ya fice daga cikin club ɗin, Koda ya fito farfajiyan club ɗin kuwa, har zuwa yanzu mutane hada hadansu kawae sukeyi, yayinda wasu keta rawa. Kansa yaɗan buga, saboda yanda yaji jiri na neman kada shi, acikin zuciarsa yake tambayan kansa shin ma meya kawosa wajen?, gashi sanadin zuwansa yasha abun da yake neman dagula masa lissafi. Cikin ɗan cijewa ya fito daga wajen gaba ɗaya, inda ya ajiye motarsa ya nufa, yana zuwa kuwa ya bude murfin motar nasa ya shiga, da wani irin speed kuwa yacilla motar kan titi, Duk da kuwa cewar baya cikin hayyacinsa, amma hakan bai hanashi, dagewa wajen ganin ya hana kansa, wrong driving ba. Saidai kuma sanin dare ya raba sosae ne yasashi ƙarawa motar tasa gudu. Kae tsaye ya nufi gida, sam baedamu da me zaije ya tarar agidan ba, duk da cewar bae taɓa raba dare haka awaje ba. Isowarsa gaban makeken gate din gidan nasu ne yasashi soma danna wani irin horn, wanda kuma kwata kwata baedamu da waĆ´anda horn ɗin nasa zae katsewa baccin ba. Sama da 7 minute ya ɗauka yana ta faman danna horn ɗin, ganin da yayi kuma ba'a buɗe masa bane, yasashi ci gaba da dannawa, yayinda kuma ƙaran horn ɗinnasa kaɗae zakaji ka fahimci cewa baya cikin hayyacinsa. Acan cikin gidan kuwa jin matsanancin ƙaran horn ɗin mota da yaƙici yaƙi cinyewane, yasa amatuƙar razane me gadin dake onduty ya farka daga nannauyan baccin daya ɗaukesa, fitowa daga ɗakinsa yayi, tare da zuwa jikin ƙofar gate ɗin yaɗan leƙa, ganin motar Maleek ɗinne keta danna horn yasa ahanzarce ya wangale masa gate ɗin. Maleek kuwa da yakejin kansa asama, da wani irin gudu ya shiga cikin gidan. Ko gama daedaeta parking ɗin nasa da kyau kuwa baiyi ba, ya buɗe murfin motar nasa ya fito, kallo ɗaya zaka masa kasan cewa baya hayyacinsa. Maida murfin motar nasa yayi ya rufe yana juyowa kuwa ya sauke ganinsa akan Abbou Jaheed dake tsaye ya harɗe hannayensa, akan fuskarsa kuwa sam babu alaman fari'a. *9/January/2021* 1/19/21, 8:28 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna *Chapter 36* Tsaye yaga Abbou Jaheed ya harde hannayensa, fuskarnan tasa babu ko alaman murmushi, kallo daya kuwa zakayi mishi kafuskanci cewa yana cikin matsanancin bacin rae, duba da irin yanda yanayin fuskarsa take. Sosae ganin Abbou Jaheed din yasa jikinsa yin matukar sanyi, duk da kuwa cewar bawae yana wani cikin hayyacinsa sosae bane, ahankali yayi kasa da kansa tare dasa hakwaransa ya cije teeth dinsa. kallon tsab Abbou Jaheed ya masa, cikin hade fuska yace. "Daga ina kake?" jin tambayan da Abbou Jaheed din yayi masane yasashi sake sunkuyar da kansa, dan ahakikanin gaskia karya ba al'adarsa bace, bakuma yason farata ayanzu. Shirun kuwa da yayine yasa ran Abbou Jaheed Kara baci, cikin muryar fada yace. "Tambayarka nake daga Ina kake, da har sae yanzun kake shigomin gida? kenan hakan na nufin kanason maedamin gida kamar nightclub, da zaka fita alokacin da kakeso kakuma dawo alokacin da kakeso? to kasani bazae taba yiwuwa ba, domin bazan taba lamuntar hakan ba." Idanunsa da sukayi ja ya dago ya kalli Abbou Jaheed din, ahankali ya dan motsa labban bakinsa, kamar wanda zae ce wani abu sae kuma yayi shiru, tare da dan girgiza kansa wanda yakejinsa yadanyi masa nauyi, saboda yanda yakejin wani irin bacci da kuma yanayin maye na dibansa. agogon dake sakale atsintsiyar hannunsa ya duba, ganin karfe daya harda kusan mintuna 20 ne, yasa batare da tunanin komae ba ya raba ta gefen Abbou Jaheed din ya soma tafiyarsa dake bayyana yanayin mayen da yake ciki karara. Ganin yanda yake tafiyan aharde ne yasa Abbou Jaheed riko hannunsa, tare da juyo dashi ya zamana suna fuskantar juna. ganin yanda idanunsa sukayi jajur ne yasa Abbou Jaheed rumtse idanunsa da karfi domin sarae yagano cewa Maleek din ba acikin hayyacinsa yake ba. “Meyake shirin faruwa dashine haka? Lallai hakika Allah ya aiko masa babban jarabawar rayuwa, shin ma yana ina yabari hakan ya kasance?â€? Atake yayiwa kansa duka wayannan tambayoyin da bashi da amsarsu, sassauta rikon da yayiwa Maleek din yayi saboda yanda yaji zuciyarsa tayi matukar raunana, yayinda kuma idanunsa suka ciko da kwallan tausayin kansa da kuma sabuwar rayuwar dannasa Maleek yasamu kansa aciki. Ahankali cikin yanayin sanyi ya saki hannun Maleek din, wanda kuma hakanne ya bashi daman cigaba da tafiya, batare kuma da ya sake juyowa ya kalli Abbou Jaheed din ba. Dakallo kuwa Abbou Jaheed ya bisa harya bacewa ganinsa, idanunsa ya rumtse da karfi tare da jingina bayansa ajikin motar Maleek din. zuciyarsa dake yi masa kuna ya dafe tare da soma ambaton sunan Allah. B’angaren Maleek kuwa ta babban falon gidan yabi inda kae tsaye ya wuce part dinsa. Ahankali ya maida kofar dakin nasa ya rufe,tare da karasowa bakin gadon dake cikin dakin ya zauna. Hannayensa biu yasa ya kama kansa dake wani irin ciwo, hakanan yakejin kunci da damuwa acikin rae da zuciarsa, lokaci daya ya tambayi kansa." shin meyasa ma'aikacin hotel din ya yaudaresa,ta hanyar basa wine me alcohol aciki?." Shima baesaniba bakuma shi da hanyar da zaesan meyasa hakan ta faru. Ahankali ya dago idanunsa da sukayi jajur ya saukesu akan hadadden zanen hotonta daya manna ajikin bangon dakin nasa. Tashi tsaye yayi tare da karasawa wajen da zanen hoton nata ke lik’e. Ahankali ya daura hannayensa akan hoton tare da sakin wani kayataccen murmushin da ya kara bayyana zalla da kuma tsananin kyawun fuskarsa. “Always you looking so good bae!â€? Yafadi hakan cikin matsanancin shaukinta dake matukar addabar zuciarsa. Idanunsa ya kurawa zanen fuskartata wanda musamman yasa akayi masa. “Komae naki me kyaune Laylerh, daga yarintarki har zuwa girmanki, murmushinki, magananki, dariyanki, tafiyanki, komae natsarin halittarki abun burgewane, hakika har yanzu ina bulayi da kuma neman hanyar da zaesa na iye jure zafin rashinki Laylerh, amma kowacce hanya da nake tunanin bi ta toshe, narasa hanya guda daya, please L.M say something, maybe hakan zaisa zuciyata tayi sanyi, domin haryanzu nakasa gano meyasa, da kuma dalilin da yasa ako da yaushe k’addara ke d’awainiya da rayuwata, tabbas nasan cewa ba komae ne idan mutum naso yake samu ba, hakika wannan kaddarace dake sauyawa akowani lokaci!â€? Dakatawa da maganar tasa yayi tare da lumshe idanunsa. Cikin matsanancin sanyin zuciyar da ya samu kansa aciki yace, da wata irin sassanyar murya. “Kaddara ta nesantaki dani, amma har yanzu ina numfashi, tabbas kaddara itace me hadawa kuma me rabawa, ta rabamu akaron farko, Insha Allahu Kuma zata hadamu akaro na biyu, nasani zanrayu dake Laylerh, domin kedin abu buyuce awajena, ma' ana bugun zucia da numfashina, tabbas naji ajikina cewar wata sabuwar k'addaran tana nan zuwa, wanda kuma asanadinta zaki rayu dani Insha Allah!!." Yak’are maganar tasa da wani irin murya dake bayyana asalin abunda ke kwance acikin zuciyarsa. Hannayensa ya zura acikin aljihun wandon dake jikinsa, Kallo daya yayiwa zanen hoton nata dake manne ajikin bango, ahankali ya dauke Kansa, tare da matsawa daga jikin hoton, cikin tafiyarsa ta maye kaetsaye ya nufi bathroom dan so yake yadan watsawa kansa ruwa ko hakan zaesa yaji sanyi da kuma salama acikin zuciyarsa. Bud’e k’ofar bathroom din yayi ya shige, anutse ya gama cire kayan jikinsa, tare da karasawa yasakarwa kansa shower, ajiyar zuciya me karfi ya sauke alokacin da yaji saukan ruwan shower’n ajikinsa, idanunsa ya lumshe yana mejin yanda bugun zuciyarsa ke tafiya ahankali. Sanin kuma da yayi cewar dare ya raba ne, yasa baiwani tsaya b’ata lokaci acikin toilet d’inba ya kashe shower’n tare da sako bathrobe ya fito, kasancewar kuma tuni bacci yacika idanunsa ne yasa ko tsayawa goge jikinsa baiyiba, ya haye saman gado ya kwanta, take kuwa cikin abun da baiwuce 9min ba bacci ya d’aukesa. B’angaren Abbou Jaheed kuwa bayan wucewan Maleek din cikin gida, akalla ya bata lokaci masu tsawo yana tsaye ajikin motar M.Jay din kafun daga bisani ya wuce part dinsa, kasancewar dama karan horn din motar Maleek dinne ya tasheshi daga bacci. Koda ya koma dakinsa kuwa zugum yayi, acikin rae da zuciyarsa kuwa yake ta sak’a abubuwa kala kala,domin ba kad’anba halin da yaga Maleek aciki ya d’aga masa hankali. Saboda yasan hakan alamace dake nuna cewar yana sakaci da rayuwar D’ansa, wanda kuma ya tabbata yau da’ace Mahaefiyar Maleek na raye, sae hakan yafi kona rae da zuciyarta fiye da nasa. Ajiyar zucia me k’arfi ya sauk’e sakamakon tunawa da yanda yakaranci abubuwan dake cikin zuciyar Maleek d’in kwance acikin idanunsa, hakika yazame masa dole ya aiwatar da abunda ya kudurta acikin ransa, saboda yasan hakan shi kadaine mafita. Da wannan tunanin nakawo k’arshen matsalan Maleek d’in ya kwanta, Wanda aransa yabarsa amatsayin dole bawae ra’ayi ko tunani ba. *Washegari* 8:00 am dai-dai alarm d’in dake cikin d’akin ya buga, hakan kuma yayi daidai da fitowar Najeeb daga cikin bathroom, Wanda ke sanye da rigar wanka ajikinsa, yanayin kuma yanda gaba daya jikinsa ke d’auke da danshin ruwa ne, ke nuna cewar fitowarsa daga wanka kenan. D’an k’aramin towel d’in dake rik’e ahannunsa ya’ajiye tare da juyowa ya kalli kan gadon. Har yanzu bacci take, saidai kuma yanayin kwanciyar da tayine yasa gaba daya kusan rabin rigar baccin dake jikinta ta d’age sama. Ajiyar zuciya ya sauk’e tare da k’arasowa jikin gadon, alarm d’in dake saman bedside carbonated wanda gaba daya k’aransa ya cika d’akin ya kashe, ahankali ya d’an rank’wafo da kansa tare da tsurawa kyakkyawar fuskar Laylerh’n idanu, domin yanayin yanda zarazaran eyelashes d’inta suka kwanta ak’asan idanunta ba k’aramin kyau suka k’ara mata ba, sannu ahankali ya shiga yawo da idanunsa akan fuskarta har zuwa kan breast d’inta da suka d’an bayyana saboda yanayin kwanciyar da tayi. “Sleeping beauty!â€? Ya fad’a abayyane adaedae lokacin daya sauk’e idanunsa akan Fararen shining skinny legs d’inta, wanda kwad’ayi da kuma son jin taushinsu yasashi d’aura hannunsa akansu, ahankali yad’an matsar da k’afafun nata gefe, wanda hakan ya bashi daman zama akusa da’ita. Anutse yasa hannunsa ya shafi gefen wuyanta, jin da yayi jikinnata babu zafi ne yasashi sauk’e ajiyar zuciya. “Laylerh!â€? Yak’ira sunanta cikin sassanyar murya, duk da kuwa yasan cewar baccin nata yayi nauyi sosae, tun d’azu yaso tashinta saidai kuma ganin da yayi cewar akwae gajiya atattare da ita ne yasashi k’yaleta, yanzu kuwa idan yabarta baisan sai yaushe ne zata tashi ba, gashi ko sallan asuba batayi ba, kuma k’arfe takwas hartayi. “Laylerh!!â€? Yasake k’iran sunanta akaro na biyu. Still kuwa ko motsi batayi ba, bare yasa ran farkawanta. Ahankali ya d’an matso kusa da’ita cikin yanayin sanyi yashiga busa mata iskan bakinsa akan fuskarta. Acikin baccin nata kuwa takejin sauk’an iska akan fuskarta, hakan yasa tad’an soma motsa jikinta, ahankali ta bud’e idanunta da suka d’an k’ank’ance, ras kuwa idanunnata suka sauk’a akan fuskarsa, ganin fuskar Najeeb d’in da kuma yanda ya sunkuyo kanta ne yasa cikin sauri tatashi zaune, tare da soma d’an mummurza idanunta. “Sleeping beauty dama haka kikene ke bakya k’oshi da bacci?â€? Najeeb da haryanzu bai dauke idanunsa akanta ba ya fad’a. D’an k’aramin bakinta ta turo masa gaba, ashagwab’e tace. “Ni ae baccin bai isheni ba.â€? “Uhumm.â€? Ya fad’a yana me sake matsowa kusa da’ita. Ganin hakanne kuma yasa ta d’ago da sauri ta kalleshi, ganin yanda idanunsa ke tsaye akan k’irjinta ne, yasa itama tayi saurin kallon k’irjinnata da rabin breast d’inta suka bayyana har yakai ga, ana iya hango y’an jajayen nipples d’inta, da sauri tasa hannayenta ta b’oye k’irjinnata, cikin hanzari kuma ta diro daga saman gadon, ganin hakane kuma yasa cikin sauri Najeeb yayi yunk’urin rik’o hannunta, saidai kuma batare da ta bari yasamu daman hakan ba ta gudu toilet. Idanunsa da suka sanja kala lokaci d’aya ya lumshe tare da sauk’e wani irin ajiyar zuciya, abayyane cikin yin k’asa da murya yace. “I swear nanda someday wannan yarinyar zata kasheni,because feeling d’inta kad’aima barazana yake ga numfashina, Yah Allah Help me!â€? Ya k’are maganar yana me dafe saman mararsa dake d’anyi masa zafi,saboda har yanzu jarababben feelings dinnasa bai sauk’aba, mik’ewa tsaye yayi tare da k’arasawa wajen drawer dan Zab’an kayan da zai saka. Laylerh kuwa koda ta shiga cikin toilet d’in da sauri ta maida k’ofar ta rufe, tare da sauk’e ajiyar zuciya, anutse ta zare rigar dake jikinta, k’arasawa jikin bathtub tayi, tare da had’awa kanta ruwan wanka me d’an d’umi, shigarta kuwa cikin bathtub dinne yasata lumshe idanu, musamman da taji d’umin ruwan na ratsata, anutse kuwa tayi wankanta, koda ta gama wankan d’aya daga cikin bathrobe d’in dake cikin toilet d’in tasaka tare da d’auro alwala, k’arasawa jikin k’ofar bathroom d’in tayi ta tsaya, hakanan takejin kunyan fita ahakan, duk da cewar ma rigar wankan ya sauk’o har kan guiwowinta, sanin kuma da tayi cewa bata da yanda zatayi ne yasa dole ta bud’e k’ofar bathroom d’in tafito. Saidai kuma rashin ganin Najeeb d’in da tayi acikin d’akin yasata sauk’e wani ajiyar zuciya, da sauri ta k’arasa gaban mirror, k’aramin towel ta d’auka ta goge jikinta dashi, cikin hanzari kuwa batare da ta tsaya shafa Mai ba, ta nufi wajen drawer. Bud’e drawer‘n tayi cikin yanayin sauri batare da ta tsaya dubawa ba kuwa ta zaro wata doguwar rigar spectrum mai kalan lightpink, tare da wani lightpink bra, and skintight, cikin sauri sauri tasaka kayan domin bataso Najeeb ya shigo d’akin yasamu tana saka kaya. Sosae kuwa rigar me hawa hawa ta zauna ajikinta tare dayiwa fatarta kyau, wani hijab ta saka tare da shumfud’a sallaya ta tada sallah duk dama ta makara sosae. Koda ta idar da sallan kuwa bata tashi akan sallayan ba, Azkhar ta soma karantawa, tana gama karatun azkhar dinnata kuwa Najeeb na shigowa cikin d’akin. Sanye yake da shigan jumper da wandon na wata tsadaddiyar shadda skyblue colour, sosae kuwa shigar tayi masa kyau, musamman yanda ya kafa hula me kalan sky akansa, K’amshin turarensa daya cika mata hancine yasata d’anyi k’asa da kanta. Ahankali cikin takun nutsuwa ya k’araso inda take, tare dasa hannayensa ya d’agota tsaye, sakeyin k’asa da idanunta tayi, dan hakanan tasamu kanta dak’in son kallonsa. Shikuwa Najeeb gane hakan da yayine yasashi d’ago hab’arta cikin kulawa yace. “G/M madam, hope kintashi lapia.â€? Wani irin nauyinsa da taji ne yasata jinjina masa kae alaman “Lapia.â€? Cire hannunsa akan kafad’unta yayi, fuskarsa d’auke da murmushi yace. “Kishirya Abbou Jaheed yak’iramu yin breakfast.â€? Again kai ta jinjina masa alaman “To.â€? “Inajiranki a falo.â€? Ya fad’a yana me sakinta tare da juyawa yafita daga cikin d’akin. Itakuwa Laylerh hakanan taji wani irin sanyi ya ratsa zuciyarta, saboda tasan koba komae zataga Yah M.Jay d’inta, da d’an sauri ta k’arasa gaban mirror, body lotion me k’amshi ta shafa ajikinta tare da murza powder akan fuskarta, sama sama tashafa lipstick akan lips d’inta, dama ita bagwanar kwalliya bace shiyasa bayan kwalli da mascara ba abun da tasake sawa akan fuskarta, sai turare me dad’in k’amshi da tafesa. Bud’e drawer tayi ta zaro wani baby vail pink ta yane kae zuwa wuyanta dashi, sosae kuwa hakan ya k’arawa shigar nata kyau, wani pink flat shoe tasaka ak’afanta, saboda yanda ta matsu taga Mr.Soldier ne yasa takasa koda duba kanta amadubi, anutse ta murd’a handle d’in k’ofar ta fice. Najeeb kuwa dake zaune afalon k’amshin turarenta da yajine yasashi d’ago kansa ya kae dubansa ga k’ofar bedroom d’in, ganin kuma irin kyaun da Laylerh’n tayi ne yasashi lumshe idanunsa,tare da bud’esu alokaci guda. “Masha Allah!â€? Ya fad’a yana me k’are mata kallo from head to toe, saboda sosae yaga tayi masa kyau. Harta k’araso kusa dashi kuwa bai d’auke idanunsa daga gareta ba. Laylerh kuwa ganin irin kallon da yake matane yasa ta sunkuyar da kanta k’asa, had’e da kama y’an yatsun hannunta tashiga murzawa. Najeeb kuwa badon ya k’oshi da kallonta ba, haka dolensa ya mik’e tsaye, cikin muryarsa da ta koma chan k’asan mak’oshi yace. “Muje, amma kinyi kyau sosai.â€? Sarai taji abunda yace, amma tayi muk’us kaman batajisa ba. Haka suka fito daga cikin falon yana gaba tana biye dashi abaya. Koda suka fito compound d’in gidan, kaitsaye part d’in su Abbou Jaheed suka nufa. Saura kuma baefi taku kad’an su k’arasa part d’inba wayar Najeeb ta soma k’ara alaman shigowan k’ira. Screen d’in wayartasa ya duba, ganin da yayi k’iran me amfanine yasashi juyowa ya kalli Laylerh’n dake bayyana. “Ummina ne kiyi gaba inazuwa.â€? Baijira me zatace ba ya d’auki wayar tare da matsawa can gefe. Laylerh kuwa bata damu ba kaetsaye ta murd’a handle d’in k’ofar babban falon ta shiga bakinta dauke da sallama. Jin sallaman Laylerhn ne yasa Momy dake zaune a dining area ta d’ago kae ta kalleta. Laylerh kuwa ganin Momy zaune a dining d’inne yasata k’arasowa wajen, cikin girmamawa tace. “Momy good morning.â€? “Morning, yanaganki ke d’aya, Ina Najeeb d’in?â€? Momy ta tambaya tana me lek’a bayan Laylerh’n. “Yana amsa waya awaje.â€? Tabawa Momyn amsa asanyaye. Wani irin murmushi me d’auke da ma’anoni daban daban ne ya bayyana akan fuskar Momy. “Dama ta farko.â€? Ta fad’a acikin zuciyarta, abayyane kuwa kallon Laylerh’n tayi cikin salon isar da manufarta tace. “Dama ke nake jira tun d’azu amshi wannan ki kaiwa Captain.â€? Wani d’an madaidaicin flask Momyn ta miko mata. Jin an anbaci captain ne kuma yasa zuciyar Laylerh sakeyin sanyi, anutse ta karb’i flask d’in batare da tunanin komae ba kuwa ta nufi dakin Maleek d’in. Da kallo Momy ta bita, tare da sakin wani killer smile, cikin zuciyarta tace. “Da irin wannan salon duk zan wargaza tunaninku.â€? Shigewar Laylerh sashin Maleek d’in kuwa yayi daidai da shigowar Najeeb cikin falon. Ganinsa yasa Momy sakin murmushi dan tasan tarkonta ya Kama. Ganin Momyn ne yasa Najeeb K’arasowa dining area d’in, cikin yanayin girmamawa ya gaisheta fuska asake kuwa ta amsa masa. D’aya daga cikin Kujerun dake dining table d’in yaja ya zauna, rashin ganin Laylerh’n kuma da yayi ne, yasashi d’an soma kalle kallen inda zae hangota. Gane hakan da Momy tayine yasata sakin murmushi cikin kulawa tace. “Amaryarka kake nema ko?.â€? Jin abunda Momyn tace ne yasashi d’an sunkuyar da kansa k’asa alaman kunya. Again murmushin mugunta d’auke akan fuskar Momy tace “Karka damu tanashigowa ta wuce sashin Maleek, da’alama kwana tayi tana mafarkinsa, amma nasan yanzu zata dawo.â€? Jin abunda Momyn ta fad’a ne yasashi saurin d’ago kansa ya kalleta. *(🙏🏻Nagode matuka da add’u’oinku Allah Yasaka da alkhairi, insha Allah yanzu nadawo zan daura daga inda na tsaya, kuyi hakuri kuma yanzu yanayin typing din ya sanja saboda nadaena amfani da touchpal)* *13/Jan/2021* 1/19/21, 8:29 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna *(Wayyoni😔 saida nayi typing ya goge, I am so sad wallahi😭 jinake kamar ma naciji kaina🥺)* *Chapter 37* Gaba d’aya jin kalaman Momyn yayi wani iri, saboda kwatakwata bai tsammaci jin hakan ba. “Meye Laylerh tajeyi wajen Maleek?.â€? Tambayar da yayiwa kansa kenan wacce kuma bashi da amsarta, idanunsa yadan lumshe tare da jingina bayansa da jikin kujeran da yake kai. Momy dake kallonsa kuwa ganin irin yanayin da yashiga ne yasata sakin Murmushi, cikin son nuna abun da ta had’ad’in ba wani babba bane tace. “Baikamata ka damu akan wannan ba, I think ma kashiryawa irin hakan:â€? Jin abun da Momyn ta fad’ane yasashi k’ak’alo murmushi ya daura akan fuskarsa, saboda sam bayaso Momyn tafahimci cewa yaji babu dad’i a zuciyarsa. Kansa ya sunkuyar k'asa tare da d'an lumshe idanunsa. Ahankali ta d’aura hannunta akan handle d’in k’ofar d’akin tare da murd’a handle d’in ahankali ta tura k’ofar ciki, sassanyan k’amshin turaren daya ratsa hancinta ne yasa ta d’an lumshe idanunta tare da sauk’e wata siririyar ajiyar zuciya, ahankali ta shiga k’arewa komai na had’add’en falon nasa kallo, kamar kullum kuma kamar koda yaushe komai nasa need yake, dan kuwa ko kad’an baya jurewa k’azanta. Wani irin k’awataccen murmushi ne ya bayyana akan fuskarta alokacin da ta sauk’e idanunta akan d’an madaidaicin hotonsa dake cikin falon, duk dama yanayin yanda aka d’aukesa ya d’an juya baya, hakan baisa hotonnasa k’inyin kyau ba, yayinda faffad’an surar bayansa ta bayyana kasancewar yana sanye ne da shirt na uniform d’in soldier irin mai kama jikinnan. “My beautiful broâ€? ta fad’a a daidai lokacin da take k’arasowa tsakiyar falon, tare kuma da d’auke idanunta dake kan hoton ta maidashi ga k’ofar bedroom d’insa wanda ke d’an bud’e da dukkan alama ba’arufe k’ofar da kyau bane. Ahankali tasoma takawa har zuwa bakin k’ofar tasa sannan ta tsaya, tana me sauraran yanda heart d’inta ke beating, kafun yanzu k’warai idanunta cike suke da so had’i da kwad’ayin ganinsa, ayanzu kuwa da yarage tsakaninsu baifi wasu y’an taku ba, saitaji k’irjinta na bugawa da sauri, bata kuma san dalilin hakan ba. Hannunta d’aya dayake empty tasa ta d’an tura k’ofar d’akin nasa kad’an, ba tare kuma da tasaka kanta acikin d’akinba da siririyar muryarta tayi masa sallama, tare da d’an matsawa gefe saboda tana tunanin zai amsa mata. Saidai kuma jin shiru ba’a amsa sallaman nata bane yasa take tayi tunanin cewar watak’ila yana wanka shiyasa baijita ba, ahankali ta sake tura k’ofar d’akin tare da d’ansa kanta ta lek’o kad’an, take kuwa idanunta suka sauk’a akansa. Ganinsa kwance ak’asa ne yasata saurin bud’e k’ofar d’akin da kyau ta shigo gaba d’aya. Kwance yake akan wata k’atuwar darduma, yayinda yayi matashin kai da hannunsa na dama, yanayin yanda yayi kwanciyartasa ta hanyar takure jikinsa waje d’ayane yasa kallo d’aya zakayi masa kafahimci cewa baishiryawa baccin da yakeyi d’inba, dan da’alama daga idar da sallan asubane baccin ya d’aukesa. Wani irin matsanancin tausayinsa ne ya dira azuciyarta,take kuwa taji idanunta sun ciko da hawaye, akan kyakkyawar fuskarta kuwa wani d’an murmushi ne ya bayyana, wanda kuma azahirance yake fitar da asalin abundake cikin zuciyarta. Maida k’ofar d’akin tayi ta rufe, ahankali tashiga takowa harzuwa inda yake kwance. Flask d’in dake hannunta ta ajiye tare da d’an rank’wafowa anutse ta zube guiwowinta k’asa daidai inda yake kwance, idanunta da suke d’auke da danshin hawaye ta sauk’e akansa, tare da tsaida ganinta akan kyakkyawar fuskarsa, dake yalwace da had’adden sajen dake k’ara masa kyau akoda yaushe. Y’an saffa saffan labb’ansa masu yanayi da nata had’e da zara zaran eyelashes d’insa ta kalla, murmushi ne ya sub’uce mata saboda yanda taga ya k’arayi mata kyau, da kwarjini. Idanunta ta d’an lumshe tare da shak’an wani irin sassanyan numfashi, wanda ya taho da daddad’an k’amshinsa me nutsar da zuciya. Ahankali taji wani irin feeling d’insa na ratsa duk ilahirin jikinta, wanda hakan yasa tasamu kanta acikin matsanancin shauk’insa, ware idanunta dake alumshe tayi tare da zuba masa narkakkun idanunta akaro na biyu bata ko k’yaftawa, hak’ik’a wani irin abu takeji na musamman adangane dashi, ahankali ta zauna dab’as akan k’afafunta tare da sa tafin hannunta adaidai saitin hancinsa, huci da kuma d’umin numfashinsa da ya bugi hannun natane yasata lumshe idanunta tare dajan wani dogon numfashi me kama da nishi, bakomae yaja hakan ba kuwa face dad’in da taji ya ratsata, wanda har yasa takasa d’auke hannunta daga kan fuskarsa, cikin wata irin sassanyar muryar da itakanta batasan tana dashi ba ta k’ira sunansa, duk da kuwa tasan cewar ba amsawa zaiyi ba, dan baccin nasa yayi nisa sosae. Sardae Kuma azuciyarta cike take da mamakin abun da zai rabasa da gado, da har sae dawo k’asa ya kwanta, kwanciyar ma kuma irin na takura kai. “Kodai yana da wata damuwa ne?.â€? Wani yanki na zuciyarta yayi mata tambayar dayasa taji take jikinta yayi sanyi, lokaci d’aya Kuma ta marairace fuska, cikin salon maganarta tace. “No namasan baya cikin wata damuwa, Ya M.Jay dagaske baka cikin damuwa ko?â€? Yanayin yanda tayi maganar tana me sake matsowa kusa dashi ne, ya bayyana cewar lallai amsarsa takeso, saidai kuma tayaya shi da yake bacci zai bata amsa?. Shirun nasa kuwa baisa tawani damuba, ita kad’ai kuwa tabawa kanta amsa ta hanyar cewa. “Dama nasan baka cikin damuwa, amma Katashi ak’asa kaji, kaga wajen akwae sanyi sosai, please kahau gado kaji Ya M.Jay, kadaina kwanciya ak’asa saboda jikinka zaiyi ciwo, kuma zakaji ba dad’i, dan Allah Nidae Yah M.Jay kadaina bacci ak’asa pleaseeeee!!!â€? Ta k’are maganar amatuk’ar shagwab’e, tare da sa hannunta ta shafa gefen fuskarsa. Gaba d’aya ta shagala, yayinda tamanta asalin abun daya kawota d’akin nasa. Acan falo kuwa yanzu sama da 15 minute kenan da Najeeb ke zaune akan dining table d’in yana tunanin dawowan Laylerh daga sashin Maleek, zuwansu Abbou Jaheed dining table d’inne yasashi d’an sakin fuskarsa, saidai kuma har suka fara cin abinci zuciyarsa bata samu nutsuwa ba, tunaninsa d’aya shine me Laylerh keyi awajen Maleek da haryanzu bata dawo ba? Agogon dake d’aure a tsintsiyar hannunsa ya duba, almost 20min kenan yanzu da tafiyanta, idanunsa ya rumtse da k’arfi domin duk yanda yaso tsaida zuciyarsa waje d’aya ya kasa, wasu irin tunani na dabanne ke yawo acikin k’wak’walwarsa, wanda kuma ko kad’an bayaso suyi tasiri. Momy kuwa tun d’azu tana ankare da komai,domin komai da ta tsara yazo mata ayanda takeso. D’ago kanta tayi ta kalli dukansu, Inda Abbou Jaheed da kuma Abbou Kareem ke zaune akujerar dake facing na juna, gefen Abbou Kareem kuwa Oum Ayush ce zaune, cikin nutsuwa da kwanciyar hankali dukansu sukecin abincinsu, idan kacire Najeeb dake tsakuran abincin da kad’an kad’an. Murmushi tayi again kana cikin daidaita nutsuwarta tace. “Inamamakin abunda zai zaunar da Laylerh ad’akin Maleek harzuwa wannan lokacin basu fito sunyi breakfast ba.â€? Jin abunda Momyn ta fad’ane yasa Abbou Jaheed d’ago kai ya kalleta, cikin yanayin mamaki yace. “What Laylerh da Maleek kuma suna tare ne.â€? Murmushin samun nasara Momy tayi cikin nuna halin ko inkula tace. “Eh, tunkafun shigowarku suke tare.â€? Spoon d’in dake hannunsa ya ajiye, lokaci d’aya fuskarsa ta sanja, cike dason nuna rashin dacewar hakan yace. “For how reason zasu kasance atare har tsawon wannan lokacin?.â€? Cewar Abbou Jaheed da fushin da yakeyi da Maleek d’in ya dawo sabo, har acikin ransa bawae yana k’in kusancin Laylerh da Maleek bane, aa yana gudun faruwar wani abune, duk da cewar akodayaushe zatawa kai alkhairi yafi komai, amma kuma duniya tariga da ta sanja, shaid’an yana yawo ajikin mutane kamar jini, wanda kuma akoda yaushe zai iya zugasu su aikata b’arnan da zaijawo b’acin zuciya, sam kuma agaba d’aya rayuwarsa baya fatan hakan takasance, domin Laylerh amanace awajensa, duk abu na rashin dad’i da zai tab’a rayuwarta zai zamana akwae sakacinsa aciki, bawae yana zargin wani abu na daban bane adangane dasu, kawae dai yasan zuciya bata da k’ashi, wannan yasa tun tana k’arama yake guje mata mu’amala da maza any how, badan komae ba kuwa saidan son tsare mata mutumcinta. Tunawa kuma da hukuncin da yayanke akan Maleek d’inne yasashi sauk’e ajiyar zuciya, tare da kawar da duk wani tunani dake ransa, ahankali ya d’auki spoon d’insa ya cigaba da cin abinci. Ganin kuma yaci gaba dacin abincinne yasa Momy yin k’wafa dan sam bahaka taso ba, koba komae taso ace Abbou Jaheed din yayi fad’a sosae, saidai kuma duk da haka bata fad’iba domin akwae dama masu yawa da zasu zo mata, dan abubuwan da ta shirya musu sunada yawa. Najeeb kam gaba d’aya yakasa cewa komae dan zuwa yanzu zuciyarsa tafara yi masa zafi. Laylerh kuwa da kasancewarta da Maleek d’in ya shagaltar da’ita, Ahankali ta d’aga kansa cikin nutsuwa tasaka masa pillown dake rik’e ahannunta, d’an rank’wafowa kansa tayi, anutse cikin muryarta da tayi sanyi sosae tace. “Kayi mafarki me dad’i kaji Yah M.Jay.â€? Tana gama fadin haka ta D’ago daga durk’uson da tayi flask din data shigo dashi ta d’auka tare da matsar dashi can gefe. Juyowa tayi ta kalleshi wani murmushi ta sakarmasa, batare kuma da tasakeyin komae ba tafice daga cikin dakin, yayinda takejin zuciyarta wasai babu wani damuwa. Sam tama manta cewar tazo part dinne danyin breakfast. Bata kuma ankare dasu Abbou Jaheed ba har saida ta karaso dining area’n. Najeeb kuwa K’amshin turaren dayaji na Maleek ahancinsane yasashi d’ago kansa. Ganin Laylerh da yayi da kuma gane cewar k’amshin turaren Maleek d’in daga jikinta yake fitane yasashi rumtse idanunsa da k’arfi. *5:56 pm* 1/19/21, 8:29 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna *(🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻 Kuyi hak’uri dan Allah Wllhy sim d’ina danake chat dashine yasamu matsala yau 3days kenan da kyar aka gyaraminshi, shiyasa kukajini shiru saboda ya riga yasamu matsalan da bazan hau whatsapp dashi ba, amma yanzu naje angyaraminshi Kuyi hak’uri please nasan kunsha zaman jira)* *Chapter 38* Ganin Laylerhn da kuma gane cewar k'amshin Maleek d'in dake tashi daga jikinta yake fita ne yasa shi rumtse idanunsa k'am, yayinda take yaji wani irin abu me suka ya caki k'irjinsa, lokaci daya wani irin kishinta ya Kama sa. Wanda har yakaisa ga cije labb'ansa, hakika shi kansa baisan cewar yana kishin Laylerh'n sosai har haka ba sae yau, saboda jin k'amshin Maleek ajikinta bak'aramin k'untata masa zuciya yayi ba. Itakuwa Laylerh k'arasowanta dinning table d'in ganin su Abbou Jaheed da tayi ne yasa ta tsayawa tare da dan daidaita nutsuwarta, cikin yanayin sanyi ta k'araso dab dasu, hakan kuma ya farune saboda lura da tayi da irin Kallon da Abbou Jaheed ke mata. "Good morning Abbou Jaheed."  Ta fad'a cikin yanayin nutsuwarta. Abbou Jaheed kuwa dake goge bakinsa da tissue jin gaisuwar Laylerh'n ne yasa batare daya motsa bakinsa ba, ya jinjina mata kai alaman ya amsata. Ganin hakanne kuma yasa jikin Laylerh K'arayin sanyi duk da kuwa batasan meye ma'anar hakan ke nufi ba. D'ago Kanta tayi ta dubi Abbou Kareem tare da gaishesa, fuskarsa amatuk'ar sake kuwa ya amsa mata, tare da nuna mata kujeran dake facing ta Najeeb, alama yayi mata akan ta zauna, babu musu kuwa taja kujeran ta zauna tana me gaishe da Oum Ayush. Murmushi Oum Ayush tayi cikin sakin fuska tace.    "Ina fata kindai tashi lafiya?." "Lafiya lau." Tafad'a tana me gyara zamanta akan kujeran. Plate d'in soyayyen chips da kuma plaintain Oum Ayush ta turo mata gabanta. Abbou Jaheed kuwa kasancewar ya gama cin abincin nasa tuntuni mik'ewa tsaye yayi batare da yace da kowansu k'alaba yabar dining table d'in. Murmushi me d'auke da ma'anoni daban daban Momy tayi domin koba komae manufarta ya isa inda takeson ya isa. Jan kujeran da take kai baya tayi tare da mik'ewa tsaye ta rufawa Abbou Jaheed baya. Ganin hakane kuma yasa Abbou Kareem ma mik'ewa tsaye dan dama dukansu sun kammala cin abincin nasu. Kusan kuma atare suka mik'e tsaye shida Oum Ayush, dan itama tanaso tabawa Laylerh da Najeeb d'in waje, duk dama bataji dad'in zuwan da Laylerh'n tayi wajen Maleek ba, domin Sam bataso zargi ya fara shigowa tsakaninta da Najeeb. Hakan yasa batare da sunce da kowannensu wani abuba suka nufi hanyar barin falon. Ganin haka kuwa yasa Laylerh'n ta bisu da kallo har saida suka b'acewa ganinta, sassanyar ajiyar zuciya ta sauk'e tare da maida kallonta ga plate d'in abincin dake gabanta, fork d'in dake cikin abincin ta d'auka tare da tsakalo chips d'in takai bakinta. Jin test d'in abincin daban da wanda ta saba cine yasa ta gane cewar girkin Oum Ayush ne bana laure me aiki ba. Batare da ta gama tauna abincin dake bakinta ba, ahankali ta d'ago kai ta kalli Najeeb dake zaune suna facing d'in juna, wanda kuma har yanzu bai d'ago kansa ya sake kallonta ba, tunkuwa kallon farko daya mata, ahankali yake d'an jujjuya spoon d'in dake hannunsa, domin hakanan yaji abincin yafita aransa duk da kuwa bawai wani sosae yaci ba. D'auke idanunta tayi daga garesa, dan kwata kwata bata fahimci yanayin nasa ba. Azahirin gaskia abincin takeci, yayinda acikin zuciyarta kuwa tunanin M.Jay ne yayi tasiri, kana kuma shi ya maye duk wani gurbin nutsuwarta, tuna yanda kyakkyawar fuskartasa take idan yana baccine yasa ta sakin murmushi me sauti tare da d'an lumshe idanunta. Sauti da kuma amon murmushinta da yaji ne yasa shi d'ago kansa, tare da zuba mata idanunsa wanda suka d'anyi ja, kana kuma suke bayyana zallan abun dake zuciyarsa. Murmushin kuma daya gani kwance akan fuskarta ne yasa shi sake jin wani abu ya tokare masa k'irji. "Mekenan me hakan yake nufi? tana farinciki ne saboda wani abu daban, wani abu dake b'oye acikin zuciyarta, meyasa bata farinciki alokacin da take tare dashi sai akasin haka?" Yayiwa kansa tambayar yana me yawo da idanunsa akanta, tabbas wani abu me kama da zargine ke neman mamaye zuciya da tunaninsa, wanda kuma yarda da hakan zai iya lalata rayuwar aurensu, because aure da zargi haramunne. K'ok'arin daure zuciyarsa yayi ta hanyar mik'ewa tsaye daga zaunen da yake, domin yasan zamansa awajen bazai k'ara masa komai ba sai zafin zuciya. Jin alaman tashinsa ne kuma yasa Laylerh d'ago kai ta kalleshi. Ganin yana k'ok'arin barin dining area d'inne yasa ta tsura masa ido, domin tuni ya d'auke idanunsa daga gareta. Kansa tsaye kuwa ya nufi hanyar fita daga falon, batare dako waiwayenta yayi ba. Laylerh kuwa har ya fice daga falon bata d'auke idanunta daga kallon hanyar da yabi d'in ba, hakanan duk taji ta tsargu da irin mood d'in da tagani akan fuskar kowannensu. Saidai kuma rashin son tsanantawa Kanta damuwa yasa ta share duk wani tunani dake ranta, tare da maida hankalinta ga abincin dake gabanta. Fitarta daga cikin d'akinne yasa shi bud'e idanunsa, wanda suka d'an k'ank'ance ahankali ya sauk'e wata sassanyar ajiyar zuciya, tare da fesar da wani sassanyan numfashi ta bakinsa, duk da kuwa cewar baya cikin mood maidad'i amma hakan bai hanasa bayyana wani k'awataccen murmushi akan fuskarsa ba, tare da shak'an daddad'an k'amshinta da ya cika d'akin. Maganganun sakalcinta da tayi ta fad'a masane suka shiga dawowa cikin kunnuwansa, wanda hakan yasa shi d'an lumshe sexy eyes d'insa. Cikin wata irin kasalalliyar muryar dake bayyana abunda ke cikin zuciyarsa yace. "Yeah before zuwanki am not okay Laylerh, amma yanzu da kikazo am okay!" Ya k'are maganar yana me yun k'urin tashi zaune, duk da kuwa yana jin jikinsa very weak,  hannunsa yakai ya shafi gefen wuyansa inda Laylerh'n ta tab'a. Still murmushin da baizamo al'adarsa ba ya sakeyi, domin yasan da ace Laylerh'n tasan cewa baccinsa baiyi nisa ba da bazata tab'a sakin jiki dashi har haka ba, ganin tasaki jiki dinne kuma yasashi yin shiru tare dayin kamar bacci me nauyi ne ya d'aukesa, alhalin kuma duk abun da takeyi yana jinta. Ahankali ya d'an yunk'ura ya mik'e tsaye, hannayensa duka biyu  yasa ya kama waist d'insa, Kallon pillown da Laylerh'n ta ajiye masa yayi, maganarta da take cewa.  ya daina kwanciya ak'asa ne ya dawo masa, take kuwa sauti da amon zazzak'ar muryarta suka shiga dawo masa, tamkar alokacinne abubuwan ke faruwa, d'an murmusawa kawai yayi, ahankali ya soma rage kayan jikinsa, saida ya rage dagashi sai dogon wandon dake jikinsa kafun ya wuce bathroom dan watsa ruwa. B'angaren Laylerh kuwa anutse ta kammala cin abincin nata, tare da d'aukan tissue ta goge bakinta. Mik’ewa tsaye tayi tare da k’arasowa cikin falon nasu ta zauna, hankali da Kuma idanunta ta tsaida akan k’aton tv plasman dake cikin falon, tashar MBC Bollywood take kallo inda suke haska film d’in Force 2 na john abraham, kallon yanda murd’add’iyar surar JohnAbraham d’in yake ne yasa take Maleek ya fad’o mata saboda shima irin jikin John dinne dashi, saidai kuma fuskar Maleek d’inta yafi na John Abraham d’in kyau, samun kanta acikin sabon Shauk’i da tayi ne yasata lumshe idanunta tare da jingina bayanta da jikin kujeran da take kai, lokaci d’aya kuwa ta fad’a duniyar tunani. Najeeb kuwa koda ya fita daga falon direct part d’insu ya koma, hakanan yakejin zuciyarsa duk ba dad’i shiyasa duk yaji zaman gidan ya ishesa, key d’in motarsa k’iran Benz ya d’auka kaitsaye ya fito daga part d’in nasu, babban parking space d’in dake gidan ya fito tare da bud’e motarsa ya shiga, ganinsa da maigadi yayi ne kuma yasashi wangale masa gate d’in gidan ya cilla hancin motar tasa waje, duk da kuwa cewar baiyi niyar fita yau d’inba amma dole haka zaije ya zaga gari ko hakan zaisa ya d’anji sanyi acikin zuciyarsa. Asashin Maleek kuwa baiwani d’au lokuta masu tsawo acikin bathroom d’inba, koda ya fito towel ne d’aure akan waist d’insa, yayinda gaba d’aya jikinsa ke d’auke da danshin ruwa, Wanda kuma hakan yasa gargasan jikinsa kwanciya sukayi lub lub dasu, cikin takunsa me d’auke da nutsuwa ya k’araso gaban tabkeken dressing mirror d’insa Wanda yake wadace da kayan shafa kala kala. Saida ya d’auki wani d’an k’aramin towel ya goge jikinsa, kafun ya murzawa jikinsa had’adden body lotion d’insa me dad’in k’amshi, kana kuma yabi fatar jikin nasa da turaren oud na jiki. Handryer yajona tare dayin amfani dashi wajen busar da lallausan gashin kansa, bayan ya gama ne kuma kaitsaye yanufi wajen da drawer’nsa yake, direct b’angaren da yake ajiye Kayan training d’insa ya bud’e, kamar kuma yanda yasaba yawancin lokuta idan zaiyi training tracksuit yake sawa, yau d’inma hakance takasance domin tsab yagama shirya kansa cikin wani had’add’en riga da wandon tracksuit masu kalan red yasanya, yayinda ak’afansa kuwa yasa wasu fararen snickershoe masu ratsin ja, duk da kuwa cewar shid’in mai kyaune, amma shigar dake jikin nasa ya k’ara masa kyau Sosae. Wayoyinsa dake aje akan bedside ya d’auka yasanya acikin aljihunsa, jakar da yake zuwa training da ita ya rataya akan kafad’arsa na dama, makullin motarsa ya d’auka cikin takunsa na nutsuwa ya fice daga cikin d’akin. Kasancewar kuma bayason had’uwa da kowa ne yasashi zagayawa yabi ta k’ofar baya. Koda ya fito compound d’in gidan part d’insu Oum Ayush ya kalla, dan sai alokacinnema ya tuna cewar tun zuwansu baije ya gaisheta ba, tuna hali da kuma kirkin OumAyush d’inne yasashi sakin murmushi, hakanan yaji zuciyarsa ta bashi umarni da zuwa b’angaren su Oum Ayush d’in, dama kuma yunwa yakeji, yasan kuma Bazai rasa abinci awajen Oum d’inba. Cikin takunsa na nutsuwa yak’arasa bakin k’ofar da zata sadashi da babban falon dake part d’in. Knocking k’ofar yayi saidai kuma jin ba’a amsa masa bane yasashi murd’a handle d’in k’ofar ya shiva bakinsa d’auke da sallama. Shiru falon bakowa sai k’amshin turaren wuta dake dashi, k’arasowa cikin falon yayi tare da sauk’e jakan dake kafad’ansa, batare da damuwa kowani shakku ba ya k’arasa dining area d’in dake cikin falon. D’aya daga cikin yankakkun apple d’in da aka jera akan wani plate ya d’auka tare da kaiwa bakinsa. Oum Ayush dake cikin kitchine kuwa jin motsi afalon nata ne yasata tsayawa da abunda take yi tare da lek’owa dan ganin ko waye. Saidai kuma rashin ganin mutum acikin falon yasa ta tsayawa tare da d’ansoma yin nazari, domin tabbas taji motsi acikin falon amma kuma gashi ta lek’o bataga kowa ba. “Gani nan fa anan.â€? Cewar Maleek dake tsaye abayanta, kasancewar dama dining area d’innasu yashiga lungu shiyasa bata gansa ba. Jin muryar Maleek d’inne yasa Oum Ayush sauk’e wata irin nannauyar ajiyar zuciya, saboda kafun yayi maganan ta d’an tsorita. “Yadai kinji tsorone?.â€? Ya fad’a adaidai lokacin da yake sake gutsuran apple d’in dake hannunsa. Kallo me kama da harara Oum Ayush ta watsa masa, cikin yanayin hasala tace. “Bansani ba.â€? Murmushin daya bayyana kyawawan hak’oransa yayi cikin halinsa daya saba mata yace. “I miss you so much.â€? “Miss yo mata, koda yake ma ai idan da sabo nasaba da wannan halin naka, sai yau kaga daman dubani kenan?.â€? Still murmushi yayi batare kuma da yace komae ba, yaja d’aya daga cikin kujerun dining table d’in ya zauna, kallon Oum Ayush d’in yayi, cikin yanayin d’an yamutsa fuska yace. “Am hungry, kuma zanfita training please Oum ki had’amin ko tea ne Nasha.â€? Murmushi Oum Ayush tayi tare da k’arasowa dining table d’in, cikin sigar tsokana tace. “Ae dole dama kayita fama da yunwa, tunda har yau kakasa tsaida matar aure.â€? Tafad’a tana me k’ok’arin bud’e d’aya daga cikin kulolin dake saman table d’in. Jin Oum Ayush d’in tayi masa batun aure ne, yasashi yin k’asa da kansa, cikin yanayi me kama da k’osawa yace. “Please Oum Ayush ki had’amin Lokaci na k’urewa zantafi training ne.â€? Yafad’i hakan yana me kallon agogon dake d’aure atsintsiyar hannunsa, wanda kuma yayi hakanne dan son kawar da zancen da Oum Ayush d’in keyi. Gane nufinsa ne kuma yasa Oum Ayush d’in ta saki murmushi, batare kuma da tasake cewa komae ba, ta zuba masa chicken pepper saup d’in da ta gama girkawa yanzun, tare da had’a masa tea, har gabansa kuwa ta kawo masa abincin ta ajiye, batare da ya tsaya b’ata lokaci ba kuwa ya soma cin abincin. Anan gefensa Oum Ayush ta zauna tana kallon yanda yake cin abincin, wanda yanayin yanda yake d’iban abincin da kad’an kad’an ya tabbatar mata da cewar baya kulawa da kansa sosai, tausayinsu takeji Matuk’a shida Laylerh, saboda yanda rayuwarsu ke cike da maraici da kuma zallan kad’aici, Bazata ce Abbou Jaheed baya k’ok’arin kulawa dasu ba, saidai kuma ba kulawan Abbou Jaheed d’in kad’ai suke buk’ata ba, kulawan Uwa shi dukansu suke buk’ata acikin rayuwarsu, domin Uwa itace ginshik’in y’ay’anta. Ahankali ya cire hannunsa daga cikin abincin, tare da d’aukan kofin tea d’in dake gefensa yakai bakinsa. Batare kuma daya wani sha tea d’in sosae ba ya mik’e tsaye tare da d’aukan tissue ya goge bakinsa. “Thank youâ€? Ya fad’a cikin yin k’asa da murya tare dasa hannunsa acikin aljihun wandonsa ya ciro sweets guda biyu, b’are sweets d’in duka biyu yayi ya jefa d’aya abakinsa, kallon Oum Ayush yayi cikin sigar tsokana tace. “Bud’e bakinki nasa miki sweet.â€? Jin abunda ya fad’a yasata watsa masa hararan wasa, cikin maganarta da baikai zuci ba tace. “Akan ina wasa dakai?â€? Awannan karon kam murmushi maikama da dariya yayi, batare da Oum Ayush d’in tayi zato ko tsammani ba kuwa ya matso gab da’ita, bakinta ya bud’e ya jefa mata sweet d’in aciki, baijira me zata ce masa ba kuwa yayi saurin k’arasawa cikin falon ya d’au jakarsa, ahanzarce ya fice dan yayi latti sosae, kasancewar kuma yaud’in akwae soldiers d’in da yakeson horarwa ne, yasa yana fitowa daga part d’in Oum Ayush d’in motarsa ya fad’a, batare kuma da yanemi Abdoul ba da kansa yayi driving motar, maigadi na wangale masa gate d’in gidan ya cilla hancin motar tasa waje. Jin k’aran tashin motarsa ne kuma yasa Oum Ayush sakin murmushi, sweet d’in daya sa mata abaki ta cire tare da d’aukan ledan sweet d’in daya zubar anan falon, sunan sweet d’in ta karanta tare da amfanin da yakewa mutum, ganin cewar sweet d’in na k’arawa mutum kuzari da kuma k’arfi ne yasata sake sakin murmushi abayyane tace. â€? Mai hali baya tab’a sanja halinsa, wato yabani sweet me k’ara kuzari nasha, dannayita jibgan aiki, d’an baccin rana dana sabayi ma bazan samu nayi ba to bazan shaba, dama aina sani Maleek baya kyauta haka kawae miskilin soja kawai.â€? Ajiye mintin tayi akan table tare da mik’ewa ta shige d’aki dan so take tad’an huta. Ab’angaren Laylerh kuwa sama da awa d’aya ta kwashe zaune acikin falon tana kallon film d’in da Bollywood ke haskawa, jin bacci yacika idanunta ne yasata tashi asanyaye ta nufi part d’insu zuciyarta cike da fatan kada Allah Ya had’ata da Najeeb. Bak’aramin dad’i kuwa taji ba alokacin da tashiga part d’innasu ta tarar da Najeeb d’in bayanan, hayewa saman gado tayi cikin abunda baiwuce mintuna kad’anba kuwa bacci ya d’auketa. Bacci sosai tayi domin ba ita ta farka ba sai k’arfe 2:56 pm, ganin kuma irin lokacin da ta d’auka tana baccin ne, yasa ta shiga mamaki, dan bata tab’a bacci me nauyi irin haka ba, ahanzarce ta wuce toilet ta d’auro alwala koda tafito kuwa sallaya ta shumfud’a tare da hawa kai ta tada sallah, koda ta idar da sallan bata tashi akan sallayanba saida ta sallame sallan la’asar, azkhar d’in yammaci tayi tare da mik’ewa tsaye ta soma rage kayan jikinta, bayan ta gama cire kayan nata ne kuma, ta wuce toilet wanka tayi tare da d’auro sabon alwala, koda ta fito ganin yamma tayi sosai ne yasa sama sama tashafa lotion ajikinta, powder da kuma lipstick wanda ya saje da kalan labb’anta ta shafa. Ahanzarce ta k’arasa gaban sif d’in kayanta, kasancewar kuma bata fiye son kaya masu nauyi sosai bane yasa ta zaro d’aya daga cikin had’add’un dogin rigunan da Oum Ayush takawo mata tsarabarsu, duk da kuma kasancewar rigar nada d’an fad’i kad’an amma hakan bai hana had’add’iyar surar jikinta bayyana ba, yayinda kuma adon fararen duwatsun dake gaban rigar keta faman shining suna d’auke ido. Anutse ta nad’a vail d’in rigar akanta kasancewar kuma vail d’in nada d’an girma kad’anne yasa ya sauk’o har kan k’irjinta, cool perfume ta shafa ajikinta tare da komawa kan gado ta zauna, d’an k’aramin handbag d’inta dake aje saman bedside ta jawo, wanda tun daren jiya da Oum Ayush ta ajiye mata shi bata sakebi takansa ba, zuge zip d’in jakan tayi, ganin kud’ad’e masu yawa acikin jakanne yasata d’an zaro idanunta, cike da yanayin mamaki kuwa ta sa hannu ta d’ebo kud’ad’en wanda bandir biyu na cikinsu suka kasance 2/2 hundred K, d’ayan bandir d’in kuma 100k ne. D’an soma jujjya kud’ad’en tayi tare da sake lek’a cikin jakan ta zaro car key d’in da tagani aciki, sai kuma wayarta, maida kud’ad’en tayi tare dajan zip d’in jakan ta rufe, wayarta dake kashe ta kunna take kuwa sak’onnin Teemah suka fara shigowa, wanda dayawan sak’onnin kuma d’auke suke da zallan tsokana. Share sak’onnin tayi batare da ta kulasuba ta somayin game dan shid’inne kad’ae zaihana k’wak’walwarta yin tunani marassa amfani. Tana nan zaune kuwa har aka k’ira sallan magriba, sanin kuma da tayi cewar tana da alwala ne yasata shumfud’a sallaya ta tada sallah. Tana nan zaune akan sallaya aka k’ira sallan Isha, bayan ta sallame sallan kuwa batawani tsaya yin dogon addu’aba ta mik’e tsaye saboda tun tashinta take jin cikinta na kukan yunwa. Turare ta sake fesawa ajikinta tare da d’aukar wayarta tafice daga cikin d’akin, kaitsaye babban parlor’n gidan ta nufa, kasancewar tasan adaidai wannan lokacin ne sukeyin dinner. Acan cikin falon kuwa zaune suke su dukansu ciki kuwa harda Maleek wanda ya maida gaba d’aya hankalinsa ga wayarsa dake rik’e ahannunsa. Shigowarta cikin falonne kuma yasa Najeeb dake zaune ya d’ago kansa ya kalleta, hakan yafarune kuma saboda daddad’an k’amshinta da yaji ya ratsa cikin hancinsa. Tabbas duk da cewar fushi yakeyi da’ita amma ganinta da yayi yanzun yasa shi jin zuciyarsa tayi masa sanyi, hakanan yaji ya nemi duk wani b’acin ransa ya rasa, kallon tsab yayi mata, tunawa kuma da abunda ke cikin zuciyarsa ne yasakashi sakin murmushi, domin alk’awari yayiwa kansa cewar ayau a kuma awannan daren babu abunda zai hanashi disvirgin d’inta. Anutse ta k’araso dining table d’in, tare da d’agawa su Abbou Jaheed gaisuwa, saidai kuma wannan karon fuska asake Abbou Jaheed ya amsa mata. Kujeran daya zamana shikad’aine awajen taja ta zauna, daidai lokacin kuwa idanunta suka Sauk’a akan Maleek wanda shigar jumper’n dake jikinsa tayi matuk’ar yimasa kyau. Azahirance kuwa zaman nata, yayi daidai da mik’ewarsa tsaye, k’ok’arin barin dining area d’in yayi, domin matuk’ar Laylerh zata kasance akusa da Najeeb to bazae tab’a iya jurewa ba, saidai kuma k’iran sunansa da Abbou Jaheed yayi ne, yasashi tsayawa, batare kuma daya juyoba ya amsa k’iran Abbou Jaheed d’in. Abbou Jaheed kuwa da ya tsaya dacin abincin da yakeyi, Sam baidamu darashin juyowan Maleek d’inba, cikin muryarsa da sam bata d’auke da alamar wasa yace. “Kashirya gobe da safe za muje kaga matar dana zab’a maka, ma’ana wacce zaka aura, inason kasani kuma ba shawara bane umarni ne.â€? *(Nasan dayawanku kunayiwa Abbou Jaheed kallon mutum meson kai, amma anan gaba kad’an zaku fahimci komae, then kada kuji haushi dan Abbou Jaheed yace zaiyiwa Maleek Aure, saboda saida wata hanyar k’addaran ake samun wani cikar burin, sannan kuma wata k’addara takan rikid’e tazamo alkhairi, please banaso kuyi saurin yanke hukunci domin bakusan wani future M.Jay da Laylerh kedashi agaba ba. Sannan ku k’ara hak’uri dani please danaso na bud’e WhatsApp dawani new sim saikuma naga abun bazaiyiwuba shiyasa na hak’ura har aka gyara wannan d’in.)* *16/Jan/2021* 1/19/21, 9:09 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna *Chapter 39* Tamkar sauk’an rugugin aradu haka su biyun sukaji sauk’an kalaman Abbou Jaheed d’in acikin kunnuwansu, wanda kuma ba iya su bama harta su Oum Ayush saida sukaji maganar Abbou Jaheed d’in tazo musu abazata. “What!!!â€? Ya fad’a cikin wata irin murya dake bayyana zallan tashin hankalinsa, tare da juyowa cikin sauri ya fuskanci Abbou Jaheed d’in, wanda jin kalaman da ya fad’a d’inne kuma yasa shi saurin juyowa tare da zazzaro idanunsa waje, cike kuma da rashin fahimtar inda kalaman Abbou Jaheed d’in suka dosa, cikin mauryarsa da tasanja amo lokaci guda ya maimaita kalmar ta. “Aure!!â€? abakinsa dan hakanan yajita wata iri, duba da irin yanda shigar Kalman cikin kunnuwansa ta haifar masa da matsanancin bugun zuciya, da kuma fad’uwar gaba. Abbou Jaheed kuwa ganin yanayin tashin hankalin da Maleek d’in ya shiga ne yasashi d’aure fuskarsa tamau, batare kuma da alaman wasa ko wargi ba akan fuskartasa yace. “Eh Aure zakayi kamar yanda kaji na fad’a, saboda bazan zuba maka idanu ka zauna haka ba, inaso kuma kasan cewa hakan umarnine ba wai shawara ba, na riga dana gama yanke hukunci, ba kuma zan tab’a sanjawa ba, saboda haka koda Yaushe yazamana kana cikin shiri, saboda ba neman amincewa ko yardarka nake da buk’ata ba, domin na baka dama amma kayi wasa dashi, atunaninka haka zanzuba maka ido, ina kallo kanayimin duk abunda kaga dama acikin gida? bayan kuma kasan cewar bazan tab’a lamuntar hakanba, sannan zab’i ya rage naka ko kaso ko karka so aurenka babu fashi, domin kai ba k’aramin yaro bane da za’a tsaya tambayar amincewarka ko akasin haka.â€? Idanunsa da sukayi jajur lokaci d’aya ya rumtse da k’arfi, domin hakanan yaji k’afafunsa na neman gaza d’aukar nauyinsa, yayinda kuma take guiwowinsa suka yi sanyi, shikam idan ba yaudarar kansa yakeyi ba saiyakejin kamar kunnuwansa basu jiye masa maganganun Abbou Jaheed d’in adaidai ba, kansa ya d’an soma girgizawa ahankali, cikin cijewa da kuma k’ok’arin daure zuciyarsa ya had’e labb’an bakinsa ya ciza, wani irin tafasa da yaji zuciyarsa nayi ne kuma yasashi juyawa cikin sauri ya soma sauk’a daga kan y’an k’ananan steps d’in da zai nesanta ka da dining area’n. Laylerh kuwa dake zaune wanda tuni kalaman Abbou Jaheed d’in sun sa tazama kaman statue, bayan Maleek d’in tabi da idanunta wanda suka cika da ruwan hawaye batare da ta sani ba, yayinda kuma taji wani irin abu mekaman dutse ya tokare k’irjinta. “Mekenan me hakan yake nufi, M.Jay aure zaiyi kaman yanda itama tayi aure? Wannan wace iriyar k’addarace me matsanancin girma?â€? Tayiwa kanta tambayar da har acikin zuciyarta bata da gamsuwa akan hakan, meyake shirin faruwa da’ita ita kanta batasani ba, raunannun idanunta wanda suke shirin zubo da k’wallan dake cikinsu ta lumshe, cikin karyewar zuciyar daya risketa ta kifa kanta anan saman table d’in dake gabansu, tare kuma dasa hannu ta dafe daedae saitin zucuyarta dake bugawa da sauri, tabbas wani abu me kama da matsanancin fad’uwar gaba da kuma tsoro takeji, wanda hakanne kuma yasa ta keji ajikinta kaman tarasa wani babban kaso na babin nutsuwarta. Saidai kuma jin da tayi Abbou Jaheed d’in na fad’awa su Abbou Kareem cewar y’ar gidan abokin aikinsa ne ya zab’awa Maleek d’in, wato Alhaji Faruk yasa tayi saurin d’ago kanta, domin kuwa tasan cewa Alhaji Farouk d’in baida wata y’a sai Munnira, matashiyar budurwar dake matsanancin jin kai, da kuma isa had’i da d’agawa wacce akoda yaushe take ganin tafi kowa, duk da kuwa cewar baza’a k’irata da sunan mummuna ba amma bata da wani kyau irin na fitar hankali. Lips d’inta ta ciza tare da d’anyin kasa da kanta, domin sam bataso wani daga cikinsu yakaranci yanayin da take ciki. Saidai kuma duk yanda taso ga b’oye yanayin nata hakan baisa Najeeb kasa fahimtar sanjawar da mood d’inta yayi lokaci d’aya ba. Saidai kuma sanin abunda ya shirya acikin zuciyarsa yasa shi kasa ce mata komae, saima maida hankalinsa da yayi akan plate d’in abincin dake gabansa. Ab’angaren Maleek kuwa zuciyarsa cike da k’una haka ya k’arasa part d’insa, kaitsaye bedroom d’insa ya wuce, ahankali ya maida k’ofar bedroom d’in nasa ya rife, cikin yanayin daya samu kansa ya jingina bayansa ajikin k’ofar tare da rumtse idanunsa da k’arfi, yayinda kalaman Abbou Jaheed kedawowa cikin kansa filla filla. Abayyane ya tambayi kansa cewar. “Meyasa k’addara zata zab’a masa irin wannan rayuwa me cike da k’uncin? Shin tayaya nema zuciyarsa zata iya jure d’aukan way’annan manya manyan k’addarorin da suke tunkarosa? Meyasa Abbou Jaheed zaiyi masa haka? Meyasa!!!â€? Yafad’a cikin k’araji tare dasa hannunsa ya naushi k’ofar d’akin, tabbas da ace zai iya bud’e baki ya furta rashin amincewarsa ga kalaman Abbou Jaheed d’in ayau da yayi hakan, ko da zaiji sanyi da nutsuwa acikin zuciyarsa, saidai kuma amma bashi da wani zab’i domin kasantuwar Abbou Jaheed amatsayin mahaifinsa yasa ya zame masa dole yin biyayya agaresa. Asanyaye ya tako zuwa tsakiyar d’akin nasa, hakanan yakejin duk zuciyarsa ba dad’i. Abakin gadonsa ya zauna tare da sa tafukan hannayensa ya rufe fuskarsa, magana ta gaskiya shine baya ji ajikinsa cewar zai iya zama da wata mace amatsayin mata, saboda fata da kuma buri d’aya kawae yake dashi, wanda kuma ya riga da yayi losing d’insu tuntuni, hakan yasa sam bayajin wata mace amatsayin abokiyar zamansa, tabbas ya yarda cewa soyayyar Laylerh tana d’aya daga cikin manyan k’addarorinsa haka ma kuma rasata, shima k’addara ne me d’auke da k’alubale na musamman, hak’ik’a yasan cewa akoda yaushe Allah Ne ke tsarawa bawa fad’uwa da kuma nasararsa, shi ne kuma ya tsara masa komae, amma bayajin acikin tarin k’addarorinsa akwae wata bayan Laylerh, saboda yayi Imani cewa Laylerh ita kad’aice mace da aka rubuta masa acikin k’addaransa, kuma itace rauninsa, samunta nasara ne rashinta kuma nak’asu ne acikin rayuwarsa, ya yarda cewa zae rayu da dafin sonta acikin zuciyarsa, zafi k’una da kuma radad’in da yakeji na soyayyarta akoda yaushe k’onasa suke, k’una me tsananin zafi, duk da hakan kuwa akullum salon soyayyarta sanjawa yake acikin zuciyarsa, wanda ayanzu shi kansa baisan wani irin soyayya bane yakeyiwa Laylerh’n, abu d’aya kawai yasani shine, da gaba d’aya zuciya da rayuwarsa yake sonta, zai kuma ci gaba da sonta har k’arshen rayuwarsa, saboda soyayyarta agaresa babban garkuwa ne dake k’arawa zuciyarsa k’wari. Wani irin numfashi me tafiya da ajiyar zuciya ya sauk’e, ahankali ya sulale jikinsa ya kwanta akan gadon tare da lumshe kyawawan idanunsa, wanda suka sanja launi daga farare zuwa ja. Sama da mintuna 10 ta d’auka tana aikin jujjuya spoon d’in abincin dake hannunta, duk kuwa ga yanda taso samawa kanta nutsuwa ta kasa, yayinda kuma ta kasa sa koda lomar abinci d’aya ne abakinta. Tana nan ahaka kuwa harsu Abbou Jaheed suka kammala cin abincinsu suka tashi, hakan yasa daga ita sai Najeeb ne suka rage akan dining table d’in. Wanda kuma gaba d’aya a ankare yake da yanayin Laylerh’n, duk da baisan asalin dalilin dayasa tasamu kanta ahakan ba, amma yaji ba dad’i saboda ko kad’an bayason ganin damuwa akan fuskarta. Ahankali ya d’ago kansa tare da sauk’e idanunsa akanta. Ganin yanda ta sadda kanta k’asa ne yasashi k’iran sunanta asanyaye, batare kuma daya d’auke idanunsa akanta ba. Jin amo da kuma sautin muryarsa ne yasa ahankali ta d’ago kanta cikin muryarta da tayi sanyi sosae ta amsa masa, saidai kuma sam bata yarda ta sauk’e k’wayoyin idanunta acikin nasa ba, tayi hakanne kuma dan gudun kada ya karanci yanayinta. “Tunanin me kike?â€? Ya jefo mata tambayar da bata shirya amsa masa ba, saidai kuma gudun kada ya zurfafa har yakai ga gano asalin abunda ke damunnata ne yasa asanyaye tace. “Ba komai!â€? “Kin tabbata?â€? Yafad’a yana me yawo da idanunsa akanta. Kai ta jinjina masa alaman “Eh.â€? “To kici abincinki idan kuma kin k’oshi kitashi kije ki kwanta dare yayi.â€? Ya fad’i maganar yana me kai dubansa ga agogon dake d’aure atsintsiyar hannunsa, wanda yake nuna k’arfe 8:45 pm. Jin abunda yace dinne kuma yasata mik’ewa tsaye da sauri, domin dama neman hakan take, duk da cewar kuwa acikinta tanajin yunwa saidai bata da dama ko nutsuwar cin abinci, Jan kujeran da ta zauna baya tayi, cikin yanayin sanyin daya rusketa ta soma k’ok’arin barin wajen cin abincin. Da wani irin kallo ya bita har ta fice daga cikin falon, ajiyar zuciya me k’arfi ya sauk’e tare da d’aukan bottle water ya soma sha. Laylerh kuwa cikin yanayin sanyi ta k’arasa part d’innasu, ahankali ta tura k’ofar bedroom d’in ta shiga, direct gaban had’add’en dressing mirror ta nufa, hakanan tasamu kanta tana me k’urawa kyakkyawar innocent face d’inta idanu ta cikin madubin, take kuwa abubuwa da yawa suka shiga yawo akwanyarta, hannu tasa ta dafe k’irjinta dake dukan uku uku, hakanan takejin wani irin yanayin tsoro na sauk’ar mata, yayinda maganar auren Maleek d’in yayi mata tsaye acikin ranta, wanda yasa duk takejin komai ba dad’i. “Mezai faru idan Yah M.Jay yayi aure? Then me auren nasa yake nufi? Rayuwa zaiyi da wata mace na har abada? kyakkyawar fuskarsa, da kuma murmushinsa, had’i da komae da komae nasa wata dabance zata ke gani, hakan na nufin kusancina dashi yazo k’arshe?â€? Abayyane tayiwa kanta duka tambayoyin, wanda kuma hakan yasa wasu irin hawaye masu zafi suka biyo kan k’uncinta, hak’ik’a tana da fata da kuma buri akan Mah Boo d’inta, dukkuwa da cewar akwae auren Najeeb akanta, amma koda da sau d’ayane bata tab’ajin d’igo d’aya na zazzafar soyayyarsa ya ragu acikin zuciyarta ba, akullum kuma tanajin cewa lallai watarana zasu kasance atare kamar yanda take gani amafarkinta yawancin lokuta, wani irin so takeyiwa Maleek tarasa, saidai tayi imani cewa zata iya sadaukar da komae na rayuwarta akansa. Najeeb. Ahankali ya turo k’ofar d’akin ya shigo, saidai kuma ganinta atsaye da yayi ne yasashi maida k’ofar ya rufe ahankali, jingina bayansa da jikin k’ofar d’akin yayi had’e da sauk’e idanunsa akan tsararriyar surar jikinta, duk da cewar kuwa tabawa k’ofar shigowa d’akin baya amma hakan baihanashi gane cewar kuka takeyi ba, gajiyayyun idanunsa masu d’auke da kasala ya lumshe, saboda yanda yakejin wani irin feelings na musamman akanta. Anutse yasoma takawa zuwa gareta, saidai kuma yanayin yanda gaba d’aya tunaninta ya tafi zuwa wani waje na daban yasa sam bata ji motsin takunsa ba. Isowarsa gareta da kuma yanda sassanyan k’amshin turarenta ya bugesa ne yasashi lumshe ido, tare da fesar da wani irin numfashi. Ahankali cikin wani sabon yanayin daya samu kansa aciki, yasa hannayensa ya rik’o kafad’arta tare da juyo da ita hakan yasa jikinsu had’ewa waje d’aya. Da sauri ta d’aga d’ara d’aran idanunta ta kalleshi domin kwata kwata bata kawo aranta cewar zai shigo d’akin yanzu ba. Jefa idanunta acikin nasa da tayi ne kuma yasa tsikar jikinsa motsawa, yayinda kuma yaji wani irin abu na yawo ajikinsa. Da idanunsa wanda suka d’an soma lumshewa, ya kalli y’an siraran hawayen dake kwance akan fuskarta, sake matso da jikinsa gab da nata yayi, wanda sanadin hakan kuma yasa numfashinsu gauraya waje d’aya. Yanayin yanda take iya jiyo sautin bugun zuciyarsa ne kuma yasa ta lumshe idanunta. Shi d’inma Najeeb da yakai k’ololuwa kasa jurewa yayi, har saida ya lumshe idanunsa, tare da kamo tafukan hannayenta, cikin wani irin sanyin yanayi ya d’aura bakinsa akan nata. *19/1/2021* *Note edit* 1/20/21, 8:26 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna *Chapter 40* Cikin wani irin sanyin yanayi ya d’aura bakinsa akan nata. Amatuk’ar bazata taji sauk’an lips d’in nasa akannata, wanda kuma koda wasa bata tsammaci hakan daga garesa ba, musamman a irin lokacin. Wani irin abu me kama da shock ne taji ya shigeta, yayinda lokaci d’aya duk wani tunani dake yawo acikin brain d’inta ya tsaya cak, haka taji kanta kamar wata bak’uwar halitta, domin harta numfashinta saida yatafi hutun wucin gadi. Najeeb kuwa k’ok’arin fusgo numfashinsa dake shirin k’wace masa yayi, cikin wani irin gigitaccen yanayin daya samu kansa aciki ya sauk’e wata irin nannauyar ajiyar zuciya, ba iya tsikar jikinsa ba kuwa hatta gargasan dake jikinsa saida suka mimmik’e saboda yanayin yanda lips d’insa suka sauk’a akan nata lips d’in, wanda tsananin taushinsu yasa shi k’ara rasa nutsuwarsa, cikin yanayin zautuwa, da kuma yanda yakeji ajikinsa, hakan yasa bayajin zai iya daurewa, lips d’inta na k’asa ya tura acikin bakinsa, lokaci d’aya yayi mata wani irin tsotsan da yayi sanadiyar dawo mata da numfashinta, yayinda shi kuma nasa numfashin yasoma k’ok’arin d’aukewa sakamakon d’and’ana gard’in saliva d’in bakinta da yayi wanda take ya haukata duk wata nutsuwarsa. Jajayen idanunsa masu d’auke da fitinannen sha’awarta ya lumshe, kana ahankali ya shiga tura harshensa acikin bakinta, had’uwar harshensa da nata waje d’ayane kuma yasashi yi mata wani irin runguma, azafafe yasoma kissing lips to tongue d’inta, yayinda yakejin wani irin yanayin dad’i, irin wanda bai tab’a jiba na ratsa duk ilahirin jikinsa. Tabbas yanayin nasa yazo mata abak’o, wanda kuma yasa ta kasa motsa koda y’ar k’aramar yatsarta ne, yanayin kuma da tashiga ne yasa taji kamar jinin jikinta ya daina gudana yanda ya kamata, azahirin gaskia ma so take ta farka daga nannauyan baccin da take tunanin ya d’auketa, saboda bata gamsu da cewar azahirance hakan ke faruwa bawai amafarkiba. “Da gaskene Najeeb ne yake kissing d’inta ko kuwa?â€? Zuciyarta tayi mata tambayar da yayi sanadiyar dawo da ita cikin hayyacinta. Wanda kuma d’and’anon saliva d’in Najeeb d’in da yagame bakinta ne, ya sake tabbatar mata da cewar bawai mafarki take ba, reality abun ke faruwa. Irin runguman da yayi matane kuma yasata jan dogon numfashi, tare da rumtse idanunta k’am, domin sam batajin zata iya taimaka masa wajen enjoying yanayin. Duk da cewar Najeeb ne agabanta yana kissing d’inta, amma hakan bai yana zuciyarta bugawa da sunan Maleek ba, kana kuma tunaninsa bai bar cikin k’wak’walwarta ba, lallai tayi imani cewa babu wani yanayi da zata shiga aduniya na dad’i kona wahala, da zaisa Maleek ya gusa daga cikin rai da kuma tunaninta, domin dan shine kawae har yanzu zuciyarta take bugawa. Karyewar zuciyan da tasamu kanta acikine kuma yasa ahankali wasu sabbin hawaye masu d’umi, suka silalo daga cikin idanunta, duk da kuma cewar k’afafunta sun soma gajiya da tsayuwar, amma babu yanda zatayi, saboda har yanzu bata gama tantance dawowar nutsuwarta ba. B’angaren Najeeb kuwa, zuwa yanzu ya riga daya gama rud’ewa, yayinda yake jin yakai k’ololuwa wajen sha’awarta, saboda d’umin numfashinta kad’ai da yake shak’a k’ara zautar dashi yake, hak’k’a shikam acikin wata sabuwar duniya yake jin kansa, duniya ta daban wanda baitab’a kasancewa ak’ark’ashin inuwarta ba. Jinda yayi k’afafunsa na neman gaza d’aukarsa ne, yasa ahankali ya zare bakinta daga cikin nata. Wani rin numfashi me zafi ya fesar, kana jikinsa amatuk’ar sanyaye ya had’e forehead d’insu waje d’aya. Jajayen idanunsa da suke cike da mayen sha’awarta ya bud’e ahankali, duk da kuwa cewar sun d’an k’ank’ance kad’an saboda azabebben feelings d’inta dake cin naman jikinsa. Sauk’e ganinsa akan kyakkyawar fuskarta da yayine kuma yasashi ganin hawayen dake kwance akan kumatunta. Waist d’inta dake cikin hannayensa ya rik’e da kyau, ahankali ya d’anyi k’asa da kansa, wanda kuma hakan yabashi daman sanya gefen fuskarsa dake d’auke da beard ya share mata hawayen dake kan fuskar nata. “Stop crying!â€? Yafad’a da k’yar ta hanyar motsa light pink lips d’insa, duk da cewar kuwa maganar tasa ya mak’ale acan k’asan mak’oshinsa, amma hakan bai hana kunnuwan Laylerh jiyo abunda ya fad’a ba. “Open your eyes.â€? Still ya fad’a in a silently voice, yana me sanya hannayensa duka biyu ya tallafo hab’arta, kyakkyawar fuskarta ya zubawa ido, azuciyarsa yana me raya abubuwa dayawa. Itakuwa Laylerh kasa bud’e idanun nata tayi kamar yanda ya buk’ata, dan hakanan taji wani irin nauyi da kunyarsa sun dirar mata, saboda kwata kwata bata saba da abunda yayi matan ba, duk da cewar Maleek shine Namiji na farko aduniya daya fara kissing d’inta, sai kuma shi da ayanzu ya zama na biyu. Tabbas bazata tab’a manta first kiss nata ba aduniya, musamman ma wanda ya fara kissing d’innata, saboda akansa ne tafara jin wani irin yanayi na musamman, yanayin da kuma har abada bazata tab’a mantashi ba, hak’ik’a sosae taji wani abu na musamman alokacin da Maleek ya d’and’ana mata gard’in saliva d’insa, wanda kuma bazata ce the same irinsa taji ayanzu da Najeeb ke kissing d’inta ba, idan ma ta fad’i haka to tayi k’arya, tabbas bazata ce bataji komae akan kissing d’inta da Najeeb d’in yayi ba, taji abubuwa da yawa amma kuma saidai bazata tab’a had’ashi da yanayin M.Jay ba, domin shi nasa yanayin dabanne, duba da cewar yayi kissing d’inta ne adaidai lokacin da suke tsaka da muradin juna, lokacin da take buk’atarsa fiye da abinci ko ruwan sha, ya shayar da ita wani sinadarin da har abada bazata tab’a mantawa dashi ba, akansa tafara sanin menene feelings saboda haka dole komae nasa da zaiyi mata yazama daban da wanda kowa zaiyi mata. Ahankali ya hura mata sassanyar iskan bakinsa akan fuskarta, wanda hakan yasa take taja wani dogon numfashi. Y’ar yatsar hannunsa dake kan fuskarta yasa ahankali ya soma zagaye smalls lips d’inta wanda suka k’ara zama ja saboda kissing d’inta da yayi. “Tunanin me kike?â€? Yayi mata tambayar yana me sake matso da ita jikinsa. Kai ta d’an girgiza masa alaman “Babu.â€? “Ban yarda ba.â€? Yafad’a adaidai lokacin da yake daura hannunsa akan zip d’in dake gaban doguwar rigar dake jikinta. Jin haka yasa tayi saurin bud’e idanunta tare dasa hannayenta ta soma k’ok’arin janye jikinta baya. Gane abun da take nufi yasashi sassauta rik’on da yayiwa waist d’inta. Ahankali kuwa tashiga jan jikinta baya, ganin haka yasa shi d’an soma matsowa kusa da ita. Da idanunta da sukayi raurau take kallonsa, haka ta ci gaba dajan jikinta baya shikuma yana matsota har kuwa ta kawo kanta jikin bango batare da tasani ba, saida taji bayanta ya had’u da bango kafun dan dolenta ta tsaya cak. Murmushin daya bayyyana kyawun fuskarsa yayi, cikin yanayin feelings d’inta da yake ciki yasanya hannunsa na dama ya dafa jikin bangon, wanda hakan yasa yazama kaman yayi mata k’awanya ne. D’ago idanunta tayi daniyar ta kalleshi amma saidai ganin irin mayataccen kallon da yakeyi mata yasa ta sadda kanta k’asa, saboda wani yanayi na daban ta gani kwance acikin idanun nasa. Najeeb kuwa kamar yanda ya k’udura acikin ransa, yanzun ma bai fasaba, hannunsa yasake d’aurawa akan zip d’in rigar nata, batare kuma da tayi auneba ya zuge zip d’in rigar fiye da rabi, take kuwa had’add’iyar surar k’irjinta ya bayyana, inda kuma fitinannun idanunsa suka sauk’a akan kyawawan breast d’inta, wanda hakan yasa take tsikar jikinsa suka soma zubawa, wani irin abune yashiga yawo ajikinsa, wanda yasashi kasa daurewa har saida ya sake matsowa kuwa sosai da ita. Laylerh kuwa ganin yanda ya matso kusa da’ita sosai, da kuma yanda ya bud’e mata asirin k’irjinta ne yasata maida idanunta ta kulle k’am, sosai wani irin tsoro ya dirar mata, wanda har hakan yakasa b’uya akan fuska da kuma jikinta. Saman k’irjinta ya k’urawa ido yana mejin kamar ya maida ita cikin jikinsa, tabbas ya yarda cewa had’uwar Laylerh’n ya wuce duk wani tunaninsa. Yatsar sa d’aya ya d’aura adaidai saman k’irjinta, ahankali kuma ya soma yi mata tafiyan tsutsa akan fresh skin d’inta. Jin abunda yake matanne kuma yasa tsikar jikinta mimmik’ewa, rashin sabo da hakan yasa tayi saurin sa hannayenta ta kare breast d’inta, duk dama basu bayyana kansu duka ba, amma tasan bak’aramin kunya zata shaba, matuk’ar ta bari Najeeb d’in ya gama kalle mata asirin k’irjinta. Cikin yanayin dauriyar son ta k’waci kanta daga garesa, ashagwab’e tace. “Nidae dan Allah Yah Nahjeeb ka k’yaleni baccifa nakeji.....â€? tunawa da yanda ta k’ira sunansa ne yasa tayi saurin sa hannu ta toshe bakinta, domin daga saninsa da tayi zuwa yanzu bata tab’a ambatan sunansa a gaban idanunsa ba sae yau. Rikitattun idanunsa ya watsa mata, cikin kafeta da ido yace. “Fad’amin meye sunana?.â€? Idanunta tad’an zaro waje, ahankali tace. “Babu fa.â€? “Okay bani da suna kenan?â€? Murmushin da bata shiryawa zuwansa ba tayi, hakanne kuwa yasa Najeeb kasa d’auke idanunsa akanta, domin ba kad’anba tayi kyau da tana murmushin. Matsanancin shauk’inta daya d’ebesa ne yasashi d’an durk’usawa, batare kuma da tayi aune ba taji ya d’agata cad’ak kamar wata y’ar baby. Idanunta ta zazzaro waje, bakinta ta bud’e daniyar cewa wani abu, da sauri yasa hannunsa ya toshe mata baki, kaitsaye saman makeken gadonsu ya nufa da ita. Yana k’arasawa jikin gadon kuwa ya shumfud’eta tare dasa hannunsa yayi switch off na wutan d’akin, take kuwa duhu ya mamaye ganinsu. Kasancewar ta me tsananin tsoro ne kuma yasa ganin duhu ya mamaye d’akin tayi saurin rik’e hannunsa, cikin muryar tsoro tace. “Please ka kunna mana haske.â€? “Meyasa?â€? Ya tambayeta adaidai lokacin daya kammala cire rigar dake jikinsa. “Tsoro nakejiâ€? tafad’a da muryarta dake rawa. Mik’a hannunsa yayi inda ya danna makunnin bedside lamp, take kuwa wani d’an haske ya bayyana acikin d’akin saidai kuma hasken bashi da fawa sosae. Ganinsa haka agabanta Babu rigane yasa tayi saurin janye jikinta baya, tare da kawar da kanta gefe. Sam bai damu da yanayin da ta shigaba ya jawota jikinsa, wanda kuma hakan ya haifar mata da fad’uwan gaba. K’ok’arin kwace kanta tasomayi amma yakasa bata daman hakan, saima kissing d’in wuyanta da ya shiga yi kamar wani zautacce haka yasoma k’ok’arin yage mata rigar dake jikinta. Sauyawar da yayi lokaci d’aya bak’aramin d’aga mata hankali yayi ba, yayinda wani irin mummunan tsoro ya shigeta, musamman da taga yanda jikinsa ke rawa, itama soma rawa jikinnata yayi amma ba irin nasa rawanba, domin shi jikinsa na b’arine saboda shauk’inta, ita kuwa jikinta na b’arine saboda tsoronsa. Ganin dagaske yana k’ok’arin rabata da rigar jikinta ne yasa, hawayen da suka cika idanunta suka samu daman gangarowa. Shikam Najeeb yariga daya kai k’ololuwa wajen ficewa acikin hayyacinsa, bashi da wani buri ayanzu wanda ya wuce yaji Laylerh’n naked acikin jikinsa. Hakan yasa yaci gaba da k’ok’arin cire mata rigar dake jikinta. K’ank’ame jikinta waje d’aya da tayi tare da soma girgiza masa kai, cikin muryarta me d’auke da amon kuka tace. “Am scared, please leave me!â€? Jin abunda ta fad’a me yasashi d’ago kansa ya kalleta, da jajayen idanunsa wanda suka k’ank’ance, cikin sark’akk’iyar muryarsa da ta dashe kana kuma ta daina fita da kyau yace. “Pleaseeee LAYLERH!â€? *(Guys kunaga abawa Najeeb dama kuwa?🤔 nidae baruwana banshirya karb’an shik’a daga wajen Maleek ba😝)* *(Note Edit*) *20/1/2021* 1/23/21, 4:32 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna *Chapter 41* “Pleaseee Laylerh!â€? Yafad’i hakan cikin dashashshiyar muryarsa, dako fita da kyau batayi, hak’ik’a kuma kallo d’aya zakayi masa kafahimci cewa yakae wani matsaya wanda k’iris ya rage ya zauce, domin kuwa idanunsa k’ank’ance wasn’t sukayi tare dayin jajur kaman anwatsa musu garin barkono acikinsu, yayinda gaba d’aya hannayensa ke rawa, tabbas yaje wani level me tsananin wahala, saboda kallon surar Laylerh’n da yayi naked ba k’aramin wargaza masa lissafi yayi ba, duk dama iya saman k’irjinta kawae yake iya kallo amma hakan baihanashi zaucewa da rud’ewa ba. Hak’ik’a tsoron dake kwance acikin zuciyarta ya bayyana akan fuskarta k’arara, domin da ace Najeeb d’in Zae dawo cikin nutsuwarsa yayi mata duban tsab to tabbas da yakaranci yanayin da take ciki, dan kuwa harta labb’an bakinta karkarwa suke saboda matsanancin tsoron da ya shigeta. Sake k’ank’ame jikinta waje d’aya tayi, tare da had’e tafukan hannayenta waje d’aya, cikin yanayin firgici da kuma alaman rok’o, da muryarta dake matsanancin rawa tace. “Dan Allah Kayi hakuri, kabarni tsoro nakeji!!â€? Yanayin yanda tak’are maganar tana me d’an janjikinta bayane, yasa Najeeb saurin rik’o hannunta yasaka acikin nasa, da idanunsa wanda sukayi luhu luhu ya kalleta, cikin sark’akk’iyar muryar yace. “Please Laylerh help me, wallahi ni kad’ai nasan abunda nakeji acikin gangar jikina, ina matuk’ar buk’atar kulawanki Laylerh please Laylerh karki cemin a’a!â€? Yanayin yanda ya k’are maganar cikin sigar dake bayyana rok’o agareta, da kuma bayyana gaskiar abunda ke ransa yasa, Laylerh soma d’an girgiza kanta, tare da cigaba dajan jikinta baya, tabbas har acikin ranta amatuk’ar firgice take dashi, tsoro da fargabane suka cika mata zuciya, wanda hakan yasa bazata tab’a iya control d’in kanta ba, hak’ik’a tanajin tsoron Najeeb d’in sosae, amma kuma har acikin zuciyarta tasan cewar hanasa hakk’insa tamkar sab’awa Ubangijinta ne, sannan kuma zata kwana mala’ikun Allah na tsine mata. “Shin tayaya zata iya jure duk way’annan? Tayaya zata iya mallakawa Najeeb kai dama jikinta gaba d’aya? Hak’ik’a budurci shine abu mafi girma da kowacce y’a mace ke tink’aho dashi, burin kuma duk wata macece tabada budurcinta ga wanda ya dace sannan ya kuma cancanta, akuma guri d’aya ne idan kabada budurcinka baka da danasani, shine gidan aurenka da kuma masoyinka na gaskiya, wanda har abada bazaka tab’a danasanin hakan ba, tabbas Najeeb mijinta ne, amma kuma baizamo zab’in zuciyarta ba, shin zamowarsa mijinta kad’ai ya isa ya cancanci karb’an budurcinta?â€? Tayiwa kanta duka tambayoyin alokacin guda batare kuma da tana da gamsasshiyar amsar da zata bawa kanta ba. “Tabbas bawa Najeeb jikinta da zatayi ayanzu daidai yake da ruguza duk wani mafarkintaâ€? Wani yanki na zuciyarta ta tasanar da ita hakan. Sanin bata da zab’i ne kuma yasata rumtse idanunta, tare da soma taune labb’anta, cikin zuciyarta tasoma ambatan sunan Allah Domin kuwa shikad’aine sarkin da zai taimaketa adaidai wannan lokacin. Najeeb kuwa ganin yanda ta rumtse idanunta da kuma yanda take aikin taunan lips d’inta tamkar wata zautacciya ne yasashi matsowa kusa da ita sosae, idanunsa ya k’ura mata, take yaji wani irin matsanancin tausayin ta ya cika masa zuciya, lokaci d’aya yaji gaba d’aya guiwowin jikinsa sunyi sanyi, yayinda wani irin yanayi na daban ya sauk’ar masa, ahankali ya matso gareta cikin sabon yanayin daya samu kansa aciki kuwa ya kamo hannunta tare da jawota jikinsa yayi mata wani irin runguman da saida k’ashin jikinta yayi k’ara, idanunsa wanda sukayi jajur ya lumshe lokaci d’aya ya saki wani irin ajiyar zuciya me k’arfi. Hab’arsa ya d’aura akan kafad’an Laylerh’n, wanda hakan ya bashi daman cigaba da shak’an daddad’an k’amshin dake fita ajikinta. Akaron farko kenan da ya gano cewar zuciyarsa tayi nisa wajen tausayin Laylerhn, domin yanayin daya ganta aciki yanzu yasa gaba d’aya jikinsa yayi sanyi, sam koda wasa bai tab’a tunanin cewar zuciyarsa tayi k’arfi sosae har haka awajen tausayin Laylerh’n ba. Hak’ik’a ya k’udurta aransa cewar yau zai tabbatarwa kansa da zama cikakken ango kuma Namiji, tabbas gangar jiki da zuciyarsa amatuk’ar buk’ace suke da Laylerh’n, amma kuma bayajin zai mata dole, domin bata hanyar k’arfi yakeson karb’an budurcinta ba, duba da irin k’ananan shekarunta yasa shi so da buk’atar amincewarta, domin rashin neman yardarta zai iya jawo komae, ayanzu da takasance matarsa soyayyarta yake buk’ata fiye da komai, yana da yak’inin zai samu hakanne kuma kad’ai tahanyar lallami da kuma rarrashinta, saboda yasan cewa ba abun dake jawo k’akk’arfan tsana kamar karb’an virgin d’in mace ta k’arfi, ko kuma ba’a bisa son ranta ba, bakuma yason hakan yafaru atsakaninsa da Laylerh’n, lallai dole zaiyi hak’uri adaren yau, saboda ya fahimci cewa akwae k’alubale dayawa agabansa, abu na farko kuma shine dole ne ya koyawa Laylerh’n zama tare dashi, son kasancewa dashi da kuma son yin magana dashi. Ahankali yakai bakinsa daidai saitin kunnenta,cikin yanayin sanyi had’i da karkarwar da muryarsa keyi yace. “Is okay Laylerh, i promised you bazan miki komae ba, ki daina kuka please, kawai dai nakasa control d’in kaina ne, amma Laylerh kimin alk’awarin cewa watarana zaki bani kanki cikin amincewa da kuma yarda, please Laylerh kimin wannan alk’awarin...â€? yakai k’arshen maganartasa yana me rumtse idanunsa da k’arfi saboda yanda yaji mararsa na murd’awa. Tabbas maganganun nasa sunsa jikinta matuk’ar yin sanyi, take kuma tausayin kanta dana Najeeb d’in ya kamata, domin tasan cewa K’addara ce kawae ke bibiyan rayuwarsu, shi yana sonta ita da zuciyarta kuma suna son wani, tasani cewa Maleek bugun zuciya da numfashinta ne, amma kuma Najeeb Mijinta ne, kuma yana iko da komae najikinta. Tambaya d’aya kawae take ta nanatawa azuciyarta shine ya zatayi? Najeeb kuwa jin tayi shirune yasa ahankali ya janye jikinsa daga nata, tare da mirginawa gefe ya kwanta irin kwanciyar nan ta rubda ciki, hannunsa yasa ya dafe kan maransa dake masa wani irin ciwo, har wani zugi yakeji awajen. Wasu irin hawaye ne suka silalo daga cikin idanunta, wanda kuma ita kanta batasan hawayen nata na meye bane, haryanzu tana neman hanyar da zaisa ta juri d’aukan duka way’annan nauyin akanta, ahankali ta sulale ta kwanta akan gadon tare da jawo rigarta da Najeeb din ya soma cire mata sama, dunk’ule jikinta waje d’aya tayi tare dajan tattausan wadataccen blanket d’in dake kan gadon ta rufe gaba d’aya jikinta dashi, ahankali take sakin wani irin numfashi, wanda yake fita da sautin sheshshek’an kuka. Kasancewar kuma bata cikin mood me dad’ine yasa ko mintuna 15 batayi ba bacci ya d’auketa. Duk da cewar baya cikin bargon amma yana iya jiyo sautin fitan numfashinta me had’e da sheshshek’a, yanayin yanda yaji fitan numfashinnata ne kuma yasa shi gane cewar bacci takeyi. Ahankali ya bud’e idanunsa dake alumshe, tare da juyowa ya k’urawa Bayan Laylerhn idanu, haka yakejin wani irin abu na yawo acikin zuciyarsa. Duk da cewar kuwa yanajin ciwon Mara me tsanani, amma haka dan dolensa ya daure, da Allah Yatashi taimakonsa kuwa baiwani jima ba bacci ya d’aukesa. *Washegari* 9:30 am daidai k’aran alarm d’in dake gefen had’add’en gadon ya karad’e cikin d’akin, bugawan alarm din kuwa yayi daidai da shigowar k’iran wayan dake aje gefen alarm clock d’in. K’aran daya karad’e kunnuwansanne yasa ahankali ya soma bud’e kyawawan idanunsa masu kalan maye wanda ke cike da bacci. Cikin yanayin k’osawa da k’aran yakai hannunsa ya kashe alarm d’in, akasalance ya jawo wayartasa dake ta faman tsuwa, k’ok’arin kasheta gaba d’aya yasoma yi saidai kuma ganin sunan Abbou Jaheed da yayi rubuce akan screen din wayar ne yasashi fasa kashe wayar, swiping na wajen picking call d’in yayi tare da kara wayar akan kunnensa. Abbou Jaheed kuwa jin Maleek d’in ya d’aga wayar batare da yatsaya yaji ta bakinsa ba yace. “Mekake jira da har zuwa yanzu baka fito ba?.â€? Jin tambayan da Abbou Jaheed d’in yayi masa ne yasashi d’an rumtse idanunsa, cikin muryarsa da ke d’auke da yanayin bacci yace. “Bantashi abacci ba.â€? “Badamuwata bane hakan, nabaka nan da 30 minute kazo kasameni afalona, dannayi alk’awari ba kuma zan zama mai sab’a alk’awari ba.â€? Cewar Abbou Jaheed ransa amatuk’ar b’ace, wanda jin yanayin yanda muryar Maleek d’in ya sanja, yasashi yin Tunanin ko wani abun mayen Maleek d’in ya sake sha, kashe wayartasa yayi tare da maida ita cikin aljihu, ya zauna zaman jiran zuwan Maleek d’in. Jin Abbou Jaheed ya kasha k’iranne yasashi zare wayar akunnensa, Allah Yasani maganar auren da Abbou’n yace zaiyi masa ya matuk’ar d’aga masa hankali, wanda har yake fatan ace mafarki yake bawai gaske bane. Ahankali ya yaye blanket d’in dake jikinsa tare da tashi zaune ya zuro da k’afafunsa k’asa daga kan gadon. Hannayensa yasa ya d’an murza idanunsa, kana kuma cikin yanayin kasalan da yakejin kansa aciki ya mik’e tsaye. Kamar kullum kuma kamar koda yaushe hotonta yasaba kallo Aduk sanda ya tashi daga bacci, to yanzun ma hakanne takasance, domin saida ya sauk’e idanunsa akan d’an k’aramin hotonta dake aje bisa bedside d’insa. Idanunsa ya d’an lumshe tare da sauk’e sassanyar ajiyar zuciya, tabbas ya aminta cewa kallon kyakkyawar cute face d’inta yana sama masa nutsuwa, saidai kuma akoda yaushe idan ya tuna cewar ayanzu matsayin mata take ga waninsa sai yaji gaba d’aya komae na duniyar ya daena yi masa dad’i. Cikin son kawar da duk wani tunani daga cikin zuciyarsa kaitsaye ya nufi toilet, yana shiga kuwa ya sakarwa kansa ruwa, wanka yayi tare da d’auro towel akan waist d’insa ya fito. Sanin halin Abbou Jaheed ne yasashi goge jikinsa cikin hanzari ya shags mai ajikinsa, k’arasawa gaban drawer’nsa yayi tare da ciro kayan da zai saka. Wani riga da wandon jeans masu d’an kauri yasanya ajikinsa, kasancewar ana d’an yanayin sanyi, sosae kuwa kayan suka amshi murd’add’iyar surar jikinsa, yayinda suka k’ara bayyana kyawunsa, kasancewar kuma kayannasa nada kalan dark blue ne yasashi saka wasu dark blue d’in takalma masu yanayi da sneakers shoe, dark blue d’in hulan facing cap ya saka akansa, tare da d’aura agogon Gucci ahannunsa. Sassanyan perfumed d’insa ya fesa, tare da d’aukan wayarsa yasa acikin aljihunsa, duk da cewar kuwa bayajin dadi acikin ransa, amma dole haka ya daure tare da kokarin samawa kansa nutsuwa. Yayinda acikin zuciyarsa kuwa yake mamakin cewar wae kamanshi Maleek za’ayiwa auren dole. Wani murmushi ne ya bayyana akan fuskarsa daidai lokacin da yake ficewa daga cikin dakin nasa, badan komae yayi murmushinba kuwa face ji da yayi ajikinsa cewar auren da Abbou Jaheed d’in keson d’aura masa bazae tab’a yiwuwa ba. Locking k’ofar d’akinnasa yayi, tare dasa kansa direct b’angaren Abbou Jaheed ya wuce. Yana zuwa kuwa ya samu Abbou Jaheed tsaye yana jiransa. Ganinsa yasa Abbou Jaheed soma k’are masa kallo kamar zaice wani abu kuma saiya fasa, cikin had’e fuska yace. “Muje.â€? Haka suka fito daga sashin Abbou Jaheed d’in Maleek na biye dashi abaya. Kaitsaye wajen da motar Abbou Jaheed d’in ke fake k’iran tundra suka nufa, gidan baya suka shiga dukansu, take kuwa driver’n Abbou Jaheed d’in yaja motar suka bar cikin gidan. *(Am sorry Nagajine Wllhy😰)* 1/25/21, 9:16 AM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna *Note edit* *Chapter 42* Sassanyar iskan dake hura jikinta ne yasa ta soma bud’e idanunta ahankali, samun kanta da tayi kuma cikin sabon yanayi ne yasa ahankali tasa hannunta ta shafa saman mararta da takejin na d’anyi mata ciwo kad’an, wanda kuma tun asuba da ta tashi yin sallah takejin hakan, saidai kuma yanda taji abun ya tsananta mata yanzunne yasa ta d’an rumtse idanunta tare da cizon labb’anta. D’an yunk’urawa tayi ta tashi zaune, tare da juyawa ta kalli gefenta. Rashin ganin Najeeb kwance awajenne yasata d’an soma k’arewa d’akin kallo, tare da kasa kunnuwanta ko zataji k’aran ruwa acikin toilet. Saidai kuma jin shiru babu alaman motsi wani bayan ita da take cikin d’akinne yasa ahankali ta zuro da k’afafunta k’asa daga kan gadon, tare da mik’ewa tsaye, anutse take taka k’afafunta harta k’arasa bakin kofar toilet d’in dake cikin d’akin, ahankali ta tura k’ofar toile d’in ciki tare dasa kai ta shige, kayan dake jikinta ta rage, cikin kuma yanayin sanyin da ta samu kanta aciki ta k’arasa gaban babban bathtub d’in wankan dake cikin toilet d’in. Kasancewar kuma Ana sanyi sosae ne yasa ta surka ruwan dake cikin bathtub d’in dana zafi, ganin hasken ranan da tayi ta cikin windown toilet d’inne yasa ta gane cewar safiya tayi sosae, kasancewar tun da tayi sallan asuba ta koma bacci, bata sake tashi ba kuma sae yanzu. Duk da kuwa cewar tanajin marar nata naci gaba da murd’awa, amma haka ta daure tayi wankan nata cikin nutsuwa, tana fitowa daga cikin bathtub d’in wankan kuwa taji wani irin abu me d’umi na fitowa daga jikinta, wanda ko tantama batayi cewar period d’inta ne yazo. Wanda kuma akoda yaushe idan taga period d’inta saitaji duk ba dad’i, saboda ba kad’anba yake takurata musamman ma menstrual pain d’in da takeyi wanda yake matuk’ar wahalar da’ita amma wani abun mamaki hakanan yau ganin period d’in yasa ta d’anji wani sanyi acikin zuciyarta. Bathrobe tasa ajikinta, sanin kuma bakowa adakinne yasa kaitsaye ta bud’e k’ofar bathroom d’in ta fice, direct wajen da hand bag d’inta ke ajiye ta nufa, zuge zip d’in handbag din tayi, cikin sa’a kuwa taga d’an jakan pad d’inta aciki, d’aukan pad d’innata tayi tare da komawa toilet ta kimtsa kanta, still harta sake fitowa daga toilet d’in kuwa Najeeb bai shigo cikin d’akinba. Hakan kuwa bak’aramin dad’i ya mata ba, domin matuk’ar yana cikin d’akin bazata tab’a sakewa ba. Agaban dressing mirror ta zauna, tare da bud’e body lotion d’inta me dad’in k’amshi ta shafa ajikinta, duk da cewar kuwa bata wani damuwa da kwalliya sosae ba, amma hakanan taji yau tanaso ta d’anyi light meckup akan fuskarta, cikin mintuna kad’an kuwa ta kammala kwalliyan da yayiwa fuskarta kyau sosae. Yanayin kuma yanda weather’n garin yake ne, yasa ta saka wani dogon wandon jeans da kuma baby top me d’an kauri wanda ya lafe ajikinta, ya kuma bayyana shafaffen surar cikinta. Kana ta d’aura wata denim jacket me kalan bak’i akan shigar nata, duk da cewar jacket d’in bashi da girma sosae, amma kuma zai hana mata Jin sanyi sosae. Kasancewar kuma ita d’aya ne ad’akin yasa bata wani damu da saita sanya d’ankwali ba, komawa kan gado tayi ta kwanta, tare da jan blanket ta rufe jikinta, saboda har yanzu tanajin mararta na d’an murd’awa hakan, wannan dalilin yasa ko breakfast bata nema ba tana kwanciya kuwa wani sabon bacci ya d’auketa. Tunda suka kama hanyan unguwan na Wuse Zone 3, idanunsa ke kan titunan da suke ta wucewa, tabbas azahirance kuwa idan ka kallesa zakayi tunanin cewa gaba d’aya hankali da nutsuwarsa naga titin ne, saidai kuma sam bahaka abun yake ba, tabbas idanunsa titunan suke kallo, amma tunaninsa da kuma zuciyarsa ba’anan suke ba, domin tun fitowansu daga gida abu d’aya ne ke yawo acikin tunaninsa, shine maganar Auren da Abbou Jaheed d’in yace zai masa. Sam zuciyarsa bata gaya masa gaskiya akan auren, yayinda ajikinsa kuwa yakejin kamar wata sabuwar k’addara ne ke shirin tunkarosa, k’addaran da zata sauya masa gaba d’aya rayuwa. Babban abunda yake tambayar kansa kuwa shine. “Agaba d’aya rayuwarsa tayaya zai fara zama da wata mace amatsayin matarsa? tayaya zai iya had’a shumfud’a da wata ta daban?â€? Sam bayajin yiwuwar hakan, saboda yasan so ana ginasa ne azuciya, idan kuma yayi k’arfi sai ya mamaye dukkan sassan jiki, tabbas auna mizanin abunda ka taso kanaso daban yake da wanda zakazo agaba ko kuma ayanzu, sannan kuma kowani irin soyayya takan iyayin tsuntsuwa tatashi amma Banda soyayyar da aka halittata acikin jini da tsoka, wannan so d’in baya tab’a fita har abada. Auna mizanin son da yakeyiwa Laylerh kuwa abune, me matuk’ar wahala, saboda ya gina gaba d’aya rayuwarsa ne akan soyayyarta, Hak’ik’a ya raini sonta acikin zuciyarsa tun tana k’arama, tsari yanayi dama body structure d’inta yayi masa yanda yakeso, saboda haka bayajin cewa akwae wata mace aduniyarnan da zaigani ya kwad’aitu da ita ko kuma tashiga ransa idan ba Ayshnoor d’insa ba. Idanunsa ya lumshe adaidai lokacin da yaji driver’n na danna horn d’in motar, wanda kuma hakan alamane dake nuna cewar sun iso inda zasu je. Ko minti 1 ba ayiba kuwa aka wangale musu babban gate d’in gidan dayaji had’uwa, wanda dagani kasan cewar gidan attajirin maikud’i ne. Anutse driver’n ya kutsa hancin motar cikin gidan. Jin tsayuwar motar ne kuma yasa shi bud’e idanunsa wanda suka d’an sanja kala. Daidai lokacin kuwa Alhaji Farouk wato abokin Abbou Jaheed ya k’araso wajen motar tasu da gaggawa, fuskarsa d’auke da murmushi kana kuma cikin mutuntawa ya bud’ewa Abbou Jaheed murfin motar ya fito, mik’a masa hannu Abbou Jaheed yayi sukayi musabaha. Ganin hakanne kuma yasa Maleek d’inma bud’e murfin motar ta b’angaren da yake ya fito. Kallonsa Alhaji Farouk yayi cikin sakin fuska da walwala yace. “Captain Maleek Gwani sannu da zuwa.â€? Sanin cewa Alhaji Farouk d’in abokin babansa ne, kuma mutum me mahimmanci ne awajen Abboun sa yasashi d’an bayyana murmushi akan fuskarsa, cikin muryarsa da ako yaushe take tafiya da aji yace. “Yauwa barka da gida.â€? Murmushin fuskar Alhaji Farouk d’inne ya fad’ad’a, cikin halinsu na y’an boko bawani surukunta ya mik’owa Maleek d’in hannu suka gaisa. Cikin son nuna zallan farincikin dake ransa, da kuma murnar ganinsu agidan nasa yace. “Masha Allah Bismillah mu isa daga ciki.â€? Babu musu kuwa suka rufa masa baya, saidai kuma Maleek kam ko kad’an baiso hakanba, sanin da yayi cewa idan sun shiga ciki d’in surutu su Abboun zasu tayi, shikuma Sam Ko kad’an bayason damuwa, amma gudun kada ya b’ata ran Abbou Jaheed yasashi rufa musu baya. Kaitsaye babban falon Alhaji Farouk inda yake sauk’e bakinsa na musamman suka nufa. Koda suka k’arasa cikin falon kuwa sake gaisawa sukayi, inda kuma Buzuwa wato matar Alhaji Farouk d’inkenan ta shigo suka gaisa, tun shigowarta kuwa ganin Maleek d’in yasa take ta sakin murmushi, domin dama Alhaji Farouk ya fad’a mata komai agame da had’a auren Maleek d’in da tilon Y’arsu, wanda kuma hakan bak’aramin nasara da d’aukaka zai jawo musu ba, domin sun san had’a zuri’a da Alhaji Jaheed Gwani ba k’aramin girma da k’ima zai k’ara musu awajen mutane ba. Bata kuma sake yarda da hakan ba sai ayanzu da tayi ido hud’u da Maleek d’in, wanda ta tabbatar cewa idan y’arta tasamu daman aurensa to bak’aramin sa’a tayi ba, ko shakka babu kuwa sai y’arta tazama autar mata, sannan kuma lokacin arzikin yarinyar nata ya soma, dan musamman tasa akayi mata bincike akan Maleek d’in da kuma irin tarin dukiyar da ya mallaka wanda shi kansa baisan iya adadinta ba, tabbas ya had’a komae na more rayuwar duniya, ga kyau ga to kud’i. Shikuma Maleek ganin matar da take matsayin wai uwar wacce zai aura, yasa lokaci d’aya yagano wani irin zab’ine Abbou Jaheed d’in yayi masa. Fuskarsa ya kwab’e tare da tab’e bakinsa, acikin zuciyarsa yace. “Banji ajikina cewar zan rayu da wani tsatso na gidannan ba, because a irin gidannan ba asamun choice d’ina.â€? B’angaren Buzuwa kuwa jikinta yana b’ari tasa aka cika gaban su Captain Maleek d’in da kayan sha dana ciye ciye. Saidai Maleek ko ruwa bai shaba bare ma yace zaikai wani abu bakinsa. Abbou Jaheed kuwa sanin abunda suka shirya shida abokinnasa ne yasa su mik’ewa tsaye suka fice daga cikin falon. Inda suka bar Maleek d’in zaune, M.Jay kuwa ganin sun barsa shi kad’aine yasashi zaro wayarsa k’iran iPhone12pro dake cikin aljihunsa ya soma dannawa. After 10 minutes. Ahankali aka turo k’ofar falon aka shigo, wata matashiyar budurwace wanda bazata wuce 23 years bane ta shigo, sanye take cikin wani tsadadden atamfa wanda yaji d’inkin riga da sket, ak’afanta kuwa wani uban takalmi ne me tsini, duk da cewar kuma tana da tsayi amma takalmin ya k’ara mata tsayi, yanayin yanda kayan jikinnata suka kamata ne kuma yasa d’an k’aramin surar jikinta bayyana, kaitsaye za’a iya k’iranta da fara amma ba irin farinnan na turawa ko larabawa ba farin buzaye, akan fuskarta kuwa meckup ne kwance wanda dagani kasan anb’ata lokaci ana zana shi, bata da wasu manyan ido, sannan kuma bata da tsayin hanci sosae, haka kuma bata da babban baki, tabbas ga wanda baisan kyauba idan ya ganta zai iya k’iranta da kyakkyawa, amma kuma abad’inance ba haka abun yake ba, domin kyaun nata bawani kyau bane, saidai kawae tana da yanga. Munnira kenan y’a d’aya tilo awajen Alhaji Farouk, yarinya mejin kanta da wayewa kasancewar a k’asar syprus tayi karatunta na degree. Tabbas ayangance ta shigo cikin falon tana me taunar chewing gum abakinta, yayinda take ta faman baza k’amshi, saidai kuma sam babu wani mayafin kirki ajikinta. Shigowarta cikin falon da kuma sauk’e idanunta akansa da tayi ne, yasa ta tsayawa cak yayinda taji wani irin abu mekama da shock ya shiga jikinta. Sallaman da take k’ok’arin yine ya mak’ale abakinta adaidai lokacin daya d’ago kansa, Dan ganin ko waye ya shigo cikin falon. Kusan fad’uwa Munnira tayi saboda tozali da tayi da kyakkyawar fuskar da aduniya take mafarkin ganinta face to face, fuskar da sau d’aya ta tab’a ganinta ajikina jaridar Daily Trust, fuska mafi tsadan gani da kyau, tabbas zata iya cewa tunda take aduniya bata tab’a ganin Namiji me kyau da had’uwarsa ba. “Handsomeâ€? Tafad’a acikin zuciyarta saidai kuma batasan cewa maganar nata ya fito fili ba. Kallo d’aya kawai yayiwa tsigau fiyau d’in da yagani agabansa ya kau da kai, tare da cigaba da latsa wayarsa, cikin zuciyarsa yace. “Allah kasa ba wannan tsigau fiyau’n Abbou Jaheed ya kawoni na aura ba.â€? Munnira kuwa ganin da tayi ya d’auke kansa daga kallonta ne yasa, ta k’arasowa cikin falon, cike da d’okin ganin had’add’en Namijin dake gabanta, da k’yar ta had’o kalaman bakinta wajen fad’in “Sannu da zuwa.â€? Shiru yayi tare da shareta yayi kamar baiji abunda ta fad’a d’inba. Ganin haka kuwa yasa duk saitaji guiwowinta sunyi sanyi, saidai kuma amatsayinta na gwanar rawan kai kasa yin shiru tayi cikin son jin muryarsa tace. “Ina wuniâ€? Again shareta yayi bai d’ago kansa bama bare ya amsa mata. Still kuwa Munira bata daddara ba, zama tayi akan kujeran dake facing nasa, cike dason nuna masa ita wayayyace tace. “Please say something kodai bakajin Hausa ne, nayi maka magana da English?â€? M.Jay kuwa jin abunda ta fad’a d’inne yasashi d’an dakatawa da abunda yakeyi, cikin zuciyarsa yace. “Wae English, har wannan tsigigiyar yarinyar tana da bakin turancin da zata iya min magana dashi.â€? Idanunsa ya d’an lumshe kana kuma ya bud’e su alokaci guda, batare daya damu da d’ago kai ya kalleta ba yaci gaba da danna wayarsa. Munnira kuwa abunnasa mamaki yasoma bata, cikin zuciyarta tace. “Anya kuwa ba kurma bane?â€? Da sauri kuma ta girgiza kanta, cikin son k’arfafawa kanta guiwa tace. “No nasan ba kurma bane saboda Abbana bazai tab’a kawomin kurma amatsayin wanda zan aura ba.â€? D’an gyaran muryarta tayi cikin son jawo hankalinsa tace. “Sunana Munnira, kuma Ina fata zamu kasance atare kamar yanda mahaifanmu suke fata da buri? I promise you kuma bazaka tab’a samun matsala dani ba, sannan...,â€? “Kindameni da surutu!!â€? Ya katseta daga maganan nata ta hanyar fad’in haka cikin d’an d’aga murya. Munnira kuwa amatuk’ar bazata maganan nasa ya shiga kunnenta hakanne kuwa yasa ta bud’e baki tana kallonsa, domin tabbas da farko batayi tunanin cewa da gaske yana jin hausa ba, domin harta fara tunanin idan tayi magana yanzu bae amsa mata ba to zatayi masa da turanci, still I dan bai amsa mata ba saita zuba masa idanu, dan ko za’a samata wuk’a awuyanta ace za’a yankata bata iya larabciba, abu d’aya kawai tasani akalmar rabaci shine ta’al da yellah suma kuma dan tana yawanji ana fad’a acikin series film na larabawa ne, shiyasa ta rik’e amma bayan haka batasan komae ba. Tabbas jin amon sautin muryarsa da tayi yasa ta shiga shock sosae, domin kuwa sound d’in muryarsa daban yake dana mutanen da ta saba ji. Lokaci d’aya taji wani irin matsanancin sonsa ya daki zuciyarta. “Wallahi Inasonshi.â€? Tafad’a acikin zuciyarta saidai kuma batasan maganan nata ya fito fili ba. Idanunsa ya rumtse asakamakon jin hakan daga bakinta. “Wae har k’ananan y’an mata marassa aji irin way’annan suna da zab’i?â€? Ya fad’i hakan acikin zuciyarsa adaidai lokacin dayake mik’ewa tsaye, dan bayajin zai iya cigaba da zama acikin falon, saboda yanda warin parfume d’inta ke neman hautsuna masa ciki, yeah yana son k’amshi amma bakowani irin mahaukacin k’amshi ba. Sam bayajin yarinyar ta ishesa kallo shiyasa ko juyawa baiyi ya kalleta ba, tun kallon farko kuwa da yayi mata baisake yin na biyu ba, nafarkon ma kuma yabarsa amatsayin tsautsayi ne, cikin isa da tak’ama ya fice daga cikin falon. Haka Munnira ta bud’e baki da ido tana kallonsa harya fice. Wani irin murmushi tayi cikin yanayin jin dad’i tace. “Tabbas ayanzu nasan nasamu Mijin aurena, Mijin da babu wata wacce zata sameshi saini kad’ai, wow gaskiya ni Munnira me sa’ace.â€? Tafad’a tana me mik’ewa tsaye cike da farinciki tasoma zagaye falon. Maleek kuwa yana fitowa daga cikin falon direct wajen da motarsu ke fake ya nufa, inda kuma anan jikin motar Abbou Jaheed da Alhaji Farouk ke tsaye. “Bazan tab’a auren wannan yarinyar ba mace kaman 1 babu komae na burgewa ajikinta, kai ni ko akwaima bana sonta, banason kowacce mace aduniya sai Laylerh.â€? Abunda yake fad’a acikin zuciyarsa kenan adaidai lokacin da ya k’araso inda su Abbou Jaheed d’in suke. Ganinsane yasa Alhaji Farouk washe baki, cikin jindad’i yace. “Masha Allah Kaga Munniran ko, inafatan kun daidaita.â€? Jin abunda Alhaji Farouk d’in ya fad’ane yasa shi sake had’e fuskarsa, tare da kawar da kansa gefe. Sanin halin Maleek d’in kuma da Abbou Jaheed yayine yasashi yiwa Alhaji Farouk bankwana domin dama sungama duk maganan da zasuyi. Cikin fari’a kuwa suka rabu, saidai Maleek kuwa fuskarsa atsume suka bar cikin gidan. Buzuwa Ne ta shigo cikin falon inda ta taradda Munnira nata imagine rayuwar da zatayi da Captain Maleek. Shigowarta cikin falonne kuma yasa Munnira rik’o hannunta cikin zumud’i tace. “Inasonsa Sosae Ummi inasonsa.â€? Murmushi Buzuwa tayi domin dama tasan dolene Munnira taso shi, to wayema zata k’isa. Shigowar Alhaji Farouk cikin falonne yasa suka juya suka kalleshi. Murmushi ne kwance akan fuskarsa har ya k’araso kusa da Buzuwa, jakan dake hannunsa ya mik’a mata, tare da neman waje ya zauna cikin bayyana farincikinsa afili yace. “Sadakin Munnira ne naira million d’aya 1,000,000 yanzu Alhaji Jaheed ya bada, munkuma tsaida lokaci nanda sati 2 za’ayi biki, saboda yace bayason jinkiri, b’angaren mu ma kuma babu amfanin yin jinkirin saboda ashirye muke, inason kusan rasa Captain Maleek Jaheed Gwani amatsayin suruki baban asarane, saboda haka kada mubari murasa wannan daman.â€? *(😭😭😭😭😭Hak’ik’a Inatsananin buk’atar taimakon ku, dan Allah Ina rok’onku da babban murya kutaimakawa YAYANA da addu’o’inku wallahi yana cikin halin matsanancin ciwon k’afa shekara da shekaru dan Allah Kutaimaka mana da addu’a akan Allah Yabasa Lafiya dan Allah idan kunyi sallah kuyimin wannan alfarmar dan Allah😭😭😭😭😭😭 Wallahi Burina aduniya shine naga Yayana ya samu lafiya !!)* *24January/2021* 1/28/21, 9:43 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna *Note edit* *Chapter 43* Wani irin gud’a me k’arfi Buzuwa ta sake tare da zuge zip d’in jakan dake hannunta, take kuwa mak’udan kud’ad’en dake cikin jakan suka bayyana. Murmushin dake nuna tsananin farincikin ta tayi, cikin bayyana jin dad’inta tace. “Dama ni nasan cewar banyi haihuwar banza ba, gaskiya Y’ata Munnira me sa’ace.â€? “Sosae kuwa, yanzu dae zama bata kama muba dolene mu fara shirye shiryen biki domin satin biyu kaman yanzu ne, kinsan lokaci yanzu saurin gudu ne dashi.â€? Cewar Alhaji Farouk dake k’ok’arin mik’ewa tsaye ya wuce d’akinsa dake cikin falon. Munnira kuwa ganin irin mak’udan kud’ad’en da aka kawo amatsayin sadakinta yasa ta fad’a jikin mahaifiyartata, cikin matsanancin farincikin da takejin kanta aciki tace. “Ashe burina zai cika Momy? ashe zan samu irin namijin da nake mafarki da buri?.â€? D’an tsagaitawa da maganan nata tayi tare da d’agowa ta kalli mahaifiyar tata, cike dason bayyana abunda ke cikin ranta tace. “Yana da kyau sosae Momy, agaskiya ban tab’a ganin wani Namiji me kyau irinsa ba, inasonsa Momy ina tsananin sonsa, domin na fahimci cewa aurensa zae sa na zama kamar sarauniya, zan banbanta da sauran mata, lallai zan samu future me kyau agaba, yanzu ne nagane dalilin dayasa zuciyata takasa aminta da Sadeeq, ashe rabon samun wani had’add’en gaye ne yake jirana, kai gaskiya am so so happy.â€? Tafad’a tana me kissing goshin mahaifiyar nata. Murmushin dake bayyana zallan nasara Buzuwa tayi, kamo hannun Munnira’n tayi cikin son k’arfafawa y’ar nata guiwa tace. “Insha Allah bazamu rasa shiba Munnira, bakuma zamu tsaya sanyin jiki ba daga yau d’innan zamu fara shirye shiryen biki, domin so nake muyi biki irin wanda ba’a tab’a yinsa acikin garin Abuja ba, gaba d’aya sati biyunnan zamu sharesa acikin hidiman biki, tun yanzu kuwa zan fara sanar da y’an uwa da kuma abokan arziki.â€? Murmushin jin dad’i Munnira tayi domin jin abunda mahaifiyartata ta fad’a yasa taji zuciyarta tayi sanyi, tare kuma da k’arajin son Maleek d’in acikin ranta. Haka dae suka zauna ita da mahaifiyarta ta suka shiga tsara yanda suke so hidiman bikin ya kasance. Laylerh. Sama da 30 minute ta d’auka kwance akan makeken gadonnata tana ta juyi tare da murk’ususu, gaba d’aya batajin dad’in komae, saboda zuwa yanzu ciwon da marar nata keyi ya tsananta sosai. Ahankali ta zuro da k’afafunta k’asa daga kan gadon, yunk’urin mik’ewa tsaye ta somayi amma kuma jin yanda marar nata ya rik’e waje d’aya ne yasa ta d’an rumtse idanunta, tare da danne jajayen labb’anta, cikin son daure ciwon da takeji d’in tayi yunk’urin daidaita nutsuwarta tare da mik’ewa tsaye, hannunta ta d’aura adaidai saman mararta anutse ta soma taka k’afafunta zuwa gaban makeken drawern dake cikin d’akin, wani hulan turban ta d’auka tasa akanta, wanda hakan yasa dogon gashin dake kanta, ya sake bajewa akan gadon bayanta. Ahankali ta k’arasa bakin k’ofar d’akin, tare da d’aura hannunta akan handle d’in k’ofar, cikin yanayin sanyin daya rusketa ta bud’e k’ofar ta fice gaba d’aya daga cikin d’akin. Kasancewar kuma batajin dad’in jikinta ne yasa cikin yanayin sand’a ta k’araso cikin had’add’en falon nata, wanda aka k’awatasa da had’add’un kayan furnitures masu kyau da tsada, k’amshin turaren Najeeb d’in daya daki hancinta ne yasata d’an lumshe idanunta tare kuma da bud’esu alokaci guda, tabbas taji k’amshinsa amma kuma ko alamarsa bata gani acikin falon ba. D’an soma k’arewa falonnata kallo tayi, tare kuma da tunanin inda Najeeb d’in ya tafi, domin kuwa tun tashinta bata sashi acikin idanunta ba, ajiyar zuciya ta sauk’e batare kuma da ta kula da kayan break fast d’in daya ajiyemata akan dining table d’in dake cikin falon nasu ba, tasa kai ta fice. Saboda yanayin yanda takejin jikinnata yasa ta kwad’aita dason jin d’umin rana, dan sanyi akeyi sosai, ya waitan jin sanyin nata kuma ya k’arune saboda wani irin zazzab’i na daban da yake k’ok’arin kamata. Ahaka kuma tana tafiya ahankali har ta iso babban compound d’in gidan. Wanda kwata kwata yau d’in babu yalwan mutane acikinsa, domin dama yawanci soldiers d’in M.Jay ne, wanda yanzu duk sun koma bakin aiyyukansu, saura y’an tsiraru masu kula dashi ne kawae suka rage. Ayanayin da takejin kanta ne yasa sam bata damu da irin shigar riga da wandon dake jikinta ba, kaitsaye ya wuce inda M.Jay d’in ke parking cars d’insa, kasancewar wajen ya d’anfi rana shiyasa ta zab’i zama anan d’in ko hakan zai rage mata sanyi da kuma ciwon da takeji, anan kuwa gaban wata had’add’iyar corolla d’insa ta tsugunna tare dasa tafukan hannayenta ta rufe fuskarta. B’angaren Captain kuwa tunda suka baro gidan Alhaji Farouk d’in ya kasa sakin rai da fuskarsa, hakanan yakejin wani irin k’unci acikin zuciyarsa, yayinda gaba d’aya takaicin yarinyar da ake k’ok’arin lik’a masa dan ya aura yabi ya cika masa zuciya, domin kwata kwata baiyi tunanin cewa irin wannan zab’in Abbou Jaheed zaiyi masa ba, shin wai ma tayaya zai fahimtar da Abbou Jaheed cewar agaba d’aya rayuwarsa bayason kowacce irin mace idan ba Laylerh ba? Hak’ik’a baya mafarki da burin mallakan wata na daban arayuwarsa, so da k’auna acikin zuciyarsa guda d’aya ne kuma ya riga daya bawa Laylerh su, duk da cewar bai sameta amatsayin mata ba kuwa soyayyarta bazata tab’a fita daga cikin zuciyarsa ba, tabbas yasan cewa ayanzu cigaba da tunani ko kuma muradin Laylerh zunubi ne agaresa, amma kuma bashi da ikon hana kansa sonta, tabbas soyayyarta acikin jini da tsokansa take, haka kuma halittaciyar abace da aka halicceta tun shekaru masu yawa da suka shud’e, yayarda cewa soyayyar Laylerh k’addarace agaresa, yayarda ya d’auki hakan amatsayin k’addara, daga haka kuma baya fatan wata sabuwar k’addaran ta sake shigowa rayuwarsa. Arayuwa Laylerh yaso kuma ita zaicigaba da so har zuwa k’arshen rayuwarsa. Jin wani irin burkin da drivern ya taka ne yasashi d’ago kansa dake duk’e, ganinsu da yayi agaban tamfatsetsen gate d’in gidan nasu ne yasashi maida idanunsa ya lumshe. Akasalance yasa hannu ya bud’e murfin motar yafice, kasancewar tun fitowarsu daga gidan Alhaji Farouk Abbou Jaheed ya sanar dashi cewa zasu sauk’eshi abakin gate ne dan zai wuce office. Hakan kuwa akayi domin yana fita daga cikin motar Abbou Jaheed yasa drivern yaja motar suka bar wajen. Ahankali yasa hannu ya tura y’ar k’aramar k’ofar dake jikin gate d’in. Maigadi kuwa dake zaune jin alaman za’a shigo cikin gidanne yasashi tashi azabure cikin fad’a fad’a yace. “Waye haka yake tab’a mana k’ofa.....â€? Sauran maganganun dake cikin bakinnasa ne suka mak’ale asakamakon ganin Maleek d’in da yayi, cikin sauri ya k’ame jikinsa waje d’aya, duk da cewar kuwa shid’in ba soja bane, amma yayi hakanne dan girmamawa da kuma son kare kansa, kasancewar tunda yake agidan baitab’a ganin murmushin Maleek d’inba, wannan dalilin yasa yake masifar tsoronsa, domin yasan irinsune da idan suka tashi lokaci d’aya suke raba k’ashin mutum gida biyu, abu me sauk’ine shiga huruminsu yasa su b’abb’allaka. “Barka da dawowa Sir.â€? Ya fad’a cikin yin k’asa da murya, domin a yanda yaga fuskar M.Jay d’in amurtuk’e, lashakka zai iya bindigesa ma. Duk da cewar kuwa baya cikin mood me dad’i, amma haka yasamu kansa da jinjinawa gateman d’in kai, alaman ya amsa gaisuwar tasa, wanda yayi hakanne kuma saboda sam wulak’anta mutane baya d’aya daga cikin halayyarsa, saidai wanda ya zubar da kansa, yasani cewa shi miskiline na k’arshe sannan babu ruwansa da rayuwar kowa, amma kuma baya wulak’anta na k’asa dashi, hakan kuma ya zame masa d’abi’a da kuma al’ada because zuciyarsa akwae rauni sosai, shi mutum ne me matuk’ar tausayi, saidai kuma amma tausayin nasa ba abayyane yake ba, yakanyi ne kawae idan yanayi yazo da hakan. Da kallo gateman d’in ya bisa, yayinda shi kuma cikin takunsa na isa, ya k’arasa shigowa cikin gidan, kaitsaye part d’insa ya so nufa, amma kuma saidai tunawa da yayi cewar yau tun safe baiyi training bane yasashi fasa shiga b’angaren nasa kaitsaye ya juya akalan tafiyannasa zuwa inda yake aje motocinsa. Tunkafun ya k’araso wajen kuwa ya gama yankewa kansa hukunci cewar, babbar Corolla d’insa zai hau, kasancewar tunda aka kawo masa ita sau uku kawai ya tab’a hawanta, duk da kuwa cewar motar me tsadace sosae amma baiwani damu dason shiganta ba. Isowarsa jikin motar ne kuma idanunsa suka sauk’a akan Laylerh wanda har yanzu ke durk’ushe awajen yayinda tafukan hannunta ke kan fuskarta. Sauk’e idanunsa akanta da yayi kuwa yayi daidai da bugawar zuciyarsa, yayinda kuma atake yaji wani irin sanyi na ratsa gaba d’aya ilahirin jikinsa, har zuwa k’asan k’afarsa, wani irin abu da yaji acikin zuciyarsa ne yasashi d’an lumshe idanunsa tare da jan wani dogon numfashi. “Metakeyi anan?.â€? Yayiwa kansa tambayar yana me sake bud’e idanunsa ya sauk’esu akanta. “Tana da damuwa.â€? Cewar zuciyarsa wanda akoda yaushe take jib’antan al’amuran Laylerh’n. Labb’ansa yad’an cije tare da zuba mata, tsumammun idanunsa, take kuwa yanayin na yanzu ya juye masa zuwa wasu shekaru dasuka wuce, wani lokaci daya saba ganinta tana zaune cikin kad’aici da k’unci, lokacin da take kuka. Tabbas Laylerh GARKUWA take so, bawai iya miji kad’ai ba, dole kafun tasamu wanda zai sata farinciki sai tasamu wanda yasan gaba d’aya yanayinta. Wanda yasan kukanta ya kuma san dariyarta, tabbas ya taso acikin maraici amma kuma maraicin Laylerh yafi komai tsaya masa arai, yanajin matsanancin tausayinta fiye da kowa da komai, har idan aka cire soyayya irinta So da So, to k’aunan da yakeyiwa Laylerh ta y’an uwantaka tana da matuk’ar yawa, saboda yayi imani cewa akanta zai iyaba da komai nasa, ciki kuwa harda rayuwarsa, kamar yanda baya iya manta sunansa, haka ako da yaushe baya manta kalaman da Mahaifiyarta ke fad’a masa ashekarun baya, koda yaushe cewa take zata bar masa Laylerh ya kula mata da ita, ya sama mata farinciki marar yankewa, domin Laylerh tasace har abada, ko da kuwa wata k’addara tasa ya rasata, wata k’addara zata sake had’asu. Tabbas akullum yana tuna wannan maganganun, wanda suke sa yaji zuciyarsa tayi matuk’ar rauni sosae, yanayin idanunsa ne suka sanja launi, wanda kuma hakan alamace dake bayyana asalin hak’ik’anin abunda ke cikin zuciyarsa. Ahankali ya sake murfin motar dake hannunsa, cikin yanayin sanyi yayi takun da baiwuce taku hud’u ba, ya iso gareta. Tsayawa akanta yayi duk da cewar kuwa yanajin zuciyarsa na bugawa sosae, haka ya d’aure ya d’an rank’wafo kanta. Almost 2 minute yanason had’a kalman sunanta abakinsa, amma ya kasa, hakanan yaji harshensa ya masa nauyi, cikin sabon yanayin daya samu kansa aciki, ya d’aura hannunsa adaidai kan nata hannun, ahankali cikin wata irin murya me kama da rad’a ya k’ira sunanta. Tabbas taji motsin mutum akusa da ita, saidai kuma kwata kwata bata kawo aranta cewar shi d’in bane, duk da cewar kuwa dadddad’an k’amshinsa ya kawowa hancinta ziyara amma tayi tunanin cewa kwad’aituwa da tayi dason jin k’amshin nasa ne yasa ta jin hakan. Sauk’an sautin muryarsa acikin kunnuwanta kuwa shiyasa duk taji tsikar jikinta sun mimmik’e, ahankali ta d’an janye tafukan hannunta daga kan fuskar nata. Cikin sa’a kuwa tajefa idanunta acikin nasa idanun, idanun da har abada bazasu tab’a daina yi mata gizo ba, idanun da suka zama tamkar sinadari acikin rayuwarta. Sam bazata iya jurewa kallon cikin rikitattun idanunsa dake sauya mata tunani akoda yaushe ba, wani irin fitinannen yanayin da ta samu kanta aciki ne kuma yasata d’an lumshe idanunta, wanda hakan da tayin kuma ya bawa hawayen dake cikin idanun nata daman gangarowa kan k’uncinta. Maleek kuwa ganin hawayen da yayi akan fuskarta ne, yasa shi rumtse idanunsa, batare kuma daya bud’e idanun nasa ba, da muryarsa wanda baya fita sosae yace. “Me yake damunki?.â€? Jin tambayan da yayi mata d’inne kuma yasa ahankali ta bud’e idanunta, masu d’auke da zallan yanayin shagwab’a, wuyanta ta karyar gefe tare da d’an soma mamul mamul da bakinta, dagani kasan ba iya ciwo ne ke damunta ba harma da zallan shagwab’a. Ganin kuma yanda takeyi da bakinnata ne yasa shi gane irin yanayin da take ciki, ahankali ya sauk’e ajiyar zuciya me tafiya da jan numfashi. Hakanan yaji kaman ya jawota jikinsa yayi mata kyakkyawan hugging ko hakan zaisa ta samu relief daga damuwan dake cin zuciyarta, saidai kuma bashida iko da kuma daman hakan. Hannunsa dake kan fuskarta ya janye, cikin son daidaita nutsuwarsa yace. “Oum Ayush na k’iranki.â€? Yanayin yanda ya fad’i maganar yana me juya bayansa ne yasa ta k’ura masa ido, domin kuwa bak’aramin kyau taga yayi mata acikin sigar yanayin maganar tasa ba. Shikuwa Maleek ya fad’i hakanne dan rage mata damuwa, musamman yasan cewa idan taje wajen Oum Ayush bazata barta ta zauna da damuwa aranta haka ba, duk da cewa k’arya ba d’abi’arsa bane, amma gashi akanta dan dolensa saida yayi. Ko juyowa kuwa baiyiba haka ya shige cikin motarsa. Ganin hakan kuwa yasa ta mik’e tsaye duk da cewar kuwa har yanzu tanajin ciwon marar na damunta, amma ganinsa da tayi yanzu yasa tanemi kaso 40 na daga cikin ciwon nata ta rasa, dan kafun yanzu ko mik’ewa da kyau batayi amma gashi yanzu ta mik’e. Asanyaye ta juya tare da kama hanyar sashin Oum Ayush d’in, dan amsa k’iranta kamar yanda ya fad’a mata. Murfin motar tasa ya mayar ya rufe tare da bin bayanta da idanunsa masu d’auke da matsanancin soyayyarta, kasancewar sai ayanzune ma ya lura da shigar dake jikinta yasashi d’an lumshe idanunsa, saboda sauk’a akan had’add’iyar surar jikinta da sukayi, yasa shi jin wani iri ajikinsa. Take kuma wani abu me kama da matsanancin kishi ya tokare masa k’irji. Saidai kuma babu yanda ya iya, dole haka ya ja motar tasa da reverse yabar wajen. Laylerh kuwa direct sashin Oum Ayush d’in ta nufa. Ahankali ta murd’a handle d’in k’ofar falon ta shiga, bakinta d’auke da sallama. Shigowar nata cikin falon kuwa yayi daidai da fitowar Oum Ayush daga cikin d’aki tana waya. Saidai kuma ganin Laylerhn yasa bata wani ja wayan yayi tsayi ba ta kashe. Kallon Laylerh’n tayi cikin kulawa tace. “Yau amarya ne kuma da yawo.â€? D’an K’aramin bakinta ta turo gaba, sakamakon Jin da tayi Oum Ayush d’in ta k’irata da sunan amarya. Saidai kuma ganin Oum Ayush d’in acikin farinciki da tayi ne yasa ta neman waje ta zauna, cikin halin nata na shagwab’a tace. “Oum Ayush gani, amma naga kamar kina cikin farinciki sosai, Allah Yasa Abbou Kareem ne yace bazaku sake komawa wata k’asa ba anan zaku ci gaba da zama.â€? Jin abunda Laylerh’n ta fad’a yasa Oum Ayush sakin murmushi, had’e da neman waje itama ta zauna, cikin nuna jin dad’in labarin dake bakin ta kuwa tace. “Ko d’aya ba abunda kike tunani bane, domin yanzu nagama waya da Abbou’nki (Abbou Jaheed) yace Nafara had’a kayan lefe domin nanda sati biyu masu zuwa auren Yayanki yau yaje yaga yarinya ta masa kuma har anbada sadaki.â€? *(Chab gaskia akwae biki ashe yarinyar ma ta masa amma bamuda labari😹 team Maleek kunshirya kuwa? Gaskia yau comment nake bukata dan inason sanin ko kun shiryawa hakan)* 1/31/21, 9:06 PM - Ummi Tandama: *L.M* *Writting By* fatymasardauna *Note Edit* *Chapter 44* A wani irin yanayi taji sauk’an kalaman Oum Ayush d’in acikin kunnuwanta, wanda kuma hakanne yasa tayi saurin d’ago kai ta kalli Oum d’in, domin hakanan taji kaman kunnuwanta basu jiye mata gaskiyar abunda Oum Ayush d’in ta fad’a ba. Lokaci d’aya kuma tasamu kanta cikin tsinkewar zuciya, da kuma tarin fargaba, had’i da k’unan k’irji, yanayin yanda take kallon Oum Ayush d’inne yasa itama Oum d’in tsayawa tana kallon ta. Cikin muryarta wanda yayi sanyi sosae tace. “Aure kuma Oum auren waye?â€? Jin tambayan da Laylerh’n tayi matane yasa ta sakin murmushi, batare kuma da ta lura da halin da Laylerh’n ta shiga asakamakon jin maganan nata ba tace. “Auren Maleek mana kodai bakiji abunda na fad’a da kyau bane, ko bayan shi kina da wani yayane?.â€? D’an tsagaitawa da maganan tayi ta hanyar d’aukan fruit juice d’in dake gabanta ta d’anyi sipping kad’an, fuskarta d’auke da murmushi tace. “Tabbas naji dad’in wannan al’amarin domin kuwa batun yau ba nafahimci cewa, rashin mace akusa da Maleek shiyasa duk ya zama wani k’aton miskili, baidamu da kowa ba, bayason kowa yasan damuwarsa, koda kuwa zai shekara acikin k’unci bazai tab’a furtawa ba, shi kad’ai yake shanye duk wata damuwarsa komin d’acinta, da yardar Allah Yanzu komae zaizo da sauk’i, saboda ko ba komai matarsa zata zama k’awa kuma abokiyar d’ebe masa kewa.â€? Idanunta wanda suka ciko da k’walla ta rumtse, ahankali kuma ta had’e labb’an bakinta waje d’aya ta taune su, hak’ik’a sosae maganganun Oum Ayush d’in suka daki zuciyarta, yayinda kuma sukayi fatali da duk wata nutsuwarta. “Zaiyi aure? hakan na nufin cewa lallai tilas zai rayu da wata kenan amatsayin matarsa? shin dagaske ne kuma abunda Oum Ayush ta fad’a na cewar ya amince da wata tazamo mata, kuma abokiyar rayuwarsa?.â€? Abunda zuciyarta ta tambayeta kenan wanda ahak’ik’anin gaskiya bata da amsar sa. Lallai shigowarta cikin barayin Oum Ayush d’in ya jawo mata tashin hankali, domin kuwa maganganun da taji daga bakin Oum Ayush ba k’aramin gigita mata tunani sukayi ba, wanda har hakan yasa hawayen dake cikin idanunta kasa control d’in kansu, saida suka gangaro kan k’uncinta, lokaci d’aya kuma taji wani irin masifaffen sanyi na shiga jikinta, yayinda kuma har yanzu bugun zuciyarta ya kasa dawowa normal. D’ago kai Oum Ayush dake faman danna wayarta tayi, asakamakon jin Laylerh’n tayi shiru ne yasa ta d’an gyara zamanta, cikin kulawa ta k’ira sunanta, tare dason ganin fuskar Laylerh’n kasancewar ta d’an bata baya kad’an. Laylerh kuwa jin da tayi Oum Ayush d’in ta k’ira sunanta ne, yasa cikin sauri ta kai hannu ta share hawayen dake kwance akan fuskarta, ahankali ta juyo da kanta ta fuskanci Oum Ayush d’in, saidai kuma duk da cewar ta goge hawayen nata hakan baihana Oum Ayush fahimtar cewa Laylerh’n kuka tayi ba. D’anjim tayi tare da kafe Laylerh’n da ido,domin kuwa so take ta fahimci wani abu daga gareta. Ganin hakanne kuma yasa Laylerh yin k’asa da kanta, asanyaye ta soma wasa da y’an yatsun hannunta. Murmushin da yake iya kan labb’an baki Oum Ayush tayi, domin dama tasan dole hakan zai iya faruwa, wannan dalilinne ma yasa tafad’awa Laylerh’n cewa Maleek ya yaba da zab’in da Abbou Jaheed yayi masa, domin ta hakanne kad’ai take ganin cewa Laylerh’n zata saduda ta cire Maleek daga cikin ranta, saboda ci gaba da rayuwa da sonsa acikin zuciyarta babban haramci ne saboda tana da aure. “Tunanin me kike?.â€? Oum Ayush ta fad’a ta hanyar katseta daga tunanin da take. “Babu.â€? Ta fad’a asanyaye tana me wasa da y’an yatsun hannunta. “To yayi kyau, amma meyasa kika baro Najeeb shikad’ai kika taho nan?â€? Oum Ayush ta fad’i hakan tana me sake zubawa Laylerh’n idanu. Shagwab’abbiy’ar fuskarta ta kwab’e cikin muryarta dake d’an rawa tace. “Bayanan bansan inda yake ba, kuma ba Yah M.Jay ne yace nazo kina k’irana ba.â€? Idanu Oum Ayush ta zaro waje, cikin yanayin mamaki tace. “Ni nace ina k’iranki?.â€? “Eh mana haka Yah M.jay ya fad’a.â€? Ta fad’i hakan tana me d’an mammatse cinyoyinta, saboda yanda taji ciwon marar nata na neman dawowa. Shiru Oum Ayush tayi ta kasa cewa komae, saboda Jin abunda Laylerh’n ta fad’a ya d’an sata mamaki kad’an, saidai kuma rashin sanin dalilin da yasa Maleek d’in yayi hakan yasa, ta sauk’e ajiyar zuciya. Gyara zamanta tayi had’e da fuskantar laylerh’n cikin yanayin sanyi ta k’ira sunanta tare da kamo hannayenta, anutse ta yanda ta tabbatar da cewa Laylerh’n zata fahimceta tace. “Kada ki bari koda wasa damuwa ko k’unci suyi tasiri acikin rayuwarki Laylerh, tabbas nasan halin da kuke ciki dukanku keda Maleek, amma hakan bawai yana nufin akoda yaushe kuyita biyewa son zuciyarku bane, hak’ik’a nasan zuciyarki na sak’a miki abubuwa da yawa akan d’an uwanki Maleek, amma komai zai faru dake Laylerh ki daure, kada wani abu na daban ya hanaki kulawa ko bawa mijinki hakk’insa, domin yin hakan zaisa Allah Yayi fushi dake, sannan kuma nasan zakiji ba dad’i saboda Maleek zaiyi aure, amma inaso kusani aduniya babu wani d’an Adam da yake da ikon yin abu dan kansa, komai Allah Ne ke tsarawa bawansa, sannan babu wani me iya canja k’addara, abunda Allah ya tsara kuma ya hukunta shine kawai ke faruwa, sannan ako yaushe ki rik’e cewar saudayawa bako wani abu da kakeso kake samu ba.â€? D’an numfasawa da maganan nata tayi, kana kuma cikin sakeyin k’asa da murya tace. “Babu buk’atar na tsaya tambayanki akan hakk’in Najeeb dake kanki, shid’in Mijinki ne, idan har baki basa hakk’insa dake kanki ba watace daban zata basa? Tabbas Najeeb Namiji ne me nutsuwa, dan Allah Laylerh kada kiyi gangancin rasa Namiji me nagarta kaman Najeeb, domin samun kamarsa acikin sauran maza ba abu bane me sauk’i, saboda haka ki tashi ki koma d’akin ki, ki kuma aikata duk abunda Najeeb ya umarceki dashi, matuk’ar bai sab’awa Allah ba, ya kamata kuma kisan cewa yanzu ba lokaci ne da zaki tsaya kuka ko damuwa ba, kamata yayi kimanta komai, domin damuwarki bazae tab’a sanja komae ba.â€? Takai k’arshen maganan nata tana me d’an bubbuga kafad’un Laylerh’n, wanda tuni sabin hawaye sun sake cika idanunta. K’asa tayi da kanta ahankali tare dasa hak’waranta ta datse labb’anta, hak’ik’a ayanzun ita kad’ai tasan abunda takeji acikin zuciyarta, so take tayi kuka sosae dan rage rad’ad’i da kuma zafin abunda takeji acikin zuciyarta. Saidai kuma awannan karon sam bataso Oum Ayush tasake ganin hawayenta, dan faruwar hakan alamace dake nuna gazawarta, sam ita kuma bata fata hakan yakasance. Ahankali kuma cikin yanayin sanyi ta zare hannayenta daga cikin na Oum Ayush d’in. ********************** ? ************************** ********** Ai Hausa Novels **************** *************************? ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ? ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ? ************************** Sanin da tayi kuma cewa idan tace zatayi magana wani sabon kukane zai zo mata babu controll yasa ta jan bakinta tayi shiru, asanyaye ta mik’e daga zaunen da take, batare kuma da ta kalli Oum Ayush ko ta sake cewa wani abuba kaitsaye ta nufi hanyar fita daga cikin falon. Da kallo me d’auke da tsananin tausayi Oum Ayush ta bita, harta fice daga cikin falon kuwa bata d’auke kanta ba. Ajiyar zuciya ta sauk’e tare dasa hannayenta ta tallafi hab’arta, sam takasa gano wace irin soyayya ce haka, me k’arfin gaske da ke tsakanin Laylerh da Maleek d’in, saboda zuwa yanzu al’amarin nasu sosai yake bata mamaki, ita dai addu’a da kuma fatanta d’aya shine kada Allah Yasa watarana Najeeb yafahimci hakan, harta kaisa ga rabuwa da Laylerh’n ko kuma ya fara yi musu mummunan zargi. Laylerh kuwa tun fitowarta daga sashin Oum Ayush d’in tafiya kawai take tana jefa k’afafunta batare da tasan inda take takawa ba, hak’ik’a abu d’aya ne keyi mata yawo acikin ranta shine auren Maleek, hakanan taji duk wata nutsuwarta ta k’aurace mata tunda taji batun auren nasa, yayinda a gefe guda kuwa kalaman Oum Ayush ne ke yawo acikin k’wak’walwarta. Da tunani kala kala acikin ranta haka ta iso part d’in su. Ahankali ta tura k’ofar falon tashiga, kamar kuwa dama hawayen dake cikin idanunta jira suke ta shigo cikin falon, take suka soma gangarowa kaman ana turosu. Maida k’ofar tayi ta rufe, ahankali kuma ta zame ta zauna abakin k’ofar dab’as. Tayaya ma zata iya jure duk way’annan matsalolin? Tayaya zata iya cire soyayyar Maleek acikin jikinta? Soyayyar da ta zame mata kamar numfashi, soyayyar da ta zama itace gaba d’aya rayuwarta, lallai tayi imani cewa koda kashe ta za’ayi har abada bazata tab’a iya daina so da tunanin Maleek ba, domin saida tunaninsa kad’ai take samun nutsuwa, tunaninsa ne abincin ruhinta, yayinda kuma akullum idan ta ganshi take k’ara jin matsanancin soyayyarsa na k’ara shiga zuciyarta. Asanyaye sautin sheshshek’an kukanta ya fara fitowa, saboda takai wani matakin da bazata iya jurewa ba. “LAYLERH!â€? Najeeb dake tsaye tun d’azu acikin falon ya k’ira sunanta, da muryarsa wacce tayi sanyi sosae, domin tun shigowarta cikin falon yake tsaye abakin dining table, saboda dawowansa shima kenan, ganin kuma food flask d’in abincin daya ajiye mata a yanda ya barshi ne, yasashi k’arasowa wajen ya duba dan yaga ko taci abincin. Jin amo da kuma sautin muryarsa acikin kunnuwanta ne yasa tayi saurin bud’e idanunta wanda suka b’aci da hawaye, saboda kwata kwata bata kawo aranta cewar akwae wani acikin falon bayan itaba Ahankali ta janye idanunta daga kallon da yake mata, tare da sunkuyar da kanta k’asa. Shikuwa Najeeb anutse ya shiga takowa zuwa gareta, har ya k’araso inda take kuwa bata sake d’ago kae ta kalleshi ba. Isowarsa kusa da ita ne kuma yasashi d’an durk’usawa agabanta, cikin yanayin sanyi yasa hannayensa ya d’ago hab’arta, hakanne kuwa ya bashi daman kallo full face d’inta. Ahankali yasa d’ayan hannunsa ya shafi gefen fuskarta. “Me yake da munki?â€? Ya fad’a asanyaye tare dasa hannayensa ya share mata hawayen dake mak’ale atsakankanin eye lashes d’inta. “Babu.â€? Ta fad’a da k’yar cikin muryar ta dake fitar da sheshshek’a. Ahankali ya maida hannayensa kan kafad’unta ya d’agota saboda dama yasan cewa ba lallaine ta fad’a masa gaskiya da kuma hak’ik’anin abunda ke damunta ba. K’ok’arin mik’ar da ita tsaye yayi ta hanyar rik’o hannunta, ahankali yajawota zuwa tsakiyar falon. Zama yayi akan d’aya daga cikin kujerun falon, still kuma hannunsa na rik’e da nata ya jawota ta fad’a jikinsa. Hannayensa duka biyu yasa yayi hugging d’inta. Ahankali ya kawo bakinsa daidai saitin kunnenta, cike da kulawa yace. “Meyasa har yanzu bakiyi breakfast ba, kodai baki ga kayan breakfast d’in dana ajiye miki bane?â€? Yanayin yanda yayi mata tambayan cikin rad’a ne yasa ta sake shagwab’e fuska, y’an yatsun hannunta ta shiga murzawa cikin muryarta da bata fita sosae tace. “Nak’oshi ne.â€? “Me kikaci da har yasa kika k’oshi haka? bakisan cewa rashin cin abinci yana sa mutum ya kamu da ulcer ba? koda yake ma duk ba wannan ba, meyasa meki kike kuka? saboda na tabbata bazakiyi kuka haka kawae babu wani daliliba, fad’amin idan kuma bankai na sani bane shikenan.â€? Jin abunda ya fad’a d’inne yasa ahankali ta d’ago kai ta kalleshi, ganin kuma shid’in ma ita yake kallo ne yasa tayi k’asa da idanunta, tabbas baicancanci shariya ko k’arya awajen ta ba, amma kuma saidai wani lokaci bisa dole ake aje gaskiya ayi k’arya, musamman idan akayi duba da cewar fad’an gaskiyan kan iya ruguza komai. “Marana ne yake ciwo.â€? Ta fad’a atak’aice domin gudun kada ya gano cewa ba gaskiya ta fad’a masa ba. “Meya samu marar naki yake ciwo?â€? Ya jefo mata tambayar da sam batayi tsammanin jinta daga garesa ba, hakan yasa ta kau da kanta gefe, Dan ayanzu kam bata da amsar da zata basa. Gane hakan da yayine kuma yasa baisake tambayar taba, saima tashi da yayi ya k’arasa gaban dining table d’in, da kansa ya had’o mata breakfast d’in acikin plate. Zuwa yayi har gabanta ya zauna, tare da sata agaba dole saida yaga ta d’anci abincin kafun ya k’yaleta. Itakuwa Laylerh anan cikin falon ta kwanta, haka zuciyarta ta dinga sak’a mata abubuwa da yawa acikin ranta, cikin mintuna k’alilan kuwa bacci b’arawo ya d’auketa. Tunda tafara baccin kuwa Najeeb ya tsura mata mayun idanunsa, baya ko k’iftawa, tunani daban daban kawai yake tayi acikin zuciyarsa, shima ahaka bacci ya d’aukesa. Har yayi baccin nasa ya farka kuwa Laylerh bata tashi ba, wanka ya je yayi tare da sake shirya kansa cikin shiga me kyau, batare kuma da ya ta she ta ba ya fice daga cikin gidan na gaba d’aya, saboda ya lura zamansa atare da Laylerh’n shine ke k’ara haukatar dashi yayi ta jin feelings. Laylerh kam bacci tayi sosae dan sai wajajen 3 tatashi, hakanan taji duk duniyar batayi mata dad’i. Wanka ta sakeyi inda ta shirya kanta cikin kaya marassa nauyi. Atak’aice dai haka ta k’are gaba d’aya wuninta na wannan rana batajin dad’in yanayinta, domin kuwa da zaran tatuno cewar Maleek zaiyi aure nanda 2 weeks saitaji komae ya tsaya mata. Ahaka har dare yayi, yau dai kam Najeeb ko kusa da ita baizoba akan doguwar kujeran dake cikin d’akin yayi kwanciyarsa saboda ya lura dagaske cewa Laylerh’n batajin dad’i, idan ya matso kusa da ita kuwa ba k’aramin azabtuwa yakeyi ba, wannan dalili yasashi samawa kansa nutsuwa ya kwanta akan kujera. Laylerh kuwa sosae taji dad’in hakan saboda yau d’in duk adagule take. Washegari. Awayewan garin na yau ne kuma su Abbou Jaheed da Oum Ayush suka tashi da shirye shiryen auren Maleek haik’an, inda Oum Ayush ta shiga shirye shiryen abubuwan da ya kamata ayi, b’angaren kayan lefe kuwa tunjiya ta bada order’nsu wa k’awarta Hajiya Nana dake can k’asar Dubai, wanda kuma nan da kwana hud’u kayan zasu iso. (kuyi hakuri muna biki bansamu zama ba shiyasa, wannan page dinma atsatstsaye nayi ba editing.) 29January/2021 2/1/21, 3:27 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna *Chapter 45* Wayarsa k’irar Samsung wanda ke aje bisa saman wani had’add’en table ne ke ta faman kuwa, da’alama dae k’iran wayannasa ake babu k’akk’autawa. Ahankali ya d’ago kansa daga durk’uson da yake, wanda hakanne kuma ya bani daman kallon idanunsa wanda sukayi jajur, kallo d’aya kawai zakayi masa ka fuskanci cewa d’auke yake da damuwa me tarin yawa. Kasancewar yanzu kusan sama da 40min kenan da ya d’auka zaune awajen, yayinda ya duk’ar da kansa k’asa. Hakanan yakejin gaba d’aya duniyar batayi masa dad’i, yayinda ajikinsa yakejin sauyin yanaji, wanda hakan ke yawan haifar masa da fad’uwar gaba, saboda yanda yakejin wani abu na daban na neman haukata tunaninsa, yayinda yakeji ajikinsa cewar wani abu na daban na shirin tunkaro rayuwarsa. Daga gefe guda na zuciyarsa kuwa tunani da kuma k’aunar Laylerh ne ke hura masa wuta, wanda har hakan yasa yakejin kamar zuciyar tasa zata buga. D’ago kansa yayi tare da jingina bayansa ajikin had’add’iyar kujeran da yake kai, wanda ke cikin katafaren office d’insa. Hannunsa yakai kan wayarsa dake ta faman tsuwa, batare kuma da ya duba wanda ke k’irannasa ba ya kashe wayar tasa gaba d’aya. Idanunsa wanda sukayi ja sosai ya lumshe, tare da fesar da wani irin zazzafan numfashi. Ahankali aka turo k’ofar office d’innasa aka shigo. Fou’ad wanda shine ya shigo cikin office d’in ganin yanda M.Jay d’in ke zaune ya rumtse idanunsa ne yasa shi d’an tsayawa tare da kafesa da idanu. Ganin da yayi kuma kaman Maleek d’in baisan da zuwansa bane, ya sashi sauk’e wata irin ajiyar zuciya, ahankali kuma ya shiga takowa zuwa tsakiyan office d’in. D’aya daga cikin kujerun da aka tana da musamman dan zaman bak’i ya ja ya zauna, har zuwa lokacin kuwa Maleek bai bud’e idanunsa ya kalli Fou’ad d’in ba, duk da kuwa cewar ya ji shigowansa, k’amshin turaren D&G kuma da yaji ya shiga hancinsa ne ya sashi gane cewa Fou’ad d’inne ya shigo, saboda aduk mutanen dayasan zasu iya shigo masa office kai tsaye, Fou’ad ne kad’ai ya fiye amfani da turaren na kamfanin Dolce & Gabbana. “Captain.â€? Fou’ad ya k’ira sunansa cikin d’an d’aga murya ta yanda zai jisa da kyau, saboda atunaninsa Maleek d’in yayi nisa ne acikin tunanin da yakeyi shiyasa baiji shigowarsa ba. “M.Jay.â€? Fou’ad ya sake k’iran sunansa akaro na biyu, tare da d’ansa hannu ya buga table d’in dake gaban Maleek d’in. “What?.â€? Maleek d’in ya fad’a cikin cushewar murya, domin sam baiyi farinciki da zuwan Fou’ad d’in ba, because yasan zuwan Fou’ad d’in babu abunda zae k’ara masa sae yawan tension. Fou’ad d’in kuwa jin abunda Maleek d’in ya fad’a ne yasa shi, d’age kafad’ansa cikin yanayin mamaki yace. “Dama kenan kanajina amma kashareni kayi kaman baka ji ba? anyway duk ma ba wannan ba, Ashe har babban abu me girma zai taso maka amma ka kasa fad’amin, atunani na dai baka da wani aboki aduniyarnan sama dani, meyasa ka b’oyemin hakan?.â€? Idanunsa wanda ke alumshe ya bud’e kana ahankali ya sauk’e su akan Fou’ad d’in dake zaune facing d’insa. Hannunsa yasa ya d’an shafi gefen fuskarsa, inda lafiyayyen sajen daya k’arawa fuskartasa kyau ke kwance lub. “Me na b’oye ma?â€? Ya fad’a cikin muryarsa dake bayyana zallan miskilancinsa, wanda kuma da alama yau miskilancinnasa ne ya motsa fiye dana kullum. “Abubuwa da yawa ciki kuwa harda maganan aurenka da Munnira y’ar gidan Alhaji Farouk, na tabbatar da ace Abbou Jaheed bai k’irani ya fad’amin akan mufara shirye shirye da wuri ba da bazaka tab’a fad’amin ba, why Maleek meyasa kake shashantar da duk wani abu naka me mahimmanci ne?â€? Cewar Fou’ad da ya tsaresa da idanu. “Abu me mahimmanci? meye shi? Aure shine abu me mahimmanci? Hmmm.â€? Idanunsa ya d’an lumshe tare dasa teeth d’insa ya ciji jajayen labb’ansa, cikin wata irin murya dake bayyana gaskiya da kuma zallan abunda ke cikin zuciyarsa yace. “Ba yanzu ba ko agaba bana tunanin akwae wani abu me mahimmanci’n da zai sake tunkarar rayuwata, duk way’annan abubuwan sun isa Fou’ad nagaji da komai, ba kuma nason komai da kowa banason wata mace ta rab’eni domin ban tsarawa kaina rayuwa da wata ba, impact ma babu zanen k’addara da sunan wata mace daban acikin jinina, so please leave me alone banason sake jin wani zance na daban akan wata!!â€? Yanayin yanda ya k’are maganar yana me dunk’ule hannayensa ne yasa Fou’ad sakin murmushi. Cike da takaicin halin da M.Jay d’in ya jefa kansa aciki yace. “Da kyau komae ka tsarawa rayuwarka daidai ne awajenka, bakason sake jin wani zance na daban akan wata, amma kana son sake jin wani zance akan matar da take mallakin wani, kana kuma da lokacin da zaka b’ata sama da awanni kana tunaninta, koda sau d’aya ne kuma baka tab’a tunanin yawan zunubin da kake kwasawa kanka bako? Good Maleek bazan hanaka gudanar da rayuwarka daidai da irin yanda kakeso ba, amma kasani amatsayina na abokinka dole ne na fad’a ma gaskiyar abunda ke akwae, koda kuwa hakan zaisa kaji ba dad’i, nasan cewa kanason Laylerh so kuma matsananci, amma cire ta acikin zuciyarka shine abu me sauk’i, domin tariga ta haramta agareka karka manta ita fa ayanzu matar wani ce, kuma......”â€? “Enough is enough Fou’ad, banason jin komae, domin babu wani abu da zaka fad’a wanda zaiyi tasiri acikin rai da zuciyata, saboda ba kasan menene SO ba, Fou’ad nayi imani cewa koda da second d’aya ne bakasan hak’ik’anin abunda nakeji acikin zuciyata ba, soyayyar zuciya kawae kasani bakasan ta jini ba, bakasan komae ba Fou’ad, ba kuma zaka tab’a sani ba, saboda nasan babu wani wanda za’a k’ara halitta masa matsanancin so azuciyarsa kaman yanda aka halittamin na Laylerh acikin jiki da jinina, ka tashi kaje Fou’ad banason ganinka please!!â€? Yafad’i hakan cikin wata irin raunannan zuciya, wanda kuma salo da yanayin maganar tasa ta matuk’ar bayyana rauninsa, saboda hakan kuwa harsaida yasa hannu ya dafe daedae saitin zuciyarsa. Fou’ad kam kasa koda motsa k’afarsa yayi saidai idanu kawae daya zubawa Maleek d’in. K’warai yana mamakin irin sonda Maleek keyiwa Laylerh, soyayyar da har rana me kaman ta yau yakasa furta mata, soyayyar da yakeyinta da gaba d’aya rayuwarsa, tabbas shikam baya fatan Allah Ya d’aura masa k’addaran so me tsananin zafi irin ta Maleek, domin kuwa rashin samun abunda kake so d’in ba k’aramin nakasar maka da rayuwa zaiyi ba. “Maleek!!!â€? Fou’ad ya k’ira sunansa da wata irin sassanyar murya. Bai d’ago kansa ba haka kuma bai amsawa Fou’ad d’inba, domin kwata kwata bayason jin kalaman Fou’ad d’inma acikin kunnuwansa, saboda yasan ba abunda Fou’ad d’in zai iya cemasa face ya cire son Laylerh azuciyarsa. Soyayyar Laylerh azuciyarsa kuwa abune da har abada bazae tab’a fita ba, domin ayanzu soyayyar tata ce kad’ai ke rik’e dashi, rashinta rasa rayuwarsa ne gaba d’aya. Fou’ad kuwa ko kad’an baidamu da rashin amsawan Maleek d’in ba, domin yasan halin Maleek d’in sometimes ma baicika yawan son adameshi da magana ba, saboda kamar yanda yake bazai yiba haka ma bayaso amasa. Saidai kuma ayanzu tunanin da zuciyarsa tayi masa ya sashi d’anjin sanyi acikin ransa, domin yana ganin cewar idan Maleek d’in yayi aure komae zaizo da sauk’i, duk dama dae yasan cewa abune me wahala Maleek d’in ya iya jure kallon Munnira amatsayin mata, amma yasan yau da gobe k’addara zata sa ya k’arbi Munniran dan dolensa, ko ba komae kuma zata d’an rage masa zafi. Tabbas zuwan sa wajen Maleek d’in da yayi yanzu ya sashi fahimtar cewa Maleek bazae tab’a shigowa ayi sha’anin bikin auren tare dashi ba. Wannan yasa shi yanke hukuncin cewa shi da kansa zai tsara duk wani abunda ya dace har zuwa lokacin bikin, zai kuma gayyaci iya mutanen daya sani, duk da cewar yasan zai buk’aci me tayasa, amma zaiyi iya nasa k’ok’arin shima, saboda daga shi sae SOORAJ ne Maleek d’in ya aminta dasu, saidai daga Maleek d’in har SOORAJ jirgi d’aya ne ya d’ebosu, afannin halayya kamar uwa d’aya uba d’aya suke, domin koda sun had’u kowannensu zai iya sha re 40 minute baice da d’an uwansa k’alaba, sunan kuma waisu manyan abokai, amma kuma magana wahala take basu, wannan yasa bazae ma nemi SOORAJ d’inba shikad’ai zai tsara komae. Ahankali ya mik’e tsaye daga zaunen da yake, kallon Maleek d’in da har yanzu ke dafe da daidai saitin zuciyarsa yayi, kamar kuma zai ce dashi wani abu, amma sae ya fasa tare dajan bakinsa yayi shiru, kaitsaye kamar yanda Maleek d’in ya buk’ata ya fice daga cikin office d’in da yake kamar wani hamshak’in falo, anzuba masa komae da komae na burgewa. Jin ficewar Fou’ad d’inne kuma yasa shi bud’e idanunsa ahankali. K’ofar office d’in ya k’urawa ido, kamar me nazartar wani abu, yayinda acikin zuciyarsa kuwa tunani yake daban daban, akan auren da Abbou Jaheed ke k’ok’arin lik’a masa, saidai kuma kaman yanda yake har acikin zuciyarsa baya son auren, haka baya tunanin zai shiga koda hidima d’aya ne da za’ayi abikin hasalima ko ganinsa babu me sakeyi, daga Abbou Jaheed d’in har kowa. Kyakkyawan idea d’in daya zo masa ne yasashi mik’ewa tsaye, ahankali ya k’arasa gaban wani d’an sif da yake aje abubuwansa masu amfani, wata bak’ar jaka ya d’auko tare da bud’e ta ya zuba duk wasu abu nasa masu amfani nasa aciki. Wayarsa dake kan table ya d’auka, kaitsaye kuma ya fice daga cikin office d’in nasa. Koda ya fito daga office d’in nasa duk inda ya wuce soldiers ne ke sara masa, yayinda sauran soldiers d’in da suka kasance securities d’insa suka take masa baya. Direct babban compound d’in wajen da yake kaman camp d’insu ya fito, Abdoul dake zaune yana ganin Ogan nasa ya taho da sauri. Saidai kafun ma ya k’araso Maleek d’in yayi masa alama akan ya tada mota, take kuwa ba b’ata lokaci ya shiga motar ya tayar. Kamar yanda ya saba gidan baya ya shiga, bayan ya dakatar da sauran soldiers d’in dake take masa baya, ta hanyar nuna musu cewar yau d’in b’aya buk’atar rakiyar kowa. Sanin halinsa da sukayi ne kuma yasa duk suka dakata. Abdoul kuwa a 360 yaja motar suka bar farfajiyan wajen gaba d’aya. Saeda sukayi d’anyi nisa atafiyar tasu kuwa kafun Maleek d’in ya fad’awa Abdoul d’in inda yakeso ya kaesa. Kaitsaye kuwa can d’in suka nufa, wato Maitama Estate, inda acan b’oyayyen gidan na Maleek yake, wanda ko su Abbou Jaheed d’in basu san dashi ba, yayi gidanne kuma musamman dan hutawa, saboda dama shi ba mutum bane me son hayaniya, kasancewar sa soldier kuma shiyasa ako da yaushe yake matuk’ar son privacy. Isowarsu katafaren gate d’in gidanne yasa Abdoul fitowa daga cikin motar ya wangale had’add’en gate d’in, saboda babu maigadin da zae bud’e musu. Bayan sun shiga cikin gidan da yake kaman aljannar duniya ne kuma Abdoul ya koma ya rufe gate d’in. Zuwa lokacin kuwa Maleek ya fito daga cikin motar. Kallon Abdoul d’in yayi, cikin halinsa na ko da yaushe fuskarnan babu alaman dariya yace. “Banason kowa yasan inanan, idan nace kowa kuma Ina nufin harda mahaifina, da kuma Fou’ad, sannan ka tabbatar kana kulawa da cutie yanda ya kamata, kana bata abinci sosae.â€? “Okay Sir.â€? Abdoul ya fad’a ahanzarce yana me d’an jinjina kansa, alaman yaji. Baisake cewa komae ba kuwa ya juya kai tsaye ya nufi cikin gidan. Abdoul kuwa juyawa yayi ya fice daga cikin gidan baki d’aya. K’arasowansa cikin had’add’en falon wanda ko wani kusurwa na cikinsa ke d’auke da hotunan Laylerh da yayi ne yasashi d’an lumshe idanunsa tare da sauk’e wata sassanyar ajiyar zuciya, hakanan yaji wani irin sanyi na ratsa gaba d’aya jikinsa, har zuwa tafin k’afarsa, wannan yasa ahankali ya shiga takowa har zuwa tsakiyan falon da had’uwarsa ya zama abun burgewa. Akan d’aya daga cikin hotunan nata ya sauk’e idanunsa, wanda take sanye da wani riga da sket na atamfa, tana zaune ne kuma ak’asan carpet, yanayin yanda fuskarta ya kasance acikin hotonne kuma yasa duk wanda ya kalla zaigane cewar tana cikin yanayin damuwa ne aka d’auki hoton. Idanunsa ya k’urawa hoton nata baya ko k’iftawa, domin a irin yanayin da fuskar nata ke ciki haka shima yanzu yakeji acikin zuciyarsa. Janye idanunsa daga kan hoton nata yayi, kana asanyaye ya zauna akan d’aya daga cikin had’add’un original royal cushions d’in dake cikin falon. Hannunsa yakai yad’an shafa idanunsa, adaidai lokacin da suka sauk’a akan hoton mahaifiyarsa dake cikin falon. Akaron farko kenan da murmushi ya bayyana akan fuskarsa, take kuma yaji zuciyarsa ta karye, hakanan yaji wani abu me kaman ruwa na neman cika masa idanu, wannan yasa shi saurin d’auke kansa daga kallon hoton, y’ar k’aramar jakar da ya shigo da ita ya jawo, tare da bud’e ta ya ciro wani Ledan cocaine. B’ud’e ledan yayi tare dakai hancinsa ya shak’i cocaine fowder d’in ta yanda har saida yajita acikin kansa. Haka ya lumshe idanunsa tare da ci gaba da shak’an cocaine d’in har saida yajisa acan sararin samaniya, cikin wata duniya ta daban, duniyar imagine. Shi kad’ansa haka yayita bulayi acikin falon hardai ya zamana ma hankalinsa yabar jikinsa, inda yatafi wata duniya ta gushewan hankali me kama da bacci. After 2 days Acikin kwana biyun nan gaba d’aya mood d’in Laylerh ya sanja, domin tunda taji maganan auren Maleek ta kamu da wani irin zazzab’i me zafi, ga kuma ciwon maran period dake damunta, abu kaman wasa kuwa sai gashi takai ga kwanciya, acikin Kwanaki biyun kuwa Najeeb koda sau d’aya baisake zuwa mata da wata buk’atarsa ba, koda kuwa romancing d’inta ne, saidai kuma yana iyaka bakin k’ok’arinsa wajen bata kulawa. B’angaren su Oum Ayush da Abbou Jaheed harma da Fou’ad kuwa shirin biki sukeyi sosae, hakama b’angaren gidansu amarya, sukamma abunnasu yafi na kowa, Dan tuni amarya munnira ta fara karb’an gyaran amarya, yayinda tabi kan k’awayenta tasanar musu irin mijin da zata aura, kyau da had’uwa had’i da matsayinsa duk ba wanda ta b’oye musu, hakanne kuwa yasa suka k’ara fasa mata kai, hakan yasa takejin kanta tafi kowa. Awajen Momy kuwa har yanzu wasu makirci take shirin k’ullawa, saidai kuma jin Maleek d’in zaiyi aure ne yasa ta sauya akalan makircin nata zuwa wani waje na daban. (Uhummm su Maleek za’a angwance 😝 Insha Allah Gobe zaku samu update saboda da yardar Allah Mungama biki yanzu Ina free, duk dama ankoma school amma hakan ba damuwa bane.) *31January/2021* 2/2/21, 8:42 AM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna *Chapter 46* Sassanyar iskan yammacin da ake kad’awa wanda ahankali yake ratsa dukkan sassan jikinta ne yasa ta soma bud’e idanunta ahankali ta sauk’e ganinta akan had’add’en zanen p.o.p’n dake saman d’akin wanda aka k’awata jikinsa da zane me kyau. Amatuk’ar kasalance da kuma irin yanayin da ta samu kanta aciki ta janye idanunta daga kallon da takeyiwa saman d’akin. Wani irin numfashi me fitar da hucin zafi ta fesar tare da maida kallonta ga agogon bangon dake mak’ale acikin d’akin. 5:45 pm dai dae da agogon ya nuna mata ne yasa ta d’an yunk’urawa ta tashi zaune, hannunta takai daidai saitin mararta da takejin yana d’an murd’awa kad’an, kasancewar kuma yau zata gama period d’innata ne yasa ciwon keyi mata da kad’an kad’an, wanda ayanzu kuma abunda yafi damunta shine yawan fad’uwar gaba da take samun kanta aciki kwana biyun, da kuma zazzab’in da har yau yakasa barinta ya huta, ko yanzun ma zazzab’in takeji ajikinta wanda kuma shiya kwantar da ita har na tsawon mintuna 40 batare da ta motsa ba sai yanzun. Kanta ta jingina da jikin saman gadon, tare da sake jan lallausan blenket ta rufe jikinta dashi. Idanunta wanda suka sanja kala ta lumshe. “Saura y’an kwanaki ne kawae suka rage.â€? Ta fad’i hakan ahankali, kana cikin wata irin murya me sanyi sosae, da alama kuma abunda ke zuciyarta ne ya fito fili batare da ta sani ba. Lokaci d’aya kuma hawaye suka cika idanun nata, domin aduk lokacin da zata tuna da auren Maleek d’in ko shakka babu sae taji hawaye sun cika idanunta, take kuma duk wani d’an ragowan farinciki da yayi mata saura zae gudu. Jin alamun turo k’ofar d’akin da akayi ne kuma yasa tayi saurin kawar da kanta gefe tare dasa hannu ta murza idanunta gudun kada hawayen dake cikinsu su samu daman zubowa. Ahankali ya maida k’ofar d’akin ya rufe, ganin da yayi mata azaune ne kuma yasa shi d’an jingina bayansa da jikin k’ofar ya zuba mata ido, duk dama baisamu daman kallon cikakkiyar fuskarta ba, kana kuma duk da kasancewar ta lullub’e rabin jikinta da blanket amma hakan bai hana idanunsa gane masa raman da tayi ba, domin acikin y’an kwanakin har wuyanta saida ya k’ara tsawo saboda yanda gaba d’aya komae nata ya sanja. Idanunsa ya d’an lumshe ahankali tare da sakin wata b’oyayyar ajiyar zuciya, tabbas sha’anin damuwa da kuma rashin lafiyan Laylerhn na matuk’ar damunsa, musamman idan ya tuna cewa amanarta aka bashi, kuma sannan hakk’insa ne ya bata kulawa, da kuma cire ta acikin duk wata damuwa, saidai amma saudayawa yakan ga kamar ya kasa yin hakan, saudayawan lokuta yakan tambayi kansa menene dalilin da yasa tun da sukayi aure da Laylerh’n rayuwa tasoma tafiyar musu ahaka, domin shi sam ba haka ya tsara musu ba, farinciki da kuma jin dad’in rayuwa ya tsara musu sab’anin yanzu da gaba d’aya kowannensu zuciyarsa ke d’auke da abubuwa maban banta. Ayanzu shida Laylerh’n suna neman cimma sati guda da aure amma koda sau d’aya wata alak’a ta auratayya bata tab’a shiga tsakaninsu ba, ba kuma don baya buk’atar hakan ba, hak’ik’a amatuk’ar buk’ace yake da ita, ako wacce rana, a kuma duk lokacin da zaisata acikin idanunsa sae yaji wani irin feeling me k’arfi yazo masa, ko yauma saida yasha tablet kafun yasamu matsanancin sha’awarta da yakeji ya d’an kwanta, Saidai kuma wani k’alubale daya fara fahimta shine zuwa yanzu hak’urinsa ya kusa k’arewa akanta, faruwar hakan kuwa zai iya sashi ya aikata mata komae, dan ayanzu shikansa baya control d’in sha’awarsa akanta, koda sau d’aya ne kuwa baya so ace ya gwada mata k’arfi saboda hakan zai iyasawa ta zamana koda yaushe cikin matsanancin tsoronsa. Saidai kuma ayau d’in yana tunanin yin amfani da shawarar da zuciyarsa ta basa, ta hanyar lallab’ata ta yanda zaisa ta saba da zama ajikinsa ko yaushe, domin hakan ba k’aramin sauk’i zai kawo masa wajen yin Disvirgin nata ba, kuma zuwa lokacin ta riga da ta saba bazata wani ji zafi sosae ba. Yarda da shawaran da zuciyartasa ta basane kuma ya sashi, sakin wani d’an guntun murmushi, ahankali ya shiga takowa zuwa kan gadon da Laylerh’n ke zaune. Laylerh kuwa jin ya iso wajen gadon ne yasata lumshe idanunta, domin har acikin zuciyarta kunyan had’a idanu dashi take, musamman sanin da tayi cewar bata kyautata masa, ta hanashi duk wani hakk’insa dake kanta, takasa basa farinciki kamar yanda kowacce mace ke bawa mijinta, takasa d’aukar nauyi da jib’antan al’amuransa, impact ma takasa tsaida zuciya da tunaninta akansa, alhali kuma tasan cewa bashi da laifi ko makusa ajikinsa, shima cikakken Namiji ne, me aji da kuma nutsuwa, Namiji ne shima irin wanda mata da yawa ke mafarki da fatan samu, haka zalika Namiji ne wanda ba kowacce mace bane keda arzikin samu, sauda dama takanso ta tambayi kanta cewar “Menene Laifin Najeeb ko kuma aibunsa?â€? Saidai amsar akoda yaushe shine “Babu.â€? Abunda har yanzu zuciyarta ke zaune akansa kuwa shine SOYAYYAR MALEEK. Abazata taji sauk’an tafukan hannayensa akan fatar wuyanta, hakanne kuwa yasa ta bud’e idanunta da sauri ta sauk’esu akansa,wanda tuni har ya zauna abakin gadon batare da ta Ankara da hakan ba. “Har yanzu jikinki akwae zafi sosae, ko zamuje hospital?.â€? Yafad’i hakan yana me k’ok’arin zare hannayensa daga wuyanta. Yayinda ita kuwa takasa d’auke idanunta daga kansa, Dan yau akaron farko kenan da taji wani abu na daban adangane dashi wanda wannan abun kuma ba komai bane face tausayi da kuma raunin da zuciyarta tayi. Hakanan taji ajikinta cewa tanason kasancewa tare dashi, ma’ana tana buk’atar ya zame mata mafaka ta yanda zata shiga jikinsa tayi masa kuka sosae ko hakan zaisa taji sauk’in abunda takeji. Shikuwa Najeeb jin tayi shirune yasashi d’ago idanunsa ya kalleta, ganin da yayi kuma shi take kallo ne yasashi k’ak’alo murmushi ya d’aura akan fuskarsa, cikin muryarsa da tayi sanyi sosai yace. “Yadai Laylerh ko akwae wani abu bayan fever da yake damunki ne?â€? Kai ta girgiza masa alaman a’a, azahirance kuwa y’an k’ananan labb’an bakinta ta soma motsawa da alama kuma wani abu takeson cewa, amma amon maganan nata ya kasa fitowa fili. Idanunsa ya d’an lumshe ahankali, domin ganin hakan da tayi yasan cewa bazata yi masa wani magana ba. “LAYLERH.â€? Yak’ira sunanta da d’an k’arfi tare dasa hannayensa ya kama kafad’unta. Cikin wani irin sabon yanayin da tasamu kanta aciki ta fad’a jikinsa tare dasa hannayenta akaron farko dan kanta ta rungumesa, tare da sakar masa wani kuka me d’auke da zallan sakalci da shagwab’a. Tabbas kuwa yaji runguman da tayi masa d’in har acikin jikinsa, hakan yasa ahankali shima yasa hannayensa ya rungumeta, cikin sanyin yanayi yakai fuskarsa daidai saitin kunnenta, ahankali kuwa ya d’an soma sakar mata numfashinsa adaidai cikin kunnen nata, cikin muryarsa da ta d’an sanja amo lokaci guda yace. “Kidaina kuka please, ko kinaso na kaiki hospital doctor ya miki allura?â€? Cikin yanayin sheshshek’an kukan nata ta girgiza masa kanta, alaman “A’aâ€? “Good to kiyi shiru kinji My beautiful Laylerh nah, kinci abinci?.â€? Ya fad’i hakan yana me d’an d’ago innocent face d’inta. “A’a nak’oshi.â€? Tafad’i hakan tana me mamul mamul da d’an k’aramin bakinta. “Mekikeso kici to? za kisha chocolate da ice cream?.â€? Da sauri ta kad’a masa kai alaman “Eh.â€? Murmushin daya k’arawa fuskarsa kyau yayi, cikin son kwaikwayon yanayinta yace. “Good girl gueen of shan zak’i.â€? Saketa yayi tare dasoma k’ok’arin tashi daga kan gadon, amma ga mamakinsa sai yaga ta rik’o hannunsa, yayinda hawaye suka zubo daga cikin idanunta. Hakan da yagani ne kuma yasashi dawowa ya zauna akusa da ita, tare dasa hannu ya jawota jikinsa, fuskarsa ya kawo kusa da nata, har takai ga suna jin d’umin numfashin juna. D’ayan hannunsa yasa ya rik’o waist d’inta, cikin sabon feelings d’inta da ya samu kansa aciki ya had’e fuskarsu waje d’aya, hakanne kuwa yasa sajen dake kwance akan fuskarsa ya soma gogan nata fuskar. Amatuk’ar sanyaye ya d’aura lips d’insa akan nata, tare da sauk’e mata wani kiss me had’e da sucking lips. Wanda yasa gaba d’aya tsikar jikin Laylerh’n mimmik’ewa, saboda hakan da yayi mata d’in yazo mata amatuk’ar bazata, saidai kuma ayau d’in ko kad’an bataji haushinsa dan yayi mata hakan ba, hasali kuma batayi yunk’urin k’wace bakinta daga nasa ba. Shikuwa Najeeb ganin hakanne yasashi sake kamo lips d’inta ya tsotsa, batare kuma daya tsawaita hakan ba ya zare bakinsa daga nata, sakamakon sanin abunda zai biyo baya da yayi, yasan ba bashi kanta zatayi ba, saidai ta barshi da azababben ciwon mara, gashi kuma lokacin Sallah yayi har ansoma k’iraye k’irayen sallan magriba. Janye jikinsa yayi ahankali tare dasa hannu ya shafi gefen fuskarta, cikin kulawa yace. “Kishirya idan nadawo daga sallah sai muje kisha ice cream.â€? Batare kuma da ya jira amsar da zata bashi ba ya wuce toilet, minti kad’an ya fito da alwalansa ya wuce masallaci. Itakuwa Laylerh duk da cewar batajin k’warin jikinta haka ta sauk’o daga kan gadon itama ta wuce toilet, sama sama tayi wanka da ruwa me d’an d’umi, bayan ta fitone kuma ta shirya kanta cikin wata simple Dubai Abaya me ratsin gold da ash sosae kuwa kayan yayi mata kyau. Tana kammala sa kayannata kuwa Najeeb d’in ya dawo, ganin kuma yanda tayi kyau sosae ne yasashi kama hannunta suka fice daga cikin d’akin. Direct compound d’in gidan inda motarsa ke fake suka nufa, koda suka k’arasa shida kansa ya bud’e mata murfin motar b’angaren me zaman banza ta shiga, saida kuma yaga ta zauna kafun ya zagaya ya shiga b’angaren driver, anutse ya tada motar mai gadi ya wangale musu gate d’in gidan suka fice. Har tafiyar tasu kuwa tayi nisa babu wanda yace da d’an uwansa k’ala, domin kowannensu da abunda yake sak’awa acikin ransa, ahaka har suka iso Shoprite. Atare suka shiga cikin shoprite d’in inda ya bata daman d’aukan duk abunda takeso. Kasancewarta ma’abociyar son zak’i ne kuma yasa ta d’aukan dangin chocolates da sauransu. Shikuwa abubuwan da yasan zai buk’ata ya saya sannan suka fito daga cikin shoprite d’in. Kaitsaye hanyar dawowa gida suka nufa, yayinda tun acikin motar kuwa Laylerh ta shanye roba d’aya na Ice cream. Koda suka dawo gida a fridge ta saka sauran ice cream d’innata, bayan ta rage kayan dake jikinta ne kuma ta hau kan gado ta kwanta, saboda yanda takejin kanta agajiye ne kuma yasa tana kwanciya bacci ya d’auketa. Najeeb kuwa ganin da yayi tayi bacci ne yasashi zuwa bayanta ya kwanta, ahankali yake wasa da dogon gashin kanta har bacci ya d’aukesa shima. 2:30 am Matsanancin gumi ne ke ketowa daga kowani sashi na jikinta, yayinda kuma alokaci d’aya duk gaba d’aya jikinta ya d’auki rawa, cikin matsanancin firgita had’i da razana tafasa wani irin k’ara me tada hankali wanda kuma acikin sautin k’aran nata ta ambaci sunan MALEEK da wata irin murya, wanda hakan yasa Najeeb dake kwance tashi arud’e, daidai lokacin kuwa itama ta tashi azabure daga baccin da takeyi cikin kid’ima da tashin hankali marar misaltuwa. *1February/2021* 8:00 pm 2/4/21, 8:44 AM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna *Chapter 47* “LAYLERH!â€? Najeeb wanda gaba d’aya k’ara da kuma sautin ihun nata yasa shi tashi afirgice ya k’ira sunanta cikin yanayin d’an d’aga murya tare dasa hannunsa ya soma k’ok’arin kama nata hannun. Saidai kuma yanayin yanda gaba d’aya jikinta ke b’ari yasa shi kasa yin hakan, musamman da yaga ta dunk’ule hannayen nata waje d’aya, da d’an k’arfi take jijjiga kanta, yayinda lokaci d’aya hawaye suka shiga zirya akan fuskarta kaman an kunna famfo, cikin yanayin tsoro da kuma firgicin da ta samu kanta tasoma k’ok’arin dirowa daga kan gadon. Ganin haka yasa cikin sauri Najeeb ya rik’o hannunta, hankalinsa ad’an tashe yace. “Lafiyanki k’alau kuwa Laylerh? What’s wrong with you?â€? Yayi mata tambayar yana me d’an girgiza kafad’unta daya rik’esu da hannayensa. Kai ta soma girgizawa tare da soma yunk’urin ya kice hannayensa dake kan kafad’anta, saboda a yanda yanayin nata yake ayanzu bazata iya ce masa komae ba. Gane hakan da yayi da kuma fahimtar cewa bata cikin hayyacinta, yasa shi matsowa kusa da ita ahankali, ya shiga shafa bayanta, cikin muryarsa me d’auke da yanayin kwantar mata da hankali yace. “Please Laylerh ki nutsu kinji, ki dawo cikin hayyacinki, babu abunda zai sameki gani atare dake, kuma bazan tab’a bari wani abu yazo ya cutar dake ba, kidawo hayyacinki kinji!!â€? Ya k’are maganan yana me kamo hannayenta, da har yanzu suke b’ari. Fuskarta ya k’urawa ido, saboda yanda yaga labb’an bakinta na motsawa duk da karkarwan da sukeyi da alama wani abu take son fad’a. Tabbas kuwa abunda ta gani amafarkin nata takeson bayyanawa, saidai kuma hakanan taji harshenta yayi mata nauyi, da k’yar cikin wata irin murya me d’auke da shaking tace. “Yah M.Jay ne, ina tunanin wani abu ya sameshi, wata mota ta buge shi na gansa da jini ajikinsa, baya numfashi, komae nasa ya tsaya, wayyo Yah Najeeb dan Allah kabarni naje na dubashi, Inaso na gansa, Inaso naga ko yana lafiya, banason wani abu ya same sa banasoo!!!!â€? Ta k’are maganan nata cikin wani irin matsanancin kuka, me tada hankali da kuma bayyanar da gaskiyar abunda ke cikin zuciyarta. Idanu Najeeb d’in ya zuba mata cike da mamakin jin abubuwan da take fad’a. “Anya kuwa Laylerh bata da aljanu?â€? Yayiwa kansa tambayar da dagashi sai zuciyarsa da ta sak’a masa hakanne suka sani, azahirance kuwa wata irin sassanyar ajiyar zuciya ya sauk’e, ganin yanda Laylerh’n ke kuka sosaine kuma yasashi jawota jikinsa, inda ya d’aura kanta akan faffad’an chest d’insa, tabbas kalaman da ta fad’a akan Maleek d’in ya daki zuciyarsa, wanda hakan yasa yaji wani abu me kama da kishi, take ya wanzu acikin ransa, saidai kuma amma ko kad’an bayason yanda Laylerhn ke nuna damuwa akan d’an uwannata yake damunsa, har yakai ga ya haifar masa da mummunan zargi acikin zuciyarsa, duk da cewar kuwa yana iyaka bakin k’ok’arinsa wajen gujewa zargin hakan, amma kuma yasan wani lokaci zuciya bata da k’ashi, komae yazo cikinta turawa k’wak’walwa take. K’ok’arin sha re gurb’ataccen tunanin dake cikin ransa yayi, ahankali cikin sassanyar murya yace. “Babu abunda ya samu Maleek Laylerh, saboda haka ki daina kuka, ko kin manta cewa da yawan mafarki ba gaskiya bane? ba lallaine abunda kika gani amafarki ya zama gaske ba, haka ko anan gaba ba lallaine hakan ya faru ba, da yawan mafarki baya tab’a zama gaskiya, ki kwantar da hankalinki kinji nasan Maleek yana lafiya!â€? Ya k’are maganan yana me d’an shafa bayanta da hannunsa. Kanta tad’an girgiza, still cikin muryan sheshshek’a tace. “Inajin tsoron kada wani abu ya faru da shi, nagani dagaske, naga wata mota ta bugeshi, nasan mafarki ba gaskiya bane, amma wannan mafarkin inajin tsoro kada......â€? “Shiii!!! kiyi shiru babu abunda zae faru, ki sakeyin addu’a ki koma ki kwanta kinji.â€? Ya fad’i hakan ta hanyar katseta daga maganan da takeyi, domin sam bayason koda jin ta ambaci sunan Maleek d’inne, saboda fad’an hakan da kuma nuna damuwarta akan Maleek d’in, yana sawa yaji k’unci acikin zuciyarsa. Jin abunda ya fad’a yasa ta d’ago kai da idanunta wanda suka cika tab da k’walla ta kalleshi, cikin yanayinta na abun tausayi da kuma kukan dake cinta ta bud’e baki da niyar sake yi masa wani magiya akan yabarta taje wajen Maleek d’in. Cikin cracking voice tace. “Dan Allah....â€? Saurin sa hannunsa yayi ya toshe mata baki, tunkafun ma ta ida fad’an abunda zata fad’a d’in, lokaci d’aya kuma yanayin fuskarsa ya sanja, sake ta yayi tare da sauk’owa daga kan gadon, direct wajen k’ofar d’akin ya nufa, batare da tunanin komae ba kuwa ya murzawa k’ofar key, sanin kuma dayayi cewa idan yabar key d’in ajiki zata iya bud’ewa ta fitane yasashi zare key d’in ya rik’e a hannunsa, dawowa kan gadon yayi ya kwanta, irin kwanciyar nan ta rub da ciki, tare da rumtse idanunsa. Laylerh kuwa ganin abunda yayi d’inne yasa ta k’ara sautin kukanta, had’e da matsawa can gefe ta takure jikinta waje d’aya, da iya k’arfinta ta shiga rera masa kukan da gaba d’aya yaso haukata masa tunani. Adaidai lokacin kuwa ya bud’e idanunsa wanda suka kwashe tsawo awanni suna rufe, ahankali ya d’an yunk’ura ya tashi zaune daga kwancen da yake, cikin wani irin sabon yanayin daya samu kansa aciki yasa hannu ya dafe daidai saitin zuciyarsa dake bugawa da k’arfi. D’an cije labb’an bakinsa yayi, domin kuwa ayanayi guda d’ayane yakejin irin wannan bugun zuciyar, shine idan yakasance Laylerh na cikin damuwa, ko kuma idan yaji sautin kukanta, tabbas hakan yakansa yasamu kansa cikin bugun zuciya, ko yana kusa ko baya kusa kuwa idan Ayshnoor d’insa na cikin damuwa yakanji yanayinsa ya sauya. “Acikin wannan daren me yake damun Laylerh?â€? Zuciyarsa tayi masa tambayar da Allah Ne kad’ai masanin amsarta. Idanunsa yakai kan agogon dake aje gefen gadon. 3:00 am daidai idanunsa suka nuna masa, hakanne kuwa yasashi soma yunk’urin sauk’owa daga kan gadon, ahankali ya aje k’afafunsa ak’asa, koda yazo mik’ewa tsaye kuwa saida ya rumtse idanunsa kafun ya iya mik’ewa, domin kwana biyunnan duk bayajin dad’in jikinsa, ko abinci baya ci daga drinks sai tea kawai yake iya sha, baya fita ko ina daga d’aki sae falo, daga gefe guda kuwa ya kashe gaba d’aya wayoyinsa, yayi hakanne kuma gudun kada su Abbou Jaheed su sake tunkararsa da maganan jarababben auren da suke son lik’a masa. Addaddafe ya k’arasa toilet, duk da cewar kuwa ana d’an sanyi hakan bai hanashi sakarwa kansa ruwan shower me sanyi ba. Ak’alla kuwa sama da 20minute ya d’auka ruwan na dukan jikinsa, har saida ya d’anji zuciyarsa ta samu relief kafun ya kashe shower’n kana ya d’auro alwala. Bayan yafito daga toilet d’in kuwa wata navy blue jallabiya yasaka ajikinsa, tare da shumfud’a sallaya ya tada sallah, domin so yake ya rok’i Allah Ko hakan zaesa ya samu sassaucin abunda ke azalzalan zuciyarsa babu dare ba rana. Acan B’angaren su Najeeb kuwa, tsawon mintuna 20 Laylerh ta kwashe tana ta faman aikin kuka, tabbas ada yaso yin k’ok’arin jure kukannata saidai kuma jin yanda take k’ok’arin shid’ewa ya sashi kasa jure hakan. Ahankali cikin sanyin da zuciyarsa tayi ya juyo da kallonsa zuwa gareta. “Laylerh!â€? Yak’ira sunanta cikin sassanyar murya me d’auke da rarrashi. Laylerh kuwa duk da cewar tajisa amma haka ta cigaba da kukanta, me d’auke da abubuwa da dama, shagwab’a, sakalci, da kuma tsoron faruwar abunda tayi mafarki akai d’in, saboda ba yanzune karo na farko da take mafarkin Maleek d’in acikin mawuyacin hali ba, ay’an kwanakinnan acikin mafarkinta duk haka take ganinsa acikin damuwa. Najeeb ko ganin da yayi bata kulasa bane yasa shi tashi zaune, asanyaye ya matso kusa da ita, cikin murya me kama da rad’a yace. “Am very sorry My Wife, am so sorry kiyi hak’uri kinji, kuma kiyarda cewa Maleek yana nan lafiya, sannan ban hanaki zuwa wajensa haka kawae ba, yanzu fa tsakiyar dare ne, ke kanki idan zakiyi tunani baidace ace kinje wajensa awannan talatainin daren ba, amma I promise you gobe da safe zakije ki dubasa, but nasamma yana lafiya, amma kiyi hakuri kinji, kizo mukwanta, banason jin kukanki ko kad’an.â€? Ya fad’i maganar yana me kamo hannayenta duka biyu, ya jawota jikinsa, ahankali ya shiga share mata hawayen da duk suka mata dama dama da fuska. Ko kad’an kuwa batayi yunk’urin hanasa ba domin dama kukan da tayin yasa mata wani irin fitinannen ciwon kae. Kwanciya tayi akan gadon tare da juya masa baya, ahankali take sakin sheshshek’an kukan da ya zame mata dole. Cike da tsoro da kuma fargaban abunda kunnuwanta zasu jiye mata gobe bacci yasake d’aukarta. Jin yanda take ta faman sauk’e ajiyar zuciya ne, yasa Najeeb matsowa kusa da ita sosae tare da jan blanket ya rufa musu. Da tunani kala kala acikin ransa shima bacci ya d’aukesa. Washegari. Tunda ta tashi tayi sallan asuba bata sake komawa bacci ba, sakamakon yanda takejin matsanancin fad’uwar gaba da kuma tsinkewar zuciya na ziyartarta, ahaka dae ta daure zuciyarta, har zuwa k’arfe bakwai kafun ta shirya kanta cikin wata atamfar chiighanvy me ratsin green, wacce akayi d’inkin pencil sket da kuma riga fitted sosae atamfar ta karb’i jikinta yayinda, kuma had’add’en d’inkin ya lafe ajikinta, duk da kuwa cewar kwana biyun ta d’anyi rama amma hakan baisa cikakkun hips d’inta komawa ba. Batayi wani kwalliya sosae afuskarta ba, wani siririn vail me showing ta yafa ajikinta, tare da zura wasu flat shoe marassa nauyi, cikin yanayin zak’uwa ta fice daga cikin d’akin, anan falo ta samu Najeeb yana aikin danna laptop d’insa, k’arasowa tayi asanyaye ta gaisheshi. Fuska asake ya amsa yana me k’arewa had’add’iyar surar jikinta kallo, hakanan tunda yaga tayi sallah yaudin yakejin kansa acikin nishad’i. Batare da ta tsaya jira ko sauraransa ba kuwa kaitsaye ta fice daga cikin falon, shikuwa da kallo ya bita har ta b’acewa ganinsa. Kaitsaye part d’in su Abbou Jaheed ta nufa, koda ta k’arasa kuwa acan ta iskesu dukansu zaune akan dining table. Saidai rashin ganin Maleek awajen ya sake haifar mata da fad’uwar gaba. Haka dae ta k’araso jiki asanyaye ta zauna tare da gaidasu duka, dukansu fuska asake suka amsa mata, saidai banda Momy wanda ita fuskartata ko alaman annuri ma babu akanta. Bayan ta zauna akan d’aya daga cikin kujerun wajenne kuma tayi saving kanta. Duk da cewar batajin yunwa sosae amma haka ta soma tsakalan abincin, yayinda ta maida gaba d’aya hankalinta ga k’ofar d’akin Maleek d’in, burinta ayanzu baiwuce taga ya bud’e k’ofar d’akin ya fito. After 20minue. Rai adagule Abbou Jaheed ya ajiye wayar dake hannunsa tare dajan d’an guntun tsaki. Hakanne kuwa yasa Abbou Kareem ya d’ago kae ya kalleshi, ganin kuma ran Abbou Jaheed d’in ab’ace ne yasashi d’anyin gyaran murya, cikin kulawa yace. “Lafiya kuwa naga yau duk ranka ajagule?.â€? Cikin d’an yanayin takaici Abbou Jaheed yagirgiza kansa, domin kuwa duk yanda yaso shanye b’acin ransa abun yaci tura, saida ya d’an kurb’i ruwa kafun ya d’ago kae ya kalli k’anin nasa cikin k’unan rai yace. “Yau kwana 4 kenan Maleek baya kwana agidannan, sannan ya kashe wayoyinsa gaba d’aya, nasa abincikamin shi ance ba’a gansa ba, rabon dana sashi a idanuna yanzu yakai kwana 5, tabbas nafahimci cewa so yake maidani mutumin kawae, ae shi bak’aramin yaro bane da zai keyin duk abunda yaga dama, nasan duk me yake sashi way’annan guje gujen maganar aurensa ne dae babu fashi Insha Allah nanda 5 days za’a d’aurashi.â€? (Note edit. kuyi hkr typing d’in yau bashida tsawo naje school ne bandawo da wuri ba kuma.. Please two days bakwamin comment, banajin dad’i yau kam please kuyi comment😰) *3February/2021* *6:51 pm* 2/5/21, 9:20 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna *#Destiny* *Chapter 48* Ajiyar zuciya Abbou Khareem ya sauk’e, cikin yanayin fahimtar k’unan da d’an uwannasa yakeji acikin zuciyarsa yace. “Tabbas nasan kanajin babu dad’i acikin zuciyarka, amma ni sai nake ganin cewa Maleek yabar gida ne saboda bayason wannan auren da za’ayi masa, saboda ayanzu yasan cewa shi ba k’aramin yaro bane, cikakken Namiji ne shi da yake da y’anci kamar kowa, yana da choice d’in da zai nemo mace aduk inda yake ya aura, gaskia gaba d’aya tunanina ya tsaya akan cewar Maleek bayason wannan auren ne, meyasa ba za’a fasa maganan auren ba, asake bashi lokaci ya nemo matar aure da kansa inaga hakan zae fi yiwa kowa dad’i, amma fa ban fad’i hakan amatsayin umarni ba shawara ce kawae atak’aice.â€? Ahankali Abbou Jaheed d’in ya d’ago kai ya kalli k’aninnasa wato Abbou Kareem. Maida kansa yayi batare da yace komai ba, sai wani irin murmushi me d’auke da ma’anoni daban daban da yayi, tabbas tuntuni dama yasan cewa watarana sae hakan ya faru, shikuwa ba wae kawae yanayin abunda yaso akan y’ay’annasa bane, duk wani abu da yakeyi yana yine saboda nesanta faruwar abun kunya. Mug d’in coffee d’in dake hannunsa ya ajiye tare da d’an gyara zamansa, ahankali cikin muryarsa da tayi sanyi sosae yace. “Bawae ina tauyewa Maleek hakk’insa bane na neman mata da kansa, na basa dama almost 3 times amma ya share abun, ya yi watsi da duk wata magana na, duk dacewar bana nuna masa bayyananniyar soyayya amatsayinsa na tilon d’ana hakan bawae yana nufin cewa bana sonsa bane, ayanzu muna cikin wani rayuwa da bayyana matsanancin soyayya ga d’a kan jawo masa tab’arewar rayuwa, tabbas bazan iya jure ganin Maleek acikin wani hali ba, ko ya yake kuwa, saidai inason kowa yasan cewa na bawa Maleek dama amma yayi watsi da ita, na basa zab’i amma ya kawar, k’warai shiba yaro bane da zan tursasa sa dole akan sae ya auri wacce na kawo masa amatsayin zab’in a, hak’ik’a ni kaena ban tab’a tunanin tursasa Maleek akan auran wacce baya soba, saidai kuma ayanayin yanda naga ya fara karkata akalar rayuwarsa izuwa wani waje na daban yazame min tilas na d’au mataki na kuma dage wajen dawo dashi hanya, bansan me yake damun Maleek ba, bansan meyasa yake son maida rayuwarsa wata abar banza ba, da idanuna nagansa ya dawomin gida acikin maye, cikin talatainin dare, Kareem bazan iya jure hakan ba, wannan dalilin shiyasa na yanke shawarar cewa dole saiyayi aure, saboda komae wani lokaci aure yakan zamo silar gyara rayuwar d’an Adam, tabbas nasan akwae damuwa me tarin yawa acikin zuciyar Maleek, saidai kuma bani da wata hanya da zan iya magance masa ita sai ta hanyar sama masa abokiyar zama, wacce zata d’ebe masa kewa, tun yana k’arami ya taso da maraicin rashin mahaifiya, yayi gaba d’aya rayuwarsa cikin kad’aici da kewa, shin yanzu bai cancanci zama da mace ba? ko idan harshi bazai ne ma ba ni saina zauna bannema masa ba? lokacin da zan zubawa Maleek idanu ya wuce, yanzu lokaci ne da ya kamata ace yasan waye shi, wani irin dukiya ne baitara ba? yana da kud’i dukiyar da har ya mutu bazasu tab’a k’arewa ba, idan har mutum yana da hankali yana kuma da jini ajikinsa sannan yana da sana’ar yi aure shine abunda ya kama ce sa, koba komae idan Allah Ya azurtasa da zuri’a zasu zamar masa garkuwa anan gaba.â€? Gama fad’in hakan da yayi yaja kujerarsa baya, batare daya tsaya jin wani abu daga bakin kowannensu ba ya mik’e tsaye anutse ya nufi hanyar babban d’akinsa dake nan cikin falon. Ajiyar zuciya me k’arfi Oum Ayush da kuma Abbou Kareem suka sauk’e, tabbas sun gamsu da kalaman Abbou Jaheed d’in domin kuwa duk wani abu yana da iko akan y’ay’ansa, sannan hakk’in kowani ubane ya zab’awa y’ay’ansa rayuwar da ta dace wanda agaba zasuyi alfahari da ita. Hak’ik’a ada suna ganin kamar wani abu da Abbou Jaheed d’in keyi baya dacewa, amma ayanzu sun fahimci gaba d’aya dalilin da yasa yake hakan. Jiki asanyaye Abbou Kareem ya mik’e tsaye yabar dining area din domin dama ya kammala cin abincin sa. Hakan yasa dining table d’in ya rage daga Oum Ayush Momy sai kuma Laylerh da tunda Abbou Jaheed ya fad’i maganarsa ta farko ta sunkuyar da kanta k’asa har zuwa yanzu kuwa bata d’ago da kannata ba, yayinda ayanzun kuma babu abunda ya tsaya mata arai kaman jin da tayi cewar yau kwana 4 kenan da M.Jay d’in baya gidan, abunda yafi girgizata kuwa shine jin da tayi Abbou Jaheed yace da idanunsa yaga Maleek d’in acikin yanayin maye. Tabbas way’annan abubuwa guda biyun sun matuk’ar d’aga hankalinta, wanda har hakan yasa ta kasa kai koda loma d’aya na abinci bakinta. Sosae jikinta yayi sanyi, yayinda a gefe guda kuwa idanunta tab suka cika da k’walla, awannan karon kam sanadin k’wallan nata ya banbanta dana kullum, saboda wani irin matsanancin tausayin d’an uwan nata ne ya shiga jikinta, wanda har hakan ya haifar da bayyanar rauninta. Ahankali ta lumshe idanunta dake cike da k’walla, hakanne kuwa ya bawa hawayen dake cikin idanunnata daman gangarowa kan fuskarta. Cikin wata irin sassanyar muryar da babu wani me iya jin amo ko sautin sa tace. “Kana ina Yah M.Jay!!!â€? Zuciyata da tunanina kullum a kanka suke, lallai nayarda cewa SONKA NE k’addarata, haka zalika an rubutamin soyayyarka acikin jini da tsokana, tabbas ayau kawae kuma ayanzu naji ajikina cewa da gaske kaene k’addarata, k’addara mafi girma. “INASONKA Yah MALEEK INA MATUK’AR SONKA! hak’ik’a kuma koda ace bansame ka ba zan cigaba da sonka har mutuwata...â€? Idanu Oum Ayush ta zuba mata da kyau, sakamakon yanda taga tun d’azu bakinta na motsi amma kuma batajin amon sautin maganar nata acikin kunnuwanta. “Laylerh.â€? Ta k’ira sunanta cikin d’an d’aga murya. Hakanne kuwa ya zaburar da ita had’e da dawo da ita cikin hayyacinta, cikin sauri tasanya hannu ta shiga share hawayen dake kan fuskarta. Cike kuma da son daedae ta nutsuwarta ta d’ago kae ta kalli Oum Ayush d’in. Oum Ayush ko kasa d’auke idanunta daga kan Laylerh’n tayi, domin taga duk wani sigar damuwa ya bayyana k’arara akan fuskarta. Gama karantar yanayin Laylerh’n kuma da tayi ne yasa ta d’an numfasawa, ahankali tace. “Kibar duk wani tunani kici abincinki, tun d’azu ko loma d’aya bakiyi ba gashi sae hucewa yake, ko baki da lafiya ne?â€? Kai ta d’an girgiza cikin kuma muryarta da ta zama very slowly tace. “Kaina ne yake ciwo.â€? “Sannu kinsha magani ne?.â€? Cewar Oum Ayush tana me d’an daga kafad’anta. “A’a bansha ba.â€? “Okay kici abincin saikisha magani ko.â€? Jin ance Tasha maganine yasa ta kwab’e fuska, akasalance tace. “Ni nak’oshi da abincin zanje nasha magani kawai.â€? Batare kuma da tajira me Oum Ayush d’in zata ceba, tayi saurin mik’ewa tsaye, koda ta fara tafiya kuwa har k’afafunta suna hard’ewa saikace wata marar gaskiya. Da kallo kawae Oum Ayush ta bita harta fice daga cikin falon kafun ta d’auke kanta. Itama tashi daga kan dinning d’in tayi, domin dama duk sun kammala cin abincin, harta Momy Abbou Kareem na barin wajen itama ta tashi ta tafi. Jikinta amatuk’ar sanyaye haka ta koma sashinsu, koda ta shiga falonnasu kuwa bata samu Najeeb ba, saidai k’amshin turarensa wanda ya cika falon da tajine, ya tabbatar mata da cewar ya gama abunda zaiyi har ya shirya ya fita. Bata wani damu da zama acikin falon ba, direct d’aki ta wuce tayi kwanciyar ta akan gado, tare dajan blanket ta rufe jikinta dashi. Wayarta dake aje akan bedside drawer ta d’auka, tare da kunna data’nta ta shiga Tiktok dan son d’ebewa kanta kewa da kuma rage tunani. Munnira Da fuskarta wanda tasha uban meckup ta d’ago kae ta kalli mahaifiyarta ta dake tsaye agefe, itama tasha meckup da ado, kallo d’aya kuma zakayi musu dukansu kasan cewa suna cike da k’asaita, da kuma arrogance, babuma kamar Buzuwa wanda ita gaba d’aya jitake tafi kowa saboda y’arta zata shiga gidan k’asaita kud’i da kuma wayewa, kasancewar kuma yau zasu fara gudanar da events d’in da suka tsara na bikin shiyasa duk suka sha ado, mutanen da suka gayyata kuwa sae wane da wane, saboda ayanzu sunce sunfi k’arfin mutane masu d’an matsakaicin k’arfi, Dan nan da y’an kwanaki suna saran zamowarsu millionaires. “Mom.â€? Munnira ta k’ira sunan maman nata murya d’auke da damuwa. Jin yanayin yanda amon muryan Munniran yasanja ne kuma yasa Buzuwa juyowa batare da ta amsa ba ta fuskanci y’artata. Marairaice fuska Munniran tayi tare da kamo hannun Maman nata, murya k’asa k’asa tace. “Mama nifa agaskiya kwana biyunnan inacikin damuwa, tunfa lokacin da Captain Maleek yazo ya tafi bai kuma sake zuwa ba har yau, kuma ko d’an irin k’irana awaya d’innan ma bayyiba Anya ma kuwa yana sona kamar yanda nake sonsa?.â€? Jin abunda Munniran ta fad’ane yasa Buzuwa ta saki Murmushi tare da neman waje ta zauna, kamo hannun Munniran tayi cikin son kwantarwa da y’ar nata hankali tace. “Wannan sam bae kamata ya dameki ba Munnira, kuma da ace baya sonki ae kwata kwata bazae amincewa aurenki ba, kinsan irin mijin da zaki aura yawan ci kullum a busy suke, saboda haka karki damu kanki wae dan ayanzu baya nemanki, da zaran kinshiga gidansa to fa mungama dashi, Insha Allah shi da kansa zaina bibiyanki ke kuma kina ja masa aji, wannan alk’awarine na miki.â€? Wani irin murmushin jin dad’i Munnira tayi tare dayin fari da idanunta, cike dajin dad’in kalaman Mahaifiyar nata tace. “Shiyasa nake alfahari dake Mom, saboda nasan zaki tsayamin akan komae.â€? “K’warai kuwa kedae tashi muje Jama’a sunata jiranmu.â€? Cewar Buzuwa dake yunk’urin tashi tsaye. Mik’ewa Munniran tayi cikin jin dad’i da farinciki tabi bayan mahaifiyar tata suka fice. Ahankali yake taka steps d’in da zae bashi daman k’arasa shigowa cikin falon, sanye yake da dogon wandon uniform d’insa na soldiers da kuma wata white rubber crazy shirt, sosae kayan sukayi masa kyau, saidai kuma gaba d’aya yanayinsa ya sanja, kallo d’aya zaka masa kafahimci cewa baya cikin yanayi me dad’i, saboda duk wani alaman rashin lafiya ya bayyana ajikinsa, yayinda yabar yalwataccen beard akan fuskarsa, wanda hakanne kuma ya k’ara k’awata fuskar tasa. Kasalalliyar ajiyar zuciya ya sauk’e adaedae lokacin da ya gama sauk’owa daga kan steps d’in, wanda kuma hakanne ya bashi daman samun kansa acikin k’awataccen falon. Sauk’e idanunsa da yayi kuma akan hoton Laylerh ne yasa shi d’an lumshe idanunsa tare dasa hannu ya dafe daedae saitin zuciyarsa dake beating da sauri, sam baisan meyasa ba hakanan yau tun tashinsa yake jin fad’uwar gaba da kuma wani irin tsinkewar zuciya mai tsanani, hakanne ma yasashi rik’e addu’a k’am abakinsa, amma kuma wani abun mamakin har yanzu baiji bugun zuciyar tasa ta lafa ba, yayinda ajikinsa yakejin kamar wani abu ne zai samesa yau d’in, jin kuma da yayi gaba d’aya zaman gidan ya dameshi ne yasashi shiryawa tsab dan zuwa zaga gari ko hakan zae rage masa kewa da kuma kad’aicin dake damunsa. Domin tunda yazo gidan gaba d’aya tunanin Laylerh ya hanasa sukuni, ko idanunsa ya rufe ita kawae yake gani. Car key d’insa dake aje akan d’an madaidaicin table d’in dake cikin falon ya d’auka, sannan kai tsaye ya nufi hanyar fita daga cikin falon. Batare kuma da ya tsaya locking k’ofar falon ba kaitsaye ya nufi wajen da motarsa k’irar Mercedes benz ke fake, akasalance ya bud’e murfin motar ya shiga, duk da kuwa cewar baya wani jin k’arfi sosai ajikinsa, haka ya daure ya tada motar. Kasancewar kuma yasa Abdoul ya ne momasa maigadi ne yasa kafun ya iso bakin gate d’in ma tuni maigadin ya wangale masa k’ofa, hakan yasa kaitsaye ya cilla hancin motar tasa kan shumfud’adden titin da ya mamaye gaba d’aya unguwar. Tafiya kawae yake akan shumfud’add’en titin batare da yasan inda ya dosa ba, daga gefe guda kuwa mood d’insa ne keci gaba da sauyawa daga yanayin farinciki zuwa akasin hakan. Fad’uwar gaban da yakeji ne ya tsananta, wanda hakan yasa shi cigaba da ambaton sunan Allah Abakinsa. Daidai ya sha wata kwana, d’aya daga cikin wayoyinsa k’iran Samsung Galaxy fold 2 ta soma k’ara, kasancewar kuma yau ya kunna wayoyin nasa ne yasashi maida kallonsa ga wayar dan ganin wake k’iransa. *Hak’ik’a wannan lokacin,da kuma way’annan y’an sakannin sune mafarin k’addaransa ta biyu, sannan kuma mafarin tsautsayi, tsautsayi me matuk’ar girgiza rayuwa, lallai wannan itace k’addaran da zata sauya masa rayuwa, K’addara mafi girma agaresa. Tabbas kamar yanda Babu wanda ya isa gujewa mutuwa, haka ma babu wanda ya isa gujewa K’addaransa. Lallai dole abu biyu zasu kasance Arayuwar Maleek farinciki ko akasin haka, tabbas sae da wata k’addaran wani MURADI da kuma BURI ke samun daman cika.* Maida idanunsa ga wayar tasa da yayine, yasa batare da sani ko ankara ba motarsa da kuma wata motar da ta shawo kwanan sukayi wani irin mummunan karo, wanda hakan yasa duka motoci biyun sukayi wani irin k’ara da kuma mummunan buguwa har saida yakai ga kowaccensu ta fad’i rigingine. *(Dan Allah Banason yawan k’orafin da kukemin kan cewar wae na takurawa Maleek da yawa, Wallahi haka labarin LaylerhMaleek yake, ba kuma naso na sanja ko kuma na cire wani abu daga ciki, Dan Allah Kudaena nunamin cewa kamar bansan me nake rubutawa ba, nasani kuma Idan kukayi hak’uri komae zai tafi Normal rashin hakuri shi zaisa kuga kaman anayin ba daidaiba🙏🏻🙏🏻🙏🏻 kuyi hakuri mun koma school wallahi shiyasa duk bana samun zaman yin editing.)* *5February/2021* 3:45 pm 2/8/21, 9:26 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna *Note edit* *Chapter 49* Ahankali ta bud’e idanunta wanda suka share kusan one hour a kulle, cikin sauri tasanya hannunta ta dafe daidai saitin zuciyarta dake wani irin mummunan bugawa, yayinda kuma lokaci d’aya taji wani irin tsinkewar zuciya had’i da fad’uwar gaba me k’arfi ya ziyarceta. “Subahanallah!!â€? Tafad’a cikin wata irin muryarta da tayi sanyi sosae, Jin da tayi kaman ana buga mata guduma a tsakiyar kanta ne yasata tashi zaune, tare da zuro da k’afafunta k’asa. Idanunta tad’an lumshe tare da sake dafe daidai saitin zuciyarta, da har yanzu ke cigaba da bugawa, tabbas batasan da yaushe ne bacci ya d’auketa ba, ita dai tasan cewa kafun yanzun ta rik’e wayartace a hannunta tana kallo. Ahankali ta d’aga kanta ta kalli babban agogon bangon dake sak’ale acikin d’akin, ganin da tayi lokaci ya d’an ja ne yasa ta yunk’ura ta sauk’o daga kan gadon gaba d’aya. Ahankali cikin rashin k’arfi da kuma kuzarin da ta samu kanta aciki ta wuce toilet. Yanayin yanda k’aran fad’uwar motoci biyun suka cika gaba d’aya wajenne yayi sanadiyar dawowan hankalin mutane garesu, ganin irin mummunan accident d’in da akayi ne kuma yasa, hankalin jama’an dake wajen yayi mummunan tashi, domin tuni har d’aya daga cikin motocin tafara hayak’i. Hakan yasa cikin gaggawa da kuma son ceto rayuka, Jama’a suka nufi wajen da motocin suke da gudu. Lokaci d’aya wasu daga cikin mutanen suka soma k’ok’arin ciro Maleek da kuma d’ayan mitumin daya kasance shine matuk’in d’aya motar, yayinda wasu kuwa suka shiga k’iran emergency dan basu taimakon gaggawa. Kasancewar motocin duk sun kwanta ne yasa da k’yar mutanen suka iya ciro ko wannensu daga cikin motarsa, saidai kuma abunda ya k’ara d’agawa jama’ar dake wajen hankali shine, babu mutum d’aya acikinsu dake numfashi, sannan gaba d’ayansu duk jini ya wanke musu fuska. Salati da sallallami kawae jama’ar wajen keyi, domin ganin da sukayi ya nuna musu cewa, dukansu basa numfashi, da alaman ma cewa babu rai ajikinsu. Nanfa wasu daga cikin mutanen dake tsaye awajen suka shiga duba motocin acewarsu ko zasu samu wayoyinsu da kuma ID card dan sanin ko sud’in su waye, ta yanda za’a samu asauk’ak’e asanar da y’an uwansu. Cikin sa’a kuwa suka tsinci wayar Maleek da kuma ID card d’insa, abun mamakin kuwa wayarsa ko fashewa d’aya batayi ba, tana nan normal, hakama na d’ayan me motar saidai nashi screen d’in wayar ta d’an fashe kad’an. Isowan Emergency wajen cikin gaggawa ne yasa mutanen suka taimaka musu wajen saka su Maleek d’in acikin mota, duka wayoyi da kuma ID card d’in da suka samu suka mik’awa ma’aikatan lafiyan. Nanfa cikin gaggawa motar Emergency d’in ta kama hanya zuwa babban asibitin nan me suna Nizamiyye Hospital. Yanayin yanda motar Emergency’n ke matsanancin gudu ne kuma yasa cikin y’an k’alilan d’in mintuna suka samu isowa cikin harabar babban asibitin. Da wani irin sauri Doctor’s suka zo da irin gadon nan da ake d’aukan marassa lafiya acikinsa. Anan kan gadon aka d’auki kowannensu cike dason basu taimakon gaggawa kaitsaye aka wuce dasu Intensive Care Unit wato (ICU) dan basu taimakon gaggawa kasancewar duk acikinsu babu wanda yake numfashi. Likitotine wanda ak’alla zasu kai guda 6 suka duk’ufa akan Maleek wanda kansa keta faman zubda jini, tabbas babu numfashi ajikinsa, amma kuma wani babban abun mamakin shine zuciyarsa na bugawa, al’amarin daya d’aure musu kai kenan, sanin kuma da sukayi cewar Idan har basu dage wajen yin k’ok’arin dawo da numfashinsa ba to tabbas bugun zuciyartasa ma zai iya tsayawa, hakan kuma zai iya jawo sanadiyar rasa rayuwarsa gaba d’aya, nan fa cikin azama suka shiga k’ok’arin tsaida jinin dake zuba akansa, kasancewar ya bugu sosae akannasa shiyasa yake ta zubarda jini ba k’akk’autawa, Uwa uba kuma duk glasses d’in motar ya caccake masa jiki. Sab’anin abokin accident d’in nasa da buguwa kawae ya samu, akai da kuma k’afarsa, saidai kuma buguwar k’afartasa yafi na ko ina muni, dan k’afartasa taji ciwo sosae, saidai shi bashi da wata matsala bayan wannan, Inda kuma cikin sauk’i likitotin dake kansa suka samu daman ceto numfashinsa, ganin kuma da sukayi cewar akoda yaushe zai iya dawowa cikin hayyacinsa ne, yasa suka kaishi wani d’aki na daban. Yayinda doctors d’in dake aiki akan Maleek kuwa suka ci gaba da gudanar da aikinsu, domin har yanzu sun kasa samo numfashin Maleek d’in. Laylerh Ahankali ta bud’e murfin k’ofar bathroom d’in ta fito, yayinda fuskarta da kuma hannaye da k’afafunta ke d’auke da danshin ruwa, wanda hakan nuna cewar alwala ta d’auro acikin toilet d’in. Cikin yanayin sanyin jikin da takejin kanta aciki ta k’arasa gaban drawer’nta, ta ciro wani d’an madaidaicin Hijab d’inta ta saka, juyawa tayi tare da jingina bayanta da jikin drawer’n ahankali ta lumshe idanunta, wanda tun d’azu takejin k’walla nason taruwa acikinsu wanda kuma sam batasan dalilin hakan ba, gaba d’aya tun tashinta abacci takejin mood d’inta ya sauya batare kuma da tasan dalilin hakan ba, fad’uwar gaba take taji, da wani irin tsoro wanda batasan daga inane yake b’ullowa ba, babban abunda ke k’ara da gula mata lissafi kuwa shine tunanin Maleek dake fad’o mata akai akai, wanda kuma hakanne ke haifar mata da k’arin bugun zuciya. “Yah Allah Kasa komai yazomin cikin sauk’i, Allah Kaga zuciyata ayanzu gab take da bugawa, ina rok’oka kada ka tabbatar da mummunan mafarkin da nayi akan Yah M.Jay, Ya Allah Kaduba maraicin mu!!!â€? Tafad’i hakan cikin muryarta da tayi rauni sosai, tare dasa d’an yatsanta ta share hawayen dake k’ok’arin sauk’a daga cikin idanunta. Hak’ik’a ayanzu nutsuwar zuciya da kuma farinciki takeso, domin su kad’aice zasu kore mata tsanancin tsoron da takeji. Asanyaye cikin bawa kanta k’warin guiwa ta k’arasa gaban d’an madaidaicin carpet d’in dake shumfud’e a gefen gadonta, wanda kuma an shumfud’a carpet d’inne musamman dan akeyin Sallah akansa. Daidaita tsayuwarta akan carpet d’in tayi, tare fuskantar gabas ta tada sallah’n azahar wanda tuni masallacin dake gefen gidannasu har sun shiga salla’n. Kasancewar ayanzun kusan k’arfe 1 da wasu y’an mintuna ake nema. Koda ta idar da sallan kuwa anan kan sallayan ta kwanta, duk da cewar tanajin yunwa na k’wak’ulan cikinta amma batajin zata iya saka ko wani irin abinci acikinta. After 1hour. Kusan atare gaba d’aya likitotin da har yanzu ke tsaye akan Maleek d’in suka d’ago kansu suka kalli juna, yayinda kowannensu yanayin fuskarsa ke d’auke da matsanancin damuwa, tabbas sunsha wahala matuk’a wajen ganin Maleek d’in ya tsira da numfashi, sunkuma yi sa’a domin Allah Ya dafa musu wajen ganin sun dawo masa da numfashinsa, duk da cewar bai farfad’o ya dawo hayyacinsa ba, amma tabbas suna saka ran farfad’owarsa akoda yaushe, ganin da sukayi kuma ya bugu sosai akansa da kuma sauran sassan jikinsa ne yasa suka d’anyi masa gwaje gwaje dan tabbatar da lafiyar jiki da kuma na kansa, sunji dad’i k’warai da sukaga cewar buguwan da yayi akannasa bai tab’a masa kansa ba, saidai wani babban matsala da suka gani daga wani waje na dabanne yasa su shiga alhini tare dajin matsanancin tausayin Maleek d’in ya cika musu zuciya. D’aya daga cikin doctors d’inne yayi masa duk wasu alluran da suka dace, sannan sukayi treating duk wani ciwo dake jikinsa, duk dama ciwukan nasa y’an k’ananan yankane daya samu ta sanadin glasses d’in da suka d’an cakesa. Nanfa biyu daga cikin doctors d’in suka tura gadon da yake cikin wani special room, inda babu yawan hayaniya sosai. After 2hours Acan gida kuwa Abbou Jaheed ne zaune acikin katafaren falonsa wanda yaji komai da komai na more rayuwa, domin kuwa falo ne wanda ya amsa sunan falo, irin na manya manyan masu kud’i da kuma matsayi. Zaune yake akan d’aya daga cikin luntsuma luntsuman kujerun dake cikin falon, agabansa kuwa wani babban stool ne wanda samansa ke d’auke da wasu invitations card’s masu yawan gaske, d’aya bayan d’aya kuwa haka yake d’aukan cards d’in yana dubawa, da dukkan alamu kuma katunan dake gabannasa na d’aurin auren Maleek ne. Turo k’ofar falon da kuma sallaman da yaji anyi ne yasashi d’ago kansa, abakinsa kuwa yana me amsa sallaman, da Abbou Khareem da kuma Fou’ad ne sukayi ta. Ganinsu da yayine yasashi d’an sakin murmushi, tare da cewa. “Kuyi hak’uri na d’ago ku akan uzururrukan da kukeyi.â€? Murmushi dukansu sukayi tare da k’arasowa cikin falon, wato inda Abbou Jaheed d’in ke zaune. “Babu komae Yayah Allah Dai yasa muji alkhairi.â€? Cewar Abbou Kareem fuskarsa d’auke da yalwatacciyar murmushi. “Insha Allah Ma alkhairi ne.â€? Abbou Jaheed ya fad’a yana me d’an gyara zama. Fou’ad kuwa dake k’ok’arin zama akan had’adden sofan dake malale atsakiyar falon, cikin girmamawa yace. “Abbou barka da gida.â€? “Yauwa barka dae Malam Fou’ad ya aiki, da kuma fama da Jama’a?.â€? “Lafiya Alhamdulillah.â€? Fou’ad ya amsa yana me d’an shafa kansa. “To Masha Allah dama haka akeso.â€? Abbou Jaheed ya fad’a yana me k’ok’arin har had’a cards d’in dake zube agabansa. Shiru sukayi na d’an wani lokaci kafun Abbou Jaheed d’in ya zaro wasu daga cikin invitations cards d’in dake gabansa ya mik’awa kowannensu, fuskarsa d’auke da damuwar da sam ya kasa b’oyeta afili da kuma bad’ininsa yace. “Ga katin auren Maleek nan, d’azu way’anda na bawa kwangilan bugawa suka kawomin, abunda yasa na k’iraku kuma kenan, domin nasan kuma kunada naku jama’an da zaku gayyata, gasunan sai ku d’ebi wanda zai isheku.â€? Ya k’are maganar yana me tura musu katunan gabansu. Jin abunda Abbou Jaheed d’in ya fad’ane kuma yasa, Fou’ad d’ago kai ahankali ya maida dubansa ga Abbou Jaheed d’in, wanda take ya karanci zallan damuwa akan fuskarsa, tabbas yasan abunda Abbou Jaheed d’in keyi k’arfin haline kawae, saboda kallo d’aya zakayi masa kafahimci cewa yana cikin damuwar rashin ganin d’ansa. Ajiyar zuciya ya sauk’e kana jikinsa amatuk’ar sanyaye, cikin ladabi da kuma sanyin murya ta yanda ya tabbatar cewa Abbou Jaheed d’in zai fahimcesa yace. “Kayi hak’uri da abunda zan fad’a Abbou domin nasan ba lallaine yayi maka dad’i ba, saidai kuma ya zama dole na fad’a maka cewar kwata kwata Maleek bayason auren nan, domin saboda hakanne ma yaje ya b’oye kansa awani waje, wajen da babu wanda yasani acikin mu, hak’ik’a inajin tsoron abunda zaije ya dawo bayan an d’aura aurennan, saboda akullum Maleek yana ikirarin cewa shi bazai tab’a zama da wata mace ba, burinshi akoda yaushe shine yayi rayuwarsa shi kad’ai, please Abbou Dan Allah Ajanye maganar auren nan.â€? Murmushi me d’auke da dattako Abbou Jaheed yayi, tare da d’ago kansa ya kalli Fou’ad d’in. Tabbas shi kansa ya jima da fara irin wannan tunanin, amma kuma saidai yasan ko kad’an babu alfano acikin tunanin nasa, barin cikakken Namiji me lafiya kamar Maleek babu aure sam ba daidai bane, saboda arayuwar ko wani d’a Namiji me lafiya yana buk’atar Mace, domin Mace itace duk wani ginshik’in jin dad’i, saida Mace arayuwar ko wani Namiji zai kasance acikin farinciki, tabbas Mace itace komai na rayuwar d’a Namiji, domin saida mace ne kowani Namiji zaisan wanene shi. Ajiyar zuciya Abbou Jaheed d’in ya sauk’e, tare dayin gyaran murya, cikin tausasa kalamansa yanda yake da yak’inin cewa Fou’ad d’in zai gamsu yace. “Bawai ina son tursasawa Maleek koyi masa auren dole bane, ina duba abunda ya dace ne, hak’ik’a burin kowani uba shine yaga ya aurar da y’ay’ansa bawai y’ay’ansa mata ba kawae harda maza, domin barin cikakken Namiji baligi agida wanda ya haura shekaru 30 ba daidai bane, matuk’ar yana da lafiya kuma yana da halin yin aure to yayi kawai, saidai kuma idan yana da hujjar cewa bazae tab’a kusantar zina ba, wannan zai iya zama yayi rayuwarsa shi kad’ai, tabbas ada bandamu akan Maleek yayi aure ko a’a ba, domin duk da cewa zuciya bata da k’ashi, amma Ina da yak’ini akansa, tabbas Ina da yak’inin cewa ban haifi fasik’i ba, hak’ik’a najima da bawa Maleek zab’i akan ya nemo matar da yakeson aura, amma yayi watsi da magana ta, haka na hak’ura na k’yalesa, nabarsa ne kuma saboda inaso naga iyaka gudun ruwansa, saboda tabbaci da nake dashi akansa, saidai kuma lokaci d’aya ya ruguza duk wata yarda ta da nake dashi akansa, nagansa da idanuna ya dawo gida acikin maye, cikin k’azamammen yanayin da duk wani Uba na duniya bazai so yaga d’ansa aciki ba, tabbas nasan Ilan maye, yakansa mutum ya aikata komai, ciki kuma harda zina, to Fou’ad ka gayamin tayaya zanbar tilon d’ana Maleek ya kasance acikin irin wannan halin? wannan dalilin shiyasa na yanke hukuncin d’aura masa aure ko da yana so ko bayaso, bankuma yi hakan don banason sa ba, saidan Ina guje masa fad’awa halaka da kuma tsinuwar Allah..â€? Sosae jikin Fou’ad yayi sanyi asakamakon jin kalamai da kuma hujjar Abbou Jaheed nason yiwa Maleek aure, hak’ik’a ada yana ganin kamar cewa Abbou Jaheed d’in nason tauye Maleek ne, amma ayanzu tabbas ya fahimci komai, domin shi kansa yana da yak’inin cewa matuk’ar Maleek d’in ya fara shaye shaye to watarana maye zata iya sawa ya aikata ba daidaiba, domin sarai yasan abokinnasa yana da k’arfin sha’awa. Baki ya bud’e da niyar cewa wani abu amma kuma saidai k’iran da ya shigo wayar Abbou Jaheed ne yasashi tsuke bakinsa. Abbou Jaheed kuwa akaron farko kenan da yaji k’iran waya ya tsinkar masa da zuciya. Asanyaye ya kai hannu ya d’aga wayar, duk da cewar bakuwar number ya gani amma hakan bai hanashi d’agawa ba tare da kara wayar akan kunnensa, sallaman da akayi masa ya amsa, saidai kuma jin abunda wanda ke kan wayar ke fad’ane yasashi jin wani irin matsanancin fad’uwar gaba da kuma tashin hankali me tsanani wanda har saida ya kaisa ga mik’ewa tsaye, cikin kid’ima da kuma rud’ewa ya ambaci kalmar “Innalillahi Wa’inna Ilaihirraju’un!!!â€? Batare kuma daya daidaita nutsuwarsa ba yasaki wayar tasa ta fad’i k’asa. Hakan da yayin kuwa shiya saka hankalin su Abbou Khareem da kuma Fou’ad yayi wani irin masifaffen tashi, cikin yanayin mamaki da kuma rud’ewa suka shiga tambayarsa ko lafiya. Kasa amsa musu yayi sai sa hannu da yayi ya dafe daedae saitin zuciyarsa, da kuma k’irjinsa dake bugawa sosae, ganin hakane yasa Fou’ad nufar wajen fridge ya d’auko goran ruwa me sanyi, mik’awa Abbou Jaheed d’in goran ruwan yayi, cikin yanayin damuwa yace. “Abbou lafiya meyake faruwa ne?.â€? Wani irin numfashi Abbou Jaheed da gaba d’aya hankalinsa baya jikinsa yayi, cikin muryarsa da ta sark’e yace. “Maleek ne yayi accident, Khareem Maleek d’ana yayi accident, baisan inda kansa yake ba, Innalillahi Wa’inna Ilaihirraju’un, Ya Allah Kasa kada na zamo silar rasa rayuwar.......â€? Cikin tashin hankali Abbou Khareem yasa hannunsa ya toshewa Yayan nasa baki, kansa ya d’an girgiza cike dason samarwa d’an uwannasa nutsuwa yace. “Kada kace haka Yayah Allah Yana tare damu, yafi kowa sanin niya da kuma nufin dake cikin zuciyarka, awani asibiti Maleek d’in yake, mu hanzarta zuwa dansanin halin da yake ciki.â€? “Nizamiyye hospital!â€? Abbou Jaheed d’in ya fad’a da muryarsa wanda take fitar da zallan tashin hankalin da yake ciki. Yayinda Fou’ad kuwa tsabar shocking d’in da ya samu kansa aciki, kasa furta komai yayi, sai jikinsa dake ta faman karkarwa. Hannun Abbou Jaheed d’in Abbou Khareem ya kamo cikin dauriya yace. “Muje muje lokaci na k’urewa.â€? Haka suka fice daga cikin falon dukansu babu wanda yake da gamsashshiyar nutsuwa atattare dashi, ko awajen tuk’in mota ma Fou’ad ne ya iya dauriyan tuk’asu, saidai kuma irin gudun da yake tsulawa yasa duk wanda ya ga motar tasu saidai ya kauce ya basu hanya. Yanayin yanda Fou’ad d’in ke gudu kaman zai tashi sama ne yasa cikin mintuna kad’an suka iso farfajiyar asibitin. Ko tsayawa gama daidai ta parking baiyi haka suka fito cikin tashin hankali sukayi cikin asibitin, murafen motar ma a bud’e suka barsu. Abbou Khareem ne ya d’auki wayar Abbou Jaheed d’in ya k’ira numbern da aka k’irasu dashi d’azun dan sanin inda aka ajiye Maleek d’in. Da yake kuma numbern na d’aya daga cikin doctors d’in asibitin da suka karb’i Maleek d’inne, yasa cikin sauk’i Doctorn ya musu kwatancen office d’insa, suna zuwa kuwa suka samu duka doctors d’in atare awaje d’aya. Ganin irin tashin hankali da kuma damuwan dake d’auke akan fuskokinsu ne yasa Doctors d’in soma k’ok’arin kwantar musu da hankali. Ta hanyar ce musu Maleek d’in yana nan lafiya. “Kufad’amin idan wani abu ya samu d’ana, yana Ina ku kaini naga Maleek, shi kad’aine d’an dana Haifa aduniya Dan Allah ku fad’amin cewa Maleek yana darai bai mutu ba!!!â€? Abbou Jaheed ya fad’i hakan cikin tashin hankalin da yakejin kansa aciki. Murmushi Dr.Mouhammad yayi, wanda shine babban likitan dake kan case d’in Maleek d’in, cikin son kwantarwa da Abbou Jaheed d’in hankali yace. “Alhaji Jaheed Gwani ka kwantar da hankalinka domin d’anka bai mutu ba, domin tabbatar da hakan kuwa kana iya Bina muje kaga d’anka.â€? Ae ma kafun Dr Mouhammad ya rufe bakinsa, tuni Abbou Jaheed yace. “Muje Doctor muje nagansa.â€? Shigewa gaba Dr Mouhammad yayi, yayinda su Abbou Jaheed suka rufa masa baya. Kaitsaye d’akin da Maleek d’in ke kwance suka nufa, bud’e musu k’ofar d’akin Dr. Mouhammad yayi tare dayi musu alama akan su shiga, riga rigen shiga kuwa sukayi, yayinda kuma suna shiga suka sauk’e idanunsu akan Maleek d’in dake kwance flat akan gado, kansa nad’e da bandage. Cikin sauri Abbou Jaheed ya k’arasa kusa da gadon, tare dasa hannayensa duka biyu ya rungume Maleek d’in, lokaci guda yaji wasu irin hawaye sun cika idanunsa, matsanancin tausayin d’annasa ne ya kamasa, hakan yasa ya d’aura kansa akirjin Maleek d’in daidai inda zuciyarsa take, wani irin ajiar zuciya me k’arfi ya sauk’e alokacin da kunnuwansa suka jiye masa sautin bugun zuciyar Maleek d’in, cikin zuciyarsa yace. “Alhamdulillah!â€? K’arasowa wajen Maleek d’in su Abbou Khareem da Fou’ad sukayi, cike da tausayin Maleek d’in suka shafa kansa dake lik’e da bandage. Gaba d’ayansu tausayi suka bawa Dr.Mouhammad hakan yasa shi d’anyin gyaran murya cikin kulawa yace. “Ayanzu Maleek hutu yake da buk’ata, bazan hanaku zama awajensa ba, amma saidai ku kiyaye yin surutu, sannan zai iya bud’e idanunsa any time, zuwa anjima kad’an akwai alluran da zanzo na sake yi masa, so dan Allah Ku kula sosae.â€? “Insha Allah Zamu kula doctor.â€? Cewar Fou’ad dake k’ok’arin maida k’wallan dake cikin idanunsa. Kai Dr.Mouhammad ya jinjina, anutse yasa kai ya fice daga cikin d’akin, zuciyarsa cike da alhinin ta yanda zai fara fad’awa Alhaji Jaheed abunda ya samu d’ansa sanadiyar accident d’in da yayi. Fitan Dr. Mouhammad ne yasa su Abbou Jaheed d’in neman waje suka zauna, nan fa Abbou Khareem ya zaro wayarsa dake cikin aljihunsa, ya turawa Oum Ayush sak’on cewa Maleek d’in yayi accident, bayan ya tura mata sak’onne kuma ya turawa Momy da kuma Najeeb suma, daga haka baisake turawa kowa ba ya ajiye wayartasa. Acan gida kuwa Oum Ayush dake zaune tana kallo, Jin alamar shigowan sak’o cikin wayarta ne yasa ta d’aukan wayar ta duba, saidai kuma ganin abunda ke rubuce ajikin sak’on ba k’aramin d’aga mata hankali yayi ba, take cikin matsanancin damuwan da ta samu kanta aciki tayi dialing numbern Abbou Khareem d’in, cikin sa’a kuwa tana k’ira ya d’aga, Jin yanda hankalinta ya tashi sosae ne kuma yasashi soma k’ok’arin kwantar mata da hankali, ta hanyar fad’a mata cewar Maleek d’in bai wani ji ciwo sosai ba. Nantake kuwa tace masa gatanan zuwa. “Kitaho da Laylerh.â€? Abunda ya fad’a kenan ak’arshe ya kashe wayar. Cikin gaggawa kuwa Oum Ayush ta d’auko mayafinta, tare da makullin motar ta, koda ta fito daga sashin nasu kai tsaye sashin su Laylerh’n ta nufa. Kusan sau biyu tayi knocking k’ofar falon amma shiru ba’a amsa mata ba, kasancewar damuwa ne kwance aranta, hakan yasa batare da wani tunani ba ta tura k’ofar falon ta shiga, ganin da tayi kuma babu kowa acikin falonne yasa ta shiga k’walawa Laylerh’n k’ira. Laylerh kuwa da har yanzun ke kwance anan kan carpet d’in da tayi sallah, kamar daga sama taji muryan Oum Ayush na kwad’a mata k’ira, hakan yasa cikin sauri ta mik’e tsaye, tare da bud’e k’ofar d’akin ta fice. Ganinta sanye da Hijab ne yasa Oum Ayush kamo hannunta, cikin muryarta da tayi sanyi sosae tace. “Zo muje ki rakani wani waje Laylerh.â€? Batare kuma da ta jira me Laylerh’n zata ceba ta kamo hannunta suka nufi hanyar fita daga falon. Fuskar Laylerh’n d’auke da mamaki had’i da rud’u tace. “Oum Ayush Ina zamuje?, bani da takalmi kibari na d’auko takalmi na.â€? Jin abunda tace ne yasa Oum Ayush tsayawa, tare da cewa. “Kiyi sauri ki d’auko takalmin naki.â€? Ganin damuwa kwance akan fuskar Oum Ayush d’inne yasa Laylerh juyawa cikin sabon faduwar gaban da ta samu kanta aciki ta koma cikin d’aki, wani black half cover shoe me tsananin kyau tasa ak’afanta, cikin sauri ta fito. Sake kamo hannunta Oum Ayush tayi suka fice daga cikin falon. Ita dai kam kamar rak’umi da akala haka take bin bayan Oum Ayush d’in. Har saida suka iso jikin mota kafun Oum Ayus d’in ta sake mata hannu. Nanfa Oum Ayush ta shiga wajen driver itakuwa ta shiga gefen me zaman banza. Da wani irin speed Oum Ayush ta ja motar yayinda maigadi ya wangale musu gate suka hau saman shumfud’add’en titin dake malale a k’ofar gidan. Tunda suka shiga motar Laylerh ke kallon Oum Ayush da gaba d’aya yanayinta ya nuna cewa tana cikin damuwa. Asanyaye kana cikin voice d’inta dake cracking tace. “Oum tun safe k’irjina bugawa yake, gaba na yana ta fad’uwa, tsoro nakeji matsananci, Dan Allah Oum kifad’amin meke faruwa? Kuma Ina zamuje haka?.â€? Shiru Oum Ayush tayi ta kasa amsawa Laylerh’n tambayoyinta, daidai lokacin kuwa suka kawo cikin asibitin. Ganinsu acikin asibiti ne kuma yasa Laylerh zaro manya manyan idanunta, cikin matsanancin tsoro tace. “Wayene bashi da lafiya Oum, Dan Allah Karki cemin Yah M.Jay ne, karki cemin mafarkina na jiya ne yakeson zama gaskiya, pleaseee.....â€? da katawa da tafiyan Oum Ayush tayi tare da juyowa ta fuskanci Laylerh’n, cikin muryarta da yayi sanyi sosae tace. “Shi ne Laylerh Maleek ne yayi accident!â€? Wani irin bugawa zuciyar Laylerh tayi wanda yayi sanadiyar durk’ushe wanta awajen, tare da zub’e guiwowinta ak’asa. 8February/2021 *7:30 pm* 2/13/21, 7:53 AM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna *Chapter 50* Kyawwwan idanunta ta runtse da k’arfi wanda hakan ya bawa hawayen dake cikinsu daman gangarowa kan fuskarta, cikin matsanancin tsoron da ya shigeta ne kuma, ta soma girgiza kanta ahankali, yayinda take kuma lokaci guda jikinta ya soma b’ari, tamkar wacce aka jonawa shocking, ahankali labb’an bakinta suka soma d’an motsawa, da’alama kuma wani abu take son fad’a daga bakinnata, amma takasa. Ganin hakanne kuwa yasa Oum Ayush da gaba d’aya jikinta ya riga da yayi sanyi tasa hannu ta dafa kad’an Laylerh, cikin muryarta dake bayyana zallan tausayin ta tace. “Ki kwantar da hankalinki Laylerh, domin kuwa Ina da yak’inin cewa da izinin Ubangiji mai sama da k’asa babu wani abu da ya samu Maleek, koda ma kuwa ace yana cikin wani hali na rashin dad’i, ayanzu addu’ar mu yake da buk’ata bawae kuka ko firgicewa ba, ki tashi mu k’arasa cikin asibitin kinji, Dan Allah Karki ce zakiyi kuka.â€? Tak’are maganan nata tana me yunk’urin mik’ar da Laylerh’n tsaye, wanda tuni hawaye sun wanke mata fuska, yayinda wani hawayen na korar wani. D’agota Oum Ayush d’in tayi, wanda hakan kuwa yasa tsab ta mik’e tsaye kamar yanda Oum Ayush d’in ta buk’ata, saidai kuma ko kad’an ta kasa iya daidaita nutsuwarta, wani irin tsalle k’irji da zuciyarta keyi kaman zasu fito waje, domin kuwa ta sake samun kanta acikin k’arin fargaba da kuma tashin hankali, asakamakon jin da tayi cewa M.Jay d’inta ne bashi da lafiya. Cikin wata irin muryar dake shaking, kana kuma wanda take bayyana tsananin tsoron dake cikin zuciyarta, murya ararrabe tace. “Tsoro Nakeji Oum Ayush, Wallahi tsoro nakeji, nasani dama tunjiya nakeji ajikina cewar wani abu zai sameni, nayi mafarki cewar Yah M.Jay yayi accident, amma kuma da na fad’awa Najeeb sai ya k’aryatani, nasani dama da yawan mafarkaina akansa gaskiya ne, wayyo Allah Na tayaya zan iya d’aukar wannan k’addaran? Tayaya zan iya jurewa? Tabbas nasan cewa aduniya babu wanda zaisan me nakeji ajikina aduk sanda wani abu na cutarwa ya samu Yah M.Jay, wallahi nayi imani cewa akansa zan iya mutuwa, Oum Ayush ki tab’a zuciyata kiji, Wallahi gab take da rabewa gida biyu, menakeji wazai san me nakeji babu, babu wanda zai gane hakan sai ni kad’ai, tabbas K’addarorin Ubangiji sun cika rayuwarmu ....â€? kasa k’arasa maganan nata tayi, saboda wani irin kuka daya so kwace mata. Hakanne kuma yasa Oum Ayush tayi saurin sanya hannu ta toshewa Laylerh’n baki, domin kuwa itama tuni idanunta sun ciko da kwalla, yayinda wani irin matsanancin tausayin Laylerh’n ya cika mata zuciya, k’warai tasan cewa akwae wata soyayya me tsananin zafi dake tsakanin Laylerh da Maleek d’in, amma sam batasan da cewar k’arfin d’i maucewar Soyayyar tasu har takai haka ba. Cikin son arawa kanta jarumta da kuma bawa Laylerh’n k’arfin guiwa tace. “Ya isa haka Laylerh, kuka da fad’an wasu maganganu ba naki bane, muje ciki kawae.â€? ta k’are maganan agajarce tana me kuma kama hannun Laylerh’n batare da ta jira ta bakinta ba suka kutsa kansu cikin asibitin, domin dama tuni Abbou Khareem yayiwa Oum Ayush d’in kwatancen d’akin da aka kwantar da Maleek d’in kuma ta gane, shiyasa ma bata tsaya tambayar kowa ba, kaitsaye suka nufi sashin da zai sadasu da d’akin, duk da cewar wajen privet waje ne babu yawan hayaniyan mutane da kuma sawunsu. K’warai da gaske Laylerh bata gamsu da cewar akwae wani abu wai shi tsoro, fargaba da kuma bugun zuciya ba saida ta ga sun tsaya adaidai bakin wata k’ofa wanda take akulle gam, ahankali tasa hannu ta dafe daidai saitin zuciyarta dake wani irin bugawa akaron na barkatai, lokaci d’aya kuma taji numfashinta nayin sama da k’asa cikin yanayin fusga tamkar wanda zae d’auke gaba d’aya. Daidai lokacin ne kuma Oum Ayush da ita kanta jikinta ke ta faman tsuma tasa hannu ta bud’e k’ofar d’akin, ahankali ta kutsa kanta ciki, yayinda bakinta ke d’auke da sallama. Su Abbou Khareem dake zaune akan wasu fararen kujerune suka amsa mata, ciki kuwa harda Najeeb wanda da zuwansa asibitin zuwa yanzu da yake cikin d’akin bai wuce 14 minutes ba, kasancewar lokacin da Abbou Khareem ya k’iarasa ya fad’a masa yana kusa da asibitin shiyasa bai wani d’au lokaci ba ya taho. Turus haka Oum Ayush d’in taja ta tsaya adaidai lokacin da idanunta suka sauk’a akan Maleek dake kwance flat akan gado kamar gawa. Cikin muryarta da tayi sanyi sosai, kana cike kuma da tausayin Maleek d’in tace. “Innalillahi Wa’inna Ilaihirraju’un!â€? Kalmar da ta fad’a kenan wanda ya sa zuciyar Laylerh dake waje sake harbawa da k’arfi. Wanda kuma sanadin jin hakan ne ya bawa hawayen dake cikin idanunta daman gangarowa kan k’uncinta, ahankali cikin wani irin yanayin da ita kanta bazata tab’a iya fassarasa ba, ta soma d’an jan k’afafunta dake rawa zuwa cikin d’akin. K’afarta ta fara sakowa cikin d’akin kafun kanta ya biyo baya, tana shigowa kuwa idanunta wanda ganinsu ya d’an disashe saboda hawayen dake cikinsu, suka sauk’a akan mutumin dake kwance, wanda tayi imani cewa koda makancewa tayi Indai yana kusa da ita to babu abunda zai hanata iya zayyano halittar kyakkyawar fuskarsa dama murd’add’iyar surar jikinsa dake cike da matsanancin kwarjini. Hawayen dake cike a cikin idanunnata ne suka samu daman soma yi mata ambaliya akan k’uncinta, hakanne kuwa yasa ganinta ya sake disashewa, yaza mana bata iya tantance yanayin tsarinsa. Ahankali ta d’aga k’afafunta wanda take jinsu kamar an sark’e mata su da igiyan kaca, cikin yanayin dake bayyana zallan rashin nutsuwa da kuma firgicin da take ciki, ta shiga takawa kaitsaye zuwa inda Maleek d’in ke kwance, tayi hakan kuwa batare da ta iya rarrabe inda take jefa k’afafun nata ba. Jin sautin tafiyan nata ne kuma yasa duk hankalin su Abbou Jaheed ya dawo kanta, ganinta acikin mawuyacin hali yasa suka zuba mata ido, saidai kuma dukansu kaman an kulle musu baki. babu wanda ya iya koda k’iran sunanta ne, haka suka zuba mata idanu. Laylerh kuwa tunkafun ta k’arasa kusa dashi taji wani irin jiri mai k’arfi na neman kada ita, saidai sam a irin yanayin da take jin kanta aciki batajin zata iya bawa wani abu daman katse mata hanzarinta nason zuwa garesa. Isowarta jikin gadon nasa da tayi kuwa yayi daidai da sauk’an wasu hawaye masu tsananin zafi akan fuskarta. Ahankali kana kuma cikin rawan da hannayenta dama duk jikinta keyi, ta matso gab dashi, hannunta takai ahankali ta d’aura akan kyakkyawar fuskarsa da ko d’igon tabo ko kwarzane babu akanta. Batare kuwa da tasan me takeyi ba ta soma d’an yawo da hannun nata akan kyakkyawar fuskarsa harzuwa kan faffad’an chest d’insa dake abayyane, kasancewar doctors d’in sun cire masa rigar dake jikinsa, domin duk ta b’aci da jini, kuma akwai y’an kananun raunuka da yaji, wanda dole sai sunyi treating d’in wajen, shiyasa ma gaba d’aya suka rabashi da rigarsa. Isowar hannunta da har yanzu keta faman b’ari daidai kirjinsa inda zuciyarsa take ne yasa gaba d’aya ilahirin jikinta ya sake d’aukan rawa, har yakai ga hak’waranta na kartan juna is.... Da k’yar cikin wata irin murya me d’auke da wani rikitaccen amo, sannan kuma mai fitar da shaking sound d’in dake d’auke da matsanancin raunin zuciya tak’ira sunansa, in a slowly tone. “Y...A...H M...J...A...Y!!â€? Yanda sauti da kuma amon muryar nata ya fita ne yasa su Abbou Jaheed kafesu da ido basa ko k’yaftawa. “Y...A...H M...JAY......!!!â€? Still Ta sake k’iran sunan nasa, saidai kuma awannan karon amon muryar nata yafi na farko fitarda rauni. Again bud’e labb’an nata tayi,da niyar sake k’iran sunansa saidai kuma awannan karon harshenta bazae tab’a iya motsa kansa ba, domin kuwa takai wani stage da yin maganarta zai iya haifar mata da d’aukewar numfashi. Ahankali ta sauk’e tattausan tafin hannunta akan nasa hannun, batare kuma da tunanin komai ba ta d’ago hannun nasa tare da kawosa daidai saitin bakinta, labb’an bakinta ta d’aura akan lallausar fatar hannun nasa, cikin wani irin yanayi ta fashe da wani kuka me tsananin ban tausayi da kuma tsayawa arai, duk da cewar kuwa har yanzu jikinta na b’ari, amma hakan bai hanata rik’e hannun nasa da k’arfi, ta shiga rera wani irin kuka me sauti da kuma tsuma zuciya ba, tabbas kukan da ya amsa kuka Laylerh’n keyi, ma’ana irin wanda ke fitowa daga cikin zuciyar mutum me d’auke da matsanancin rauni, haka zalika kuma kukane dake bayyana yanda wanda keyinsa yakeji acikin rai da zuciyarsa, sannan kuma kukane da zautattun mutanen da zuciyarsu ta narke acikin zazzafan soyayya keyi, Kuka take irin wanda bata tab’a yinsa ba aduniya, kukan da ya firgita zuciyar su Abbou Jaheed, kukan daya saka kowannensu acikin matsanancin shock, har ya kai ga sun tsaya kallonta tamkar gumaka babu wanda yake motsi acikinsu. Laylerh kuwa kukanta take sosae wanda gaba d’aya sautinsa ya cika d’akin, yayinda kuma har yanzu take rungume da hannun Maleek, wanda tayi masa wani irin rik’o, tun tana fitar da sheshshek’a kuwa acikin kukan nata har ya zamana ta fara shid’ewa, yayinda numfashinta ya shiga ja baya yana me k’ok’arin d’aukewa. Ganin hakane kuma yasa Oum Ayush da tuni hawayen tausayin Laylerh Da Maleek d’in sun zubo kan k’uncinta, cikin rawan murya ta k’ira sunan Laylerh’n, da ko kad’an bataji k’iran Oum Ayush d’in ba. “LAYLERH.â€? Oum Ayush ta sake k’iran sunanta akaro na biyu, tare da soma k’ok’arin danne kukan da ya zo mata. Still Laylerh bata amsa taba, bata kuma tsaya da kukan nata dake nuna musu zaucewarta ba, haka kuma har yanzu tana rik’e da hannun Maleek d’in bata sake ba. Saurin juyawa Abbou Jaheed yayi da k’arfi ya rumtse idanunsa wanda suke cike tab da k’walla, k’wallar kuma dake d’auke da abubuwa da yawa, wani irin karaya da rauni zuciyarsa tayi, wanda hakan yasa dole yasa hannu ya dafe zuciyartasa, saidai kuma duk yanda yaso hana hawayen dake cikin idanun nasa fitowa, abun yaci tura, dole haka yanaji yana gani wasu hawaye suka ziraro masa. Awajen Abbou Khareem ma kuwa hakan take domin shima tuni idanunsa sun cika da k’wallan tausayin y’ay’annasu. Fou’ad kam dama shi mai raunine sosae akan abokinnasa, sanin kuma abundake cikin zuciyar Laylerh da Maleek d’inne da kuma yanda Laylerh’n ke kukane yasashi sanya hannu ya kama kansa, domin kwata kwata bashi da ikon hana idanunsa kuka ayau, watarana abanza ma haka yake kuka, bare yau da abun kukan ya samu, shi Soja ne amma yasan yana da raunin zuciya sosai. Najeeb. Tayaya zai iya d’auke idanunsa daga kallon Laylerh’n, hak’ik’a duk da cewar kukan da Laylerh’n keyi yana matuk’ar tab’a masa zuciya, amma hakanan ya samu kansa da kasa janye idanunsa daga gareta, duk da kuwa cewar idanun nasa sun kad’a sunyi jajur tamkar wanda aka watsawa borkono, k’warai a yanzun shi kad’ai yasan meyakeji acikin zuciyarsa, wanda ayanzu bazai tab’a iya fassarawa kansa ma’anan hakan ba. Ahankali cikin son tausasa harshe da kuma bawa Laylerh’n baki, Oum Ayush ta k’arasa zuwa gareta, hannunta tasa ta dafa kafad’an Laylerh’n, cikin muryarta da ke cike da tsananin tausayin su asanyaye ta k’ira sunan Laylerh’n, wanda har yanzu bata daina kukan da takeyi ba. “Laylerh!!â€? Oum Ayush ta sake kiran sunanta akaro na uku, hade dasa hannunta ta jawo Laylerh’n jikinta. Jin da tayi kuma Oum Ayush din ta rik’e ta ne yasa Cikin sheshshek’an kuka ta d’aura kanta akan kafad’an Oum Ayush d’in, k’ok’arin fad’in wani abu takeson yi amma ta kasa, saboda tuni kuka ya riga da yaci k’arfinta. Ahankali Oum Ayush ta soma kokarin zare hannun Maleek d’in daga rik’on da Laylerh’n tayi masa. Cikin sa’a kuwa ta samu Laylerh’n ta saki hannun Maleek d’in. “Muje ki huta kinji, ya isa haka ki daina wannan kukan, ai Maleek d’in ba mutuwa yayi ba, yana da rai kuma zai bud’e idanunsa Insha Allah.â€? Oum Ayush ta fad’i hakan cikin tausasa murya tare dajan Laylerh’n anutse ta zaunar da ita akan wani kujera dake d’an gefe da gadon da Maleek d’in ke kwance kana itama ta zauna a gefen Laylerh’n, hakanne kuwa yasa ahankali Laylerh dake ta faman sakin sheshshek’an kukanta da har yanzu ya kasa tsayawa ta d’aura kanta akan cinyar Oum Ayush d’in. Saidai kuma karfin kukan nata ya d’an ragu ba kaman d’azu ba da gaba d’aya sautinsa ya cika d’akin. Haka gaba d’aya d’akin ya d’auki shiru, ba abunda ke tashi acikinsa sai fitan numfashi da kuma amon gunjin kukanta. Hakika gaba d’ayansu duk acikin wani irin yanayi suke musamman ma Abbou Jaheed da zuciyarsa ta riga da tafi na kowa rauni awajen, bakuma iya rauni kawai ba, wani abune na daban ayanzun ke damun zuciyarsa akan Laylerh da Maleek d’in. Ahankali Dr.Mouhammad ya turo kofar dakin ya shigo, bakinsa dauke da sallama, wanda hakanne kuma yasa duk hankalinsu ya koma kansa. Ganin irin kallon da sukeyi masa ne kuma yasa shi d’an fad’ad’a murmushi akan fuskarsa sab’anin da da yanayin fuskartasa ke d’auke da damuwa. “Ya naga duk kuna kallona kodai ya Far fad’one?â€? Dr.Mouhammad d’in ya fad’i haka cikin raha da kuma d’an sakin fuska. Kusan kowannensu ajiyar zuciya ya sauk’e, asanyaye Abbou Khareem yace. “Aa har yanzu dai bai farfad’o ba, fatan mu dai shine Allah Yasa ya farfad’o d’in.â€? “Karka damu Insha Allah Zai farfad’o, wannan matarsa ce?.â€? again Dr. Mouhammad ya tambaya adaidai lokacin da ya d’aura idanunsa akan kyakkyawar matashiyar budurwar dake sakin kananan sheshshek’a wato Laylerh kenan. Tabbas tambayar tasa tazo musu awani irin siga, hakan yasa suka d’anyi shiru, saida aka d’an d’au sakanni kafun Abbou Jaheed ya numfasa, asanyaye yace. “Aa k’anwarsa ce.â€? Wata irin gagarumar ajiyar zuciya Dr.Mouhammad ya sauk’e tare da sake kallon Laylerh’n da kyau, sosai kuma amsan da Abbou Jaheed d’in ya basa ya sashi samun gamsuwa, tare dajin wani sanyi aransa, domin kuwa da ace kyakkyawar yarinyar da yake gani d’in ta kasance matar Maleek d’inne dakuwa akwai matsala sosae, domin asonsa zaifi son jin cewa Maleek d’inma bashi da mata, domin kuwa sabuwar matsalan daya fuskanta ta sanadiyar accident d’in da yayi bak’aramin ci baya zata kawo garesu ba. Ahankali ya kawar da kansa daga kallon Laylerh’n, tare da k’arasawa gaban gadon da Maleek d’in ke kwance, ruwan allura da kuma sirinjin alluran dake hannunsa ya had’a, anutse ya so kawa Maleek d’in alluran akan damtsen hannunsa, wanda jijiyoyinsa suka fito sukayi rad’au akai. Bayan ya gama yi masa alluran ne kuma ya juyo ya kalli Abbou Jaheed. Kasancewar kuma yasan cewa Abbou Jaheed d’in babban mutum ne da sunansa ya zagaye wajeje da dama, saboda kud’i da kuma halin k’irkinsa hakan yasa cikin basa girma yace. “Alhaji Jaheed Gwani idan babu damuwa ko zaka iya biyoni office d’ina?â€? Jin abunda Dr.Mouhammad d’in ya fad’a ne kuma yasa Abbou Jaheed jinjina kae ahankali yace. “Ba damuwa Doctor muje.â€? Kai Dr.Mouhammad ya jinjina kafun ya wuce gaba, Abbou Jaheed kuwa ya bisa abaya, domin Jin cikakkiyar rahoto akan d’ansa Maleek. *(Afuwan bansamu daman turowa da wuri ba wallahi two days ba anutse nake ba shiyasa, duk typing d’in rabi da rabi atsaye nake kareshi, amma Insha Allah Zanyi k’ok’ari na gobe yafi nayau yawa.)* *Friday12/2/2021* *11:33 am* 2/13/21, 9:39 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna *Not Editing* *Chapter 51* Fitan su Abbou Jaheed da kuma Dr. Mouhammad daga cikin d’akinne yasa Najeeb da gaba d’aya yaji duk tsayuwar da yake ta isheshi ya juya tare da kama hanya ya fice daga cikin d’akin, Laylerh kuwa da zuwa yanzu kukan nata ya tsagaita sosai, sake kwantar da kanta akan cinyar Oum Ayush tayi tare da lumshe idanunta, saboda kukan da tayi d’inne kuma yasa lokaci d’aya cikin abunda bai wuce 15 minutes ba bacci me nauyin gaske ya d’auketa, duk da cewar kuma bacci take, amma hakan bai hanata sakin wani gunjin kuka acikin baccin nata ba, yayinda daga gefe guda kuwa ajiyar zuciya kawai take ta sauk’ewa akai akai. B’angaren Abbou Jaheed kuwa direct office d’in Dr.Mouhammad suka nufa, suna shiga cikin office d’in kuwa Dr. Mouhammad d’in yayiwa Abbou Jaheed nuni da wata kujeran da musamman aka ajiye ta dan zaman bak’i na musamman. Zama Abbou Jaheed yayi, tare da d’ago kansa ya kafe Dr.Mouhammad da idanu, wanda ya zauna akan permanent sit d’insa na Office. Ahankali ya bud’e wasu files dake gabansa ya shiga dubawa, ak’alla kuma wasu y’an mintuna ya d’auka yana duba files d’in, saida ya kammala sannan ya d’anyi rubutu acikin kowannensu, d’ago kansa yayi ya kalli Abbou Jaheed da har yanzu baidaina kallonsa ba. Shiru yayi tare da d’an sunkuyar da kansa, domin kuwa zuciyarsa cike take da fargaba da kuma halin da Abbou Jaheed d’in zai samu kansa aciki matuk’ar ya sanar dashi hak’ik’anin gaskiyar abunda ya faru da d’ansa, saidai kuma yasan dole babu yanda zaiyi, wanda ya wuce ya fad’awa Abbou Jaheed d’in komai, domin babu wani bawa aduniya daya wuce wa samun irin wannan k’addaran. “Kai nake saurare Dr. Mouhammad amma kuma har yanzu naji baka ce komae ba, kodai akwai wata matsala babba daya samu Maleek ne wanda bakason fad’a miji?.â€? Abbou Jaheed ya fad’i hakan cikin yanayi na d’an damuwa, domin daga yanda yaga yanayin Dr.Mouhammad d’in yasan baiwuce ace masa akwai wata gagarumar matsala. Ajiyar zuciya Dr.Mouhammad ya sauk’e tare da d’an gyara zamansa, cikin yanayin sanyi yace. “Kayi hakuri Alhaji da irin tambayoyin da zan maka dole ce tasa hakan, shin Maleek yana da mata ne ko kuma y’ay’a?.â€? K’irjin Abbou Jaheed ne ya buga, asakamakon jin tambayan da Dr.Mouhammad d’in yayi masa, lokaci d’aya yaji zuciyarsa ta karye yayinda kirjinsa ya shiga dukan uku uku, cikin sassanyar murya da kuma fargaban abunda kunnuwansa zasu sake jiye masa anan gaba yace. “A’a ko d’aya bashi da mata kuma bashi da y’ay’a, hasalima shid’in bai tab’ayin aure ba, amma Dr. wani abune ya faru?.â€? Idanu Dr.Mouhammad ya d’an lumshe, yayinda gaba d’aya jikinsa ya k’arayin sanyi, lokaci d’aya yaji wani irin matsanancin tausayin matashin saurayin da ko auren fari baiyi ba amma kuma ya had’u da babbar matsala. “Doctor Mouhammad kaifa nake saurare, amma naga kayi shiru.â€? Abbou Jaheed ya katsesa ta hanyar fad’in hakan. Ajiyar zuciya ya k’ara sauk’ewa akaro na biyu, kana ahankali ya d’an gyara zamansa, cikin nutsuwa da kuma son kwantarwa da Abbou Jaheed d’in hankali ta yanda zai fahimcesa asanyaye yace. “Kayi hak’uri da abunda zan fad’a maka Alhaji Jaheed, hakika kamar yanda kasani kowani bawa aduniya yana rayuwane da irin k’addara da kuma jarabawan da Allah Ya d’aura masa, mai kyau ko akasin haka, sannan kuma Allah Baya d’aurawa bawansa abunda bazai iya ba, tabbas Maleek ya had’u da k’addara wanda jurewa hakan Insha Allah Zai kaisa ga samun kyakkyawan sakamako awajen Ubangiji...â€? D’an tsagaitawa da maganan nasa yayi tare da d’ago kai ya kalli Abbou Jaheed daya zuba masa ido baya ko k’yaftawa. Kansa ya sauk’e k’asa domin yasan abu ne me girma fad’awa Iyaye irin wannan gagarumin matsala musamman idan y’ay’ansu ne suka kasance sun samu kansu acikin irin matsalan. D’an gyara zamansa yayi akaro na barkatai, cikin hikima irin tasu ta likitoti yace. “Zan sake baka hak’uri Alhaji Jaheed, domin kuwa a bisa tsautsayin hatsarin da d’anka Maleek ya had’u dashi ya samu wata matsala, ya samu mummunan buguwa sosae akan mararsa wanda hakan yasa abinciken da mukayi mungano cewar D’ANKA MALEEK bazae tab’a haihuwa ba, bi ma’ana k’wayoyin haihuwarsa sun samu matsala ta yanda bazasu iya riki d’ewa su zama k’wayar halittan da zata Samar da y’a ko d’a ba...â€? k’irji da kuma zuciyar Abbou Jaheed ne suka shiga bugawa akai akai, yayinda ya samu kansa cikin wani sabon matsanancin tashin hankalin da ya gigita tunaninsa, tabbas kalaman da suka fito daga bakin Dr.Mouhammad sun kusan tarwatsa masa zuciya, har saida yaji kansa na yi masa wani irin sarawa. Lokaci d’aya gaba d’aya mood d’in Abbou Jaheed d’in ya sanja, yayinda idanunsa suka cika tab da k’wallan tausayin d’ansa. Cikin wata irin sassanyar murya me d’auke da matsanancin tausayawa ya shiga furta kalamar. “Innalillahi Wa’inna Ilaihirraju’un!!!â€? Saboda yasan ita kad’aice kalmar da zata daidaita nutsuwarsa. Ganin hakanne kuma yasa Dr.Mouhammad gyara zamansa, ahankali yace. “Dan Allah Alhaji Jaheed kada ka tashi hankalinka, domin kuwa ba akan Maleek aka fara samun irin wannan matsalan ba, duk da cewa abune da baiyawaita ga maza ba, anfi samun irin way’annan case d’in ga mata, saidai kasani shi Maleek yasamu wannan matsalarne ta sanadiyar accident d’in daya samu, hak’ik’a Allah Yakan jarraba bawansa da k’addara kala kala, yayinda kuma wata k’addaran takanfin wata sauk’i, sannan ko acikin k’addarori Allah Yakan musanyawa bawa daga me tsananin had’ari izuwa me sauk’i, kamar dai yanda ya juyawa Maleek nasa, lallai na tsorata sosai alokacin da aka kawosa cikin asibitinnan musamman yanda naga kansa na fitar da jini, wanda kuma hakan alamace dake nuna cewar ya bugu sosae akannasa, wanda hakan yasa nafara tunanin cewa, ko ta sanadiyar hakan zai zamana cewa yayi losing memory d’insa, sai kuma da mukayi bincike sosai akansa nida abokan aikina sai muka gano cewar kokad’an kansa da kuma k’wak’walwarsa basu samu wani matsala ba, tabbas munyi farinciki da ganin hakan, domin kuwa abune me tsananin d’aga hankali ace mutum ya manta kowa da komai nasa, tayaya rayuwa zatayi masa dad’i? kwarai zai dawo kaman wani bak’on halittane acikin mutane, lallai nayarda cewa k’arfin ikon Ubangiji da kuma k’udurarsa ya wuce duk tunanin mai tunani, domin kuwa shine ya kawar wa Maleek da wannan matsalan, ya kuma jarrabesa da wata matsalan amararsa, wanda da ace yaso had’a Maleek d’in da mummunan k’addara tofa da ayanzu labari ya riga ya sanja salo, domin kuwa inda matsalan ya kasance akansa ne to fa komai zai iya faruwa ciki kuwa harda gushewar hankali ma’ana zai iya zama mahaukaci, amma da yake Allah baiso hakan ba sai ya had’ashi da wata tawayar, tabbas lokacin da nagano cewa Maleek yana d’auke da wannan matsalan na tausaya masa k’warai, duba da cewar ya kasance jarumin matashin Soja me jini ajika, amma saidai Allah Ne kad’ai yasan me yake nufi da faruwar hakan.â€? Hannu Abbou Jaheed yasa asanyaye ya share hawayen da suka silalo daga Cikin idanunsa, wani irin matsanancin tausayin Maleek d’insa ne ya cika masa zuciya, wanda har hakan ya kaisa gajin kamar yayi ta rusa kuka, saidai kuma amatsayinsa na cikakken Musulmi ya zame masa dole d’aukan hak’uri da k’addara me kyau ko akasin haka. Duk da kuwa bai tab’a kawo wa aransa cewar watarana wai d’ansa jininsa zai iya gamuwa da wannan mummunan k’addaran ba, saidai kuma duk da haka saidai ya godewa Allah da bai gama d’annasa da ciwon hauka ba, domin kuwa ciwon hauka yafi kowanne ciwo Muni. Wani irin dogon numfashi me d’auke da karyewar zuciya yaja, asanyaye yace. “Idan har na fahimci abunda kake fad’amin Dr.Mouhammad shine Maleek d’ina bazai tab’a haihuwa ba har abada, har ya koma ya ubangijinsa bazai ga d’ansa kuma jininsa ba, sannan kuma nima har abada bazan tab’a ganin Jika daga garesa ba, lallai tabbas Maleek ya had’u da babban k’addara wanda zatayi sanadiyar kasantuwarsa cikin k’unci, ba kuma zan iya jure hakan ba Dr. domin kuwa Ina matuk’ar son Maleek? dan haka wannan matsalar batasa bace shi kad’ai, wai ma shin tayaya xan fara fuskantar Maleek da wannan maganan tayaya????â€? Ya k’are maganar muryarsa na d’an rawa da’alama kuka ne ke neman k’wace masa. Kai Dr.Mouhammad ya girgiza cikin tausasa zance da kuma bada baki yace. “Ayanzu Maleek Addu’ar samun sauk’i kawai yake buk’ata awajen baki d’ayan mu, domin kuwa hakan bawai yana nufin cewa har abada bazae tab’a warkewa bane, tabbas lalurar daya samu babbace, wanda da yawanta ba’a tab’a warkewa, amma kuma komai na Allah Ne shike sa cuta a lokacin da yaso, haka kuma shi ke sauk’ar da waraka alokacin da yaso, saboda haka mujira komai daga garesa, kar ka manta kuma cewa Alhaji Jaheed d’aukan k’addara yana d’aya daga cikin abunda yake k’ara inganta imanin mutum, saboda haka ka kwantar da hankalinka, sannan kuma inaso katuna cewa Allah Baya tab’a d’aurawa bawansa abunda yasan bazae iya d’aukansa ba.â€? Wata irin nannauyar a ajiyar zuciya Abbou Jaheed ya sauk’e, tare dasa tafukan hannayensa ya rufe fuskarsa dasu, tabbas wannan sabuwar matsalan da ta kunno musu tayi matuk’ar d’aga masa hankali da kuma gigita tunaninsa, babban abunda yake tsoro kuwa shine. “Tayaya zai fara fad’awa Maleek wannan matsalan da ta sameshi? Yaya Maleek d’in zaiji? wani irin k’una da kuma zafin zuciya zai samu kansa aciki?. Lallai Rayuwar Maleek acike take da tarin k’addarori, da fari yayi rashin mahaifiyarsa haka ya taso cikin kad’aici da kewa, bashi da y’a ko kuma k’anwar da suke uwa d’aya uba d’aya, ahakansa yake rayuwa har kawo yanzu, da adaidai wannan lokacinne yakamata ace yayi aure ya hayayyafa ta yanda y’ay’ansa za su zame masa abokan hira da kuma d’ebe kewa, amma kuma sai gashi rana d’aya Allah Ya sauk’ar masa da wannan k’addaran, sai yaushene Maleek Zaiyi farinciki arayuwarsa? Sai yaushe k’unci da kad’aicin da suke mamaye da rayuwarsa zasu yaye?â€? Sam Abbou Jaheed d’in bashi da amsar tambayoyin, wanda hakan ya tilasta zubowar wasu y’an guntayen k’walla daga cikin idanunsa. Ahankali ya mik’e daga zaunen da yake, cikin sanyin yanayi batare kuma daya ce da Dr.Mouhammad k’ala ba ya juya tare da nufar hanyar fita daga office d’in. Dr.Mouhammad kuwa da idanu ya raka Abbou Jaheed d’in har ya gama ficewa daga cikin office d’in. Wani irin matsanancin tausayin ahalinne ya kamasa, domin kuwa k’warai yasan cewa abune me matuk’ar ciwo da kuma tada hankali ace mutum Namiji ya samu irin wannan matsalan na rashin haihuwa, saidai kuma sanin da yayi cewa Maleek d’in bai rasa cikakken lafiyarsa ta zamowa d’a Namiji ba ne yasashi sauk’e ajiyar zuciya, domin yasan matsalar za tafi muni ne Idan akace Maleek d’in bazae iya biyawa Mace buk’atar taba, Alhamdulillahi kuma domin kuwa hakan bata faru ba, domin abincikensu sun gano cewa babu abunda ya samu manhood d’insa, zai iyayin sex da mace bama d’aya ko biyu ba, kuma ta samu cikakken gamsuwa, sannan kuma k’arfin sha’awarsa Yana nan bai ragu ba, saboda haka awannan fannin baida matsala kona d’igo ne kuwa. Matsalar tasa dai guda d’aya ce, wato rashin haihuwa, wanda kuma ako da yaushe Allah Yakan iya sanja al’amura yanda yaso. Abbou Jaheed kam jikinsa amatuk’ar sanyaye ya fita daga office na Dr. Mouhammad d’in, kaitsaye d’akin da aka kwantar da Maleek d’in ya nufa, haka yakejin duk gaba d’aya gangar jikinsa ba k’arfi, domin kuwa fargaba tausayi da kuma rauni su suka riga suka cinye masa zuciya. Isowarsa jikin k’ofar d’akinne yasa shi soma k’ok’arin daidaita nutsuwarsa gudun kada su Abbou Khareem su gane cewar yana d’auke da damuwa, ahankali ya tura k’ofar d’akin ya shiga, bakinsa d’auke da sallama. Oum Ayush da kuma Abbou Khareem ne suka amsa masa, sai kuma Fou’ad da ya amsa murya kasa kasa, saboda damuwar dake kwance acikin zuciyarsa. K’asa Abbou Jaheed d’in yayi da kansa ba tare da ya yarda idanunsa sun sauk’a akan Maleek dake kwance ba, domin kuwa yasan matuk’ar ayanzu ya d’aura idanunsa akan Maleek d’in to ko shakka babu kukane me k’arfi zai k’wace masa. Oum Ayush dake zaune Laylerh na bisa cinyarta ya kalla, asanyaye yace. “Oum ki tada Laylerh ku koma gida, nida Abbou Khareem zamu zauna anan, kaima Fou’ad akwai buk’atar kaje kad’an huta idan yaso ko zuwa anjima saika dawo, kema Oum zaki iya dawowa anjima ko akwai wani abu da Maleek d’in zai buk’ata bayan ya bud’e idanunsa, idan ba damuwa sai a taho masa dashi.â€? Numfash Oum Ayush tad’an fesar, kana asanyaye tace. “To.â€? Yayinda acikin zuciyarta kuwa sam bataji tanason barin asibitin batare da taga farfad’owar Maleek d’in ba, saidai amma sam batason yiwa Yayan Mijinnata musu shiyasa. Ahankali tasa hannunta ta d’an shiga tashin Laylerh’n, cikin sa’a kuwa Laylerh ahankali ta bud’e idanunta wanda suka kumbura suntum saboda kukan da tayi. “Tashi muje gida ko Laylerh.â€? Oum Ayush ta fad’a tana me gyarawa Laylerh’n zaman lufayan dake jikinta. Laylerh kuwa jin abunda Oum Ayush d’in ta fad’ane yasa ahankali ta girgiza kanta, saboda har yanzu bata dawo daidai ba, asanyaye cikin muryarta da ya d’an dashe tace. “Bazan iya tafiya ba Oum Ayush, bazan iya koda fita daga d’akin nan ba, har sai naga Yah Maleek ya bud’e idanunsa yana numfashi kaman yanda mukeyi, sannan kuma yana motsa jikinsa kamar yanda muke motsa namu jikin.â€? *(Dan Allah Banason yawan k’orafi, Labarin Laylerh Maleek ahaka yake, komai dake cikinsa haka yake, sannan kuma babu wani wanda yafi k’arfin karb’an tarin k’addarorin Ubangiji, da gani har kowa, abun so dai shine Allah Ya had’amu da kyakkyawar k’addara ako da yaushe.)* *Saturday13/2/2021* *8:37 pm* 2/16/21, 9:12 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna *Not editing* *Chapter 52 Oum Ayush dake tsaye, wanda jin abunda Laylerh’n ta fad’a ya sa ta sauk’e wani irin sassanyar ajiyar zuciya, k’warai ta d’anyi mamakin jin hakan daga bakin Laylerh’n, amma kuma sanin hak’ik’anin abunda ke cikin zuciyar Laylerh’n, yasa babu wani amfanin mamakinnata. D’an gyara tsayuwarta tayi, tare da sa hannu ta dafa kafad’an ta, cikin yanayin tausasa murya da kuma salon da tasan zai taimaka mata wajen jawo hankalin Laylerh’n ahankali tace. “Kiyi hak’uri mutafi gida kinji, na miki alk’awarin cewa anjima kad’an zamu dawo, ko bakyaso idan Yah M.Jay d’innaki ya bud’e idanunsa, kuma yaji yana jin yunwa yaci abinci ne? kinsan dole dae zaiji yunwa ko? saboda haka muje gida ki tayani mu dafa masa abinci mai dad’i, nasan idan ya farfad’o zaiji dad’i sosae.â€? Jin hakanne yasa ta d’anyi jim, tare kuma da d’ago kanta ahankali ta kalli Maleek d’in da har yanzu ke kwance kaman gawa, yayinda wata na’ura me yanayin computer dake gefensa ke tafiya yanda ya dace, wanda kuma acikin na’urar ne ake iya ganin bugun zuciyarsa. D’an guntun hawayen daya fito daga cikin idanunta ta share, asanyaye ta d’an karyar da wuyanta gefe, cikin muryarta da har yanzun bata dawo daidai ba tace. “Tsoro nakeji Oum Ayush, banason bayan natafi wani abu ya samesa, yanzu ma haka nasan yanajin zafi, ki kalli jikinsa fa kiga, duk ya d’anji rauni glasses duk sun caccaka masa jiki, tayaya ma zai misalta irin wannan zafin da yakeji? ko yanzu ma me yakeji? Nasan ma....â€? Kasa k’arasa maganan nata tayi, sakamakon wani kuka daya so k’wace mata, wanda bisa dole hakan ya tilasta mata lumshe idanunta, take kuwa ruwan hawaye masu tsananin zafi suka sauk’a akan kumatun ta. Wani abun mamaki kuwa kusan atare hawayen dake cikin idanun nata, da kuma wanda suke cikin idanun Abbou Jaheed suka zubo, wanda duk yanda yaso hana hawayennasa fita ya kasa, saboda tsananin tausayin Maleek d’in da yakeji yasa gaba d’aya ya kasa controlling rauninsa, hak’ik’a ayau d’in da ace shi ba babban mutum bane me yawan shekaru da sanin ya kamata ba, to da ba abunda zai hanasa zama yayi kuka sosai kamar yanda k’ananan yara keyi, saidai kuma babu yanda ya iya, ya zame masa dole ya tausashi zuciyarsa, saboda bai isa hana Allah gudanar da Ikonsa ba. Saurin saka hannunsa yayi ya share hawayennasa tun kafun su lura da hakan, saidai kuma abunda bai sani ba shine, tuni Abbou Khareem ya ga hawayennasa, domin kusan akan idanunsa ma suka zubo. Oum Ayush kuwa hannu takai ta sharewa Laylerh hawayen dake kwanace akan fuskarta, batare kuma da ta jira cewar kowanne daga cikinsu ba ta jawo hannun Laylerh’n tare da mik’ar da ita tsaye, anutse ta nufi hanyar fita daga cikin d’akin, ba tare kuma da ta sake hannun Laylerh’n ba, haka suka fice daga cikin d’akin. Fou’ad dake zaune Abbou Jaheed ya kalla, cikin yin k’asa da murya yace. “Fou’ad kuje ku huta, ka kai su Laylerh gida, zaka iya dawowa anjima kaima.â€? “To.â€? Kawai Fou’ad yace kana asanyaye ya mik’e daga zaunen da yake, na’urar dake bayyana bugun zuciyar Maleek d’in dake kwance ya kalla, kafun ahankali ya sauk’e ajiyar zuciya tare dasa kai ya fice daga cikin d’akin. Kamar rak’umi da akala haka Laylerh kebin Oum Ayush dake rik’e da hannunta, har zuwa wajen da sukayi parking motarsu. Gefen me zaman Banza Oum Ayush ta bud’e mata, jikinta amatuk’ar sanyaye ya shiga ta zauna, tare da juya kanta tana me kallon cikin asibitin, hakanan takeji ajikinta kamar idan tayi nesa da asibitin wani abu zai sake samun Maleek, sam Allah Yasani har acikin zuciyarta bataso ta fiya ba, amma babu yanda zatayi. Isowar Fou’ad garesu ne yasa Oum Ayush d’agowa ta kalleshi, asanyaye tace. “Fou’ad Ina kuma zakaje, badai kaima tafiya zakayi ba?.â€? Gajerar ajiyar zuciya Fou’ad d’in ya sauk’e, cikin kuma yanayin nutsuwa yace. “Abbou Jaheed yace nazo nayi driving d’inku, amma ba damuwa zuwa anjima kad’an zan dawo, kafun nan ma nasan Maleek d’in ya dawo hayyacinsa.â€? Kai Oum Ayush ta jinjina cike da gamsuwa, take kuwa ta mik’a masa makullin motar, tare da bud’e murfin motar ta shiga gidan baya. Shi kuwa Fou’ad b’angaren driver ya shiga, anutse ya tada motar suka bar farfajiyar wajen. Tunda suka d’auki hanya kuwa babu wanda yace da d’an uwansa k’ala, domin kuwa ko wannensu da abunda yake sak’awa acikin rai da zuciyarsa, musamman Laylerh da gaba d’aya ma tunaninta baya jikinta. Ahaka dai suka k’araso gaban makeken gate d’in gidan, jin k’aran horn d’insu ne kuma yasa take mai gadi ya wangale musu wawakeken gate d’in, anutse Fou’ad ya tura hancin motar ciki, tare da neman waje yayi parking. Kusan atare dukansu suka fito daga cikin motar, ganin yanda Laylerh’n ke layi kaman zata fad’i ne yasa Oum Ayush tayi saurin rik’o hannunta, kana cikin kulawa tace. “Laylerh ya dai kina lafiya kuwa?.â€? Kanta tad’an girgiza tare dasa hannu ta dafe daidai saitin kanta dake masifar ciwo har wani sarawa yake kaman zai rabe gida biyu haka takeji. “Kaina ne yake ciwo sosae.â€? Tafad’i hakan cikin muryarta dake shaking. “Ayya sannu to kije kisha magani sai ki kwanta kinji, dole dama da irin wannan kukan da kikayi sai kanki yayi ciwo.â€? Cewar Oum Ayush tana me k’ok’arin sake hannun Laylerh’n. Ahankali ta soma d’an taka k’afafunta, saidai bai wuce taku uku tayi ba ta tsaya tare da juyowa ta kalli Oum Ayush d’in, cikin wata irin sassanyar muryar dake bayyana rauni tace. “Dan Allah Oum Ayush kada ki koma kibarni idan zaki koma ki gayamin!â€? Yanayin yanda ta k’are maganar cikin karyar da wuya ne yasa Oum Ayush ta sake jin matsanancin tausayinta, asanyaye tace. “Insha Allah Zan gaya miki, kuma kema ki tabbatar da cewar kinsha magani.â€? “To.â€? Tace tare da juyawa cikin tafiyarta na rarrabe hanya ta nufi sashin su. Ajiyar zuciya Oum Ayush ta sauk’e tare da kallon Fou’ad daya kafe Laylerh’n da idanu baya ko k’yaftawa, yayinda idanunsa kuwa suka zama jajur dasu. “Fou’ad.â€? Oum Ayush ta k’ira sunansa cikin tausasa murya. Jin K’iran da Oum d’in tayi masa ne kuma ya sashi d’auke idanunsa daga kan Laylerh wanda harma ta isa sashinsu, dawo da kallonsa ga Oum Ayush d’in yayi, cikin yanayin bayyana damuwar dake cin zuciyarsa yace. “Yanzu shikenan Oum Ayush haka rayuwar Laylerh da Maleek zata ci gaba da tafiya? sai yaushe ne zasu samu farinciki arayuwarsu? sai yaushe abunda dukkanin su ke b’oyewa zai zama kammalalle? Tabbas Ina matuk’ar jin tausayinsu, musamman Laylerh da ta kasance yarinya k’arama dudu du ko 20years bata cika ba, amma k’addara nata wasa da rayuwarta, dama duk wani burinta, lallai na gamsu cewa akwae abunda Allah Ya b’oye atsakanin Laylerh da Maleek, domin kuwa abune me girman gaske soyayyar da Laylerh keyiwa Maleek, domin na fahimci cewa bawai da iyaka zuciyarta take son shiba, harma da gaba d’aya rayuwarta, wata soyayyace ta daban atsakaninsu bawai kuma irin normal soyayya da kowa ya sani ba, soyayyace ta musamman wanda Ina da tabbacin cewa har abada bazata tab’ayin k’arshe ba.â€? Ajiyar zuciya me k’arfi Oum Ayush ta sauk’e tare dasa hannu tad’an sharce hawayen dake idanunta, lallai tabbas ta gamsu da duk kalaman Fou’ad, domin kuwa babu kuskure acikinsa komai ya fad’a gaskiya ne. Ita kanta ayanzu tsoron soyayyar Laylerh Maleek takeyi, saboda ta fuskanci cewa, ba soyayya bace irin ta kowa, wata sabuwar halittace da bata tab’a ganin irinta ba, duk da kuwa cewa daga Laylerh har Maleek d’in Miskilai ne amma hakan bai hana Soyayyar tasu tumbatsa har ta bayyana kanta a idanun mutane ba, hak’ik’a da ace Laylerh bata da auren Najeeb akanta, to da babu wata k’addara da ta isa hanata aurawa Maleek Laylerh, koda kuwa su Abbou Jaheed basa so, amma kuma saidai k’addara ta riga fata, Auren Najeeb dake kanta ya zama shamak’i. Numfashi taja tare da soma k’ok’arin daidaita nutsuwarta, kallon Fou’ad tayi kana cikin nutsuwa tace. “Baka kaini jin tausayinsu ba Fou’ad saboda dukansu yara ne da suka taso cikin maraici, Laylerh tataso babu Uwa da Uba, Maleek kuwa ya taso babu Uwa, tabbas maraicin Uba akwai wahala, amma Maraicin Uwa yafi komai ta gayyara da k’unci saboda Uwa itace gaba d’aya duniyar duk wani bawa, ba komai Amma akwae Allah, muje ciki kaci abinci.â€? (Yah Allah Kabarmin Mamana Araye, cikin koshin lafiya da farinciki, saboda itace komaina itace Haskena, kuma farincikina🙏🏻 dama duk wasu mutanen duniya, wanda kuma nasu suka rasu Allah Yajik’ansu da rahama Ameen.) Asanyaye Fou’ad ya bi bayan Oum Ayush kaitsaye suka nufi sashinta. Laylerh. Ahankali ta tura k’ofar falon nata ta shiga bakinta d’auke da sassanyar sallama. Shiru haka falon yake ba abunda yake tashi acikinsa sai k’amshin turare da kuma sanyin A/C, harta k’atuwar tv plasma d’in dake aje akan wani had’add’en glass table dake d’an manne da jikin bango wanda girmansa yakai 65inch shima akashe yake, Banda k’aran A/C ba abunda ke tashi acikin falon. Dama ita ba gwanar son zama afalo bane wannan yasa kai tsaye ta nufi bedroom d’inta. Sam ko da wasa bata tab’a kawo cewar Najeeb na d’akin ba, shiyasa anutse ta tura k’ofar d’akin ta shiga, sanin da tayi cewar ba kowa acikin d’akinne yasa tana shiga ta cire hijab d’in dake jikinta, tare dasa hannunta abayanta ta zuge zip d’in rigarta, batare kuma da ta juya bayanta ba, ta zauna abaki bakin had’add’en original royal bed d’inta. Tafukan hannayenta duka biyu tasa ta rufe fuskarta dasu, haka takejin zuciyarta na wani irin bugawa, yayinda wani sabon kuka ke shirin zuwar mata, duk da kuwa cewar kanta na mata ciwo sosai amma babu yanda ta iya da wannan kukan dake cinta, lallai tabbas tana buk’atar tayisa ko hakan zaisa taji zuciyarta ta d’anyi sanyi. Take kuwa ita kanta batasan ya akayi ba kawai sai jin kanta tayi ta fashe da kuka mai sauti. Najeeb kuwa dake zaune a gefen gadon kan sofa yana wasu rubuce rubuce ganin shigowarta ne yasashi saurin b’oye paper’n dake gabansa, tare da k’ura mata ido domin da’alama ya fahimci cewar idanu da hankalinta basu gane mata shiba. Ganin kuma da yayi ta fara kuka ne yasa shi sake k’ura mata ido tare dasa hannu ya zare AirPod d’in dake kunnensa, ahankali ya mik’e tsaye daga zaunen da yake, cikin nutsuwa ya zauna adaidai bayanta, batare kuma da ya k’ira sunanta ba yasa hannunsa ya dafa kafad’anta. Cak kuwa kukan da takeyi d’in ya tsaya, a matuk’ar tsorace ta juyo dan ganin ko waye. Ido hud’u da sukayi dashi ne ya sa ta k’walalo idanunta waje, tare dasa hannu ta dafe k’irjinta dake tsalle saboda tsoro. Hawayen dake kwance akan kyakkyawar fuskartata ya kalla, tare dasa harshensa ahankali ya d’an lashi pink lips d’insa. Ita kuwa Laylerh ganin irin kallon da yake matane yasa tayi saurin sanya hannu ta shiga share hawayennata. Murmushin daya bayyana kyawun fuskarsa yayi, ahankali ya kamo hannayenta, Jin yanda hannayen nata keda zafi ne yasashi d’an zaro idanunsa waje, ahankali ya d’an matso kusa da ita, cikin yanayin damuwa yace. “Kinyi kuka sosae gashi har jikinki yayi zafi, still kuma kinzo kina sakeyin wani kukan, sai yaushe ne zaki daina ta kura kanki da yawan kuka? kin manta cewar Dr. yace kina da hypertension? ko so kike kullum ya zama baki da lafiya?.â€? Ya k’are maganan nasa cikin sanyin murya, had’e kuma dasa hannu ya jawo Laylerh’n jikinsa. Tabbas awannan lokacin tana da buk’atar rarrashi da kuma nutsuwa, hakan yasa ta kwantar da kanta akan chest d’insa, tare dasa hannayenta ta zagaye cikinsa zuwa bayansa. Jinta acikin jikinsa ne yasa shi sakin sassanyar ajiyar zuciya, hannunsa d’aya ya d’aura akan naked skin d’in bayanta, tare da soma shafa bayannata ahankali, bakinsa ya kawo daidai saitin kunnenta cikin murya me kama da rad’a asanyaye yace. “Ya jikin Maleek?.â€? Yanayin yanda yayi mata maganan acikin kunnenta ne yasa ta shagwab’e fuska, tare dajin wani irin motsawan tsikar jiki, kamar kuwa dama jira take ya tambayeta jikin Maleek d’in saiga hawaye sun sake cika idanunta, hakan yasa tayi raurau da idanunta tare da karyar da wuyanta gefe, araunace tace. “Har yanzu baya motsi, kuma bai bud’e idanunsa ba, abu d’aya ne kawai me motsi ajikinsa, itace zuciyarsa.â€? D’an tsagaitawa da maganan nata tayi tare da d’agowa daga jikinsa, hannayensa ta kamo ta rik’e acikin nasa. Cike kuma da tsananin damuwa taci gaba da cewa. “Inason naga ya bud’e idanunsa, Inaso naga yana motsi kaman yanda kowa keyi, banason nagansa acikin k’unci, sannan kuma banason duk wani abu da zai cutar dashi, saboda shi kad’aine Yayah nah, shi kad’aine acikin duniyar nan, bana tantamar basa rayuwata Idan har hakan zaisa ya zamo kamar kowa!!!â€? Lumshe idanunta tayi wanda hakan ya bawa hawayen dake cikinsu daman sauk’a akan k’uncinta. Najeeb kuwa idanu ya zuba mata baya ko k’yaftawa, yayinda yakejin wani irin soyayyarta na ratsa duk ilahirin jikinsa, daga wani b’angaren na zuciyarsa kuwa tausayinta ne yayi masa k’awanya wanda har hakan ya sashi kasa jurewa, har saida ya sake jawota ya rungumeta k’am, labb’ansa ya d’aura adaidai saitin forehead d’inta, tare da sakar mata wani irin kiss, take kuwa idanunsa sukayi jajur dasu. Abundake yawo acikin k’irjinsa ya soma k’ok’arin dannewa, ta hanyar saita nutsuwarsa, d’an d’ago Laylerh’n yayi cikin kulawa yace. “Jikinki yana k’ara zafi sosae bari na d’auko miki magani kisha.â€? Baijira me zata ce masa ba kuwa ya mik’e tsaye. Direct gaban bedside drawer d’insu ya nufa, murfin drawer’n ya bud’e ya ciro sachet d’in paracetamol, k’waya k’wayan paracetamol d’in guda biyu ya b’alla, tare da fita falo ya d’auko goran ruwa marar sanyi sosai. Dawowa yayi ya zauna akusa da ita, had’e da mik’o mata k’wayan magananin. Ba musu kuwa ta amsa Tasha. Murmushin dake bayyana damuwar da yakeji acikin zuciyarsa yayi, ahankali ya kama kafad’un Laylerh’n ya kwantar da ita akan gadon, tare dajan blanket ya rufa mata, Dan ran k’wafowa yayi ya sake kissing goshinta, cike da kulawa yace. “Zanje wani waje, bazan jima ba zan dawo ki d’anyi bacci ki huta kinji.â€? Kai ta girgiza masa cikin muryarta da ta disashe tace. “Anjima zamu sake komawa asibiti nida Oum Ayush.â€? Jin ta ambaci asibiti ya sashi d’an lumshe idanunsa, kansa kawae ya jinjina mata alaman “To.â€? Baatare kuma da ya iya cewa komai ba ya d’au wayarsa tare da juyawa ya fice daga cikin d’akin. Ganin kuma ya fita ne yasa ta lumshe idanunta, duk da cewar kuwa sam sam batajin bacci amma lallai tana buk’atar nutsuwa. Asibiti. Akaro na barkatai kenan da Abbou Khareem ke d’ago kai ya kalli d’an Uwa kuma Yayan sa, da duk yanayinsa ke baiyana matsananciyar damuwa. Gyara zamansa yayi tare da fuskantar d’an uwannasa kana cikin sanyin murya yace. “Tabbas Kallo d’aya kawai za’ayi maka asan cewa kana cikin damuwa, amma ko kusa ban tab’a kawowa araina cewar akwai wata damuwa da zata dameka wanda har zaka iya kasa fad’amin ba, musamman damuwar da ta shafi Maleek domin koba komae shid’in matsayin d’ana yake.â€? Jin maganan Abbou Khareem d’inne yasa Abbou Jaheed sauk’e ajiyar zuciya. Hak’ik’a ko zai jinkirta fad’an damuwarsa to baga d’an uwannasa ba, sannan kuma matsalar da Maleek d’in ya gamu da ita ba irin wacce za’a b’oye bane, saboda haka ya zame masa dole ya gayawa k’aninnasa abundake faruwa. Kansa ya d’an sunkuyar k’asa, tare da tattaro nutsuwarsa, duk dama baya da kuzari amma dole zai nemo jarumta, barayin da Maleek d’in ke kwance ya kalla, cikin muryarsa me d’auke da sanyi yace. “Tabbas Maleek ya had’u da jarabawar Ubangiji, wanda kuma ya d’aura masa itane bawae don baya sonsa ba, ba kuma yayi hakanne wai don Maleek d’in ya aikata masa zunubi ba, domin kuwa jarrabawa ce da kowani bawa na duniya zai iya fuskanta, domin kuwa shafin dake cikin littafin k’addara yawane da su, bayan ka gama da wannan sai wata sabuwa ta sake bud’ewa, Dr. Mouhammad ya fad’amin cewa asanadiyar accident d’in da Maleek yayi, ya samu matsala acikin mararsa, wanda hakan yasa, k’waya k’wayan haihuwarsa ba zasu iya rikid’ewa su zama k’wayar halittan da zasu samar da d’a ko y’a ba, bi ma’ana Maleek bazae tab’a haihuwa ba saidai wani ikon Allah.â€? Idanu Abbou Khareem ya zaro waje cikin matsanancin tashin hankali, Jin cewar wai Maleek bazai sake haihuwa ba. Domin kuwa maganan ya zo masa amatuk’ar ba zata, wanda har saida yasa idanunsa suka ciko da k’walla, masu d’auke da matsanancin tausayin Maleek d’in. Asanyaye ya shiga ambaton sunan Allah dan kuwa al’amarin ya sakashi a shock sosae. Magana yakeson yi amma duk sai yaji ya kasa. Daidai lokacin kuwa k’iran Alhaji Farouk wato Baban Munnira ya shigo wayarsa. Take Abbou Jaheed yaji k’irjinsa ya buga, domin yasan cewa lallai acikin biyu za’ayi d’aya, abu me yiwuwar ce kuwa bazaiyyi dad’i ba. *16February/2021 *4:13 pm* 2/18/21, 8:33 AM - Ummi Tandama: *L.M* *Not Edit* *Chapter 53* Ci gaba da ruri wayan Abbou Jaheed d’in tayi, yayinda ya k’urawa screen d’in wayar idanu, zuciyarsa cike da fargaban abunda zai biyo baya nan da y’an kwanaki kad’an. Ganin kuma da yayi wayar tasa ta kusa tsinkewa ne yasashi d’aga wayar tare da karata akan kunnensa, gudun kuma kada yawan maganansa yayi yawa acikin wayarne yasashi tashi tsaye ya fice daga cikin d’akin, don amsa wayar tasa awaje. Abbou Khareem kuwa da har yanzu tausayi, da kuma aljabin daya shigesa najin matsalan Maleek da yayi baisake saba, maida kallonsa yayi ga Maleek d’in, tare dasa hannu ya tallafi hab’arsa. Tausayin Maleek d’inne tsantsa ya cika masa zuciya, domin kuwa shi kansa yasan ya zafi da rad’ad’i had’i da ciwon rashin haihuwa yake, yasan abune me tsananin ciwo da k’unci, abune dake sa zuciyar mutum koda yaushe ta zamana cikin rauni, saidai kuma babu wanda ya isa gujewa k’addararsa, domin kuwa abunda Allah Ya tsara tabbataccene sai ya faru ko min jimawa. Y’an guntun k’wallan da suka zuba masa yasa hannu ya share, tare da maida kansa jikin kujera, ahankali kuma cikin sanyin murya yace. “Yah Allah Ina rok’onka da kabawa Maleek ikon cin wannan jarrabawa mai tsananin k’una da ciwo daya sameshi, Allah kasa ya d’auki k’addararsa da hannu bibbiyu, domin kuwa kafi kowa sanin abunda ka shirya.â€? D’an tsagaitawa da maganan nasa yayi tare da soma ambaton sunan Allah dan samawa kai nutsuwa. Baiwani jima ahaka ba kuwa Abbou Jaheed ya dawo cikin d’akin bayan ya gama amsa wayar. Kallon d’an uwansa yayi kana cikin sanyin murya yace. “Alhaji Farouk ne ya k’ira nakuma shaida masa cewa Maleek ya samu accident, yanzu haka Insha Allah yace suna zuwa shida iyalansa.â€? Kai Abbou Khareem ya jinjina tare da cewa. “Allah Ya kawosu lafiya.â€? Daganan kuwa shiru sukayi babu wanda ya sake cewa d’an uwansa wani abu. Acan gida kuwa duk yanda Laylerh taso samarwa kanta nutsuwa ta kasa, abubuwa da yawane ke faman ci da azalzalan zuciyarta wanda hakan yasa taji bazata iya jurewa kwanciyar da takeyi d’in ba. Ahankali ta yaye blanket d’in da Najeeb d’in ya rufa mata, tare da zuro da k’afafunta k’asa, yanzun kam Alhamdulillahi domin kuwa ciwon kan da takeji d’in ya d’an lafa mata, duk da kuwa cewar kannata baidaina ciwo duka ba, amma baya mata ciwo sosai kaman na d’azu da takejinsa kaman zai rabe biyu. Hannunta tasa abayanta ta k’arasa zuge zip d’in rigar dake jikin nata, tare kuma da zare rigar gaba d’aya daga jikinta. Hakanan taji tanason yin wanka, saboda tana da yak’inin cewa yin wankan zai taimaka mata ta d’anji kuzari ajikinta. Doguwar rigar da ta cire d’in ta d’auka tare da jefata acikin dustbin d’in wanki, cikin tafiyarta me d’auke da sanyi ta k’arasa gaban makeken drawer’n dake cikin d’akin, anutse ta bud’e murfin drawer’n inda ta ciro wani mini pink towel sabo k’al ta d’aura ajikinta. Brush da kuma Maclean d’inta dake aje akan mirror ta d’auka, kai tsaye kuwa ta wuce toilet. Kasancewar kuma akwai komai da komai na kayan wanka acikin toilet d’inne yasa tana shiga ta zare towel d’in dake jikinta, d’aya daga cikin showercap d’in dake jere akan wani abu na glass dake cikin toilet d’in ta d’auka tare da suturce gashin kanta dashi, tayi hakanne kuma saboda sam bataso yau d’in ruwa ya tab’a kanta, saboda ana busa sanyi sosae. Ruwa me d’an d’umi ta had’awa kanta acikin had’add’en bathtub d’in wankan nasu me yanayi da jikin kakkauran glass. Ahankali ta shiga cikin babban bathtub d’in ta kwanta, tare da nutsa duk jikinta acikin ruwan, wanda dad’i da kuma d’uminsa yasa ta lumshe idanunta ahankali. Take kuwa kaman jira idanunnata suke ta rufesu, kyakkyawar fuskarsa ce ta soma yi mata gizo, wanda hakan yasa bisa dole ta karyar da wuyanta gefe, cikin muryarta da tayi sanyi kana take fidda rauni sosae tace. “Banason ka tafi ka barni, domin kai bawai iya duniyata bane kawae, gaba d’aya rayuwata ce kai, bana fatan ciwo da kuma k’unci su d’ore acikin rayuwarka Yah Maleek!!!â€? Ahankali wasu irin hawaye masu zafi suka gangaro kan kumatunta, yayinda kuma lokaci d’aya ta sakejin matsanancin tausayin kanta da kuma na Maleek d’in ya cika mata zuciya. Asanyaye cikin rashin kuzari tayi wankan, koda ta fito daga cikin bathtub d’in kuwa alwala tayi domin taga yamma ya d’an soma rufawa sosai. Fitowarta daga cikin toilet d’in kuwa yayi daidai da bugawan agogon dake nuna cewa daidai lokacin k’arfe biyar tayi. K’arasawa gaban dressing mirror d’inta tayi tare da d’aukan wani towel ta tsane ruwan jikinta. Body lotion na Nevea me dad’in k’amshi ta shafa ajikinta, batare kuma da tunanin shafa powder ko kuma yin kwalliya ba ta k’arasa gaban sif d’in kayanta. Wani riga da sket d’in Australia’n lace me kalan blue da golden ya ciro, wanda akayi masa simple style d’in pencil sket da kuma riga fitted wanda iyakanta cinyarta. Koda ta sanya kayan kuwa sosae sukayi mata kyau, musamman ma rigar da ta zauna ajikinta, tamkar ma ajikinta aka d’inka rigan. Dogon gashinta ta nannad’e da ribbom, tare da d’auko wani siririn Australia’n vail ta yafa ajikinta, wanda ya tsaya daga wuyanta zuwa cinyoyinta, kasancewar kuma d’an kwalin kayannata babbane yasa ta d’aurashi akanta irin d’aurin nan da ake parking d’insa a tsakiyar kai, sosai kuwa d’aurin ya sake fito da kyaun da tayi, wani cool parfume me dad’in k’amshi ta fesa, batare kuma da ta sake kallon madubi ba ta zura wasu new designer half cover shoe ak’afanta kai tsaye ta fice daga cikin d’akin. Direct sashin Oum Ayush ta nufa koda ta k’arasa part d’in Oum Ayush d’in kuwa ta samu harta kammala had’a abincin da zasu kai asibitin, yayinda Fou’ad kuwa tuni ma ya koma asibitin. Ganin Laylerh’n ne kuma yasa Oum Ayush d’auko mayafinta, domin dama itama already ta shirya don komawa asibitin. D’aya daga cikin basket d’in da food flask d’in abincin ke ciki Laylerh’n ta d’auka, yayinda Oum Ayush kuma ta d’auki sauran. Kusan atare suka fito daga cikin sashin na Oum Ayush d’in tana me tambayanta. “Ya ciwon kannata?.â€? “Da sauk’i.â€? Ta bawa Oum Ayush d’in amsa adaidai lokacin da suka iso bakin motar Oum Ayush d’in. Kamar dae yanda suka tafi d’azu haka yanzun ma Oum Ayush da kanta tayi driving. Tunda suka d’auki hanyar asibitin kuwa Laylerh keta faman sak’awa da kuncewa, yayinda acikin zuciyarta take fata da kuma burin idan taje ta samu Maleek d’in ya farfad’o, domin kuwa tasan akasin hakan zai k’ara sata acikin wani sabuwar fargaba da kuma fad’uwar gaba. Isowarsu cikin asibitin kuwa yayi daidai da isowar Alhaji Farouk da kuma Ilayansa wato Hajiya Buzuwa da kuma Munnira wanda take matsayin amarya, duk da kuwa cewar asibiti suka zo amma fuskarnan tata ayalwace take da meckup yayinda kuma kallo d’aya kawae zakayi mata ka fahimci cewa, cike take da yauk’i. Kasancewar kuma motarsu ce agaba yasa sam basu lura da ta su Laylerh’n ba, suna gama daidaita parking kuwa suka fito direct suka nufi cikin asibitin. Su kuwa su Laylerh sam basu ma lura dasu ba, domin saida su Munnira’n suka wuce kafun su Laylerh suka fito daga cikin motar ita da Oum Ayush. Hannayensu d’auke da basket suka nufi sashin da aka kwantar da Maleek d’in. Daf da zasu haura steps d’in da zai sadasu da d’akin Maleek d’inne kuma bisa tsautsayi Laylerh tayi missing d’aya daga cikin steps d’in take kuwa tatafi su ta fad’i k’asa. Wanda hakan yayi sanadiyar zubewar gaba d’aya kayan dake hannunta, fad’uwan da tayinne kuma yasa ta saki wani irin k’ara, saboda ta d’an bugu kad’an ahannunta. Adaidai lokacin kuwa zuciyar da bugawanta ke tafiya slowly tayi wani irin harbawa, har saida gangar jikin mamallakin zuciyar nan ta samu motsawa. *(Bani da enough charge shiyasa na muku wannan kud’an rage lokaci kafun gobe Idan Allah Ya kaimu. Shin me kuke tunani akan Maleek? Idan Alhaji Farouk yaji matsala da kuma lalurarsa zai bashi auren yarsa? koma me Insha Allah Zakujishi a page d’in gobe.)* *9:10 pm* 2/19/21, 9:36 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna *Not editing* *Chapter 54* K’ara da kuma ganin fad’uwar da Laylerh’n tayi ne yasa Oum Ayush da ta wuce gaba tayi saurin juyowa tare da d’an dawowa baya. Hannunta tasa ta kamo hannun Laylerh’n wanda ta d’an yunk’ura ta tashi tsaye. “Subahanallah sannu Allah Yasa bakiji ciwo ba?.â€? Oum Ayush ta tambaya tana me mik’ar da Laylerh’n tsaye. Fuska ta b’ata tare da marairaice idanunta wanda tuni suka ciko da hawaye, d’aya hannunta da ta fad’i akai ta rik’e, wanda asanadin hakan yasa hannun nata ya d’an kuje har da jini, ganin jinin da tayi ne kuma yasa ta langwab’ar da fuska, ashagwab’e tace. “Nabuge Oum Ayush hannuna zafi yakemin.â€? Kallon hannun nata Oum Ayush tayi, ai kuwa gashi kujewan har ya d’an fara fitar da jini, kasancewarta farar fata ne kuma yasa take wajen yayi jajur dashi. “Ya Ilahi tabbas kinji ciwo gashi harma da jini, sannu ko bari nak’ira ko da nurse ce ta d’an miki treating wajen.â€? Oum Ayush ta fad’i hakan cikin kulawa tare da d’an soma rarraba idanunta a sonta wai ko zataga nurses d’in hospital d’in. Cikin sa’a kuwa saiga wata nurse ta fito daga cikin wani d’aki. Da sauri Oum Ayush d’in ta k’arasa ta k’ira nurse d’in, cikin kulawa kuwa nurse d’in tazo wanda tun kafun ma Oum Ayush ta gama yi mata bayanin kujewan da Laylerh’n tayi, har idanunta sun sauk’a akai, saboda yanda Laylerh keta faman yayarfa hannun harda kuwa acikin idanunta, wanda kuma bawai k’wallan na zafin ciwon bane kawae, tsantsar sakalcine kawae yake damunta. Hannun Laylerh’n nurse d’in ta kamo, kana cikin kulawa tace. “Ayyah Sorry baby girl muje ko na d’anyi miki treating wajen, yana miki zafi sosai ne?â€? Sake shagwab’e fuskarta tayi, musamman ma da taji nurse d’in tace zatayi mata treating wajen, tasan dole acikin biyu sai anyi d’aya, dole ne ma sai sun wanke mata wajen, takuma san cewa ba k’aramin zafi zataji ba. D’an k’aramin bakinta ta turo gaba cikin d’ari d’ari da kuma tsoro tace. “Bayamin zafi sosai, nasan ma da kansa zai warke basai an wanke ba.â€? Idanu nurse d’in ta d’an zaro cikin d’an mamaki tace. “Abarki ahaka kenan kije ciwon yata miki zafi, tun yana k’arami har ya dawo babba?.â€? Kai ta sunkuyar k’asa tare da soma mamul mamul da bakinta. “Please nurse karki biye mata kuje ki wanke mata, idan angama treating wajen sai kizo ki sameni ad’akin da aka kwantar da Maleek d’in, mun gode sosae nurse.â€? Oum Ayush ta fad’i hakan tana me tattare kayayyakin abincin da Laylerh’n ta watsar, kuma cikin ikon Allah Ba abunda ya zube acikinsu. Jin abunda Oum Ayush d’in ta fad’ane yasa nurse d’in kama hannun Laylerh wanda tuni hawaye har sun wanke mata fuska, suka nufi wani sashi na daban. Oum Ayush kuwa kaitsaye d’akin da aka kwantar da Maleek d’in ta nufa. Hak’ik’a bugawan da zuciyarsa tayi da k’arfi shiya haifar masa da motsawan gangan jikinsa, cikin abunda baiwuce 12minute ba kuwa numfashinsa ya dawo, wanda kuma hakan shi ya sake daidaitawa wajen taimakawa bugun zuciyartasa ya zama tana tafiya adaidai yanda ya kamata. Ahankali yakejin kansa na wani irin juyawa, tamkar wanda ake wainasa. Wannan dalilin yasa shi soma motsa y’an yatsun hannunsa da kuma na k’afarsa, Take kuma ahankali ya soma bud’e idanunsa wanda suka d’an k’ank’ance kad’an. Sauk’e ganinsa yayi asaman d’akin da yake ganin rufinsa dishi dishi, yayinda yakejin kansa na wani irin sarawa. Ahankali ya maida idanun nasa ya lumshe, domin koda ya bud’esu bai fahimci a ina yake ba, saboda dishi dishi yake gani. Sannu ahankali abubuwan da suka faru dashi na accident d’in suka shiga dawowa cikin kansa filla filla, har saida komai da ya faru ya gama dawowa cikin tunaninsa kafun ya sake bud’e idanunsa akaro na biyu, cikin sa’a kuwa ko kad’an wannan karon idanunnasa basu nuna masa dishi dishin ba, rass yake gani bawani yana ko gizo. Wata irin nunmfashin da ya fusgane kuma yasa gaba d’aya hankalin su Abbou Jaheed ya dawo kansa, ganin idanunsa a bud’e ne yasa su Abbou Jaheed d’in saurin k’arasawa inda yake kwance. “Maleek! Maleek!! ka farfad’o ka bud’e idanunka Alhamdulillah!!!â€? Abbou Jaheed ya fad’a cikin yanayi na d’an rud’ewa da kuma farinciki. Kamar amafarki kuwa haka yaji muryar Abbou’n nasa hakanne kuma yasashi d’an juyowa ya kalli inda Abbou Jaheed da kuma Abbou Khareem ke tsaye. Idanu ya d’an k’ura musu na y’an wasu sakanni kafun ahankali ya d’an soma yunk’urin tashi. Da sauri Abbou Jaheed yasa hannayensa duka biyu ya soma k’ok’arin d’ago Maleek d’in fuskarsa d’auke da matsanancin farinciki. Maleek kuwa dake k’ok’arin tashi idanunsa ya rumtse da k’arfi sakamakon wani azababben zafin da yaji acikin mararsa, wanda har saida yasa ya kasa hak’uri saida yasa teeth ya datse lips d’insa. Ganin hakanne kuwa yasa Abbou Jaheed cike da matsanancin tausayin sa yace. “Sannu ko Maleek, bari ak’ira Dr. yazo ya dubaka.â€? Aikuwa ko rufe baki Abbou Jaheed d’in baiyiba Dr.Mouhammad ya turo k’ofar d’akin ya shigo, bayansa kuwa su Alhaji Farouk ne. Ganin Maleek d’in azaunene yasa Dr.Mouhammad had’iye sallaman da yake k’ok’arin yi cikin hanzari ya k’araso jikin gadon, hannunsa d’aya yasa ya dafa kafad’an Maleek d’in fuskarsa d’auke da yalwataccen murmushi yace. “Alhamdulillah naji dad’i matuk’a dana ga ka farfad’o har kuma kana iya zama, yanzu Ina da inane keyi maka ciwo?.â€? Dr.Mouhammad d’in ya k’are maganan yana me d’an tattab’a jikin Maleek d’in. Idanunsa dake alumshe ya bud’e cikin yanayin kasala da kuma rashin kuzarin daya samu kansa aciki yayiwa Dr. Mouhammad d’in nuni da kansa da kuma mararsa. D’an Jim Dr. Mouhammad d’in yayi tare da sauk’e ajiyar zuciya, cikin yanayin tausayawa yace. “Don’t worrie zasu daina ciwo Insha Allah, burinmu mu dama shine ka samu dawowa hayyacinka, akwai magungunan da zan baka dakasha komai zai zama normal da Yardar Allah, bari naje na kawosu.â€? Cikin sauri Dr. Mouhammad ya juya ya fice daga cikin d’akin, matsawarsa daga kusa da Maleek d’inne kuma yabawa su Alhaji Farouk wanda suke gaisawa dasu Abbou Jaheed daman sauk’e idanunsu akansa, ciki kuwa harda Munnira da ganinsa haka babu riga yasa ta k’ara tabbatarwa da kanta cewar ashe ma duk yanda take ganin had’uwarsa ya wuce haka. Take kuwa taji wani irin abu na musamman akansa, har saida taji kaman taje ta fad’a jikinsa ahaka. Kyawawan red lips d’insa masu shining ta kalla, wanda kuma bisa dole kallonsu yasa ta had’iyi wani yawu, idanunta ta d’an lumshe cikin k’asa da murya ta yanda ba maijinta acikinsu tace. “Wow hot and handsome guy, gaskiya wannan man d’in komai nasa is so special, tayaya ma zan fara imagine duniyar da zaikaini idan munyi aure?.â€? Wani murmushine ya sub’uce mata, sakamakon imani da tayi cewa, irin sane suke shid’ar da mace, su sata manta kowa da komai. Sake bud’e idanunta tayi tare da soma yawo da idanun nata akansa, Lallai dan mahaifiyarta ta gargad’etane kafun su taho, amma bayan haka da babu abunda zai hana ta zuwa tayi hugging d’insa, koda kuwa sau d’aya ne tanaso taji ni’imar jikinsa wanda aka horasa da Gym, duk da cewar jikinnasa bawai ko ina bane yake amurd’e damatsan hannayensa ne kawae, sai kuma lafiyayyun six packs d’in dake kwance akan cikinsa. K’arasawa jikin gadon Alhaji Farouk yayi, cikin yanayin tausayawa kuwa yayiwa Maleek d’in ya jiki. Kansa kawai ya jinjina alaman da sauk’i tare da maida idanunsa ya lumshe, domin kuwa tun farfad’owarsa baiyi magana da kowa ba, komai kallonsa kawae yake da ido. Koda Buzuwa ma ta yi masa ya jiki da kuma Allah Ya tsare na gaba, ita d’inma dakai ya amsa mata. Munnira kuwa tsayawa tayi tana kallonsa baki da hanci takasa yi masa koda ya jikinne ma, abu d’aya kawae tun sauk’e idanunta akansa taketa imagine shine wae ita Allah ya bawa wannan daman na zamowa matar, d’aya daga cikin mazan da irinsu basu da yawa aduniya, lallai Allah Ya had’a ta da babban rabo. Shikuwa Maleek sam baimasan da wata wai Munnira awajen ba, domin kuwa ko gefen da take idanunsa basu kalla ba, hasali shi yama manta da ita dama kamanninta gaba d’aya. Fitan Dr.Mouhammad kuwa bai wuce da mintuna 10 ba sai gashi ya shigo, yayinda Oum Ayush ke biye dashi, wanda hannunta ke d’auke da basket d’in abinci. Shigowarsu ne kuma yasa su Buzuwa suka dawo da kallonsu ga Oum Ayush d’in, ciki kuwa harda Maleek. Oum Ayush kuwa ganin Maleek d’in ya farfad’o da kuma arba da surukan su da tayi ne yasa murmushi da fari’a suka bayyana akan fuskarta, cikin kulawa tayi musu sannu da zuwa, fuska ba yabo ba fallasa Buzuwa ta amsa, tare da soma yiwa Oum Ayush d’in kallon k’urulla musamman da ta sauk’e idanunta akan lace d’in dake jikin Oum Ayush d’in wanda ak’alla kud’insa yakai 100k, irin dai lace d’innan ne wanda matan shugaban k’asa ko kuma manyan k’usoshin gwammanati ke sawa. “Lallai akwai kud’i awannan family’n.â€? Buzuwan ta fad’a acikin ranta, tare da soma hasashen yanda zata samu daman k’ulla alak’a da Oum Ayush d’in duk dama bataji matar ta kwanta mata arai ba, amma zata daure su k’ulla alak’a kodan fahimtar da tayi cewa, Oum Ayush d’in y’ar fashion ce sannan kuma akwai naira da had’uwa. Oum Ayush kuwa bama takan Buzuwan take ba, basket d’in dake hannunta ta ajiye, tare da k’arasawa wajen Maleek d’in fuskarta d’auke da murmushi tace. “Masha Allah Maleek lafiya tasamu kenan, Allah Abun godiya ya jikinnaka?.â€? Murmushin daya d’an bayyana secret dimple d’insa yayi, tare da lumshe idanunsa, akasalance ya jinjina mata kai alaman “Da sauk’i.â€? Acikin zuciyarsa kuwa sunan Layleh ya k’ira, tare kuma da tambayan kansa cewar Ina take, wani irin azalzala yakeji acikin zuciyarsa, ita kawae yakeson ya fara gani ayanzun, yunwa da k’ishin ruwanta yakeji, tabbas yasan kuma rashin ganinta awajen shi ya k’ara haifar masa da kasala, yayinda sam ajikinsa bayajin komai waidan yayi tunanin Laylerh’n kasancewarta matar wani, domin yasan hakan k’addararsa ne, duk da cewar kuma yasan tunaninta haramunne agaresa, amma baya tunanin akwai wani second na cikin rayuwarsa dazai wuce batare da tunanin Laylerh’n ba. Wata allura da Dr. Mouhammad ya tsikara masa akan jijiyan hannunsa ne, ya sashi d’an bud’e idanunsa. Kallonsa Dr. Mouhammad yayi kana anutse yace. “Ya kamata kasawa cikinka abinci koda tea ne ka samu kasha, idan yaso bayan kaci abinci sai kasha way’annan magungunan Dan sune zasu taimaka k’warai wajen rage maka ciwon da kakeji amararka da kuma kanka, please ka daure kashasu saboda pain relievers ne masu kyau.â€? Kamar ko yaushe kansa kawai ya jinjinawa Dr. Mouhamad d’in, tare kuma da maida idanunsa ya rufe. Dr.Mouhammad kuwa juyawa yayi ya fice daga cikin d’akin. Hakan kuwa shi Ya bawa Munnira daman matsowa kusa da Maleek d’in, cikin yauk’i da kuma siranta murya had’i dason jawo hankalinsa gareta tace. “I’am sorry Dear ya jikin naka?â€? Bak’uwar muryar da yaji akusa dashi ne yasashi d’an bud’e idanunsa tare da sauk’e ganinsa akanta. Kallo d’aya kawae yayi mata ya watsar, acikin zuciyarsa yace. “Tsinken sigari ta sake biyoni Yah Allah Kanesantani da wannan babyn roban, because I hate her.â€? Ita kuwa Munnira ganin baice da ita komai bane yasa tasake matsawa kusa dashi, tare da soma yin magana k’asa k’asa. Oum Ayush dake kallon yarinyar da wai itace zata auri Maleek d’in ajiyar zuciya ta sauk’e tare da d’auke kanta, itakam bata d’auka irin zab’in da Abbou Jaheed yayiwa Maleek d’in kenan ba. Sam yarinyar bata mata ba, because daga ganinta bata da kunya, irin fand’ararrun y’an matan nanne marassa kamun kai. Food flask d’in da ta shigo dashi ta jawo tare da d’aukan plate ta soma k’ok’arin zubawa Maleek d’in abinci aciki. K’aran turomin k’ofar d’akin da akayine yasa gaba d’aya duk suka maida idanunsu ga jikin k’ofar. Ciki kuwa harda Maleek da hakanan turo k’ofar d’akin da akayi yasa zuciyarsa soma bugawa da k’arfi. Kyawawan fararen k’afafunta wanda suke sanye cikin half cover shoe ta fara sakowa cikin d’akin, kafun daga bisani sauran gangar jikinta suka shigo, hannunta na damane ke rik’e dana hagu, wanda kuma shine ke d’auke da ciwon da akayi treating d’insa, akasa masa magani da kuma auduga, bisa umarnin wannan nurse d’ince kuma yasa tasaka y’ar yatsarta ta danne audugan kada ya fad’i, domin kasancewar ciwon nata bawani babba bane yasa ba’a saka fulasta an suturceshi ba. Tabbas shigowarta cikin d’akin ya haifar da bugawar zuciyar wasu, saidai kuma amma bugawa ne ma banbanta. Yayinda bugawar zuciyar Maleek ta zama ta musamman dana sauran. Ahankali ta d’ago idanunta daga kallon ciwon nata da take, tare da d’ago gaba d’aya kanta, wanda hakan yasa cikin yanayin bazata ta sauk’e ganinta akansa. Kyawawan idanunta dake d’auke da danshin hawaye ta zaro waje, cike da alamun mamakin ganinsa da tayi azaune. Lokaci guda kuwa taji wani irin sanyi na ratsa cikin tafin k’afanta har izuwa duka gangar jikinta. Wani abu me kama da matsanancin farinciki ne ya lullub’e duk zuciyarta, wanda har hakan yasa idanunta sake cika tab da k’walla. Sam ba zata iya jurewa kallon da sukeyi juna ba, domin kuwa kallone dake shigar da sak’onni kala kala wa gangar jikinsu. Haka zalika kallone dake rura watar abunda ke cin zuciyarta. Tabbas tayi imani cewa da ace daga ita saishi ne ad’akin to tabbas da babu abunda zai hana bataje ta fad’a jikinsa ba. Kanta ta sunkuyar k’asa tare kuma da kasa koda motsa k’afartane, asanyaye ta had’e y’an yatsunta tare da soma jujjuyasu. Shima akaron farko kenan daya janye idanunsa daga gareta, domin kuwa ad’an kallon sakannin da ya mata shi kad’ai yasan me yaji, inama da ace yau ita d’in takasance matarsa, tabbas da ajikinta zai kasance domin hakan ba k’aramin cire masa radad’i zaiyi ba. Bayansa ya jingina da jikin bango had’e da lumshe kasalallun idanunsa. Munnira dake gefensa kuwa wani irin bugawa zuciyarta keyi asakamakon ganin Laylerh’n da tayi, tabbas bazata manta fuskar Laylerh’n ba domin ta tab’a ganinta sau d’aya, saidai kuma amma alokacin Laylerh’n bata kai haka girma ba. K’warae ganin Laylerh’n ya tayar mata da hankali, tare da jin wani irin matsanancin kishin Laylerh’n da Allah Yayiwa baiwar kyau da kuma kyawun halitta, wanda asanadin hakanne kuma yasa duk taji ta muzanta, saita ji cewar ita ba komai bace a had’uwa. Ae kuwa baga Munnira kad’ai ba harga Buzuwa ganin da tayiwa Laylerh yasa taji gabanta ya fad’i, domin kuwa ko za’a had’a sama da k’asa akwai tazara da kuma banbanci me masifar yawa atsakanin Laylerh’n da kuma y’arta Munnira, nesa ba kusa ba Laylerh tafi Munnira hundred percent. Bakomai ne kuma ya d’aga mata hankali ba kuwa, fa ce irin kallon da taga Maleek nayiwa Laylerh’n. “LAYLERH! anwanke miki ciwon?.â€? Maganan Oum Ayush kenan daya sa Laylerh’n sake d’ago kanta asanyaye tace. “Eh.â€? Kai Oum Ayush ta jinjina, yayinda cikin mamaki su Abbou Jaheed suka shiga tambayan abunda ya samu Laylerh’n, bayani Oum Ayush ta musu tare da d’aukan plate d’in abincin dake hannunta ta mik’awa Maleek. Kallon flate d’in ferfesun chicken soup d’in yayi, ahankali ya d’an girgiza kai, akaron farko ya motsa bakinsa cikin wata silent voice da zak’inta yasa Laylerh lumshe ido, Munnira kuwa ta zura masa na mujiya yace. “Nak’oshi.â€? “Ka k’oshi kuma Maleek? ko bakaji abunda Dr.Mouhammad ya fad’a bane cewar saikaci abinci kafun kasha magani.â€? Cewar Abbou Khareem. D’an b’ata fuska yayi asanyaye yace. “Tea kawae.â€? Jin hakanne kuma yasa Oum Ayush sakin murmushi, cikin kulawa had’i da d’an d’aga murya tace. “Laylerh had’amasa tea, akwae ruwan zafi a flask, sannan kuma akwai kayan tea d’inma duka na taho dasu.â€? Laylerh dake tsaye asanyaye tace “To.â€? Sam har yanzu ta kasa sake kallonsa duk kuwa da cewar zuciya da gangar jikinta na azalzalarta akan cewa lallai sai ta kalleshi amma takasa. K’ok’arin soma had’a masa tea d’in tayi daidai lokacin kuwa aka soma k’wala k’iran sallan magriba. Wanda hakan yasa Abbou Jaheed da kuma Abbou Khareem suka mik’e don fita waje d’auro alwala da kuma yin sallah. Ganin hakane kuma yasa Alhaji Farouk shima tashi tsaye, kallon Buzuwa yayi cikin kulawa yace. “To kuzo mu wuce ko naga dare na sakeyi.â€? Bisa dole badon sun soba suka taso suma. Munnira kam wani haushine ya kamata dan ko kad’an bataso tafiya tabar Maleek d’in ba, domin zama akusa dashi kad’ai da tayi yasa taji ta acikin wata duniya ta daban. Koda suka zo fita daga d’akin wani uwar harara ta shiga watsawa Laylerh, wanda ita bata masan tanayi ba, ganin sun fitane kuma yasa Oum Ayush bi musu baya, amutumce dan koba komae gaisuwa suka zo musu. Fitan Oum Ayush d’innne kuma yasa suka zama saura su biyu kad’ai acikin d’akin. Anutse ta kammala had’a tea d’in acikin wani had’add’en cup, kasancewar kuma tea d’in na da zafi ne kuma yasa ta tallafi k’asa da kuma hannun kofin. Ahankali cikin wani irin yanayin sanyi da ta samu kanta aciki ta shiga takowa zuwa gareta, batare kuma da ta d’ago kanta ta kalleshi ba. Isowarta jikin gadon nasa ne kuma ya sata tsaya, asanyaye ta mik’o masa kofin tea d’in, still bata d’ago kai ta kalleshi ba, hasalima idanunta cike suke tab da hawaye. Kyawawan yatsun hannunta ya zubawa ido, batare kuma daya karb’i cup d’in tea d’in ba, ya dawo da kallonsa ga kyakkyawar fuskarta. Yah Subahanallah wani irin matsanancin Soyayyarta ne yaji tana dukawa k’irjinsa, yayinda kuma sassanyan k’amshin cool parfume d’in dake fita ajikinta yasa shi jin hot feelings d’inta na neman rikita masa lissafi, akasalance ya lumshe kyawawan idanunsa masu d’auke da kyawawan lashes, cikin sanyi yace. “Na k’oshi.â€? Kalmar tasa ta cewa ya k’oshin da yayinne yasa tayi saurin d’ago kanta, daidai lokacin kuwa shima ya bud’e idanunsa akanta. Hakan yasa idanunsu sark’ewa awaje d’aya, dalilin hakan kuwa yasa dukansu sukaji wani irin kasala da sanyi ya sauk’ar musu, asanadin hakan kuwa har basu san lokacin da sukayi kusa da juna ba. Kallon cikin idanun juna kuma akusa da juna shiya k’ara sawa zuciyarsa wani shauk’i, tare kuma da matsanancin rauni. Ahankali hawayen da suka cika idanunta suka samu daman gangarowa kan fuskarta, lallai tabbas da sexy eyes d’insa yake azabtar da ita, da kuma kallon da yake mata yakeson zautar da ita, bisa dole ta lumshe idanunta. Shikuwa Maleek ganin hawaye akan fuskarta yasashi sake jin kansa acikin rauni, ahankali kuma cikin feeling mood d’in daya samu kansa ya matso kusa da ita, har ya zamana numfashinsu na gauraya waje d’aya. Batare da zato ko tsammani ba, ya d’aura lallausan sajen dake kwance agefe da gefen fuskarsa adaidai nata gefen fuskar. hakanne kuwa yasa tsikar jikinta yayi wani irin mahaukacin zubawa, har yakai ga ta kasa iya rik’e cup d’in dake hannunta, bisa dole ta ajiye cup d’in akan gadon, tabbas sauk’an lallausan beard d’insa akan fuskarta bak’aramin sanya ta acikin wata sabuwar duniya da yanayi yayi ba, wanda har hakan yasa numfashinta ya tafi luuu kaman zai d’auke, idanunta ta sake lumshewa tare da bud’e y’an k’ananan lips d’inta, saboda feeling d’in dake shiganta kuwa itama kanta batasan tayi hakan ba. Shima nasa idanun ya lumshe ahankali kuma shima ya bud’e labb’ansa, still kuma har yanzu gefe da gefen fuskarsu na manne dana juna. Lallai tabbas ba zasu sake kara iya minti daya ahaka ba tare da sun had’e sun zama abu guda ba, domin kuwa gangar jikinsu amatuk’ar buk’ace suke da junansu, hatta tongue d’in kowannensu buri yake yajisa acikin mahad’insa. Lallai wannan yanayine da babu wanda yasani ko ya tab’aji sai wanda ya jima acikin mayen so da sha’awa. Daidai lokacin kuwa aka turo k’ofar d’akin. Acan waje kuwa Abbou Jaheed ne ya dubi Alhaji Farouk cikin sanyin murya yace. “Idan babu damuwa Alhaji Farouk zan so had’uwarmu gobe dan tattauna wata sabuwar matsala da ta ruskemu.â€? D’an jim Alhaji Farouk yayi cikin mamakin wata irin matsalace haka yace. “To babu damuwa Alhaji Jaheed Allah Ya kaimu goben.â€? Da “Ameen.â€? Abbou Jaheed ya amsa sannan sukayi sallama, daga haka su Abbou Jaheed suka wuce masallaci shikuwa Alhaji Farouk kaitsaye ya nufi wajen motarsa. *Friday19/2/2021* *7:26 pm* 2/21/21, 10:47 PM - Ummi Tandama: *L.M* *55* “AYSHNOOR!!!.â€? Ya k’ira sunanta da wata irin kasalalliyar muryarsa wacce da k’yar take iya fita, irin dai murya me d’auke da tsananin shauk’in dake bayyana yanayin da yakeji ajikinsa, yanayin kuma da bashi da misali, yanayin daya saka su fad’awa cikin wata irin sabuwar duniya ta daban, yanayin daya bayyana asali da kuma gaskiyar muradinsu. Ahankali kuwa sauk’an muryarsa acikin kunnuwanta yasa gaba d’aya duk taji jikinta ya zama very weak, wani irin sassanyan yanayi ta samu kanta aciki wanda har ya kaita ga kasa jurewa, ahankali ta sake lumshe tsumammun idanunta, wanda suke cike da azabebbiyar soyayyarsa, ji takeyi kaman ta saka masa kuka, amma kuma zazzafan yanayin da tasamu kanta aciki yanzun ya kasa bata daman hakan, domin kuwa zuwa yanzu gaba d’aya zuciyarta ta riga da ta narke, sonsa da k’aunarsa ne kawai ke ruruwa acikin zuciya da kuma ganganar jikinta, amatuk’ar zauce kuma cikin wani irin yanayin dake fusganta ta daura hannunta dake rawa adaedae saitin kirjinsa wanda yake d’auke bandage, kanta ta d’an soma jujjuyawa cikin kuma muryarta dake shaking ta soma k’ok’arin harhad’a kalmar sunansa, saidai kuma amma duk yanda taso ga had’a kalmomin bakinta don su bada ma’ana abun yaci tura, hakan yasa ta rumtse idanunta tare da soma fitar da hucin numfashi ta bakinta. Tabbas sauk’an dumin numfashinta akan wuyansa ne yasashi sakin wani irin numfashi, ahankali yasa d’aya daga cikin hannayensa ya jawota jikinsa. Atare suka sauk’e wani irin k’akk’arfar ajiyar zuciyar, da yasa dukka zuk’atansu amsawa, batare kuma da sun hana rai da zuciyarsu abunda suke soba, still atare suka sake shigewa jikin juna, wanda kuma hakanne ya bawa gangar jikinsu daman kasancewa da juna. Ahankali Fou’ad dake tsaye abakin k’ofar d’akin kusan mintuna 4 da suka wuce ya d’an lumshe idanunsa, cikin yanayin sand’a kuma ya juya tare da jawo k’ofar d’akin ya rufeta da sauri, batare da ya bari sun gansaba, duk da kuwa yasan cewar basa cikin hayyacin da zasu gansa d’in, domin yanayin daya gansu aciki bawae yanayine da kowa zai iya shigansa ba. Ahankali ya jingina bayansa da jikin k’ofar d’akin, tare dasa hannu ya d’an dafe k’irjinsa dake bugawa da d’an k’arfi, wanda ba komae ne kuma ya jawo hakan ba, face ganin da yayiwa Laylerh Maleek d’in. Mekenen idanuwansa suka gani? Wani irin zunubi me girma Laylerh da Maleek suke aikatawa haka? hak’ik’a tunda yake bai tab’a kawowa aransa cewa soyayyar da Maleek keyiwa Laylerh zai iyasawa idanunsa rufewa, har ya kasa banbance halak da kuma haram ba, wannan wani irin Zunubi ne haka? Tayaya Maleek da Laylerh zasu kasance a irin wannan yanayin bayan kasantuwar matsayin Matar wani? Yayiwa kansa tambayar cikin yanayin mamaki da kuma al’ajabin abunda idanuwansa suka gane mai, lallai yau ya sake gamsarwa kansa cewar rayuwar Laylerh da Maleek cike take da k’addara. “Da ace Najeeb ne kuma ya gansu ahaka fa?.â€? Wani sashi na zuciyarsa ta jefo masa tambayar daya sashi, saurin fad’in kalman. “Innalillahi Wa’inna Ilaihirraju’un.â€? Domin kuwa yasan faruwar hakan ba k’aramin tashin hankali zai haifar ba, saboda abune mawuyaci ace Najeeb ya iya b’oye zargi da kuma b’acin ransa. Lallai yasan cewa so makahone amma sam baiyi tunanin cewa soyayya zata rufewa Maleek idanu har haka ba. Duk da cewar baisan me sukeji acikin gangar jiki da zuciyarsu ba, amma yanajin cewa hakan da sukayi sam baikamata ba. Hannunsa yakai ahankali ya share gumin daya fito daga goshinsa, kana asanyaye yace. “Insha Allah Komae yakusa zuwa k’arshe, domin kuwa acikin irin wannan al’amarin dole sai wani abu na daban ya faru.â€? Sauk’ak’akk’iyar ajiyar zuciya yayi tare da k’arasawa ya zauna akan wani chair dake nan aje gefen d’akin. Zamansa akan chair’n kuwa yayi daidai da hango Oum Ayush da yayi ta nufo sashin. Cikin sauri had’i da tsoron kada Oum Ayush d’in taga abunda ke faruwa, ya mik’e tsaye tare da k’arasawa jikin k’ofar, da d’an k’arfi ya daki k’ofar d’akin wanda hakan yasa gaba d’aya ta wangale. K’aran dukan k’ofannasa ne kuma yasa Laylerh da gaba d’aya jikinta ya soma narkewa acikin na Maleek d’in tayi saurin jan jikinta baya, tare da soma k’ok’arin k’wato numfashinta dake fusga da kuma barazanar d’aukewa. Haka ma Maleek k’aran bud’e k’ofarne yasashi d’ago kansa da sauri, idanunsa wanda sukayi ja suka kuma k’ank’ance ya zubawa Fou’ad dake tsaye ajikin k’ofar wanda ya tamke fuska kamar anyi masa mutuwa. Ganin Fou’ad d’inne yasashi lumshe idanunsa tare da kawar da kansa gefe. Laylerh kuwa gaba d’aya jikintane ya d’auki rawa, yayinda ta kasa koda d’ago kai ta kalli Fou’ad d’in, hakanan taji wani irin matsanancin kunya ya kamata, tare kuma da fahimtar cewa sam bata aikata daidai ba. Take kuwa taji wani irin abu maikama da fargaba ya daki zuciyarta. Wanda hakan yasa asanyaye wasu sabin hawaye suka silalo daga cikin idanunta zuwa kan k’uncinta. Daidai lokacin kuwa Oum Ayush ta k’araso da d’an sauri musamman ganin k’ofar d’akin da tayi abud’ene ma yasa hankalinta ya d’an tashi. Ganin Fou’ad da tayine kuma tsaye abakin k’ofar yasa ta d’an fad’ad’a murmushin dake kwance akan fuskarta, cike da kulawa tace. “Fou’ad ashe har ka dawo? Yanzu Abbou Khareem yake cemin wae kaje sayayyan kayan fruits.â€? Murmushi Fou’ad ya d’an k’ak’alo tare da d’an jinjina kansa. “Yanzun nan dawowa na sai naga ashema M.Jay d’in ya farfad’o.â€? Ya fad’i hakan yana me aje ledan fruits d’in dake hannunsa. Baki Oum Ayush ta bud’e daniyar bashi amsa, saidai kuma ganin da tayiwa Laylerh tsaye agefen Maleek d’in sororo yasa tayi shiru, idanu ta zubawa Laylerh’n na d’an sakanni kafun daga bisani ta dawo da kallon ta ga kofin tea d’in dake aje akan gadon Maleek d’in, yayinda shikuwa ya juyawa cikin d’akin baya. Cikin yanayin mamaki Oum Ayush tace. “Laylerh baki bashi tea d’in ba ajiye masa akan gado kikayi?.â€? Laylerh da kanta ke k’asa jin tambayar da Oum Ayush d’in tayi matane yasa tayi saurin girgiza kai, asanyaye cikin muryarta dako fita da kyau batayi tace. “A’a na basa tea d’in amma yace ya k’oshi!â€? Ta k’are maganan cikin hard’ewar murya. Ajiyar zuciya Oum Ayush ta sauk’e tare da maida kallonta ga Maleek d’in, kaman zata ce masa wani abu kuma saita fasa, ahankali ta k’arasa jikin gadon nasa tare dasa hannu ta d’auki kofin tea d’in, da har yanzu zafinsa bai huce ba. “Maleek.â€? Ta k’ira sunansa cikin alaman rashin wasa. Ahankali cikin kuma yanayin salon daya riga yabi jikinsa ya juyo da kansa, tare da zubawa Oum Ayush d’in mayun idanunsa. B’ata fuska Oum Ayush d’in tayi tare da watsa masa harara, cikin kuma yanayin had’e fuska tace. “Ka d’auki tea d’innan kasha tun kafun ranka ya b’aci.â€? Yanayin yanda tayi maganan tana me mik’o masa kofin tea d’inne yasashi d’an lumshe idanunsa, tare kuma dasa hannu ya karb’i kofin tea d’in. Domin kuwa har acikin zuciyarsa yasan bai isa hana kansa sha ko cin abunda Laylerh’n ta had’a da hannunta ba. Ahankali kuwa yakai cup d’in bakinsa, cikin yanayin nutsuwa da kuma kasalan dake damunsa ya shiga sipping tea d’in, kasan cewar har yanzu baigama dawowa cikin nutsuwarsa ba. Oum Ayush kuwa ganin ya fara shan tea d’inne yasa ta dawo da kallonta ga Laylerh wacce har yanzu kanta ke k’asa. Fahimtar kuma da tayi cewar Laylerh’n bata cikin mood mai dad’ine yasa ta d’an tausasa murya asanyaye tace. “Har yanzu hannun naki ne yake miki zafi?â€? Sanin da ita Oum Ayush d’in take ne yasa ta d’an girgiza kanta, alaman “A.a.â€? Batare da tajira abunda Oum Ayush d’in zata kuma cewa ba, ta juya cikin yanayin sanyi ta nufi k’ofar toilet d’in dake cikin d’akin. Ganin haka yasa Oum Ayush girgiza kanta kawae tare da shumfud’a d’aya daga cikin sallayan da tazo dashi ta tada sallah, domin tun awaje ta d’auro alwalanta. Laylerh kuwa tana shiga cikin toilet d’in ta kifa kanta da jikin bango tare dasa hannu ta dafe daidai saitin zuciyarta dake bugawa da k’arfi, asanyaye tasa hannu ta share hawaye masu d’umin da suka zubo mata. Sanin kuma da tayi cewar babu wadataccen lokacine yasa bata wani tsaya b’ata lokaci ba ta d’auro sabuwar alwala, had’e da gyara rufin mayafin dake jikinta. Bud’e murfin kofar toilet d’in tayi ta fito. Hakan kuwa yayi daidai da mik’ewa tsaye da yayi. Da k’arfi ya rumtse idanunsa, tare dasa hannu ya dafe saman mararsa, wanda tsananin ciwon da yake masa yasa shi sakin wani numfashin azaba, saidai kuma kasancewarsa jarumin soldier yasa shi daurewa duk da kuwa zafin ciwon da yakeji. Akaron farko kenan tun faruwar abun da ta d’ago idanunta ta kallesa, saidai kuma ko second biyu batayi tana kallonsa ba tayi saurin sadda kanta k’asa musamman da taga ya nufo inda take. Saura kuwa baifi taku uku ya iso kusa da I taba tayi saurin matsawa gefe, hakanne kuma yabashi daman rab’awa ta gefenta ya bud’e k’ofar toilet d’in ya shige. Jin shigarsa da tayi cikin toilet d’inne kuma yasa ta sauk’e wata b’oyayyar ajiyar zuciya, cikin sauri kuwa ta matsa daga wajen. Tare da d’aukan d’ayan sallayan da yayi saura ta shumfud’a, cikin nutsuwa ta tada sallah. Shikuwa Maleek koda ya shiga cikin toilet d’in, ahankali cikin kuma tafiyarta mai kama da d’ingishi ya k’arasa gaban wani d’an babban mirror dake lik’e saman sink. Fuskarsa kawai ya kalla acikin mirror’n ya d’auke kai. Hannunsa yakai ahankali ya b’alle aninin wandon dake jikinsa, wanda hakanne kuma ya bawa saman mararsa daman bayyana. Idanunsa ya d’an lumshe tare dasa tafin hannunsa ya d’an shafa saman marar tasa wanda anan ne yakejin matsanancin ciwo. Wani abu da yaji yana bin hannunsa ne kuma yasa shi saurin bud’e idanunsa tare da kai dubansa ga saman marar nasa. Abunda ya ganine kuma yasa shi zaro idanunsa waje, yayinda take hankalinsa yayi wani irin mummunan tashi. *(Manage please and please Insha Allah Gobe kafun na tafi skull zan baku update, nima dai na samu na gama littafinnan na huta kuma ku huta😨)* 2/23/21, 7:11 AM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna *Chapter 56* Hannunsa yakai ahankali ya shafa saman marar sa inda yaga jini kwance, d’aya daga cikin yatsar hannunsa da ta dangwalo jinin ya d’ago tare da d’an k’urawa jinin nasa idanu. Akasalance ya d’an lumshe idanunsa tare da sauke wata irin b’oyayyar ajiyar zuciya, tabbas duk da baisan cewa jinin na meye bane, amma yaji hankalinsa ya d’an tashi kad’an, saboda dai yasan baiga ciwo akan marar tasa ba, amma wani abun al’ajabi kuma ga jini, wani tunani kuma daya fad’o ransane yasashi share duk wani abundake zuciyarsa, tissue d’in dake aje agaban sink ya d’auka had’e da goge saman marar tasa, kana kuma yasa ruwa ya wanke wajen. Gaba d’aya jikinsa yabi da kallo, wanda hakanan yakejin wani irin abu duk babu dad’i, ayanzu kam babu abunda yakeson yi face wanka, Dan hakanne kad’ai zaisa yajisa ya k’ara zama normal, duk da cewar toilet d’in da yake cikin nada tsabta sosae saidai bayajin zai iya sakewa acikinsa har yayi wanka. Duk wani sashi na jikinsa da yasan akwae najasa saida ya wanke tas kafun ya d’auro alwala. Ahankali ya bud’e k’ofar toilet d’in ya fito, zuwa lokacin kuwa har su Oum Ayush sun idar da nasu sallah’n. Ganin jikin Maleek d’in d’auke da danshin ruwane yasa Fou’ad dake zaune gane cewar Maleek d’in alwala yayi. Babban ledan daya shigo da ita tun zuwansa na farko ya d’auko tare da bud’ewa ya zaro wani riga da wando, wanda suke sabi k’al k’al, domin musamman ya sayosu awani Big super market saboda Maleek d’in idan ya farfad’o ya samu kayan da zaisa. Mik’a masa kayan Najeeb yayi, shikuwa batare da wani dogon tambaya ba ya amshi kayan tare da juyawa ya koma cikin toilet d’in. Bajimawa kuwa sai gashi ya fito sanye da kayan ajikinsa, wanda suka matuk’ar yi masa kyau, kasancewarsu kuma kalan bak’i shiyasa suka k’ara bayyana hasken fatarsa. Laylerh kuwa da har yanzu take zaune akan sallayan da tayi sallah, kyawawan k’afafunsa ta zubawa ido, ba abundake d’aukar hankalinta agaresa kuma kamar yanda yake taka k’afafunnasa ahankali. Isowarsa kusa da itane kuma yasa tayi saurin lumshe idanunta, tare dajin wani irin bugun zuciya wanda bata tab’a jin irinsa ba. Shikuwa Maleek kaitsaye ta gefenta ya rab’a ya wuce ya d’auki sallayan da Oum Ayush tayi sallah akansa, shumfud’a sallayan yayi tare da fuskantar gabar ya tada sallah. Ganin haka yasa asanyaye tatashi daga zaunen da take tare kuma da nannad’e sallayan da take kai ta ajiye agefe. Daidai lokacin kuwa su Abbou Jaheed suka dawo daga tafiya masallacin da sukayi. Kallon Oum Ayush Abbou Khareem yayi cikin kulawa yace. “Likita yace bazai sallamemu yau ba sai zuwa gobe, saboda haka ni zan kwana da Maleek d’in, ku kuma zuwa yanzu ya kamata ku koma gida, domin dare na k’ara yi.â€? Jin abunda ya fad’a d’inne yasa Oum Ayush ta d’an jinjina kanta, tare da mik’ewa tsaye, domin dama itama harta fara jin bacci, koba don haka bama ya kamata ace sun koma saboda ayanzu tasan duk inda Najeeb yake to yana buk’atar dawowar Laylerh gida, hakanan kuma bazasu tauye masa hakk’insa ba. Fou’ad dake zaune agefe kuwa jin Abbou Khareem yace shi zai kwana a asibitinne yasashi kafewa akan cewar lallai shi zai kwana tare da a Maleek d’in idan yaso su Abbou Khareem d’in dukansu sai su koma gida. Abbou Khareem kam yaso cewa aa amma kuma sai Abbou Jaheed yace ba damuwa abar Fou’ad d’in ya kwana. Haka dai suka tsaida magana akan cewa Fou’ad d’inne zai kwana. Laylerh kuwa tunda taji ance sutafi duk ta k’ara sururucewa, sam hakanan taji batason koda fita daga d’akinne balle ma daga cikin asibitin gaba d’aya, amma kuma sanin da tayi cewar babu yanda zatayine yasa ta gyara rufin mayafin dake jikinta. Asanyaye ta saci kallonsa ta gefen idanunta, domin kuwa har yanzu sallah yakeyi bai idar ba, kasancewar yana ramakon sallan azahar da kuma na la’asar ne da ake binsa, wanda lokacin da akayi su baya cikin hayyacinsa. “Muje ko.â€? Muryar Oum Ayush ta katseta daga d’an guntun tunanin da takeyi. Haka dole batare da ranta ya soba tabi bayan Oum d’in da har ta isa bakin k’ofa suka fice. Koda suka fito compound d’in asibitin kai tsaye wajen da Oum Ayush tayi parking motar ta suka nufa. Asanyaye Laylerh ta bud’e murfin motar ta shiga. Cikin d’an yanayin sauri kuma Oum Ayush taja motar suka tafi. Har sukayi nisa da tafiyan nasu kuwa babu wanda yace da d’an uwansa k’ala, kowannensu da irin abunda yake sak’awa acikin zuciyarsa, yayinda acikin zuciyar Laylerh ya kasance tunanin Maleek ne zallan, Oum Ayush kuwa mamaki da kuma tunanin abunda ya hana Momy zuwa hospital d’in take. Da wannan tunanin nasu ahaka har suka iso gida. Acan asibiti kuwa Koda ya idar da duka sallan da ake binsa bai tashi akan sallayan ba har saida ya sallan Isha. Bayan ya idar da sallanne kuma ya d’auki magungunan da Dr. Mouhammad ya kawo masa yasha, tare da komawa saman gadonsa ya kwanta, domin kuwa wani irin ciwo yakejin jikinsa da mararsa nayi masa, ga kuma wani irin bacci mai k’arfi dake fusgarsa, hakan kuwa yana da nasaba da allurar da Dr. Mouhammad yayi masa d’azu, saboda alluran tanabin jikin mutum ne da sannu saita saka macewar jiki da kuma bacci. Ahankali Fou’ad ya turo k’ofar d’akin ya shigo, dawowansa daga masallaci kenan, yayinda su Abbou Jaheed kuwa suna idar da sallah’n Isha suka wuce gida shida Abbou Khareem. Ganin Maleek d’in da yayi kwance akan gadone yasashi k’arasowa cikin d’akin tare dajan kujera ya zauna akusa da M.Jay d’in wanda yasa hannayensa duka biyu ya dafe mararsa, duk da kuwa cewar idanunsa alumshe suke, amma Fou’ad yasan cewa ba bacci yakeyi ba, domin duk wani kwanton b’aunan Maleek d’in babu wanda baisani ba. Idanu ya zuba masa nad’an wasu sakanni kafun daga bisani ya kawar da kansa gefe, cikin tausasa murya yanda yasan Maleek d’in zai fahimcesa yace. “Bai kamata ace har yanzu kabar zuciyarka taci gaba da son Matarwani ba, Laylerh fa matar wani ce Maleek kuma kasan hakan, kana kasan zunubin dake cikin hakan amma kuma kake aikatawa, meyasa ba zakayi k’ok’arin cireta acikin rayuwarka ba? ko kamanta cewar ba lallaine abunda kakeso shi kake samu ba? Kada kayi tunanin wai don kanason Laylerh watarana dole saika sameta, Tabbas nasan kanajin k’una da kuma radad’in rashinta amma hakan bawai shi yake nufin cewa bazaka rayu idan ba itaba zakayi rayuwa cikin farinciki da inganci Idan har kaso hakan, Dan Allah Captain M.Jay kamanta da Laylerh ka k’yaleta tayi rayuwa da mijinta, saboda ta sanadiyarsa ne zata samu aljannarta, shin tayaya kake tunanin Laylerh zata iyayin zaman aure matuk’ar tana ganinsa akusa da ita? sannan kuma idan kana bibiyarta hakan bazae tab’a yiwuwaba, na tabbata ganin da nayi muku d’azu da ace Mijintane yayi muku da zuwa yanzu labari ya sanja salo, shin kanason Najeeb yafara zargin Laylerh da aikata fasik’anci da aurensa ne? Kasani basai na fad’a maka ba Laylerh yarinyace k’arama duk abunda aka koyar da ita dashi zata tashi, kada ka koyar da Laylerh wannan d’abi’ar Maleek sam kada ka fara.â€? Idanunsa wanda suka rune sukayi ja kaman Jan barkono ya bud’e, tare dajan wani irin dogon numfashi, ahankali ya kamo hannun Fou’ad dake gefensa ya d’aura akan kirjinsa daidai saitin inda zuciyarsa take. Sauk’an hannun Fou’ad akan saitin zuciyar Maleek d’inne kuma yasashi zaro idanunsa waje, cike da mamaki had’i da tsoro yake kallon k’irjin Maleek d’in. Asakamakon wani irin mummunan bugawa da yaji zuciyar Maleek d’in nayi fast fast kaman zata faso k’irjinsa ta fito. “Yin shiru zaifi sauk’i Fou’ad akan kacemin na daina son Laylerh, bakasan ya nakeji ba aduk kwanan duniya idan na tuna cewar Laylerh tana ak’ark’ashin inuwar wani sai naji zuciyata tana k’una kaman ana gasamin ita, Ya nakeji me nakeji babu wanda ya sani Fou’ad saini kad’ai, cire soyayyar dake yawo acikin gangar jiki da jini ba abu bane me sauk’i, nayi imani cewa da soyayyar Laylerh acikin zuciyata zan mutu, so yakan tashi ya k’aura zuwa wani waje na daban amma ba irin soyayyar da nakeyiwa Laylerh ba, wannan soyayyar daban take, soyayyar Ayshnoor tafi gaban kwatancen kowa, ta wuce hasashe Fou’ad, ba kuma zata tab’a misaltuwa ba, halittace da bazata tab’a mutuwa ba, domin kuwa koda babu rai ajikina soyayyar Ayshnoor bazata daina rayuwa ba!!â€? D’an tsagaitawa da maganan nasa yayi, saboda yanda yaji k’irjinsa na rik’ewa, Sam yawan magana ba d’abi’arsa bace, wannan dalilin yasa sanadin maganan da yayi yanzun yaji k’irjinsa ya rik’e. Idanunsa wanda suka cika da ruwan hawaye ya mayar ya lumshe, tare da sakin hannun Fou’ad dake kan k’irjinsa, gyara kwanciyarsa yayi tare da juyawa ya bawa Fou’ad d’in baya. Fou’ad kuwa hawayen da suke kokarin zubowa daga cikin idanunsa ya shanye, asanyaye ya zubawa bayan Maleek d’in idanu. K’warai sosai tsananin soyayyar da Maleek keyiwa Laylerh ke basa mamaki, wacce irin soyayyace wannan da k’arfinta yake neman zarce hankali? shikam Allah Ya sani zuwa yanzu tsoron soyayyar LaylerhMaleek d’in yakeyi, domin kuwa soyayyace Bawae mai hankali ba. Sanin cewa sha’anin su Layerh’n yafi k’arfinsane yasa baisake cewa komae ba, jingina bayansa ajikin kujeran da yake kai yayi tare da lumshe idanunsa. Almost 20minute kenan yanzu da shigowarta cikin d’akin, amma gaba d’aya har yanzu ta kasa daidaita nutsuwarta, Sam batasan me yake damunta ba, amma saidai tayi amanna cewa moment d’inta dashi na d’azune duk ya rikita ta. Domin kuwa har yanzu idan ta tuna da yanda lallausan sajen dake kwance akan fuskarsa ya gogi nata fuskar saitaji tsikar jikinta ya tashi. Idanunta dake bayyana zallan gajiya ta lumshe ahankali tare kuma da bud’esu alokaci guda, kana ta sauk’e wata irin sassanyar ajiyar zuciya, agogon bangon dake sak’ale acikin d’akin ta kalla. 8:30pm daidai da idanunta suka nuna matane yasata mik’ewa tsaye, tare da nufan toilet donyin wanka, saboda asonta sam bataso Najeeb ya dawo gidan ya sameta idanunta biyu. Koda ta shiga cikin toilet d’in kayan dake jikinta ta rage tare da had’awa kanta ruwan wanka mai d’an d’umi a bathtube. Sam bata wani b’ata lokaci awajen wankan nata ba, bayan ta gama wankanne kuma ta fito daga cikin toilet d’in jikinta sanye da bathrobe. Ad’an hanzarce ta tsane ruwan dake jikinta, tare da k’arasawa gaban dressing mirror ta shafa wani body lotion dinta tare da turaren body spray maidad’in k’amshi. Yanayin kuma yanda takejin kanta agajiyene yasa akasalance ta k’arasa gaban makeken drawer d’inta, wani sauk’akk’en doguwar rigar bacci mai kalan light blue ta saka ajikinta wanda gaba d’aya jikinsa ya kasance na net ne, sosai kuwa rigar ta amshi jikinta tare kuma da bayyana zallan kyawunta. Koda ta kalli madubi kuwa ita kanta tasan cewa tayi kyau. Hasken wutan daya cika d’akin ta rage tare da hayewa saman gado ta kwanta. Mintuna kad’an da kwanciyarta kuwa bacci mai nauyi ya d’auketa, duk da cewar rabonta da tasa wani abu abakinta tun safe, amma haka ta gwammacewa kwana da yunwa. Ahankali Najeeb ya turo k’ofar d’akin ya shigo, ganin kuma babu wadataccen haske acikin d’akinne yasashi k’arasawa jikin makunnin wutan ya kunna, take kuwa haske ya mamaye d’akin. Yalwatan haske acikin d’akinne kuma yayi sanadiyar sauk’e idanunsa akanta. Baccinta take cikin kwanciyar hankali yayinda ta dunk’ule duka hannayenta ak’irjinta. Wani irin murmushine ya sub’uce masa sakamakon yanda yaga tayi masa matuk’ar kyau, ahankali ya k’arasa shigowa cikin d’akin, tare da ajiye ledodin dake hannunsa akan bedside. Batare kuma daya yi abunda zai tashetaba ya shiga rage kayan jikinsa, saida ya cire komai sannan ya d’aura towel kaitsaye ya wuce bathroom. Wanka kawae yayi batare kuma daya d’au wani dogon lokaci acikin bathroom d’inba ya fito duk gaba d’aya jikinsa d’auke da danshin ruwa. Zama yayi na musamman a gaban dressing mirror ya kimtsa kansa, bayan ya gamane kuma ya zura wasu simple riga da wando wayanda basuda nauyi. Haka ya nufo kan gadon yana ta zuba k’amshi. Sanin kuma da yayi cewar Laylerh’n bataci abinci bane yasashi soma k’iran sunanta. Acikin magagin bacci kuwa ta amsa masa batare da ta tashi zaune ba, ganin hakanne kuma yasashi d’agota ya zaunar da ita. Hannunsa yasa ya shafa gefen fuskarta, cikin matsanancin so da kuma sha’awarta dake cinsa ko wacce rana yace. “I’m sorry na tasheki ko, nasan bakici abinciba shiyasa, kici idan yaso saiki koma baccin.â€? Fuska ta shagwab’e tare da karyar da wuyanta gefe, cikin yanayinta na bacci da kuma zallan shagwab’a tace. “Nifa nak’oshi.â€? Kansa ya d’an girgiza tare da jawo ledan daya shigo dashi babban robar vanilla ice cream din daya sayo mata ya bud’e tare da d’aura mata roban akan cinyarta. Cikin kulawa yace. “Naji kin k’oshi to amma kisha Ice cream.â€? Jin ya ambaci ice cream ne yasa ta bud’e idanunta, ganin kuma da gaske Ice cream d’inne agabanta yasa ta d’an saki murmushi, batare da ta sake cewa komae ba kuwa ta d’auki robar ice cream d’in ta shiga sha tana wani lumshe idanunta masu yalwar lashes asamansu, sosae kuwa take enjoying shan ice cream d’innata. Shikuwa Najeeb kwalin pizza’n da yayi ordering ya ciro tare da bud’ewa ya soma ci. Time to time yake kallon Laylerh’n da zuwa yanzu Tasha kusan fiye da rabin roban ice cream d’in. Kusan mintuna 20 ya d’auka yana cin abincin saidai kuma jin shiru babu motsin Laylerh’nne yasashi juyowa ya kalli b’angaren da take. Cike da mamaki ya d’an zaro idanunsa sakamakon ganin da yayi cewa Laylerh’n har ta sake komawa bacci, ga hannunta kuwa rik’e da robar ice cream d’in da zuwa yanzu ya kusa zama ruwa dukansa. Yanayin yanda take baccin azaune ne yasashi d’an sakin murmushi, asanyaye yace. “I’m sorry kingaji sosae ko kuma nazo na tasheki.â€? Hannunsa yasa ya dauke robar ice cream d’in tare da gyara mata kwanciyan da tayi. Sauran pizza d’in dayaci ya d’auka yakai kitchine. Bayan ya dawone kuma ya rage musu hasken wuta, had’e da hayewa saman gadon ya kwanta agefen Laylerh, tattausan blanket ya rufa musu ajikinsu, ahankali kuma ya lumshe idanunsa yana me shak’an daddad’an k’amshin dake fita ajikinta, duk da cewar yaud’in baiyi kusa da ita sosae ba, amma kuma hakan baihanashi jiyo sassanyan k’amshin dake fita ajikinta ba. Hakika yana matuk’ar buk’atar ta, yana tsananin son yajita acikin jikinsa, yanason ya Santa acikakkiyar y’a mace, amma har yau yakasa samun daman hakan, saudayawa yakan tambayi kansa cewar. “Shin meyasa har yau ya kasa kusantar Laylerh’n duk da cewar bataso?.â€? Saidai bashi da amsar dayake bawa kansa, haka dai yabar abun acikin zuciyarsa. Da tunani kala kala bacci b’arawo ya d’aukesa. Washegari. Tun tashinta yau d’in ta gyara komai nata, duk da cewar babu wani abu na part d’in nata dake da datti amma haka ta gyara komae. Yayinda acikin zuciyarta kuwa Allah Allah Take Oum Ayush ta k’irata tace tazo suje asibiti, hakanne kuwa yasa tayi wanka ta kuma shirya kanta cikin riga da sket na atamfa wanda sukayi mata kyau sosae. Saidai abunda batasani ba kuwa shine tuni har Oum Ayush ta bada breakfast ankai asibitin domin tunda sassafe Abbou Khareem da kuma Abbou Jaheed suka tafi asibitin kasancewar Dr.Mouhammad yace yau zai bawa Maleek d’in sallama. B’angaren Najeeb kuwa yau da sassape ya tafi office kasancewar yana da wani aiki mai mahimmanci dazai gudanar, shiyasa koda Laylerh’n ta tashima bata sashi acikin idanunta ba, saidai yabar mata sak’on breakfast. Ganin da tayi shiru Oum Ayush bata k’irata bane yasa kaitsaye ta wuce sashin Oum Ayush d’in, koda taje afalo ta samu Oum d’in. Ganintane yasa Oum Ayush fad’ad’a murmushin dake kan fuskarta cikin kulawa tace. “Laylerh yana ganki kodae su Maleek d’in sun isone?â€? Kanta ta girgiza ahankali cikin sanyin murya tace. “Aa amma Oum Ayush baza muje asibitin bane?â€? “Eh ae zuwa asibiti ya k’are mana saboda anjima kad’an za’a sallamo Maleek d’in, Dr. yace babu wata damuwa kuma kinsan halin Maleek baicika son takuraba kinga kuma zama a asibiti koya yake akwae ta kura acikinsa.â€? Kanta ta d’an rausayar gefe tare da neman waje ta zauna acikin falon, hakanan duk sai taji wani iri domin kuwa burinta ayanzu shine taga Maleek d’in. Acan asibiti kuwa Dr. Mouhammad ne yashigo d’akin shida sauran wasu doctors suka sakeyiwa Maleek wasu gwaje gwaje bayan sun kammala gwaje gwajen nasune kuma suka rubuta masa irin magungunan da zaisha dama ta kardar sallamansa, duk da cewar akwae buk’atar yake zuwa duk bayan 1 weak suna duba lafiyar mararsa. Godiya sosai su Abbou Jaheed sukayiwa doctors d’in, tare da d’aukan duk wani abubuwan da suka zo dashi suka kai mota. Koda sukazo tafiya d’in kuwa har bakin mota Dr.Mouhammad ya rakosu sukayi sallama ta mutumci, tare da shaidawa Maleek cewar lallai yake zuwa suna dubashi. Shidai kam da kai kawae yake amsawa Dr. d’in domin kuwa sam bayason yawan magana. Koda suka kama hanyar dawowa gida jingina bayansa da jikin kujerar motar yayi tare da lumshe tsumammun idanunsa. Bai bud’e idanun nasaba kuwa har saida suka iso compound d’in gidan nasu. Ahankali ya bud’e murfin motar ya fito, wanda kuwa hakan yayi daidai da shigowar motar Alhaji Farouk cikin compound d’in gidan. Da Mamaki Ya shiga kallon motar, yayinda Abbou Jaheed kuwa yaje ya taro abokinnasa cikin karramawa. Juyawa Maleek d’in yayi danufin tafiya sashinsa, amma saidai jin Abbou Jaheed na cewa dukansu su wuce falonsa ne yasashi da katawa badon ransa ya soba kuma haka yabi bayan su Abbou Jahedd d’in. Koda suka k’arasa falon Abbou Jaheed d’in mai yanayi da aljannar duniya, zama kowannensu yayi. Nanfa Abbou Jaheed da kuma Alhaji Farouk suka shiga sabon gaisawa. For the second time kenan dayaji gabansa na d’an fad’uwa, wanda kuma tun acikin asibiti yakejin hakan, baikuma san dalili ba, ahankali ya shiga addu’a da kuma fatan cewa koma meyene yazo masa cikin sauk’i. Shigowar Oum Ayush da kuma Laylerh dake biye da ita abayane yasashi d’an lumshe idanunsa, domin kuwa duk da bai d’aga idanunsa ya kalleta ba amma k’amshinta ya isar masa. Laylerh kuwa da k’irjinta keta faman dukan uku uku ahankali ta nemi waje anan k’asan sofa ta zauna, Sam batasan meyasa tunda Oum Ayush ta fad’a mata cewar Abbou Jaheed na nemansu ba, taji gabanta na fad’uwa domin kuwa tasan cewa Abbou Jaheed baya neman mutum haka kawae. Ae kuwa zuciyarta bata k’ara tsinkewa ba saida taga Najeeb ya shigo cikin falon, hakanan taji wani irin tsoro ya lullub’eta, take kuwa zuciyarta ta raya mata cewa. “Kodae Najeeb ne ya kawo k’aranta akan cewa bata basa hakk’insaâ€? Tabbas hakan zaiyiwu, amatuk’ar tsorace ta hade jikinta waje d’aya tare da sunkuyar da kanta da sauri. Abbou Jaheed kuwa ganin dukansu sun ballara acikin falonne yasashi gyara zamansa tare da duban kowannensu, lokaci d’aya kuma yanayinsa ya sanja, ahankali cikin karyewar zuciya da kuma sanyin yanayi yace. “Tabbas ban had’aku awajennan don maganan da zanyi ya zamo tashin hankali agareku ba, K’warai nasan cewa zakuji babu dad’i kamar yanda nima naji kuma har I yanzu nake kan ji. Lallaine kuma Tabbas kamar yanda dukkaninku kukasani K’addara takan iya zuwawa bawa tako wanni siga, haka kuma Allah Yakan jarraba bawansa ta hanyar da duk yaso, da bara ko wayo kuma bazaisa ka kub’ucewa hakan ba. Sannan kuma inason kowannenku yasan cewar zan fad’i maganan nan a gabansa ne saboda matsayi da kuma cancantar cewa ya kamata yasani, gaba d’ayanku duka k’ok’arin zama y’an Uwa muke, saboda haka nayi imani cewa matsalar d’aya daga cikinmu na mune dukan mu.â€? D’an jinkirtawa da maganan nasa yayi sakamakon wasu irin hawaye da kuma raunin da yaji yazo masa, domin kuwa baisan tayayane zasu fuskanci maganar tasa ba, yaya zasu d’auketa Allah Kad’ai masani, babban abun ji da tambayan kuma shine Maleek da k’addaran ta zama akansa ne. Ahankali ya d’ago kansa ya kalli Maleek d’in wanda kansa ke k’asa, tsananin tausayinsa ne ya rufesa wanda har hakan yasa ya Kasa controlling kansa, harsaida wasu guntun hawaye suka sauk’a akan fuskarsa. Cikin sanyin muryar dake bayyana zallan damuwarsa ya k’ira sunan Maleek d’in. Maleek dake zaune kuwa jin yanayin yanda Abbou Jaheed d’in ya k’ira sunansa ne yasashi gane cewar Lallai akwae matsala. Ahankali ya d’ago kansa ya kalli Mahaifinnasa. Kai Abbou Jaheed ya d’an girgiza saboda girman abunda bakinsa ke kokarin fad’a, yasan cewa Lallai ba abu mai dad’ine zai fito daga bakinsa ba, amma to yaya zaiyi idan bai fad’i wannan matsalar a gaban kowa ba, meye amfanin b’oyewa? hakan zai zama kaman cutarwa ne. Kansa ya d’an sunkuyar domin babu yanda za’a yi ya fuskanci d’annasa ya fad’a masa magana marar dad’i kaman wannan. Cikin dauriya da kuma son ganar da Maleek d’in yace. “Hakika Maleek nasan amatsayinka na Musulmi kayarda da k’addara mai kyau ko akasin haka, sannan kuma nasan kayi imani cewa Allah Yakan iya jarraba bawa takowanne siga, lallai tabbas kai kuma kalan naka Jarrabawar ahaka tazo, saidai nayi imani cewa amincewa da kuma yarda da hakan ba k’aramin karamci zai jawo maka awajen Ubangijin kaba, kayarda cewa komae Allah Ne Ya tsarashi!!â€? Gaba d’aya falon shiru ya d’auka yayinda dukkaninsu suka zubawa Abbou Jaheed idanu. Kowannensu buri yake yaji abunda Abboun Zai fad’a, amma banda Abbou Khareem dayasan komae akan zancen. Kusan mintuna 5 aka share gaba d’aya ko ina ya d’auki shiru, rumtse idanu Abbou Jaheed yayi kana asanyaye yace. “Kayi hak’uri Maleek asanadiyar accident d’in da ka samu Dr. ya shaidamin cewa kasa mu matsala amararka wanda hakan yasa ba zaka tab’a haihuwa ba!!!â€? *22/2/2021* *10:30 am* 2/24/21, 8:11 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna *Not editing* #Life and Destiny *Chapter 57* Amatuk’ar Razane gaba d’aya mutanen dake cikin babban katafaren parlor’n suka d’ago kai dukansu suka kalli Abbou Jaheed. Domin kuwa maganar da ta fito daga bakinsa ba k’aramin rugurguza musu k’wak’walwa tayi ba, har hakan yakai ga kowannensu ya shiga kokonton cewa kodae baiji abunda Abbou Jaheed d’in ya fad’a da kyau bane. Abbou Khareem kuwa da yasan kwanan zancen kansa kawae ya sunkuyar tare da soma ambaton sunan Allah acikin zuciyarsa. Idanun Maleek wanda suka matuk’ar k’ank’ance lokaci d’aya kuma sukayi wani irin ja mai ban tsoro ya zubawa Abbou Jaheed d’in, yayinda kuma sannu ahankali kalaman da Abbou Jaheed d’in ya fad’a suka shiga yawo acikin brain d’insa filla filla, tamkar dae wanda aka bud’e aka watsasu. Take kuwa wani irin matsanancin zufa ya shiga ketowa ta kowani sashi na jikinsa, b’angaren zuciyarsa kuwa bugawa take da k’arfin gaske tamkar zata faso kirjinsa ta fito waje. Lallai hak’ik’a akaro na biyu kunnuwansa sunjiye masa magana mafi muni da kuma girma, maganan da tasa shi zama tamkar wani statue, maganar da ta tsayar da duk wani tunani da kuma gudun jininsa. Ba kuma iya shi d’in kawae ba hatta Laylerh dake zaune ak’asa saida gaba d’aya ilahirin jikinta ya d’auki rawa, tare da shiga cikin wani k’aton tashin hankali, duk da kuwa tafara tunanin cewa kunnuwanta basu jiye mata komae adaidai ba. Alhaji Farouk, Oum Ayush, Fou’ad harma da Najeeb wanda ke zaune ad’an nesa da Laylerh kad’an. Kalmar. “Innalillahi wa inna Ilaihirraju’un!!â€? Kawae suke furtawa, domin kuwa ba kad’anba maganan ta tada musu da hankali, wanda har hakan yasa suka kasa furta komae bayan salatin da sukeyi. Abbou Jaheed kuwa akaron farko kenan bayan yayi maganan ya d’ago kansa ya kalli Maleek daya tsura masa jajayen idanunsa baya ko k’yaftawa. Wani irin rauni da kuma matsanancin tausayin d’annasa ne ya cika masa zuciya, wanda kuma har ya kaisa ga kasa jurewa. Ahankali ya tashi tsaye, cikin yanayin sanyi da kuma karyewar zuciyar daya samu kansa aciki ya k’araso inda d’ansa Maleek d’in ke zaune. Inda su Abbou Khareem suka rakashi da ido. Asanyaye ya zauna akan kujeran da Maleek d’in ke zaune, tare dasa hannunsa ahankali ya dafa kafad’an Maleek wanda zaman Abbou Jaheed d’in akusa dashi yasashi rumtse idanunsa. “Kayi hak’uri Maleek Tabbas kowani bawa da irin yanda Allah Yake jarabtansa, babu kuma wanda ya isa ya tsallakewa k’addararsa, tabbas ka had’u da k’addarori masu girman gaske tun daga k’uruciyarka har zuwa yanzu, damuwa sunyiwa rayuwarka k’awanya, yayinda kuma rashin samun fata da muradi ke sake bibiyarka akoda yaushe, amma hakan ba shine ke nuna cewar baka da farinciki kwata kwata arayuwarka ba, sannan kuma bashi yake nuna cewa Allah Baya sonka ba.â€? D’an numfasawa Abbou Jaheed d’in yayi tare da zaro wani farin handkerchief daga cikin aljihunsa ya share d’an guntun k’wallan daya cika idanunsa. Still asanyaye Abbou Jaheed d’in yace. “Tabbas nasan kasan cewa Allah Baya tab’a d’aurawa bawansa abunda bazai iyaba, Ina kuma fata da ka karb’i wannan jararrabawar Insha Allah watarana zakayi nasara, watarana lallai zakayi dariya Maleek, komai yakan faru sannan kuma yakan wuce har abada kaman bai tab’a faruwa ba, bakowa ke samun abunda yake soba, sannan kuma bakomai Allah ke baka dan kana tsananin soba, wani lokaci musanya maka yake, ya toshe wani ya kuma baka wani, hak’ik’a nasan zakaji k’unci da kuma ciwo acikin zuciyarka, amma hak’uri da fawwalawa Allah komae shi yafi, rashin haihuwa abune me tsananin ciwo da kuma k’unci, amma hakan Bawae yana nufin takura kai da yawan damuwa bane, Dan Allah Maleek kada kabar hakan ya zamo silar k’unci da kuma bak’inciki arayuwarka, ko ba aje ko inaba kayi dubi ga Abboun ka Khareem da kuma matarsa Oum Ayush, wanda tunda suke arayuwarsu basu tab’a haihuwa ba, sama da shekara 20 kenan yanzu amma kuma ahaka suke rayuwarsu, duk da cewar kuma sunajin ciwon abun acikin ransu amma hakan baisa sun tauye hakk’in farincikinsu ba, babu d’aya daga cikinsu daya daina murmushi ko dariya asanadiyar hakan, saboda sunyi imani cewa Allah Shike bayarwa shi kuma ke hanawa aduk lokacin da yaso, saboda haka kaima ka d’auki k’addararka kasa sanyi da salama acikin zuciyarka watarana Insha Allahu zakaga nasara da riban hakan.â€? Again sake tsagaitawa da maganan nasa yayi tare da d’an numfasawa ahankali ya d’ago kai ya kalli Alhaji Farouk da duk wani tashin hankali da kuma tausayin Maleek d’in ya bayyana k’arara akan fuskarsa. Idanu Abbou Jaheed d’in ya d’an lumshe kana asanyaye yace. “Kayi hak’uri dajin kalamaina adaidai wannan lokacin Alhaji Farouk, domin dama na gayyatokane dan kasan halin da ake ciki, domin koba komae kai ubane agaresa, sannan kuma matsayin suruki kake dashi agaresa, kaine mutumin da yake shirin basa auren kafun wannan mummunan k’addaran ta shigo rayuwarsa, K’warai nasan jin wannan maganan zaisa kaji babu dad’i acikin zuciyarka, sannan zai kuma iya sawa kasanja ra’ayi akan tunaninka na baya, duk da cewar kuwa lokaci ya k’arato sosai, amma kuma babu yanda muka iya, a irin wannan al’amarin ba ayin dole ba kuma acutarwa, saboda haka kana da y’ancin da zaka yanke ko wani irin hukuncine, zakuma ka iyayin shawara da iyalanka da kuma ita kanta yarinyar, domin abune me matuk’ar ciwo atauye mata hakk’inta mai girma irin wannan...â€? Yanayin yanda Abbou Jaheed d’in ya k’are maganar cikin sanyin muryane yasa Alhaji Farouk yin shiru tare da sunkuyar da kansa k’asa, gumine kawae ke tsatstsafo masa saboda gaba d’aya ya samu kansa cikin tashin hankali. Wasu irin hawaye masu matuk’ar zafi da kuma k’unane suka sauk’o daga cikin idanunta zuwa kan k’uncinta, saboda tsananin yawansu ne kuma yasa har suka soma sauk’a akan k’irjinta. Wani irin matsanancin juyawa taji kanta nayi, yayinda gaba d’aya duk wani tunaninta ya tsaya cak. Abu d’aya kawae brain d’inta ke nanata mata cewar. “Yah M.Jay d’inta bazai tab’a haihuwa ba, k’wayoyin haihuwarsa sun samu matsala.â€? Wannan tunanin kuwa shi yake k’ara mata jin jiri da kuma juyawar da kanta keyi. Da k’yar ta iya motsa y’an k’ananan labb’anta, cikin kuma wani irin fusgan numfashi ta soma ambaton sunan Allah acikin zuciyarta. Domin ta shiga tashin hankali maitsanani. Tambayar kanta take. “Shin wannan wacce irin k’addarace? wace irin jarrabawace haka mai tsananin zafi? tayaya Maleek zai iya jure duka way’annan k’uncin rayuwar? meyasa k’addara ke wasa da rayuwarsu? sai yaushene zasu samu nutsuwa da kuma farinciki arayuwarsu? yaushe k’addara zata barsu suyi dariya ita da d’an uwannata har hak’waransu su bayyana kowa ya gani?.â€? “Lallai tabbas Laylerh babu wannan ranan, domin kuwa munanan k’addara sun riga sunyiwa rayuwarku k’awanya!â€? Wani sashi na zuciyarta ya fad’a mata hakan. Kanta ta d’an soma girgizawa ahankali, domin kuwa bazata iya jure abunda takeji acikin zuciyarta ba, Tabbas so take tayi kuka sosai, kuka irin wanda zai rage mata koda kaso d’aya daga cikin d’ari na k’uncin dake damun rayuwarta ne. Ahankali ta had’e k’afafunta tare da cusa kanta atsakankanin cinyoyinta, batare da ta iya controling kanta da rauninta ba kuwa ta fashe da wani irin kuka mai tsananin tab’a zuciyar mai saurare. Oum Ayush dake zaune akusa da Laylerh’n itama hawayene suka silalo daga cikin idanunta, natsananin tausayin Maleek da kuma su kansu ita da mijinta, domin kuwa tasan zafi da ciwon dake cikin rashin haihuwa, abune da iya juresa keda matuk’ar wahala, musamman ga Namiji matashi mai jini ajiki kamar Maleek, wanda ayanzune ya kamata ace rayuwarsa na tsaka dayi masa dad’i, amma kuma sab’anin hakan sai ya zama k’unci da damuwa ne akewaye dashi. B’angaren Fou’ad kuwa tuni hawaye sun fito daga cikin idanunsa, dama shi akoda yaushe me raunine, Jin matsalar da abokinnasa ya samu ne kuma ya k’ara jaddada rauninsa, tausayin Maleek d’inne kuma ya cika zuciyarsa. Najeeb kuwa hannayensa duka biyu yasa ya tallafi hab’arsa tare da aje idanunsa akan had’add’en carpet d’in dake malale atsakiyar d’akin, sosai jin matsalan da Maleek d’in ya samu ya sashi acikin shock, akaron farko kuma kenan da yaji tausayin Maleek d’in, tare dajin wani irin abu na musamman acikin zuciyarsa. Yanayin yanda falon yayi shirune kuma yasa dukansu suke iya jiyo gunjin kukan Laylerh dake tashi k’asa k’asa, kasancewar ta b’oye kanta atsakankanun cinyoyinta. Tabbas acikin irin wannan yanayin dukansu babu wani mai iya rarrashinta domin kowannensu da abunda yakeji acikin zuciyarsa. Hannayensa dake adunk’ule kusan sama da mintuna 15 ya ware, ahankali kuwa ya shiga bud’e k’ank’antattun idanunsa da suka sake rikid’ewa, kana kuma suka bayyana abubuwa da yawa acikinsu. Lallai tabbas ruwan hawayene kwance acikin idanunnasa wanda kuma har abada bayajin zai barsu su gangaro zuwa kan fuskarsa, hak’ik’a shikansa ayanzu bai isa fassarawa kansa gaskiyar abunda yakeji ba, domin kuwa abune da yake da tsananin girma da kuma ciwo. Saidai kuma akan meyasa zai k’untatawa kansa? shin baiyarda da cewar Allah shike tsara komai bane? shine kuma ya tsara masa hakan, shiya tsara masa way’annan k’addarorin acikin rayuwarsa, yasani kuma cewa kin karb’an k’addararsa butulcewa ne, ba kuma ya fatan koda sau d’ayane na rayuwarsa ya butulcewa mahaliccinsa daya bashi ido biyu, kafafu biyu, ya bashi baki da hanci, Uwa uba rai da numfashi, wanda suke manya manyan rahamomi, idan bai gode akan wannan ba kuwa To bai cancanci yayi bak’inciki akan sabuwar k’addaran da tasameshi ba, saboda yayi imani aduniya idan Allah Zai hanaka komai ya baka rai,numfashi,lafiya, ji da gani, da kuma tafiya, to koya hanaka sauran abubuwa ba abun d’aga hankali bane, hakan ba kuma yana nufin cewa baya sonka bane, Tabbas shikam ya amincewa k’addararsa ya kuma yarda cewa zai rayu da ita, zai karb’eta hannu bibbiyu, ba kuma zai tab’a yiwa Allah K’orafi akan hakan ba. Maida idanunsa yayi ya lumshesu ahankali, tare kuma da soma ambaton sunan Allah, saidai kuma har acikin zuciyarsa a yanzun babu abundake azabtar da ruhinsa kamar sautin kukan Laylerh da yakeji, wanda yake hautsuna duk wani tunaninsa, Sam ko kad’anne bayason kukannata, saboda yana matuk’ar tab’a masa zuciya. Ganin kuma yanda Maleek d’in ke motsa labb’an bakinsa ne, yasa Abbou Jaheed dake gefensa tsura masa ido cike da matsanancin tausayawa, kasancewarsa kuma uba mahaifi agaresa yasa take ya fahimci cewar Maleek d’in yayi imani ya kuma amincewa sabuwar k’addaran da ta sameshi. Hakanan Abbou Jaheed yaji zuciyarsa tayi wani irin sanyi, wanda har hakan ya bashi k’arfin guiwar dawo da kallonsa ga Laylerh dake kuka. Cikin sanyin murya da kuma tausasawa yace. “Najeeb kama hannun Laylerh kutafi can sashinku watak’ila zatayi shiru idan ka rarrasheta.â€? Jin abunda Abbou Jaheed d’in ya fad’ane kuma yasa Najeeb mik’ewa anutse ya k’araso inda Laylerh’n ke zaune. Cikin sanyin murya da kuma son lallab’ata yace. “Please Laylerh stop crying ki tashi mutafi kinji, ai dama Maleek ne kuma ya dawo, sannan zai samu sauk’i Insha Allah.â€? Ya k’are maganar yana me k’ok’arin kama shoulders d’inta ya mik’ar da ita tsaye. Saidai kuma yanayin yanda tatafi suuu zata fad’ine yasashi saurin kamo hannunta, ahankali ya rab’a ta bayan Oum Ayush yana rik’e da hannun Laylerh suka nufi hanyar fita daga cikin falon. Laylerh kuwa sam ta kasa koda d’aga idanunta ta kalli M.Jay d’inne, saboda wani irin tsananin tausayinsa da takeyi, wanda tayi imani sa kasa acikin idanunta ayanzu daidai yake da faruwar komae. Haka dai Najeeb yaja hannunta batare kuma da tana cikin cikakkiyar nutsuwarta ba suka fice daga cikin falon, yayinda binsa kawai take don yana rik’e da ita, amma ko ganin gabanta batayi saboda yanda hawaye ke tururuwan fitowa daga cikin idanunta. Fitan su Laylerh’n acikin falonne yasa Alhaji Farouk da gaba d’aya jikinsa yayi sanyi shima ya mik’e, asanyaye cikin kuma rauni ya kalli Abbou Jaheed. D’an gyaran murya yayi tare da zura hannayensa acikin aljihun rigar jumper’n dake jikinsa. Cikin yanayin maganan dayasan idan yayita su Abbou Jaheed d’in zasu gamsu yace. “Zan wuce gida Alhaji Jaheed, domin wannan maganace da ta cancaci kowannensu ya sani, sannan kuma wannan k’addarar da ta sauk’a akan Maleek tana iya sauk’a akan kowa, babu wanda yafi k’arfinta, idan tanine kuma akan wannan bazae sa na fasa bawa Maleek auren Munnira kamar yanda nayi niya ba, domin kuwa koba komae Maleek matsayin d’a yake awajena, saidai kuma amma bazanyi gaban kaina ba, saboda a irin wannan yanayin yarinya da kuma mahaifiyarta suna da hakk’i, wanda ya kamata ace ambasu dama sun fad’i ra’ayinsu, matuk’ar sun amince da auren ahaka tofa Insha Allahu Za’ayisa babu fashi, domin haihuwa Allah Ne maikawowa aduk alokacin da yaso, domin koda likitotin duniya ne suka taru akan mutum suka kuma shaida cewar har abada bazae tab’a haihuwa ba, idan Allah Yasa yana da rabo, tofa komai daren dad’ewa sai Allah ya bashi.â€? Kai Abbou Jaheed ya jinjina cike da gamsuwa yace. “Insha Allah.â€? Mik’ewa tsaye sukayi dukansu shida Abbou Khareem tare dayiwa Alhaji Farouk d’in godiya sosai, kana suka rufa masa baya donyi masa rakiya, hakan yasa falon yayi saura daga Maleek, sai Oum Ayush da kuma Fou’ad wanda yayi jigum. Momy dake b’oye ajikin labule sama da yawan minutes d’in da suka kwashe suna magana, ganin su Abbou Jaheed zasu fitane yasa tayi saurin b’uya, tare kuma da sauk’e wata ajiyar zuciya mai k’arfi, yayinda takejin wani irin matsanancin farinciki na ratsa zuciya da gangar jikinta, lallai yau taji abunda yasata farinciki ba d’an kad’an ba. Abbou Jaheed yak’i k’iranta saboda fushin da yakeyi da ita, tun jiya akan bataje ta duba Maleek a asibiti ba, amma kuma gashi hakan bai hanata sanin matsalar da Maleek d’in ya gamu da ita ba. Wani irin murmushi tayi tare da lumshe idanunta cike dajin dad’i tace. “Maleek ya samu matsala bazae tab’a haihuwa ba, shikenan ya zama fankon banza, Ya Allah Nagode ma da kakawomin cikar burina asauk’ak’e batare da nasha wahala ba, ayanzu Idan nakawar da Maleek da Laylerh shikenan babu wani mai iko da tarin dukiyar nan saini kad’ai, hak’ik’a duniya zatamin dad’i sosae!â€? Tak’are maganar cikin matsanancin farincikin dake cin zuciyarta, gudun kuma kada su Abbou Jaheed d’in su dawo su isketa awajenne yasa cikin sauri ta juya ta nufi b’angaren ta, zuciyarta fara tas. Acan cikin falon Abbou Jaheed d’in kuwa Oum Ayush ne tataso daga inda take zaune, asanyaye ta k’araso inda Maleek d’in ke zaune, wanda kuma har zuwa yanzu idanunsa alumshe suke, still kuma labb’an bakinsa suna d’an motsawa. Matsanancin tausayinsa daya kamata ne yasa ta d’aura hannunta akan kafad’ansa. “MALEEK!â€? Ta k’ira sunansa cikin sanyin murya. Jin muryar Oum Ayush d’in acikin kunnuwansa ne kuma yasashi d’an bud’e idanunsa, ahankali ya sauk’e ganinsa akan fuskarta, saidai kuma bai iya amsa mata ba, saidai idanu daya zuba mata kawae. Hakanne kuwa yasa take idanunta suka cika da k’wallan tausayinsa, still kuma cikin murya mai rauni tace. “Nasan mekakeji acikin zuciyarka Maleek, domin nima na d’and’ani wannan d’acin kuma har yanzu Ina kan d’and’ana, amma hak’uri da fawwalawa Allah yafi dukkan wani koke koke da k’unci, kayi hak’uri kaji Insha Allah Allah Yana tare dakai!!â€? Ta k’are maganar cikin son k’arfafa masa guiwa yanda zaiji sanyi acikin zuciyarsa. Kansa ya d’an jinjina, ga mamakinta kuma sai taga wani sihittaccen murmushi ya bayyana akan kyakkyawar fuskarsa, cikin dauriya da kuma shanye damuwarsa yace. “Na aminta cewa komae muk’addari ne daga Allah Oum Ayush.â€? Maida idanunsa yayi ya lumshe tare da fesar da wani sassanyan numfashi. Hakan kuwa shiyasa Oum Ayush ta kasa hak’uri bisa dole saida ta fashe da kuka. Jin sautin kukan Oum Ayush d’inne kuma yasa shi saurin bud’e idanunsa, ahankali ya kamo hannayenta tare da girgiza mata kai, domin kuwa har cikin zuciyarsa yakejinta kamar mahaifiyarsa, ahankali ya d’an matso kusa da ita, cikin sanyi da kuma son samawa kansa nutsuwa ya d’aura kansa bisa cinyarta, tare da maida idanunsa ya lumshe. Hakanne kuwa yasa Oum Ayush d’in tayi saurin tsaida kukanta, tare dasa hannunta ahankali ta shiga shafa tarin suman kansa, wanda yasha aski irin na turawa, wai ahakan an aske amma kuma kamar ba’a aske ba. Idanu Fou’ad ya zuba musu yana mejin tsananin tausayinsu. *Najeeb.* Bud’e k’ofar d’akin yayi ahankali tare dajan hannunta suka shiga ciki, anan kan luntsumemen bed d’insu ya zaunar da ita, tare kuma da zama agefenta. Ahankali ya kamo hannunta, cikin kuma sanyin murya me had’e da ban baki yace. “Har abada kuka baya tab’a maganin damuwa Laylerh, kiyi hakuri ki daina kuka kinji!â€? Kai ta shiga girgizawa tare da juyowa ahankai ta fuskancesa, cikin sheshshek’an kukannata ne kuma murya na shaking tace. “Tayaya zan daina kuka Yah Najeeb? tayaya zuciyata zatayi sanyi? Wannan wacce irin k’addarace haka da take wasa da rayuwar d’an uwana? hak’ik’a nasan cewar ni yarinyace amma kuma hakan bashi zaisa na kasajin zafi akan duk wani abu daya samu Yah M.Jay ba, ya yakeji? meyakeji? shi kad’aine ya sani, amma kuma bashi kad’ai yakejin zafin ba, hardani zafin yana k’ona zuciyata!â€? Tsagaitawa tayi tare da rumtse idanunta wanda suke fitar da zafafan k’walla. Duk da kuwa tana da abun cewa amma hakanan taji bakinta yayi mata nauyi, bisa dole ta sa tafukan hannayenta ta rufe fuskarta. Najeeb kuwa mik’ewa tsaye yayi tare da takawa ahankali ya k’arasa gaban dressing mirror tare da tsayawa ya k’urawa mirror d’in idanu yana me kallon kansa aciki, yayinda wani sashi na zuciyarsa ke ci gaba da sak’a masa abubuwa masu yawa, wanda batun yauba zuciyartasa take yawan sak’amasa hakan. Wanda ayanzu yayi imani cewa acikin biyu za’a yi d’aya. B’angaren Alhaji Farouk kuwa zuciyarsa cike da tarin tunani kala kala haka ya nufo gidansa, bakinsa d’auke da al’amari mai girma wanda baisan taya iyalannasa zasu fahimci maganar ba. Wanda yasan dolene ma acikin biyu za’a yi d’aya ko fahimta ko kuma rashinsa, haka amincewa ko kuma akasinsa. K’warae yasan cewa rashin haihuwa abune me girman gaske, kuma dama ana aurene dan a hayayyafa, asamu abunda za’a yi alfahari dashi anan gaba. Shin tayaya matarsa BUZUWA da kuma MUNNIRA zasu d’auki wannan zancen? Idan son da y’arsa Munnira keyiwa Maleek tana da yawa hakan yasa ta amince, shin mahaifiyarta zata amince? Munnira ita kad’aice y’a agaresu bayan ita babu wata, dole ne kuma zasu so ganin jika daga gareta, domin idan ba awajenta d’inba basa saran ganin jika daga wajen kowa, aurenta da Maleek kuwa yana nufin cewa har abada kenan bazasu tab’a samun jika ta wajenta ba. “Anya kuwa koda amincewarta aura mata Maleek bazai zamo cutarwa agareta ba??â€? Yayiwa kansa tambayar, kana abayyane yace abune me matuk’ar wahala. Daidai lokacin kuwa ya shigo cikin falon matarsa wato Buzuwa dan sanar da ita dukkan halin da ake ciki. *24/February/2021* *7:52 pm* 2/26/21, 8:07 AM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna *Not editing* *Chapter 58* Gaba d’ayansu zaune suke acikin falon daga Buzuwa har Munnira wacce ke zaune akan sofa tana ta shirye shiryen event d’in da zasu yi yau ita da k’awayenta na Bride To Be. Ganin yanda Alhaji Farouk d’in ya shigo cikin falon duk gaba d’aya jikinsa asanyaye ne yasa Buzuwa k’ura masa ido cikin yanayin mamaki kuma tace. “Alhaji lafiya kuwa naganka duk jikinka asanyaye, meke faruwa?.â€? Sauk’akk’ar ajiyar zuciya ya sauk’e tare da neman waje anan kusa da ita ya zauna. Kallon Munnira dake ta faman izurin gabanta yayi, kana cikin sanyi ya k’ira sunanta wanda hakanne kuma yasa bisa dole ta tsaida abunda takeyi d’in tare da d’agowa ta kalli mahaifinnata. Buzuwa kuwa idanu ta zuba masa cike da mamakin ganin sabon yanayinsa domin kuwa tasan kafun fitansa ya sanar da ita cewar gidan Alhaji Jaheed zaije, fuskarsa kuma dauke da fari’a ya fita sab’anin yanzu da damuwa ta maye gurbin fari’ar. “Wai meke faruwane Alhaji kodae wani abune na daban ya samu Maleek d’in?.â€? Tayi masa duka tambayoyin ta hanyar cigaba da tsura masa ido. Asanyaye cikin kuma taraddadin yanda zasu d’auki abun ya d’an jinjina masu kai, kana cikin nutsuwa yace. “Tabbas wata matsala ta kunno kai wacce bamusan tayayane zamu maganceta ba, ban kuma san wani ba hagon fahimta zakuyi wa maganar ba.â€? Shiru yayi tare da kallonsu duka biyu, wanda kuma sud’inma kallonsa sukeyi basa ko k’yafta ido. Shi kuwa gyara zama yayi kana asanyaye yace. “Asanadiyar hatsarin motar da Maleek ya samu likita ya tabbatar da cewar bazae tab’a iya haihuwa ba, bi ma’ana k’waya k’wayan haihuwarsa sun samu matsala, duk macen da zata zauna dashi saidai ta zauna da hak’uri amma bazae tab’a haihuwa ba!!â€? Darammm dammm haka zuciyoyi da k’irjin Buzuwa da kuma Munnira suka buga, saboda tsananin mamaki da kuma al’ajin jin maganan daya fito daga bakin Alhaji Farouk d’in. Amatuk’ar razane Buzuwa ta zazzaro idanunta waje, kana cikin yanayin tashin hankali tace. “Subahanallah, Innalillahi Wa’inna Ilaihirraju’un, Maleek bazai tab’a haihuwa ba? Ya samu matsala amararsa? Ya ilahi yanzu ya zamuyi kenan wannan wani irin sabon tashin hankaline da ba’a samasa rana ya tunkaro mu.â€? Ta k’are maganar tana me sharce gumin dake tsatstsafo mata. Munnira kuwa gaba d’aya cikin wani irin shock ta samu kanta, lokaci d’aya kuma taji har wani ciwon kai da jiri na neman kwasheta, domin kuwa sosae maganan Abban nata ya bata tsoro, idan dagaske Maleek ya samu matsala ita meye makomarta kenan? Tayiwa kanta tambayar da bata da amsarta. Alhaji Farouk kuwa matartasa ya kalla kana cikin sanyin murya yace. “Lallai tabbas Maleek ya had’u da k’addara, ayanzu kuwa zab’i ya rage garemu, nidai kam idan asonane bazan hanashi auren Munnira ba, duk da kuwa ita kad’aice y’a d’aya tilo da Allah Yabamu, dole za musu muga jika ta wajenta, amma kuma to ya zamuyi k’addara ta riga fata, saidai kawai mujira Allah yayi ikonsa.â€? Kallo mai d’auke da ma’anoni Buzuwa ta watsawa mijinnata, lallai kuwa Tabbas sunga samu sunkuma ga rashi nan take, hakika ita macece maison dukiya da kuma jin dad’in rayuwa, kasancewar kuma munnira itace y’a d’aya tilo da Allah Yabata wannan yasa ta d’iga duk wani burinta akan Munniran, tana matuk’ar son y’artata ta auri mai dukiya, wannan dalili yasa koda Alhaji Farouk d’in ya kawo maganar Maleek sanin irin tarin dukiyar da Alhaji Jaheed da kuma shi kanshi Maleek d’in ke dashi yasa tayi saurin amincewa, Tabbas tasan cewa ayanzu idan Munnira ta auri Captain M.Jay d’in bak’aramin dukiya da arziki zasu tara ba, kasancewarsa wanda bazai tab’a haihuwa ba hakan zaisa ya sakewa Munniran kud’i, saidai kuma amma bazata tab’a iya jurewa tanaji tanagani y’arta lafiyarta k’alau amma ace bazata haihu ba, Tabbas tana da burin ganin jinin Munniran. “Lallai wannan shine tsaka me wuya, ga arziki b’aro b’aro ga kuma tawaya.â€? Tafad’i hakan cikin yin k’asa da murya tare kuma dasa hannu ta dafe kanta da lokaci guda ya d’au charge. Alhaji Farouk kuwa Munnira wanda idanunta suka ciko da k’walla ya kalla, cikin tausasa murya yace. “Duk da inason aurenki da d’an Aminina Maleek, amma hakan bazai tab’a sawa na tauyeki ba, lallai dole kina da zab’i, shin kinaga zaki iya rayuwar aure da Maleek duk da wannan lalurar da ta sameshi? zaki iya zama dashi batare da haihuwa ba har abada?.â€? Shiru gaba d’aya falon ya d’auka duk da kuwa taji tambayar da Abban nata yayi mata. Kanta ta sunkuyar k’asa tare da lumshe idanunta tana me tuno tsananin had’uwa da kyawun Maleek d’in, wanda ayanzu ke tayi mata gizo acikin idanunta. K’warae shid’in Miji ne na nunawa sa’a, sannan kuma atattare dashi akwae abubuwan burgewa, ya had’u tako ta ina, yayinda kuma komai nasa ya kasance anutse, tayaya wata mace da ta samu dama zata bari cikakken gwarzon Namiji kamarsa ya sub’uce mata? Tabbas rasashi asarace babba, domin tayi imani auren Namiji kamarsa ba k’aramin d’aga mata darajarta zaiyi ba, aurensa sa’ane kuma samun hakan sai mace mai sa’a, Ina batajin zata barsa waidan kawae saboda baya haihuwa, itakam wallahi tana kwad’ayin zama dashi ahaka, Kodan fitinannen kyaun dayake dashi kuwa, duk da kuwa cewar zata so ace ta haifa masa kyawawan yara masu kama dashi. D’ago kanta tayi kana cikin sauri tace. “K’warai nikam na amincewa aurensa ahaka Abba, zan zauna dashi.â€? Idanu Buzuwa ta zazzaro cike da mamaki had’i da tsoron abunda y’arta ta ta fad’a, hatta Alhaji Farouk d’in kuwa idanu ya zubawa y’ar tasa, sakamakon jin abunda ta fad’a. Buzuwa kuwa kai ta d’an soma girgizawa, domin kuwa ta riga da ta gama yanke hukunci, duk da cewar tasan zasuyi asara sosae amma kuma gwara wannan asarar da wata asarar, fuskarta babu alaman wasa tace. “Lallai yau Munnira nasake tabbatarwa da kaina cewar baki da hankali, ke shashasha ce, kina tunanin cewar wae kyau da kud’i sunfi haihuwane? hmmm to idan ma haukane yasa kika amincewa auren Maleek ahaka to ki dawo hayyacinki ki jini, bazaki tab’a aurensa ba, matuk’ar yana tare da wannan lalurar, maganar kud’i da kyau kuwa duniyarnan da fad’i take, domin kuwa bashi kad’ai bane kyakkyawa, akwai kyawawa da yawa ciki da wajen k’asarnan, saboda haka Allah yasa shid’inma ba mijinki bane, duk da cewar kuwa yanzu aurennan saura kwana uku amma hakan bashi zaisa afasa soke shiba, naji nayarda zan fuskanci jama’ar dana gayyata na fad’a musu cewa an fasa auren, yaje Allah Ya had’asa da mai aurensa amma bawai keba.â€? Tsaida maganar nata tayi tare da juyowa ta kalli Alhaji Farouk cikin nuna babu sauyi akan maganarta tace. “Batare da wani dogon nazari ba kak’irasu kasanar dasu cewa anfasa maganar auren, har abada babu aure tsakanin Y’armu munnira da kuma d’ansu wanda baya haihuwa.â€? Idanu Alhaji Farouk ya d’an zazzaro waje cikin yanayin damuwa kuma asanyaye yace. “Kada kiyi haka dan Allah ko kinmanta cewa Alhaji Jaheed Gwani abokinane, tayaya zan k’i basa auren y’ata akan wannan dalilin, koba komai kuma Maleek matsayin d’a yake awajena, kuma ya kamata mu tausaya masa kodan lalurar da ta samesa.â€? Saurin girgiza kanta tayi kana cikin kafiya tace. “Wallahi awannan zancen babu wani batun tausayawa, shin atunaninka yau idan da ace Munnira ce ta samu wannan matsalan Maleek d’in zai iya yarda ya aureta ne? musamman yasan cewa yana tashen kyau da dukiya mai zaiyyi da macen da bata haihuwa? to haka muma y’armu bazata auri Namijin da baya haihuwa ba, dama can ahalinsu bayawane dashi ba, basu da wani dangi shiyasa sukeso muma su yankemu ya zama bamuyi gaba ba, nidai na gama magana kakira danka sanar dasu ma ehe.â€? Tana gama fad’in haka ta mik’e tsaye tare da kamo hannun Munnira ta wuce da ita d’akinta. Alhaji Farouk kuwa haka ya zauna shiru acikin falon shi kad’ai, zuciyarsa cike da nauyin yanda zai fuskanci mutum mai kamala da mutumci kamar Abbou Jaheed yace, suyi hakuri da alk’awarin auren da yayiwa d’ansu, yanzu bazai iya basu yarsa ba, lallai abun da matuk’ar kunya sosae, amma kuma to ya zaiyi? Allah ma yasani yana matuk’ar bin maganan matarsa, duk abunda ta fad’a koba mai kyau bane babu yanda ya iya bisa dole haka zaibi. Jikinsa duk amace haka ya mik’e ya nufi bedroom d’insa. Acan cikin d’akin Buzuwa kuwa munnira ta kalla, wanda duk tayi jugum zuciyarta cike da alhinin matsalar da ta samu Maleke d’in, Allah yasani itakam tana jin wani feelings d’insa, duk da cewar ayanzu tasan ta rasasa kenan amma zata so ace koda sau d’ayane ta rab’i jikinsa, bi ma’ana tasamu shiga jikinsa ta yadda zata mallaka masa kanta koda kuwa babu aure atsakaninsu, domin kuwa tun da ta sakashi acikin idanunta kullum da feelings d’insa take kwana take tashi, jarababben sha’awarsa takeji, saboda tasan cewa maza irinsa sam basu da wasa, duk macen da ta shiga hannunsu to ba makawa sai sun zautar da ita da salonsu. Buzuwa kuwa kafad’an y’ar tata ta dafa, cikin son bata nutsuwa tace. “Ko kad’an kada kiji wani abu akan barin Maleek, saboda akwae maza kyawawa da zasu soki har kuma ki mori dukiyarsu, Tabbas kam nasan munyi rashin abunda muke so, amma ae akwae gaba, rashin haihuwa ba abubane da za’a iya shanyewa, balle ma matsalar badaga gareki take ba, can daga wajensane kuma har abada ake kira Bawae na k’alilan d’in lokaci bane, ninasani zaki samu wani wanda ya fisa.â€? Saurin girgiza kae Munnira tayi kana cikin sanyin murya tace. “Har abada Momy har abada bazan tab’a samun wanda ya kaisa ba, saboda ko tantama banayi cewar irinsa shi kad’aine, tayaya ma kike tunanin zan samu wani Namiji irin Maleek? mutumin daya had’a komae da komae na rayuwa, mutumin da ganinsa ma sai mai sa’a arayuwa, mutumin da ko kusa ban tab’a tunanin taka inda ya taka ba, kin kuwa sam wayeshi Momy? Wallahi irinsa ko babu dukiya kuka still ba haihuwa mata rububinsa za sukeyi, saboda shid’in na dabanne komai nasa na musammanne, kuma Momy keda kanki ma kinsan hakan.â€? Ta k’are maganar tana me lumshe idanunta had’e da rungume hannayenta, saboda wani irin shauk’in da takeji akansa, duk da cewar kuwa baya kusa da ita amma haka takejin feelings d’insa. Ganin hakanne kuma yasa Buzuwa tab’e baki, tare da soma tattare kayayyakin dake baje akan gadonta, Dan itakam Allah Yasani ta gama magana ba kuma zata tab’a bari y’arta ta auri wanda likitoti suka tabbatar da cewa bazae tab’a haehuwa ba. *Maleek* Ahankali ya d’ago kansa wanda ya kwashe sama da 20min kan cinyar Oum Ayush, Kallon Oum Ayush d’in yayi tare da d’an gyara zamansa, ahankali kuma cikin sanyi kamar wani k’aramin yaro yace. “Please Oum Ayush zanci abinci.â€? Kallonsa Oum Ayush d’in tayi cike da kulawa, tare kuma dajin sanyi aranta, sakamakon jin cewar da kansa yau d’in ya buk’aci abinci, sab’anin sauran kwanakin da saidai ayita binsa da abincin amma yana sharewa. Cikin yanayin dake bayyana samun nutsuwarta tace. “To Maleek mekakeson ci sae na dafa ma.â€? Idanunsa ya d’an lumshe kana akasalance yace. “Southern baked BBQ chicken and fruit salad kawae!â€? Yanayin yanda ya k’are maganar yana d’an taune jajayen lips d’insane yasa cikin sauk’i zagane cewar mararsa ce ke ciwo, musamman saboda yanda ya dafe kan marar da tafin hannunsa. Take kuwa tausayinsa ya kama Oum Ayush wanda hakan yasa cikin kulawa tace. “Sannu ko bari naje yanzu na had’a maka, amma akwae chicken biryani dana dafa d’azunnan kona kawoma kafaraci?â€? Kansa ya d’an girgiza alaman “A’a.â€? hakanne kuwa yasa ta juya cikin sauri ta fice daga falon don sama masa abunda ya buk’ata d’in. Shikuwa sake lumshe tsumammun idanunsa masu kyau yayi, kana ahankali cikin daure ciwon da yakeji amarar tasa yace, da Fou’ad wanda ke zaune acan gefe kad’an yaje d’akinsa akwae laptop d’insa ya d’auko mae. Hakan kuwa akayi babu musu Fou’ad ya mik’e tsaye tare da ficewa daga falon kaitsaye yanufi sashin Maleek d’in. Shikuwa Maleek sake jingina bayansa yayi da jikin kujera, tare da sauk’e wata irin sassanyar ajiyar zuciya, sannu ahankali yakejin wani irin sanyi na ratsa duk ilahirin jikinsa yayinda wata irin sassanyar iska ke shiga kowani sashi na jikinsa. Lallai tabbas koda ace bai bud’e idanunsa ya sauk’e ganinsa akanta ba babu makawa yasan cewa itace tazo, domin yayi imani cewa akanta kad’ae yakejin irin wannan difference mood d’in, matuk’ar kuwa tana kusa dashi to koda bai bud’e idanunsa ba yasan itace. *25/February/2021* *7:40 pm* 2/28/21, 10:13 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna *Not editing* *59* Sanyayyun idanunta wanda suke d’auke da danshin hawaye ta lumshe, tare dasa hannu ahankali ta dafe daidai saitin zuciyarta. Duk da cewar ta fita ta barshi afalon sam batayi tunanin sake da wowa ta sameshi ba, musabbabin dawowarta falon kuma shine manta wayarta da tayi. Saurin mannewa ajikin kofar falon tayi tayanda tasan koda ya bud’e idanunsa bazai ganta ba. Shikuwa ahankali ya bud’e kyawawan idanunsa tare da sauk’e ganinsa adaidai saitin k’ofar shigowa cikin falon, saidai kuma rashin ganin kowa awajen yasa shi sauk’e wani irin gauron numfashi, tare kuma da tsaida idanunsa adaidai k’ofar shigowa cikin falon, domin kuwa Tabbas zuciya da gangar jikinsa sun shaida masa cewar lallaine tana kusa dashi, because akanta kad’ai yakejin irin wannan yanayin. Ita kuwa Laylerh ba koma one ya hanata k’arasa shigowa cikin falon ba kamar yanda taji zuciyarta na bugawa da sauri sauri, musamman ma ganinsa da tayi ayanzun, ahankali tasa hannunta ta dafe kirjinta dake tsalle kaman zai fad’o waje, tare kuma da sake lumshe idanunta. Asanyaye ta fitar da wani numfashi mai sauti, yayinda kuma lokaci d’aya duk taji jikinta yayi relax. “Laylerh!!.â€? Fou’ad ya kira sunanta, wanda yanzu dawowansa daga sashin Maleek d’in, ganin Laylerh’n da yayi atsayene kuma yasashi jin mamaki k’warai. Ita kuwa Laylerh jin muryar Fou’ad dinne yasa tayi saurin bud’e idanunta, wani irin kunyansa da tajine kuma yasa tayi k’asa da kanta tare da soma wasa da y’an yatsun hannunta. Fou’ad kuwa kallon tsab ya mata tare da d’an gyara tsayuwarsa anutse yace. “Halan Oum Ayush kike nema ko?.â€? Kanta ta d’an girgiza kana asanyaye tace. “Aa phone d’ina nazo d’auka.â€? Jin yanda tayi maganan asanyaye cikin fusgan numfashine kuma yasashi saurin jinjina kai alaman ya fahimta, batare kuma daya sake ce mata komae ba yasakai ya shige cikin falon, aransa yana me tabbatarwa da kansa cewar koda ga salon maganarta kad’ai dole ta jawo hankalin d’a Namiji, ballantana kuma idan aka tafi ga tsarin halittarta, tana da wani irin body structure mai kyau da d’aukar hankali, wanda ba iya Namiji d’aya ba, maza da yawa idan suka ganta to fa lallai zasu haukace akanta, duk da kuwa cewar bata da yawan shekaru sosae amma kuma ayanzu duk wani cikar halittar y’a mace ya bayyana ajikinta, tabbas Laylerh’n ta cika macen da dole soyayyarta bazatayiwa zuciyar da ta kama da sauk’i ba. Saurin kauda tunanin dake zuciyarsa yayi tare da fad’in. “Astaghfirullah!â€? domin yasan ita d’in matar wanice, haka kuma fasalta yanayin tsarin halittarta sam ba daidai bane. K’arasowa gaban Maleek d’in da har yanzu idanunsa ke kan k’ofar falon yayi, mik’a masa laptop d’in yayi tare da neman waje ya zauna. Daidai lokacin kuwa ta sako k’afarta cikin falon, cikin kuma yanayin sanyin da ayanzu yake neman zame mata jiki ta ke tafiya ahankali, yayinda kanta ke k’asa tana me aikin mummurza y’an yatsun hannunta. Hakika shigowanta cikin falon shiya sanya zuciyarsa tsananta bugawa, yayinda yasakejin komai nasa ya zama very weak, ahankali ya sauk’e idanunsa akan kyakkyawar fuskarta, wanda kuma hakanne ya tilasta masa d’an lumshe idanunsa, saboda yanda yaji wani irin sanyi na ratsa cikin jiki da b’argonsa. Ita kuwa Laylerh duk da cewar bata d’aga kanta ta kallesa ba, amma hakanan taji ajikinta cewar idanunsa na yawo akanta, hakanne kuwa yasa takejin kamar k’afafunta zasu hard’eta ta fad’i. Ta bayan wasu had’add’un Royal Gothic Chairs dake cikin falon tab’i tare da k’arasawa inda ta zauna d’azun, cikin sa’a kuwa tana isa wajen taga wayartata aje akan sofa, d’aukan wayar tayi tare da juyawa cikin yanayi na d’an sauri ta soma tafiya don barin cikin falon, wanda tun shigowarta cikinsa heart d’inta ke abnormal beating, duk yanda idanunta ke so da mararin ganinsa kuwa ta kasa iya d’aga kai ta kallesa, Sam batasan meyasa yau d’in takejin hakan akansa ba, duk da cewar sometimes takanji hot feelings akansa, amma feeling dinta na yau akansa da banne, wannan dalilinne ma yasa take sauri wajen ganin tabar cikin falon. Agarin saurinnata ne kuma batare da ta lura ba adon dake jikin d’aya daga cikin Gothic chairs din ya kama k’asan skirt d’inta, wanda bisa dole hakan ya tilasta mata tsayawa. Asanyaye ta b’ata fuska ganin da tayi cewar dole saita tsugunna kafun ta iya cire k’asan skirt dinnata daga jikin abun. Kyawawan fararen k’afafunta da suka bayyana saboda d’an d’agewa da skirt dinnata yayi ya zubawa idanu, tare da maida hankalinsa ga kallon kyakkyawan red anklet chain d’in dake sak’ale a k’afarta na dama, sosai anklet d’in ya karb’i fatar nata kasancewar sa red colour mai adon white stones. Kallon k’afafunnata yake da kyau baya ko k’yaftawa yayinda kuma sannu ahankali yakejin zuciyarsa nayi masa sanyi. B’angarenta kuwa hardai yanzun tanajin idanunsa na yawo akanta, wanda kuma hakanne yasa ahanzarce ta janye skirt d’inta, cikin sauri sauri ta fice daga cikin falon, domin tayi imani cewa matuk’ar ta k’ara mintuna 4 masu kyau acikin falon to fa lallai bazata iya controling kai da kuma abunda ke cikin zuciyarta ba. Da rikitattun idanunsa ya bita harta fice daga cikin d’akin kuwa bai d’auke idanunsa daga kallon hanyar da tabi ta fita d’inba. Fou’ad da tun shigowar Laylerh’n ya zubawa Maleek d’in idanu, gyara zamansa yayi tare da d’an kawar dakansa gefe cikin d’an d’aga murya ta yanda yasan Maleek d’in zai iya jiyosa yace. “Mutum dai yaci gaba da d’ibawa kansa zunubi ta hanyar yiwa abunda ba mallakinsa ba kallon k’urulla kallon haram.â€? Jin abunda Fou’ad d’in ya fad’ane yasashi juyo da kansa, ya fuskanci Fou’ad d’in wanda yayi kamar ba daga bakinsa maganar da yayi yanzun ta fito ba. Sam shikam Allah Ma yasani ayanzu bayida lokacin biyewa Fou’ad, saboda ya fuskanci cewar sai mutum nada lafiyane ma yake wani abun. Shigowar Oum Ayush cikin falon ne kuma hannunta d’auke da d’an madaidaicin tray, yasa shi maida kallonsa gareta, saboda tsabar yunwan da yakeji har wani irin jiri ne ke damunsa, yana kuma kyautata zaton cewa cikin magungunan da Dr.Mouhammad ya basa akwai wanda yakesa cin abinci sosae. A gabansa Oum Ayush ta ajiye madaidaicin tray d’in wanda samansa ke d’auke da plate d’in southern baked BBQ chicken da kuma d’an k’aramin glass bowl wanda ta zuba yankakken fruit salad mai sanyi aciki. “Bismillah!.â€? Tafad’a adaidai lokacin da take tura masa plate d’in gabansa. Kasancewar kuma dama yunwa yakeji sosai hakan yasa baijirayi komae ba, cike da nutsuwa ya fara cin abincin, yayinda kuma time to time yake d’an lumshe kyawawan idanunsa masu d’auke da gajiya da kuma yanayin bacci. Oum Ayush kuwa hira suke d’anyi kad’an kad’an da Fou’ad wanda yace shi bazaici abincin ba. B’angaren Laylerh kuwa tana fitowa daga falon kai tsaye part dinsu ta nufa, koda ta k’arasa sashin nasu bata samu Najeeb ba, wanda kuma da ‘alama baya gidanne ma baki d’aya. Anan kan d’aya daga cikin kujerun falon ta kwanta, tare da d’aukan trow pillow ta rungume ak’irjinta, ahankali haka takejin bugun zuciyarta na lafawa, yayinda kuma nutsuwarta ke dawowa jikinta. Saidai kuma har zuwa yanzun brain d’inta ta kasa daina maimaita mata kalmar da Abbou Jaheed ya fad’a cewar. “Doctors sunce Maleek bazae tab’a haihuwa ba!â€? K’warai sosai maganar ta daki zuciyarta, tare kuma da wujijjiga tunaninta. Ita da kanta take tambayar kanta dalilin shigowar wannan mummunar k’addarar cikin rayuwarsu. “Shikenan Maleek bazai samu mai sakashi farinciki ba? bazae tab’a haihuwa ba hakan kuma na nufin har abada kenan? Shin tayaya zai iya jurewa wannan k’unci da kuma ciwon?â€? “Lallaine kowani bawa da irin salon k’addararsa arayuwa, amma kuma ta Yah M.Jay ta kasance mai muni da kuma cutarwa, yah Allah Kabashi iko da kuma k’arfin jure duk way’annan damuwowin!!â€? Tafad’i hakan abayyane cikin wata raunanniyar murya, wanda kuma hakanne ya bayyana zuban hawaye akan kyakkyawar fuskarta. Tabbas tasan cewa ayanzu idan tace zatayi wani tunani ko kuka zuciyarta na iya bugawa, Hutu kawai takeson saboda har yanzu tana d’anjin ciwon kai kad’an kad’an. Wayarta dake hannunta ta kunna tare da soma duba sak’onnin da aka turo mata, wanda cikinsu kuma harda sak’on komawarta makaranta da kuma na WAEC examination d’in da zasuyi nan da 2week. Haka dae ta d’an duba sak’on da akayi mata d’in sama sama nanma saboda gudun kada tayi tunani mai zurfine shiyasa, tana cikin shafa wayar nata kuwa bacci b’arawo ya d’auketa. Acan falon Abbou Jaheed kuwa a sosae Maleek yaci abincin da a Oum Ayush d’in ta kawo masa, duk da cewar kuwa bai cinye abinci da kuma fruit salad d’in duka ba amma yaci sosae. Yana kammala cin abincin kuwa ya mik’e tsaye, da yake kuma y’an miskilancinnasa na kusa baice da su Oum Ayush d’in komae ba yasa kai ya fice daga cikin falon. Kaitsaye sashinsa ya nufa, daga cikin tangamemen falonnasa kuwa direct bedroom d’insa ya shige. Kayan dake jikinsa ya d’an rage tare da kutsawa cikin bathroom d’insa yayi wanka. Bayan ya fito awankanne kuma yasaka wasu sauk’ak’akk’un riga da wando, wanda yasan cewa bazasu ta kurasaba. Magungunansa yasha tare da hayewa saman makeken gadonsa ya kwanta. Lokaci d’aya kuwa wasu irin tunani suka shiga yawo acikin k’wak’walwarsa, wanda asanadinsu ne kuma yaji zuciyarsa tayi matuk’ar karyewa, saidai kuma a irin yanayin da yakejin kansa ayanzu yasan matuk’ar ya biyewa damuwar dake sukar zuciyarsa, to bai wuce wata sabuwar matsala ta sameshi. Sanin hakan da yayine kuma yasa lokaci d’aya yasoma k’ok’arin zeroying mind d’insa. Kyawawan idanunsa masu d’auke da abubuwa kala kala ya lumshe, tare kuma da soma fitar da wani irin breath mai sanyi. Cikin abunda bai wuce 20minutes ba kuwa wani irin nannauyan bacci ya d’aukesa, wanda kuma dama hakan shine burinsa. Tunda ya fara baccin nasa kuwa bashine ya farkaba sai kusan magriba, haka yakejin jikinnasa gaba d’aya ba k’wari, toilet ya shiga ya d’auro alwala bayan ya fito daga toilet d’inne kuma kai tsaye ya wuce masallaci. Anan cikin masallacin dake jikin gidansu yayi sallan Magrib, yana kuma zaune acikin masallacin har aka k’ira sallan Isha, bayan ansallame sallan Isha d’inne kuma ya dawo gida, again kuma wani baccin yakeji sosai, haka dolensa yasake komawa ya kwanta. Awani k’arin abun mamakin kuwa shine daga shi har Laylerh yau d’in haka suka kasance kamar wasu bugaggu, domin ita d’inma bacci tayi sosai sallah ne kawae ke ta da ita, yanzun ma koda Najeeb ya dawo akan gado ya sameta, tana ta faman aikin bacci, saidai kuma kasancewar shid’in baya cikin mood maidad’i hakan yasa bai ta she ta ba, koda ya gama abunda zaiyi rab’awa yayi ya kwanta agefenta, yayinda yakejin k’irji da kuma zuciyarsa nayi masa wani irin k’una da kuma tarin rad’ad’i, aduk lokacin kuwa da zuciyarsa ta hasko masa abunda idanuwansa suka gane masa yau d’in sai yaji wani irin haushi, takaici, da kuma tsanar kanshi ya rufesa. Haka dai zuciyarsa cike da tunani kala kala bacci ya d’aukesa. *Washegari* 8:30 am Wani irin juyi mai d’auke da alaman gajiya da kwanciyar nata tayi, kana ahankali ta soma ware kyawawan idanunta wanda suka d’auki kusan awa uku akulle, domin kuwa tunda tayi sallan asuba ta sake komawa sabon baccin da sai yanzu ta farka. Tashi zaune tayi tare kuma da soma k’arewa cikin d’akin kallo, daidai lokacin kuwa wayarta dake aje akan bedside drawer ta soma fidda sassanyar wak’an Ali Gatie na (Running On My Mind) wacce ita ta kasance ringintone d’inta, saboda tana matuk’ar son wak’ar sosae. Akasalance ta kai dubanta ga wayar, ganin kuma cewa sunan Oum Ayush ne ke yawo akan screen d’in wayar, yasa cikin sauri tasa hannu ta d’auki wayartata tare kuma da picking call d’in. Oum Ayush dake kan layi kuwa jin Laylerh ta d’auki wayarne yasa batare da ta tsaya jin ta bakin Laylerh’n ba tace. “Baccin ya isa haka, yanzu yanzu kizo dining area muyi breakfast.â€? “To.â€? Kawae tace asanyaye, Oum Ayush kuwa take ta kashe wayar. Ahankali ta zuro da kyawawan k’affunta k’asa, had’i da mik’ewa tsaye, y’ar ficikar rigar baccin dake jikinta ta kalla, wanda ita kanta ma batasan ya akayi ta saka ta ba, saboda tsabar baccin dake damunta jiyan. Kaitsaye toilet ta wuce danyin wanka, sanin da tayi kuma cewa su Oum Ayush na jiranta ne yasa bata wani b’ata lokaci awajen wankan nata ba. Bayan ta fito daga wankanne kuma ta tsane jikinta, tare da zama agaban dressing mirror ta shafawa jikinta mai, kamar kullum kuma iya powder,mascara da kuma kwalli kawae ta shafa, sai wani brown lips gloss da ta shafawa jajayen labb’anta, hakanne kuwa yasa lips d’innata ya fito da kala maikyau. Turaren oud ta shafa had’e da d’aukan wata doguwar rigar English wears mai kalan brown ta sanya ajikinta, kasancewar kuma rigar irin pencil gown d’innanne maibin jiki, hakan yasa ta d’aura wani light brown denim jacket akan shigartata, sosai kuwa hakan ya k’ara bayyana yalwataccen kyawun da tayi. K’aton agogon dake cikin d’akin ta kalla, take kuwa idanunta suka gane mata lokaci 8:55 am daidai. Agurguje ta nannad’e dogon gashinta, tare kuma dasaka wani hulan turban mai kalan brown akanta. Light brown shoes masu gashin kuliya tasaka ak’afanta, kana tasa hannu ta d’auki wayarta dake aje akan mirror. Cikin sauri haka ta fice daga cikin d’akin. Koda ta fito compound d’in gidan kaitsaye part d’in Momy ta nufa domin kuwa acan sukeyin breakfast. Gaba d’ayansu zaune suke akan babban dining table d’in ciki kuwa harda Najeeb wanda sama da mintuna 15 kenan da zuwansa wajen amma yakasa kai koda loman abincine bakinsa. Kamar kuma yanda suka hallara awajen cin abincin haka shima ya hallara, yayinda yayi wani irin kyau cikin shigar armany jeans da kuma crazy shirt d’in dake jikinsa. Tabbas kallo d’aya zaka mishi ka fahimci cewar akwai sanjin yanayi atare dashi, saidai kuma amma yakasa bari idanunsa su nuna hakan. Sab’anin mahaifinsa wanda tun zamansa awajen ya fahimci cewar Abboun nasa na d’auke da damuwa acikin zuciyarsa domin ya lura lokuta zuwa lokuta Abbou Jaheed d’in ke satan kallonsa, duk da kuwa baisan meyene azuciyar Abboun nasa ba, amma zuciyarsa ta fad’a masa cewa bawai abubane mai dad’i. Ahankali yake d’an jujjuya tea spoon d’in dake hannunsa, daga gefe guda kuwa baked mozzarella stick d’in dake gabansa ya zubawa ido, duk da cewar kuma ya d’anyi nisa atunaninsa amma hakan baihanashi ji ajikinsa cewar Laylerh’n ta shigo cikin falon ba. Wani sassanyar k’amshin daya daki hancinsane kuma ya sake tabbatarwa da kansa cewar Lallai ita d’ince, domin awajenta kad’ai yakejin irin k’amshin. Ita kuwa Laylerh ganinsu duka akan dining area d’inne yasa anutse ta k’araso wajen. Bayan ta gaishe dasu Abbou Jaheed ne kuma anutse taja kujeran dake kusa da Najeeb ta zauna. Wanda kuma hakan yasa ya zamana ita dashi suna facing juna. K’asa k’asa batare kuma da ta bari idanunta sun sauk’a akansa ba, cikin shaking voice d’inta tace. “Good morning Yah M.Jay....â€? Shiru yayi kamar baijita ba, sannan bai kuma d’ago kansa ya kalleta ba, still tea spoon d’in dake hannunsa yake ta faman juyawa. Laylerh kuwa jin bai amsa mata bane yasa ta lumshe idanunta wanda lokaci d’aya suka ciko da hawaye, Sam batasan meyasa wani lokaci idan ta gaishesa baya amsawa ba, bayan kuma yasan tasan cewar yanajinta. “Why?â€? Ta tambayi kanta. “Saboda yasan ke mairaunice akansa.â€? Wani b’angare na zuciyarta ya bata amsar hakan. Fuskarta ta d’an shagwab’e, saboda sam bataji ta gamsu da hakan ba. “Good morning!â€? Najeeb dake gefenta ya fad’a k’asa k’asa, adaidai lokacin da yake turo mata plate d’in dake gabansa, wanda samansa ke d’auke da chips and ketchup, sai kuma wani d’an bowl wanda aka zuba perfect vanilla soufflĂŠ aciki. Wani irin kunyansane ya kamata dan sai alokacinne ma take tunawa cewar sam basu gaisaba lokacin da ta tashi sallan asuba bayanan yana masallaci. D’an sunkuyar da kanta k’asa tayi, kana asanyaye tace. “I’m sorry morning Yah Najeeb.â€? Murmushin daya bayyana kyawun fuskarsa yayi batare kuma daya ce mata komae ba ya kawar da kansa gefe. Ganin hakanne kuma yasa jiki amace ta soma cin abincin daya turo mata d’in. Almost 20minutes kenan yanzu da kowa yake ta hidimansa akan dining table d’in. Ahankali Abbou Jaheed ya d’ago ya kallesu bayan kuma ya kammala goge bakinsa da tissue paper ne, yayi gyaran muryar dayasa dukanninsu d’agowa suka kalleshi, saidai banda M.Jay wanda tun d’azu yake ta abu d’aya kaman statue. Abbou Jaheed kuwa d’an satan kallon gefen da Maleek d’in ke zaune yayi, kana cikin tausasa murya yace. “Kuyi hak’uri da abunda za kuji daga bakina, domin kamar yanda na had’aku jiya na sanar daku matsalan da tasamu Maleek, haka yau ma nake mai bak’in cikin sake sanardaku wata magana wanda nasan bazata tab’a yi muku dad’i ba.â€? Tsagaitawa da maganan nasa yayi tare da kallon Maleek wanda har yanzu kansa ke k’asa. Anutse cikin kuma yanayin tausayawa yace. “Bazan tab’a gajiyawa da baka hak’uri ba Maleek, nasan cewa kanajin ciwo da kuna acikin zuciyarka, amatsayina na mahaifinka kuwa ba zanso duk wani abu dazai cutar dakai ba, amma kasani bani da wani zab’i ayanzu wanda ya wuce fad’a maka gaskiya, domin kuwa Tabbas abune da yake abayyane, cewar ba kowacce mace ko iyaye bane ke barin y’ay’ansu su auri wani Namji ko Mace wanda bazasu tab’a haihuwa ba, hak’ik’a kowa yana da irin k’addararsa amma kasani wannan k’addarar k’addarace mai ciwo, domin kuwa asanadin ta jiya da dare Alhaji Farouk ya k’ira ya sanar dani cewa, Matarsa ta shaida cewar maganar aure tsakaninka da y’arsu Munnira babu ita, Tabbas Nikam na fahimcesa domin da ace asonshine zai iya baka auren y’arsa, saidai kuma amma ita kanta uwar yarinyar tana da nata hakk’in, shin ayanzu a kuma irin zamaninnan wace y’a mace ko kuma iyayene kake ganin zasu baka y’arsu ka aura bayan kana tare da wannan lalurar? k’addarama ace zaka samu hakan to bai zama lallai ya zamana son gaskiya ake maka ba, watak’ila zata aurekane Dan dukiyarka, wata k’ila kuma zata aurekane Dan kyau da matsayinka, wata k’ila kuma zata aurekane Dan kawai tayi suna, wanda ni kuma Ina matuk’ar jin tsoron hakan Maleek inajin tsoron wani abu dazai sake samun rayuwarka, duk da cewar inaji ajikina cewar wannan k’addarar zata sama maka farinciki watarana!!!â€? *(Team Maleek inakuke🗣🗣🗣🗣🗣🗣 gobe zanyi Chapter 60, kuma kusani ga duk wani masoyin Maleek gobe ranarsace)* *28/February/2021* *1:45 pm* 3/1/21, 8:56 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna *Not editing* #divorce💔 *CHAPTER 60*. Tsagaitawa da maganan Abbou Jaheed yayi tare da d’ago kansa ya kalli Maleek d’in wanda har yanzu bai d’ago kai ya kalli mahaifinansa ba, duk da kuwa cewar yaji batun fasa auren nasa. Yayinda awajen su Abbou Khareem da kuma Oum Ayush abunda sukaji d’in ya kasance sab’anin tunaninsu, domin kuwa sam koda wasa basu tab’a kawowa aransu cewar wannan k’addarar takai matsayin da har za’ana hana Maleek d’in aure ba, wani irin sabon tausayinsa ne sukaji ya lullub’e musu zuciya, saboda sunsan dolene zaiji ba dad’i, hatta Oum Ayush da dama tuncan bawae zuciyarta ta aminta da auren Maleek da Munniran bane, taji zuciyarta tayi mata babu dad’i domin hakan alamace dake nuna ko anan gaba Maleek zai fuskanci k’alubale sosae kafun ya samu wacce zata aureshi, kuma kamar yanda Abbou Jaheed d’in ya fad’ane ba lallaine duk wata macen da zata auresa ya zama da zuciya d’aya zata zauna dashi ba. “Kayi hak’uri Maleek akan duk wata k’addarar da ta sameka arayuwa, Insha Allah Watarana komae zae wuce kamar bai faru ba!â€? Abbou Khareem ya fad’i hakan asanyaye tare dasa hannunsa ya kamo hannun Maleek d’in wanda har yanzu bai furta komae ba. Shirun da Maleek d’in yayine kuma yasa gaba d’aya dining area d’in ma ya d’auki shiru, babu wani mai motsi acikinsu, saboda ba kad’an ba maganan fasuwar auren Maleek d’in ya wujijjiga tunaninsu, kasancewar abune da sam basu tsammacesa ba. Ahankali ta lumshe Idanunta wanda suka cika tab da k’walla, akaro na biyu kenan da ta sakejin wata mummunar magana akansa ta doshi kunnuwanta, still kuma akaro na biyu kenan da taji zuciyarta ta tsananta rauni akansa, yayinda kuma wani irin matsanancin tausayinsa ya lullub’e duk ilahirin jikinta, har hakan yayi sanadiyar zubowan wasu siraran hawaye daga cikin lumsassun idanunta. Sosae hawayen nate ke d’auke da yanayin damuwa, wanda da ace wani daga cikinsu zai kali fuskarta ayanzun to fa lallai daya fuskanci hali da kuma irin ciwon da takeji acikin zuciyarta, wanda kuma ahak’ik’anin gaskiya Bawae tana kukane saboda fasa aurensa da Munniran da akayi ba, no tana kukane saboda matsanancin tausayinsa da takeji, da kuma irin k’alubalen da ta fahimci cewa yana dab da fuskanta arayuwa. Lallai tasan dolene zaiji babu dad’i, ga kuma alama abayyane domin har yanzu baice komae ba. Ahankali ya zame hannunsa dake cikin na Abbou Kareem, kujerar da yake kai yad’anja baya tare da mik’ewa tsaye, still ko k’ala baicewa kowannensu ba ya juya cikin takunsa dake amsa amo ya nufi hanyar barin falon ma baki d’aya. Ganin hakanne kuwa yasa duk suka zuba masa idanu, ciki kuwa harda Laylerh wanda tabi bayansa da idanu, yayinda acikin zuciyarta takejin kaman taje da gudu ta fad’a jikinsa, ko hakan zaisa zuciyoyinsu dake matuk’ar azabtuwa kowanni seconds da minutes su samu rangwame da salama. Ganin ya fice daga cikin falonne kuma yasa ahankali duk suka janye kansu daga kallonsa, zuciyar kowannensu cike da tunani da kuma abubuwan da suke sak’awa acikinta kala kala. Abbou Jaheed da gaba d’aya jikinsa yake asanyaye mik’ewa tsaye yayi shima, kai tsaye ya nufi sama wanda ananne kuma asalin bedroom d’insa yake. Ganin Abbou Jaheed yayi tafiyarsane kuma yasa Oum Ayush da Abbou Khareem ma mik’ewa zuciyoyinsu duk babu dad’i haka suka fice daga falon. Hakan yasa dining table d’in ya rage daga Najeeb sai kuma Laylerh’n wanda ta kasa iya controlling nutsuwarta. Sanadiyar hakanne kuma yasa duk hankalin Najeeb ya dawo kanta, ganin ta sunkuyar da kanta ne kuma yasasahi sa hannunsa ahankali ya d’ago hab’arta, bisa dole ya zama sun fuskanci juna. Kyakkyawar fuskarta ya zubawa idanu, tare kuma da tsaida ganinsa akan zararan eye lashes d’inta wanda suke d’auke da danshin hawaye. “Kuka?.â€? Ya fad’a cikin yin k’asa da murya. Ahankali ta d’an girgiza kanta, Alaman “A’a.â€? Murmushin daya bayyana kyawun fuskarsa yayi, duk da cewa kuwa yasan silar yin kukan nata, amma saiya share, cikin yanayin bada umarni yace. “Ya isa haka kici abinci!â€? “Nak’oshi.â€? Ta fad’i hakan asanyaye batare kuma da ta jira wani abu da zaice ba ta mik’e tsaye, cikin yanayin rashin kuzarin da takejin kanta aciki ta nufi hanyar barin falon, yayinda shikuwa yarakata da idanunsa harta fice. Sauk’ak’akk’iyar ajiyar zuciya yayi, kana shima ahankali ya mik’e tsaye tare dabin bayanta. Laylerh kuwa koda ta fito daga cikin babban falon gidan, kaitsaye sashinsu ta wuce, bata kuma tsaya a falo ba direct bedroom d’insu ta wuce. Yanayin yanda takejin rauni sosai azuciyarta ne kuma yasa tana shiga cikin bedroom d’in, asanyaye ta k’arasa wajen wani had’add’en sofa dake cikin d’akin ta zauna. Tafukan Hannayenta duka biyu tasa ta rufe fuskarta, tare kuma da sauk’e wani irin k’akk’arfar ajiyar zuciya, kwata kwata duniyar batayi mata dad’i, k’unci da damuwa kawai takeji acikin zuciyarta wanda ita kanta batasan sai yaushene zata samu sassauci da kuma salama akan abunda takeji acikin zuciyarta ba. Hawayen da suka gangaro kan fuskarta ta share tare da d’an cije labb’anta kana abayyane cikin kuma muryar dake bayyana damuwarta k’arara tace. “Bansan sai yaushe ne zamu samu farinciki ba, a kullum damuwa da ciwo suke tasiri acikin rayuwarmu, kana kuma su sukecin k’arfinmu, bayan wannan k’addarar sai kuma wannan jarrabawar, kullum dae abu d’ayane babu canji, shin tayaya zuciyoyinmu masu rauni zasu jure irin way’annan abubuwan? Tayaya zamu iya fuskantar k’alubalen da zasu zo rayuwarmu anan gaba? Mezai faru? Meyakeji? Wani irin ciwo yakeji duk babu wanda zai fahimta, shi ne kawae shikad’aine yasan meyakeji azuciyarsa, nayi imani cewa zafi da ciwo bazasu tab’a barinsa ya huta ba!!â€? Ta k’arishe maganan alokacin da take zamowa daga kan sofan ta zubar da guiwowinta ak’asa. “Tabbas zai huta Laylerh, sannan kuma zafi da ciwo zasu bar cikin rayuwarsa bari kuma nahar abada!!.â€? Muryar Najeeb ta karad’e gaba d’aya d’akin wanda hakan yasa da sauri ta dawo da kallonta ga Inda taji amo da kuma sautin muryartasa. Ganinsa tsaye abayanta ne kuma yasa tayi saurin sunkuyar da kanta k’asa. Shikuwa Najeeb asanyaye ya k’arasa shigowa cikin d’akin tare da zama akan sofan dake kusa da ita. Hannayensa duka biyu yasanya ya rufe fuskarsa kamar yanda tayi d’azun, cikin wata irin murya da ko kad’an batasan cewar yana da ita ba, ya jefo mata tambaya tahanyar cewa. “Me kikeji azuciyarki dangane da Maleek? Meyasa akoda yaushe kike kuka akansa? Meyasa duk wani ciwo nasa kikejinsa har acikin jiki da zuciyarki?.... kada kimin k’arya Laylerh domin ayau bana buk’atar k’arya saboda gaskiyar abunda ke zuciyarki na bayyane acikin idanunki, meyasa Laylerh meyasa???â€? Ya k’are maganar tasa cikin wata irin raunanniyar muryar da tasa bisa dole Laylerh ta d’ago idanunta ta kalleshi. Lallai ne kuma Tabbas koda ace bai yi mata wannan tambayar ba dole ne yau ta fad’a masa yanda takejin fargaba, tsoro, da kuma tsananin tausayawa akan d’an uwannata. Zafafan hawayen da suka gangaro daga cikin idanunta ta sharce kana asanyaye cikin wata murya mai d’auke da matsanancin damuwa tace. “Tausayinsa nakeji Yah Najeeb, tausayin yah Maleek nakeyi, baisan farinciki ba, haka kuma baisan jin dad’i ba, gaba d’aya mummunar k’addara ta kewaye rayuwarmu, ko yaushe k’unci da kuma muradine marar cika, nasan cewa bayajin dad’i , kuma nasan da cewar akoda yaushe yanajin k’unci acikin rayuwarsa!.â€? D’an tsagaitawa da maganan nata tayi tare da matsowa kusa da Najeeb d’in, d’aya daga cikin hannayensa ta kamo ta d’aura akan k’irjinta daidai saitin zuciyarta. Cikin wata irin raunanniyar murya tace. “Yah Najeeb please koda sau d’ayane ka tab’a zuciyata, na tabbata zakaji yanda take harbawa akan kowani damuwar sa, duk wani ciwonsa azuciyata nakejin zafin, domin shine mutum na farko aduniya da tun Ina k’arama ya fara shayar dani da yawun bakinsa, kana kuma shine mutum na farko aduniya da idanuna ke yawan yimin gizo dashi, komai zai samesa sai naji hakan ajikina, ko kuma nagani amafarkina, banason wani abu ya sameshi, banason koda d’igon abu na cutarwa ne ya sauk’a akansa, Domin saboda shine kawae nake rayuwa, Tabbas inajin ciwo sosai acikin zuciyata, amma kuma nasan nasa ciwon da yakeji ya zarce nawa zafi da rad’ad’i, ance bazae tab’a haihuwa ba, yanzu kuma ance ba za’a bashi aure ba saboda yana da lalura, nasani kwarai nasan cewar wannan masomin k’alubalen da zai ci gaba da fuskanta ne agaba d’aya rayuwarsa, Saboda wannan kawai bazai samu farinciki ba? bazai samu mai kulawa dashi koda sau d’ayane ba? shin menene laifinsa aciki dan k’addarar rashin haihuwa ta fad’a masa? kenan wannan shike nuna saboda hakan Yarasa duk wata dama nasa kenan? Bazai samu mai kulawa dashi da bashi abinci ba, bazai samu me nuna masa soyayya ba, kullum zai zauna acikin damuwar da baya iya fad’anta ga kowa, haka zaiyita jin ciwo azuciyarsa, shikenan shi bazaiyi farinciki ba, ko yaushe zuciyarsa k’uncine!!â€? Idanunta ta rumtse da k’arfi, wanda kuma hakan ke bayyana abunda takeji acikin zuciyarta mai tsananin ciwo ne, Asanyaye da kuma muryarta me rauni sosai tace. “Please Yah Najeeb ko da sau d’aya ne ka saurari bugun da zuciyata keyi, domin acikintane kawae zaka fahimci abunda Yah Maleek yakeji acikin tasa zuciyar, wanda baki bazai tab’a iya furtawa ba, wanda kuma yake kassara masa duk wani burinsa na kowacce rana, tabbas yau naji dama ina da iko, to da na d’aukewa Yah M.Jay gaba d’aya duk wata mummunar damuwarsa, tayanda shima zaiyi farinciki kaman kowa, domin ko kad’an banason gani kojin ciwonsa, saboda nayi imani ni mai matsanancin raunine akansa!!!! Ta k’are maganar nata tana me girgiza kanta tare kuma da kama hannayen Najeeb din duka biyu ta had’e su waje d’aya, lokaci d’aya kuma ta fashe da wani irin fitinannen kuka mai tsananin tab’a zuciyar mai sauraro, kukan dake zayyane duk wani abunda ke cikin zuciyarta, haka kuma kukan dake nuna cewar ta gaza, sannan kuma tazo last hope d’inta. Manyan idanunsa wanda suka kad’a sukayi jajur ya lumshe tare da kamo hannunta dake kan nasa ya matse gam, wani irin ciwo mai tsanani yakeji acikin zuciyarsa, yayinda kuma gaba d’aya gangar jikinsa ya d’auki rawa, daga gefe guda kuwa gargasan dake kwance ajikinsane suka mimmik’e, yayinda idanunsa suka cigaba da runewa zuwa kalan ja. Wani irin tsalle da zuciyartasa keyine kuma yasashi bud’e idanunsa, tare da sauk’e ganinsa akan Laylerh’n wanda take kuka sosae. Akaron farko na tarihin rayuwarsa kenan da yaji wasu irin hawaye masu d’umi sun zubo daga cikin idanunsa, yayinda zuciyarsa kuma tayi wani irin mummunan karyewa, matsanancin tausayin kansa da kuma na Laylerh’n ne ya lullub’esa, wanda har hakan ya sashi kasa iya jurewa. Saidai kuma gudun kada Laylerh’n ta d’ago kai taga hawayensa ne yasashi saurin kawar da kansa gefe tare da mik’ewa tsaye, cikin yanayin sauri da kuma son daidaita nutsuwarsa ya fad’a cikin bathroom. Laylerh kuwa da zuwa yanzu kukan da take ya soma cin k’arfinta, ahankali ta zame jikinta ta kwanta akan lallausan carpet d’in dake malale asaman tiles d’in wajen, haka takejin numfashinta na fusga kaman zai bar gangar jikinta. Najeeb kuwa yana shiga cikin toilet d’in sassanyan ruwan dake kwance acikin had’add’en jakuzzie ya d’ebo ya watsa akan fuskarsa, yayi hakanne kuma wae ko zaiji sanyi da salama na daga wutar dake cin zuciyarsa, saidai kuma sam hakan baisa yaji wani sanyi acikin zuciyarsa ba. Ahankali ya jingina bayansa da jikin bango tare kuma da sake rumtse idanunsa. Abayyane kana cikin wata irin murya mai dauke da rauni sosae yace. “Tabbas zan aikata hakan koda zan kasance acikin k’unci, saboda ayanzu dolene na samawa zuciyoyin da aka ginasu akan muradi d’aya haske da kuma farinciki, ko da ace badon komae ba, idanuwana sunganemin abunda ya zama tilas d’ina!!!â€? D’agowa daga jinginen da yake yayi tare da daukan towel ya goge fuskarsa. Cikin k’arfin hali da kuma bugun zuciyar daya samu kansa aciki ya murd’a handle d’in kof’ar bathroom d’in ya fito. Idanunsa ya sauk’e akan Laylerh da keta sakin sheshshek’an kuka, ga kuma wani wahalallen bacci daya d’auketa, wanda da’alama bata shiryawa yinsa ba sam. Wani irin matsanancin tausayintane yaji ya k’ara narkar da zuciyarsa, tare kuma da wani sabon shauk’in sonta, Saidai kuma amma ayau sam bashi da zab’i domin yayi imani cewa har abada ba kowani so bane yake iya zama tsuntsu. Asanyaye ya k’arasa gaban d’aya daga cikin bedside drawer’n dake gefen gadon su, duk da yanda kirji da kuma zuciyarsa ke tsananin bugawa amma hakan bai hanashi daurewa ba, ahankali ya jawo murfin drawer’n tare kuma dasa hannunsa aciki ya d’auko wani littafi wanda samansa ke d’auke da biro. Idanu ya tsurawa littafin dake hannun nasa kusan na mintuna 10 kafun ya dawo da kallonsa ga Laylerh wacce ke kwance ak’asa tana bacci. Wani irin kallo yake mata wanda ke bayyana sabuwar soyayyarta dake ratsa kowani kofa na jikinsa, Tabbas yanayiwa Laylerh so mai tsanani, irin wanda a kullum yake fatan yin rayuwa da ita. Yaya zaiyi? Tayaya zai bari saboda shi kawae komai ya lalace? Tabbas abunda yake shirin aikatawa yanzu cutarwane amma bashi da wani zab’i wanda ya wuce hakan. Asanyeye ya janye kansa daga kallonta. Wani irin rumtsewa yayiwa idanunsa adaidai lokacin daya d’aura hannunsa dake rik’e da abun rubuta akan farar takardan dake gabansa, ahankali ya shiga sarrafa hannunsa dake rawa wajen rubuta abundake zuciyarsa akan takardan. Adaidai lokacin daya kammala rubutun nasane kuma wasu irin hawaye masu tsananin zafi suka fito daga cikin idanunsa tare da d’iga akan takardan. *(Wayyo Allah Na Najeeb😭😭 kome ya aikata haka oho gaskiya I’m so sad 😞 son Najeeb yasa bazan iya karasa page d’innan yau ba. 1/3/2021 Najeeb first March abunda zaka mana kenan😭😭)* *8:23 pm* 3/3/21, 9:07 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Written By* fatymasardauna #hearttouching *Chapter 61* Rubutun da yayi akan farar takardar ya tsurawa idanunsa wanda suka kad’a sukayi wani irin ja tamkar wanda aka watsawa garin barkono acikinsu, yayinda yakejin wani irin zafi da kuma k’una acikin zuciyarsa, lallai Tabbas yasan yayi abunda zae damesa, saidai kuma bashi da wani zab’in daya wuce hakan, k’warai yasani daga yanzun har zuwa wasu lokuta masu tsawo zai cigaba da ruskar kansa acikin bak’inciki, hak’ik’a zuciya da kuma gangar jikinsa suna matuk’ar son Laylerh so kuma ba nawasa ba, saidai akwae wani abu daya tabbatar da cewa rashin kammaluwansa babban matsalane sannan zai iya haifar da kowani irin matsala. Janye idanunsa daga kan takardar yayi tare dasa hannunsa ya nannad’e ta, cikin wani irin rashin kuzari da kuma alhinin dake cike azuciyarsa, ahankali ya zame tare da zama abakin had’add’en gadon su, idanunsa wanda sukayi matuk’ar ja ya d’aura akan Laylerh’n wanda har yanzu ke kwance ak’asa, duk da cewar kuma bacci take, amma time to time take sakin sheshshek’an kuka, wani irin kallo mai d’auke da tsananin shauk’i ya shiga yi mata, yayinda yakejin matsanancin tausayinta na ratsa duk kowani gaba da sashi na jikinsa, zuciyarsa tayi matuk’ar karyewa, kana rauninsa ya bayyana afili, shikansa baisan cewa son da yake yiwa Laylerh’n ya girma azuciyarsa har haka ba, ya sani kuma k’warai cewa yayi babban asara, domin abune dayake abayyane cewar bazae tab’a samun mace kamarta ba, koda ma ace zai samu to da matuk’ar wahala, ba kuma sak irinta ba saidai maiyanayinta, saboda yayi imani cewa Laylerh’n ta dabance acikin sauran mata, komae nata mai kyau da tsari ne, k’warai yasan cewa zaiyi missing abubuwa da dama, musamman kallon kyakkyawan fuskarta, da kuma had’add’iyar surar jikinta, uwa uba shagwab’a da kuma yanayin yarintarta. Hawayen da suka sauk’a akan fuskarsa batare daya san da sauk’owarsu ba yayi saurin sa hannu ya share. Jin kuma yanda zuciyarsa ke bugawa kaman zata faso k’irjinsa ta fitone yasashi janye idanunsa daga kan Laylerh’n, asanyaye ya shiga jujjuya ninkakkiyar farar takardar dake hannunsa, wanda awajensa abunda ke rubuce ajikin takardar yafi komae d’acin ji da gani, badon kuma yakai zuciyarsa nesa ba, to fa da har abada bazae tab’a iya rubuta hakan da hannuwansa ba. Tayaya zai fuskanci Laylerh da wannan abun daya aikata mata? baisan ayaya zata d’auki maganar tasa ba, baisan ma zata fahimta ko bazata fahimta ba. Abu d’aya kawae yasani shine yayi iya abunda zae iya, sannan baya kuma jin zai iya fuskantar ta fuska da fuska ya gayamata abunda ke rubuce acikin takardar, saboda ita yarinyace k’arama da sam baikamata ace ta fara fuskantar k’alubalen rayuwa tun daga yanzu ba, shekarunta kad’anne hakan yasa ba komae ne zata iya jurewa ba, batasan ya abun yake ba, sannan bata kuma san ya girmansa yake ba. Labb’an bakinsa masu kalan pink da suka bushe ya d’an taune, tare da had’iyan wani yawu mai d’acin gaske daya tsaya masa amak’oshinsa. Cikin yanayin dauriya da kuma son k’arfafawa kansa guiwa akan abunda yayi d’in ya mik’e tsaye, tare da d’aukan wani envelope dake ajiye asaman bedside drawer’n ya zura farar takardar aciki. Ahankali kuma cikin yanayin son kawar da damuwar dake shirin duk’ar dashi k’asa ya shiga taka k’afafunsa zuwa inda Laylerh’n ke kwance. Hak’ik’a da ace ayau kuma ayanzu zai bayyana zuciyarsa ga kowa to da dayawan mutane sai sun tausaya masa, amma kuma yasan cewa babu daman yin hakan, domin shi kansa shaidane duk yanda zuciyarsa kejin k’una, to abayan wata zuciyar take, wata zuciyar wanda ta share tsawon shekaru tana jiran cikar burinta, ta kuma samu rauni mai ciwo asanadin watsewan duk wani muradinta, zuciyar da tun asali aka halicceta da wani irin k’akk’arfan SO, wanda yake neman gusar da hankali da kuma tunanin maiyinsa. Tabbas abunda idanunsa suka gane masa kad’ai sun isa tabbatar masa da cewa aduniya bayan wannan soyayyar babu wata, haka kuma bayan wannan muradin babu wani sauran muradi daya rage, kana idan wannan burin bai cikaba to Tabbas har abada babu wani buri aduniya nasu da zae tab’a cika. Amatuk’ar sanyaye ya d’an ran k’wafo da kansa zuwa gareta, bayan ya tsayar da duk wani zancen zuci da zuciyartasa keyi. Haka yakejin tausayinta tamkar zai fasa zuciya da k’irjinsa. Hannayensa duka biyu yasa asanyaye ya d’agota cad’ak, tamakar wata y’ar baby daga kwancen da take, still kuma idanunsa wanda suke cike da ruwan hawaye na kanta, ya k’arasa da ita kan gado, tare da shumfud’eta atsakiyar gadon. Sauk’e ganinsa kuma da yayi akan kyakkyawar fuskarsa ne yasashi kasa d’auke idanunsa daga gareta, tayayama zai iya jurewa? tayaya zai iya fasalta rad’ad’i da kuma k’unan da zuciyarsa keyi? kafun yanzu takasance wani b’arine na rayuwarsa, amma yanzun fa? shikenan ya rasata? yarasa Laylerh yarinyar da kowanni kwanan duniya sake jin sonta yake acikin zuciyarsa, tayaya zata d’auki abunda yayi mata? yasan dolene zataji zafi, saboda hakan da yayi tamkar bud’e mata sabon shafine dake cikin babban littafin k’addararta. “I’m sorry Laylerh! I’m very sorry...!!â€? Ya fad’i hakan abayyane, cikin kuma muryarsa dake shaking take kuma bayyana tsananin damuwar da yake ciki. Batare kuma da yayi aune ba yaji wani abu mai d’umi nabin fuskarsa, wanda ko tantama babu yasan cewa hawayene ke fita daga idanunsa, kasancewar kuma yayi kusa da Laylerh’n ne yasa hawayennasa ke d’iga akan fuskarta, ganin hakan da yayine kuma yasashi sake matsowa ahankali ya kawo fuskarsa gab da nata, cikin sanyi da damuwa ya d’aura bakinsa adaidai saitin forehead d’inta, batare da tunanin komae ba kuwa ya sauk’e mata wani irin hot kiss, dake bayyana condition d’in da mutum ke ciki. Bayan yayi kissing forehead d’innata ne kuma, ahankali yad’an gangaro da kansa, wanda hakan yasa fuskarsu daidaita dana juna, har takai ga hancinsu ya had’e awaje d’aya. Amatuk’ar sanyaye ya d’aura labb’an sa akan nata jajayen l’abban, atake kuma yayiwa lips d’innata wani irin kiss,wanda sanyi da kuma k’arfinsa yasa ta sauk’e k’akk’arfan ajiyar zuciya, saidai kuma kasancewar bacci take yasa bata bud’e idanunta ba. Shikuwa Najeeb idanunsa ya k’ura mata yanajin sabon soyayyarta na sake shiga zuciyarsa. Hak’ik’a ayanzu bazae tab’a iya misalta yanayin da yakejin kansa aciki ba, domin da ace yau shid’in ya kasance ajinsin mata ne ba maza ba, to da babu abunda zae masa shamaki da zama dirshan ya rera kuka har sai yaji zuciyarsa ta samu salama, amma kasantuwarsa Namiji ya zame masa tilas ya shanye hawayensa, duk da zaiyi kukan zuci amma dole ya tausashi kansa. Janye jikinsa yayi tare da nesanta kansa daga gareta, ahankali ya soma jan jikinsa baya, saidai kuma har yanzu ya kasa d’auke idanunsa daga gareta, ahaka har ya k’arasa bakin k’ofar fita daga d’akin. envelope d’in dake hannunsa ya yiwa wani irin rik’o tare da juyawa cikin sauri ya fice daga cikin d’akin. *M.JAY* Zabgegiyar kwalban wine d’in dake hannunsa yake ta faman jujjuyawa, kusan sama da mintuna 10 kenan yanzun da yake ta faman abu d’aya. Asanyaye kuma akaro na barkatai ya sake sauk’e idanunsa akan kyakkyawan hoton da gaba d’ayansa ya cika gaban screen na laptop d’in companyn Apple dake gabansa, sosae ya k’urawa hoton idanu wanda akullum kuma akoda yaushe baya tab’a gajiya da kallonsa, sam koda da second d’ayane kuwa idanunsa basu tab’a jin gajiya da kallon kyakkyawar fuskar wanda ke jikin hoton ba, haka kuma ko wani bugun zuciyarsa da tunaninta yake tafiya. Idanunsa masu kala da jin bacci ya lumshe tare da kai hannunsa ahankali ya shafa gefen cikinsa dake d’auke da k’awaraccen rubutu da akayisa kaman zanen tattoo. Ci gaba da shafa gefen cikin nasa yayi yayinda kuma ahankali idanunsa keyi masa gizo da kyakkyawar fuskarta, yanayin hakanne kuma yasashi shagala dajin wani irin kasalalllen bacci. Bisa dole haka ya kwanta flat akan had’add’en carpet d’in dake malale agaban makeken gadonsa, still kuma idanuna alumshe yana me sake shafa gefen stomach d’insa dake dauke da zanen rubutun sunanta. Fitowarsa daga cikin part d’in nasune yasashi soma tafiya ahankali, tare kuma da aro jarumta ya sakawa kansa, gudun kada wani ya fahimci zallar yanayin damuwar dake kwance akan fuskarsa. Isowarsa bakin k’ofar sashin Oum Ayush da yayine kuma yasashi tsayawa, tare dasa hannunsa ahankali yayi knocking k’ofar, shirun da yaji babu amsa ne kuma yasashi ci gaba da knocking door d’in. Oum Ayush kuwa dake cikin kitchine jin ana knocking k’ofar falonne ya sata fitowa daga cikin kitchine d’in, cikin yanayi na d’an d’aga murya ta yanda za’a jiyota, ta bawa mai knocking door d’in daman shigowa. Najeeb dake atsaye kuwa jin anbashi daman shigowa ne, yasa ahankali ya murd’a handle d’in k’ofar ya shigo. Ganin Najeeb d’inne kuma yasa Oum Ayush dake tsaye ta fad’ad’a fari’arta, cikin sakin fuska tace. “Najeeb sannu da zuwa, ae da ma shigowa kayi kai tsaye basai kayita knocking ba.â€? Murmushin daya k’ak’alo da k’yarne ta d’an bayyana, cikin yanayin sanyi yace. “Bansan bakya kusaba Oum Ayush shiyasa.â€? Kai Oum Ayush d’in ta d’an jinjina, still fuskarta d’auke da murmushi tace. “Badamuwa Ina kabaro Sarauniyar kuka da kuma shagwab’ar taka?â€? Kansa ya sunkuyar k’asa tare kuma da kasa k’arasowa cikin falon, domin tambyar da Oum Ayush d’in tayi masa ba k’aramin karyar masa da zuciya tayi ba. Oum Ayush kuwa jin Najeeb d’in bai amsa mata bane yasa ta d’ago kai ta kalleshi. Lokaci d’aya kuma taji k’irjinta yayi wani irin bugawa, domin kuwa tsananin damuwa ta hango kwance akan fuskarsa dama duk wani yanayinsa. “Najeeb lafiya kuwa? Mai yake faruwa naga duk yanayin ka ya sanja?â€? Tayi masa tambayar tana meyi masa kallon tsab, yayinda kuma wani sashi na zuciyarta ke wani irin bugawa. Najeeb da gaba d’aya gabb’an jikinsa ke rawa, asanyaye ya k’arasa shigowa cikin falon tare da neman waje ya zauna, saidai ya kasa koda d’aga ido ya kalli Oum Ayush d’in, saima shiru da yayi tare dasa tafukan hannayensa duka biyu ya rufe fuskarsa. Hakanne kuwa yasa zuciyar Oum Ayush tsananta bugawa, hankalinta tashe tace. “Please Najeeb ka fad’amin meyake faruwa? Ko wani abune ya samu Laylerh? dan Allah Ka fad’amin, domin yanayinka ya d’agamin hankali!â€? Yanayin yanda ta k’are maganar cikin matsanancin damuwane yasa Najeeb d’an numfasawa, tare da zame hannayensa dake kan fuskarsa, araunace ya kalli Oum Ayush d’in, cikin kuma son bawa kansa k’warin guiwa da iya jure damuwa, murya asanyaye yace. “Bansan tayaya zan iya jure k’alubalen da zae fuskanceni anan gaba ba Oum Ayush, akullum a kuma koda yaushe nasan cewa Laylerh tana da damuwa, duk da kasancewarta k’aramar yarinya kuma, amma kullum cikin kuka take, da yawan lokuta nakan gane cewar akwae abunda ke damunta, yakan hanata sukuni, sannan koda yaushe tunani take, sometimes murmushinta yakan zamo na dole ne, sannan tana da matsanancin rauni sosae, Bansan tayaya zata kalli abunda na aikata agareta ba, saidai nasan nan aikata hakan dan wata manufa ba, ahak’ik’anin gaskiya kawae nayi abunda nake ganin shine daidai!â€? D’an tsagaitawa da maganganun nasa yayi ta hanyar Jan wani irin doguwar ajiyar zuciya. Idanunsa wanda suka jajur ya rumtse tare dasa hannu ya kama chest d’insa, still asanyaye yace. “Ina Son Laylerh sosae, saidai kuma amma yafini sonta, duk yanda nakai ga jin soyayyarta azuciyata shi fiye da haka yakeji, babu wani irin son da yake mata, domin ba wae sone na haka kawae ba, ba irin sone da kowa ya sani ba, Tabbas ni zan iya rayuwa babu Laylerh, domin ko ada daban santa ba nayi rayuwa cikin farinciki, shi kuma fa? bazae tab’a iya rayuwa babu itaba Bawae don soyayya kawae ba, no itace numfashinsa,rayuwarsa, dama zuciyarsa, duk yanda wani zai sota aduniya bayan son da yake matane, soyayyarta halittace acikin jikinsa da akayi wanda har abada bazae gushe ko goge ba, sannan halittace dake girma tana hab’aka akowanni rana bayan kuma kowani minutes, kullum zafi yakeji azuciyarsa haka itama, because zuciyoyin nasu abu d’ayane basu da banbanci da juna, mafarkinsa itace haka itama mafarkinta shine, ita cefa duniyarsa Oum Ayush, itace komae nasa, ban tab’a ganin irin wannan soyayyar ba, wanda komae zai faru da junansu sai d’aya daga cikinsu ya sani, Tabbas na yarda cewa Laylerh zanen k’addarar muce muduka biyun, amma nasa k’addarar tafi k’arfin nawa, hasalima Ba za’a tab’a had’awa ba, domin ni soyayyar Laylerh azuciyata kawae take, shi kuma soyayyartata rayuwarsace gaba d’aya, acikin jijiya da jini b’argo dama duk gangar jikinsa take, bazan iya jurewa hakanba Oum Ayush, domin sabodani kawae koda yaushe zunubi ake rubuta musu, aduk lokacin da sukayi tunanin juna, ko sukayi imagine junansu, k’warai nayarda cewa k’addara babu yanda bata juyawa rayuwar d’an adam, sannan na kuma yarda cewa komae rubutaccene kuma tsararrre, Dan haka ina fatan abunda na aikata ya zamo silar farinciki arayuwarsu!â€? Ya k’are maganar cikin dauriya da kuma tsananin cijewa, asanyaye kuma ya d’an durk’usa agaban Oum Ayush wanda tunda ya fara maganganun nasa ta zuba masa ido. “Kiyi hak’uri Oum Ayush bani da wani zab’i ne wanda ya wuce hakan, Dan Allah Na mik’a komae ahannunki kiyi k’ok’ari wajen ganin Laylerh bata sake shiga k’unci ba, Sam bansan tayaya ne zan fara fuskantarta da wannan maganan ba, Brain d’inta k’aramane saboda haka sam bai kamata na hautsuna tunaninta ba, sannan ban barta dan banasonta ba, Ina sonta sosae wallahi, koda yaushe da soyayyarta acikin zuciyata, yafini buk’atar ta sosae, domin akan fatar jikinsa ma sunantane arubuce, please Oum Ayush idan tayi kuka ki rarrasheta, domin ayanzu ita d’in batawa bace!!!â€? Wasu irin hawaye masu tsananin zafin gaskene suka silalo daga kan kumatunsa, wanda kuma hakan ya tilasta masa rumtse idanunsa, asanyaye ya mik’awa Oum Ayush envelope na takardar dake hannunsa. Sosae jikin Oum Ayush ya d’auki rawa alokacin da ta sa hannu ta karb’i envelope d’in da Najeeb d’in ke mik’o mata, wanda kuma tun fara maganarsa zuciyarta ke tsinkewa, ga kuma kirjinta dake bugu da k’arfi, tuni kuwa hawaye sun cika idanunta, domin tunkafun ya ida maganganun nasa ta fahimci komae. Da hannayenta dake matsanancin rawa ta bud’e envelope d’in tare da zaro y’ar white paper’n dake ciki. Duk da tafahimci takardar ta meyene amma kuma tun kafun ta bud’e ta taji wani irin bugawan zuciyar dayasa tayi saurin ambaton sunan Allah. Ahankali kana jiki amace ta warware takardar. Abunda idanunta suka gane matane kuma yasa tayi saurin rumtsesu, take kuwa hawayen dake cikinsu suka shiga fitowa wasu na Koran wasu kamar an kunna famfo, cikin wani irin matsanancin tashin hankali, tsoro, fargaba, da kuma wani yanayi na daban wanda batasan dame zata k’irasa ba ta ambaci kalmar. “Innalillahi Wa Inna Ilaihirraju’un!!â€? *3/3/2021* *8:12 pm* 3/5/21, 5:50 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna *Not editing* *Chapter 62* Idanu Oum Ayush ta rumtse tare kuma da cigaba da ambatan kalmar “Innalillahi wa inna Ilaihirraju’un!!â€? Domin kuwa ba kad’anba abunda idanuwanta suka gane mata ajikin farar takardar da Najeeb d’in ya bata suka d’aga mata hankali. Sake k’urawa rubutun dake cikin takardar idanu tayi, aranta tana mejin wani irin k’unci da ciwo. Cikin muryarta kuma dake d’an carkewa kana kuma yake bayyana alaman tsananin damuwar da ta samu kanta aciki tace. “Yah Subahanallah Najeeb ka saki Laylerh? meyasa zaka aikata haka batare da neman shawara ba? Meyasa Najeeb, shin bakasan cewa Allah Bayason saki ba, duk da kasancewarsa halak, Why Najeeb why kayi gaban kanka? Menene fa ida da kuma ribar aikata hakan? sannan da wacce irin hujja ka aikata hakan? shin ma kasan ya ciwo da kuma d’acin maida y’a mace bazawara yake? Musamman ga Laylerh yarinya k’arama?â€? Idanunsa wanda suke zubar da k’walla ya bud’e, tare da d’ago kansa ya kalli Oum Ayush d’in, cikin wata irin sassanyar murya yace. “Ko kad’an banyi niyar tozarta Laylerh ba Oum Ayush, saboda Ina sonta, inasonta sosae, amma ya zanyi da soyayyar da takewa Maleek? yaya zanyi? soyayyar Maleek dake zuciyarta ya wuce duk wani gaban kwatance Oum Ayush kuma kema kinsan hakan, a iya soyayyarta kad’ae ya kamata na saudakar, balle kuma idan akaje ga zuciyar Maleek, wallahi nayi rantsuwa Oum Ayush bazan kumayi kaffaraba akan soyayyar da Maleek da Laylerh keyiwa juna, Bawae soyayyace da kowa yasani ba, wata irin halittace dake sake ginuwa akowacce rana, k’arfinta da kuma zafinta ya wuce duk yanda kowa ke zato, tayaya zan zama silar katse fara da burinsu? tayaya zan zamo maison kae haka? Tayaya? Bazan iyaba Oum Ayush domin Maleek ne kwance acikin zuciyar Laylerh bani ba, nayarda zan jure rashinta domin kuwa haka Allah Ya tsaramin, sannan inason dan Allah Ki fahimci cewar ban aikata hakan dan banasonta ba, Inason Laylerh wallahi Inasonta sosae!!!â€? Kasa k’arasa maganan nasa yayi asakamakon wani irin yanayin da yaji ya samu kansa aciki, hakanan yaji kamar ya fashe da kuka, saidai kuma amma yasan yin hakan tamkar maida kansa rago ne. Kansa ya d’an shiga girgizawa ahankali batare kuma daya sake cewa komae ba ya juya ya nufi hanyar fita daga falon gaba d’aya. Tsura masa idanu Oum Ayush tayi har ya gama ficewa daga cikin falon. Still wasu irin hawaye masu zafine suka silalo daga cikin idanunta, yayinda acikin zuciyarta takejin wani irin matsanancin tausayin Laylerh’n na k’ara shiga jiki da jininta, Tabbas bazatace Najeeb baiyi Namijin k’ok’ari ba, domin ba kowane zaiyi irin abunda yayi ba, saidai kuma har acikin zuciyarta bataso ya gano matsananciyar soyayyar dake tsakanin Laylerh da Maleek d’in ba. Jikinta amatuk’ar sanyaye ta maida paper’n cikin envelope d’in tare dasa hannayenta duka biyu ta tallafi hab’arta, Allah Yasani har acikin zuciyarta bataji dad’in sakin da Najeeb d’in yayiwa Laylerh’n ba, domin saki ko yaya yake bashi da dad’i, duk dama tasan cewar hakan mafarin k’arshen wata matsalace, amma koba komae ayanzun Laylerh’n ta zama wata k’aramar bazawara, tunda auren nasu ko wata d’aya bai wuce ba, tasan kuma zuwa yanzu baza’ace wani abu na auratayya bai tab’a shiga tsakanin Laylerh da Najeeb d’inba. Acan b’angaren Najeeb kuwa lokacin daya fito daga falon Oum Ayush d’in direct sashinsu ya nufa, yayinda gaba d’aya jikinsa ke asanyaye, Sam bayajin dad’in zuciyarsa, abubuwa tare da damuwa duk sun masa yawa. Ahankali ya murd’a handle d’in k’ofar d’akin, cikin kuma muryarsa wanda bata fita da kyau yayi sallama, tare da kutsa kansa ciki. Yana sa kansa acikin d’akin kuwa idanunsa suka sauk’a akanta, har yanzun dae kwance take kamar yanda ya tafi ya barta. Idanunsa masu d’auke da rauni ya lumshe, tare kuma da jingina bayansa ajikin k’ofar shigowa d’akin. Wani irin sabon sonta da k’aunarta yakeji na ratsa zuciyarsa, hak’ik’a baesan cewa yanason Laylerh’n ba saida ya rabu da ita. Inama da ace k’addara zata barshi ya rayu da ita rayuwa tahar abada, Inama da ace babu Maleek acikin rayuwar ta, lallai tabbas da yasan watarana zata soshi, domin zaiyi iya k’ok’ari wajen ganin ya koya mata sonsa, saidai amma kuma Ina, k’addara ta riga fata. Ahankali ta d’an soma bud’e idanunta, wanda suka d’an k’ank’ance saboda kukan da tayi, bud’e idanun nata da tayi kuwa, yayi daidai da soma sarawa’n kanta, wani irin sassanyar ajiyar zuciya ta sauk’e, tare dakai hannunta ahankali ta rik’e kannata, cikin kuma son samawa kanta kuzari ta tashi zaune. D’an soma k’arewa d’akin nasu kallo tayi, batare kuma da tayi zato ko tsammaniba ta sauk’e idanunta akansa, saboda har yanzu tsaye yake ajikin k’ofar still kuma idanunsa alumshe suke, wanda kuma hakan alamane dake nuna cewar yayi nisa acikin duniyar tunaninsa. Cikin yanayin mamaki take kallonsa domin bata tab’a ganinsa acikin irin wannan yanayin ba, saidai kuma yanayin yanda taga yayi tsayuwar nasane ya d’auki hankalinta, domin yayi kyau sosai, sai yanzunne kuma ta lura da shigar maroon jumper’n dake jikinsa, da kalanta ya bayyana kyau da kuma hasken fatarsa, Ji kuma da tayi ajikinta cewar yana cikin damuwa ne, yasa taji zuciyarta ta karye. “Yah Najeeb!!â€? Ta k’ira sunansa murya amatuk’ar sanyaye. Jin amo da kuma sautin muryarta da yaji acikin kunnuwansane ya sashi dawowa daga duniyar tunanin daya fad’a, ahankali kuma ya bud’e idanunsa ya sauk’esu akanta. Sanadiyar hakan kuwa yasa idanunsu suka fad’a cikin na juna. Wani irin murmushin daya bayyana asalin kyawun fuskarta tayi, cikin kuma murya mai d’auke da sakalci tace. “Tunanin mekakeyi? yanda zaka d’auko Dr yamin injection ko?â€? Idanunsa da suka ciko da k’walla ya sunkuyar k’asa tare da d’an jinjina mata kai, cikin son b’oye matsanancin damuwarsa akanta yace. “Eh saboda naji har yanzu jikinki da zafi, bansan sai yaushe ne zakiyi lafiya ba Laylerh!â€? Ya k’are maganan yana me kokarin maida k’wallan dake cikin idanunsa. D’an k’aramin bakinta ta turo gaba, tare da sake shagwab’e fuska, asanyaye tace. “Yanzu ma fa kaena ciwo yakeyi Yah Najeeb, please kabani ruwa nasha.â€? Jin abunda ta fad’ane ya sashi sake d’ago kae ya kalleta, ganin ita d’inma kallonsa takeyi ne yasashi sakar mata wani murmushi mai kama dana k’arfin hali, anutse ya k’arasa gaban maidaidaicin fridge d’in dake cikin d’akin, bud’e murfin fridge d’in yayi tare da dauko bottle water marar sanyi ya nufo gareta. Koda ya iso jikin gadon kuwa mik’a mata goran ruwan yayi, tare da matsawa can gefe ya tsaya. Itakuwa kafa goran ruwan tayi abakinta har saida tasha fiye da rabin ruwan kafun ta janye bottle d’in daga bakinta. K’afafunta ta zuro k’asa tare da mik’ewa tsaye. Najeeb kuwa ta gefen idanunsa yake kallonta, harta gama zura bedroom slippers ak’afanta. Kaitsaye ta nufi hanyar toilet, hakanne kuma ya bashi daman d’ago kansa ya bita da kallo, har saida ta shige cikin toilet d’in kuma kafun ya d’auke idanunsa daga kanta. Wani irin sassanyar murmushi mai d’auke da ma’anoni daban daban yayi, saboda har acikin ransa yana buri da kuma fatan da cewa da auren wata macen kamarta. Laylerh kuwa tana shiga toilet d’in fuskarta kawae ta wanke, tare da juyowa ta fito, wanda tayi hakanne kuma saboda yanda takejin idanunta da sukayi nauyi, da kuma ganinta dake d’an disashewa. Jin bakinta ba dad’ine kuma yasa direct ta k’arasa wajen da take ajiye hand bags d’inta, d’aya daga cikin handbags d’in ta d’auka tare kuma da zuge zips d’insa ta ciro wani babban chocolate. Akan madaidaicin stull din dake gaban dressing mirror ta zauna, tare da b’are ledan chocolate d’in ta soma gutsura da kad’an kad’an. Ganin hakan da yayine kuma yasashi d’an soma matsowa inda take ahankali, duk da cewar kuwa k’irji da zuciyarsa bugawa suke sosae amma haka ya cije, tare da soma yunk’urin bawa kansa k’arfin guiwa. “Laylerh!â€? Ya k’ira sunanta cikin wata irin muryarsa da yayi sanyi sosae. Yanayin yanda amo da kuma sautin muryartasa suka fitane kuma yasa Laylerh tayi saurin d’ago kai ta kalleshi. Saidai kuma wani bak’in abu da ta hango acikin idanunsa yasata saurin sadda kanta k’asa. Ahankali ya d’an rank’wafo gareta tare da d’aura hannayensa akan shoulders d’inta ya mik’ar da ita tsaye. Wani irin kallo ya shiga yi mata da idanunsa wanda sukayi jajur, kana awahalce yace. “I’m very sorry Laylerh!!.â€? Yanayin yanda yayi maganar da muryarsa wacce ke bayyana abunda ke kwance acikin zuciyarsa ne, ya tilasta mata d’ago kae ta kalleshi, cikin mamaki, da kuma wani bak’on yanayin da ta samu kanta aciki tace. “Yah Najeeb Sorry for what?â€? Idanunsa ya d’an lumshe, tare da sake matse shoulders d’inta dake cikin hannayensa, asanyaye yace. “Saboda nayi wani abu da bansan ya zaki d’aukesa ba, bansan tayaya zaki fuskanci hakan ba Laylerh, amma nayi imani cewa hakan shine mafita, sannan banyi komae dan na cutar dake ba Laylerh, please forgive me!!!â€? Ya kai k’arshen maganan nasa yana me had’e tafukan hannayensa waje d’aya, alaman rok’o. Idanunta wanda suka d’an soma sanja kala ta zuba masa, domin sam ta kasa sanin inda kalaman nasa suka dosa. “Inasonki Laylerh, inasonki sosae, amma sonda yake miki ya zarce nawa, buri da kuma fatansa akanki ko kad’an ba yankakke bane, yana miki son da daga shi, babu wani wanda yake miki irinsa, ni a iya zuciyata kawae nakejinki Laylerh amma shi ked’ince gaba d’aya rayuwarsa, I don’t mean to hurt you Laylerh, just kawae na yarda komae yazone amatsayin k’addara, amma bazan tab’a mantawa dake ba Laylerh har abada....â€? Kasa k’arasa maganan nasa yayi saboda yanda zuciyarsa ke wani irin tsalle da kuma harbawa. Laylerh kuwa idanu kawae ta tsura masa sam ma bata fahimtar ma’anar abu ko d’ayane daga Cikin kalamansa, babban abunda ya jefata acikin rud’ani da mamaki kuma shine hawayen da idanunta ke gane mata kwance acikin idanun Najeeb d’in, abunda ko sau d’aya bata tab’a gani ba. Hakanan taji yanayin yazo mata wani na daban, yayinda jikinta ke bata cewar Lallai tabbas akwae abunda yake faruwa. “Yah Najeeb meyasa.....â€? “Shiii!! Karkice komae please, sannan kije Oum Ayush na k’iranki.â€? Ya katseta daga maganar da takeyi d’in ta hanyar fad’an haka. Idanunta dake kansa ta d’an lumshe tare da dafe daidai saitin zuciyarta da takejin tana bugawa akai akai. Yayinda wani abu maikama da tsoro da kuma fargaba suka lullub’e ta, wanda duk batasan dalilin faruwar hakan ba. Ahankali ta rab’a tagefensa tare da soma tafiya ahankali dan zuwa amsa k’iran da yace Oum Ayush nayi mata. Idanu ya tsura mata tare dasa hakw’aransa Ya cije labb’ansa da k’arfi. Ganin kuma ya isa bakin k’ofar fita daga cikin d’akinne yasashi d’an d’aga murya. Sunanta ya k’ira, da wani irin tone din da bata tab’a jinsa atattare dashi ba. Duk da cewar kuwa harta kai jikin k’ofar amma hakan bai hanata tsayawa ba tare da juyowa ta fuskancesa. Murmushin da yafi kuka ciwo da kuma kallo mai d’auke da tsananin shauk’i yayi mata, hannayensa ya hard’e akan k’irjinsa, cikin silently mood yace. “Please ki kula da kanki, kada kiyi kuka mai yawa, sannan kuma karkiyi fushi mai yawa!â€? Duk da batasan cikakken ma’anan kalaman nasa ba amma haka tasamu kanta da jinjina masa kai, kana asanyaye ta murd’a handle d’in k’ofar ta fice. Haka ta nufi sashin Oum Ayush zuciyarta cike da fargaba, duk yanda kuma taso daidaita nutsuwarta, ta yanda k’wak’walwarta zata bata ma’anonin kalaman Najeeb d’in abun yaci tura. Isowarta sashin Oum Ayush d’inne kuma yasa ta tsaida tunaninta waje d’aya tare da murd’a handle d’in k’ofar ta shiga. Najeeb kuwa ganin fitan Laylerh’nne yasa shi d’aukan wani big trolly ya zuba kayansa dama duk wani abu dayasan zae buk’ata aciki, passport d’insa ya d’auka sai kuma car key da wayoyinsa. Kaitsaye ya fice daga cikin d’akin. Koda ya fito compound d’in gidan kuwa babu kowa sai y’an tsirarun soldiers d’in Maleek dake shawagi suna kewaye gidan. Cikin motarsa k’irar Mercedes benz C300 2018 ya saka trollyn nasa, batare da tunanin komae ba kuwa ya shiga cikin motar tare dayi mata key, bayan kuma mai gadi ya wangale masa gate d’in gidanne ya cilla hancin motar tasa waje. Daga gidan kuwa kaitsaye office d’in Abbou Jaheed ya nufa, domin kuwa da bakinsa yakeson sanar masa abunda ya aikata batare da tambaya ko neman shawaran kowa ba, yana kuma da hujja akan hakan koda kuwa duk mutanen duniya zasu k’alubalance sa. Ci gaba da kutsowa cikin falon tayi saidai kuma abunda idanunta suka gane matane yasa ta tsayawa, tare da kafe Oum Ayush d’in da idanu. Wanda tun da Najeeb ya tafi yabarta take ahaka, ta zuba tagumi da duka hannayenta biyu, kallo d’aya zaka mata kafahimci kuma cewar tana cikin damuwa. “Oum Ayush!â€? Laylerh’n ta k’ira sunanta adaidai lokacin da ta k’araso tsakiyar falon. Amon sautin muryar Laylerh’nne kuma yasa Oum Ayush dawowa hayyacinta, wanda hakan yasa ta sauk’e idanunta akan Laylerh’n, take kuwa cikin sauri ta b’oye envelope d’in dake hannunta, tare da k’ok’arin samawa fuskarta fake smile wanda zata yak’i duk wata tambaya da Laylerh’n zata zo mata dashi. Cikin kuma son kauda tantama acikin zuciyar Laylerh’n tace. “Na’am Laylerh yaushe kika shigo?â€? “Yanzu na shigo, amma Oum Ayush meyake faruwa naganki ahaka? Kodai jikin Yah Maleek ne ya sake tashi!!â€? Ambatan sunansa kad’ae da tayi acikin maganar nata shiya raunata duk wani gab’a dake jikinta, saboda dama shid’inne acikin mine d’inta. Baga ita ba kuma harga Oum Ayush d’in jin da tayi Laylerh’n ta ambaci sunan Maleek shi ya k’ara sanyaya mata jiki, har takai ga damuwar ta ta bayyana k’arara. Tabbas sai ayanzunne tasake hango abunda Najeeb ya hango, shin ma tayaya zai iya jurewa yanda Laylerh’n ke mu’amalantuwa da sha’anin Maleek d’in? kowani magananta d’aya fa da zatayi akansa ne, komae shine, shine acikin zuciyarta, tunaninta dama jinin jikinta. Itakuwa Laylerh zuciyartace ta sake karyewa musamman da taga yanda Oum Ayush d’in ke kallonta bata ko d’auke ido. “Please Oum Ayush meyake faruwa? Yah Najeeb yace kina k’irana, Dan Allah idan wani abune yasake samun Yah M.jay ki fad’amin please!!!â€? Ta k’are maganar cikin yanayin magiya, lokaci d’aya kuma hawaye suka cika idanunta. “Ba abunda ya sake samun Maleek, hasalima yana nan lapia.â€? Ta fad’i hakan dan son samawa zuciyar Laylerh’n nutsuwa. Amma kuma sam Laylerh bataji zuciyarta ta gamsuba, saidai babu yanda ta iya, asanyaye tace. “Yah Najeeb yace kina k’irana.â€? Kai Oum Ayush d’in ta jinjina alaman “Eh.â€? Duk da kuwa tasan bata fad’i hakan ba, amma saitaji wani irin tausayin Laylerh’n ya lullub’e zuciyar ta. Wanda Hakan yasa taja wani irin dogon numfashi, tare da d’an matsawa ta kamo hannun Laylerh’n ta zaunar da ita akan kujeran dake kusa da nata. K’warai so take Laylerh’n ta fahimci abunda zata fad’a mata, duk da cewa kalaman dake bakinta suna da nauyi sosae amma ya zama dolene tasan hakan, Dan awannan lokacin ba amfanin b’oye saki ga wanda aka saka. hannunta tasa ahankali ta shafi fuskar Laylerh’n, cikin so da kuma bata k’warin guiwa tace. “Tabbas wata k’addarar takan zuwa da sauyi, sannan kyakkyawar k’addara takan zo ta kori mummuna, kamar yanda yake komae da zae faru da bawa rubutaccen al’amarine, wanda Allah Ya tsara masa tunkafun zuwansa duniya, ba kuma Lallai ne fahimtarka da kuma abunda ya sameka su zamo abu d’aya ba. Lallai littafin k’addara guda d’ayane amma yana da shafuka mabanbanta, yau idan mai dad’i ya bud’e, gobe watak’ila akasinsa ne zai bud’e.â€? D’an tsagaitawa da maganan nata tayi tare da sake damk’e hannun Laylerh’n dake cikin nata. “Kada zuciyarki ta tab’a karaya Laylerh, domin babu abunda yake dawwamemme, watarana abunda kakeso karasa, watarana kuma abunda kakeso ka samu sannan wanda bakaso ya nisanta dakai, idan kuma kasamu abunda bakaso yau, to hakan Bawae yana nufin cewa har abada bazaka tab’a samun wanda kakeso bane, ba akanki ba kad’ai dayawan matan duniya suna fuskantar wannan k’alubalen, hakan kuwa yakansa suji babu dad’i koda kuwa ba wanda suke so bane ya aikata musu hakan, Tabbas matuk’ar sunsan ciwon kansu dole zasuji babu dad’i, domin hakan kamar ragewar wata k’ima ne na y’a mace, banason kiyi kuka bakuma naso ki zargi kanki, kawae ki d’au k’addararki domin kuwa hakan ma wata damace.â€? Takai k’arshen zancennata adaedae lokacin da take sawa Laylerh’n envelope d’in Najeeb ya bata ahannunta. Tabbas k’wak’walwa da zuciyarta sun d’au charge, wanda hakan yasa ta kasa tantance ma’anar wasu maganganun. Envelope d’in dake saman hannunta ta tsurawa ido, yayinda takejin wani sashi na zuciyarta na bugawa. Ahankali ta bud’e envelope d’in tare da zaro takardar dake cikinsa ta warware. Take kuwa idanunta suka sauk’a akan d’an tak’aitaccen rubutun dake cikinsa. Tsurawa rubutun idanu tayi yayinda kuma take ware kowacce kalma d’aya bayan d’aya, ahaka har tazo kan kalmomin dake k’arshe wanda suke d’auke da harafin Divorce. Adaidai kan kalmar ta tsaida idanunta bata ko k’yaftawa, yayinda kuma duk wani tunanin da Brain d’inta keyi ya tsaya cak. Adaedae lokacinne kuma wayar M.Jay dake kan kunnensa ta zame ta fad’i k’asa, saboda jin maganan da Abbou Jaheed ke fad’a masa cewar yayi maza yaje sashin Oum Ayush yasanar da ita cewar kada ta sanar da Laylerh duk wani abu dake faruwa, sannan kuma kada ta bata takardar sakin da Najeeb ya rubuta mata. *5/March/2021* *1:15 pm* *(🙏🏻Kaena ya dau charge ne nashiga test sai yanzu na nutsu, amma dai kam yau nasha da k’yar🤢.)* 3/9/21, 4:41 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna *NOTE: Please and Please masu karantamin novels d’in LaylerhMaleek a YouTube kudaina tunda bada izinina kukeyi ba, sannan baku tambayeni ba kawae kuna ta karantamin book, bayan kuma kunsan book d’in ba free bane, abunda kukeyi ba abubane me kyau saboda a k’a ida duk abunda ba mallakinka bane kafun kayi amfani dashi yana da kyau kafara neman izinin mamallakin abun, kudaina please hakan bashida kyau tunda bawae izinina kuka nema ba, gaban kanku kukayi, banason abunda zaisa na samu matsala da mutane, so kuma kada kubari ku samu matsala dani🙏🏻* *Chapter 63* Kyawawan idanunta wanda cikinsu ke fitar da shek’in ruwan hawaye ta ci gaba da zubawa takardar dake hannunta, Tabbas idan tunanin ta zai isa ga k’wak’walwarta adaidai to hakan na nufin wani sabon babi ne ya sake bud’e mata, amma kuma saidai duk da abunda idanuwannata ke gani sam zuciyarta ta kasa aminta da hakan, kamar yanda gangar jikinta ya kasa aminta da daina b’ari. Wani irin sabo da kuma bak’on yanayin da bata tab’a jin kanta aciki bane ya rusketa, lokaci guda duk wani tunani da hasashenta suka tsaya, sai bugun zuciyarta dake ta faman harbawa kaman zuciyarta ta zata faso k’irjinta ta fito. Ahankali cikin kuma wani irin yanayi mai wahalar fassaruwa ta d’ago da kanta ta kalli Oum Ayush wanda itama d’in ta zuba mata ido. Kanta ta d’an girgiza tare kuma da had’e idanunta waje d’aya ta rumtse su, cikin wata irin murya dake bayyana tsananin rauni da kuma karyewar da zuciyarta tayi, asanyaye tace. “Oum Ayush da gaskene Yah Najeeb ya sakeni? Menayi masa wanda bansani ba? â€? Takai k’arshen maganan nata murya araunane wanda kuma hakan shiya bawa hawayen dake cike a idanunta daman gangarowa kan fuskarta. D’an numfasawa Oum Ayush tayi, cike kuma da tausayin Laylerh’n tace. “Komai muk’addarine daga Allah Laylerh, sannan kuma komae tsararrene saboda haka babu wanda ya isa sanjawa ko juya abunda yake rubutacce acikin littafin k’addara, ba ki kuma yiwa Najeeb komae ba Laylerh, ya sakeki ne kuma Bawae don baya sonki ko kaunarki ba, kawai k’addara da kuma lokacine yazo da hakan, saboda haka kiyi godiya ga Allah da kuma fatan ya sanja miki k’addararki izuwa ba madubin rayuwarki, bak’in ciki ya koma farinciki, fargaba, k’unci, damuwa, da kuma duk wani tsoro ya gushe, kisa aranki cewar hakan shine mafi alkhairi domin Allah baya zab’awa d’an Adam zab’i mafi muni, saidai idan shi d’an Adam d’in ya kasance mai sab’one, Tabbas amatsayinki na yarinya k’arama nasan zakaji ciwo da kuma k’unci acikin zuciyarki, amma duk da haka sawa kanki damuwa ba shine ba, da k’arfafawa kanki guiwa ne kad’ae zaki samu salama da kuma hanyar b’ullewa, kamar kuma yanda na fad’a miki tun farko ki d’auka cewa komae muk’addarine daga Allah, kuma shima aure rai ne dashi, da zaran lokacin mutuwarsa yazo to babu wanda ya isa ya hana.â€? Kanta tad’an soma girgizawa ahankali kuma cikin wani irin kuka dake so da neman k’wace mata tace. “Bansan meyasa k’addara take wasa da rayuwarmu ba Oum Ayush, duk da cewar kuma bani da yawan cin shekarun da zan iya fuskantar wasu manya manyan k’alubalen amma still k’addara bata jin tausayin tahowa gareni akoda yaushe, duk da cewar bani da confidence d’in da zanke kare kaina aduk yanda tazomin, bansan ya akeji ko me akeji idan akayi saki ba, koda wasa ban kuma tab’a kawowa araina cewar hakan zae faru dani watarana ba.â€? Idanunnata dake arumtse, wanda kuma har yanzu suke tsiyayar da hawaye ta bud’e tare da juyowa ta kamo hannun Oum Ayush ya zamana suna fuskantar juna. Kanta ta d’an sunkuyar k’asa kana araunace tace. “Kalmar Saki itace wacce take tabbatar da cewa aurena da Yah Najeeb ya k’are, itace kuma take nuna cewar bazan sake rayuwa da shi amatsayin miji ba har abada, meyasa Yah Najeeb zai aikata haka? bayan kuma yasan da cewar aduk lokacin da akayi saki sai al’arshin Ubangiji ya girgiza.â€? D’an tsagaitawa da maganan nata tayi tare da sake lumshe idanunta, sanadiyar hakan kuwa yasa wasu irin hawaye masu tsananin zafi suka sauk’a akan kyakkyawar fuskarta. Saidai kuma awannan karon d’in baga itaba harta Oum Ayush ta kasa danne hawayenta, saboda sosae takejin tausayin Laylerh’n. Ahankali tasa hannu na dama ta d’ago hab’ar Laylerh’n, cikin kulawa, da kuma tsananin tausayawa tasa d’ayan hannunta ta sharewa Laylerh’n hawayen dake kwance afuskarta. Kana murya atausashe tace. “Ko kad’an kada kiga laifin Najeeb Laylerh, domin kuwa yayi babban abunda ya dace, zuciyarsa cike take da alkahiri, sannan kuma shima bai aikata hakan ason ranshi ba, Tabbas yana da dalili.â€? Jin abunda Oum Ayush d’in ta fad’a cewar Najeeb d’in yana da daliline yasa ta d’ago kai ta kalleta, ahankali ta bud’e bakinta da niyar yin magana amma kuma sai taji wani irin kuka mai sauti ya k’wace mata, wanda kuma ta kasa iya control d’insa, bisa dole ta fad’a jikin Oum Ayush, cikin yanayin sanyi ta shiga rera wani kuka mai d’auke da ma’ana biyu, wanda kuma sam duk iya ganiyar mutum bai isa tantance ma’ana da kuma manufar kukannata ba, domin kuwa hatta ita kanta da take kukan batasan dalili da kuma hak’ik’aninsa ba. Domin kuwa ba kukane dake fitowa daga sassanyar zuciyarta ba, kukane kawae dake fita daga cikin Idanunta abayyane, yayinda kuma bad’ininsa ya kasance sanyi da kuma wani irin yanayi na daban. Ahankali Oum Ayush ta sa hannunta ta shiga shafa bayan Laylerh’n, cikin yanayin rarrashi kuma tace. “Kukan ya isa haka Laylerh please ki daina shi ko so kikeyine kanki yayi ta ciwo, tashi kije d’akina ki kwanta zansa atattaro miki duk wasu suturun sawa dama abubuwan buk’atarki dake wancan sashin, saboda yanzu maganar zama acikinsa ya k’are, haka Allah Ya tsara bazakuyi doguwar rayuwa da juna ba.â€? Ahankali ta janye jikinta daga na Oum Ayush d’in, kana cikin yanayin sanyi ta mik’e tsaye. Har yanzun dae ta kasa tsaida hawayen dake zuba daga cikin idanunta, hakanan takejin abun kamar al’amara, wae yau kuma yanzu haka babu auren Najeeb akanta, ayanzu ta zama ba matar aure ba, sab’anin awannin baya da suka shud’e da take amatsayin matar Najeeb. Asanyaye take taka k’afafunta wanda takejin sunyi mata sanyi sosae. “Laylerh.â€? Oum Ayush tak’ira sunanta cikin tausasawa. Wanda kuma sanadin hakanne yasa ta tsaya cak daga tafiyan da takeyi tare da juyowa ta kalli Oum d’in. Oum Ayush kuwa nannauyar ajiyar zuciya ta sauk’e tare da d’an kafe Laylerh’n da idanu, azahirin gaskiya nauyin tambayar da zatayiwa Laylerh’n takeji, saidai kuma amma ya zama dole tayi mata tambayar, musamman ayanzu da zuciyarta ta raya mata wani abu. Mik’ewa tsaye tayi tare da soma takowa anutse harta k’araso inda Laylerh’n ke tsaye, wanda zuwa yanzu ta sunkuyar da kanta k’asa. Hannayen Laylerh’n ta kamo tare da d’an cigaba da tsura mata ido, Allah Yasani har acikin zuciyarta jin Laylerh’n take kamar y’ar da ta Haifa acikinta, tana matuk’ar so da tausayin yarinyar, musamman duba da cewar tun tana k’arama ta taso da maraicin rashin uwa da uba, duk da kuwa Abbou Jaheed ya tsaya mata amatsayin uba, amma ko yaya dai ba kaman iyayen da suka haifeta ba. D’an numfasawa tayi tare kuma da sanyaya murya ta yanda tasan Laylerh’n zata fahimceta, a hikimance tace. “Kada kimin k’arya Laylerh, inason ki fad’amin gaskiya, shin wani abu na auratayya ya tab’a shiga tsakaninki da Najeeb aduk zamanku koda sau d’aya ne?â€? Awani irin bazata Laylerh taji tambayar da Oum Ayush d’in tayi mata, wanda har saida hakan yasa taji zuciyarta tayi wani irin tsalle, domin ita sai alokacinne ma tatuna da cewar akwae wani abu wae shi hakk’in Najeeb dake kanta. Take taji zuciyarta ta karye, yayinda kuma wani irin tausayinsa ya kamata, domin tabbas tasan ya buk’aceta amma ta juya masa baya. “Laylerh tambayarki fa nayi kibani amsa.â€? Muryar Oum Ayush ya katseta daga tunanin da takeyi. Ahankali kuma cikin tarin fargaba ta girgizawa Oum Ayush d’in kanta alaman. “A’a.â€? Idanu Oum Ayush ta d’an zaro waje cike da mamaki, domin koda wasa bata tab’a tunanin hakan zai faru ba, lokaci d’aya kuma taji duk jikinta yayi sanyi, harta idanunta sai gashi sun ciko da k’walla. Asanyaye tace. “Shikenan jeki kwanta.â€? Kamar kuwa dama jira take cikin sauri ta juya ta shige d’akin Oum Ayush d’in, domin dama har ta kawo bakin k’ofar jin maganan Oum d’inne ya tsaida ita. Itakuwa Oum Ayush bayan Laylerh’n tabi da idanu, zuciyarta cike da tarin sak’e sak’e maban banta, lallai ta sake yardarwa kanta cewa. “Da akwae abunda Allah Ya tsara, wanda babu mai sani ko iya ganewa saishi kad’ai.â€? Dawowa cikin falon tayi ta zauna tare da soma, al’ajabin rashin kasantuwar wani abu atsakanin Laylerh’n da Najeeb. Wani tunani daya zo cikin brain d’inta ne kuma yasa sakin wani d’an murmushi, duk da kasancewar tana cikin bad situation, saidai kuma babu inda murmushin nata yaje, domin tasan abunda zuciya da kuma tunaninta ke shirin bata, abune da faruwarsa zaiyi matuk’ar wahala, domin kuwa ba Lallai bane, tunani da kuma hasashensu ita da Najeeb ya zama ya wanzu acikin sauk’iba, musamman tunawa da tayi cewar watarana abunda kake so da hasashe bashine yake tabbata ba. Koda yaushe kasa rai da kuma tsammanin cewa wani abu sab’anin tunaninka yana iya afkuwa. *M.JAY* Wayartasa k’irar iphone12promax ya zubawa idanu baya ko k’yaftawa, yayinda kuma k’wak’walwarsa ke tayi masa yawo da maganan da Abbou Jaheed d’in ya fad’a. Cikin rashin fahimta da kuma gane inda maganganun Abbou Jaheed d’in suka nufa yasa hannu ahankali yad’an bugi kansa dake juyawa. Daidai lokacin kuwa wani k’iran Abbou Jaheed d’in ya sake shigowa cikin wayar. Akasalance ya mik’a hannunsa ya d’au wayartasa da tuntuni ta fad’i ak’asa, lumshe sexy eyes d’insa yayi adaidai lokacin dayayi picking call d’in. Daga can cikin wayartasa kuwa muryar Abbou Jaheed ne ke tashi, inda cikin bada umarni yace. “Maleek kaje kayi abunda nasaka yanzun nan.â€? Batare kuma daya jira abunda Maleek d’in zaice ba ya kashe wayar. Maleek kuwa jin da yayi Abbou Jaheed d’in ya kashe wayarsa ne yasashi bud’e idanunsa da suka d’ayi ja. Har yanzu shikam kwata kwata bai fahimci komae na daga cikin kalaman da sukeyi masa yawo acikin kansa ba. “Yaje yacewa Oum Ayush kada ta bawa Laylerh takardar sakin da Najeeb ya bata, why way’annan maganganun duk na menene? Najeeb yayi divorced d’in Laylerh ne?â€? Yayiwa kansa tambayar cikin rarrabewar tunani, saidai kuma tambayar da yayiwa kansa na k’arshe ita ta zaburashi da sauri ya mik’e tsaye, tare dasa hannu ya dafe daidai saitin zuciyarsa, da lokaci d’aya yaji ta soma bugawa, wani irin abu mai kama da fargaba ne yaji ya shiga dukan k’irjinsa, take kuma yaji wani abu mai kama da zufa na fitowa ta kowanni k’ofar gashi dake jikinsa. Red soft lips d’insa ya d’an cije tare da k’arasowa gaban bed d’insa, ya zura wasu bedroom slippers dake zube agaban gadon, cikin yanayin sauri ya nufi hanyar fita daga d’akin ko wayartasa bai tsaya d’auka ba. Direct sashin Oum Ayush ya nufa, koda ya k’arasa bakin k’ofar da zata sadashi da babban falon dake cikin sashin nata, knocking door d’in ya somayi. Bai kuma wuce 2knocking yayi ba, yaji muryar Oum Ayush na bada izinin shigowa. Ahankali ya murd’a handle d’in k’ofar ya shiga bakinsa d’auke da sallamar da shi kad’ae yasan yayi ta, saboda labb’ansa ne kawae suka motsa. Ganinsa da Oum Ayush tayi ne yasa ta saurin daidaita nutsuwarta, tare da kafesa da idanu. Shid’inma kallonta yakeyi, ahaka har ya k’araso tsakiyar falon, k’warai so yake ya fahimci wani abu daga yanayin fuskarta shiyasa ma ya k’ura mata mayun idanunsa. Gane hakanne kuma yasa Oum Ayush d’in sake controlling kanta, cikin son b’atar da tunaninsa tace. “Lafiyanka k’alau kuwa kaketa kallona, haka baka ko k’yafta idanu?â€? Sam bai tanka mata ba, saima gyara tsayuwarsa da yayi, duk da cewar yanajin zuciyarsa na bugawa amma haka ya daure, saboda baisan menene sababin bugawar zuciyar tasa ba. Cikin halin ko inkulawarsa daya sabayin magana yace. “Abbou Jaheed ya k’ira wayarki baki d’auka ba.â€? Hannu tasa ta d’an dafe kanta, cikin nuna rashin saninta tace. “Subahanallah gaba d’aya na sha’afa nabar wayartawa acikin d’aki bari naje na d’auko.â€? Mik’ewa tsaye tayi da sauri tare da juyawa ta nufi hanyar bedroom d’inta. Saidai ko taku hud’u batayi ba ta tsaya cak tare da juyowa ta kalli Maleek d’in, da abubuwan dake cikin zuciyarsa suka bayyana akan fuskarsa. Shikuwa Maleek falonnata ya soma bids kallo, ganin babu wata alama da zuciyarsa keyi masane yasa shi dawo da kallonsa ga Oum Ayush din, wanda tayi saurin dawowa ta d’auki farar envelope d’in da ta bari akan kujera. Envelope d’in hannun nata ya zubawa ido, kamar wanda zai nazarci wani abu kuma sai ya fasa ahankali ya juya, taku biyu kacal yayi ya tsaya tare da juyowa ya fuskanceta. “INA AYSHNOOR?.â€? Ya tambaya cikin wata irin murya da ita kanta Oum Ayush d’in batasan yana da ita ba. Sanin kuma da tayi cewar Laylerh’n yake k’ira da Ayshnoor ne yasa ta tsuke fuska, cikin son rashin bashi daman ganin Laylerh’n tace. “Batanan.â€? Idanunsa ya d’an lumshe tare da bud’e jajayen labb’ansa, magana yasoyi amma kuma sai ya fasa, madadin hakan sai ya d’an juya tongue d’insa, batare daya sake cewa komae ba kuwa ya juya ya fice daga cikin falon. Hakanne kuwa yasa ta bisa da kallo, ganin ficewarsa yasa ta sauk’e wani irin ajiyar zuciya, idanunta ta d’an lumshe kana asanyaye tace. “Daga yanzu har zuwa wani lokaci mai tsawo bazaka sake ganin Laylerh ba Maleek wannan alk’awarine!!!â€? *(ALHAMDULILLAH two days na d’an shiga busy, amma yanzu komae normal zanyi kokari wajen baku update kullum, saboda na gama duk wasu tests d’ina💃💃 littafi yazo gangara mutanen Maleek how far😉)* *7/March/2021* *6:14 pm* 3/9/21, 4:53 PM - Ummi Tandama: *LaylerhMaleek* *Writting by* fatymasardauna *Chapter 64* “Daga yanzu har zuwa wani lokaci mai tsawo ba zaka sake ganin Laylerh ba Maleek wannan alk’awarine.â€? Cewar Oum Ayush da har zuwa yanzu ta kasa d’auke idanunta daga kallon hanyar da Maleek d’in yabi ya fice. Ak’alla kuma saida ta d’auki almost 5minutes tsaye awajen kafun daga bisani ta juya ta nufi d’aya daga cikin bedroom d’inta wanda kuma anan cikinsa ta manto wayartata. Laylerh. Akaro na barkatai kenan da take ta so da kuma k’ok’arin daidaita nutsuwarta amma abun yaci tura, duk yanda taso tsagaita tunaninta kuwa abun na neman gagararta. Tabbas amatsayin bak’o takejin komae dama duk yanayin. Sannan kuma hak’ik’a zuciyarta acike take da fargaba, wanda takasa tantance k’arfinsa da kuma yanayinsa, ayau d’in akuma wannan lokacin shine karo na farko da ta fara jin wani abu akan Najeeb, wanda yasa gaba d’aya hawayen dake cikin idanunta kasa daina gangarowa kan fuskarta. Sake rumtse idanunta dake aikin zubar da k’walla tayi, tare da mirginawa ta gyara kwanciyar da tayi akan makeken gadon Oum Ayush. Sannu ahankali kana cikin wani irin sassanyan yanayi gaba d’aya rayuwar da tayi da Najeeb d’in suka shiga dawowa cikin kanta filla filla, yayinda take ganin fuskarsa nayi mata gizo acikin idanunta. Tabbas Najeeb Ya isa Namjin da kowacce mace zata soshi, yana kulawa da ita matuk’a, ko da kad’anne kuma bayason ganin damuwar ta, akoda yaushe idan tana cikin k’unci yakanyi k’ok’ari wajen ganin ya magance mata duk wani damuwarta, koda kuwa baya cikin mood mai dad’i yakanyi k’ok’arin wanzar da murmushi akan fuskarsa matuk’ar yana gabanta, bai damu da hakk’insa ba matuk’ar zatayi farinciki, sannan yakan iya danne duk wani abu dake zuciyarsa wajen ganin ya mu’amalance ta yanda bazata ga komae na b’acin ransa ba. Idanunta ta kuma rumtsewa, wanda sanadin hakan suka fitar da wani irin hawaye mai zafi, ahankali tasa hannunta ta dafe daidai saitin zuciyarta dake d’an bugawa da k’arfi. Tabbas tasan Najeeb yayi halacci agareta duk da bata da masaniya akan dalilin dayasa ya saketa. Matsanancin kukan dake shirin k’wace mata ta shanye tare da jawo wani pillow tayi hugging d’insa, still har yanzu maganganun Najeeb d’inne ke dawowa cikin brain d’inta, musamman ayau d’in dayake fad’in cewa. “Yafini buk’atarki Laylerh, domin ni da zuciyata kawai nake sonki, shi kuma ke d’ince rayuwarsa gaba d’aya.â€? Kalmarsa na “I love youâ€? daya furta mata da ta tuno ne yasa ta fashewa da wani irin kuka mai tsuma zuciya, cikin kuma wata irin muryarta mai d’auke da tsananin rauni tace. “I’m sorry Yah Najeeb, I’m very sorry, banyi maka abunda ya dace nayi maka ba tuntuni, sanadin hakan kuwa gashi ayanzu bansan me kakeji acikin zuciyarka ba. Lallai Tabbas da ace inada dama da ikon sauya k’addara dana sauya tawa k’addarar, duk da nasan cewa rayuwa babu soyayyar Yah M.Jay abune agareni da har abada bazae tab’a yiwuwa ba, so da k’aunarsa acikin jiki da jinina suke, babu wani second ko minute da zai wuce batare da naji soyayyarsa acikin jinina ba, hasalima ina rayuwane da sonsa, bansan tayaya zan iya jurewa hakan ba, domin ako da yaushe sonsa shi yake maye gurbin duk wani tunanina.â€? D’an tsagaitawa da maganan nata tayi, saboda yanda zuciyarta ke wani irin tsalle, numfashinta kuwa haka yake yi kamar zae d’auke, hakan ya farune kuma saboda kukan da tayi sosae. Sake gyara kwanciyarta tayi had’e da nutsa kanta acikin pillow, take kuma ta shiga sauk’e wani ajiyar zuciya akai akai, wani irin sanyi ne takeji na ratsa duk ilahirin jikinta, wanda hakan shiya tilasta mata, jan babban blanket d’in dake kan gadon ta rufe gaba d’aya jikinta dashi. Sake takure kanta waje d’aya tayi, tare kuma da sanya hannayenta duka biyu ta toshe kunnuwanta, tayi hakanne kuma saboda muryar Najeeb da takeji na yawo acikin kunnuwanta, wanda kuma hakan shike sanya mata jin fad’uwar gaba maitsanani, musamman idan ta tuna da cewar azamansu koda sau d’ayane bata tab’a bashi hakk’insa na aure dayake kanta ba. Wannan abu shike k’arasawa taji hawaye sun tsananta zuba daga cikin idanunta, Tabbas awani sashi na zuciyarta taso ace ta rayu da Najeeb d’in ko da na d’an k’ank’anin lokaci ne, musamman ayanzu da k’addara ta fad’awa Maleek, ta yanda zata iya jure duk wani wahala wajen ganin ta haifi d’a ko y’ar da zata bawa Yah M.Jay d’in nata kyauta na har abada. Asanyaye ta share hawayen da suka zubo mata, tare kuma da soma ambaton sunan Allah acikin zuciyarta, domin kuwa zuwa yanzu ta kawo wani matakin da zuciyarta ta riga da ta gama karyewa, hasalima ayanzun so takeyi tayi bacci ko hakan zaisa ta d’anji sauk’in abunda ke damun zuciyarta. Cikin ikon Ubangiji kuwa ko mintuna 15 bata share ahakaba wani irin bacci mai nauyin gaske ya d’auketa, wanda cikinsa ke d’auke da tarin mafarkai kala kala. Acan b’angaren Maleek kuwa koda ya fito daga part d’in Oum Ayush d’in kaitsaye nasa part d’in ya nufa, saidai yanayin yanda zuciyarsa ta kasa nutsuwa waje d’aya ne yasa duk yaji zaman gidan ya ishesa. Yanaji ajikinsa cewar lallae Tabbas akwae abunda yake faruwa, amma kuma menene shi abun ya kasa sani, duk da kasancewar kunnuwansa sun jiye masa abunda Abbou’n nasa ya fad’a da kyau, amma sam ko kusa ya kasa aminta da abunda zuciyarsa ke gaya masa akan hakan. Akan wata had’add’iyar sofa dake gefen gadonnasa ya zauna, tare kuma dasa hannu ahankali ya dafe kansa da yakejin yanayi masa wani irin sarawa, atake kuma ganin da yayiwa wannan farar envelope d’in dake hannun Oum Ayush ya fad’o masa. Wani irin abune yaji ya daki k’ahon zuciyarsa, wanda har saida hakan kuma ya tilasta masa zabura. Lallai ne Tabbas yanason sanin gaskiyar abunda ke faruwa. Idan kuma har da gaskene cewa Najeeb ya saki Laylerh to yana da buk’atar sanin dalili da kuma hujja. Idanunsa da sukayi ja ya sake rumtsewa da k’arfi, wani irin tafasa zuciyarsa keyi, domin lokaci d’aya tunaninsa ya basa cewar Najeeb d’in ya auri Laylerh’nne dama dan kawae ya tozartata, maybe ya samu abunda yakeso awajenta shiyasa yake k’ok’arin tozartata, wanda shi kuma Allah Yasani bazae tab’a iya jurewa hakan ba, har abada bazae tab’a barin wani abu na damuwa mai tsanani ya samu Laylerh ba. Raya hakan da yayi acikin ransa ne kuma yasashi d’an soma girgiza kai, tare kuma da dunk’ule hannayensa waje d’aya, lokaci d’aya idanunsa sukayi wani irin ja tamkar wanda aka watsawa garin barkono, yayinda jijiyoyi da kuma gargasan dake jikisa suma duk suka mimmik’e. K’una sosae yakeji ak’irjinsa wanda ke d’auke da matsanancin b’acin rai. Hakanne kuwa yak’ara sawa yaji komae bayayi masa dad’i. Kaitsaye wajen da yake ajiye car keys d’insa ya nufa, key d’in wata had’add’iyar BMW 5201 k’iran 2018 navy blue colour ya d’auka, tare da d’aukan wayoyinsa, kai tsaye ya nufi hanyar fita daga cikin d’akin, duk da cewar sam bayajin dad’in jikinsa ko kad’an, amma yana da yik’inin cewa fitansa daga cikin gidan yafiye masa zamansa. Koda ya fito compound d’in gidan, Abdoul dake zaune yana hango Ogan nasa ya tashi tsaye da sauri tare da k’arasowa wajen Da Maleek d’in yake. Cikin girmamawa yace. “Barka da fitowa Oga, ya jiki?.â€? Da kai kawae ya iya amsawa Abdoul d’in, batare kuma da yace komae ba ya sa key ya bud’e murfin motar. Idanunsa da suka sauk’a akan cutie cat d’insa dake ta shawagi acikin babban compound d’in gidan ya d’auke, tare da shigewa cikin motar b’angaren driver ya zauna. Ganin hakanne kuma yasa Abdoul d’an rank’wafowa cikin yin k’asa da murya yace. “I’m sorry Sir bai kamata ka fita kai d’aya ba, kodan gujewa abunda ya faru...â€? Kasa k’arasa maganan Abdoul yayi saboda wani irin kallo da yaga Maleek d’in yayi masa. Bisa dole haka yaja bakinsa yayi shiru tare da d’an Jan jikinsa baya. Shikuwa Maleek rufe murfin motar nasa yayi, tare da danna wani irin horn da ya saka maigadi wangale masa makeken gate d’in tun kafun ma ya k’araso. Da wani irin speed ya cilla hancin motar tasa waje, ko sauraron mai gadi ma da yakeyi masa adawo lapia baiyiba yasa kai ya fice. Da wani irin isa yake murza kan steering motar nasa, duk da cewar kuma yanajin k’asan mararsa nayi masa ciwo amma haka ya cijewa fitan, kaitsaye CASH and CARRY ya nufa. Abdoul kuwa jiki asanyaye ya koma can gefe ya zauna, domin dama yasan halin Ogan nasu watarana idan ya juye babu mai iya gane gaba da bayansa. After 2hours.. Abbou Jaheed, da kuma Abbou Khareem sai Oum Ayush ne ke zaune acikin babban falon, daya kasance mallakin Abbou Jaheed d’in, Inda ya kasance kuma kowannen su da abunda yake sak’awa acikin rai da zuciyarsa. Daga gefen Oum Ayush kuwa Aunty Zee ce, (k’anwar Oum Ayush) ke zaune, wanda da zuwanta gidan kuwa yanzu bai wuce 20 minute ba. Inda sukayi zama na musamman suna masu tattauna sabin matsalolin da suka fuskantosu batare kuma da sun shiryawa hakan ba. Ahankali Abbou Jaheed ya d’ago kansa wanda kallo d’aya zakayi masa kafahimci cewar yana cikin matsananciyar damuwa, da kuma zallan fargaba. Kallon Oum Ayush wanda tayi tagumi yayi, asanyaye cikin kuma muryarsa da ke matuk’ar bayyana damuwarsa sosae yace. “Ayush kije ki k’iramin Laylerh, domin nasan zuwa yanzu tatashi daga baccin da kikace tanayi, sa’annan idan kin k’irata d’in kuma kibiya ta part d’insu ki had’a mata duk wani kayanta, da kuma abunda zata buk’ata, Saboda na yarda na amince da shawararku, tabi Zainab can gidanta idan yaso bayan ta kammala iddanta saita dawo, nayi hakanne kuma badon komae ba saidan bazan iya jurewa ganinta acikin halin da take ciki ba, kasancewarta kuma marainiya banason k’uncin rayuwa yayi mata yawa.â€? *(Not ending Gaskia yau banacikin mood😒 mai dad’i so bazaku samu long typing ba.)* *6:52pm* *8/March/2021* 3/11/21, 9:28 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna *Not editing* *Chapter 65* Mik’ewa Oum Ayush tayi domin zuwa k’iran Laylerh’n kamar yanda Abbou Jaheed ya buk’ata, acikin zuciyarta kuwa tana mejin dad’in yarda da shawararsu da Abbou Jaheed d’in yayi, domin kuwa ko ba komai tafiyan Laylerh’n gidan Aunty Zee zai d’an rage mata kad’aici da kewa, kasancewar akwae y’ar k’anin Mijin Aunty Zee d’in Aliya agidan kuma bata wuce sa’ar Laylerh’n ba. Ahankali ta tank’washe kyawawan k’afafunta dake aje bisa kan sallayan da take zaune akae, maida gajiyayyun idanunta tayi ta lumshe, tare kuma da fesar da wani sassanyar numfashi, Tabbas sallah’n da tayi yanzu da kuma addu’o’in da tayi sune suka sanyaya mata zuciya, duk da cewar kuwa bata wani jima da tashi abaccin daya d’auke ta ba, yanzu tashinta kenan tayi wanka tare kuma da gabatar da sallan la’asar wanda lokacin da akayisa tana bacci. Jingina bayanta tayi da bango, tare kuma da ware idanunta ahankali ta sauk’esu akan kyawawan y’an yatsunta, akan k’aramar yatsar hannunta na dama wanda ke d’auke da had’add’en gold ring ta sauk’e ganinta, hakanan taji wani irin abu mai sanyi na yawo acikin zuciyarta, lokaci d’aya kuma taji duk wani k’warin guiwar dake jikinta ya somayin k’asa, yayinda tunani kala kala suka soma bijirowa cikin k’wak’walwarta, Hak’ik’a ta yarda cewa ita mai matsanancin raunine akansa, saidai batasan meyasa ba akowani lokaci idan tunaninsa ya motsawa mind d’inta sai taji kamar tayi kuka, haka kuma zata ke jin kanta amatsayin wata na daban wacce tarasa duk wani abunda takeso. Still sake lumshe idanunta wanda suka ciko da k’walla tayi, daidai lokacin kuwa aka turo k’ofar d’akin aka shigo. Duk da kuwa cewar taji alaman wani ya shigo cikin d’akin amma hakan baisa ta ta bud’e idanunta ba, saboda tasan cewa tana bud’esu tofa hawayen dake cikinsu ne zasu sauk’a akan fuskarta, ita kuwa ayanzu sam bata son wani yaga gazawarta. Ahankali Oum Ayush ta maida k’ofar ta rufe, hango kuma Laylerh’n da tayi akan sallayane yasa duk taji jikinta yayi sanyi, saboda kallo d’aya kawae zaka mata kafa himci cewa tana d’auke da damuwa mai tarin yawa acikin zuciyarta. D’an girgiza kae Oum Ayush d’in tayi, cike kuma da tausayin Laylerh’n ta k’arasa shigowa cikin d’akin. “Laylerh!!â€? Oum Ayush ta k’ira sunanta da wata irin sassanyar murya. Jin muryar Oum Ayush acikin kunnuwanta ne kuma yasa tasoma kokarin shanye hawayen dake idanunta, saidai Ina duk yanda tasoyin hakan ta kasa, kasancewar hawayen dake cikin idanun nata sunzo wani gab’a da shanye su abune me wahala, musamman ma idan za’ayi duba da abunda ke cikin zuciyarta. “Laylerh!!â€? Oum Ayush ta sake kiran sunanta akaro na biyu, bayan ta k’araso gab da inda ta ke zaune. Hannunta tasa ahankali ta dafa kafad’an Laylerh’n, kana anutse tace. “Yauwa kin tashi daga baccin ko? dama babu kyau bacci bayan la’asar naso na tasheki amma kuma tuna irin yanayin da kike ciki yasa na k’yaleki, kinyi sallah ne?â€? Ahankali ta d’an jinjina kanta alaman “Eh.â€? Saidai kuma har yanzu bata bud’e idanunta ba. D’an Jim Oum Ayush tayi tare da zuba mata idanu, saboda hakanan azuciyarta taji ta k’ara tausayin Laylerh’n, musamman ma yanzu da ta tab’a ta, dan ta d’anji d’umin zazzab’i kad’an ajikinta. Uwa uba kuma shirun da taga tayi, lallaine tasan abun yana damunta azuciya, domin kasancewar babu soyayya atsakaninta da Najeeb, shine zaesa ta kasajin wani iri adangane da rabuwa dashi ba. D’an rank’wafowa Oum Ayush d’in tayi tare da kamo hannayen Laylerh’n duka biyu, cikin yanayin kulawa irin wacce Uwa zata bawa duk y’ay’anta idan ta gansu acikin damuwa tace. “Kiyi hak’uri ko Laylerh, Tabbas dukkan tsanani yana tare da sauk’i, watarana kuma Insha Allah komae zae wuce kaman bai faru ba, tashi kije Abbou Jaheed na jiranki afalon saâ€? Ta kai k’arshen maganan nata tana me tada Laylerh’n tsaye. Wanda kuma sai asannanne ta bud’e lumsassun idanunta, wanda suka taho da wasu irin siraran hawaye. Ganin kuma hawaye akan fuskarta ne yasa Oum Ayush girgiza mata kai, alaman kada tayi kuka, had’e dasa hannunta ahankali ta share mata hawayen da suka zubo mata. Again Murmushi tayi mata tare da cewa. “Kiyi sauri su Abbou Jaheed suna jiranki.â€? Still kanta kawae ta jinjina, batare kuma da ta motsa labb’an bakinta ba, ta juya asanyaye ta fice daga cikin d’akin. Oum Ayush kuwa da kallo ta bita har ta fice, wani irin sanyi taji jikinta yayi, musamman da tafahimci cewa ayanzu Laylerh’n tana da buk’atar wanda zae bata ingantacciyar kulawa, wanda zai hanata kuka, ya kuma iya jure shagwab’anta, Tabbas wani take buk’ata mai zuciya irin nata, wanda tunani da komansa yakasance yana da alak’a da tata zuciyar, wanda zai fahimci hak’ik’anin damuwarta koda kuwa bata furta masa da bakinta ba. Ajiyar zuciya mai k’arfi ta sauk’e tare kuma dajan wani dogon numfashi, Tabbas komae abayyane yake, amma saidai kusancin Laylerh’n ga abunda zuciyarta keso ayanzu babu abunda zae haifar sai wata sabuwar matsala, Sam bakuma zata so hakan ya faru akaro na biyu ba. Wannan dalilin yasa tayi saurin kawar da duk wani tunanin dake cikin ranta, direct itama ta juya ta fice daga cikin d’akin, koda ta fito compound d’in gidan kuwa kaitsaye part d’in su Laylerh’n ta nufa, musamman dan had’a mata abubuwan da tasan zata buk’ata. Acan b’angaren Laylerh kuwa tun fitowarta daga sashin Oum Ayush d’in falon Abbou Jaheed ta nufa. Koda ta k’arasa ahankali ta tura k’ofar falon ta shiga, bakinta d’auke da sassanyar sallamar, da sai mutum yayi dagaske zai iya jiyo amonta. Amma kuma kasancewar mutanen dake cikin falon kowannensu acikin alhini yake, hakan yasa sukaji sallaman nata rad’au acikin kunnuwansu. Abbou Jaheed ne ya d’ago da kansa ya kalleta adaidai lokacin da ta gama k’arasa shigowa cikin falon, tare da neman waje ta zauna acan gefe. “AYSHA taso kizo nan!â€? Ya fad’i hakan cikin matsanancin tausayinta da yakeji na dukan k’irjinsa. Ai kuwa babu musu ahankali ta mik’e tsaye, cikin yanayin sanyin da tasamu kanta ta k’araso inda Abbou Jaheed d’in ke zaune, yayinda acikin ranta take me mamakin yanda yau Abbou Jaheed d’in ya k’ira realname d’inta. Adaidai kusa da k’afafunsa ta zauna, wanda sai alokacinne kuma ta lura da Aunty Zee dake zaune acan gefe, yanayin fuskarta ne tad’an sanja daga damuwa zuwa murmushi, gaishe da Aunty Zee d’in tayi, da kuma Abbou Khareem dake zaune. Dukansu cike da kulawa suka amsa mata, yayinda Aunty zee kuwa muryarta ta kasa b’oye tausayin Laylerh’n da takeji. “Abbou gani.â€? Tafad’a tana me gyara tank’washewar da tayiwa k’afafunta. Abbou Jaheed kuwa da zuciyarsa ta gama yin rauni, kamo hannayenta yayi ya rik’e, akaron farko kenan da yaji kuma yaga yanayin fuskarta ya juye masa izuwa na mahaifanta, take kuma lokacin daya d’auketa amatsayin amana ya shiga dawo masa, lokacin da tarasa Uwa mahaifiya agareta, rik’onta ya dawo wajensu, still k’addara ta sake rabata da Mahaifinta, hakan yasa ta zama bata da kowa sai su, meyasa alokacin baiyi abunda ya dace ba? Meyasa ya d’auki alk’awarin da nauyinsa ya zo ya zame musu damuwa gaba d’ayansu? Hak’ik’a arana irin ta yau yanajin kamar baiyiwa amanarsa rik’o mai kyau ba, gaba d’aya rayuwar Laylerh’n da tayi abayane ya shiga dawowa cikin kansa, ci da sha, dama duk wani farincikinta yana samuwa ne daga wajen mutum d’aya, wanda yakasance alokacin shine mutum na farko daya fi kowa kusanci da ita, shine wanda yasan abunda ke fili da kuma wanda ke b’oye acikin zuciyarta. Tabbas idan akwai k’addara to shima akwai wani hakk’i daya tauye, wanda ya tabbata da ace iyayen Laylerh’n suna raye, to da yau sai sunfi kowa jin ciwo da kuma k’uncin abunda ya faru, tayaya zai iya warware wannan al’amarin? Tambayar da yayiwa kansa kenan wacce kuma bashi da amsarta. Lokaci guda kuwa idanunsa suka cicciko da k’walla, saboda raunin da yake cikine kuma yasa hawayen dake cikin idanun nasa suka soma k’ok’arin gangarowa zuwa kan fuskarsa. Laylerh da tun rik’e hannunta da yayi take kallonsa, ganin hawaye a idanunsa ne yasa, taji gaba d’aya hankalinta ya tashi, hannunsa daya rik’e nata dashi ta kama gam, cikin nuna tsananin kulawa da kuma damuwa ta k’ira sunansa, bakinta ta bud’e daniyar yin magana, amma sai hakan ya gagareta saboda wani irin abu da taji ya soki kirjinta. Idanunta ta rumtse da k’arfi saboda Allah Yasani cewar bazata iya jurewa ganin hawayen Abbou Jaheed d’inta ba. Asanyaye ta sake matsowa kusa dashi tare da d’aura kanta akan guiwowinsa. Hakan da tayi d’inne kuma yasa Abbou Jaheed controlling hawayensa, ahankali ya soma shafa kanta, murya atausashe kana kuma cikin yanayin dake bayyana k’aunarsa agareta yace. “Hak’ik’a da ana iya sauya k’addara go goge zanen abunda ya wuce da nayi hakan Laylerh, da na nesantaki da duk wasu munanan k’addarorin dake bibiyar ki, da kuma ace nasan wannan ranan zata zo, to da har abada ban bari an d’aura aurenki da Najeeb ba, duk da kuwa nasan cewar Najeeb baiyi hakan dan ya cutar da rayuwarki ba, kamar yanda nasani cewa har abada bazae tab’a iya cutar dake ba, Tabbas na zab’a miki Najeeb ne amatsayin miji, saboda ya cancanta, na kuma yi musu alk’awarin bashi aurenki tun lokacin kina k’ank’anuwa, sam ko kusa banyi hakan dan na cutar da rayuwarki ba Laylerh, domin duk da kasancewar bani na haifeki ba, amma ina miki son da nakeyiwa d’an cikina, kuma koda banine mahaifinki ba, jinin dake gudana acikin jikinki na d’an uwanane, ke d’in wata kyautace guda d’aya da Allah Ya bamu, saboda haka bazan tab’a son abunda zai cutar dake ba Laylerh...â€? D’an tsagaitawa da maganganun nasa yayi, tare dasa hannunsa ya d’ago kanta, cikin son bata k’arfin guiwa da kuma nuna mata cewar tana da gobe mai kyau yace. “Kada kiyi bak’inciki ko k’unci Laylerh domin k’addararki ce tazo ahaka, sannan kuma kada ki yiwa Najeeb mummunan zato akan abunda ya aikata, domin ko kad’an Najeeb baiyi haka dan ya cutar da rayuwarki ba, yamin bayanin komai kuma nafahimta, sannan nasan kema watarana In sha Allah Zaki fahimta, domin ni Abbou Jaheed har abada bazan tab’a yi miki zab’in da zai cutar da rayuwarki ba, sannan kuma akullum inaso kina tuna cewar komae daya faru da kuma wanda zai faru duk k’addararren al’amarine, Allah Baya tab’a d’aurawa bawansa abunda bazae iyaba, aduk kuma lokacin da kikaji k’unci ki ambacesa zae sauk’ak’amiki kinji!!â€? Kanta tajinjinawa Abbou Jaheed d’in alaman gamsuwa, tare kuma da k’ok’arin b’oye duk wani abunda ke damun zuciyarta. Ganin k’warin guiwa akan fuskarta ne kuma yasa Abbou Jaheed yaji zuciyarsa tayi wani irin sanyi. Kanta ya sake shafawa, domin har acikin ransa yana me alfahari da ita. Cikin kuma son jin ta bakinta yace. “Mun yanke shawara nida Abbou Khareem da kuma Oum Ayush cewar zakije gidan Aunty Zainab kiyi iddah’n ki acan, saboda acan din zakifi samun nutsuwa, idan yaso bayan kin gama iddah’n saiki dawo, idan kuma kinaga zaki zauna anan d’in shikenan.â€? Kâ€™asa tayi da kanta tare da d’an soma wasa da y’an yatsun hannunta, cikin kuma yanayin sanyi mai kaman shagwab’a daya zame mata sabo tace. “Abbou Jaheed duk hukuncin da kuka yanke akaina daedae ne.â€? Jin abunda tace d’inne kuma yasa Abbou Jaheed da kuma Abbou Khareem jinjina kai. Daidai lokacin kuwa Oum Ayush ta shigo cikin falon, jaye da wani babban trolleybag da ta zubawa Laylerh kayan ta aciki. Ajiye trolleybag d’in tayi, tare da kallon Aunty Zee cikin kulawa tace. “Ya kamata kutafi domin naga magriba na k’ara shigowa.â€? Hakan da tace d’inne kuma yasa Aunty Zee mik’ewa tsaye, tare da jan trolleybag d’in Laylerh’n ta nufi hanyar waje dashi. Ganin hakanne kuma yasa Oum Ayush ta rufa mata baya. Laylerh kuwa asanyaye ta mik’e tsaye, Abbou Khareem ne ya rik’o hannunta ya samata bandir d’in kud’i na 50/50k, had’e kuma da damk’a mata ATM CARD d’inta, wanda tun lokacin da akayi bikinta atm card din ke hannunsa, wanda ayanzu ya k’ara zuba mata kud’ad’e masu yawa aciki. Bakinta na shagwab’a ta bud’e, saidai kuma saurin girgiza mata kai dayayi yasa dole tayi shiru. Haka suka fito daga falon Abbou Jaheed d’in tana tsakiyarsu, har wajen da motar Aunty Zee ke fake suka rakata, bayan ta shiga motar ta zaunane kuma Oum Ayush ta mik’o mata wayarta. Karb’an wayar tayi tare da ajiyewa akan cinyarta, kana ta jingina bayanta da jikin kujeran motar. Idanunta da sukayi raurau ta tsayar akan had’add’en part d’insa da take hangowa, haka takejin zuciyarta na wani irin bugawa, shi kawae taji tanason gani ayanzun, domin tasan ba k’aramin kewa da kuma wahalar da ita soyayyarsa za suyi ba. Idanunta da suka d’an ciko da k’walla ta lumshe. Adaidai lokacin kuwa da motar Aunty Zee zata fita daga gidan, motarsa ta kunno kai. Jin k’ara da kuma horn d’in motar tasane yasa tayi saurin bud’e idanunta, cikin sa’a kuwa ta sauk’esu akansa, inda yake zaune ab’angaren driver. Idanunta ta tsura masa bata ko k’yaftawa, shikuwa samma bai kula dasu ba domin sauri yake sosae. Ganin hakanne kuma yasa Aunty Zee ta matsa gefe saida ya shige cikin gidan kafun sukuma suka fita. Fitansu daga cikin gidan kuwa yayi daidai da zubowar hawayen dake cikin idanunta. Shikuwa Maleek da sauri ya fito ko gama daidaita parking d’in motar tasa ma baiyi ba. Hakan yasa hankalinsu Abbou Jaheed dawowa kansa, cikin yanayin mamakin irin saurin da yakeyi Abbou Khareem yace. “Captain lafiya kake kuwa?â€? Kansa ya jinjina, cikin kuma yanayinsa na wanda bai cika yin magana ba yace. “Zanbar Nigeria yau, wani aikin gaggawa ya tasomin, 7:00 pm daidai flight d’inmu zai tashi.â€? Cike da mamaki dukansu suka bud’e baki suna me binsa da kallo, kasancewar yayi musu maganar ne yana tafiya batare dako tsayawa yayi ba. *5:30 pm* 3/13/21, 10:08 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna *Not editing* *Chapter 66* Sosae jin maganan tafiyar tasa ta basu mamaki, amma kuma saidai ganin kwata kwata bai juyo ya kallesu bane, yasa suka bisa da idanu har saida ya b’acewa ganinsu. Abbou Jaheed ne ya d’an girgiza kansa, Yayinda kuma acikin ransa yake mamakin hali irin na Maleek d’in, baidamu da kowa ba sam, shikad’ai yake son gudanar da rayuwarsa ako da yaushe, kimin damuwa da k’uncin dake cikin zuciyarsa kuwa yakan iya shanyeta, ta yadda bazae bari wani ya fahimci hakan ba. Juyawa yayi batare daya sake cewa Komai ba ya nufi sashinsa, domin tun sanda Najeeb yaje masa da zancen sakin Laylerh yakejin zuciyarsa nayi masa wani iri, komai bayayi masa dad’i, duk da kuwa cewa Najeeb din yayi masa gamsashshiyar bayanin daya fahimta. Tafiyar tasa ce kuma tasa Abbou Khareem dama Oum Ayush suma suka wuce sashinsu. Ab’angaren Maleek kuwa koda ya k’arasa cikin part d’innasa direct bedroom d’insa ya wuce. Wani d’an madaidaicin jaka irin wanda ake goyawa abaya ya d’auka, tare da zuge zip d’in jakan, anutse ya soma shirya duk wani abu dayasan zae buk’ata, saidai kuma acikin shirin nasa sam babu kaya ko d’aya, domin hakanan ya saba ko ina zaije tofa baya tafiya da kayan sawa, saidai idan yaje duk inda zashi d’in ya saya sabi. Laptops d’insa guda biyu ya tura acikin jakar, domin kuwa yasan sosae yake da buk’atar kowannensu, domin d’aya na aikinsa ne, d’ayan kuma acikinsa yake ajiye duk wasu abubuwansa musamman privacy d’insa, hakanne kuma yasa kusan gaba d’aya sirrukansa na cikin wannan laptop d’in. Maida zip d’in jakan yayi ya rufe, tare da d’ago kansa ahankali ya sauk’e idanunsa akan zanen kyakkyawan flower’n dake gefen gadonsa, wanda idan mutum ya kalla, azahiri babu abunda zai fahimta sai zanen flower’n, saidai kuma amma abad’ini bawae iya zanen flower’n bane kawae, ga wanda yayiwa zanen kallon tsab kuwa, Tabbas zai iya hango zanen hoton fuskar mace, wanda aka k’awata zanen flowers masu kyau akan fuskarta, wannan yasa ba kowa ne zae fahimci cewar bayan flowers akwae wani zanen fuskar mutum awajenba. Lumsassun idanunsa dake bayyana gajiya ya d’an lumshe ahankali, kana ahankali ya shiga takawa, har zuwa inda zanen flowers d’in suke, ahankali cikin kuma wani irin sassanyar yanayin daya samu kansa aciki, ya d’aura hannunsa adaidai saitin fuskar dake jikin zanen. Hakika sosae da sosae yakeson zanen, wannan shiya sama ya manna sa agefen gadonsa, bawai kuma yanason zanen dan mak’udan kud’ad’en daya kashe wajen yinsa bane, yanason zanen ne saboda hasken fuskar mace d’aya ya bayyana acikinsa, macen da akowanni bugun zuciya da numfashinsa soyayyarta ke k’aruwa, macen da har yau bayajin wani a zuciyarsa kamar yanda yakejinta, macen da ya d’auki sama da shekaru yana rayuwa da soyayyarta maitsanani acikin zuciyarsa, sannan kuma macen da zai iya sadaukar da komae nasa akanta, arziki dama rayuwarsa gaba d’aya, wanda baidamu ba idan shi zaiyi bak’inciki matuk’ar ita zata kasance acikin farinciki. Sassanyar ajiyar zuciya ya sauk’e, tare da sanya hannayensa duka biyu ya d’auko zanen, da aka k’awata acikin wani glass d’in ruwan diamond. Sassanyun idanunsa ya sake lumshewa akaro na biyu, Yayinda har acikin rai da zuciyarsa yakejin wani irin abu na ratsashi. “I will miss you!!â€? Yafad’i hakan cikin wata irin murya dake fitar da slowly sound, irin dai muryarnan dakesa mai sauraronta bacci. Ahankali ya maida zanen ya ajiye tare kuma da juyawa ya d’auki jakansa, wanda ya gama had’a komansa da yasan zai buk’ata aciki. Rataya jakan akan kafad’ansa na dama yayi, tare da d’aukan phones da kuma passport and ticket d’in flight d’in da zaibi. Kamar dai yanda ya saba akoda yaushe, idan zaiyi nisa sai yayi light off na gaba d’aya wutan part d’insa kafun yake tafiya, yanzun ma dai hakanne ta kasance saida ya kashe komai kafun ya fice daga cikin part d’in nasa. Yana fitowa cikin compound d’in gidan kuwa Abdoul wanda shine zai kaisa airport, da sauri ya k’araso ya k’arbi jakan dake kafad’an Maleek d’in, tare da bud’e masa murfin wata black car range rover velar 2019, wanda acikinta ne zaikai M.Jay d’in airport. Shiga cikin motar yayi ya zauna, tare kuma da jingina bayansa ajikin kujeran motar, ya saki wani irin sassanyan numfashi, idanunsa ya d’an lumshe kamar yanda hakan ya zama wata d’abi’arsa, batare kuma daya bud’e idanun nasa ba, cikin halinnasa nason rashin tsawaeta magana yace da Abdoul. “Kawomin cutie.â€? “To.â€? Kawae Abdoul yace had’e kuma da juyawa cikin sauri ya nufi d’aya daga cikin gardens d’in dake cikin gidan, wanda ananne cat d’innasa take hutawa. Shikuwa Maleek tafiyan Abdoul d’inne yasashi d’ago kansa tare da bud’e idanunsa, ya sauk’esu akan part d’in su Laylerh’n, hakanan yakejin wani irin abu na yawo acikin rai da zuciyarsa, duk da yasan cewar adaman abunda yakeji d’in akwae babban rauni, amma koda wasa bazae tab’a bari zuciyarsa ta cigaba da kassara ba, duk da kuwa yasan cewar zaiyi kewarta sosae. Dawowan Abdoul wajen hannunsa d’auke da cutie ne kuma yasashi tsayar da duk wani tunaninsa, bud’e murfin motar yayi tare dasa hannu ya k’arb’i cat d’innasa, lallausan gashin jikinta ya soma shafawa ahankali, kamar dai yanda ya saba yi mata akoda yaushe. Wanda ganin hakanne kuma yasa Abdoul shiga cikin motar, batare daya tsaya wani b’ata lokaci ba kuwa yayiwa motar key, had’e dayin reverse tayanda zai fita daga cikin gidan asauk’ak’e, dan tuni maigadi ya wangale musu makeken hate d’in gidan. Cilla hancin motar kan titi da Abdoul d’in yayi ne kuma yasashi sake maida bayansa ya kwanta ajikin kujeran motar, still har yanzu kuma cutie d’innasa na jikinsa yana shafa gashinta ahankali. Yayinda Abdoul kuwa cike da k’warewa yake murza steering motar, kaitsaye suka nufi airport. Kamar kuma yanda suke akan hanya haka ya kasancewa ga su Laylerh ma, saboda kuma gidan Aunty Zee d’in nada nisa sosae ne yasa basu isa da wuri ba. Tunda suka kama hanya kuwa Laylerh bata sake koda wani k’wakk’waran motsi ba, kasancewar zuciyarta cike take da abubuwa maban banta, duk yanda Aunty Zee d’in taso janta da hira dan d’ebe mata kewa kuwa, sam takasa sakin rai da zuciyarta, Tabbas ayanzu Bawae sakin da Najeeb d’in yayi mata bane ke damunta, wani irin matsanancin kewa da takeji ne ke damunta, dan gani take kaman bazata sake had’uwa da Yah M.Jay d’innata ba. K’aran da taji da kuma alaman cewar sun iso gidan Aunty Zee d’inne yasa ta bud’e idanunta ahankali. Daidai lokacin kuwa maigadi ya wangale musu gate d’in gidan, Aunty Zee ta shiga da motar ciki. Anutse ta gama daidaita parking d’in motar tata, cikin kuma fari’a da sakin fuska ta dawo da kallonta ga Laylerh’n. “Muje ko.â€? Tafad’a tana me k’ok’arin bud’e murfin motar. Asanyaye ta jinjina kanta alaman. “To.â€? Tare kuma da bud’e murfin motar itama ta fito waje. Sannu ahankali take k’arewa had’add’en gidan Aunty Zee d’in kallo, wanda sosae aka kashe masa mak’udan kud’ad’e wajen k’awatasa. Trolleybag d’inta dake gidan baya Aunty Zee d’in ta ciro, ita da kanta ta rik’e trolley d’in tare kuma da kama hannun Laylerh’n sukayi cikin gidan da ita. Da sallama abakinta suka kutsa kai cikin babban falon gidan. Aliya dake zaune afalon tana kallon film d’in Nollywood, jin sallaman Auntynta ne yasata d’agowa da sauri, tare da mik’ewa tsaye tana fad’in. “Oyoyo Aunty Zee sannu da dawowa.â€? “Yauwa Aliya sannu.â€? Aunty Zee ta bata amsa adaidai lokacin da suka k’arasa shigowa cikin falon. Wanda kuma sai alokacinne idanun Aliya suka sauk’a akan Laylerh. “Masha Allah ji wata kyakkyawa!â€? Tafad’i haka acikin ranta, tana me sakarwa Laylerh’n murmushi. Itama Laylerh’n murmushi tayiwa Aliya’n wanda bazata tab’a finta ashekaru ba, haka kuma itama kyakkyawace duk da kasancewarta Brown skin amma tana da kyau sosae. Trolleybag d’in Laylerh’n Aunty Zee ta mik’awa Aliya, kana cikin kulawa tace. “Ki kaimata trolleybag d’inta d’aki, daga yau kinsamu k’arin y’ar uwa, saura kuma ki dameta da shegen surutunki, domin Laylerh ba mai yawan son hayaniya bane.â€? Murmushi Aliya tayi tare da amsar trolleybag d’in, cikin matuk’ar jin dad’i tace. “No bazan dameta da surutu ba, ae sometimes kina bani labarinta, yau dai kam gashi Allah Yayi naga Beautiful Night da idanuna.â€? Idanu Aunty Zee da Laylerh suka d’an zaro, cikin kuma yanayin mamaki Aunty Zee tace. “Beautiful night kuma Aliya?â€? Kai Aliya ta gyad’a, kana tana dariya tace. “Eh mana Aunty Zee beautiful night, ma’anan Laylerh ai dare ne, to ita kyakkyawan dare ne mai yawan stars.â€? Dariya Aunty Zee tayi, tare kuma dajan wani d’an guntun tsaki, domin kuwa idan da sabo to ta saba da halin Aleeya, always acikin shirme da yawan surutu take. Laylerh ma murmushi tayi, saidai batace komae ba, hannunta Aleeya ta kama suka nufi d’aya daga cikin d’akunan dake k’asa wanda acikinsane d’akin Aleeya d’in yake. Har sunkai bakin k’ofar muryar Aunty Zee ya tsaidasu inda take cewa. “Idan sun shiga d’akin Aleeya ta shiryawa Laylerh kayanta acikin drawer, sannan kuma ta taimaka mata tayi wanka, daganan sai suzo suci abinci.â€? Da “To.â€? Aleeya ta amsa sannan suka shige cikin d’akin, itakuwa Aunty Zee sama ta haura, Dan anan bedroom d’inta dana mijinta da kuma na two kids d’inta suke. *M.Jay* Shigowarsu cikin airport d’in kenan aka soma k’iraye k’irayen sallan magrib, hakan yasa Abdoul na gama parking ya bud’e murfin motar ya fito. Saidai ma tun kafun ya gama fitowa abokan aikinsa wanda dasu za’ayi tafiyar, sukayi saurin k’arasowa wajen tare da sara masa, kasancewar dukansu shine ogansu, duk da cewar kuwa suma sunada babban matsayi amma nasa matsayin ya fi nasu, kuma akowanni tafiya shine shugabansu, haka ko awajen horarwa ma shine mai horar dasu. Yana gama fitowa daga cikin motar tasa kuwa Fou’ad na k’arasowa wajen, wanda shima yau shirye yake tsab cikin soldiers uniform d’insa, da suka k’ara bayyana zallan kyawunsa, wanda har idan ka kallesa ba zaka ce shine wannan mai raunin ba. Hannu ya mik’awa Maleek d’in suka gaisa, tare da soma yi masa wani irin kallo mai d’auke da tambayar. “Har yaushe ka warke da zaka iyayin wannan tafiyar?â€? Gane abunda Fou’ad d’in ke nufine kuma yasa Maleek d’auke kai daga kallonsa, murfin motarsa ya bud’e ya d’auko goran ruwa, batare daya kula kowannensu ba kuwa ya soma gabatar da Alwala’n sallan Magriba. Ganin hakan da sukayine kuma yasa dukkaninsu kowa ya nemi ruwa yayi alwala. Bayan dukansu sun kammala alwalan ne kuma dukansu suka had’a jam’i sukayi sallan magriba. Daganan gaba d’ayansu suka nufi jirgi, domin tuni wasu harsun fara shiga. Kasan shine yayi na k’arshen shiga jirgin, wanda yana shiga baijimaba kuma aka kulle k’ofar jirgin. Kamar kuma yanda yake atsare 7:00 pm daidai jirginnasu ya d’aga zuwa sararin samaniya. Abdoul kuwa ganin tashinsu ne yasashi komawa cikin mota inda ya tarar da kuliyar Maleek d’in nata harkokinta kamar yadda ta saba, tuna halin Captain d’innasu ne kuma yasa shi sakin murmushi, tare da yiwa motar key kaitsaye ya kama hanyarsa ta dawowa gida. Kallon Momy Aunty Aina’u tayi fuskarta d’auke da tsananin mamaki tace. “A gaskiya bangane abunda kike son fad’aminba Aunty Suwaeba, wai kina nufin da gaske Najeeb ya saki Laylerh, yanzu kwata kwata babu aure atsakaninsu?.â€? Wani irin Murmushi mai d’auke da ma’anoni daban daban Momy dake zaune akan kujera tayi, Tabbas ayanzu ita kad’ai tasan abunda take sak’awa acikin rai da zuciyarta, domin alk’awari tayi cewar bazata tab’a bari wannan lokaci da kuma daman da tasamu su tafi abanza ba. D’an k’walin dake kanta tad’an turo gaba, cike kuma da son bayyana gaskiyar abunda ke cikin zuciyarta tace. “Abune da kika sani Aina’u akan wannan bazan tab’a gaya miki ba gaskiya ba, Tabbas Najeeb ya saki Laylerh, wanda kuma dasa hannuna hasalima ninayi duk wani abu dayasa ya saketa, Nina bankad’a masa sirrin da ke b’oye, har kuma nasa yaga hakan da idanunsa, yanzu kuma na samu abunda nakeso.â€? Takai k’arshen maganar nata da wani irin alfahari. Wanda yasa Aina’u zuba mata ido, domin kuwa har yanzu bata gane inda kalaman Yayartata suka dosa ba. Saidai kuma k’aguwa dason sanin mene plan d’in yayartata na gaba yasa ta cewa. “Yanzu Mekika shirya musu anan gaba? Sannan kuma mekika aikata haka dahar yasa Najeeb ya saketa? Saboda meyasa kuma kikayi hakan?.â€? Jin tambayar da Aina’un tayi matane yasa ta mik’ewa tsaye. Tare da d’an soma tafiya, saidai kuma ko taku uku batayi ba ta tsaya da tafiyan da takeyi d’in. Still wani shu’umin murmushi ta sakeyi tare da had’e hannayenta waje d’aya. Cikin muryar dake bayyanar da gaskiyar mummunan manufarta tace. “Saboda inason na maida ita karuwarsa, tayanda zasu kusanci juna batare da aure ba, idan kuma har baki fahimci abunda nake nufi ba, to ma’ana ina nufin su aikata ZINA kenan, so nake nasa musu wani abu na daban, wanda har abada zuciyarsu bazata tab’ayin sanyi ba.â€? *13/3/2021* *8:14 pm* 3/16/21, 8:55 AM - Ummi Tandama: *L.M* *Note editing* *Chapter 67* Idanu Aunty Aina’u ta d’an zaro waje, domin ita kanta mummunan fatan da kuma mugun nufin da Yar uwarta ta ke bin su Maleek d’in dashi ayanzu ya fara tsoratata, saboda ta fahimci cewa da gaske Momy’n keyi, burinta d’aya kawae shine taga ta kawar da duk wani farincikin daya shafi rayuwar LAYLERH MALEEK. Juyowa Momyn tayi ta kalli Aunty Aina’u, wanda tayi shiru ta kasa cewa komae. Baki ta bud’e daniyar yiwa Aunty Aina’un magana, amma kuma wani abu da ta tuna ne yasa ta fasa fad’in maganan dake cikin bakinta, juyawa tayi direct d’akinta ta nufa, tana me sakin wani munafukin murmushi. Aunty Aina’u kuwa da idanu tabita, domin kuwa ayanzu itakan takanji zuciyarta ta karaya daga aikatawa su Laylerh’n mugunta, saboda taji awa’azi babu kyau cutar da Maraya, tana kuma tsoron abunda zaije ya dawo, dan abune dayake abayyane duk wani mai mugun nufi da aniya baya k’arewa k’alau. Acan gidan Aunty Zee kuwa tsab Aleeya ta gama jerewa Laylerh kayanta dake cikin trolleybag zuwa drawer, sannan kuma ita tayiwa Laylerh’n jagora har tayi wanka. Yanzuma zaune take bisa sallayan da tayi sallah’n magriba akai. Idanunta wanda suke d’an bayyana kasala ta lumshe, Yayinda kuma sannu ahankali takejin wani irin sanyi na ratsa duk ilahirin jikinta, duk da cewar kuwa bawani sanyi sosae ake busawa ba, amma ita sanyin takeji. Yanayin yanda ta lumshe idanunnata da kuma shirun da tayi ne, yasa idan mutum ya kalleta zai tsammaci cewa tayi nisa acikin tunani ne, wanda kuma ahak’ik’anin gaskiya bawai hakan bane. Ta daiyi shirune kawai tana me sauraran yadda kowani bugun zuciyarta d’aya, ke mu’amalantuwa da tsananin soyayyarsa, ta yadda takejin kamar soyayyar tasa ce ke sake ruruwa acikin zuciya da gangar jikinta, Yayinda daga gefe guda kuwa takejin wani abu na musamman a kansa me kama da kewa. D’an muskutawa tayi tare da sanya hannayenta duka biyu ta k’ank’ame jikinta waje d’aya, danji take kaman ana cakan k’ahon zuciyarta. “Laylerh.â€? Aleeya dake tsaye tun d’azu agefenta ta k’ira sunanta. Jin muryar Aleeya’n da tayi acikin kunnuwanta ne kuma yasa tayi saurin bud’e idanunta, tare da d’ago kanta ta fuskance ta. Murmushi Aleeya ta sakar mata tare kuma da d’an rank’wafowa ta kama hannun Laylerh’n, cikin tausasa murya da kuma nuna alaman tausayawa tace. “Tunanin me kike? Kodae baki da lafiyane na fad’awa Aunty Zee takaiki hospital?.â€? Murmushin daya bayyana kyawawan teeth d’inta tayi, hak’ik’a yau ne zuwanta gidan, amma acikin abunda bai wuce 1hour ba ta fahimci cewar Aleeya na sonta. “Babu komae kawai dai sanyi nakeji, kuma shid’inma bawani sosae ba.â€? Tafad’i hakan cike dason kawarwa da Aleeya kokwanton dake cikin ranta. Jin hakanne kuma yasa Aleeya, kamo hannunta suka mik’e tsaye atare, batare kuma da tajira komai ba tace. “To Muje falo muci abinci idan muka gama saikiyi sallan Isha ki kwanta, naji ma Aunty Zee tace wae jibi zaku fara WAEC (West African Examination Council), dole kina buk’atar time d’in da zakiyi karatu.â€? Kai kawae Laylerh’n ta iya jinjina mata, daga haka suka fice daga cikin d’akin. Koda suka fito falo kuwa direct dining table suka nufa, wanda tuni house girl d’in Aunty Zee d’in ta rigada ta shirya komae. Coconut rice and fruit salad Aleeya ta zuba musu, tare da matsowa kusa da Laylerh’n tace suci. Sam bata wani jin yunwa sosae, amma kuma saidai ganin yanda Aleeya’n keta d’awainiya da itane yasa ta d’aukan spoon ta soma cin abincin. Yayinda Aleeya ke ta bata labarai kala kala, wanda yawancinsu duk labaran Films ne, saboda Aleeyan bayan zuwa school bata da wani aiki sai kallon films. Tunkuwa Laylerh’n bata enjoying labaran films d’in da Aleeya’n ke bata, har ta fara enjoying, ahaka har suka kammala cin abincin daidai lokacinne kuma aka fara k’iraye k’irayen sallan Isha. Hakan yasa dukansu atare suka mik’e dan zuwa gabatar da salla’n Isha. *Washington DC🇺🇸* Kusan kota Ina dake cikin babban airport d’in d’auke yake da jama’a wanda kuma kusan gaba d’aya mutanen dake wajen suka kasance fararen fata, Yayinda kuma kowannensu da abunda yakeyi. Saidai kuma isowar babban jirgin da Kusan dukkaninsu shi suke jirane yasa gaba d’ayansu kowa ya nutsu. Sannu ahankali kuma jirgin daya sauk’a ya gama daidaita tsayuwarsa. Bayan kuma sauk’arsa da mintuna kad’an aka bud’e babban k’ofar fita daga cikinsa. Wanda hakanne ya bawa mutanen dake cikinsa daman soma firfitowa anutse. Ahankali ya bud’e idanunsa wanda suka b’ata tsawon some minutes arufe, wani irin sassanyar ajiyar zuciya ya sauk’e, had’e da zare sit belt d’in dake jikinsa ya mik’e tsaye. Ganin hakanne kuma yasa Fou’ad dake zaune shima ya mik’e tsaye, tare dabin bayan Captain Maleek d’in wanda tuni ya riga daya fara tafiya, kasancewar tuni sauran abokan aikinsu da suka taho tare sun riga dasun sauk’a. Cikin takunsa mai d’auke da izza yake sauk’owa daga kan matattakalan jirgin, Yayinda hannunsa na dama ke d’auke da jakarsa. Jin yanda Fou’ad dake bayansa ke d’an magana k’asa k’asane yasashi d’an juyawa ya kalleshi, saidai kuma bai tankawa Fou’ad d’inba ya k’arasa sauk’owa daga kan steps d’in jirgin, duk da kuwa yasan cewar dashi Fou’ad d’in yake. Yana gama sauk’owa daga kan steps d’in kuwa, sauran soldiers d’in da yake wakilta, da kuma way’anda suka zo tarbansa suka soma sara masa, wasu daga cikinsu kuwa murfin had’add’iyar motar da suka zo d’aukansa aciki suka bud’e masa, batare daya jira komae ba kuwa ya Sakai ya shige cikin motar. Ganin hakanne kuma yasa duk sauran soldiers d’in suma suka shishshiga motocinsu, kaitsaye suka nufi waje na musamman daya kasance masauk’insu. Koda suka k’arasa wajen dayake kaman camp d’insu, cike area’n wajen yake da soldiers hakan yasa hayaniyan dake wajen ya d’anso yin yawa. Kasancewarsa kuma ba maison yawan hayaniya ba shiyasa yana fitowa daga cikin mota kaitsaye yanufi can cikin gurin, inda anan room d’insa mai number 15 yake. Yana shiga cikin d’aki me kaman aljannar duniyar kuwa, ya turo k’ofar d’akin ya rufe, tare dasa key domin kwata kwata bayason damuwa, ya kuma san yana barin d’akin abud’e to fa Fou’ad zaizo ya takura rayuwarsa. Bud’e wani glass drawer’n dake cikin d’akin yayi tare da jefa jakar dake hannunsa aciki. Anutse ya soma rage kayan dake jikinsa, bayan kuma ya kammalane ya d’aura wani white towel akan waist d’insa, cikin zak’uwa da kuma son hutawa gajiyar dake jikinsa ya wuce toilet d’in dake cikin d’akin wanda ya kasance shima na zallan Glass ne, saidai kuma amma na waje sam Bazai tab’a iya ganin na ciki ba, saidai kuma wanda ke cikin toilet d’in zaiga wanda ke waje. Sassanyan ruwan dake cikin shower ya sakarwa kansa, batare kuma daya damu da irin sanyin da akeyi a garin ba. Bawae kuma dan bayajin sanyin bane, kawai k’arfin hali da kuma taurin zuciyane irin nasa. Batare kuma daya b’ata lokacinsa sosae ba ya kammala wankan nasa tare da d’auro alwala, dan gabatar da sallan Isha. Ahankali ya bud’e k’ofar toilet d’in ya fito, hannunsa rik’e da d’an madaidaicin towel yana goge ruwan dake jiki da kuma kansa. Bayan ya kammala goge jikinnasa ne kuma yayi amfani da wani new edition handryer ya busar da tarin suman kansa. Gaban wani makeken dressing mirror ya kalla, wanda aka ci kasa da kayan shafa irin wanda ya ke amfani dasu, wanda hakan kuma yasan ba aikin kowa bane, sai na mutanen dake k’asa dashi, domin kowa yasansa to yasan halinsa, idan har zayyi tafiya to baya d’aukan wasu shirme, yafison atanadar masa da komae a inda zaije d’in. Body lotion da kuma turaren D&G kawae ya shafa ajikinsa, yana tsaye agaban mirror d’in kuwa aka soma yi masa knocking k’ofa. Sanin wanda ke knocking d’inne kuma yasashi k’arasawa ya bud’e k’ofar, tare kuma da d’an matsawa, ya bawa D’aya daga cikin ma’aikatan soldiers d’in nasu daman shigowa cikin d’akin, anan kan gado ya ajiye masa manya manyan ledodin da cikinsu ke d’auke da new clothes, cikin harshen turanci kuma ya tambayesa ko akwae wani abunda yake buk’ata. Kansa kawai ya girgiza alaman “Babu.â€? Ganin hakanne kuma yasa soldier d’in juyawa ya fita, shi kuwa atake yasake locking door d’in. Tare da bud’e d’aya daga cikin manya manyan ledodin clothes d’in. Wani dogon wandon combat had’e da white shirt wanda agabanta aka rubuta “To be a strongâ€? da blue painting ya ciro tare da sanyawa ajikinsa. Sosae kuwa kayan sukayi masa kyau, again wani babban sallaya ya ciro daga cikin ledan, had’e da shumfud’asa ak’asa ya tada sallah. Almost 13minutes ya d’auka kafun ya idar da sallan. Saboda kuma gajiya da ciwon da yakejin mararsa nayi masane yasashi tak’aita addu’oinsa. Mik’ewa tsaye yayi tare da cire rigan dake jikinsa, wanda kuma yayi hakanne don ba al’adarsa bace kwana da riga, sannan kuma akwae raunuka ajikinsa wanda basa buk’atar arufesu. K’arasawa inda ya ajiye jakarsa yayi tare da zuge zip d’inta, ya ciro pain relievers d’insa da kuma wayoyinsa da tuntuni suke akashe. Kunna wayoyinnasa yayi, had’e kuma da d’aukan goran ruwa, yasha magungunansa, domin zuwa yanzu har wani irin zogi yakejin cikin marar nasa nayi masa. Bayan ya kwanta akan makeken gadon dake cikin d’akinne kuma, akasalance ya mik’a hannunsa ya kashe gaba d’aya hasken wutan dake cikin d’akin, saidai kuma sanin da yayi cewar babu kyau kwana acikin duhu ne, yasa ya d’an kunna electric kindle d’in dake gefen gadon, hakan kuwa shiyasa haske ya d’an bayyana acikin d’akin. Wata irin numfashi mai sauti yaja adaidai lokacin daya ajiye kansa akan tattausan pillow’n dake kan gadon. Asanyaye kuma yasa hannunsa na dama ya dafe saman mararsa. Tabbas shi kad’ai yasan me yakeji ayanzun, duk da cewar yanayin nasa Bawae bak’o bane agaresa, amma ya d’an kwana biyu baiji hakan ba. Ahankali ya lumshe sassanyun idanunsa masu d’auke da yanayin bacci, wani irin abu ne yakeji na yawo acikin jikinsa, wanda hakan yasa gaba d’aya gargasan dake jikinsa suka mimmik’e. Tabbas akowacce duniya yake ita kad’ai ce acikin tunaninsa, koda da second d’aya ne kuwa zuciyarsa bata tab’a bugawa batare da ita acikinta ba. Wannan dalilin yasa har yakan kasa tantance matsayin yanda yakejinta acikin zuciyarsa, domin dayawan lokuta tunaninta kan rikid’e ya dawo matsanancin kewa. Kamar dai ayanzu da yakejin sonta na game duk ilahirin jikinsa, wanda kuma sanadin k’arfin hakan, ya haifar masa da wani irin feeling mai k’arfi. Jajayen red lips d’insa ya d’an ciza, tare dasa hannunsa ya sake dafe saman maransa. Tayaya zai misalta irin hot feeling d’inta da yakeji yau d’in? sannan kuma tayaya zai iya jurewa imagine d’inta da eye balls d’insa keyi? Sake matse jikinsa waje d’aya yayi, had’e da d’aukan pillow ya d’aura akan fuskarsa. Cikin dakiya da k’arfin hali kuwa yasoma k’ok’arin k’ak’alowa kansa baccin dole. Akuma daidai wannan lokacin itama ta lumshe Idanunta wanda suke cike da ruwan hawaye. Ahankali ta juyar da kanta daga kallon Aleeya dake ta faman bacci, zuwa kan had’add’en agogon dake cikin d’akin. 12:45 am. Kenan amma har zuwa yanzu bacci ya kasa d’aukarta, duk da cewar tanajinsa cike a idanunta, amma sam zuciyarta bata da nutsuwar yinsa. Domin kuwa yau d’in ganin kanta takeyi acikin wata irin sabuwar rayuwa. Pillown dake gefenta ta rungume, tare kuma da cusa kanta acikinsa. Lallai ayau ta yarda cewa k’addara kan iya sauyawa in a few second, ba kuma lallaine sauyinta ya zamo mai sauk’i ba. Haka zalika ba Lallai abunda kake hange da tunani ya zamanto shine akwae ba. Tabbas ayau ta fahimci cewa akwae abubuwa da yawa da basu zoba, sannan akwae kuma way’anda suka zo suka wuce, da har abada bazasu tab’a dawowa ba. Sannan akullum akuma koda yaushe sanyawa kai k’warin guiwa, shi ke taimakawa izuwa Nasara. Still sassanyar ajiyar zuciya ta sake sauk’ewa, akaro na biyu kuma ta lumshe idanunta, Yayinda acikin ranta take fatan bacci ya d’auketa. Ae kuwa Allah Ya duba zuciyarta, cikin mintuna k’alilan wani bacci mai nauyi ya d’auketa, saidai kuma acikin baccin nata akwai mafarkai da yawa mabanbanta. *Washegari* Alhamdulillah Yau tun tashinta takejin zuciyarta asanyaye, hakanne ma yasa ta taimakawa Aleeya suka shirya breakfast. Ganin kuma yanda Laylerh’n ta d’an sakene yasa Aleeya jin dadi sosae haka ta dinga Jan Laylerh’n da hira. Bayan anyi sallan azahar ne kuma Oum Ayush tazo, ita da Teemah inda ta kawowa Laylerh’n sabon uniform da kuma kayan fiye ciye ciye. Sosae Laylerh’n taji dad’in ganin Oum Ayush da kuma Teemah’n, musamman ma Teemah wanda tayi missing dinta sosae. Anan cikin babban falon Aunty Zee suka zauna inda Teemah ta shiga koyawa Laylerh’n abubuwan da akayi a school d’in bayan bata nan. Sosae kuwa ta fahimci abunda Teemah’n ke son fahimtar da ita. Haka dae Teemah da Oum Ayush d’in suka zauna har saida dare yayi kafun suka tafi, Inda Oum Ayush da kanta tamayar da Teemah’n gida, domin dama ita taje ta d’auko ta. *8:46 pm* *15/3/2021* 3/18/21, 9:36 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna *Not editing* *Chapter 68* 7:00 am daidai haka k’ararrawar dake jikin babban agogon bangon dake cikin d’akin ya buga. Daidai lokacin kuwa ta d’ago kanta ta kalli agogon, domin dama tun d’azu 7 d’in take jira ya cika, kasancewar k’arfe 8:00 am ne daidai zasu shiga exam d’innasu. Shiyasa ma tunda tayi sallan asuba bata koma bacci ba, d’aukan takardun da Teemah ta kawo mata tayi ta soma karantawa. Yayinda Aleeya ko keta sharar bacci, duk da cewar itama yau d’inne zasu fara exam a school d’insu, amma kuma saidai b’ata lokacin da tayi Daren jiya tana kallon film ne yasa ko sallah’n asuba da k’yar ta iya tashi tayi. Kallonta ta mayar ga Aleeya, kaman kuma zata tasheta saita fasa, ahankali ta mik’e tsaye, tare da zare hijab d’in dake jikinta, kaitsaye toilet d’in dake cikin d’akin ta nufa. Koda ta k’arasa cikin toilet d’in kayan dake jikinta ta cire tare da sanya shower cap akanta, kasancewar kuma yau d’in ana d’an yanayin zafi ne yasa ta k’arasawa gaban shower ta sakarwa kanta ruwa. Bayan tagama wankanne kuma tayi brush, tare da d’aukan wani d’an k’aramin towel ta shiga tsane ruwan dake jikinta. Ahaka ta fito daga toilet d’in, still sake kallon Aleeya dake ta faman sharara bacci tayi, yanzun kam lokaci ya d’an tafi shiyasa bazata iya barin Aleeya’n ta cigaba da bacci ba. Hannunta tasa tad’an tab’a Aleeya’n hakanne kuwa yasa Aleeya’n tashi zaune, cikin yanayin magagin bacci tace. “Namakara ko?â€? “Kindai kusa amma kuma ci gaba da baccinki daidai yake da makaranki.â€? Laylerh’n ta bata amsa adaidai lokacin da take k’arasawa gaban mirror. Body lotion na company’n Nivea ta shafa ajikinta, sai kuma powder da wani brown lipsgloss da ta shafa akan jajayen labb’anta, iya kwalli kawae ta shafa acikin idanunta, daga haka kuwa bata sake goga komae akan fuskar nata ba, direct wajen drawer’n dake cikin d’akin ta nufa, koda ta bud’e drawer’n sabon uniform d’in da Oum Ayush ta kawo mata ta ciro tare da sakawa ajikinta, sosai kuwa uniform d’in ya zauna ajikinta, sannan kuma ko kad’an bai bayyana wani shatin sura na jikinta ba, ya rufe ko ina d’inta, hatta hijab d’inma duk da cewar bashi da girma amma ya rufe guiwan hannayenta. Wasu White socks d’inta masu tsayi ta saka, tare da wasu fararen takalma wayanda suke yanayi da sneakers shoe. Sake d’ago kanta tayi ta kalli agogon dake cikin d’akin, wanda yake nuna 7:30 am daidai. Face mask d’inta ta d’auka tare kuma da wasu fararen papers cikin sauri ta nufi hanyar fita daga cikin dakin, daidai lokacin kuwa Aleeya ta fito daga toilet jikinta d’auke da danshin ruwa. Ganin da tayi kuma Laylerh’n ta shirya ne yasa itama cikin hanzari ta soma shirya kanta. Laylerh kuwa tana fita daga cikin d’akin direct falo ta fito, inda ta samu Aunty Zee da Mijinta zaune akan dining table. Aladabce ta gaishesu dukansu kuwa fuska d’auke da murmushi suka amsa mata, kana cikin kulawa Aunty Zee tace. “Yanzu nake da shirin zuwa k’iranku kuyi breakfast, domin naga har takwas d’in ma ta kusa baku fito ba, Ina Aleeya’n kuma ta tsaya?.â€? “Tana shiryawa.â€? Tafad’i hakan asanyaye, tare kuma da d’an sunkuyar da kanta k’asa. Kai kawai Aunty Zee tajinjina domin dama ita tasan halin Aleeya badai saib’i ba. Kujera ta nunawa Laylerh’n had’e da cewa. “Kizo kici abinci.â€? “To.â€? Kawae ta iya cewa duk da cewar kuwa bata wani jin yunwa sosai, saidai kuma amma sam batason cewa Aunty Zee d’in a’a, musamman ma da tafahimci cewa Aunty Zee d’in da kuma Mijinta wanda Aleeya take k’ira da Yah Jameel suna da mutumci sosae. K’arasowa dining area d’in tayi tare da zama akan kujeran da Aunty Zee d’in ke nuna mata. Itakuwa Aunty Zee da kanta tayi serving Laylerh’n. Suna fara cin abincin kuwa Aleeya ta fito itama cikin shirinta. Akujerar dake kusa dana Laylerh ta zauna, cikin sauri sauri ta soma cin abincin gudun kada tajawo musu latti, domin driver’n da zai kaisu makarantar saiya fara kai Laylerh kafun ita, kasancewar school d’in su Laylerh’n yafi kusa. Kwata kwata kuwa ko mintuna 10 ba suyi sunacin abincin ba kuwa, kowaccensu ta ajiye spoon d’in dake hannunta. Laylerh ce ta fara mik’ewa tsaye, domin kuwa taga time d’insu nata tafiya. Ganin hakanne kuma yasa Mijin Aunty Zee d’in sa hannunsa aciki aljihun rigar dake jikinsa, fararen 1k ya ciro tare da bawa kowaccensu d’aya, Laylerh kam bata saba hakan ba, shiyasa tak’i k’arb’a, amma kuma ganin yanda ya had’e fuska yasa ta k’arb’a tare dayi masa godiya. Aunty Zee kuwa addu’a da fatan samun nasara ta musu, Laylerh kuwa har takai bakin k’ofar fita daga falon, Jin da tayi kuma Aunty Zee d’in tak’ira sunanta ne yasata tsayawa tare da juyowa ta fuskanceta. Murmushi Aunty Zee d’in ta sakar mata, cikin kuma tsananin kulawa tace. “Ina fata baki manta maganganun da Oum Ayush ta fad’a miki ba, sannan kome zakiyi kada ki tab’a mantawa da matsayin dakike kai ayanzu, kada ki kulawa kowa saidai idan yazama dolen dole, sannan ki k’ebe kanki waje d’aya, banda yawan surutu, da zaran kunfito a exam kuma ki k’ira wayana zan turo driver ya d’aukeki, dan Allah Laylerh kikula da kanki sosae, kinga fita ma sam baikamaceki ba saidon kawae ya zamanto dole ne.â€? Ahankali ta d’an jinjina kanta, cikin kuma son nunawa Aunty Zee d’in cewa ta fahimci abunda suke son nusar da ita tace. “Insha Allah Zankiyaye.â€? “Allah Yasa.â€? Aunty Zee d’in tafad’a. Itakuwa Laylerh juyawa tayi ta fice daga cikin falon, Dan tuni Aleeya tayi waje. Koda ta fito compound d’in gidan kuwa direct inda motar da za’a kaisu makarantar ke fake ta nufa, tana zuwa kuwa ta bud’e murfin motar tashiga, akusa da Aleeya ta zauna. Take driver’n kuwa yaja motar suka tafi. Kamar yanda yake makarantar su Laylerh’nce afarko hakan yasa ita driver’n ya fara sauk’ewa, saida suka ga shiganta cikin skull d’in kuwa kafun suka juya suka tafi. Tana shigowa cikin school d’in nasu kuwa ta hango Teemah, hakanne yasa ta k’arasa wajen da Teemah’n ke zaune. Teemah kuwa dake zaune ganin Laylerh’n ta nufota ne, yasa ta fad’a d’a murmushin dake kan fuskarta, take kuma duk wani tausayin Laylerh’n da takeji acikin zuciyarta ya bayyana kansa acikin k’wayoyin idanunta. Tabbas Allah Yasani tana tausayin Laylerh’n sosai, ko adacan ma bare yanzu da k’addara ta fad’a mata. Wasu irin hawaye da suka cika idanunta ne yasa ta wayance. Cikin salon tsokana tace. “Ke kuma ya haka kin b’oyemana kyawun fuskar taki da face mask, kodai har anfara tattalawa Mr.Soldier fuskar ne?â€? Hararan wasa Laylerh’n ta watsa mata tare da cewa. “Tayaya hakan zai faru bayan kinjima kina sonshi.â€? Murmushi mai had’e da dariya Teemah tayi, tare da mik’ewa tsaye ta kamo hannun Laylerh’n, Idanunta ta d’an lumshe, cikin yanayi da kuma sigar da tasan Laylerh’n zata fahimceta tace. “Tabbas ada nayi tunanin cewa abunda nakeji a kansa sone, but amma yanzu na tabbar da cewa ba sonsa nake ba, just kawae yana burgeni ne, kuma kin dai san Namiji irin Mr. Soldier babu macen da bazae burgeba, sannan kuma hak’ik’a nikam na yarda SO d’aya ne, akuma duniyar nan gaba d’aya babu wacce zata soshi kamar yanda kike sonsa, sannan kuma ke kad’ai ce choice d’insa, saboda ke da shi d’in kun kasance MURADI d’aya ne, rabaku ayanzu daidai yake da raba mutum da rayuwa, infact ma ayanzu wanda yace zai katse wannan burin zai iya mutuwa, ko dai kinason na mutu anan kusa ne?.â€? Kai Laylerh’n ta girgiza mata, tare kuma da lumshe idanunta, wanda kuma hakanne ya bawa hawayen dake cikin idanunnata, daman gangarowa kan fuskarta. Tabbas maganganun da Teemah’n ta fad’a mata ayanzu, sunsa wani irin matsanancin soyayyar Maleek d’in ya sake motsa mata, hakanne kuma yasa ta kasa cewa komae. Teemah kam tasan komai, da kuma irin raunin da zuciyar Laylerh’n ke dashi akan Maleek, shiyasa ma bataso sake jin wani abu daga bakinta ba. Ahankali ta kamo hannunta, batare kuma da tasake ce mata komae ba, kai tsaye suka nufi exam hall d’in, da acikinsa ne zasu gudanar da jarrabawar tasu, inda kowannensu yake d’auke da number’n kujerarsa. Kasancewar kuma numbers d’insu basa kamanceceniya da juna, wannan yasa koda suka shiga cikin exam hall d’in kowacce ta nufi mazauninta. Suna zama kuwa aka soma raba musu questions papers. Time na cika kuwa suka fara answer questions d’in. Sosai kuwa abun yazowa Laylerh da sauk’i, domin kusan rabin questions d’in takaranta amsansu ayau da asuba bayan tayi sallah, wannan yasa bata wani sha wahala ba. Duk da cewar kuma 1hour and 30 minutes kad’ai aka basu sugama answering questions d’in, sai gashi kuma acikin 1hour kad’ae kusan gaba d’aya students d’in sungama amsa questions d’in da zasu iya amsawa. Ciki kuwa harda Laylerh da Teemah bayan sun gama ne kuma dukansu sukayi submit papers d’in suka fita. Anan k’asan wata bishiya suka zauna ita da Teemah, tare da soma karatun next paper’n da zasu shiga anan gaba wanda tsakaninsa da wancan papern kwata kwata 40minute ne. Karatu sukayi sosae mintuna 40 na cika kuwa suka sake komawa exam. Sosae wannan paper’n ya basu wahala kasancewar sa na Geography ne. Amma kuma cikin ikon Ubangiji sun samu sun rubutasa tare dasa ran cewa zasu samu marking mai yawa. 11:30 am daidai suka fito daga exam d’in nasu, kamar yanda Aunty Zee ta fad’a kuwa, suna fitowa Laylerh ta ciro wayarta dake kashe, kasancewar da zasu shiga exam d’in kashe wayoyinsu sukayi kana suka bada ajiya, saboda doka ne ba’a shiga exam d’in da waya. Kunna wayartata tayi tare dayin dialing Number’’n Aunty Zee. Bugu biyu kuwa Aunty Zee d’in ta d’aga wayar. Gaya mata kuma da Laylerh’n tayi cewar sun gama exam ne yasa ta cewa gatanan zuwa, zata zo ta d’auketa, domin ayanzun tana kusa da makarantar su Laylerh’n. Cikin abunda bai wuce 15minutes ba kuwa saiga Aunty Zee d’in tazo, har bakin Mota Teemah ta raka Laylerh’n, saida taga tafiyarsu kuma kafun ta koma cikin makarantar dan a cewar ta zata shiga library’n makarantar tasu fad’an tab’a karatun exam d’in da zasuyi gobe, saboda goben ma two papers zasuyi. B’angaren Laylerh’’n ma hakance takasance dan Koda suka koma gida karatu ta wuni yi, duk da yanda takejin soyayyarsa nayi mata suka acikin zuciyarta amma haka ta daure, musamman ma da ayanzu ta gano cewa idan babu tunaninsa acikin mind d’inta to babu abunda zata iya. Koda dare yayi kuwa bata wani iya samun bacci sosae ba, karatu tayi sosai, Yayinda kuma kewarsa ke k’ara cika wani sashi na zuciyarta wanda har hakan yake sawa taji kamar tayi kuka. Haka dai tayi ta abu d’aya har saida dare ya raba kafun ta iya samun bacci. *Washegari* Kamar dai yanda jiyan suka tafi school tare da Aleeya, haka ma yau, still saida aka sauk’eta kafun aka wuce da Aleeya. Balaifi kuma exam d’in nasu na yau ya d’anyi musu sauk’i. Paper biyu sukayi saidai yau ba kaman jiya ba sai 12 dukansu sukabar makarantar. Daga wannan ranan kuwa koda yaushe ya zamana Laylerh’n tana cikin karatu, duk da kuwa tanajin matsanancin kewarsa acikin rai da zuciyarta amma haka take daurewa, aduk lokacin da tayi imagine d’insa kuwa haka takejin kaman zata shid’e. Yayinda akullum hot feeling d’in da takeji akansa ke sake k’aruwa **** *** *** Tabbas adaidai irin wannan lokacin idan tace batajin dad’in zama agidan Aunty Zee tayi k’arya, domin suna bata kulawa maikyau, sannan kuma kullum sai tayi waya da Abbou Jaheed da kuma Oum Ayush, Yayinda Abbou Khareem ma ke k’ok’arin k’iranta. Afannin mu’amala kuwa ita da Aleeya yanzu sun zama k’awaye sosae, aduk lokacin da sukaje exam suka dawo sukan zauna su taya Aunty Zee aikace aikacen gida, hakan kuwa bak’aramin dad’i yakeyiwa Aunty Zee d’in ba, shi yasa ma yanzun bata shakkan saya musu komai na k’yale k’yale idan ta gani. Babban abun da yake bawa Aunty Zee d’in mamaki kuwa shine, yanda har abada, Laylerh’n bata tab’a gajiyawa da kallon wani hoton Maleek dake cikin wayarta, domin da yawan lokuta Laylerh’n takan zauna tayi shiru, idan kuma tana kallon hoton Maleek d’in abune mawuyaci kaga babu k’walla acikin idanunta, wannan abun kuwa shiyasa Aunty Zee take mamakin irin tsananin soyayyar da Laylerh’n keyiwa Maleek. Kamar yanda ranar yau ta kasance Friday, wanda ayau d’inne kuma zasu kammala WAEC examination d’insu. Hakan yasa duk d’aliban dake zana waec zuciyarsu ke cike da farinciki, ga masu shirin zana neco exam kuwa hankalinsu ya tafi gaba. Kasancewar kuma yau itace ranan k’arshe, shiyasa d’aliban suka b’ata lokaci mai tsawo basu fito a exam d’in ba, domin ba kad’an ba paper’n da ta kasance na Maths ta basu wahala. Wanda hakan yasa sai k’arfe 11am suka fito. Gaba d’aya compound d’in school d’innasu cike yake da d’alibai maza da mata, Yayinda kuma fiye da rabin students d’in suka b’ata uniform d’insu da zanen maka different colours. Tabbas awannan lokacin zuciyar gaba d’aya d’aliban cike take da farinciki. Saidai kuma ita acikin nata zuciyar banbanci ne da nasu, dake d’auke da wani irin yanayi. Yanayin da akowacce rana yake gudana acikin jikinta kamar jini. Tabbas ba zata iya fad’in sunan yanayin nata kaitsaye ba, domin akullum salo da zafinsa sanjawa yake, saboda yana hurting d’in zuciya da gangar jikinta sosae. Duk da kuwa cewar yanayin ada bai zamo bak’o agareta ba, amma ayanzu tanajinsa wani daban. Domin kuwa koda Idanunta ta lumshe saitaga nasa idanun acikin nata. Tabbas kuma hakan shi ne ke k’ara haddasa mata matsanancin kewarsa. Koda sau d’ayane kuwa tanason sake sanyashi acikin idanunta, Kamar dai yanda sau d’aya tak kawai ya bar mata wani azababben yanayin da har abada bazata tab’a iya mantawa dashi ba. Yanayin daya zamo sanyi kuma Garkuwa agareta, kana kuma yanayin da tunda take aduniya bata tab’a sanin akwaesa ba. Wani irin tashi tsikar jikinta ya shiga yi, haka ma y’an hairs d’in dake jikinta suka mimmik’e, lokaci d’aya sweet moment d’in ya shiga yawo acikin Brain d’inta, wanda hakan ya haifar mata da wani irin bugun zuciya. Hakanan taji tamkar yazune abun ke faruwa. Hannayenta duka biyu tasa ta k’ank’ame jikinta, tare kuma da lumshe idanunta, wanda suke dake dawo mata da ganin lokacin daya sauk’e lips d’insa akan nata, acikin yanayin sanyi kuma ya tura sweet tongue d’insa acikin bakinta. Wayyo Allah Tayaya ma zata iya mantawa da wannan best moment d’in? Lallai jure hakan abune mai wahala, domin tayi imani a zuciyarta cewa idan irin hakan ya sake faruwa, babu ko tantama zata iya rasa numfashinta, domin abune mai matuk’ar girma da daraja samun professional kiss daga wajen wanda zuciya da gaba d’aya gangar jiki keso. Tabbas wani lokaci magana bata aika sak’o zuwa ga inda zuciya keso, domin wani lokaci magana a iya kunne kawae take tsaya wa, bata kaiwa izuwa gangar jiki, madadin hakan kuwa abu biyune kawae ke tasiri wa gangar jiki da kuma k’wak’walwa, wannan abu biyun kuma sune KISS and HUGGING. Amatuk’ar kasalance ta bud’e idanunta dake lumshe, tare da zubawa wayarta dake ringing idanu. Ganin kuma numbern da ake k’iranta dashi d’in ba na Nigeria bane yasa ta d’an tsurawa wayar idanu. Saidai kuma ganin k’iran na shirin katsawa ne Yasa tayi saurin d’aukan wayar tare da kara ta akan kunnenta. Hakan kuwa yayi daidai da samun kanta da tayi cikin wani irin bugun zuciya, take kuma taji wani irin sanyi mai tsananin dad’i na ratsa duk ilahirin jikinta, irin dai sanyin da awajen mutum d’aya kawae take samunshi, Tabbas wannan yanayin shi ya sauk’ar mata da kasala, wanda har hakan yasa ta kasa cewa komae. Daga can b’angaren kuwa sauk’an numfashinta acikin kunnuwansa ne , yasa shi lumshe idanunsa wanda sukayi jajur, tare dasa hannunsa ahankali ya dafe saman mararsa. Cikin wani irin sabon yanayin daya samu kansa aciki kuwa ya d’an saki wani silent growing tare da bud’e gaba d’aya labb’an bakinsa. *18/March/2021* *6:32 pm* 3/19/21, 9:08 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Chapter 69* Hak’ik’a shiru da kuma dad’in yanayin da ta samu kanta aciki ya masifar shagaltar da ita, wanda har hakan ya sata maida idanunta ta lumshe, kana ahankali ta cigaba da sauk’e wani irin breath, wanda ita kanta batasan tayaya akayi sautin numfashin nata ke tashi har haka ba, sassanyar iskar dake ci gaba da k’ara ratsa duk ilahirin jikinta ne, kuma yasa ahankali cikin yanayi mai kama da zallan shagwab’a ta bud’e y’an k’ananun jajayen labb’anta. Da muryarta wanda ke fitar da shaking sound tace. “Assalamu Alaekum!!â€? Adaidai lokacin kuwa, yaji wani irin abu me kama da shocking ya ratsa duk ilahirin jikinsa, wanda hakan yasa take kwantattun gargasan dake jikinsa suka soma mimmik’ewa tsaye, haka ma tunaninsa ya tsaya cak, hakan ya faru ne kuma saboda sauk’an, da daddad’a da kuma kasallliyar muryarta a cikin kunnuwansa. Ahankali ya fusgo numfashinsa dake k’ok’arin d’aukewa, tare kuma da saurin zare wayar daga kan kunnensa, batare kuma daya amsa sallaman nata, ko yace wani abu ba ya k’urawa gaban screen d’in wayar tasa idanu. Hak’ik’a yanzu shi kad’ai yasan meyake ji acikin jikinsa, domin jin muryarta da yayi ya goge masa duk wani lissafi da nutsuwarsa, musamman yanayin yanda maganan nata ke d’auke da wani irin salo na daban, salo mai cike da kasala, da kuma bayyana abunda ke cikin zuciyarta, domin kasancewarsa ma’abocinta, ad’an jin muryar ta da yayi yanzu, har zuciyarsa ta fassara masa yanayin da Laylerh’n nasa ke ciki. Wani irin abune yaji nayi masa yawo acikin zuciya da kuma gaba d’aya gangar jikinsa. Duk kuma ga yanda yaso motsa harshe da kuma labb’an bakinsa abun yaci tura, atak’aice ma dai haka yakejin kamar an nannad’e masa tongue d’insa. K’warae yanason bayyana abundake cikin zuciyarsa, ko da hakan zaisa ya d’anji sanyi. Saidai kuma amma tayaya zai iya furta hakan? Yau sama da 2weeks kenan da yakejin wani irin matsanancin kewarta na Adda ae zuciya da gangar jikinsa, duk da cewar tunda yazo USA d’in bai zauna ba, amma kome yake yi tana nan acikin zuciyarsa, da tunaninta yake kwana, haka kuma da matsanancin kewarta yake wuni. Sau dayawan lokuta yakan tambayi kansa shin yaushe ne zasu ji dad’in rayuwa shida ita? yaushe ne munanan k’addara zasu daina bibiyar rayuwarsu? sai yaushe ne zai sake samun wannan daman da ya samu abaya? Daman kusantarta akullum akuma koda yaushe, hakika ada yana sake tsammatawa kansa rayuwa da ita, ko da sau d’aya yana buk’atar sake shagwab’ata kamar yanda yayi abaya lokacin tana k’arama, yana buk’atar zama da ita, ta yadda jikinsa zai zame mata wajen bacci, sannan idan tayi kuka ya bata, finger d’insa ta tsotsa kamar yadda yakeyi mata abaya. Tabbas yasani aduniya ita kad’ai ce macen da zata fuskanci al’amuransa, sannan ita kad’aice macen da zai iya fuskanta da koma wacce irin damuwarsa, duk da cewar babu wanda yasan hakan amma shi ya sani, k’warae yasani cewar Laylerh ce kad’ae zata san damuwa da kuma abunda ke cikin zuciyarsa koda bai furta mata ba, ita ce kawae zata jurewa al’amuransa, itace wacce har abada yasani baza ta tab’a gajiyawa dashi ba, domin yayi imani cewa zuciyarsa da nata abu d’aya ne. Duk kuwa yanda yaso jurewa abunda yakeji ayanzu baya tab’a iyawa, domin acikin y’an kwanakin nan, zuciyarsa na yawan sak’a masa cewar bazai rayu da Laylerh ba, ba dan komae ba kuwa saidan lalura da kuma k’addarar da ta sameshi, domin yanaji ajikinsa cewa zama da ita ahaka tamkar cutar da rayuwar ta ne, duk da yasan Laylerh’n babu wata irin k’addararsa da bazata iya jib’anta ba. Saidai kuma amma akwae cutarwa aciki, ita yarinya ce k’arama da babu abunda ta sani, zuciyarta da kuma tunanin ta basu san komae ba sai abu d’aya, wanda kuma kullum akansa ne kawae take rayuwa. Idanunsa dake kan wayar tasa wanda suka sakeyin jajur, ya rumtse da k’arfi, tare dasa hannunsa d’aya ya katse k’iran. Sam ba zae iya jurewa abunda yakeji ba, saboda ayanzun zuciyarsa tayi rauni sosai, har yakai ga yanajin wani abu mai kaman ruwa na yawo acikin idanunsa. K’warae bashi da bakin da zai iyayi mata magana, saboda kowani magana d’aya da zaiyi mata, zai zama tamkar b’allewan bugun zuciyarsa ne. Acan b’angaren Laylerh kuwa jin an katse k’iran da akayi mata d’inne, yasa ahankali ta zare wayar daga kan kunnenta, kamar wanda ke na zarin wani abu kuwa haka ta k’urawa screen d’in wayarta ta idanu. Saidai kuma sam ta kasa fahimtar komae. Domin hatta tunaninta ma tsayawa yayi, saidai kuma still har yanzu bata dae na jin wannan sanyin na ratsa cikin jikinta ba. “Laylerh mekikeyi anan tun da muka fito paper nake ta nemanki, amma ban ganki ba.â€? Muryar Teemah dake k’arasowa wajen ya katse mata duk wani yanayi da take ciki. Ahankali ta d’ago kai ta kalli Teemah’n, Kamar kuma zata ce wani abu saita fasa, saboda hakanan taji duk jikinta yayi sanyi, Yayinda wani irin mood ke fusgarta. Teemah kuwa idanu ta d’an k’urawa Laylerh’n domin ta fahimci kamar tana cikin damuwa. Saidai kuma sanin da tayi cewar ako da yaushe, labarin da kuma damuwar Laylerh’n bata wuce ta Maleek shiyasa bata tambayeta agame da abunda ke damunta ba. Saima kamo hannun Laylerh’n da tayi ta mik’ar da ita tsaye. Kallon Laylerh’n tayi sosae kafun tad’anyi k’asa da muryarta, cikin siga da kuma salon tsokana irin nata tace. “Tun d’azu Aunty Zee tazo d’aukanki, gashi kuma yau dai munyi final exam saboda haka sai munzo bikin L&M I mean LaylerhMaleek kenan.â€? Teemah’n takai k’arshen maganan nata tana d’an kashewa Laylerh’n idanu. Wanda hakan yasa Laylerh’n zuba mata idanunta dake bayyanar da abubuwa kala. Teemah kuwa sam bata damu da shirun da Laylerh’n ba, because hakan Bawae bak’on abu bane awajenta, itama bata sake cewa komae ba taja hannun Laylerh’n suka tafi. Direct wajen da motar Aunty Zee ke fake suka nufa. Koda suka k’arasa Aunty Zee d’in murmushi tayi, tare da tambayan Laylerh’n ya jarrabawa. Da “Alhamdulillah!â€? kawae ta amsa daga haka ta bud’e murfin motar ta shiga, bayan sunyi sallama da Teemah akan cewar next week zata zo gidan Aunty Zee d’in. Still yauma kuma saida Teemah’n taga fitansu acikin school d’in kafun ta koma wajen sauran students din makarantar suka ci gaba da celebration. Acan gidansu Laylerh’n kuwa Abbou Jaheed da kuma Abbou Khareem ne ke zaune akan d’aya daga cikin had’addun royal chairs d’in dake cikin falon, idanu suka zubawa Oum Ayush dake zaune. Wanda da dukkan alama kallo d’aya zakayi mata kafahimci cewa akwae magana abakinta. Duk da cewar hakanne kuma amma yanzu tsawon 10mn kenan da zamansu awajen takasa cewa komae. Abbou Khareem wanda ya gaji da zamanne ya sake d’ago kae ya kalleta, cikin kuma yanayin k’osawa yace. “Ayush kince akwae muhimmiyar maganan da zaki fad’a mana amma kuma naga kinyi shiru, kodai wani abu ya faru ne?, ki fad’i koma meyene duk ke muke saurare.â€? Ahankali Oum Ayush ta d’an sunkuyar da kanta, Tabbas duk da cewa batasan a yanda zasu fahimci maganar nata ba, ya zama tilas ta fad’a musu, domin kuwa ita tasan tayi nakanne Bawae da mummunan manufa ba, Idanunta ta d’an lumshe tare da tausasa murya, cikin kuma son bayyanar da gaskiyar abunda ke cikin ranta tace “Kuyi hak’uri domin akwae abunda na b’oye ban sanar muku ba, ban kuma yi hakan da wata manufa ba, saidan duba cancanta da kuma dacewar hakan, hakika duk da cewar bani ce na haifi Laylerh ba amma har acikin zuciyata, inajin soyayyarta kamar y’ar ciki na, kasancewar ta yarinya k’arama kuma yasa dole tana da buk’atar samun nutsuwa, musamman idan muka duba irin k’addarar daya sameta ayanzu, akwae buk’atar musa ma mata Hutu, da kuma yin abun da zai sanyaya zuciyarta, aciki kuwa harda nesan ta ta da gidan nan, domin kuwa matuk’ar tana zaune cikin agidannan dole ne rayuwar da tayi da Najeeb zai dinga dawo mata, hakan kuwa zai iya shafar karatun ta.â€? D’an tsagaitawa da maganan nata tayi, wanda hakan yasa Abbou Khareem cewa. “Har yanzu dae baki fad’i abunda kikeson fad’ad’in ba, sannan kuma mu sam bamu fahimce ki ba, ba mu kuma gane abunda kike nufi ba.â€? Jin abunda Abbou Khareem d’in ya fad’ane, yasa ta sauk’e ajiyar zuciya, cikin kuma confidence d’in abunda ke cikin zuciyarta tace. “Abunda nake nufi shine kwata kwata Laylerh bata da Iddah akanta, saboda wata mu’amala ta aure bata tab’a shiga tsakaninta da Najeeb ba, ma’ana Najeeb bai tab’a kusantarta ba, saboda haka babu Iddah akanta, nasan hakanne kuma aranar da Najeeb d’in ya sake ta, koda na tambayi Najeeb d’in kuwa shima ya tabbatar min da hakan, saboda haka Laylerh bazatayi Iddah ba, na b’oye muku maganar ne kuma saboda, sai ta dalilin yin iddah’n ne kad’ae zata nesanta da gidannan, wanda hakan zae sa tayi karatun exam d’inta anutse, gashi kuma Alhamdulillah yau sun kammala exam d’in, dan haka ko ayau kuka buk’aci dawowanta gidannan zata dawo batare da wani miki ko ciwo acikin zuciyarta ba, sannan kuma Ko agobe za’a iya d’aura mata wani sabon AURE.â€? Wani irin nannauyan ajiyar zuciya gaba d’aya su Abbou Jaheed d’in suka sauk’e, asakamakon jin maganganun da Oum Ayush d’in ta fad’a musu, Yayinda fuskonkinsu kuwa suka cika da tarin mamaki da kuma al’ajabin faruwar hakan, domin acikinsu babu wanda ya tab’a kawo tunanin cewar wai Najeeb bai tab’a kusantar Laylerh ba. *(Sorry page din yau ba yawa, just na samu time ne kawae nace bari na yi)* *19/3/2021* *7:43pm* 3/22/21, 7:59 AM - Ummi Tandama: *LAYLERHMALEEK* *(Page d’in yau dai sai kun had’a da hakuri gaba daya ina busy ban zauna na nutsu ba)* *Chapter 70* Gyara zama Abbou Jaheed yayi tare kuma da sake sauk’e wata sabuwar ajiyar zuciya, Tabbas maganganun da Oum Ayush d’in ta fad’a sun matuk’ar shiga jikinsu, kana kuma sun sauya tunaninsu. Domin kuwa abune da dukkansu basu tsammata ba. Saidai kuma sam basuga laifin Oum Ayush akan b’oye musu gaskiyar al’amarin da tayi ba, saboda koba komai hakan da tayi d’in ya bawa Laylerh’n daman yin karatunta cikin nutsuwa. Still ajiyar zuciya Abbou Jaheed d’in yayi, cikin kuma nuna cewar ya fahimci abunda Oum Ayush d’in ta aikata yace. “Tabbas nafahimceki Ayush, na kuma san bazaki tab’ayin wani abu da zai cutar da rayuwar Laylerh ba, na kuma ji dad’in hakan k’warae, domin kuwa koba komae Laylerh zata samu nutsuwa acan gidan, saidai kuma aanzu duk wani abunda ya faru ya riga daya wuce, ko akwai Iddah akan Laylerh ko babu, yanzu babban abunda ya kamata mu fara fuskanta shine rayuwar da Laylerh’n zatayi anan gaba, duk da kuwa munsan cewa Allah Ne ke tsarawa bawansa komai da komai na rayuwa, amma ya kamata ace muma munyiwa rayuwar da zata fuskanta ayanzu kyakkyawan tanadi, domin so nakeyi kulawar da zata samu ayanzu daga garemu ya zarce na ko yaushe, ko badan maraicinta ba, Kodan saboda k’addarar da ta fuskanta da kuma tsananin biyayyarta.â€? D’an tsagaitawa da maganan nasa yayi, tare kuma da numfasawa. Kana yaci gaba da cewa. “Tun bayan mutuwar aurenta, na tsara cewar baza mu sake d’auko mata maganar aure da wuri ba, har sai bayan ta kammala karatun degree d’inta, domin result d’inta na fitowa zan turata karatu k’asar syprus, acan nakeso tayi degree d’inta, zuwa lokacin da zata kammala kuma nasan tasan duk wani abu daya shafi rayuwar duniya, da ma sanin ciwon kai, sab’anin yanzu da ba komai ne ta gama sani ba, saidai kuma kafun na aikata hakan dole Ina buk’atar amincewar ku, domin kasancewarta agabana, Bawae yana nufin cewa ni kad’ai nake iko da ita ba, kuma d’iyarku ce kuna da iko da ita.â€? Gaba d’aya falon shiru ya d’auka saboda jin abunda Abbou Jaheed d’in ya fad’a, Lallai tabbas tanadin da yayiwa Laylerh’n me kyaune, dukkaninsu kuma zasu yi fatan ace hakan ya kasance. Saidai kuma banda zuciyar Oum Ayush da take sak’a mata wani abu na daban, saboda sam gangar jikinta bai bata cewar abunda Abbou Jaheed d’in keso zai yiwu ba. Saidai kuma gudun kada wani abu ya sake faruwa da rayuwar Laylerh’n kamar yanda ya faru abayane yasa ta d’an gyara zamanta, tare da d’ago kai ta fuskanci Abbou Jaheed d’in, cikin yanayin kuma da tasan zai fahimceta tace. “Tabbas fatan da ka yiwa Laylerh maikyau ne, kuma dukan mu zamu so ace hakan ya kasance, saidai kuma akan komai daya shafi rayuwarta dole muna buk’atar jin ta bakinta, domin ba Lallai abunda muka zab’a mata ya zama shine zab’inta ba, watak’ila tana da wani hope d’inta na daban, saidai kuma kasancewarta yarinya mai biyayya hakan yasa kome muka zo mata dashi bazata k’i amincewa ba, koda kuwa tana da nata ra’ayin.â€? D’an tsagaitawa da maganan nata tayi, tare kuma da sake duban su Abbou Jaheed d’in. Murya atausashe kana kuma cike da tausayi tace. “Dan Allah awannan karon mubar Laylerh ta zab’i abunda takeso, mubari muji zab’inta daga bakinta, domin zai iya kasancewa bayan karatu akwai wani abu da takeso, wanda kuma take mafarkin cimmasa, saboda haka mu b’ata zab’i akan rayuwarta tanan gaba!!â€? Yanayin yanda ta k’are maganar nata murya asanyaye ne yasa, duk su Abbou Jaheed suka sauk’e ajiyar zuciya. Cikin yanayin gamsuwa da kalaman Oum Ayush d’in kuwa Abbou Jaheed, yace. “Insha Allah zamuyi hakan, saidai kuma ayau inason Laylerh’n ta dawo, domin dama Iddah ne ya kaita to yanzu kuma babu shi, sannan sun kammala jarrabawar tasu, saboda haka Oum Ayush kije ki d’aukota ta dawo, ban kuma yarda asauk’eta akowanni sashi ba sai naku.â€? Kai Oum Ayush da Abbou Khareem suka jinjina cike da gamsuwa, Yayinda Oum Ayush kuwa taji wani irin sanyi na ratsa zuciyarta, domin kuwa duk da batasan wani abune zai biyo baya ba, tanasa rai da kuma fatan cewa Alkhairi ne Insha Allah. Mik’ewa tsaye tayi cikin kuma yanayin sakin fuska ta juya ta fice daga cikin falon. Nan tabar su Abbou Khareem na tattaunawa, ita kuwa kaitsaye sashinta ta wuce tare da soma kimtsa kanta, saboda sam batason b’ata lokaci awajen d’auko Laylerh’n. Acan gidan Aunty Zee kuwa, tunda suka dawo daga makaranta. Laylerh ta shiga d’aki ta kwanta, wani irin yanayi takejin kanta aciki na musamman, tun kuma k’iran wayarta da akayi takejin hakan, Yayinda kuma takejin wani sashi na zuciyarta yayi mata nauyi. Lumsassun idanunta dake bayyana gaskiyar abunda ke cikin zuciyarta ta bud’e ahankali, tare dasa hannunta ta d’auko wayarta dake ajiye asaman bedside drawer, touching screen d’in wayar nata tayi, Kamar kuma yanda ta saba, always shine a mind d’inta, kome takeyi tunaninsa baya iya barin cikin zuciyarta, hotonsa guda d’aya rak dake cikin wayar ta zubawa ido bata ko k’yaftawa. Hak’ik’a zata iya rantsuwa cewar bata tab’a ganin wani me kya’un Yah Maleek d’innata ba, komai nasa dabanne, more expecially beautiful eyes d’insa da basu cika girma ba, har sai idan shi d’inne ya waresu, ba komae ke d’aukan hankali atattare dasu ba kuwa face yanayin tsarin cikinsu, dake d’auke da black brown eye balls, sai kuma zara zaran lashes masu matuk’ar kyau da burgewa. Ahankali ta shiga yawo da idanunta akan hoton nasa, har dai ta kuma sauk’e ganinta akan lallausan sajen dake kwance akan fuskarsa, wanda ya zauna sosai, ya kuma k’arawa fuskartasa kyau, Tabbas ko bashi da kyau, tayi imani cewa da wannan beard d’innasa kad’ai zai iya narkar da zuciya. Asanyaye wani irin tattausan murmushi ya Bayyana akan fuskarta, murmushin da ita kanta batasan tayi sa ba, saidai kuma abu d’aya kawai ta yarda dashi, wanda akansa ko tantama baza tayi ba, shine shape d’in jajayen lips d’insa da nata iri d’aya ne, domin kuwa kamar yanda labb’an bakinta suke jajaye, haka shima nasa suke. Still wani murmushin ta sakeyi, saidai kuma awannan karon harta hak’waranta saida suka bayyana. Daidai lokacin kuwa Aleeya da tun d’azu ke tsaye abakin k’ofar shigowa d’akin tace. “Har abada Laylerh, banajin akwai watarana da zata zo da zaisa, ki gaji da kallon hoton wannan balaraben yayan naki.â€? Sauk’ar muryar Aleeya acikin kunnuwanta kuwa, shiya saka tayi saurin kifa wayar ta ta, tare da tashi zaune, anutse cikin kuma son kawae da maganan Aleeya’n ta soma gyara wuyar rigar dake jikinta. Aleeya kuwa murmushi tayi, batare kuma da ta k’arasa shigowa cikin d’akin ba tace. “Oum Ayush tazo.â€? Da sauri ta d’ago kai ta kalli Aleeya’n, cikin yanayin mamaki da kuma jin dad’i tace. “Dagaske kike? Please Aleeya banason wasa.â€? Ayanzu kam Aleeya dariya tayi, saidai kuma kafun ma ta bawa Laylerh’n amsa, tuni harta Sauk’o daga kan gadon, cikin hanzari ta rab’a ta bayan Aleeya’n ta wuce. Agarin sauri kuwa har k’afarta na hard’ewa, haka ta k’araso cikin falon, ganin kuma Oum Ayush d’ince da gaske, yasa fari’ar fuskarta fad’ad’a ashagwab’e taje ta fad’a jikinta. Oum Ayush kuwa murmushin jin dad’i tayi tare da sake rungume Laylerh’n, cike da kulawa tace. “Nayi kewarki sosai Laylerh, ya exam d’in fatan kun gama lafiya.â€? Kai Laylerh’n ta jinjina mata, cikin kuma yanayinta na shagwab’a tace. “Alhamdulillah exam yayi dad’i, nima nayi kewarku sosai Ina Abbou Khareem dina!â€? Again murmushi Oum Ayush tayi, tare da cewa. “Duk suna lafiya, sune ma suka aikoni natafi dake, sunce hutunnaki ya isa haka, zaki bini mutafi ko?â€? Kanta ta jinjina alaman “Eh.â€? Domin Allah Yasani tayi matuk’ar kewar gidannasu, musamman Yah M.Jay d’inta, saboda har yanzu batasan cewar yayi tafiya zuwa USA ba. K’arasowar Aunty Zee cikin falonne kuma yasa, hirar Laylerh da Oum Ayush d’in katsewa. Bayan kuma Oum Ayush din Tasha drinks din dake gabanta ne ta shiga korawa Aunty Zee duk abunda ke faruwa, da kuma maganar tafiya da Laylerh da tazo yi. Hakika Aunty Zee din taji babu dadi, domin abune da tasani cewar zatayi kewar Laylerh’n, amma kuma to ya ta iya. Aleeya takira tare da bata umarnin taya Laylerh’n kimtsa kayanta, koda Aleeya taji cewa Laylerh’n tafiya zatayi, bataji dadi ba sam, musamman ayanzu da take matuk’ar jin dad’in zama da Laylerh’n, akwai sabo me kyau sosae atsakaninsu. Haka dai ta taya Laylerh’n duk suka had’e kayanta waje d’aya. Koda suka tashi tafiya kuwa har bakin mota Aunty Zee da Aleeya suka rakasu, Yayinda Aunty Zee d’in tabawa Laylerh kyautuka masu yawa. Aleeya kuwa cewa tayi â€? Insha Allah Zatana kawowa Laylerh’n ziyara.â€? Da haka dai suka rabu cike da kewar juna. Ko acikin Mota kuwa gaba d’aya Laylerh farincikinta ya kasa b’oyuwa, burinta ayanzu kuwa bai wuce taga Yah M.Jay d’innata ba, saboda wani irin kewarsa takeji. Oum Ayush dake driving ita kanta ta lura da hakan saidai batace komai ba. Ahaka har suka iso bakin makeken estate d’innasu. Horn d’aya kawae maigadi ya wangale musu makeken gate d’in, Oum Ayush kuwa cike da k’warewa ta tura hancin motar nata ciki. Kamar dai yanda ta saba ababban parking space d’in dake cikin gidan ta faka motar nata, bayan kuma ta gama daidaita parking d’in, Kusan atare suka fito daga cikin motar. D’aya daga cikin ma’aikatan da suke bawa flowers ruwa ne yazo ya d’auki jakar Laylerh’n, tare da nufar cikin gidan da shi. Itakuwa Laylerh bayan Oum Ayush tabi, saidai kuma bai wuce taku hud’u tayi ba, ahankali ta juyar da kanta, tare da sauk’e idanunta akan part d’in da ada yakasance nasu ita da Najeeb. Wani irin abu mai kama da fad’uwar gaba da taji ya daki zuciyarta ne, yasa tayi saurin janye idanunta had’e da sunkuyar da kanta k’asa. Daidai lokacin kuwa suka iso sashin Oum Ayush d’in. Suna shiga ciki kuwa Oum Ayush tace mata. “taje tayi wanka, sannan kuma idan ta fito daga wankan taje Abbou Jaheed na k’iranta.â€? Da “to.â€? Kawae ta amsa, tare dajan trolleybag dinta kaitsaye ta wuce d’aya daga cikin 3bedrooms d’in dake cikin falon Oum Ayush d’in. Tana shiga cikin d’akin kuwa ta soma rage kayan dake jikinta, tare da d’aukan wani towel marar nauyi ta d’aura ajikinta. Cikin yanayin da takeyin komanta na nutsuwa, ta wuce toilet. Wanka tayi sannan ta d’auro alwalan sallan la’asar. Koda ta fito awankan, zip d’in trolleybag d’inta ta zuge, tare da zaro wata doguwar riga mai yanayin Kimono ta sanya ajikinta. Zama tayi akan gado tare da d’auko wayarta, saidai kuma tunawa da tayi cewar Abbou Jaheed na k’iranta ne yasa tayi saurin mik’ewa tsaye. Rubber hijab da kuma slipper mai kalan rigarta tasa, ahanzarce ta nufi sashin Abbou Jaheed d’in. Saidai kuma tun fitowarta compound d’in gidan, ta ajiye idanunta akan sashin Maleek d’in, wanda aduk cikin gidan shine tsarinsa ya fita daban, had’uwarsa na musamman ne. Bata kuma d’auke idanunta akan part d’in nasa ba kuwa, har saida taga ta iso, sashin Abbou Jaheed. Ahankali Ta tura k’ofar falon ta shiga bakinta d’auke da sallama. Abbou Jaheed dake zaune akan lallausan Turkish sofa, yana me shan fruit salad ne ya amsa mata, fuskarsa d’auke da murmushi’n Jin dad’in ganinta. Ita d’inma murmushine kwance akan fuskarta, cikin kuma yanayi na d’an hanzari ta k’arasa shigowa cikin falon, anan gefen Abbou Jaheed d’in ta zauna, tare da gaishe sa. Fuska asake ya amsa mata, tare da tambayarta Exam. Da “Alhamdulillah!!â€? Kawae ta amsa masa. Shikuwa Abbou Jaheed ganin murmushi kwance akan fuskartane yasashi sake Jin wani irin dad’i acikin ransa, saboda yana matuk’ar son ganinta acikin farinciki. Glass bowl na fruit salad d’in dake gabansa ya turo mata, tare dayi mata alama akan tasha. Sam musu ba al’adarta bane, shiyasa bata iya ce masa a’a ba, duk da kuwa cewar bata jin yunwa amma haka ta daure tayi 3spoons na fruitsalad d’in. Abbou Jaheed kuwa gyara zamansa yayi, tare da tank’washe k’afafunsa, saboda maganar da yakeso suyi yau d’in ta banbanta dana kullum. “Laylerh!!â€? Ya k’ira sunanta cikin sanyi da kuma tausasa murya. Amon muryarsa da taji ne kuma yasa ta d’ago kanta ahankali ta kalleshi. Lokaci d’aya kuma taji zuciyarta tayi rauni sosai, wanda kuma har saida hakan ya kasa b’uya. Abbou Jaheed kuwa ayau so yakeyi yayiwa Laylerh’n magana, bawai amatsayin y’ar k’aninsa ba kawai, so yake yayi mata magana amatsayin y’ar daya haifa ta cikinsa. Saboda hakane ma ya d’anyi gyaran murya, cikin kuma yanayin da yasan cewa zata fahimce sa yace. “Ayau zan miki magana amatsayina na Uba mahaifi, bawai mai rik’onki kawai ba, Ina kuma fatan zaki fahimce ni, Kamar dai yanda yake a addinance idan aka saki mace yin Iddah ya hau kanta, har saidai idan yakasance Mijin daya aureta bai tab’a kusantarta ba, To fa wannannne Iddah bai hau kanta ba, Kamar dai ke, duk da cewar ada munyi tunanin cewa akwai Iddah akanki, saida Oum Ayush ta fayyace mana komai kafun muka fahimci cewar Iddah bai hau kanki ba, Tabbas ako da yaushe Allah Yakan jarrabtar bawa da k’addarori kala kala, wasu masu wuyar d’auka da kuma jurewa, saidai kuma hakan bawai yana nufin cewa Allah Ba yason bawannasa bane, bansan me yasa k’addara ke wasa da rayuwarku ba Laylerh, amma inaji ajikina cewar Insha Allah Watarana zaku samu farinciki....â€? D’an tsagaitawa da maganan nasa yayi, tare da sakin wata irin nannuayar ajiyar zuciya, wanda hakan ya faru ne kuma saboda tuna d’ansa Maleek da yayi. K’warae yana matuk’ar jin tausayin Maleek d’in wanda tun tasowarsa ba abunda ya sani sai dai neman cimma muradin rayuwa. Shiru gaba d’aya falon ya d’auka, almost 5mn kafun ya iya tattaro kwarin guiwarsa. Cikin kuma hikima irin tasu ta manya yace. “Ada ina wani tunani akanki na daban, wanda batare dana tambayi shawarki ba har na yanke hukunci, inda na yanke cewar zan turaki syprus kije kiyi karatunki acan, saidai kuma kamar yanda Oum Ayush ta fad’a lallai ne ya kamata aji daga gareki, ya kamata kuma abaki zab’i, wannan rayuwarki ce Laylerh, ayau akuma karon farko na baki zab’i, domin y’ancin kine, duk da bansaniba ko akwai wanda zuciyarki keso, saboda haka zab’i biyu kike dashi ayanzu, ko tafiyarki k’asar Syprus ko kuma baki daman sake kawo wani Mijin da zuciyarki keso, matuk’ar kina ga auren shine abu mafi sauki agareki, ba kuma zan tsauwala miki ba agame da hakan!!!â€? Hannunta tasa ahankali ta share gumin daya keto mata, lokaci d’aya kuma taji zuciyarta na wani irin bugawa tamkar zata faso k’irjinta ta fito. Tabbas ita kanta batasan cewar tana da wannan raunin ba sai ayau. Idanununta da suka ciko da k’walla ta rumtse, tare da soma murza y’an y’atsun hannunta. Shin tayaya zata iya zab’an wata rayuwa? Tayaya ma zata so nesanta kanta? Ko kad’an batajin zata iya, domin aikata hakan tamkar cutar da kanta ne, yaya zatayi da Rauninsa dake damu da kuma sake cika zuciyarta akullum? Wace macece zata karb’esa saboda Allah? Koda sau d’aya tana son ganinta atare dashi. Tabbas ayau zata fad’i duk wani abunda ke cikin zuciyarta, duk da kasancewar maganganun nata suna da nauyi sosai, amma Lallai ayau bazata iya dakatar da zuciyarta da akullum taje azabtuwa ba. Zafafan hawayene suka sauk’a akan fuskarta, cikin kuma muryarta dake matsanancin rawa tace..... “Yah Maleek Idan natafi wazai kula dashi? Kullum bayacin abinci, sannan koda yaushe haka yake tafiyar da rayuwarsa, babu farinciki acikinta, nakuma yi imani cewa har I yanzu baya cikin farinciki, saboda acikin zuciyata nakejin duk wani ciwo da kuma damuwarsa, waye zai basa farinciki? Koda sau daya ne kawai Abbou Jaheed inason ganin Yah M.Jay acikin farinciki, saboda haka na zab’i zama dashi fiye da kowa da komai, na sadaukar da duk wani farinciki na agaresa, bandamu Akan kowacce irin lalurarsa ba, abunda dai kawai nasani shine zan zauna dashi ahaka, zan rayu dashi, zan kuma jure duk wata damuwarsa, sannan kuma nayi imani cewa kowacce irin K’addara mai kyau ko akasinta Allah Shiya tsara mana!!!â€? *21/3/2021* 3/23/21, 9:14 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna *Not editing* *Chapter 71* Idanu Abbou Jaheed ya zuba mata, Yayinda fuskarsa ke bayyana zalla da kuma tarin mamakin daya samu kansa aciki, sam koda wasa bai tab’a tunanin cewa akwai watarana da Laylerh’n zata zo gareshi da irin wannan maganan ba. Wani irin raunin kuma daya lullub’e zuciyarsa ne yasa, take hawaye suka cika idanunsa. Sam kwata kwata ma bayajin hakan zaiyiwu, tayaya zai d’auki Laylerh ya bawa Maleek dake d’auke da lalura? tayaya zai jefa rayuwar yarinya marainiya acikin k’addarar d’ansa? Kansa ya d’an soma girgizawa, tare kuma da danne abunda ke cinsa acikin zuciyarsa, cikin wata irin muryar da takasa b’oye rauninsa yace. “Hakan bazai yiwu ba Laylerh, abunda kike fad’a ayanzu wani abune da yake karkatacce, na kuma san ba komaine ke d’ibanki ba, illa k’uruciya da kuma raunin zuciya, tayaya kike son sa kanki acikin k’addarar Maleek? k’addarar da ta zame masa tamkar tabo acikin rayuwarsa, tayaya kike son tursasa zuciyarki akan auren Namijin da likitoti suka tabbatar da cewar bazai haihu ba, meyasa Laylerh? Meyasa kikeson kasancewa ahaka? Meyasa kikeson takurawa rayuwarki? Kada kice zaki rungumi k’addarar da bata zamo dolenki ba, domin kuwa ko ba komai ke MACE ce, dole kina da hope anan gaba, saboda haka zaifi kyau kitsarawa kanki rayuwar da zata zama cikinta akwai d’orewar farinciki...â€? “Babu wani farinciki aduk wata rayuwar da babu sadaukarwa, sannan babu ingantacciyar farinciki ga wanda yasan kansa, matuk’ar har kullum zaiga d’an uwansa acikin damuwa, sai yaushe ne wanda yake cikin k’unci zaibar k’unci? Sai yaushe ne K’addarar sa zata yaye? Yaushe zai samu farinciki kamar yanda mafi yawan cin mutane ke samu? Wacece zata zauna dashi, ta sakashi murmushi, sannan kuma ta cire masa k’uncinsa? Wacece zata zauna dashi batare da ta cutar dashi ba? Saboda k’addarar da ta samesa kawai nefa, yasa aka janye maganar aurensa, bayan kuma kowa yasan cewa ba akansa aka fara halittar wannan k’addarar ba, sam banaso Abbou Jaheed, banason watarana Yah M.Jay yaji ajikinsa cewar shid’in mai yankakken farinciki ne, ba kuma nason ya fara Jin cewar shi mai nakasa ne, bana fatan wannan ranan, ranan da zaiji tamkar bashi da kowa, Tabbas bana fatan zuwanta, akullum akuma koda yaushe zanso ganin k’arfafawarsa, babu wanda yasan me yakeji, akoda yaushe shi kad’ai yake shanye duk wata damuwarsa, koda kuwa damuwar tasa takai girman da zata iya tar watsa zuciya!!!â€? Idanunta dake tsiyayar da hawaye ta bud’e, wanda suka rikid’e suka zama jajur. Gaba d’aya jikinta kuwa b’ari yake, wanda kuma hakan yasamo asaline saboda yanda wani irin azababben kuka me sauti keson k’wace mata. A karon farko na gaba d’aya rayuwarta, da taji bazata tab’a iya b’oye abunda ke cikin zuciyarta ba, hasalima ganin Abbou Jaheed d’in take tamkar mahaifinta Abbou Mahmoud ne zaune agabanta. Ahankali ta d’an matso kusa da Abbou Jaheed d’in, hannayensa duka biyu ta rik’o, cikin wani irin matsanancin kukan daya k’wace mata ta shiga girgiza masa kai, murya Amatuk’ar raunane tace. “Dan Allah Abbou! Zan rayu dashi dakowacce irin k’addara koda kuwa tafi wanda ta sameshi ayanzu muni, zan zauna dashi koda ace shid’in Majanuni ne, lokuta da yawa danshi kawai nakeyin rayuwa, tun Ina k’arama shine yake kokarin zame min Garkuwa, ga kowanni d’an Adam jinin mahaifansa ne ke gudana acikin jikinsa, amma ni acikin jikina jinin Yah Maleek ne, shine komai nawa, shine wanda bayason yaga nayi kuka, shine kuma mutum na farko da yake fara bani abinci akowacce rana, shine wanda yake sanin kowacce irin damuwa ta, ba kuma zan tab’a mantawa da hakan ba har abada, domin abayan kowani bugun zuciya da numfashinsa al’amura nane, shine wanda ya fara koyamin yanda zanyi rayuwa, komai nasani aduniyar nan ta dalilinsa ne, tun Ina da shekaru 2 har izuwa 12 shi kawai nasani acikin rayuwata, har iyanzu ma shid’in kawai nasani....â€? Wani irin kuka maitsanin sauti daya ci k’arfinta ne kuma yasa ta kasa k’arasa maganganun nata, kanta ta kifa da jikin kujera ta shiga rera wani irin kukan, dake bayyana gaskiyar abunda ke cikin zuciyarta. Sannan kuma kukane dake nuna tsananin Rauninta akan Maleek, kukan da yayi matuk’ar tab’a zuciyar Abbou Jaheed. Wanda har saida yayi sanadiyar hawayen dake kwance acikin idanunsa, suka gangaro kan fuskarsa. Domin shikansa yayi imani acikin kalaman da Laylerh’n ta fad’a sam babu k’arya, ko waye zai sota bayan soyayyar da Maleek ya nuna mata ne, kasancewar abune da ke abayyane, duk wani wanda yasan su acan baya, to tabbas zai shaida cewar Maleek yamafi son Laylerh’n akan kansa. Lallai ayau ya yarda cewa su duka biyun suna rayuwa ne akan abunda ko wannensu yake so, Muradi fata da kuma burinsu duk iri d’ayane, Laylerh ce fatan Maleek haka ma, Laylerh’n Maleek ne fatan ta. Kuma Tabbas ita kad’aice macen da zata iya zama da Maleek d’in koda kuwa munin k’addararsa ta zarce misali, hak’ik’a ayanzu kam bashi da bakin dakatar da faruwar komai, domin ya riga ya fahimci abunda Allah Yayi ikonsa akai babu wanda ya isa hanawa. Duk da cewar kuwa Auren Maleek d’in zai zama tamkar k’alubale ne agareta, Duk da cewar kuma ba shine mahaifinta ba, amma bazae tab’a so ace ta auri wani Namiji mai tawaya kamar Maleek d’in ba, zai so ace ta gina rayuwarta akan dogon tsauni ta yanda zata cimmawa nasarori da yawa. Amma kuma k’addara ta riga fata, k’addarar soyayyar dake tsakaninta da Maleek, wanda girmanta ya zarce tunanin mai tunani. Asanyaye yasa hannayensa ya share hawayen dake kwance akan fuskarsa, hannun Laylerh’n da har yanzu ke kuka ya kamo, cikin sanyin murya da kuma wata irin sabuwar k’aunarta da yaji ta sake shiga zuciyarsa yace. “Kinason zama da Maleek duk da kinsan lalurar da yake d’auke da ita?.â€? Kanta ta jinjina masa alaman “Eh.â€? Still kuma bata daina kukan da takeyi d’inba. Tsananin tausayin tane ya lullub’e zuciyar Abbou Jaheed, musamman da yayi imani cewa, har abada bazai tab’a samun y’a irin Laylerh’n ba, komai na rayuwarta daban ne, Tabbas yasan cewar koda ace babu soyayya atsakanin LaylerhMaleek d’in, zata iya zama dashi tare da duk irin k’addarar da tazo mai. Idanunsa ya d’an lumshe tare kuma da sauk’e wata sassanyar ajiyar zuciya. Hannunsa yasa ahankali ya shafa kanta, cikin nuna tsananin kulawa agareta yace. “Nagode miki Laylerh, nagode sosai da Allah Ubangiji Yabani ke, Allah Ya miki albarka, domin badan keba nasan abune mai wahala Maleek ya samu macen da zata zauna dashi, saidai kuma har yanzu inaji ajikina faruwar hakan tamkar cutar da kanki ne.â€? Kanta tayi saurin girgizawa, tare da d’an motsa labb’an bakinta da takejin sunyi mata nauyi sosai. Araunace tace. “Babu cuta ko takurawa, Abbou Jaheed Yah M.Jay ne fa!!â€? Takai k’arshen maganar nata cikin wata irin sangartacciyar murya, mai tafiya da sautin sheshshek’an kuka. Idanu Abbou Jaheed ya tsura mata, Yayinda abayyane yake nazartar wani abu adangane da ita. Adaidai lokacin kuwa Abbou Khareem da kuma Oum Ayush, wanda suke tsaye abakin k’ofar shigowa falon, almost 15mn ago suka kalli juna, gaba d’ayansu hawaye ne kwance acikin idanunsu, kasancewar sunji duk abunda Abbou Jaheed da kuma Laylerh’n suka tattauna. Cikin jin dad’i da kuma k’arfafa guiwa suka k’arasa shigowa cikin falon. Akusa da Abbou Jaheed Abbou Khareem ya zauna, Yayinda Oum Ayush kuwa ta kamo hannun Laylerh dake ta sakin sheshshek’an kuka, cikin kulawa tare da kuma son dakatar da kukan Laylerh’n tace. “Kukan ya isa haka muje kici abinci.â€? Kasancewar gaba d’aya jikinta asanyaye yake ne kuma, yasa bata musawa Oum Ayush d’in ba suka fice daga cikin falon. Abbou Jaheed kuwa fuskantar Abbou Khareem yayi, cikin yanayin fahimtar juna suka shiga tattaunawa akan sabuwar magana da kuma al’amarin daya fuskantosu batare da sun shiryawa hakan ba. Abbou Khareem ne ya gyara zamansa, tare da duban yayannasa fuska asake, cikin kuma son bawa d’an uwannasa k’warin guiwa yace. “Naji duk abunda kuka tattauna da Laylerh, na kuma fahimci komai, saidai inaso ka goge kallon cutarwa da kakewa abun, domin Laylerh da Maleek abu d’aya ne, mun riga da munsan hakan tuntuni, kowanne yana rayuwa da soyayyar d’an uwansa acikin zuciyarsa, kaima kuma shaidane akan hakan, ko azaman da yayi a hospital ka shaida Son da yake mata, wallahi matuk’ar muka sakeyin wani ganganci zamu iya rasa su gaba d’aya, domin bawai yanzu ne suka fara son juna ba, kowannensu an haliccesa ne da soyayyar d’an uwansa acikin jini da tsokarsa, saboda haka amatsayina na Yayan Mahaifin Laylerh, na bawa Maleek auren ta, batare kuma da kokonto ko wani shakka ba, mun kuma amince da lalurar da ta sa mesa, domin munyi Imani cewa k’addarace dake iya sauk’a akan kowa, saboda haka afara shirye shiryen yin aurensu Insha Allah Next Saturday za’a d’aura musu aure.â€? Ajiyar zuciya mai k’arfi Abbou Jaheed ya sauk’e, tare dasa bayan hannunsa ahankali ya goge hawayen da suka cika idanunsa, hawayen dake d’auke da ma’anoni daban daban, saidai kuma abu mafi rinjaye na dalilin hawayennasa shine, matsanancin tausayin LaylerhMaleek d’in daya cika zuciyarsa. Agefe guda kuwa sosai ya gamsu da kalaman Abbou Khareem, Insha Allah Kuma auren Laylerh da Maleek za’ayi shi kamar yanda Abbou Khareem ya tsara. Acan sashin Oum Ayush kuwa, afalo Oum din ta zaunar da Laylerh’n, tare da ajiye mata plate d’in abinci agabanta. Saidai kuma kwata kwata lomanta biyu ta ajiye spoon d’in abincin, hakan ya faru ne kuma saboda wani irin ciwon kai da takeji, ba komae ne ya jawo mata ciwon kan ba kuwa face kukan da tayi. Lura da cewar batajin dad’ine kuma yasa bayan tayi sallan la’asar Oum Ayush ta bata maganin ciwon kai tasha, bayan tasha maganinne kuma ta wuce d’aki ta kwanta, sanin kuma da tayi cewar ba kyau yin bacci bayan Salla’n la’asar ne, yasa ta kunna karatun Al’minshawy, asanyaye ta soma bin karatun. *Washington DC* Sake gyara kwanciyarsa yayi akaro na barkatai, tare kuma da lumshe idanunsa wanda sukayi jajur, sosai yakejin wani irin sauyi ajikinsa, musamman acikin kwana biyun da suka wuce, duk da cewar kuwa yasan yana da k’arfin feeling amma ayanzu abunda yakeji d’in ya soma zarce tunaninsa. Wanda har yakaisa ga fara tunanin iya jurewa abubuwa biyun dake damunsa, wanda asanadinsu yake neman zama zautacce. Hannunsa ya d’aura akan k’irjinsa, daidai saitin zuciyarsa dake wani irin bugawa, sam baisan meyasa ayanzun yake samun kansa da rashin iya b’oye rauninsa ba, abubuwa da yawa suna damunsa, wanda idan ya tuna sai yaji zuciyarsa tayi masa rauni sosai. Again sake gyara kwanciyarsa yayi, wanda hakan kuma ne yasa Fou’ad dake zaune k’ura masa ido, tun d’azu yana ankare da yanayin Maleek d’in, saboda ya fahimci cewa, tunda suka zo USA d’in kwata kwata hankalin Maleek ba ajikinsa yake ba, koda yaushe abu d’aya kawai yakeyi, sam shikam bai tab’a sanin cewa Soyayya nasa hauka ba, sai akan M.Jay. Wayarsa da tayi k’ara ne yasashi janye idanunsa akan Maleek, tare da kai hannunsa ya d’auki wayar, jin kuma da yayi Abbou Jaheed ne akan layi, yasashi daidaita kansa tare da gaishe da Abbou’n. Daga haka kuwa bai sake cewa komae ba, sai shiru da yayi yana me sauraren abunda Abbou Jaheed d’in ke fad’a masa. Wanda ni kaina bansan abunda Abbou’n ya fad’a masa ba. Ak’arshe dai “To.â€? Kawai Fou’ad d’in yace, tare da zame wayar daga kan kunnensa, fuskarsa d’auke da murmushi yasa ke kai dubansa ga Maleek. Dake ta faman juyi akan gado. Wani irin murmushi mai d’auke da ma’anoni daban daban yayi, batare kuma daya cewa M.Jay d’in komai ba ya mik’e tsaye, direct wajen drawer’n dake Cikin d’akin ya nufa, bud’e murfin drawer’n yayi, anutse ya soma tattare duk wani abu na Maleek daya sani, kama daga kan k’ananun kayan amfani harma dasu laptop. Maleek kuwa dake kwance jin motsin Fou’ad d’in yayi yawa ne yasashi bud’e idanunsa ahankali ya tsaida ganinsa akan Fou’ad d’in. Fou’ad dake zuge zip d’in jakan dake hannunsa, shima kallon Maleek d’in yayi, gane nufin kallon tambayan da Maleek d’in keyi masa ne kuma yasashi, gyara tsayuwarsa, cikin yanayin dake nuna alaman maganan da zaiyi d’in serious ne yace. “Gobe da safe zamu bar USA hakan kuma umarnine daga Abbou Jaheed bawai daga ni ba, lallai yace mubar kome mukeyi mu koma Nigeria agobe gobe.â€? Maida idanunsa yayi ya lumshe, batare kuma daya ce k’ala ba, hakanan kuma yaji bazai iya musawa tafiyar tasu ta gobe ba, duk da kuwa basu gama kammala aikin daya kawo su USA d’in ba. Fou’ad kansa yayi mamakin ganin Maleek bai musa akan tafiyar tasu ba, saboda sanin halinsa da yayi na yawan musu da kafiya, idan kuma bai shiryawa abuba to babu wanda ya isa sakashi. Da haka dai ya cigaba da kimtsa duk wasu abubuwansu, shi kuwa Maleek tamkar mai bacci haka yayi, saidai kuma bawai baccin yake ba. *Washe gari.* Tun tashinta daga baccin yau d’in takejin gaba d’aya jikinta amace, ga kuma ciwon kan da tun jiya yake damunta, duk da tasha magani kuwa har yanzu yak’i sauk’a. Wani abun daya bata mamaki kuwa shine, lura da tayi da yanda y’an gidan keta hidima, sam kuma bata kawo aranta cewar wai hidiman aurenta da Maleek ne aka somashi tun yanzu ba, domin bata da labari ma akan antsaida ranar auren. Ko yanzuma fitowarta daga wanka kenan, inda take zaune akan gado, daga ita sai wani mini towel a jikinta. Turo k’ofar d’akin Oum Ayush tayi ta shigo, hannunta d’auke da wani tray, wanda samansa ke d’auke da wasu k’ananan 3cups. Ganin Laylerh’n da tayi zaune abakin gado ne kuma yasa ta, fad’ad’a murmushin dake kan fuskarta, tare kuma da k’arasowa ta zauna a gefen Laylerh’n. “Ina kwana.â€? Laylerh’n ta fad’a asanyaye, kasancewar tun tashinta bata had’u da Oum Ayush d’in ba. “Lafiya kalau ya ciwon kan naki, fatan yayi sauki?â€? Fuskarta tad’an shagwab’e, kana cike da sakalci tace. “Da d’an sauk’i.â€? Murmushi Oum d’in tayi hade da fad’in. “Allah Ya k’ara sauk’i, karb’i wannan kishanye.â€? D’aya daga cikin cups d’in ta mik’o mata, wanda cikinsa ke d’auke da tatacciyar madarar shanu. Idanunta ta d’an zaro waje, Kamar zata ce wani abu kuma sai ta fasa, karb’an cup d’in tayi takai bakinta, kamar yanda Oum Ayush d’in ta buk’ata kuwa saida ta shanye tas, kafun ta ajiye kofin. Again wani cup d’in ta sake mik’o mata, shid’in ma dai wani abu me kamar pure honey ne acikinsa, kasancewar kuma yana da zak’i sosai ne yasa take ta shanyesa. D’ayan cup d’in daya rage kuwa ajiyesa agefen bedside Oum Ayush d’in tayi, tare da ce mata tana shan maganin dake cikin kofin duk bayan 20minutes, saboda yana da k’arfi sosai nema yasa ba’aso ashanyesa nan take. Ita dai To kawai tace, duk da akwai magana abakinta kuwa, kasa furtawa tayi, domin sam ba d’abi’arta bane, yawan tambaye tambaye. Fita kuma da Oum Ayush tayi acikin d’akinne, ya bata daman tashi ta sakawa jikinta riga da sket na wani turkish material mai kyau, wanda suka matuk’ar karb’an jikinta. Wayarta ta d’auka, har takai bakin k’ofar fita daga d’akin kuma sai ta dawo, cup d’in magani mai kaman yoghurt d’in da Oum Ayush ta ajiye mata ta d’auka, atsorace ta d’an lasa, wani irin zaki da kuma gard’in madarar da taji ya maye bakinta ne, yasa ta kafa kai har saida tasha Kusan rabin cup d’in kafun ta ajiye ta fita tana lashe baki. Tana fitowa falon kuwa direct dining area ta nufa, saboda sosai takejin yunwa, harta zubawa kanta abinci sai kuma ga Oum Ayush hannunta d’auke da bowl na yankakkun kayan fruits. Abincin dake gaban Laylerh’n ta d’auke, cikin yanayin lallami da kulawa tace. “Daga yau kayan fruits zaki na sha, madadin wani chips and ketchup da omlet.â€? Takai k’arshen maganan nata tana me ajiye mata bowl d’in fruits d’in agabanta. Domin itakam Allah Yasani ayanzu so take ta gyara Laylerh’n sosai fiye da wanda tayi mata abaya, duk dama tasan still she’s virgin. Laylerh dake jin yunwa kuwa babu musu, ta jawo bowl d’in fruits d’in ta soma sha. Saida tasha fruits d’in sosai kafun taji ta k’oshi. Dawowa cikin falon tayi ta zauna, tare da zubawa TV idanu, Tana kallon series film na Money Heist. (Lacasa De Papel) Yayinda Oum Ayush kuwa ke zaune agefe tana waya, da dukkan alama kuma furnitures takeyin order, domin asaboda bikin, za su sanja gaba d’aya furnitures d’in gidan. *10:00 am daidai jirginsu ya sauk’a acikin garin Abuja Nigeria, tun kafun ya gama sauk’owa daga kan matattakalan jirgin kuwa ya hangi Abbou Khareem yazo d’aukarsu, mamaki ne yad’an kamasa asakamakon ganin Abbou Khareem d’in da yayi, saidai kuma bai nuna ba, haka suka shiga motar Abbou Khareem d’in. Aikuwa mamakinnasa bai kankama ba, saida yaga sun d’auki hanyar d’aya daga cikin gidajensa dake Wuse zone 6. Sosai k’warai yayi mamaki, amma kuma saidai cewa da Abbou Khareem d’in yayi ana gyaran wancan gidan nasu ne, yasa shi katse mamakin nasa. Abbou Khareem na gama daidaita parking, ya bud’e murfin motar ya fito, tare kuma da wuce wa cikin gidan kaitsaye. Saboda dama time to time yakan zuwa gidan yad’an huta. Abbou Khareem kuwa da Fou’ad Koda suka shigo cikin falon, basu iskeshi ba, domin tuni ya shige bedroom d’insa dake cikin gidan danyin wanka. Saboda kafun su iso din Abbou Khareem yasa masu aiki sun tsabtace ko ina na gidan. Food flasks na abinci kala kala Abbou Khareem ya ajiye musu, wanda musamman yasa Oum Ayush ta yisu, duka kuma favorite d’in Maleek d’inne. Saida ya sake jaddadawa Fou’ad maganan kulawa da Maleek d’in kafun ya juya ya tafi. Maleek kuwa koda ya fito awanka wani 3quater jeans and blue shirt ya saka, batare kuma daya tsaya yin wani abuba ya fito zuwa falo. Inda ya samu Fou’ad ya shiga wanka. Zama yayi akan had’add’un cushions d’in dake cikin falon, tare da jawo food flasks d’in ya bubbud’e, duk da cewar baya wani jin yunwa sosai, haka ya d’ebi abincin yaci, domin bama sai an fad’a masa ba yasan cewa Oum Ayush ne tayi girkin. Koda Fou’ad ya fito awanka shima zama yayi yaci abincin sosai. Bayan ya kammala cin abincinne kuma ya soma kokarin Jan Maleek d’in da hira. Saidai shikad’ai yake ta magana, Maleek baya cewa ko k’ala, hasalima lumshe idanunsa yayi tamkar maiyin bacci, shikuwa Fou’ad dama ya saba hakan. Acan gida b’angaren Laylerh kuwa gaba d’aya wunin yau haka tayisa, afalon Oum Ayush tana kallo, saidai idan lokacin sallah yayi takan tashi taje tayi sallah. Akuma yau d’inne takejin labarin tafiyan Maleek da kuma dawowansa, taji hakanne kuma awajen Abbou Khareem da yake sanarwa awaya cewar Captain M.Jay d’in ya dawo. Yayinda agame da harkar shirye shiryen biki kuwa abun keta kankama, arana d’aya kawai har sunci k’arfin shirye shiryen nasu. Bayan kuma anyi sallan magriba ne Abbou Jaheed ya damk’awa Abbou Khareem tsabar kud’i na Two Million amatsayin sadakin Laylerh, wanda ya cire ya biya a aljihunsa, domin dama alk’awari ya d’auka cewar shi zai biyawa Maleek d’in sadakin aure’n Laylerh’n, saboda awannan karon so yake dukansu yayi musu gata sosai, tare kuma da fad’in cewa za’a kawo lefen Amarya ranar d’aurin aure. Abbou Khareem kuwa duk da yasan cewa bayar da kad’an d’in sadaki nada matuk’ar mahimmanci, amma haka ya karb’i two million d’in, saboda abune da yake abayyane cewa, Laylerh Macece mai matuk’ar daraja, sannan kuma har yanzu tana tare da budurcinta, baya ga haka kuma yayi Na’am da kawo lefen ranar d’aurin aure. Acan cikin gida kuwa Laylerh ce zaune akan sallaya, domin idar da sallah’n Magriba d’inta kenan, saidai k’ara da kuma tsuwan da wayanta keyi ne, yasa ta mik’ewa tsaye, tare da k’arasawa inda ta ajiye wayartata. Idanunta da suka sauk’a akan screen d’in wayarne, suka wani irin k’ara girma, take kuma taji zuciyarta ta soma bugawa. Rubutun dake yawo akan screen d’in wayar ta tsurawa ido, cikin kuma wata irin muryarta dake shaking tace. “NAJEEBâ€? *(Hey guys kun shiryawa tomorrow Idan darai da lafiya kuwa?)* *8:20 pm* *23/March/2021* 3/26/21, 8:37 AM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* #WEDDING FATIHA *Chapter 72* *”NAJEEBâ€?* Ta k’ira sunan dake yawo akan screen d’in wayar, cikin zallan yanayi na mamaki, domin ko kusa bata tab’a kawowa aranta cewar k’iran Najeeb d’in zai shigo wayarta adaidai lokacin ba. Tsurawa screen d’in wayar nata idanu tayi, had’e kuma da tsayawa ta kasa picking call d’in, tamkar kuma yanda numfashinta ke fita da sauri sauri haka ma bugun zuciyarta, idanunta ta d’an lumshe ahankali, tare da kai hannunta ta d’auki wayar nata k’irar iPhone11, saidai kuma cikin rashin sa’a tana d’aukar wayar, k’iran Najeeb d’in na katsewa. Ai kuwa katsewar k’iran nasa ne ya bata daman sauk’e wani irin k’akk’arfan ajiyar zuciya, lumsassun idanunta ta bud’e tare dajan jikinta ta zauna akan wani Gothic chair dake kusa da gadon dake cikin d’akin. Kunna hasken screen d’in wayar nata tayi, still kuma sunan Najeeb d’in take kallo, Yayinda a zuciyarta take tunanin sake bin k’iran nasa, saidai kuma idan ta bi k’iran nasa ya d’aga tace masa me? Samma ita batayi tunanin k’iransa ba, tun bayan abunda ya faru atsakaninsu, sai kuma gashi shid’in akaron farko ya k’irata. D’an sake lumshe idanunta tayi alokacin da hoton fuskarsa ya fad’o mata, murmushin daya sabayi akullum ne ya shiga yawo acikin tunaninta, wanda hakan yasa itama batare da tasani ba tad’an saki murmushi, Tabbas batajin soyayyarsa acikin zuciyarta, haka kuma batajin k’iyayyarsa, cause ma bashi da wani aibu ko tawaya da zaisa mace ta k’isa, kawai dai ta tsaida zuciyarta awaje d’aya ne, sannan kuma zuciyartata akan abu d’aya kawai ta ginu, wanda kuma har abada batajin zuciyartata zata tab’a sauyawa daga kan abunda ke rayuwa acikinta. Turo k’ofar d’akin da akayine kuma yasa tayi saurin bud’e idanunta, ganin kuma cewar Oum Ayush ne ta shigo cikin d’akin yasa tayi saurin kawar da tunanin da takeyi. Oum Ayush kuwa cikin kulawa ta dubi Laylerh’n tare da tambayarta ko tayi sallah. Kai Laylerh’n ta jinjina mata alaman “Eh.â€? “Yauwa to taso muje a fara miki wankan Amarya, saboda na kula idan ba mufara yanzu ba, to anan gaba bamu da wani isashshen lokaci.â€? Ta kai k’arshen maganan nata, tana me kamo hannun Laylerh’n. Laylerh kuwa jin abunda Oum Ayush ta fad’ane yasa ta d’an shiga mamaki, cikin kuma son samun gamsuwa tace. “Wankan Amarya kuma Oum Ayush? Meyasa? Ni yanzu ai ba amarya bace.â€? Murmushi Oum Ayush tayi, Kamar kuma zata ce wani abu, sai ta fasa, saboda ba yanzune take son Laylerh’n ta sani ba. Ahaka suka fice daga cikin d’akin, tana me rik’e da hannun Laylerh’n batare kuma da taba ta amsar tambayarta ba. Direct wani keb’abb’en waje dake cikin sashin Oum Ayush d’in suka nufa, inda suka taradda wasu mata biyu na zaune, wanda ga dukkan alama kuma Oum Ayush d’in ce ta gayyatosu. Ita dai Laylerh ido ta zuba musu alokacin da suka sa ta cire kayanta, wani d’an k’aramin towel suka bata ta d’aura, Kamar kuwa yanda suka umarceta akan ta shiga cikin wani abu mai kaman bathtub, haka ta shiga ciki ta kwanta babu musu. Wani irin abu mai Tsananin k’amshi matannan suka shiga shafa mata ajikinta, tare da zuba wani irin ruwa mai kaman madara acikin bathtub d’in, wanda ya zamana yana ratsa ko ina d’inta. Oum Ayush dake tsaye agefe kuwa, murmushi tayi musamman ganin yanda matan biyu ke aikinsu yanda ya dace, ta tabbata cewa awannan karon Maleek zai samu farinciki marar yankewa, domin tayi imani cewar da jikin Laylerh’n kad’ai aka barsa, zai samu gamsuwa hundred percent. Agogon dake daure atsintsiyar hannunta ta kalla, ganin time da tayi ya d’anja ne, yasa ta juyawa ta koma cikin falonta, inda tabar manya mata biyu kuma k’wararrun masu gyaran Amarya’n da ta d’auko, d’aya daga Maiduguri d’aya kuma daga Niger 🇳🇪 na k’ara Murje jikin Laylerh’n, had’e kuma da tsuma mata jikinta da daddad’an k’amshi marar gushewa. *MALEEK* Ahankali ya d’an lumshe idanunsa, wanda suka b’ata tsawon mintuna,ya suna kallon kyawawan taurarin da suka k’awata sararin samaniya, daga gefe guda kuwa wani irin ni’imtaccen iska da sanyi ne ke ratsa kowani silin b’ulin gashin dake jikinsa. Hak’ik’a kewarta yakeji sosai, wanda har hakan yasashi kasa zama acikin falon sa, ya fito wajenne kuma wai ko zai samu nutsuwar zuciya, saidai kuma amma Ina, babu abunda ya sauya, domin kowani bayan second ji yake zuciyarsa na sake azalzala dason ganinta. Wani irin sassanyan numfashi ya fitar, tare dasa hannunsa ahankali ya shafi tattausan sajen dake kwance akan fuskarsa. Tabbas shikam yayarda cewa matsanancin kewarta da yakeyi ne, ke sawa yaji wani irin hot feeling na yawo acikin jikinsa. Pink tongue d’insa ya ciro tare da kama jajayen labb’an bakinsa ya lasa, hakan da yayi d’inne kuma ya tuno masa da moment d’insu time d’in da aka d’aura mata Aure da Najeeb. Wani irin abune yaji ya tokari k’irjinsa, take kuma d’aci ya ziyarci mak’oshinsa sam baisan meyasa ba, akullum idan ya tuna cewar wani ya tab’a mallakan Laylerh’n, ya kanji kamar yayi hauka, domin k’unci da tsananin k’unane ke mamaye zuciyarsa, sosai yakejin ciwo da kuma rad’ad’in abun, wanda har hakan yasa sam sam baya mason tunawa. Idanunsa da suka d’an sanja kala lokaci d’aya ya bud’e, tare kuma da kawar da kansa gefe, haka yakejin tamkar yanzu ne abun ke faruwa, tamkar yau ne aka d’aura auren Laylerh’n da wani daban. K’arfen daya rik’e ya sake tare da d’an soma jan jikinsa dake b’ari baya, wanda tuni gargasan jikinnasa duk sun mimmik’e, abu kamar wasa kuma sai gashi mood d’insa ya sanja lokaci d’aya. Juyawa yayi cikin kunci da tafasar zuciya ya koma cikin falon. Fou’ad dake zaune acikin falon kuwa, ganin Maleek d’in ya shigo afusace ne yasashi saurin maida hankalinsa garesa, bakinsa ya bud’e da niyar yiwa Maleek d’in magana, amma kuma saidai abunda yaga Maleek d’in ya d’auko ne yasa shi jan bakinsa yayi shiru, saima idanu daya tsura masa. Maleek kuwa k’arasowa cikin falon yayi, tare da jawo wani babban table dake tsakiyar falon. Takardar cocaine d’in dake hannunsa ya fasa akan saman table d’in, batare daya jira komai ba kuwa ya kafa kansa akan table d’in ya soma shak’an fowder’n. Sauri sauri haka yake shak’an cocaine d’in, tamkar wani zautacce ko kuma mayunwacin zaki. Fou’ad kuwa dake zaune idanu ya tsurawa Maleek d’in baya ko k’yaftawa, Allah Yasani yana matuk’ar mamakin hali irin na Maleek d’in, wanda kuma har yau ya kasa sanjawa. Kansa ya d’an girgiza cike kuma da takaicin halin da Maleek d’in yasa kansa aciki yace. “Ko yaushe kasani abunda kakeyi bamai kyau bane, tayaya zaka maida cocaine tamkar wani abinci ko abun shanka? Koda yaushe idan ranka ya b’aci sai kata shak’awa kanka masifa, masifar da kasan illanta da kuma cutarwarta, har sai yaushe ne zaka girma Maleek? Sai yaushe zaka daina aikata kuskure akan kuskure? Bakajin maganan kowa, duk abunda zuciya ta fad’a maka shi kawai kake aikatawa, Why Maleek? Why? Ni nasan cewa idan Laylerh tasan kana irin wannan rayuwar bazata tab’a jin dad’i ba, dole ne kuma zatayi kuka, yanzu kafison abunda zai cutar dakai kuma ya cutar da Laylerh kenan? ahaka kuma kullum kake ganin dacewar ku da ita, hmmmm nasani da ace kowa zaisan hakan to da duniya ta gamsu cewar Laylerh da Najeeb ta dace bawai dakai me shan hodar ibilis ba!!!â€? Akaron farko ya d’ago kansa, tun bayan kifa kansa da yayi akan table d’in, idanunsa wanda suka rune sukayi jajur ya zubawa Fou’ad, wani irin kallo yake masa mai alaman magana, da kuma nuna matsanancin b’acin rai, saidai kuma acikin irin yanayin da yake sam bayajin zai iya magana, hakan yasa shi jingina da sofa, tare kuma da maida fitinannun idanunsa ya kulle. Fou’ad kuwa harara ya watsa masa, batare kuma daya sake cewa komai ba, ya tashi gaba d’aya yabar cikin falon. Fitansa daga cikin falonne kuma yasa Maleek d’an zame jikinsa ya kwanta, haka yake jin duniyar na juya masa, sama ya koma k’asa haka k’asa ta koma sama, saidai kuma idan da sabo ya sabawa hakan, domin dama ance sakai yafi bauta ciwo. Yana acikin badmood dinnasa ne kuma nannauyan bacci ya d’aukesa. Acan gidansu Laylerh kuwa Kusan awa guda matannan suka b’ata suna yi mata gyaran jiki, har dai saida tayi laushi kafun suka barta ta sarara, bayan ta koma dakinta ne kuma ta sakeyin sabon wanka tare da d’auro alwala tazo ta gabatar da salla’n Isha. Saboda tsananin gajiyan da yake damunta ne kuma yasa tana kwanciya bacci ya d’auketa, daga gefe guda kuwa kowani kusurwa na jikinta, dadda’an k’amshi yake fitarwa. Washegari Tun k’arfe 7 tatashi, Kamar kuma safiyan jiya yauma da madarar shanu ta karya, bayan kuma ta keb’e Kanta ad’akine ta d’auki sauran ragowan maganin da Oum Ayush ta bata jiya ta shanye, sam tama manta wani k’a’idar shansa da Oum Ayush d’in ta fad’a mata. Bayan tagama shanye maganinne kuma Oum Ayush tazo ta kama hannunta suka wuce wajen masu yi mata gyaran jiki. Yau ma d’indai sosai jikinta yasha gurza, saidai kuma ita kanta idan ta shak’i k’amshin dake fita ajikinta, sai taji wani irin hot feeling ya ratsa ta. Almost 1hour da shan maganin nata ne kuma, taji wani irin ciwon Mara na d’an taso mata, saidai kuma sanin da tayi cewa bawai period d’inta ne zaizo ba, yasa bata wani damu sosai ba. Koda aka gama yi mata gyaran jikin ma d’aki ta koma ta kwanta, saboda ta lura tun safe bak’i ke zuwa cikin gidannasu, gashi sai hidiman canja furnitures da kuma gyare gyara ake tayi agidan,wanda duk ita batasan na meye ne hakan ba. Tana kwanciya kuwa ba jimawa bacci ya d’auketa. Only 20mn kuwa acikin baccin nata taji wani irin azababben ciwo na tashi daga cikin mararta, wanda yayi sanadiyar bud’e idanunta. Ahankali ta tashi zaune tare dasa hannu ta dafe marar nata dake yi mata wani irin ciwon da bata tab’a jin irinsa ba. Santala santalan legs dinta ta zuro k’asa daga kan gadon, tare da yunk’urin mik’ewa tsaye, saidai kuma bata kai ga k’arasa mik’ewa tsayen ba, ta saki wani irin azababben k’ara tare da saurin komawa ta zube akan guiwowinta. Daidai lokacin ne kuma Oum Ayush da Aunty Zee harma da Aleeya suka shigo cikin d’akin. Jin ihunta da sukayi ne kuma yasasu k’arasa shigowa cikin d’akin da sauri. Oum Ayush ne tayi hanzarin rik’ota, hankalinta atashe tace. “Lafiyanki k’alau kuwa Laylerh, me yake damunki?â€? Kanta ta d’an shiga girgizawa, tare kuma da soma yarfa y’an yatsun hannunta, kasancewar zuwa yanzu sosai marar nata ta tsananta ciwo, ko tsayuwa mai kyauma ta kasa yi. “Marana Oum Ayush, marana ciwo yake inajin kaman zai fashe!!â€? Tayi maganan cikin muryar kukan daya k’wace mata, tare kuma da sake ci gaba da yayyarfa yatsunta. “Subahanallah!â€? Dukansu suka had’a baki wajen fad’a, cikin yanayin tausayawa kuma Oum Ayush dake rik’e da ita ta zaunar da ita akan gado, hannunta d’aya tasa ta d’an danna saman marar Laylerh’n, Jin kamar marar ta kunbura ne kuma yasa Oum Ayush saurin d’agowa ta kalli Laylerh’n, fuskarta d’auke da tarin damuwa tace. “Ya ilahi Laylerh me kika sha haka, kodai period time d’inki ne yayi?â€? K’ara volume d’in kukanta tayi, tare kuma da d’an girgiza kanta alaman “A’a ba period d’inta bane.â€? Kwantar da ita Oum Ayush tayi, tare da d’anyin Jim tana me son nazartar yanayin Laylerh’n, aikuwa take wannan maganin ya fad’o mata arai, Da sauri ta kamo hannun Laylerh’n tare da fad’in. “Ina maganin dana baki jiya da safe, wanda nace kina shan kad’an kad’an?.â€? Duk da azababben ciwon dake cinta kuwa, saida taji k’irjinta ya buga alokacin da Oum Ayush ta tambayeta maganin, ad’an tsorace kana kuma da muryar sheshhek’an kuka tace. “Nashanye!.â€? Idanu Oum Ayush ta zazzaro waje cike da tsananin mamaki, da kuma tsoron abunda zai biyo baya. Hankalinta amatuk’ar tashe tace. “Why Laylerh? Why? Meyasa zaki shanye shi duka? Koda na kawo miki saida na fad’a miki yanda zaki na sha, amma saboda shegen son zak’i irin naki, kin shanyesa lokaci d’aya, kin san k’arfinsa kuwa? Meyasa kikayi haka Laylerh? Wallahi ko tantama banayi shiya saka miki wannan azababben ciwon maran da bashi da magani anan kusa.â€? Idanunta dake tsiyayar da hawaye ta rumtse da k’arfi, had’e da sakin wani azababben nishin wahala. Sam kwata kwata ma ita bataji fad’an da Oum Ayush d’in keyi ba, saboda zuwa yanzu ciwon nata k’aruwa yake bayan kowani second. Ganin yanda take ta mik’ewa ne kuma yasa Oum Ayush tashi tsaye, zuciyarta cike da danasanin bawa Laylerh maganin, ta fice daga cikin d’akin. Kaitsaye d’aki ta wuce tare da d’auko wayarta, tayi dialing number’n family Dr d’insu. Bayanin ciwon Laylerh’n ta masa, take kuwa yace gashinan zuwa. Duk da tasan cewar maganin hospital bazaisa Laylerh’n ta daina jin radad’in ciwon ba, koda ma ace ta samu maganin ciwon maran, To fa feeling din da zatakeji bazai tab’a barinta ba dole sai Namiji yayi sex da ita kafun ta samu cikakken relief, Thank God Ma yanzu aurenta da Maleek d’in saura 3days. Ruwa maisanyi Oum Ayush d’in ta kai mata tasha, still har yanzu kuma kukan ciwon marar take. Mintuna 15 kacal tsakani Dr ya k’araso, checking d’inta yayi da kyau, gane kuma da yayi cewar akwai feeling mai k’arfi ajikinta ne yasashi yi mata alluran relief da kuma wanda zai sata bacci, domin yasan yawan feeling ma na d’aya daga cikin best abunda ke jawo ciwon mara. Aikuwa yana yi mata injections bacci ya d’auketa, wasu pain relievers ya bata sannan ya tafi. Ganin ta samu bacci ne kuma yasa su Oum Ayush fita waje suka jawo mata k’ofar. Aranar yau d’in gaba d’aya hidima sosai sukayi, domin ayau ne ma’aikatan OJC Concept suka zo suka sanja musu gaba d’aya furnitures d’in falukan gidan, furnitures masu kyau da tsada aka zuba musu. Acan b’angaren Laylerh kuwa tunda Dr yayi mata injections, bacci take bata farka ba, har saida aka yi sallan Isha. Koda ta tashi haka taji duk jikinta babu k’wari, hatta awajen yin wanka saida Oum Ayush ta taimaka mata, bayan kuma ta biya sallolin dake kanta ne, Oum Ayush ta kawo mata kayan fruits tasha, ko mintuna 30 ba ayiba kuwa still ta sake komawa wani baccin. Wani babban abun mamaki kuwa shine kamar yanda Laylerh’n ta wuni tana bacci, haka ma Maleek dake can gidansa, shima yau d’in wuni yayi yana abu d’aya, saboda tun cocaine d’in daya sha daren jiya har yanzu bata gama sakeshi ba, kasancewar cocaine d’in nada k’arfi sosai. The following day Thursday. Tabbas komai aka sawa lokaci sai yazo, Kamar dai yanda yakasance yau auren saura kwana biyu. Gaba d’aya yanzu gidan nasu acike yake da jama’ar Oum Ayush wanda yawancinsu k’awaye da kuma y’an uwanta ne, saidai kuma awannan karon harda mutanen Egyft suma sunzo, wanda suke matsayin y’an uwansu Abbou Jaheed. Sosai aketa hidiman biki, duk da cewar ba za’ayi program ko daya ba, amma hakan bai hana jama’a cika acikin gidan ba. Saidai kuma rashin lafiyar Laylerh’n gaba d’aya yasa jikin su Oum Ayush yayi sanyi, saboda har yanzu marar nata bai daina ciwo ba, tana dai samun relief ne kawai idan tasha maganin baccin da Dr ya bata, daga zangar ta tashi abaccin kuwa amfanin maganin na k’arewa ciwon zai dawo, ga wani matsanancin feeling d’in da yake neman haukata mata lissafi, wanda akoda yaushe hakan ke sawa taji kaman tayi kuka, wannan dalilin yasa bata ko fitowa yanzu gyaran jikin ma an d’an lafa mata dashi. Acan b’angaren su Abbou Jaheed ma sam basu zauna ba, Dan tuni sun gama raba invitations cards wa jama’arsu. Ciki kuwa harda Fou’ad wanda shine ya tsaya akan komai da komai na bikin, hatta kayan da Ango zai sa yariga daya tsara komai. Yayinda ya tura invitations card ga kowa, kama daga kan friends d’insu harma da abokan aikinsu. Ab’angaren Maleek kuwa ya lura da yawan zirga zirgan da Fou’ad d’in keyi, saidai kasancewarsa ba mutum ne me yawan shisshigi ba, shiasa bai tambaya ba, hasalima gaba d’aya wunin yau a office d’insa yayi, saboda ayyuka sun d’anyi masa yawa, shi yasama bai dawo gidan ba sai 11pm, koda ya dawo kuwa bai kula da abunda yaga Fou’ad din nayi ba, kaitsaye bedroom d’insa ya wuce ya kwanta. *Friday* Alhamdulillah yau Koda ta tashi bata ji ciwon marar nata ya tsananta kamar yanda ya sabayi mata akwana biyun da suka wuce ba. Samun k’arfi ajikinta da tayi ne kuma yasa ta fito zuwa falo. Sosai kuwa su Oum Ayush sukaji dad’in ganin jikin nata, hakan nema yasa Oum Ayush ta k’ira meyin zanen Henna ta zana mata, wani irin kyau’n da Laylerh’n tayi kuwa har d’auke idanun jama’a yake, musamman da zanen red henna d’in ya kwanta akan skin d’inta. Ita dai kam har yanzu ta kasa fahimtar komai, dake faruwa acikin gidan. Saidai ayau d’in tasa aranta cewar zata tambayi Oum Ayush dan sanin hak’ik’anin abunda ke faruwa. Hakanne kuwa ya kasance domin tana idar da sallah’n Isha ta mik’e tsaye, direct bedroom d’in Oum Ayush ta nufa. Oum Ayush dake zaune akan gado tana Ware wasu Sabin clothes din da aka kawo mata d’inki, ganin Laylerh’n da tayi ne kuma ya sata sakin murmushi. Tare da cewa. “Laylerh bakiyi bacci ba?.â€? Kanta tad’an jinjina alaman “Eh.â€? Asanyaye kuma ta zauna agefen Oum Ayush d’in, cikin muryarta dake tafiya very slowly tace. “Oum Ayush wai waye zaiyi aure? naga gaba d’aya anata hidima.â€? D’an dakatawa daga duba clothes d’in Oum Ayush tayi, tare da juyowa ta kalli Laylerh’n, fuskarta d’auke da murmushi tace. “Auren wa kike tunanin za’ayi agidannan Laylerh idan ba naki ba? Kodai baki shiryawa yin auren bane?â€? Kanta ta d’ago da sauri, tare da zaro idanunta waje, murya na rawa tace. “Aure na kuma Oum Ayush?â€? Jinjina mata kai Oum Ayush tayi, tare da kamo hannayenta ta rik’e Cike kuma dason bata k’warin guiwa tace. “Abunda zuciya keso ne zata samu Laylerh, sannan kuma muradin dake yawo acikin zuk’ata biyu ne ke son cika, Insha Allah Ayanzu babu wani abu dazai dakatar da farincikin ku, saboda haka kwanta kiyi bacci, domin gobe da sassafe za’a shiryaki..â€? Baki idanu harma da hanci ta bud’e tana kallon Oum Ayush, da kalamanta suka sa taji ta tamkar ta zama wata statue, domin gaba d’aya tunaninta tsayawa yayi, abu d’aya ne kawai ke kai kawo acikin Brain d’inta shine AURE’n da Oum Ayush tace za’a mata. Saidai tunanin nata baije ko ina ba, haka bisa dole ta katse shi, alokacin da taji Oum Ayush d’in na cewa. “Ta kwanta anan d’akin, ita zata je wajen Abbou Khareem.â€? Har Oum Ayush d’in kuwa ta fice Laylerh bata d’auke idanu akanta ba. Gaba d’aya ma tarasa tunanin me zatayi. Hakan yasa ahankali ta sulale ta kwanta akan gadon, tare da lumshe idanunta, ga mamakinta kuwa ji tayi wasu irin k’walla masu sanyin gaske na bin gefen fuskarta. K’wallan da ita kanta batasan na menene ba. Lokaci guda kuma taji wani irin sanyi na ratsa cikin tafin k’afanta dama zuciyarta. Hakan kuwa shi yasa ta dunk’ule jikinta waje d’aya, tare da soma sauk’e wani irin ajiyar zuciya. *M.Jay* *12:30 am* Sassanyar iska da kuma sanyin dake hura jikinsa ne yasashi bud’e idanunsa wanda suka b’ata tsawon lokaci a kulle, duk da cewar kuwa ba bacci yake yi ba, domin yanzu ak’alla 1 hour ya b’ata da kwanciyarsa amma sam bacci yak’i zuwarwa idanunsa. Wani irin bak’on yanayi yakejin kansa aciki, yanayin daya kasa fassarasa, domin zai iya cewa tunda yake aduniya bai tab’a jin zuciyarsa tayi sanyi irin na yau d’in ba. Ajikinsa yakejin cewa Lallai da gaske wani abu babba zai faru dashi, domin hatta bugawar zuciya da numfashinsa ayau d’in sun sanja. Sake gyara kwanciyarsa yayi akaro na barkatai, tare da d’aga idanunsa ya kalli agogo, hakanan yake ganin daren yau d’in yayi masa tsayi, tamkar ma gari bazae waye ba yake ji. Kansa ya d’an girgiza tare da tashi zaune, ahakikanin gaskiya so yake ya gano asali da kuma gaskiyar abunda yakeji, saboda yanda yakejin kamar yana zumudin wani abune wanda baisan menene ba. Ganin kuma da yayi, tunani na shirin haukata masa Brain d’insa ne, Yasashi Saukowa daga kan gadon, tare da wucewa toilet ya d’auro alwala. Koda ya fito daga toilet d’in sallaya ya shumfud’a tare da soma gabatar da nafilfilu. Haka ya d’auki lokaci mai tsawo yana sallah, har sai k’arfe 3 kafun ya sake komawa ya kwanta. Cikin ikon Allah kuwa yana kwanciya bacci mai d’auke da mafarkai kala kala ya d’aukesa. Ana soma kiraye kirayen sallah’n Asuba kuwa ya farka. Tare da Fou’ad sukaje masallaci, suna dawowa kuma ya sake komawa bacci. Fou’ad kuwa ganin Maleek d’in ya sake komawa bacci ne yasashi sakin murmushi, tare da daukan waya ya kira Abbou Jaheed. Basu wani jima suna wayan ba kuwa sukayi sallama. Fou’ad na ajiye wayan ya shiga kimtsa musu abubuwan da zasu buk’ata, shikansa ayau jin zuciyarsa yake babu ko digo na damuwa, akaron farko dai yau Captain Maleek Jaheed Gwani zai angwance. Tabbas arana irin ta yau din babu wani wanda zai iya misalta farinciki da kuma annushuwar dake cikin zuciyar duk wani wanda yasan Laylerh Maleek. Ranace ta musamman wanda bazasu tab’a manta taba har abada. Ranace da zuk’atan dake d’auke da dakon juna zasu zama abu d’aya, buri d’aya, fata d’aya, kana kuma muradi d’aya. K’warai wannan SATURDAY d’in tazo da mahimmanci sosai acikin a halin. 10:00am Daidai Hayaniya da kuma surutan dake tashi acikin falonne yasashi d’an soma bud’e idanunsa. Addu’an tashi daga bacci yayi tare da d’an yunk’ura ya tashi zaune. Tabbas hayaniya yakeji acikin falonnasa bawai kunnuwansa ne keyi masa gizo kamar yanda ya dauka ba. Yar karamar tsaki yayi domin yasan cewa, idan ba Fou’ad ba babu wanda zai tara masa jama’a acikin gida. Saukowa daga kan gadon yayi, tare da wucewa toilet kaitsaye. Wanka yayi sannan yayi brush, duk da cewar kuma yanajin yunwa sosai amma bayajin zai iyacin wani abinci. Ahankali ya murd’a handle d’in k’ofar toilet d’in ya fito, jikinsa sanye da white bathrobe. Turus haka ya tsaya yana me kallon Fou’ad da SOORAJ wanda suke zaune akan gadonsa, gaba d’aya dukansu sunyi wani irin kyau, cikin shigar babbar rigar dake jikinsu. Murmushi SOORAJ yayi masa, tare da tasowa ya k’araso kusa da shi. Hannunsa yasa yad’an bugi shoulder’n Maleek d’in. Cikin yanayinsa na wanda bai saba magana ba yace. “Congratulations!!â€? Murmushi shima Maleek d’in yayi, duk da baigane akan me SOORAJ d’in keyi masa congrats ba. Fou’ad kuwa tasowa yayi, cikin hanzari ya jawo Maleek d’in. “Kayi sauri ka shirya bamu da lokaci 11 daidai bama african time.â€? Fou’ad ya fad’a adaidai lokacin da yake kai Maleek d’in gaban mirror. Still batare daya fahimci inda kalaman Fou’ad din suka dosa ba, ya d’auki. Men body lotion d’insa ya shiga shafawa. Bayan ya kammala ne kuma ya gyara beautiful beard d’insa da kuma tarin sumar kansa. Had’add’en spray d’insa ya shafa, ganin kuma yana k’ok’arin bud’e closet d’insa zai d’auki kaya ne yasa Fou’ad yayi saurin mik’o masa set d’in wata had’addiyar white getzner da aka killacesa cikin wani had’add’en kwali. “What?â€? Ya fad’a yana me kallon kwalin da Fou’ad d’in ke mik’o masa, wanda aka k’yale jikinsa da ado. “Kasa.â€? Fou’ad ya basa amsa atak’aice, tare kuma da ajiye masa kwalin agabansa. Kallon Fou’ad d’in yayi, Kamar kuma zaice wani abu saiya fasa, tare da d’aukan kwalin ya bud’e. Idanunsa ya d’an lumshe saboda ganin had’add’iyar getzner’n da aka k’awata ta da d’inki, riga da wando da kuma babbar riga, wanda akayiwa wani fitinannen aiki da blue colour d’in zare. “What babbar riga? Nasaka saboda meye?â€? Yayi maganan cikin wata had’add’iyar muryarsa da ba’a saba jinta ba. Matsowa kusa dashi SOORAJ yayi, cikin yanayin son bashi k’warin guiwa yace. “Kasa please kada kayi musu, zamuce daurin aure, kayi sauri munajiranka afalo.â€? Ko jiran abunda Maleek d’in zaice bayyiba ya ja hannun Fou’ad suka fita daga cikin d’akin. Maleek kuwa kayan yabi da kallo, azuciyarsa yana me mamakin kyau da kuma tsadan getzner d’in, musamman aikin da akayi wa babban rigar yasan yaja kud’i. “Bikin waye To kenan?.â€? Yayiwa kansa tambayar da babu mai basa amsarta. Ganin kuma idan ya tsaya zai b’atawa kansa lokaci ne, yasashi d’aukan riga da wandon ya saka, kafun daga bisani ya d’aura babbar rigar akai. Yah Allah Bak’armin kyau kayan sukayi masa ba, wanda shi kansa saida yaji hakan ajikinsa. Aikuwa kyawun nasa bai sake bayyana ba, saida ya d’aura wata had’add’iyar hulan dake had’e da kayan, me ratsin blue colour asaman akansa. Black socks ya sakawa fararen k’afansa, tare kuma da zura wasu had’add’un classicshoe masu kalan blue, wanda suka k’ara bayyana had’uwa da kuma kyaun kwalliyarsa. Still wannan kwalin ya bud’e ya ciro agogon Rolex mai kalan bluesy ya daura akan tsintsiyar hannunsa. Sassanyan turaren Dolce&Gabbana ya fesa ajikinsa, tare da d’an juyawa ya kalli mirror. Kyawawan idanunsa ya d’an lumshe, domin ya gamsu da irin baiwar kyau da Allah Yayi masa. Ahankali ya shiga tafiya da takunsa mai matuk’ar d’aukar hankali. Hannunsa ya daura akan handle d’in kofar tare da murdata Ahankali. Wani irin fitinannen kamshinsa daya daki hancinsu Fou’ad ne kuma yasa duk suka maida kallonsu ga kofar bedroom d’insa. “Wow!!!â€? Shine abunda gaba d’ayansu suka fad’a alokacin da sukayi ido biyu dashi. Lallai Tabbas ayau ko makiyinsa zai shaida irin kyaun da yayi, Tabbas sun sake yarda cewa Maleek kyakkyawa ne ajin farko, ko su da suke maza ma ya burgesu inaga mata. Hannunsa Sooraj d’in Zeeyaderh ya kamo, tare da yiwa su Fou’ad alama akan su tashi su tafi. Ahaka suka fito gaba dayansu kowannensu kallo d’aya zaka masa, kasan cewa kud’i, Hutu da kuma kyau na kai musu. Cikin wata had’add’iyar 2020 Mercedes Benz G63 suka shiga, shida SOORAJ ne abaya, sai Fou’ad dake gaba wanda shi zaiyi driving d’insu. Sauran friends din nasu kuwa wanda basu wuce su 4 ba, kowannensu motansa ya shiga. Haka motocin suka jero akan shumfud’add’en titi’n, dagani kasan wasu masu matsayinne acikin motan. 11:40 am gaba d’aya k’ofar gidan Acike yake da dubbannin jama’a, kama daga kan manyan y’an kasuwa zuwa masu siyasa, ciki kuwa harda govenors na wasu states mabanbanta, wayanda duka bakin su Abbou Khareem da kuma Abbou Jaheed ne. Kowa ka gani acikin bakin kuwa fuskarsa dauke take da murmushi, banda su Abbou Jaheed da suka rasa inda zasu kai farincikin su. Ahankali ya d’ago kansa daga danna wayarsa da yakeyi, ganin hanyar da suka kamane kuma yasashi saurin kallon Fou’ad, cikin yanayi nadan mamaki yace. “Fou’ad Ina zamuje ne?â€? “D’aurin aurenka.â€? Fou’ad ya bashi amsa kaitsaye. Daidai lokacin kuwa suka iso bakin harabar gidannasu dake cike da jama’a. Idanunsa ya d’an zaro waje, tare kuma da sa hannunsa yad’an dafe zuciyarsa, wanda tun tashinsa yakejin tana tsananta bugawa. Mutanen dake cike awajen ya kurawa idanu, zuciyarsa cike da wasi wasi. Saidai kafun ma yayi wani tunani kamo hannunsa da SOORAJ yayi ya katse masa duk wani hanzarinsa. Abdoul ne ya karaso da sauri ya bud’e musu murfin motar, aikuwa yana sako k’afarsa waje yaji bugun zuciyarsa ya tsananta. Bai kuma tsinke da al’amarin ba saida yaji marok’a na shelan cewa Ango ya iso, wanda hakan yasa masu Algaita suka soma busawa. Abbou Khareem ne ya k’araso inda suke tare da kamo Maleek d’in suka k’arasa cikin wajen da aka k’awatasa dan d’aura auren. Koda suka shiga cikin wajen kuwa kallone ya dawo kansu, zaunar dashi Abbou Khareem yayi kana shima ya zauna. Tare kuma da sanarwa limaman dake wajen cewa Ango yazo za’a iya d’aura auren. Kamar yadda yazo a shari’ar musulunci Abbou Jaheed ne ya dubi Abbou Khareem, tare dayin gyaran murya cikin nutsuwa da kuma bayyana farincikinsa, yace. *Ni Alhaji Jaheed Ina nemawa d’ana ABDOUL MALEEK JAHEED auren AYSHA MAHMOUD NA’EB bisa sadaki Naira Million Biyu.â€?* Murmushi Abbou Khareem yayi tare da gyara zamansa cikin girmama yayannasa yace. *”Ni Alhaji Abdoul Khareem na bawa ABDOUL MALEEK JAHEED GWANI auren AYSHA MAHMOUD NAEB a bisa sadaki 2million Naira.â€?* *Alhamdulillah Aure ya d’auru*. *(This page is dedicated to all LAYLERHMALEEK fans)* *25/March/2021* *10:23 pm* 3/27/21, 7:16 AM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Not editing* *Chapter 73* Wani irin gumi ne ya shiga fitowa daga kowani k’ofar gashi na jikinsa, take kuma lokaci d’aya yaji wani irin matsanancin sanyi na busa shi, wanda hakan yasa gaba d’aya gangar jikinsa ta soma rawa. Idanunsa dake bayyana matsanancin mamaki, da kuma rashin tsammani ya d’ago ya zubawa su Abbou Jaheed, wanda tuni suka fara addu’a tare dayi musu fatan zaman lafiya mai d’orewa. Tunda yake aduniya bai tab’a samun kansa acikin irin yanayin daya samu kansa aciki yanzu ba, wani irin juyawa yakejin kansa nayi masa, yayinda duk gaba d’aya tunaninsa ya tsaya cak, Tabbas awannan lokacin zai iyacewa komai nasa ya tsaya na d’an wani lokaci, ciki kuwa harda numfashinsa. Tamkar gizo yake ganin abun daya ta’allak’asa amatsayin mafarki, domin sam bai yarda cewar wai shid’in aka d’aurawa Aure da Laylerh ba, yamafi kyautata zaton cewa kuramen kunnuwansa ne sukeyi masa k’arya, sam bazai tab’a iya misalta wannan yanayin da kuma abunda yake jiba, bisa dole haka yakejin kansa tamkar statue ko kuma wani wanda yayi losing memory d’insa. SOORAJ dake gefensa ne yasaki murmushi tare da kamo hannun Maleek d’in, cikin nuna tsananin Jin dad’i da kuma farincikinsa yace. “Alhamdulillah congratulations M.Jay, yau kazama Mijin Laylerh.â€? “Hakama Laylerh ta zama matarka, yanzu ita d’in mallakinka ne, zata rayune kuma ak’ark’ashin kulawarka, nasan kana ganin abun kamar amafarki ne, but ba mafarki bane da gaskene Maleek da gaskene Laylerh ta zama matarka ayau...â€? Fou’ad ya k’arasa maganan da SOORAJ d’in ya soma, idanunsa cike da hawaye sam shikam ya kasa jurewa, Domin sanin k’arfin soyayyar dake tsakanin Laylerh Maleek, yasa auren nasu da aka d’aura yau, ya sanyayar masa da zuciya. Ahankali ya matso ya rungume Maleek d’in da har yanzu ya kasa yin koda kyakkyawan motsi ne, still kuma har yanzu jikinsa bai bar b’ari ba, saboda ba k’aramin shock ya shiga ba. Numfashinsa dake k’ok’arin k’wace masa gaba d’aya ya fusgo, tare da sauk’e wata irin ajiyar zuciyar, da tasa duk su Abbou Jaheed suka juyo suka kalleshi. Kallo d’aya kawai da Abbou Jaheed yayi masa, take ya fahimci cewa, Maleek d’in baya cikin nutsuwarsa. Hakanne yasa Abbou Jaheed yin k’asa da murya, tare da cewa Fou’ad ya ja Maleek d’in zuwa part d’insa dake cikin gida. Kai Fou’ad ya jinjina tare da kamo hannun Maleek d’in, suka mik’e tsaye, Tashin nasu ne kuma yasa mutanen dake wajen suka dinga zuwa sunayiwa Maleek d’in murna. Shidai kam Allah Yasani ayanzu baya fahimtar komai, hakan yasa Fou’ad ne kawai ke amsa musu. Ahaka suka fice daga cikin taron dubban jama’an. Kaitsaye ta k’ofar baya suka shiga cikin gidan, direct kuma har sashin Maleek d’in. Fou’ad ne ya bud’e k’ofar falon suka shiga. Suna shiga kuwa ya sake hannun Maleek d’in, tare da dubansa suka fuskanci juna. Y’an guntun hawayen dake cikin idanunsa ya share, tare da sakin murmushi, kana Ahankali yasa hannunsa ya bubbugi kafad’an Maleek d’in, cike kuma dason bashi k’arfin guiwa yace. “Sama da kwanaki dubbai ka share a iya tsawon rayuwarka kana jiran zuwan wannan ranan, Tabbas komai mai zuwa da wuce wane Maleek, soyayyar daka rena acikin zuciyarsa almost 19 years yau gashi ta zama kammalalliya, Ayshnoor d’inka Maleek Ayshnoor d’in da kaketa fata da burin samu yau gashi ka sameta, yau Ayshnoor ta zamo mallakinka bayan tarin k’addarorin da sukayi wasa da rayuwarku, tabbas sau dayawan lokuta sai anfuskanci k’alubale masu tarin yawa kafun ake samun abunda akeso, ba kuma wata Nasara da take zuwa da sauk’i, ako ya ya dole sai gangar jiki da zuciya sun fuskanci k’alubale akan abunda suke so, shin ko kasan wani mutum ne mafi sa’a arayuwa? shine wanda zai iya d’auka da kuma jure kowani irin k’alubale akan k’addarorin rayuwa da Allah Ya rubuta masa, Kamar dai kai Maleek, duk da cewar akaron farko ka rasa Laylerh, amma baka aminta cewar ka zama Loser ba, zuciyarka ta tsaya akan abunda ta keso, duk da cewar akullum kanajin rad’ad’i k’una da kuma ciwo, amma still baka sanja daga soyayyar da kakeyi mata ba, domin da soyayyarta ne kad’ai kake iya gudanar da komai na rayuwarka, akwai kuma abunda kai kanka baka sani ba Maleek, idan babu soyayyar Laylerh acikin zuciya da jininka, kwata kwata bazaka tab’a iya cigaba da rayuwa ba, koda ma ace zaka rayu, To tamkar zero haka zaka zama, domin Laylerh itace gaba d’aya rayuwarka, itace macen da komin nauyin k’addara dole sai ta barku atare, again kuma itace macen da zata iya rayuwa dakai akowani irin hali, babu ruwanta da rashin lafiya ko kuma wata lalurarka, kai d’inne dai kawai acikin tunaninta, domin haka ne ma ta fad’awa su Abbou Jaheed cewar ta zab’i rayuwa dakai akan komai, saboda burinta akullum shine taganka cikin farinciki, Laylerh takace Maleek takace kai kad’ai kuma har abada!!!â€? Wasu irin zafafan hawayen da suka cika idanunsa ne, suka samu daman gangarowa kan k’uncinsa. Hakanne kuwa yasashi saurin juyawa kaitsaye ya nufi bedroom d’insa, duk da cewar ayanzun ko ganin gabansa da kyau bayayi. Tsura masa idanu Fou’ad yayi, Yayinda ganin hawayen M.Jay akaro na farko, yasa zuciyarsa soma wani irin bugawa, take kuma tausayin Maleek d’in ya kamasa, domin ayau dole ne yayi kuka, bayan duk gwagwarmayan da yasha gashi Yau Allah ya basa Laylerh. Shid’inma juyawa yayi ya fice daga cikin falon, tare da jawo k’ofar ya rufeta gam, saboda yasan cewa ayanzu Hutu da kuma nutsuwa Maleek d’in keso. K’afafunsa da yakejin sunyi masa nauyi, ya soma ja ahankali tare dasa hannunsa d’aya ya turo k’ofar bedroom d’in. Wani irin sanyi sosai yakeji ajikinsa, Yayinda bugun zuciyarsa kuwa har yanzu ta kasa dawowa daidai. Brain d’insa kuwa tuni dama ta haukace, domin ta kasa d’aukan tunani d’aya da zata yi, abu d’aya ne kawai yasan keyi masa yawo acikin kan nasa, shine d’aura aurensa da Laylerh da akayi yau. Baisan ta yaya, sai fara misalta irin yanayin da yake ciki ayanzun ba, abu d’aya kawai yake ta tambayar kansa, shine an d’aura masa Aure da Laylerh? hakan na nufin ya zama mijinta kenan? Kansa ya d’an soma girgizawa ahankali, tare kuma dasanya hannayensa ya zare babbar rigar dake jikinsa, kasancewar jin jiki da kansa yake tamkar an d’aura masa k’aton dutse. Ahankali ya shiga jan k’afafunsa har zuwa bakin k’ofar bathroom, murd’a handle d’in k’ofar yayi tare da kutsa kansa ciki. Batare kuma daya rufe k’ofar bathroom d’inba ya k’arasa shigewa cikin toilet d’in. Adaidai saitin shower ya tsaya, tare dakai hannunsa ahankali ya danna makunnin shower’n, take kuwa ruwa ya soma zubowa akansa, batare daya cire kaya ko takalmin dake k’afansa ba. Sauk’an ruwan atsakiyar kansa ne kuma yasashi lumshe idanunsa, tare dasa hannunsa d’aya ya dafa jikin bango, duk da yanda jikinsa ke b’ari kuwa baiji ajikinsa cewar zai kashe shower’n ba, ayanzu so kawai yake ya dawo cikin hankali da tunaninsa. Acan cikin gidannasu kuwa, koda labarin d’aura auren Laylerh da Maleek d’in ya shigo kunnen su Oum Ayush ba k’aramin farinciki da kuma godewa Allah sukayi ba. Ahankali Oum Ayush ta turo k’ofar d’akin ta shigo, hannunta d’auke da plate d’in abinci. K’arasowa jikin gadon da Laylerh’n ke kwance tayi, sam fuskarta ya kasa b’oye farincikin da take ciki, hannunta tasa adaidai kan goshin Laylerh dake kwance ta lumshe Idanunta kamar maiyin bacci. Jin kuma babu ko d’igon zafi ajikin Laylerh’n ne yasa ta, sauk’e ajiyar zuciya tare kuma da ajiye plate d’in dake hannunta asaman bedside. “Laylerh!â€? Ta k’ira sunan Laylerh’n anutse. Idanun nata dake alumshe ta d’an bud’e ahankali tare da kallon Oum Ayush d’in. Murmushi mai kaman dariya ne ya k’wacewa Oum Ayush saboda, ta gama lura da cewar gaba d’aya ciwon Laylerh’n zallan sakalci da shagwab’ane. “Tashi kici abinci, sai kiyi wanka, yau ba ranar da zakiyi ta kwanciya bane.â€? D’an k’aramin bakinta ta turo gaba, kaman zata ce wani abu kuma sai ta fasa, ahankali ta yunk’ura ta tashi zaune. Idanu Oum Ayush ta d’an zuba mata, Yayinda fuskarta ke sake wadatuwa da murmushi. Ganin hakanne kuma yasa Laylerh’n sake shagwab’e fuska, asakalce tace. “Nifa Oum Ayush har yanzu marana ciwo yakeyi, kuma nama k’oshi da abincin.â€? Hararan wasa Oum Ayush ta watsa mata, tare da d’an had’e fuska, cikin salon bada umarni tace. “Dolenki kuwa sai kinci abinci ko so kikeyi akaiki d’akin mijin naki da yunwa acikin ki? kin sandai waye Maleek cikinsa ma baikula ba bare naki.â€? Idanunta tad’an zazzaro waje cikin yanayin mamakin da ya kasa b’uya akan fuskarta tace. “D’akin mijina? Kuma Yah M.Jay?.â€? Still wani harara Oum Ayush ta watsa mata, tare da cewa. “Oh Allah yarinya saikace bakece da bakinki kikace a aura miki shi ba, To finally yau dai an d’aura muku aure yanzu ya zama mijinki ke kuma kin zama matarsa, idan kuma bakyaso yanzu sai nafad’awa su Abbou’nki su warware auren.â€? Wani irin dokawa k’irji da zuciyarta sukayi, musamman da maganganu biyun suka fito alokaci d’aya, take kuma taji wani irin abu mai tsananin sanyi ya shiga yawo acikin gangar jikinta, wanda hakan yasa Idanunta cikowa da k’walla, yayinda akan fuskarta kuwa wani irin sahirtaccen murmushi ne ya bayyana, wanda ita kanta batasan dashi ba. Ahankali tasa ta fukan hannayenta ta rufe fuskarta, domin wani irin shauk’i, kunya da kuma raunin zuciya ne suka lullub’eta alokaci guda, wanda har hakan yasa takejin kunyan Oum Ayush ta kalli fuskarta. Oum Ayush kuwa gane hakanne yasa ta saki murmushi, tare da mik’ewa tsaye, cikin kulawa tace. “Kici abincin sosai kinji Laylerh na, kinga masu meckup din dana dauko suna hanyan zuwa, idan kuma so kike akaiki wajen Maleek d’in babu kwalliya to.â€? Batare kuma da ta jira me Laylerh’n zata ceba, ta bud’e k’ofar d’akin ta fice. Laylerh kuwa jin fitar Oum Ayush d’in daga cikin d’akinne yasa ta bud’e fuskarta, wanda tuni ma harta b’aci da ruwan hawaye. “Shikenan yanzu da gaske Yah M.Jay ya zama mijina?â€? Tayiwa kanta tambayar abayyane, Yayinda azahirance kuwa takejin wani irin matsanancin soyayyarsa na k’aruwa acikin zuciyarta. Wayarta ta dauka da sauri tare da lalub’o hotonsa dake cikin wayar, kyakkyawar fuskarsa ta tsurawa idanu bata ko k’yaftawa. Cikin wata irin hot feeling voice dake fita slowly tace. “Alhamdulillah Zan kasance dakai har abada My Boo, da kaine kawai Zanyi rayuwa, sannan zan jurewa duk wata k’addararka!!!â€? K’arar wayarsa dake cikin aljihunsane ya dawo dashi daga cikin wata duniyar da yashiga, wanda batare daya ankara ba, har ruwan dake dukan jiki da kansa ya soma kokarin yi masa illa. Janye jikinsa daga bakin shower’n yayi, tare dasa hannunsa ya kashe shower’n. Gaba d’aya jikinsa ya jik’e tako ta ina, saboda tsabar sanyin daya shigesa kuwa harta hak’waran bakinsa karkarwa suke, amma da yake zuciyarsa tatafi zuwa wani waje na daban sam bayajin hakan ajikinsa. Saima k’arasawa gaban sink da yayi ya d’auro alwala. Bayan ya kammala alwalan ne kuma ya fito daga cikin toilet d’in, duk inda ya taka kuwa ruwan jikin kayansa ne ke d’iga awajen. Samun kansa kuma da yayi akan Lallausan carpet d’in dake Malale a k’asan d’akinne yasa ka shi lumshe idanunsa. Tare da zamewa ya durk’usa guiwowinsa. Hannayensa dake ta karkarwa ya sa ya dafa k’asa, tare kuma da kai goshinsa k’asa yayi Sujjada, Lokaci d’aya kuma yaji wasu irin hawaye masu tsananin zafi sun zub’o daga cikin idanunsa. Labb’an bakinsa dake rawa ya d’an soma matsawa, saidai sam harshensa bai basa daman fad’an wata kalma ba, Allah Ne kad’ai yasan abun dake Cikin zuciyarsa ayanzun, yau rauninsa ya bayyana sosai, zuciyarsa ta karye, karyewa irin wanda bata tab’a yi ba, da wani bakin da wasu kalmomin zai godewa Allah? kowani kalma dake bakinsa jinta yake tayi kad’an. Yau ya zama wani na daban, yanajin kansa amatsayin wani ba Maleek da rayuwarsa ke cike da tarin k’addarori ba, yanajin kansa amatsayin raunataccen bawa mai raunin zuciya da gabb’ai. Sunan Allah Ya k’ira adaidai lokacin da wani irin kuka, mai tsananin tab’a zuciya ya k’wace masa, kukan dake bayyana asalin abun dake cikin zuciyarsa. Tabbas yayi rauni sosai, ya kuma kai wani mataki wanda bazai iya gujewa wannan kukan ba, ayau babu maganan miskilanci, hali, ko kuma rashin yawan magana da jarumta, sam bayajin way’annan ajikinsa, musamman ayanzu daya san yana a gaban Ubangiji’n daya fi, kowa sanin sirrin zuciyarsa, Ubangijin daya ke d’aura masa k’addara ya kuma yaye masa, Ubangijin daya basa numfashi da lafiyar halitta dana ji da gani. Shin dame zai godewa Ubangiji’n daya basa Laylerh ayau? Ya rayu da matsanancin sonta, sonta ya zame masa abinci da kuma ruwan shansa. Ya rasata adaidai lokacin da yake buk’atar ta, again gashi kuma yau ya sake samunta a lokacin da yafi da tsananin buk’atar ta. Sunayen Allah ya soma k’ira acikin zuciyarsa, yana meyi masa godiya game da ni’imar da yayi masa ayau, yana godiyar acikin zuciyarsa ne kuma saboda, kukan dake ci gaba da taso mai, wanda hakan yasa harshensa kasa iya sarrafa maganganu. Almost 20minute yana ahaka still kuma har yanzu idanunsa basu daina zubar da hawaye ba, saidai kuma zuwa yanzu bugun zuciyarsa ta soma tsagaitawa, tare da rage gudun da takeyi. Ahankali ya d’ago daga sujjadar da yakeyi d’in, tare da zama ya tank’washe k’afafunsa, saboda har yanzu sanyi sosai yakeji. Takure jikinsa waje d’aya, tare da juyar da kansa ya tsaida idanunsa akan hoton Ayshnoor d’insa, Ayshnoor d’in da ayanzu ta zamo mata agareshi. Jajayen idanunsa da ke d’auke da danshin hawaye ya lumshe, tare da d’an ware hannayensa ahankali, Ita d’in kawai yanzu yakeson ji acikin jikinsa, yana so ya ganta, kallo d’aya kawai, kallon da zaiyi mata amatsayin matarsa. Idanunsa ya d’an sake rumtsewa, saboda tunawa da yayi cewar, ayanzu Laylerh’n ta shigo rayuwarsa alokacin da yake d’auke da larura, larurar da bazai tab’a iya bata y’ay’an da zatayi alfahari dasu ba. Kansa ya d’an soma girgizawa ahankali, tare kuma da had’e labb’an bakinsa waje d’aya ya taunesu. Daidai lokacin kuwa aka fara knocking k’ofar d’akin. Hannayensa yasa da sauri ya goge hawayen dake kan fuskarsa, duk da cewar kuma idanunsa sunyi jajur, dole duk wanda ya kalleshi zai san cewa yayi kuka. Ahankali duk da karkarwan da jikinsa keyi, haka ya mik’e tsaye tare da k’arasawa ya bud’e k’ofar. Kallonsa Fou’ad dake tsaye yayi from head to toe, ganin kuma yanda kayan jikinsa ke jik’e da ruwa ne ya sashi d’an zaro idanunsa, cikin yanayin mamaki yace. “M.Jay what’s wrong with you? idanunka sunyi ja, then kayi kuka ga kuma kayanka ajik’e why?â€? Kansa kawai ya girgizawa Fou’ad d’in alaman babu. Murmushi kawai Fou’ad din yayi tare da kamo hannunsa, cikin kulawa yace. “Mu tafi, domin anjima nan za’a kawo maka amaryarka, saboda haka baidace ka zauna anan d’in ba, wai koma baka ga ansawa ko ina dake cikin nand’in sabon furnitures bane?â€? Kansa ya jinjina alaman baigani ba, duk da cewar kuwa ya gani d’in. Murmushi Fou’ad yayi, saboda dama yasan mai hali baya tab’a fasa halinsa. Batare kuma daya sake cewa komae ba ya kamo hannun Maleek d’in suka fice daga cikin dakin. Duk da kuwa yasan cewa Bawae nan part d’inne za’a kawo Laylerh’n ba, kawai dai yayiwa Maleek d’in hakanne, saboda ya samu subar gidan. Kamar kuwa yanda suka shigo ta kofar baya, haka yanzun ma suka fita. Kaitsaye gidan Maleek d’in dake wuse suka nufa. *(Sorry wallahi bani da enough charge kuyi manage amma ba’anan naso tsayawa ba)* *9:7 pm* 3/29/21, 11:25 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Chapter 74* Kaitsaye gidan Maleek d’in dake Wuse suka nufa. Koda suka isa gidan kayan dake jikinsa ya sanja, tare da neman k’wayoyin da zasu sauk’ak’a masa wajen rage masa ciwon kan da yakeji, domin barin da yayi ruwa ya dakesa sosai ya haifar masa da ciwon kai. Yanashan maganin kuwa wani irin bacci mai tsananin dad’i ya d’aukesa. Acan b’angaren su Oum Ayush kuwa, kayan lefen Laylerh’n da sukayi order ne, suka iso, wanda hakan yasa suka baje kayan anan cikin babban falon gidan, kowa sai Masha Allah yake fad’i, domin ba kad’anba aka narka mak’udan kud’ad’e wajen had’a kayan lefe’n akwatuna 26 kowannensu kuma cikinsa cike yake da kaya, Yayinda aka Ware akwatuna 2 musamman, aka zuba wasu had’addun Dubai and Turkish abayas masu tsananin kyau da tsada. Bayan kuma kowa ya gama kallon kayan lefen ne, Oum Ayush d’in ta k’arasa zuwa d’akinta, wanda anan cikinsa Laylerh’n ta kwana, Koda ta k’arasa cikin d’akin nata kuwa, akwance ta tarar da Laylerh’n, ganin kuma da tayi cewar, Laylerh’n batajin dad’in jikinta sosai ne yasa, da kanta yau d’in ta taimaka mata tayi wanka da wani irin ruwa mai fitinannen k’amshi, bayan ta fito awankanne kuma Oum Ayush d’in ta turara mata jiki da turaruka masu k’amshin gaske, wanda hatta ita kanta Laylerh’n idan k’amshin turaren ya daki hancinta sai taji idanunta na lumshewa. Still ga kuma wani irin fitinannen feeling da ke taso mata, duk da cewar har yanzu bata daina jin ciwo a marar nata ba, saidai pain relievers d’in da take sha, sosai suke kashe mata zafin ciwon, amma daga zangar aikinsu ya k’are tofa ciwon marar nata zai dawo. Zaune take akan wani d’an madaidaicin abu me kaman kujera, inda take sanye da wani d’an k’aramin towel ajikinta, daga gefe guda kuwa d’aya daga cikin mata masu gudanar da gyaran jikin nanne, ke shafe mata duk jikinta da wani sassanyan turare mai dad’in k’amshi. Bayan matar ta gama shafa mata turarenne kuma tayi mata parking dogon gashinta da yasha saloon. Wata doguwar rigar atamfar Chiganvy wanda akayiwa had’add’en d’inkin boubou gown matar ta ajiyewa Laylerh’n, batare kuma da tace komai ba ta juya ta fice daga cikin d’akin. Ganin hakanne kuma yasa ahankali ta zame towel d’in dake jikinta, kasancewar kuma already dama ta shirya cikin jikinta ne, yasa anutse ta d’auki rigar boubou gown d’in ta saka ajikinta. Kasancewar kuma atamfar nada kalan red ne yasa ta bayyana tsananin hasken da skin d’in Laylerh’n ya k’ara. Yayinda kuma d’inkin ya zauna mata ajikinta cib cib. Still kuma D’an kunnayen gold d’in da aka ajiye mata bisa saman mirror ta d’auka ta sanya a kunnenta, ganin da tayi kuma cewar lokacin sallan azahar yayi ne, yasa ta d’aukan hijab ta zura ajikinta, kasancewar kuma dama tana da alwala ajikinta ne yasa ta tada sallah. Tun kan ta idar da sallah’n nata kuwa takejin mararta na d’an juyawa, wanda ko tantama batayi tasan ciwon marar nata ne ke kokarin dawowa, wannan dalilin yasa koda ta idar da sallah’n, komawa saman gado tayi ta kwanta. Abu kamar wasa kuwa sai gashi ciwon yanata cinta. Tana ahaka kuwa Theemah da Aleeya suka shigo cikin d’akin, ganinta da sukayi akwance ne kuma yasa suka shiga tsokanarta wai ciwon dad’ine ke damunta. Ita dai ido kawai ta lumshe domin ita kad’ai tasan me takeji, ahaka har wani bacci ya d’auketa. Ba’itane tatashi daga baccin ba kuwa sai 4, still kuma har zuwa yanzun bataji wani sauyi daga ciwon marar nata ba, hakanne kuwa yasa duk gaba d’aya jikinta yayi sanyi. Sallah’n la’asar tayi bayan kuma ta Idar da sallah’nne, Aunty Zee da Oum Ayush suka shigo cikin d’akin, abayansu kuwa k’wararriyar mai yin meckup ce da Oum Ayush ta kashe mak’udan kud’ad’e wajen d’aukota, musamman Dan tayiwa Laylerh’n meckup. Duk da cewar kuwa bata wani jin dad’i sosai, haka ta sakeyin wani sabon wanka, again turaruka masu k’amshi aka sake shafa mata ajikinta, tare kuma da zaunar da ita awani waje na musamman, cikin k’warewa kuwa meyin meckup d’in ta shiga zana mata akan fuskarta. duk yanda takejin ciwo amararta kuwa haka ta daure, domin ita d’inma ayau taji cewar tana buk’atar meckup d’in. Almost 1hour and 15 minutes aka kwashe ana meckup d’in, daya k’ara bayyana asalin kyau, da kuma had’uwarta, domin hatta ita kanta meckup artist d’in zata iya rantsuwa cewa, bata tab’a yiwa wata meckup d’in daya zauna akan fuskarta ba, Kamar Laylerh’n, saboda kyau ne dama ya had’u da ado. Ita kanta Laylerh da taga fuskarta acikin mirror saida ta tsaya k’urawa kanta ido, domin tasani tunda take bata tab’ayin kyau irin na yau d’in ba. Wani had’add’en blue d’in yadi mai kaman material, wanda akayiwa wani irin fitinannen outfit daga favoritefashion bintaberry ta saka ajikinta, d’inkin riga da sket ne amma ba wai irin normal sket d’innan bane, domin saboda tsawon sket d’innata har bayansa najan k’asa, Yayinda kuma aka k’awata jikin yadin da wani had’add’en ado mai colourn grey, daga ta saman rigar nata kuwa, wani had’add’en net akan samata, wanda ya bayyana gaba d’aya surar k’irjinta, kana kuma ya sake k’arawa shigar nata kyau, musamman da kayan suka zauna mata cib ajikinta, har kuma sukayi nasarar bayyana asalin kyau da kuma tsarin halittarta. Aunty Zee da Oum Ayush kuwa kansu bakinsu saida ya kasa rufuwa musamman da suka ga irin kyawun da Laylerh’n tayi. Oum Ayush d’inne ta kamo hannunta ta zaunar da ita, tare da bud’e wani d’an madaidaicin box, wanda aka k’awata jikinsa da ado. Wani tsadadden sark’a da d’an kunnen gold mai adon grey colour ta ciro, tare da d’aurawa Laylerh’n sark’an awuyanta, d’an kunnen kuwa akunnenta ta saka mata shi. Take kuwa walwali da kyaun sarkan suka k’arasa bayyana kyawun Laylerh’n. Meckup artist d’innan ne tayi mata wani d’aurin d’an kwalin turban da ya sake fidda kyawun kwalliyar nata. Oum Ayush kuwa k’afar Laylerh’n ta kamo, anutse ta zura mata wasu had’addun grey shoes masu kyau da tsini. D’an madaidaicin grey vail mai d’auke da adon duwatsun white stones Oum Ayush ta rufa mata, akai zuwa jikinta, yanayin yanda Oum Ayush d’in ta rufa mata vail d’inne kuma yasa kusan rabin fuskarta ya zamana arufe. Hakanne kuwa ya k’ara bayyana asalin matsayinta na had’add’iyar amarya. Turaruka masu dad’in k’amshi Oum Ayush ta fesa mata, tare kuma da kamo hannayenta ta rik’e acikin nata. Fuskarta d’auke da tsananin farinciki tace. “Masha Allah Laylerh kinyi kyau sosai, lallai yau ko Maleek idan ya ganki sai yayi da gaske kafun zai iya ganeki.â€? Murmushi gaba d’aya Aunty Zee da su Theemah sukayi, domin su kansu sun yaba da irin kyaun da Laylerh’n tayi. Mik’ar da ita tsaye Oum Ayush tayi, cikin nutsuwa kuma suka shiga takawa har suka fice daga cikin d’akin. Kaitsaye d’akin dake gefen na Oum Ayush d’in suka shiga, kan wani lallausan kujera Oum Ayush ta zaunar da ita, kana itama ta zauna akusa da ita. Hannayenta ta sake kamowa, cikin nuna tsananin farinciki da kuma nuna godiyarta ga Allah Tace. “Alhamdulillah hakika kowani tsanani yana tare da sauk’i, sannan babu wani k’unci ko kuma bak’inciki da yake d’orewa acikin wannan duniyar, ba kuma lallaine idan ka rasa abu, ya zama ka rasa shi ba kenan har abada, sannan acikin rayuwa fad’uwa da nasara na bibiyarmu akullum akuma koda yaushe, watarana mai nasara zai zamanto ak’asa, wanda yake k’asa kuma ya zamanto asama, rasa abunda kakeso afarko bawai shike nuna cewar har abada bazaka tab’a samun abunda kakeso ba, lallai idan kayi hakuri watarana zaka samu..â€? D’an numfasawa tayi, had’e da sake gyara zamanta, hannayen Laylerh’n dake cikin nata ta rik’e da kyau, cikin yanayin tausasa murya, da kuma nuna k’aunarta ga Laylerh’n tace. “Laylerh yau Allah Yayi kinzama mata ga Maleek, wanda hakan ke nuna cewar wani babban nauyi ya rataya awuyanki ke dashi, yana da hakk’i akanki haka kuma kema kina da hakk’i akansa, wajibinki ne kuma ki aikata duk wani abunda ya saki, matuk’ar bai kaucewa addinin musulunci ba, wajibinkine kulawa da ci da shansa, haka kuma hakk’inkine kulawa da kuma basa farinciki, Laylerh kinfi kowa sanin cewar Maleek mai rauni ne, duk da kuwa cewar a idanu shid’in cikakken jarumine, amma har acikin rai da zuciyarsa shid’in mai raunine, musamman akanki, domin duk wani masomin rauninsa kece Laylerh, amadadin komai nasa kece, ke kuma d’ince dai kad’ai zaki iya jib’anta al’amuransa, kasancewarsa d’an uwa kuma Yayah agareki, sannan dole sai kinyi hakuri kin kuma jurewa, duk wata jarrabawa da zata fuskanto ku, domin kasantuwarku amatsayin ma’aurata yanzu ya goge duk wani Nisan dake tsakaninku, ayanzu zaku kasance tamkar abu d’aya ne, dole buri da kuma fatanku zasu kasance atare da juna. Nasan kuma kinyi kokari sosai Laylerh, domin duk da irin k’addarar da ta same da, baki guje masa ko sanja tunani ba, haka kika amincewa aurensa, lallai Tabbas Allah Ne kad’ai zai baki ladan abunda kika aikata masa, na kuma yi imani cewar koda da second d’aya har abada bazaki tab’ayin danasanin kasancewar Maleek amatsayin mijinki ba, nasani k’warai cewar zai baki farinciki marar yankewa, da izinin Allah Kuma zakuyi rayuwa mai dad’i, rayuwar da babu munanan k’addara acikinta, rayuwar da zaku mantar da junanku cewar kud’in marayune, sannan rayuwar da haskenta zai haskaka kowa insha Allah....â€? Dakatawa da maganan nata tayi, tare kuma dad’an sanya hannu ahankali ta share hawayen daya cika idanunta, wanda batare kuma da ta saniba har ya gangaro kan fuskarta. Saurin share hawayen nata tayi, gudun kada Laylerh’n taga hawayen, murya atausashe tace. “Tashi muje tun d’azu Fou’ad da abokansa suka zo d’aukarki, Tabbas amma nasan zanyi kewarki sosai Laylerh na!!â€? Wasu irin siraran hawaye ne suka tsiyayo daga cikin idanunta, domin itama tasani tabbas zatayi kewar Oum Ayush da kuma su Abbou Jaheed, k’warai zatayi kewarsu sosai. Hannunta Oum Ayush ta kamo tare da mik’ar da ita tsaye, ahankali kuma cikin nutsuwa ta shiga takawa da ita har suka fice daga cikin d’akin. Koda suka fito cikin babban falon gidan kuwa, gaba d’aya kallo kansu ya dawo, musamman yanda mayafi da kuma shek’in suturar Laylerh’n ke d’auke idanu. Duk da cewar kuwa Rabin fuskarta arufe yake, amma hakan bai hana mutane da yawa soma yi mata video ba. Hannun Laylerh’n Oum Ayush ta mik’awa Aunty Zee, tare da yi mata alama akan taje tasa Laylerh’n amota. “To.â€? kawai Aunty Zee d’in tace, tare kuma da kama hannun Laylerh’n kamar yanda Oum Ayush ta buk’ata, haka suka fito daga cikin falon, Aunty Zee na rik’e da Laylerh wanda take d’an sakin sheshshek’an kuka, abayanta kuwa Theemah da Aleeya ne, wanda sune zasuyiwa Laylerh’n rakiya, sai kuma y’an uwansu dake Egyft wanda suka zo. Fou’ad wanda ya d’ebo abokanansa suka zo d’aukan auren, batare da Maleek d’in ma ya sani ba, shida kansa ya bud’ewa Laylerh’n k’ofar had’add’iyar White Range Rover car, Aunty Zee ta sanyata aciki, tare da shiga itama ta zauna. Ganin hakanne kuma yasa y’an tsirarun mutanen da zasuyiwa Laylerh’n rakiya suka shiga sauran motocin, saboda kuma tsabar yawan motocin da Fou’ad d’in ya kawo ne yasa kowacce mota mutum d’aya ne kawae ya shigeta, sauran kuwa haka suka zauna empty babu kowa acikinsu, domin koda ma ace mutanen suna da yawa, To dole akwai cars d’in da zasu koma empty. Fou’ad dake k’ok’arin driving motar da Laylerh’n ke ciki ne, idanunsa suka hango masa Aleeyah wacce ke shirin shiga wata mota ta daban, idanunsa yad’an tsaida akanta, tare kuma da soma k’arewa gaba d’aya halittar jikinta kallo, saboda lokaci d’aya yaji wani feeling akanta, Tabbas yarinyar tayi mishi sosai, domin tana da irin structure’n da yake matuk’ar so awajen Mace, kasancewarta brown skin kuma shine ya k’ara sawa yaji zuciyarsa ta narke akanta sosai. Har ma yaji ajikinsa cewar inama da ace motarsa ta shiga ba na wani can daban ba. Saidai kuma tunawa da yayi cewar duk guri d’aya zasuje ne, yasashi jin sanyi acikin zuciyarsa, anutse ya tada motar. One by one kuwa haka cars d’in suka soma fi cewa daga cikin gidan. Adaidai lokacin da suka mik’a kan titi ne kuma Laylerh, da kejin wani irin bacci na fusgarta Ahankali ta kwantar da kanta akan cinyar Aunty Zee. Hakanan bata san meyasa ba takejin wani irin abu mai kama da fargaba, tsoro da kuma fad’uwar gaba na yawan tunkararta, wanda har hakan yasa zuciyarta ke beating fast fast, awani bak’on yanayi na musamman takejin kanta, yanayin da sam bataji makamancinsa alokacin da aka d’aura mata aure da Najeeb ba. Gaba d’aya tunaninta ya tafi ga yanda zata fuskanci Maleek d’in amatsayin mijinta, har yanzu ganin abun takeyi tamkar amafarki. Batare kuma da sunyi tafiya mai tsawo ba duk motocin suka tsaya, adaidai lokacin da suka iso tsakiyar Maitama, agaban wani makeken gate mai masifar kyau da tsari, sauran cars d’inne sukayi parking awaje, Yayinda matashin maigadin gidan, ya wangale gate d’in, Fou’ad kuwa da Laylerh’n ke cikin motarsa anutse ya tura hancin motar cikin makeken gidan, da had’uwarsa ya zarce duk wani misali. Kasancewar kuma compound d’in gidan nada girma sosai ne, yasa saida Fou’ad ya d’anyi tafiya maitsawo kafun yayi parking motar, agaban wani katafaren dogon gini dake cikin compound d’in gidan. Yana gama daidaita parking d’in kuwa, ya fito tare da zagayowa cikin sauri ya bud’ewa su Aunty Zee k’ofar motar. Anutse Aunty Zee ta kamo hannun Laylerh, wacce zuwa yanzu sautin kukan nata ya tsaya, saidai hannunta na dama dafe yake da saman mararta. Ahaka suka fito daga cikin motar Aunty Zee na rik’e da hannunta, kaitsaye suka nufi wannan had’add’en ginin. Aunty Zee ne ta bud’e had’add’en k’ofar babban falon tare da cewa Laylerh tayi bismillah sannan kuma ta shiga da k’afar dama. Hakan kuwa akayi cikin zuciyarta tayi bismillah’n tare da saka k’afarta na dama acikin had’add’en falon da kaitsaye za’a k’iransa da sunan Aljannar duniya, musamman yanda aka k’awata cikinsa da 2021 Austin classic sofas masu matsanancin kyau da tsada. Two bedroom ne acikin falon, sai kuma stairs d’in da zaka taka wanda zai kaika sama, kasancewar kuma asaman d’akin Laylerh’n yake, hakan yasa direct Auny Zee ta wuce saman da ita. Again kuma wani babban falon suka Tatar asaman, wanda shima aka k’awata cikinsa da kayan furnitures masu kyau, saidai kuma sofas d’in dake cikin falon sun banbanta dana falon k’asa, kasancewar su way’annan d’in Culliana Victoria’n sofa ne. Kamar kuma yanda yake two bedrooms afalon k’asa haka ma ya kasance acikin falon saman, d’akin da yake ana biyu Aunty Zee ta nufa da ita, wanda kuma shima aka k’awata cikinsa da furnitures masu kyaun gaske. Ko ina dake cikin falo da d’akin kuwa daddad’an k’amshin turaren wuta ne ke tashi, sai kuma sanyin A/C’n dake tashi. Kan lallausan bed d’in dayasha bedsheet na alfarma Aunty Zee ta zaunar da Laylerh’n, tare kuma da gyara mata rufin mayafin dake jikinta. Daidai lokacin kuwa aka soma k’iraye k’irayen sallan magriba. Kallon su Theemah dake ta santin kyau da kuma had’uwar gidan Laylerh’n Aunty Zee tayi, tare dayi musu alama akan suje falo su jirata, babu musu kuwa haka suka juya ita da Aleeya suka fice daga cikin d’akin, Theemah kuwa da gaba d’aya bakinta ya kasa rufuwa, kallon Aleeya tayi cikin yanayin zumud’i tace. “Lallai Yau akwai show agidannan, da ace Ina da dama to da yau na zama sauro ta yanda zan morewa idanuna, Domin kuwa ko nayi imagine this night abun nasan sai yafi tunani naâ€? Dariya Aleeya tayi tare da d’an girgiza kanta, domin ad’an sabon da sukayi da Theemah’n ta fahimci cewar, Theemah’n irin mutanen nanne da basa iya b’oye gaskiyar abunda ke cikin rai da zuciyarsu. Acan cikin d’akin kuwa hannun Laylerh’n Aunty Zee ta kamo, cikin kulawa tace. “Mu zamu koma please Laylerh ki kula da kanki da kuma Mijinki kinji, duk abunda ya buk’ata awajenki kada kice masa a’a, domin komai dake jikinki halal d’insa ne, ke d’in yanzu mallakinsa ne, sannan kuma basa ingantacciyar farinciki ayanzu yana wuyanki ne, please Laylerh ki kula kinji Allah Ubangiji ya baku zaman lafiya!!â€? Hawaye masu sanyine suka fito daga cikin idanunta, lokaci d’aya kuma taji kuka mai sauti na shirin k’wace mata. Fahimtar hakan da Aunty Zee tayi ne kuma yasa ta juya, cikin sauri ta fice daga cikin d’akin, saboda tasan idan ta tsaya kukan Laylerh’n zai iya karya mata zuciya. Kallon su Theemah da kuma sauran y’an uwa dake zaune a cikin falon tayi, Cikin kulawa tace. “Kutashi mu tafi ko, kada Ango yazo ya samemu, har haushi ya kamasa ya bindigemu, kunsan wani lokaci masu bindigan nan birkitattun mutane ne.â€? Dariya gaba d’ayansu sukayi, had’e da mik’ewa tsaye duk sukayi waje, kasancewar way’anda suka kawosu sune zasu maidasu. Koda suka fita kuwa already sun samu dama su ake jira, hakan yasa basu wani b’ata lokaci ba, suka bar gaba d’aya arean unguwar. Jin k’aran mota da kuma alaman tafiyansu ne yasa Laylerh, sakin wani irin marayan kuka, me cike da tsananin kewarsu, saida tayi kukannata kuma kafun ta sauk’o daga kan gadon, kasancewar tana da alwala ajikinta ne kuma yasa, ta d’aukan wani hijab dake aje agefen gadon nata, kan wani lallausan carpet dake Malale agefen gadon ta hau, tare da tada sallah’n magriba. Still kuma Koda ta idar da sallah’n ci gaba da zama akan carpet d’in tayi, har aka kira sallan Isha, bayan ta sallame sallan ne kuma ta koma saman gadon ta takure kanta waje d’aya. Domin yanayin yanda taji gidan ya d’auki shiru, shine abunda ya k’ara fad’ad’a tsoron da ke kwance acikin zuciyarta. Tabbas akullum akuma koda yaushe burinta shine ta kasance dashi, amma meyasa yau gashi da tasan cewar Lallai zata kasance dashi takejin tsoro, da kuma wani irin fargaba na lullub’eta after 1second? *8:30 pm* Ahankali cikin kuma yanayin daya saba gudanar da al’amuransa, ya zura babbar rigar tsadadden shaddan dake jikinsa, wanda tayi masa kyau sosai ta kuma k’ara bayyana kwarjininsa, kasancewar kuma shadda getzner d’innasa nada colour’n grey, shi yasa hasken fatarsa sake bayyana, Yayinda lallausan black beard d’in dake kwance akan fuskarsa ke shining. Had’add’iyar hula ya saka akansa, wacce take yanayi da kaya da kuma takalmin Lolu soft leather dake k’afansa, wanda ak’alla kud’ad’en takalman yakai 50k, sae kuma silver colour original Rolex watch daya d’aura akan tsintsiyar hannunsa. Tabbas shikansa yasan yayi kyau sosai fiye ma da shigar da yayi d’azu, turaren Ouds d’insa masu sanyin k’amshi ya fesa wa duk jikinsa, wanda hakan yasa gaba d’aya cikin bedroom d’in nasa ya d’auki sassanyan k’amshi. Wayoyinsa da kuma car key d’insa dake kan mirror ya d’auka, cikin takunsa dake bayyana nutsuwa da kuma cikar kamalansa ya fice daga cikin d’akin. Kaitsaye compound d’in gidan nasa ya fito, sam babu kowa aharabar gidan daga Abdoul sai kuma gateman d’insa dake zaune abakin gate. Abdoul kuwa dake tsaye ganin Ogan nasa ya fito ne yasashi saurin k’arasowa kusa dashi, tare da d’aga hannu ya sara masa. Car key d’in sabuwar motarsa k’irar 2021 Mercedes Benz GLE450 dake hannunsa ya mik’awa Abdoul, cikin sauri Abdoul ya karb’i key d’in, tare da k’arasawa parking space ya ciro motar, wanda ko tab’a hawanta ba ayi ba. Agaban Maleek d’in yayi parking motar, tare kuma da fitowa ya bud’e masa murfin motar, anutse ya shiga gidan baya ya zauna. Yana gama daidaita zaman nasa kuwa Abdoul yaja motar suka fice daga cikin gidan. Kaitsaye Maitama suka nufa, yau akaron farko yana jin kansa acikin wata sabuwar duniya da kuma sabuwar rayuwa. *(Please Ina buk’atar addu’arku🙏🏻 because two days I’m in a bad mood😰)* *29/3/2021* 3/30/21, 8:48 PM - Ummi Tandama: *75* Sassanyun idanunsa ya lumshe tare da sake jingina bayansa da jikin kujerar motar. Wani irin bugawa yakejin zuciyarsa nayi, Yayinda abubuwa da yawa ke yi masa yawo acikin k’wak’walwarsa, akaron farko yanajin kansa amatsayin wani na daban, bawai Captain Maleek ba. Har yanzu jin kansa yake tamkar acikin mafarki. Komai na tunaninsa ya tsaya, saboda haka yana buk’atar wanda zai taimaka masa, saboda shi Baisan komai agame da abubuwan da zasu faru yau d’in ba, baisan tayaya kuma ya inane zai fara ba. Hannunsa dake d’an rawa ya d’aura akan saman k’irjinsa, daidai saitin heart d’insa dake beating da sauri. “Tsoro kakeji Maleek?.â€? Wani sashi na zuciyarsa tayi masa tambayar da yasashi, saurin bud’e idanunsa, ahankali ya d’an soma girgiza kansa, domin sam bayason gangar jikinsa su amince akan lallai tsorone ke damunsa, bayason hakan kwata kwata. Tabbas ayau yana buk’atar confidence, confidence d’in da zai tunkari Laylerh’n dashi, duk da kuwa cewar shid’in mai tsananin weakness ne akanta, but amma yau yakanji kamar bakinsa bazae iya furta wani abu agareta ba. Lallai yana buk’atar zama strongman, Domin yayi imani cewar, da irin wannan raunin zuciyartasa babu abunda zai iya. Maida kansa yayi k’asa ahankali, tare da sake lumshe idanunsa, wanda cikinsu ke bayyana abubuwa da dama. Daidai lokacin kuwa yaji Abdoul ya rage gudun motar tare da tsayawa, wanda hakan ke nuna masa alaman cewar sun iso gidan. Ahankali ya d’ago kansa, Inda ya sauk’e idanunsa akan Fou’ad dake tsaye ajikin motarsa, hannayensa rik’e da wasu manyan ledodi guda biyu. Saurin fitowa daga cikin motar Abdoul yayi, tare da zagayowa ya bud’ewa Ogannasa k’ofar motar. Ahankali ya sako k’afa da gangar jikinsa waje, adaidai lokacinne kuma zuciyarsa ta tsananta bugawa. Sassanyar iskar hadarin dake busawa ne ya daki fuskarsa, wanda hakan yasa shi d’an lumshe idanunsa. K’arasowa inda MALEEK d’in ke tsaye Fou’ad d’in yayi, tare da soma k’are masa kallo, domin zai iya cewa kyau da cikar halittar Maleek d’in bai tab’a bayyana irin na yau ba. Hannunsa ya kamo cikin nuna tsananin farincikinsa yace. “Kowani mutum aranar aurensa sai yayi kyau, komin miskilancinsa kuma sai annuri ya bayyana akan fuskarsa, amma kai naka kyaun daban yake M.Jay, kyawun da kayi ayau mai d’auke da sirruka daban dabanne, gashi kuma Ubangiji Ma nasonku, saboda zai raya muku wannan daren da ni’imarsa ta ruwan sama, ka daure Maleek domin Laylerh farinciki take buk’ata awajenka.â€? Yakai k’arshen maganar nashi yana me d’an bubbuga kafad’an Maleek d’in, saboda bashi k’warin guiwa. Batare kuma daya jira abunda Maleek d’in zaice ba, ya ja hannunsa kai tsaye suka nufi cikin gidan. Yayinda kowani taku d’aya zaiyi sai yaji bugun zuciyarsa ta tsananta. Ga kuma wani irin yanayi dake kokarin mamaye duk wani kafar sadarwa na jikinsa. Lokacin da suka samu kansu acikin baban falon k’asan kuwa, gaba d’ayansu saida suka lumshe idanunsu, saboda wani fitinannen k’amshin turare da kuma sanyin AC daya bugesu. Fou’ad ne ya ajiye ledan dake hannunsa, tare da kallon Maleek d’in, fuskarsa d’auke da murmushi yace. “Amaryarka tana sama d’aki na biyu, saboda haka nidai daga nan bazan k’ara gaba ba, please M.Jay kakula da Laylerh, kasani Kusan kama fi Kowa sanin wacece ita, kasani cewar itad’in yarinyace da batasan komai ba, sai abunda ka koya mata, za kuma ta cigaba da rayuwa ne akan kowani irin abu daka d’aurata akai, saboda haka ka kula da ita sosai, Domin ayanzu itace ta zab’eka bawai kaine ka zab’eta ba, then duk abunda kake buk’ata naka yana d’ayan dakin dake gefen na Laylerh, saboda haka ni zan tafi Allah Yabaku zaman lafiya da zuri’a mai albarka.â€? Idanunsa dake alumshe wanda suka d’anyi ja ya bud’e, tare kuma da sauk’e wani irin nannauyar ajiyar zuciya, ahankali ya d’an soma motsa jajayen labb’ansa, da dukkan alama kuma wani abu yake son fad’a, amma saidai kuma ya kasa. Ganin hakanne kuma yasa Fou’ad sakin murmushi, tare da juyawa batare da yace komae ba, ya fice daga cikin falon da d’an sassarfa, kasancewar zuwa lokacin har an d’an fara yayyafi, bakuma yaso ruwan ya samesa ahanya batare daya koma gida ba, baya ga haka ma Allah Allah Yake ya koma gida, saboda ya samu ya k’ira Aleeyah, domin ya samu daman karb’an phone number’n ta, d’azu da zai maida ita gida. Almost 5minute kenan yanzu da tafiyan Fou’ad amma ya kasa Koda d’aga k’afarsa daga inda yake tsaye, saidai idanunsa daya zubawa had’add’en stairs d’in da zaka bi ta kansa dan haurawa sama. Ganin abun yake tamkar bada gaske ba, Kamar amafarki haka yake ganin komai, Yayinda wani irin abu ke yawo acikin sassan jikinsa, wanda kuma kaitsaye bazae k’irasa da sunan feeling ba. Duk da kuwa abun yafi yi masa kama da feeling, amma kuma yanajin k’arfi da kuma tasirin abun tamkar acikin jininsa yake gudana. Aro jarumta yayi ya sakawa kansa, cikin yanayin nutsuwa ya shiga takawa Ahankali, har zuwa kan stairs d’in. Koda yakai k’arshen steps d’in hannunsa yasa ahankali ya murd’a wata door wanda kuma itace zata sadashi da falon saman. Sassanyan k’amshin daya daki hancinsa ne yasashi sake lumshe idanunsa akaro na barkatai, lokaci d’aya kuma yaji yanayin k’amshin ya sauk’ar masa da feeling. K’ofar d’akin da yake zaton acikinsa Laylerh’n take ya k’urawa ido, domin ayanzun shikad’ai yasan meyakeji ajikin zuciyarsa. Musamman ma gangar jikinsa da ta amsa masa da wani irin fitinannen feeling. Ci gaba da takawa yayi har zuwa, bakin k’ofar, still kuma har yanzu baiji zuciyarsa ta daina bugawa ba. Hannunsa na dama ya d’aura akan handle d’in k’ofar, tare da d’an lumshe idanunsa, cikin yanayin nutsuwa kuma ya murd’a handle d’in, take kuwa k’ofar ta bud’e. Wanda hakan ya bashi daman sako kansa, tare kuma da shak’an k’amshin dake tashi acikin d’akin. Rikitattun idanunsa masu bayyanar da zalla’n yanayin da yake ciki, ya sauk’e akanta. Zaune take akan gadon, Yayinda ta jingina bayanta da saman gadon, yanayin yanda tayi zaman nata ne kuma, yasa gaba d’aya k’afafunta da suka sha zanen jan lalle suka kasance a k’asa. Still kuma har yanzu vail d’inta na jikinta, wanda ya rufe mata jiki, da gaba d’aya fuskarta. Ahankali ya sauk’e ganinsa akan kyawawan fararen k’afanta, wanda suke cikin had’add’en hill shoe. Lucky eyes d’insa yad’an lumshe, sakamakon wani fitinannen k’amshin jikinta daya doso shi. Cikin wani irin kasalallen yanayi ya shiga takowa zuwa cikin d’akin. Har yanzu ganin abun yakeyi tamkar amafarki, gani kuma yake tamkar idan ya d’age mayafin dake kan fuskarta, ba Laylerh’n zai gani ba, wata mace zai gani daban. Isowarsa jikin gadonne kuma yasa shi jin tsanantawar bugun zuciyarsa, ahankali cikin wani irin fitinannen yanayin da baisan da me zai k’irasa ba, ya durk’usa guiwowinsa akan lallausan carpet d’in dake Malale agaban gadon, wanda kuma akansa ne Laylerh’n ta ajiye k’afafunta. Idanunsa ya zubawa kyawawan yatsun k’afan nata baya ko k’yaftawa, yayinda daga gefe guda kuwa yakejin wani irin sanyi na ratsa duk ilahirin jikinsa. Asanyaye yasa hannunsa ya d’ago k’afarta na dama, tare da ajiye k’afar nata akan cinyarsa, igiyan dake jikin shoes d’in ya soma warwarewa, wanda hakanne kuma ya bashi daman cire mata takalmin daga k’afarta. Ahankali ya saka duka tafukan hannayensa ya rik’o k’afafun nata, tare kuma da d’ago kansa ya k’urawa mayafin dake jikinta idanunsa wanda lokaci d’aya suka koma kalan bacci. Sassanyan k’amshin turare da kuma wani daddad’an sanyin da taji yana shiga cikin tafin k’afarta ne yasa ta d’an bud’e idanunta ahankali, domin dama baccin da takeyi d’in baiyi nisa ba, saboda yanayin yanda mararta ke murd’awa akai akai, sam ya kasa barin bacci mai k’arfi ya d’auketa. K’afanta dake cikin tafukan hannayensa tad’an motsa, asakamakon jinsu da tayi acikin wani abu mai laushin gaske. Atake kuma zuciya da k’irjinta sukayi wani irin bugawa saboda k’amshin turarensa, da taji ya cika mata hanci, wanda kuma hakan alama ce dake nuna mata cewar, lallai Maleek d’in yana cikin d’akin. saurin maida idanunta tayi ta lumshe, tare dasa hannunta ta dafe daidai saitin zuciyarta dake bugawa, matsanancin fargaba takeji sosai akan daren nasu na yau. Maleek dake durk’ushe akan k’afafunsa kuwa ganin da yayi tad’an motsane yasashi. Sake matsowa kusa da ita. Ahankali ya zare hannayensa daga k’asan k’afafunta. “AYSHNOOR!!!â€? Yak’ira sunanta cikin wata irin kasalalliyar muryar dake bayyana, asalin rauni da kuma abunda ke cikin zuciyarsa... Cak bugun zuciya da tunaninta suka tsaya adaidai lokacin da taji sauk’ar muryarsa acikin kunnuwanta, Yayinda taji wani irin abu maikama da tsoro ne ya lullub’eta. “AYSH......NOOR!!!â€? Ya sake k’iran sunanta akaro na biyu, tare da d’aura tafukan hannunsa akan nata hannun, wanda suka sha gold rings, saidai kuma ayanzu yanayin amon muryartasa ta banbanta da wanda taji afarko. Ayanzun ya k’ira sunanta ne da murya mai bayyanar da rauni. A yanayin yanda yakejin kai da zuciyarsa kuma bayajin zai iya tsayawa har sai Laylerh’n ta amsa masa. Ahankali yasa hannayensa yayi k’asa da mayafin dake jikinta. Take kuwa kyakkyawar fuska, da kuma idanunta wanda suka ciko da k’walla suka bayyana. Kusan atare suka lumshe idanunsu, saboda wani irin daddad’an yanayin da suka samu kansu aciki marar misaltuwa. Sake tank’washe k’afafunsa yayi akaro na biyu, tare da kamo soft hands d’inta ya rik’e acikin nasa, duk kuma da irin shocking d’in da rik’e hannun nata ya jawo masa hakan baisashi sakin tattausan hannayen nata ba. Idanunsa da sukayi ja sosai ya lumshe, tare da d’an matsowa kusa da ita sosai, wanda har hakan yasa guiwowinta suka shiga gogan chest d’insa. Hannayenta dake cikin nasa ya d’an matsa Ahankali, cikin kuma wata irin raunanniyar murya, dake bayyana gaskiyar abunda ke cikin zuciyarsa yace. “Why? Meyasa Ayshnoor? meyasa zaki zab’i rayuwa da mutumin da yake amatsayin nakasasshe? Meyasa zaki tauyewa kanki farinciki saboda ni kawai? Me yasa kika zab’i zama da mutumin da bazai iya baki d’a ko y’a daga jikinsa ba? Me yasa kika zab’i mutumin da zama dashi bazai amfaneki da komai ba? Bazan iya amfanar dake ba Laylerh, sure ba zaki samu zuri’a daga gare ni ba, ni mai raunine Laylerh, Tabbas hakika ni Mai Raunine, mai raunin da baicancan ci samun wata mace ya aura ba, tayaya zaki bada duk wani hope d’inki akaina Ayshnoor? Akullum burina shine kiyi farinciki, sannan burina ako da yaushe shine na nesantaki da munanan k’addarorina, sam banason kiji zafi asabo dani, domin kowani rauni d’aya naki acikin zuciyata nakejinsa...â€? Kanta ta d’an soma girgizawa cikin sauri tare dasa hannayenta ta toshe masa baki. Lokaci d’aya kuma wasu irin siraran hawaye masu zafin gaske suka shiga gangarowa daga cikin idanunta. Yayinda gaba d’aya duk jikinta ya d’auki b’ari. Saboda wani kuka ne na gaske ke k’ok’arin k’wace mata. Ganin hakanne kuma yasa shi durk’usa guiwowinsa akasa, ahankali ya d’aura kansa akan k’afafunta. Sanadin hakanne kuma yasa shi, jin wani irin feelings mood na yawo acikin jikinsa. 4/1/21, 9:10 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting By* fatymasardauna *Note editing* *(This page is dedicated to you My Sweetheart Munu Glams ILYSM Bae🖤🥀🥰)* #Love *Chapter 77* Idanunsa da sukayi ja sosai ya lumshe, alokacin da sassanyan k’amshin dake fita ajikinta ya shiga ratsa cikin hancinsa, wani irin k’amshine mai tsananin dad’i, ga kuma taushin skin d’in k’afafun nata da suka sauk’ar masa da kasala. Har yanzu yanajin tamkar abubuwan dake faruwa ba gaskiya bane, har yanzu yana ganin kaman idanu wansa gizo sukeyi masa, yanajin tamkar bashine da Laylerh’n acikin d’akin ba. Ahankali ya sauk’e wata irin k’akk’arfar ajiyar zuciya, tare da d’an janye jikinsa baya, idanunsa ya d’ago ya kalli Laylerh’n da har yanzu wasu siraran hawaye basu daina bin k’uncinta ba. Akaron farko daya tsura mata idanu baya ko k’yaftawa, domin shikad’ai yasan meyakeji acikin zuciyarsa ayanzun, k’arfin yanayin da yakejin kansa aciki ya wuce ya fassara sa, abunda zuciya da kuma gangar jikinsa ta jima tana buri da fatan samu, yau itace agabansa kuma amatsayin mallakinsa. Lallai ya yarda cewa babu wata k’addara mummuna ko kuma mai tawaya da zata tabbata, babu kuma wani abu wanda har abada bazai wuce ba. Again tsumammun idanunsa wanda yakejin ruwa acikinsu ya lumshe, tare da d’an janye guiwowinsa, daga durk’uson da yayi ya mik’e tsaye. Tafiya ya d’an soma yi Ahankali har zuwa gaban babban drawer’n dake cikin d’akin. Hula da agogon dake d’aure a tsintsiyar hannunsa ya cire, had’e kuma da zare babbar rigar dake jikinsa, ya ajiye akan wani original gothic chair dake cikin d’akin. D’an durk’usawa yayi anutse ya zare takalman dake sanye a k’afafunsa. Cikin kuma takunsa dake bayyana nutsuwarsa, kai tsaye ya nufi bathroom d’in dake Cikin d’akin. ahankali ya murd’a handle d’in k’ofar bathroom d’in, tana bud’ewa kuwa ya shige ciki tare da kullo k’ofar. Laylerh dake zaune kuwa jin alaman ya shige cikin bathroom d’inne yasata zamowa k’asa ta durk’ushe akan guiwowinta, d’aya daga cikin hannayenta ta d’aura adaidai kan mararta dake yi mata wani irin ciwo, mayafin dake kan nata ta d’an yaye tare da ajiye bayanta ajikin gadon, ta lumshe Idanunta, sassanyan k’amshin turarensa dake matuk’ar kashe mata jiki ta ci gaba da shak’a, wanda hakan yasa takejin kanta acikin wata duniya ta daban, duk da kuma ciwon da takeji ak’asan mararta, amma hakan bai hanata Jin wani irin abu na musamman akan Yah M.Jay d’in ba, yanayin da batasan dame zata k’irasa ba, kasancewar duk yanda tunaninta ya d’auki al’amarin ya wuce nan, jin abun take acikin gangar jiki da jininta. Ruwan daya taro acikin tafukan hannayensa ya watsa akan kyakkyawar fuskarsa, lokaci d’aya kuma ya saki wani irin ajiyar zuciya, tare dajan dogon numfashi. Kwantattun gargasan dake jikinsa wanda ayanzu suka mimmik’e tsaye ya zubawa ido. Tamkar dai wani mai nazartar wani abu. Saidai kuma azahirance bawae nazartan wani abun yakeyi ba, shiru da kuma nutsuwar da yayi, alamace dake nuna cewar gangar jikinsa na amsar abunda zuciya da kuma brain d’insa ke aika masa. Ahankali ya janye jikinsa daga gaban classic glass bathrobe d’in, tare da juyawa ya k’arasa gaban sink, hannayen riga da kuma k’afan wandonsa ya d’an nad’e, anutse ya soma gudanar da Alwala, bayan kuma ya gama alwala’nne ya juya Ahankali ya nufi hanyar fita daga cikin toilet d’in. Bud’e k’ofar toilet d’in yayi ya fito, tare kuma da soma takowa ahankali zuwa gareta. Ganinta da yayi a durk’ushe ne kuma yasa shi, d’an tsaida Idanunsa da suke lumshewa akanta, tare dasa hannunsa ahankali ya d’an janye mayafin dake kanta. “Ayshnoor kije kiyi alwala.â€? Ya fad’a cikin wani hot unique voice d’insa, daya sanya tsikar jikinta mimmik’ewa. Duk da cewar kuwa bata kallonsa amma saida taji wani irin nauyinsa ya lullub’eta. Hannunta dake kan mararta ta zare tare da mik’ewa tsaye, ahankali cikin kuma yanayin sanyin daya zame mata sabo ta nufi k’ofar da take tunanin cewa nanne toilet. Daidai takai tsakiyar d’akinne kuma vail d’in dake jikinta ya zame ya fad’i k’asa. Batare kuma da ta ankara da hakan ba, ta cigaba da tafiya harta shige cikin toilet d’in. Kasalallun idanunsa ya lumshe tare dajan wani dogon numfashi, hakan ya faru ne kuma saboda sauk’e idanunsa da yayi akan tsararren shape d’in jikinta, kasancewar d’inkin riga da sket d’innata ya bayyana komai da komai. Wani tunani na daban kuma daya shigo cikin k’wak’walwarsa ne yasashi zama abakin gado, tare da sanya hannayensa ya rufe fuskarsa. Laylerh kuwa koda ta shiga cikin toilet d’in baki ta bud’e tana k’arewa cikin toilet d’in kallo, domin had’uwarsa ya wuce duk yanda take tunani, gudun kuma kada ta b’ata lokaci ne, yasa ta k’arasa gaban sink ta d’auro alwala kamar yadda ya umarceta. Saidai kuma sam batasan meyasa har yanzu bugun zuciyarta ya kasa zama daidai ba. Gaba d’aya amatakin wani irin take kallon komai. Bata kuma tashi sanin cewar vail d’in da ta rufu dashi baya jikinta ba, sai yanzu da ya kammala alwala, shagwab’abb’iyar fuskarta ta d’an kwab’e, sanin babu yanda zatayi ne kuma yasa ta zame d’ankwalin dake kanta ta yafa ajikinta. Ahankali ta bud’e k’ofar bathroom d’in ta fito. Tana fitowa kuwa idanunta suka sauk’a akanshi, saidai kuma ganin ba ita d’in yake kallo ba ne, yasa tayi saurin k’arasawa gefen gadon ta d’auki Hijab d’in da tayi sallah dashi d’azu ta saka ajikinta. Maleek kuwa tun fitowarta daga cikin toilet d’in yana lure da ita, duk da kasancewar idanunsa ba akanta suke ba, amma zuciya da tunaninsa na gareta, shiyasa ko da ace idanunsa basu sauk’a akanta ba, To hakan bawai yana nufin baya kallonta bane, domin duk wani abu daya shafeta da idon zuciya yake kallonsa, kuma kallo bawai Lallai dole saida idanu ba, sometimes ma hankali shine gani. Mik’ewa tsaye yayi tare da juyowa ya fuskanceta, wanda hakan yasa tayi saurin sadda kanta k’asa. Wani irin bugawa kuma zuciyarta ta shiga yi adaidai lokacin da ta ga ya nufo Inda take Wanda har saida hakan ya kasa b’uya, domin zai iya cewa duk taku ae dake dad’a kusanto shi gareta sai yaji sautin bugun zuciyarta. Lokacin daya k’araso kusa da ita d’inne kuma ya tsaya cak, tare da daidaita tsayuwarsa akan wani babban darduma dake gefen gadon, wanda kuma akansa ne Laylerh’n take. Hannunta ya kamo ahankali tare da mayar da ita bayansa. Daidaita tsayuwarsa akan darduman yayi, tare da d’aga hannayensa duka biyu ya tada ik’ama. Ganin hakanne kuma yasa itama ta daidaita tsayuwarta. Tare da tsaida duk wani tunani da kuma feeling d’in dake cikin mind d’inta. Cikin yanayi na nutsuwa yajasu sallah Raka’a biyu, wanda ta d’aukesu tsawon 12 minute, kasancewar akowacce sujjada sai yayi addu’o’i masu tsawo, Kamar dai yanzu da suke sujjadar k’arshe, addu’o’i sosai ya musu, kafun daga bisani ya d’ago kansa yayi sallama. Jin sallamewarsa d’inne kuma yasa itama ta sallame nata sallah’n. Dai dai lokacin kuwa d’an yayyafin ruwan sama da akeyi ya sake k’arfi, Yayinda walk’iya mai hasken gaske ke ci gaba da haske sararin samaniya. Juyowa yayi Ahankali ya fuskanceta, kyakkyawar fuskarta ya tsurawa ido, alokacin daya sanya hannunsa na dama akanta, cikin wata irin sassanyar muryar da bata tab’ajinsa da ita ba, ya soma karanta mata addu’a. Zara zaran eye lashes d’inta da suke d’auke da danshin ruwa ya kalla, kana kuma Ahankali ya dawo da kallonsa ga jajayen lips d’inta, wanda har yanzu suke d’auke da sugar plum, still kuma shining suke. Wani irin nannauyar ajiyar zuciya ya sauk’e, tare da d’an matsowa kusa da ita, saboda feeling d’inta sosai yakeji, ahankali ya sauk’e hannayensa akan nata hannun, wanda suka sha red colour henna. Atake kuwa duk tsikar jikinsu ya zuba, Musamman Laylerh, wanda har hakan yasa ta lumshe Idanunta. “AYSHNOOR!!â€? Ya k’ira sunanta da cool voice nashi, wanda yasa ta kasa amsa masa. Saima wani irin sanyi da taji na k’ara ratsa duk ilahirin jikinta. Hannunta dake cikin nasa ya d’an murza ahankali tare kuma da k’ara matsowa kusa da ita, take kuwa k’amshin turarensa da nata suka gauraye waje d’aya, haka ma bugun zuciya da sautin fitan numfashinsu. Hannunsa dake kan nata ya zame, tare da kama hijab d’in dake jikinta ya zare Ahankali. Fitinannun Idanunsa masu d’auke da zallan sha’awa da kuma matsanancin soyayyarta ya lumshe, adaidai lokacin da ya sauk’e ganinsa, akan beautiful neck d’inta. Wanda asanadin hakan har saida yaji gaba d’aya duk wata jijiya dake jikinsa ta harba. Take kuwa duk wani Feelings d’in da ya jima ajikinsa, tsawon shekaru ya shiga tasowa. Abu d’aya kawai yakeso ayanzun shine yaji Ayshnoor d’in acikin jikinsa, so yake ya d’and’ana d’umi da kuma dad’in fatarta, so yake ya shiga jikin Ayshnoor d’insa, jikin daya jima yana kwad’ayi da kuma fatan samu. Jikin da yayi imani cewa babu wata mace mai irin jikin da zata gamsar dashi. Ayau D’and’ano da kuma dad’in saliva d’inta yake son ta shayar dashi. Hannayensa dake kan nata, ya k’ank’ame tare da sake matsowa kusa da ita sosai, cikin wani irin yanayi mai wuyar fassaruwa ya d’an jawota zuwa gareshi. Tare kuma da matso da fuskarsa gab da nata, sake had’ewar breaths d’insu waje d’aya ne kuma yasa, gaba d’aya wutar sha’awar dake jikinsu motsawa, musamman Laylerh, da takejin bazata tab’a iya jurewa yanayin ba, domin kowani fitar numfashinsa d’aya sauk’a yake akan fuskarta, hakan kuwa ba k’aramin jefata acikin wata duniya na daban yayi ba. Still kuma taushin hannayensa dake gogan nata yasa tsikar jikinta mimmik’ewa. Saboda hakan kuma Batare da ta sani ba har lips d’insa sun d’an bud’e. Wanda kuma hakan alamace dake nuna she’s ready, da karb’an duk wani sak’o dazai tura mata. Wani irin numfashi maitsananin sanyi ta fesar, alokacin da taji sauk’an soft hand d’insa akan wuyanta. Tabbas ayanzu yakai wani mataki da bazae iya jurewa ba, hakan yasa ahankali ya d’aura jajayen lips d’insa akan nata, tare da kamo lips d’inta na k’asa ya bata wani irin hot sucking, daya sa ta narkewa gaba d’aya ajikinsa, ahankali kuma ya soma tura sugar tongue d’insa acikin bakinta. “Yah Allah!!â€? Yafad’a da wata irin muryarsa dake shaking, alokacin da tongue d’insa ya samu shiga cikin bakinta kuwa, wani irin abune yaji yana ratsa Cikin jiki da b’argonsa. Hakan yasa amatuk’ar buk’ace ya soma sucking lips and tongue d’inta. Itama Laylerh da had’ewar bakinsu waje d’aya ya jefata acikin wata duniya ta daban sake shigewa jikinsa tayi, tare da kamo lips d’insa ta soma sucking ahankali. Hakanne kuma yasa shi soma fitar da wani irin breathing dake bayyana mahaukacin feeling d’inta da yakeji. Ak’agauce ya sanya duka hannayensa biyu ya sake shigar da ita jikinsa, dake matsanancin rawa, gaba d’aya d’and’anon saliva d’inta ya rikita masa lissafi, sannan ya kuma jefesa acikin wata duniya ta daban, duniyar feelings d’in da tunda yake aduniya bai tab’a sanin da akwai kalar wannan duniyar ba. Azafafe tunani da hankalinsa ke tafiya, Yayinda yakejin ya rasa duk wani control d’insa. Sosai idanunsa dake alumshe suka kad’a sukayi jajur, babu abunda yakeji da gani ayanzun sai Laylerh’n, yanayin yanda yakejin kansa dama gangar jikinsa ne, yasa shi soma tunanin iya jurewa kaiwa wannan yanayin. Gaba d’aya ya rud’ar da Laylerh, da irin salon kissing d’in da yake mata, musamman yanda yake goga mata lallausan beard d’insa agefen fuskarta, musammman idan gashin beard d’innasa ya gogeta haka takejin kamar zata shid’e. Ahannunta dake kan chest d’insa ta zare ahankali, tare da d’an janye jikinta baya, akaron farko da taji numfashinta na kokarin d’aukewa, ga kuma mararta dake murd’awa, still kuma jin wani abu na fita daga jikinta, yasa ta zare bakinta daga nasa, tare da fad’awa cikin jikinsa, ta sakar masa wani kuka mai kama dana shagwab’a, wanda kuma azahiri bawai kukan shag’wab’a bane, kukane dake bayyana yanda kissing d’in ke shiga jikinta, da kuma matsanancin feeling d’in dake taso mata wanda bata tab’a jin irinsa ba. Idanunsa da sukayi jajur suka kuma k’ank’ance ya bud’e ahankali, tare da fesar da wani Irin numfashi mai kama da growling. Sake matseta ajikinsa yayi sosai, tare da sa bakinsa adaidai saitin kunnenta, sassanyar iskan dake bakinsa ya shiga hurawa zuwa cikin kunnenta. Lokaci d’aya kuma ya tura tongue d’insa cikin kunnen nata, tare da soma wasa dashi. Wani irin numfashi taja alokacin da sanyin iskan baki da kuma tongue d’insa suka soma yawo acikin kunnuwanta. Wani yanayi na musamman da bata tab’a jin irinsa ba taji ayau d’in, yanayin da yake k’ok’arin matar da ita sunanta dama wacece ita gaba d’aya. Maleek kuwa atsananin buk’ace yake da Laylerh’n tasa, hakan yasa ahankali yasanya hannunsa abayanta, tare da soma yin k’asa da zip d’in rigar dake jikinta, kasancewar kuma bata cikin hayyacinta shiyasa ko kad’an batayi yunk’urin dakatar dashi ba. Gaba d’aya ya zuge zip d’in rigar nata, kasancewar kuma anyiwa rigar d’inkin brides ne, yasa Koda tazo saka kayan bata saka bra ba, domin dama ba’a buk’atar hakan, saboda rigar tana da tsarin breastcup mai kyau. Atare suka saki wani irin zazzafan numfashi, alokacin da tafukan hannayensa suka sauk’a akan naked soft skin d’inta. Bata kuma k’ara fi cewa acikin hayyacinta ba saida taji, yanda yake shafa skin d’in bayanta da hannayensa. Yanzu kam kukan shagwab’a ta saka masa da gaske, saboda yanda Taji brain d’inta na juyawa, saboda komai da yake mata ayanzun sabone agareta, Domin babu wani Namiji daya tab’a yi mata hakan. Sam akowani irin yanayi ba zai iya jurewa kukanta, hakan yasashi d’an yunk’urawa tare dasanya hannayensa duka ya d’agota zuwa jikinsa, duk da cewar kuma, kowacce gab’a dake jikinsa ta mutu, haka ya iya daurewa ya mik’e tsaye akan k’afafunsa, Laylerh’n na jikinsa ya nufi kan makeken bed d’insu wanda aka shumfud’awa milk colour bedsheet. Shumfud’eta yayi atsakiyar gadon, tare da kai hannunsa ya rage gaba d’aya hasken wutan dake cikin d’akin, wani yellow blue bedside lamp ya kunna, wanda yanayin haskensa ya k’awata d’akin sosai. Rigar getzner d’in dake jikinsa ya zare, tare da haurowa saman gadon yayi mata rumfa da faffad’an chest d’insa. K’afafunsa ya tank’washe tare kuma dasa Hannunsa ya d’agota zaune, ya zamana suna fuskantar juna. Lafiyayyen kiss ya d’aura mata akan wuyanta, tare da sa hannu lokaci daya yasomayin k’asa da rigar jikinta, still kuma yana sucking wuyanta azafafe. Ahaka har yayi nasarar yin k’asa da rigar jikinta. Sauk’e idanunsa da yayi akan beautiful breast d’nta kuwa kusan daidai yake da d’aukewar numfashinsa, domin bai tab’a tunanin cikar halittan Laylerh’n har yakai haka ba. Laylerh kuwa jin ya raba ta da rigar dake jikinta ne yasa ta lumshe Idanunta, tare da tura yatsun hannunta acikin gashin kansa, sosai hot sucking d’in da yakewa neck d’inta ke shigarta, domin kuwa har ji take kamar numfashinta zai d’auke. Yayinda takejin wani irin abu mai kaman k’aik’ayi na yawo akan light pink nipples d’inta, Daga gefe guda kuwa yawan feeling d’in da Maleek d’in ke jefata yawan ciwon mararta dake k’aruwa, wanda ayanzu harjin marar nata take kaman ya kunbura. Wani irin azababben nishi suka sake atare adaidai lokacin da ya d’agota gaba d’aya zuwa jikinsa. Taushi da kuma naked skins d’insu ne suka had’e waje d’aya, wanda kuma hakan yasa breast d’inta had’ewa da chest d’insa. A haukace yayi tighten hugging d’inta, tare da soma kissing d’in jikinta tako Ina, yana sakin growing. After 5minute kacal gaba d’aya ya rud’asu ya haukata gaba tunaninsa dana Laylerh’n. Ya koma tamkar wani mayunwacin zakin daya jima yana farautar abun harinsa, taushi da laushin skin d’inta sun zautar dashi sun kuma fitar dashi acikin hayyacinsa. Gaba d’aya ko’ina na jikinsa rawa yake, domin kuwa sai ayanzune yasan menene hakikanin feeling, sannan kuma ayanzu ne yasan cewar duk abunda yakeji akan Laylerh’n da ba feeling bane. Domin k’arfin sha’awarta da yakeji ayanzu na neman zautar masa da hankali, had’e kuma da shid’ar dashi. Yakai wani mataki mai wahalar fassaruwa, da burinsa ayanzu kawai shine yajisa acikin jikin Laylerh’n. Hannunsa dake rawa ya d’aura akan saman mararta tare dayin k’asa da sket d’inta, ahankali yasoma yawo da hannunsa akan marar nata. Hawayen da suka cika idanunta ne suka samu daman gangarowa alokacin da taji ya tsaida hannunsa adaidai saitin inda keyi mata ciwo. Ahankali ya cigaba da kissing d’in jikinta, har ya gangaro zuwa kan k’irjinta, da jinsu ya k’ara kunna masa wutar sha’awa. Lips d’insa masu sanyi ya d’aura akan soft breast d’inta Wanda hakan yasa lokaci d’aya numfashinta ya soma seizing, domin wannan ne karon farko agaba d’aya rayuwarta da wani Namiji ya fara tab’a breast d’inta, hakan yasa taji abun na ratsa cikin jikinta sosai, kasancewar kuma anan duk wani logon feelings d’in ta yake ne, yasa gaba d’aya duk ta fice ahayyacinta. Har batasan lokacin daya rabasu da gaba d’aya kayan jikinsu ba. Hannayensa duka biyu yasa ya juyar da ita tare da saka kansa abayanta ya soma yawo da harshensa, atsakiyar gadon bayanta. Sannu ahankali kuma yake sauk’owa zuwa sauran gangar jikinta. Yanayin yanda yake lashe skin d’in ta ne kuma yasa ta lumshe Idanunta tare da soma sakar masa growling na shagwab’a. Alokacin da taji sauk’an kansa akan mararta kuwa wani irin zabura tayi tare da soma yun k’urin mik’ewa, saidai wani irin rik’on fitar hayyaci da yayi mata yasa ta kasa motsawa. Tunaninta da kuma Brain d’inta ne suka tsaya da aiki adaidai lokacin da taji M.Jay d’in nayi mata wani abu na daban, wanda yasa gaba d’aya sassan jikinta suka amsa da karkarwa, numfashinta kuwa wani irin fusga ya somayi alokacin da taji yanda yake k’ok’arin tura tongue d’insa acikin jikinta, kuka maik’arfi da kuma Gaza jurewa ta sakar masa tare da soma kokarin janye jikinta baya, domin abunda taji bata isa misalta shi ba, kwakwalwarta tayi kadan da d’aukan feeling d’in abun. Shikuwa Maleek sam bayajin akwai wani abu daya fi komae, zautar dashi kaman d’umin cikin jikinta da tongue d’in nasa ya jiyo masa, wanda ya je fasa acikin wani irin feeling d’in ta na musamman, saboda haka tuni ma duk wata jijiya dake jikinsa ta mik’e. Sake matsowa jikin Laylerh’n yayi, wanda har hakan yasa komai nasu ya zamana yana manne da juna. Fitinannun idanunsa masu d’auke da tsananin soyayya da kuma sha’awarta ya lumshe. A iya gaba d’aya tsawon rayuwarsa baisan haka Laylerh’n nasa take ba, baisan haka komai najikinta ke da dad’i ba, Tabbas adaidai irin wannan lokacin bai kamata ace komae yazo mind d’insa ba, saidai kuma amma ya zaiyi da tabon da K’addarar su tabar musu? Tayaya zai fara goge abunda ke neman shigowa cikin tunani da k’wak’walwarsa ayanzun? Tayaya zai nesanta kansa da tunanin da ke neman ruguza masa zuciya? Meyasa wannan tunanin zaizo cikin k’wak’walwarsa ayanzu? Meyasa zuciyarsa zata tono masa mikin da yake ta kokarin bunnewa? Bayason tunawa koda kad’anne kuwa, bayason tuna cewar kafun shi K’addara ta had’a masa Ayshnoor d’insa da wani, a d’aki d’aya kuma a gado d’aya, the same kuma matsayin mata da miji. Kafunshi wani daban yaga jikin Ayshnoor d’insa, kafunshi wani ya tab’a taushi da kuma fatar jikinta, sannan ya shiga cikin jikinta ya d’an d’ana abunda shi kad’aine ya kamata ace yau ya d’an d’ana. Labb’ansa ya cije da k’arfi tare da soma girgiza kansa, cikin wani irin azababben kishi da kuma tsanar Najeeb da yakeji acikin ransa ya matsa gefe daga jikin Laylerh’n. Hannayensa duka biyu yasa ya kama kansa, Yayinda yakejin duniyar na juya masa. Haka yakejin komae na dawo masa sabo. Akaron farko kuma daya ji ya tsani k’addarar da ta kawowa Laylerh’n wani daban acikin rayuwarta. Dafe zuciyarsa dake k’una yayi, tare da sake rumtse idanunsa da k’arfi, acikin zuciyarsa yake ambaton sunan ALLAH Don samun sauk’i. Laylerh dake kwance hawaye nabin gefen Idanunta kuwa bayansa dake d’auke da zanen tattoo ta tsurawa idanu, domin ta fahimci cewar rubutu ne akayi da paint na tattoo din. “AYSHNOOR!!!â€? Ta maimaita sunan da aka rubuta d’in acikin zuciyarta. Maida idanunta tayi ta lumshe, domin sam bazata iya jurewa ganin cikakkiyar halittar Yah M.Jay d’in ba, saboda kwarjininsa ya wuce duk yanda take tunani. Ahankali yakejin zuciyarsa na ci gaba dayin rauni, Yayinda wasu ruwa masu kama da ruwan hawaye suka cika idanunsa. Yasani cewar k’addara babu yanda bata zuwarwa bawa, su kuma ahaka tasu k’addarar tazo. Dole kuma ya jurewa hakan, koba Don komai ba, kodan saboda Kaunar da yakeyiwa Ayshnoor d’insa. Lallai Tabbas zai jure, akoyaya Ayshnoor d’in tazo masa, zai kuma yi mu’amala da ita koda ace maza sama da Goma ne suka Santa amatsayinta na y’a mace, asalin Soyayya bawai yana nufin kaso mutum saboda wani abu na jikinsa bane kawae, asalin soyayya tana farawa ne daga cikin jini da zuciya, son mutum dan wani abu nasa ba tabbataccen soyayya bane, domin ba komae ne Idan kana dashi yake tabbata ba, wani abun na gushewa ta har abada, Idan karasa shi kuma rashine na har abada. K’addarar sa dana Ayshnoor tafi k’arfin ya juya mata baya saboda wannan. Tabbas sud’in abu d’aya ne, Fata da kuma muradi d’aya, saboda haka zasu rayu tare akowani irin hali. Juyowa yayi Ahankali ya fuskanceta, tare da k’urawa kyakkyawar fuskarta idanu. Wani irin sabon soyayya da shauk’inta ne yaji na k’ara ratsa cikin jikinsa. Ahankali ya sanya hannayensa duka biyu ya jawota jikinsa. Idanunta dake cike da mayen feelings d’insa ta bud’e ahankali. Tare da sauk’e ganinta akansa. Kallon da ta masa d’inne kuma yasa mararsa amsawa, tafukan hannayensa ya d’aura akan waist d’inta, azafafe ya shiga bata wani sabon kiss d’in daya fi wanda ya bata abaya. Lokaci d’aya yasake zautar dasu, saboda kuma yanda chests d’insu ke had’e awaje d’aya ne, yasa feelings d’in su ke sake k’aruwa. Still akaro na biyu yasake bin duk jikinta da hot kisses, awannan karon ma kasa jurewa sucking d’inta da yakeyi tayi, musamman ayanzu da yake sake nutsar da tongue d’insa cikin jikinta, ji takeyi kamar zai zuge mata gaba d’aya ruwan jiki. Saurin rik’e kansa tayi cikin shaking voice d’inta da kwata kwata ma baya fita sosai tace. “Please......... Yah .... M.Jay don’t ... kill me please.....!â€? Dago kansa da kuma idanunsa wanda sukayi jajur yayi, sam ayanzu baya banbance komai, shiyasa ma bai iya banbance abunda Laylerh’n ta fad’a ba. Daidaita jikinsa dana Laylerh’n yayi, cikin kuma yanayin dake nuna ya kasa iya controlling kansa ya daura bakinsa akan nipples d’inta, tare da tura mata yatsarsa d’aya acikin bakinta, adaidai lokacin daya ke kokarin ratsa cikin jikinta.. *1/4/2021* *5:00 pm* 4/4/21, 6:46 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *note editing* *Chapter 77* Idanunta dake alumshe ne suka firfito waje, lokaci d’aya kuma ta saki wani irin razanannen k’ara, tare da soma kokarin janye jikinta baya. Cikin yanayin dake bayyana mahaukacin feeling d’inta da yakeji ya d’ago da kansa ya kalleta, da jajayen idanunsa, wanda lokaci d’aya suka k’ank’ance. Kansa da yakejin ya masa nauyi ya d’an soma girgizawa, tare dasa hannunsa d’aya ya rik’o waist d’inta, ahankali ya soma motsa labb’an bakinsa, da alama kuma magana yakeson yi amma ya kasa. Saidai jikinsa dake ta b’ari, Yayinda kwantattun gashin jikinsa duk suka mimmk’e. Musamman saboda ayanzu ya kawo wani stage da bazae tab’a iya jurewa ba, domin har wani jin kansa yake akumbure. “Please Ayshnoor please.....â€? Ya fad’a amatuk’ar raunace, da kuma muryarsa wacce bata fita sosai. Kanta tad’an soma girgizawa ahankali, tare da sake janye jikinta baya, tsoro da fargaba takeji sosai, wanda hakan yasa duk jikinta ya d’auki b’ari. Yayinda kirjinta ke dukan uku uku, Tabbas tasan komai dake jikinta ayanzu mallakinsa ne, tana kuma matuk’ar son jinsa ajikinta, domin hakan muradine da ya jima yana rayuwa acikin zuciya da gangar jikinta, saidai tayaya zata iya jurewa abunda bata san ya yake ba? batasan ya zafi da kuma dad’insa yake ba, Tabbas akwai fargaba mai tsanani, duk da tana da confidence d’in cewar Yah M.Jay d’in nata bazae tab’a yin abunda zai cutar da ita ba. Idanunta dake zubar da hawaye ta lumshe ahankali tare da komawa k’asanshi ta kwanta. Ganin hakan da yayi d’inne kuma yasa shi, yi mata rumfa da faffad’an chest d’insa, ahankali kuma ya lumshe idanunsa da yakejin sun ciko da k’walla, bakinsa ya d’aura akan nata cikin yanayin sanyi da kuma mayen sha’awarta dake fusgarsa, ahankali ya tura harshensa acikin bakinta. Wani irin sassanyan nishi ta sauke adaidai lokacin da taji d’umi da kuma dad’in tongue d’insa acikin bakinta. Ahankali tad’an sakar masa jikinta tare da tura hannayenta acikin gashin kansa. Kusan atare suka saki wani irin nishi maik’arfi adaidai lokacin daya sake yunk’urin shiga cikin jikinta. Hannayenta dake cikin tarin sumar kansa ta zare, tare da d’aurasu akan damatsan hannunsa, cikin kuma sabon feeling d’in daya sake jefata aciki, ta k’ara bud’e bakinta, wanda hakan ya bashi daman sake tura mata harshensa acikin bakinta, tare kuma da soma yi mata wani irin salon sucking tongue, d’in da yasa ta kara ficewa acikin hayyacinta. Hannayensa dake kan saman breast d’inta ya janye zuwa kan waist d’inta, tare dayi mata wani irin rik’o irin wanda ke bayyana fitar hayyacinsa, idanunsa ya rumtse da k’arfi alokacin da gaba d’aya jikinsa ya d’auki rawa ne kuma ya soma karanta addu’ar da shikansa yasan ba daidai yakeyi ba, saboda yanda yakejin yana k’ara kusanta kansa da wani irin d’umi mai gigita tunani. Dad’i da kuma sha’awar da tafi k’arfinsa dayaji alokaci guda ne kuma yasashi, sake shigewa cikin jikinta da k’arfi. Daidai lokacin kuwa atare suka saki wani irin k’aran da gaba d’aya cikin d’akin nasu saida ya amsa. Saboda wani irin gigicewa da sukayi, take kuma numfashinsa ya soma wani irin fusga, wanda hakan yasashi yin wani abu kamar maiyin shak’uwa. Itakuwa Laylerh da tasaki karan azaba, sake rik’o hannayensa tayi k’am, tare da rumtse Idanunta da tsananin k’arfi, saboda yanda taji wani irin zafi, radad’i dama ciwo na bin kowani sassa na jikinta har izuwa cikin k’wak’walwarta. Take kuma numfashinta ya soma wani irin seizing, saboda yanda tajisa d’in acikin jikinta yazo mata amatuk’ar bazata. Hakanne kuma yasa taji tsinkewar wasu abu masu kaman jijiyoyi daga cikin jikinta, wanda kuma asanadin zafin da tajine ya sata sakin k’ara. Azauce ya dafe kansa dake wani irin juyawa, tare da sake nutsa jikinsa acikin nata, yana mejin kansa tamkar zai shid’e, domin kowani gaba dake jikinsa rawa yakeyi, Yayinda kuma kowacce jijiya dake jikinsa ke harbawa, k’wak’walwarsa kuwa na d’aukan wasu sak’onnin da bata tab’a sanin akwae su ba aduniya, sak’onnin da suka sashi manta suna da kuma shi kansa gaba d’aya. Wasu irin hawaye masu tsananin zafine suka shiga gangarowa ta gefen idanunsa, alokacin daya gama samun kansa acikin jikinta, adaidai lokacin ne kuma yaji gaba d’aya kunnuwansa sun toshe, saboda wani irin dad’in da yaji, wanda baitab’a sanin akwai makamancinsa aduniya ba, kasancewar kowani jijiya dake jikinsa ayanzu ta gamsu da daddad’an d’umin dake cikin jikin Laylerh’n, Tabbas yaji abunda bai tab’a tunanin zaiji ba, wanda asanadin haka yasashi jin kansa awata duniya ta daban, duniyar dashi kansa baisan a inda hayyacinsa yake ba, duniyar da takashe masa kunnuwa da bakinsa, haka kuma duniyar da ta tsayar da duk wani tunaninsa, ya zama tamkar mayunwacin zaki, ko kuma zautaccen da kwata kwata baya gane komai sai dad’in da yake ciki. Saboda shid’ewan da yayi kuwa bakinsa sam yakasa rufuwa, saidai hawaye kawai dake bin fuskarsa. Sam Maleek ya manta waye shi, da kuma Laylerh’n sa, sabuwar duniyar daya samu kansa aciki ne kawai ke wasa da tunani da kuma kwakwalwarsa, duniyar Ayshnoor d’insa ta musamman, duniyar daya jima yana kwad’ayi da fatan samu, haka kuma jikin daya jima yana muradi, tayaya zai iya misalta wannan yanayin nasa mai kama da suma? tayaya zai iya banbance daidai da rashinsa ayanzu? Tabbas yayi fi cewa ahayyacin da bazai tab’a iya controlling gangar jikinsa ba, domin ayanzu ma baya gane komai saidai sake nutsewa acikin jikinta da yakeyi, yanajin kansa na yawo asararin samaniya. 15minute only Idanunta da sukayi luhu luhu, wanda kuma hawaye ke fitowa daga cikinsu ta lumshe ahankali, adaidai lokacin da taji yanda Yah M.Jay d’in ke cigaba da heaven sex da ita, wanda zuwa yanzu ko hannunta bata iya motsawa, domin jikinta ya zama very weak sosai, kuka kuwa ayanzu ko tayi muryar nata bazai tab’a fitowa ba, saboda komai najikinta ya riga da yayi rauni, har jin kanta takeyi na wani irin juyawa, Yayinda kowani jijiya dake cikin kanta ke sarawa. Ahaka tun tana jiyo groaning d’insa na tashi sama sama, har dai ya zamana idanuwanta sun rufe ruf bata iya jiyo sautin komai, sai yanda yake sake shigewa jikinta yana enjoying mood d’in, har numfashinsa na fusga, gaba d’aya abu yakeyi mata na irin wanda kwata kwata baya cikin hayyaci da nutsuwarsa. *After 45minutes 1:30 am* Wani irin gumi ne ke yanko masa, duk da kuwa cewar gaba d’aya ilahirin jikinsa rawa yake, rawa kuma irin na wanda ke nuna cewar yanajin matsanancin sanyi. Kansa dake matuk’ar sarawa ya rik’e tare da rumtse idanunsa, domin haka yakejin tamkar ana hura masa duk wata jijiya dake cikin kannasa, Yayinda take kuma yaji wani zazzab’i mai zafi ya sauk’ar masa. Idanunsa da sukayi luhu luhu suke kuma wani irin jujjuyawa ya bud’e tare da sauk’e ganinsa akan Laylerh, da har yanzu ke kwance, idanunta alumshe still kuma har yanzu hawaye basu daina bin gefen fuskarta ba. Ahankali yad’an soma yawo da idanunsa ajikinta duk da cewar ayanzun bawai yana wani gani sosai bane, saboda har yanzu baigama dawowa hayyacinsa ba. Sauk’e idanunsa da yayi akan mararta da kuma jikin milk colour bedsheet d’insu da yayi ne, yasashi zaro idanun nasa amatuk’ar rud’e, yasa y’ar yatsarsa ya tab’a abunda yake gani ajikin bedsheet d’in. K’urawa yatsar ido yayi saboda yanason fahimtar, gane cewar abun dake jikin yatsar tasa jini ne yasashi rumtse idanunsa da k’arfi, lokaci d’aya kuma wasu irin hawaye masu tsananin zafi suka silalo daga cikin idanun nasa. Take kuma yaji wani irin matsanancin tausayin Ayshnoor d’innasa, da kuma mahaukaciyar soyayyarta na d’ibansa. Ahankali ya zube guiwowinsa akan gadon, tare da d’an mirginawa ya shige cikin jikinta, hugging d’inta yayi sosai, tare dasa hannunsa d’aya asaman mararta ya soma shafawa slowly. Again kuma bakinsa dake rawa ya d’aura adaidai saitin kunnenta. *”I LOVE YOU Ayshnoor! I Love You So Much!! and I’m very sorry Ayshnoor i don’t mean to hurt you, but please I’m so sorry...â€? Ya fad’i haka cikin wata irin muryarsa da tayi sanyi sosai, kana take kuma fidda matsanancin rauninsa da kuma tausayin Laylerh’n, domin koda wasa bai tab’a tunanin zai iya aikatawa Laylerh’n hakan ba. Hannunsa d’aya yasa acikin nata, tare da rik’eta gam, cikin kuma wani sabon yanayin da yakejin kansa aciki ya sauk’e mata wani irin hot kiss akan forehead d’inta, lokaci d’aya kuma saiga hawaye masu zafi nabin gefen fuskarsa. Hannunta dake cikin nasa ya rik’e da kyau, tare da had’e goshinsu waje d’aya ya lumshe idanunsa. Baisan tayaya zai misalta irin yanayin da yakejin kansa aciki ba, domin yanayi ne da tunda yake aduniya bai tab’a jin kwatan kwacin irinsa ba, yau Ayshnoor d’insa ta shayar dashi abunda bazae tab’a mantawa ba, ta bashi kyautan virgin d’inta abu mafi tsada dake cikin rayuwar ko wacce y’a mace, sannan kuma abu mafi daraja da ba kowa ne ke samu ba. Lallausan sajen dake kwance akan fuskarsa, ya d’an shiga goga mata akan gefen fuskarta. Cikin wata kasalalliyar murya yace. “I can’t pay you back Ayshnoor, kece mace tafarko acikin rayuwar Maleek, sannan kece mace ta farko da Maleek ya fara sani, kece kuma macen da kika fara bawa Maleek kyautan virgin , you take care of your self for me, for a while, thank you so much Ayshnoor, I can’t live without you!!!â€? Ya k’are maganar cikin muryarsa da tayi rauni sosai, tare da sake hugging Laylerh’n acikin jikinsa. Ahankali yasanya tafukan hannayensa akan naked skin d’inta yana shafawa, wani irin sonta yakeji na ratsa kowani b’argo da jijiyar jikinsa. Yayinda daga gefe guda kuwa yakejin yanda zuciyarta ke bugawa, duk da kuwa cewar numfashinta baya fita da kyau sosai. Had’e fuskarsu yayi awaje d’aya, tare da zaro harshensa ya tura acikin bakinta, ahankali kuma ya soma yawo da harshen nasa yana sucking d’in bakinta. Daddad’an d’umin saliva d’insa dake yawo acikin bakinta ne, yasa ta jan wani irin dogon numfashi, lokaci d’aya kuma ta soma kokarin bud’e idanunta, da suka b’ata sawon mintunoni akulle, duk da cewar bawai suma tayi ba, amma bata cikin hayyacinta sosai, domin dare d’aya kawai har ta rame. Kyakkyawar fuskarta dake dauke da hawaye ya zubawa idanunsa masu sanyi, harta gama ware nata idanun. Akan fuskarsa ta sauk’e ganinta, duk da cewar kuma dishi dishi take gani amma hakan baisa ta janye idanunta daga garesa ba, Yayinda takejin zafin d’umin jikinsa na shiga cikin nata jikin. “AYSHNOOR!!!â€? yak’ira sunanta cikin sanyin murya tare da d’agota ya sake mannata da jikinsa. Idanunta tad’an lumshe ahankali, tare dajan wani dogon numfashi, labb’an bakinta dake d’auke da danshin saliva d’insa ta d’an motsa Ahankali, da alamu magana takeson yi amma ta kasa. Ganin hakan da yayi ne kuma yasashi sanya tafin hannunsa ahankali ya shafi gefen innocent face d’inta. Ahankali cikin kuma yin k’asa da murya yace. “I’m sorry, forgive me please I’m very sorry Wife! kinajin zafi sosai ko? Boo d’inki baida kirki ko? sorry kinji I promise you Yah M.jay bazai sake hurting naki haka ba!!!â€? Ya k’are maganan yana me saka d’aya daga cikin yatsun hannunta na dama acikin bakinsa, wanda kuma hakan yakeyi mata tun tana k’arama, idan ya fahimci cewa tana cikin halin taimako. Sassanyun Idanunta ta lumshe,alokacin da taji yanda yake sucking finger d’inta, lokaci d’aya kuma taji wani irin matsanancin sonsa na k’aruwa acikin zuciyarta, sam ko kad’an dangane da abunda yayi mata d’in, batajin wani ciwo acikin zuciyarta, hasalima wani irin sanyi takeji, ba kuma tajin akan wannan zata iyayin fushi dashi, saboda shid’in gaba d’aya rayuwarta ne, da soyayyarsa kad’ai take samun nutsuwa acikin zuciyarta. “Yah M.jay please zansha ruwa..â€? tafad’i hakan cikin wata kasalalliyar muryarta, dako fita sosai batayi. Jin tace zata sha ruwa ne, yasa shi d’an lumshe idanunsa, tare da zare hannunta dake cikin bakinsa, new towel d’in dake gefen gadon ya d’aura akan waist d’insa, tare dajan blanket ya rufe mata rabin jikinta, ahankali ya sauk’o daga kan gadon, kaitsaye wajen fridge ya nufa, koda ya bud’e fridge d’in, cikinsa cike yake da kayan drinks da kuma bottle water, bottle water mai d’an sanyi ya d’auko, tare da dawowa anutse ya zauna abakin gadon, hannunsa yasa ya jawota jikinsa tare da bud’e murfin bottle water d’in ya sa mata abakinta. Sosai tasha ruwan har kusan fiye da rabin goran, ganin hakanne kuma yasashi janye goran daga bakinta, ahankali yasa hannu ya shafa long hair dinta, da ya watse akan kafad’unta. Itakuwa Laylerh’n ganin jini a bedsheet dinsu ne yasa ta, d’ago maraitattun Idanunta dake cike da hawaye ta kalleshi, saidai kuma wani irin kallo da taga yanayi mata ne yasa tayi saurin sadda kanta k’asa, domin abune da ke abayyane cewa bazata iya jurewa kallon cikin idanunsa dake matuk’ar rikitata ba. Shikuwa Maleek ganin yanda duk jikinta yayi weak ne, yasashi gane cewar zafi takeji sosai, maybe ma ko yaji mata ciwo, hannunsa yasa ya jawota jikinsa sosai, tare da lumshe idanunsa, saboda Allah Ma yasani shi baisan ta inane zai fara ba, baisan me akeyiwa mace idan anyi disvirgin d’inta ba. Wayarsa k’irar iphone12promax dake kan bedside ya d’auko, kaitsaye google ya shiga yayi searching, cikin sa’a kuwa yaga abun da yakeson gani. Hannunsa yasa ajikinta daya d’au zafi sosai, duk da cewar kuma shid’inma akwai zazzab’i sosai ajikinsa amma baidamu da kansa ba, saboda yasan cewa shi mai iya jure kowani irin ciwo ne. Kwantar da ita akan pillow yayi, tare da mik’ewa tsaye kaitsaye ya wuce toilet. Warm water ba kuma maitsananin zafi sosai ba ya had’a acikin babban bathtub, tare da zuba wani turaren wanka wanda ke jere kala kala agaban wani mirror glass, dake cikin toilet d’in. Bayan ya kammala komae ne kuma ya bud’e k’ofar toilet d’in ya fito, direct gaban gadon nasu ya nufo, ahankali yasa hannayensa duka biyu ya d’agota zuwa jikinsa, haka ya nufi cikin toilet d’in yana d’auke da ita ak’irjinsa. Wani wahalallen k’ara ta saka masa alokacin daya ajiye ta acikin warm water’n, tare dasa hakwaranta ta cije labb’anta, saboda wani irin zafi da kuma rad’ad’i da taji suna ratsa ta. Ganin tana k’ok’arin fitowa daga cikin bathtub d’inne kuma, yasa shi rik’e shoulder d’inta da kyau, murya atausashe yace. “Please kiyi hakuri kinji, idan baki tsaya ba, zaki ci gaba dajin zafi sosai, banason kisake jin zafi kuma har abada.â€? Yanayin yanda ya k’are maganar yana d’an danne jajayen lips d’insa ne, yasa ta tsura masa ido batako k’yaftawa, domin aduniya bata tab’a sanin cewa kyawunsa ya zarce tunaninta ba, sai ayau da taga yana magana, babban abunda yafi komai daukar hankali agaresa kuwa, shine yanda yake motsa red lips d’insa. Wani irin zufa ne ya shiga keto mata alokacin da d’umin ruwan ya gama ratsa cikin jikinta, still kuma har yanzu yana rik’e da ita. Almost 12minutes yasa hannunsa acikin ruwan, jin da yayi kuma ruwan ya salance ne yasashi sake zuba mata wani ruwan, saidai ayanzu kam kukan shagwab’a ta saka masa, tare da soma yi masa turjiya, bisa dole haka ya k’yaleta tare da komawa gefe ya zare towel d’in dake jikinsa, kana ya sakarwa kansa shower. Da sauri ta rumtse idanunta saboda bazata iya kallonsa ahaka ba. Shikuwa Maleek duk abunda yakeyi dauriya ne kawai, tare kuma da jurewa zazzab’i da kuma ciwon marar dake damunsa, bayan ya kammala wankan nasa ne kuma ya zura wata farar bathrobe ajikinsa, tare da juyowa ya fuskanci Laylerh’n. Ahankali yakamo hannunta ya mik’ar da ita tsaye, wanda hakan yasa cikin sauri tasa hannu ta kare breast da kuma nipples d’inta wanda sukayi ja, fito da ita daga cikin bathtub d’in yayi, ganin kuma yanda take layi kaman zata fad’i ne yasa shi, d’aga ta ya kaita bakin shower. Shida kansa ya taimaka mata tayi wanka. Tare da d’aukan wani mini towel ya d’aura mata ajikinta. Still kuma d’aukanta ya sakeyi ahannu suka fito daga cikin toilet d’in, akan gado ya zaunar da ita, tare da d’aukan wani towel ya shiga goge mata ruwan dake kanta, bayan ya gama goge mata ruwan ne, ahankali ya zauna akusa da ita tare dasa hannayensa duka biyu ya dafe kansa dake ciwo. Almost 5mn kafun ya d’ago kansa ahankali ya kalli Laylerh’n, Idanunta dake ta lumshewa ya kuma kallo, ahankali yasa bayan hannunsa ya tab’a wuyanta dan har yanzu akwai zafin zazzab’i sosai ajikinta. “Ayshnoor!!â€? Ya k’ira sunanta asanyaye. Ahankali ta bud’e idanunta ta kalleshi, tare kuma da d’an shagwab’e fuska. Kyawawan idanunsa shima ya zuba mata, cikin yanayinsa na asalin Maleek da baisaba magana ba yace. “Tell me what’s wrong with you, kinajin ciwo sosai ne?â€? “I’m feeling hungry!â€? tafad’a asanyaye tare da sanya hannu ta shafa lafaffen cikinta dake kukan yunwa, saboda duk abunda ke cikinsa Maleek d’in ya kwashe. Hannunsa yasa yad’an dafe kansa, saboda gaba d’aya yama manta da cewar Fou’ad ya ajiye masa leda a falon k’asa. “I’m sorry bari na baki abinci.â€? Ya fad’a yana me mik’ewa tsaye, cikin sauri ya fice daga cikin d’akin. Jin fitansa daga cikin d’akinne kuma yasa ta maida idanunta ta lumshe, saboda zuwa yanzu wani irin bacci ne ke fusgarta, saidai kuma yunwa da zafin zazzab’in dake jikinta na neman hanata sukuni. Aba’angaren Maleek kuwa yana fita daga d’akin, kaitsaye falon k’asa ya sauk’o, ledodin da Fou’ad ya basa gaba d’aya ya kwaso tare kuma da dawowa saman. Ledodin dake hannunsa ya ajiye akan sofa, tare dasa hannayensa Ahankali ya jawo Laylerh’n jikinsa, acikin jikinsa ya zaunar da ita, tare da bud’e duka ledodin da suke cike da kayan ciye ciye, wani foilpaper’n da cikinsa ke d’auke da chicken and soup ya bud’e, tare da d’aukan naman ya kai bakinta, ahankali kuma cikin yanayin bacci da kasala, tad’an bud’e bakinta ya saka mata naman, haka ta dinga d’an taunashi ahankali harta cinye ya k’ara mata wani. Feeding d’inta yayi almost 10mn tace ta k’oshi da naman, duk da cewar bata ci wani mai yawa ba. Hollandia milk d’in daya fara sha ya soma bata, nan ma bata wani sha mai yawa ba tajanye kanta, wajen juyar da kannata ne kuma ta buge hannunsa, kusan rabin hollandia milk d’in haka ya kware acikin k’irjinta. Towel d’in dake jikin nata ya zame ahankali, tare da tura kansa jikinta, ya soma lasan duk inda milk d’in ya tab’a, Yanayin yanda taji harshensa na yawo ajikinta ne kuma yasa ta narkewa, tare da lumshe idanunta, duk wani sak’o da harshensa zai tura mata kuwa enjoying d’insa take. Tana ajikinsa haka kuwa wani bacci mai nauyi ya d’auketa. Lucky eyes d’insa ya lumshe a lokacin da yaji yanda, numfashinta ke sauk’a akan saman mararsa, cikin yanayin kasala da kuma sabon feeling d’in daya saukar masa, ya matsar da kayayyakin abincin gefe, tare da d’aukanta cad’ak ya kwantar da ita agefe. Bayan kuma ya sanja Bedsheet d’insu da yayi staining ne, ya d’aukota ya dawo da ita kan gadon. Rage hasken dake cikin d’akin yayi, tare da hayewa saman gadon, bayan ya zare bathrobe d’in dake jikinsa, ne kuma ya zare towel d’in dake jikin Laylerh’n, Ahankali ya jawota jikinsa yayi hugging nata, tare da rufa musu wani lallausan blanket. Lafaffen cikinta da kuma kasan mararta yake shafawa ahankali, wanda jin hakan yasa ta sake shigewa jikinsa sosai. Shikuwa idanunsa ya lumshe yana mejin wasu abubuwa na yawo acikin tunaninsa, Yayinda akaron farko yau gashi kwance da Laylerh ad’aki d’aya, gado d’aya, kuma acikin jikin juna matsayin ma’aurata, sun riga da sun zama abu d’aya. Tabbas buri da kuma muradin zuciyoyinsu ya tabbata. *4:30 pm* 4/5/21, 9:52 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *note editing* *Chapter 78* Idanunta dake alumshe ne suka firfito waje, lokaci d’aya kuma ta saki wani irin razanannen k’ara, tare da soma kokarin janye jikinta baya. Cikin yanayin dake bayyana mahaukacin feeling d’inta da yakeji ya d’ago da kansa ya kalleta, da jajayen idanunsa, wanda lokaci d’aya suka k’ank’ance. Kansa da yakejin ya masa nauyi ya d’an soma girgizawa, tare dasa hannunsa d’aya ya rik’o waist d’inta, ahankali ya soma motsa labb’an bakinsa, da alama kuma magana yakeson yi amma ya kasa. Saidai jikinsa dake ta b’ari, Yayinda kwantattun gashin jikinsa duk suka mimmk’e. Musamman saboda ayanzu ya kawo wani stage da bazae tab’a iya jurewa ba, domin har wani jin kansa yake akumbure. “Please Ayshnoor please.....â€? Ya fad’a amatuk’ar raunace, da kuma muryarsa wacce bata fita sosai. Kanta tad’an soma girgizawa ahankali, tare da sake janye jikinta baya, tsoro da fargaba takeji sosai, wanda hakan yasa duk jikinta ya d’auki b’ari. Yayinda kirjinta ke dukan uku uku, Tabbas tasan komai dake jikinta ayanzu mallakinsa ne, tana kuma matuk’ar son jinsa ajikinta, domin hakan muradine da ya jima yana rayuwa acikin zuciya da gangar jikinta, saidai tayaya zata iya jurewa abunda bata san ya yake ba? batasan ya zafi da kuma dad’insa yake ba, Tabbas akwai fargaba mai tsanani, duk da tana da confidence d’in cewar Yah M.Jay d’in nata bazae tab’a yin abunda zai cutar da ita ba. Idanunta dake zubar da hawaye ta lumshe ahankali tare da komawa k’asanshi ta kwanta. Ganin hakan da yayi d’inne kuma yasa shi, yi mata rumfa da faffad’an chest d’insa, ahankali kuma ya lumshe idanunsa da yakejin sun ciko da k’walla, bakinsa ya d’aura akan nata cikin yanayin sanyi da kuma mayen sha’awarta dake fusgarsa, ahankali ya tura harshensa acikin bakinta. Wani irin sassanyan nishi ta sauke adaidai lokacin da taji d’umi da kuma dad’in tongue d’insa acikin bakinta. Ahankali tad’an sakar masa jikinta tare da tura hannayenta acikin gashin kansa. Kusan atare suka saki wani irin nishi maik’arfi adaidai lokacin daya sake yunk’urin shiga cikin jikinta. Hannayenta dake cikin tarin sumar kansa ta zare, tare da d’aurasu akan damatsan hannunsa, cikin kuma sabon feeling d’in daya sake jefata aciki, ta k’ara bud’e bakinta, wanda hakan ya bashi daman sake tura mata harshensa acikin bakinta, tare kuma da soma yi mata wani irin salon sucking tongue, d’in da yasa ta kara ficewa acikin hayyacinta. Hannayensa dake kan saman breast d’inta ya janye zuwa kan waist d’inta, tare dayi mata wani irin rik’o irin wanda ke bayyana fitar hayyacinsa, idanunsa ya rumtse da k’arfi alokacin da gaba d’aya jikinsa ya d’auki rawa ne kuma ya soma karanta addu’ar da shikansa yasan ba daidai yakeyi ba, saboda yanda yakejin yana k’ara kusanta kansa da wani irin d’umi mai gigita tunani. Dad’i da kuma sha’awar da tafi k’arfinsa dayaji alokaci guda ne kuma yasashi, sake shigewa cikin jikinta da k’arfi. Daidai lokacin kuwa atare suka saki wani irin k’aran da gaba d’aya cikin d’akin nasu saida ya amsa. Saboda wani irin gigicewa da sukayi, take kuma numfashinsa ya soma wani irin fusga, wanda hakan yasashi yin wani abu kamar maiyin shak’uwa. Itakuwa Laylerh da tasaki karan azaba, sake rik’o hannayensa tayi k’am, tare da rumtse Idanunta da tsananin k’arfi, saboda yanda taji wani irin zafi, radad’i dama ciwo na bin kowani sassa na jikinta har izuwa cikin k’wak’walwarta. Take kuma numfashinta ya soma wani irin seizing, saboda yanda tajisa d’in acikin jikinta yazo mata amatuk’ar bazata. Hakanne kuma yasa taji tsinkewar wasu abu masu kaman jijiyoyi daga cikin jikinta, wanda kuma asanadin zafin da tajine ya sata sakin k’ara. Azauce ya dafe kansa dake wani irin juyawa, tare da sake nutsa jikinsa acikin nata, yana mejin kansa tamkar zai shid’e, domin kowani gaba dake jikinsa rawa yakeyi, Yayinda kuma kowacce jijiya dake jikinsa ke harbawa, k’wak’walwarsa kuwa na d’aukan wasu sak’onnin da bata tab’a sanin akwae su ba aduniya, sak’onnin da suka sashi manta suna da kuma shi kansa gaba d’aya. Wasu irin hawaye masu tsananin zafine suka shiga gangarowa ta gefen idanunsa, alokacin daya gama samun kansa acikin jikinta, adaidai lokacin ne kuma yaji gaba d’aya kunnuwansa sun toshe, saboda wani irin dad’in da yaji, wanda baitab’a sanin akwai makamancinsa aduniya ba, kasancewar kowani jijiya dake jikinsa ayanzu ta gamsu da daddad’an d’umin dake cikin jikin Laylerh’n, Tabbas yaji abunda bai tab’a tunanin zaiji ba, wanda asanadin haka yasashi jin kansa awata duniya ta daban, duniyar dashi kansa baisan a inda hayyacinsa yake ba, duniyar da takashe masa kunnuwa da bakinsa, haka kuma duniyar da ta tsayar da duk wani tunaninsa, ya zama tamkar mayunwacin zaki, ko kuma zautaccen da kwata kwata baya gane komai sai dad’in da yake ciki. Saboda shid’ewan da yayi kuwa bakinsa sam yakasa rufuwa, saidai hawaye kawai dake bin fuskarsa. Sam Maleek ya manta waye shi, da kuma Laylerh’n sa, sabuwar duniyar daya samu kansa aciki ne kawai ke wasa da tunani da kuma kwakwalwarsa, duniyar Ayshnoor d’insa ta musamman, duniyar daya jima yana kwad’ayi da fatan samu, haka kuma jikin daya jima yana muradi, tayaya zai iya misalta wannan yanayin nasa mai kama da suma? tayaya zai iya banbance daidai da rashinsa ayanzu? Tabbas yayi fi cewa ahayyacin da bazai tab’a iya controlling gangar jikinsa ba, domin ayanzu ma baya gane komai saidai sake nutsewa acikin jikinta da yakeyi, yanajin kansa na yawo asararin samaniya. 15minute only Idanunta da sukayi luhu luhu, wanda kuma hawaye ke fitowa daga cikinsu ta lumshe ahankali, adaidai lokacin da taji yanda Yah M.Jay d’in ke cigaba da heaven sex da ita, wanda zuwa yanzu ko hannunta bata iya motsawa, domin jikinta ya zama very weak sosai, kuka kuwa ayanzu ko tayi muryar nata bazai tab’a fitowa ba, saboda komai najikinta ya riga da yayi rauni, har jin kanta takeyi na wani irin juyawa, Yayinda kowani jijiya dake cikin kanta ke sarawa. Ahaka tun tana jiyo groaning d’insa na tashi sama sama, har dai ya zamana idanuwanta sun rufe ruf bata iya jiyo sautin komai, sai yanda yake sake shigewa jikinta yana enjoying mood d’in, har numfashinsa na fusga, gaba d’aya abu yakeyi mata na irin wanda kwata kwata baya cikin hayyaci da nutsuwarsa. *After 45minutes 1:30 am* Wani irin gumi ne ke yanko masa, duk da kuwa cewar gaba d’aya ilahirin jikinsa rawa yake, rawa kuma irin na wanda ke nuna cewar yanajin matsanancin sanyi. Kansa dake matuk’ar sarawa ya rik’e tare da rumtse idanunsa, domin haka yakejin tamkar ana hura masa duk wata jijiya dake cikin kannasa, Yayinda take kuma yaji wani zazzab’i mai zafi ya sauk’ar masa. Idanunsa da sukayi luhu luhu suke kuma wani irin jujjuyawa ya bud’e tare da sauk’e ganinsa akan Laylerh, da har yanzu ke kwance, idanunta alumshe still kuma har yanzu hawaye basu daina bin gefen fuskarta ba. Ahankali yad’an soma yawo da idanunsa ajikinta duk da cewar ayanzun bawai yana wani gani sosai bane, saboda har yanzu baigama dawowa hayyacinsa ba. Sauk’e idanunsa da yayi akan mararta da kuma jikin milk colour bedsheet d’insu da yayi ne, yasashi zaro idanun nasa amatuk’ar rud’e, yasa y’ar yatsarsa ya tab’a abunda yake gani ajikin bedsheet d’in. K’urawa yatsar ido yayi saboda yanason fahimtar, gane cewar abun dake jikin yatsar tasa jini ne yasashi rumtse idanunsa da k’arfi, lokaci d’aya kuma wasu irin hawaye masu tsananin zafi suka silalo daga cikin idanun nasa. Take kuma yaji wani irin matsanancin tausayin Ayshnoor d’innasa, da kuma mahaukaciyar soyayyarta na d’ibansa. Ahankali ya zube guiwowinsa akan gadon, tare da d’an mirginawa ya shige cikin jikinta, hugging d’inta yayi sosai, tare dasa hannunsa d’aya asaman mararta ya soma shafawa slowly. Again kuma bakinsa dake rawa ya d’aura adaidai saitin kunnenta. *”I LOVE YOU Ayshnoor! I Love You So Much!! and I’m very sorry Ayshnoor i don’t mean to hurt you, but please I’m so sorry...â€? Ya fad’i haka cikin wata irin muryarsa da tayi sanyi sosai, kana take kuma fidda matsanancin rauninsa da kuma tausayin Laylerh’n, domin koda wasa bai tab’a tunanin zai iya aikatawa Laylerh’n hakan ba. Hannunsa d’aya yasa acikin nata, tare da rik’eta gam, cikin kuma wani sabon yanayin da yakejin kansa aciki ya sauk’e mata wani irin hot kiss akan forehead d’inta, lokaci d’aya kuma saiga hawaye masu zafi nabin gefen fuskarsa. Hannunta dake cikin nasa ya rik’e da kyau, tare da had’e goshinsu waje d’aya ya lumshe idanunsa. Baisan tayaya zai misalta irin yanayin da yakejin kansa aciki ba, domin yanayi ne da tunda yake aduniya bai tab’a jin kwatan kwacin irinsa ba, yau Ayshnoor d’insa ta shayar dashi abunda bazae tab’a mantawa ba, ta bashi kyautan virgin d’inta abu mafi tsada dake cikin rayuwar ko wacce y’a mace, sannan kuma abu mafi daraja da ba kowa ne ke samu ba. Lallausan sajen dake kwance akan fuskarsa, ya d’an shiga goga mata akan gefen fuskarta. Cikin wata kasalalliyar murya yace. “I can’t pay you back Ayshnoor, kece mace tafarko acikin rayuwar Maleek, sannan kece mace ta farko da Maleek ya fara sani, kece kuma macen da kika fara bawa Maleek kyautan virgin , you take care of your self for me, for a while, thank you so much Ayshnoor, I can’t live without you!!!â€? Ya k’are maganar cikin muryarsa da tayi rauni sosai, tare da sake hugging Laylerh’n acikin jikinsa. Ahankali yasanya tafukan hannayensa akan naked skin d’inta yana shafawa, wani irin sonta yakeji na ratsa kowani b’argo da jijiyar jikinsa. Yayinda daga gefe guda kuwa yakejin yanda zuciyarta ke bugawa, duk da kuwa cewar numfashinta baya fita da kyau sosai. Had’e fuskarsu yayi awaje d’aya, tare da zaro harshensa ya tura acikin bakinta, ahankali kuma ya soma yawo da harshen nasa yana sucking d’in bakinta. Daddad’an d’umin saliva d’insa dake yawo acikin bakinta ne, yasa ta jan wani irin dogon numfashi, lokaci d’aya kuma ta soma kokarin bud’e idanunta, da suka b’ata sawon mintunoni akulle, duk da cewar bawai suma tayi ba, amma bata cikin hayyacinta sosai, domin dare d’aya kawai har ta rame. Kyakkyawar fuskarta dake dauke da hawaye ya zubawa idanunsa masu sanyi, harta gama ware nata idanun. Akan fuskarsa ta sauk’e ganinta, duk da cewar kuma dishi dishi take gani amma hakan baisa ta janye idanunta daga garesa ba, Yayinda takejin zafin d’umin jikinsa na shiga cikin nata jikin. “AYSHNOOR!!!â€? yak’ira sunanta cikin sanyin murya tare da d’agota ya sake mannata da jikinsa. Idanunta tad’an lumshe ahankali, tare dajan wani dogon numfashi, labb’an bakinta dake d’auke da danshin saliva d’insa ta d’an motsa Ahankali, da alamu magana takeson yi amma ta kasa. Ganin hakan da yayi ne kuma yasashi sanya tafin hannunsa ahankali ya shafi gefen innocent face d’inta. Ahankali cikin kuma yin k’asa da murya yace. “I’m sorry, forgive me please I’m very sorry Wife! kinajin zafi sosai ko? Boo d’inki baida kirki ko? sorry kinji I promise you Yah M.jay bazai sake hurting naki haka ba!!!â€? Ya k’are maganan yana me saka d’aya daga cikin yatsun hannunta na dama acikin bakinsa, wanda kuma hakan yakeyi mata tun tana k’arama, idan ya fahimci cewa tana cikin halin taimako. Sassanyun Idanunta ta lumshe,alokacin da taji yanda yake sucking finger d’inta, lokaci d’aya kuma taji wani irin matsanancin sonsa na k’aruwa acikin zuciyarta, sam ko kad’an dangane da abunda yayi mata d’in, batajin wani ciwo acikin zuciyarta, hasalima wani irin sanyi takeji, ba kuma tajin akan wannan zata iyayin fushi dashi, saboda shid’in gaba d’aya rayuwarta ne, da soyayyarsa kad’ai take samun nutsuwa acikin zuciyarta. “Yah M.jay please zansha ruwa..â€? tafad’i hakan cikin wata kasalalliyar muryarta, dako fita sosai batayi. Jin tace zata sha ruwa ne, yasa shi d’an lumshe idanunsa, tare da zare hannunta dake cikin bakinsa, new towel d’in dake gefen gadon ya d’aura akan waist d’insa, tare dajan blanket ya rufe mata rabin jikinta, ahankali ya sauk’o daga kan gadon, kaitsaye wajen fridge ya nufa, koda ya bud’e fridge d’in, cikinsa cike yake da kayan drinks da kuma bottle water, bottle water mai d’an sanyi ya d’auko, tare da dawowa anutse ya zauna abakin gadon, hannunsa yasa ya jawota jikinsa tare da bud’e murfin bottle water d’in ya sa mata abakinta. Sosai tasha ruwan har kusan fiye da rabin goran, ganin hakanne kuma yasashi janye goran daga bakinta, ahankali yasa hannu ya shafa long hair dinta, da ya watse akan kafad’unta. Itakuwa Laylerh’n ganin jini a bedsheet dinsu ne yasa ta, d’ago maraitattun Idanunta dake cike da hawaye ta kalleshi, saidai kuma wani irin kallo da taga yanayi mata ne yasa tayi saurin sadda kanta k’asa, domin abune da ke abayyane cewa bazata iya jurewa kallon cikin idanunsa dake matuk’ar rikitata ba. Shikuwa Maleek ganin yanda duk jikinta yayi weak ne, yasashi gane cewar zafi takeji sosai, maybe ma ko yaji mata ciwo, hannunsa yasa ya jawota jikinsa sosai, tare da lumshe idanunsa, saboda Allah Ma yasani shi baisan ta inane zai fara ba, baisan me akeyiwa mace idan anyi disvirgin d’inta ba. Wayarsa k’irar iphone12promax dake kan bedside ya d’auko, kaitsaye google ya shiga yayi searching, cikin sa’a kuwa yaga abun da yakeson gani. Hannunsa yasa ajikinta daya d’au zafi sosai, duk da cewar kuma shid’inma akwai zazzab’i sosai ajikinsa amma baidamu da kansa ba, saboda yasan cewa shi mai iya jure kowani irin ciwo ne. Kwantar da ita akan pillow yayi, tare da mik’ewa tsaye kaitsaye ya wuce toilet. Warm water ba kuma maitsananin zafi sosai ba ya had’a acikin babban bathtub, tare da zuba wani turaren wanka wanda ke jere kala kala agaban wani mirror glass, dake cikin toilet d’in. Bayan ya kammala komae ne kuma ya bud’e k’ofar toilet d’in ya fito, direct gaban gadon nasu ya nufo, ahankali yasa hannayensa duka biyu ya d’agota zuwa jikinsa, haka ya nufi cikin toilet d’in yana d’auke da ita ak’irjinsa. Wani wahalallen k’ara ta saka masa alokacin daya ajiye ta acikin warm water’n, tare dasa hakwaranta ta cije labb’anta, saboda wani irin zafi da kuma rad’ad’i da taji suna ratsa ta. Ganin tana k’ok’arin fitowa daga cikin bathtub d’inne kuma, yasa shi rik’e shoulder d’inta da kyau, murya atausashe yace. “Please kiyi hakuri kinji, idan baki tsaya ba, zaki ci gaba dajin zafi sosai, banason kisake jin zafi kuma har abada.â€? Yanayin yanda ya k’are maganar yana d’an danne jajayen lips d’insa ne, yasa ta tsura masa ido batako k’yaftawa, domin aduniya bata tab’a sanin cewa kyawunsa ya zarce tunaninta ba, sai ayau da taga yana magana, babban abunda yafi komai daukar hankali agaresa kuwa, shine yanda yake motsa red lips d’insa. Wani irin zufa ne ya shiga keto mata alokacin da d’umin ruwan ya gama ratsa cikin jikinta, still kuma har yanzu yana rik’e da ita. Almost 12minutes yasa hannunsa acikin ruwan, jin da yayi kuma ruwan ya salance ne yasashi sake zuba mata wani ruwan, saidai ayanzu kam kukan shagwab’a ta saka masa, tare da soma yi masa turjiya, bisa dole haka ya k’yaleta tare da komawa gefe ya zare towel d’in dake jikinsa, kana ya sakarwa kansa shower. Da sauri ta rumtse idanunta saboda bazata iya kallonsa ahaka ba. Shikuwa Maleek duk abunda yakeyi dauriya ne kawai, tare kuma da jurewa zazzab’i da kuma ciwon marar dake damunsa, bayan ya kammala wankan nasa ne kuma ya zura wata farar bathrobe ajikinsa, tare da juyowa ya fuskanci Laylerh’n. Ahankali yakamo hannunta ya mik’ar da ita tsaye, wanda hakan yasa cikin sauri tasa hannu ta kare breast da kuma nipples d’inta wanda sukayi ja, fito da ita daga cikin bathtub d’in yayi, ganin kuma yanda take layi kaman zata fad’i ne yasa shi, d’aga ta ya kaita bakin shower. Shida kansa ya taimaka mata tayi wanka. Tare da d’aukan wani mini towel ya d’aura mata ajikinta. Still kuma d’aukanta ya sakeyi ahannu suka fito daga cikin toilet d’in, akan gado ya zaunar da ita, tare da d’aukan wani towel ya shiga goge mata ruwan dake kanta, bayan ya gama goge mata ruwan ne, ahankali ya zauna akusa da ita tare dasa hannayensa duka biyu ya dafe kansa dake ciwo. Almost 5mn kafun ya d’ago kansa ahankali ya kalli Laylerh’n, Idanunta dake ta lumshewa ya kuma kallo, ahankali yasa bayan hannunsa ya tab’a wuyanta dan har yanzu akwai zafin zazzab’i sosai ajikinta. “Ayshnoor!!â€? Ya k’ira sunanta asanyaye. Ahankali ta bud’e idanunta ta kalleshi, tare kuma da d’an shagwab’e fuska. Kyawawan idanunsa shima ya zuba mata, cikin yanayinsa na asalin Maleek da baisaba magana ba yace. “Tell me what’s wrong with you, kinajin ciwo sosai ne?â€? “I’m feeling hungry!â€? tafad’a asanyaye tare da sanya hannu ta shafa lafaffen cikinta dake kukan yunwa, saboda duk abunda ke cikinsa Maleek d’in ya kwashe. Hannunsa yasa yad’an dafe kansa, saboda gaba d’aya yama manta da cewar Fou’ad ya ajiye masa leda a falon k’asa. “I’m sorry bari na baki abinci.â€? Ya fad’a yana me mik’ewa tsaye, cikin sauri ya fice daga cikin d’akin. Jin fitansa daga cikin d’akinne kuma yasa ta maida idanunta ta lumshe, saboda zuwa yanzu wani irin bacci ne ke fusgarta, saidai kuma yunwa da zafin zazzab’in dake jikinta na neman hanata sukuni. Aba’angaren Maleek kuwa yana fita daga d’akin, kaitsaye falon k’asa ya sauk’o, ledodin da Fou’ad ya basa gaba d’aya ya kwaso tare kuma da dawowa saman. Ledodin dake hannunsa ya ajiye akan sofa, tare dasa hannayensa Ahankali ya jawo Laylerh’n jikinsa, acikin jikinsa ya zaunar da ita, tare da bud’e duka ledodin da suke cike da kayan ciye ciye, wani foilpaper’n da cikinsa ke d’auke da chicken and soup ya bud’e, tare da d’aukan naman ya kai bakinta, ahankali kuma cikin yanayin bacci da kasala, tad’an bud’e bakinta ya saka mata naman, haka ta dinga d’an taunashi ahankali harta cinye ya k’ara mata wani. Feeding d’inta yayi almost 10mn tace ta k’oshi da naman, duk da cewar bata ci wani mai yawa ba. Hollandia milk d’in daya fara sha ya soma bata, nan ma bata wani sha mai yawa ba tajanye kanta, wajen juyar da kannata ne kuma ta buge hannunsa, kusan rabin hollandia milk d’in haka ya kware acikin k’irjinta. Towel d’in dake jikin nata ya zame ahankali, tare da tura kansa jikinta, ya soma lasan duk inda milk d’in ya tab’a, Yanayin yanda taji harshensa na yawo ajikinta ne kuma yasa ta narkewa, tare da lumshe idanunta, duk wani sak’o da harshensa zai tura mata kuwa enjoying d’insa take. Tana ajikinsa haka kuwa wani bacci mai nauyi ya d’auketa. Lucky eyes d’insa ya lumshe a lokacin da yaji yanda, numfashinta ke sauk’a akan saman mararsa, cikin yanayin kasala da kuma sabon feeling d’in daya saukar masa, ya matsar da kayayyakin abincin gefe, tare da d’aukanta cad’ak ya kwantar da ita agefe. Bayan kuma ya sanja Bedsheet d’insu da yayi staining ne, ya d’aukota ya dawo da ita kan gadon. Rage hasken dake cikin d’akin yayi, tare da hayewa saman gadon, bayan ya zare bathrobe d’in dake jikinsa, ne kuma ya zare towel d’in dake jikin Laylerh’n, Ahankali ya jawota jikinsa yayi hugging nata, tare da rufa musu wani lallausan blanket. Lafaffen cikinta da kuma kasan mararta yake shafawa ahankali, wanda jin hakan yasa ta sake shigewa jikinsa sosai. Shikuwa idanunsa ya lumshe yana mejin wasu abubuwa na yawo acikin tunaninsa, Yayinda akaron farko yau gashi kwance da Laylerh ad’aki d’aya, gado d’aya, kuma acikin jikin juna matsayin ma’aurata, sun riga da sun zama abu d’aya. Tabbas buri da kuma muradin zuciyoyinsu ya tabbata. *4:30 pm* 4/7/21, 7:48 AM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting by* fatymasardauna *Note editing* *Chapter 78* Washe gari. 5:00 am. Ahankali ya soma bud’e idanunsa wanda cikinsu ke cike da mayen bacci, duk da cewar kuwa abaccin ya tashi, saidai da dukkan alama baccin bai ishesa ba. Kyawawan idanunsa ya sauk’e akan Laylerh’n da gaba d’aya ta gama shigewa cikin jikinsa ta manne. Ahankali ya d’an matsa tare da janye jikinsa baya, hannunsa ya daura adaidai saitin wuyanta, jin har yanzu jikinnata da zafi sosai ne kuma yasashi gyara mata kwanciya, tare dajan blanket ya rufa mata. Anutse ya sauk’o daga kan gadon, saboda sam bayaso motsinsa ya tada ita daga bacci. Kaitsaye toilet ya wuce, yana shiga kuwa ya sakarwa kansa ruwa, saboda yasan hakan zai taimaka masa wajen jin k’arfi ajikinsa. 8minute kacal ya d’auka ruwan na dukan jikinsa, bayan ya kashe shower’n ne kuma ya d’auro alwala, tare da fitowa daga cikin toilet d’in. Direct wani temporary glass drawer’n dake cikin d’akin ya bud’e, anan kuwa yaga kusan rabin kayan sawarsa, ak’agauce ya d’auko wani long combat jeans mai kalan mocha ya saka ajikinsa, tare da wata farar T-shirt mai kauri, saboda yanayin garin akwai sanyi sosai, kasancewar daren jiya and’au lokaci maitsawo ana ruwa. Wasu simple slipper yasaka ak’afansa, tare da d’aukan darduma kaitsaye ya fice daga cikin d’akin, da d’an sassarfa saboda saura baiwuce 3minutes bane ya rage ashiga sallah’n asuba. Babban Masallacin dake kusa da gidannasa ya nufa, yana zuwa kuwa ana tada sallah, hakanne yasashi shiga cikin jam’i akayi sallah’n dashi. Koda suka idar da sallah’n, mik’ewa tsaye yayi bayan ya shafa addu’a, saboda sanin halin daya bar Laylerh acikine kuma, yasa bai ko tsaya yin Azkhar ba, kaitsaye ya nufi gida. Ahankali ya tura k’ofar d’akin ya shiga bakinsa d’auke da sallamar, da kunnuwansa ne kad’ai suka jiye masa sautin. Har yanzu tana nan kwance kamar yanda ya barta, saidai sautin numfashinta dake fita sama sama, wanda kuma hakan alamace dake nuna cewar zazzab’in dake jikinta na k’ara hawa. Darduman dake rik’e a hannunsa ya ajiye, tare da d’an rank’wafowa ya lek’a fuskarta, ahankali yasanya hannayensa duka biyu ya d’agota zuwa jikinsa, cikin yanayin sanyi da kuma murya mai kama da rad’a ya k’ira sunanta “Ayshnoor!â€? “Ayshnoor!!â€? Yasake k’iran sunan nata adaidai lokacin daya sa tafin hannunsa, ya shiga shafa gefen fuskarta, tare da matsar da dogon gashinta da yayiwa fuskartata rumfa. Acikin baccin nata tajiyo sauti da kuma amon muryar, da har abada bazata tab’a manta mai itaba, hakan yasa ahankali ta soma bud’e idanunta, da sukayi luhu luhu, kana kuma suka d’anyi ja. Akan kyakkyawar fuskarsa ta sauk’e ganinta, wanda hakan yasa ta shagwab’e fuska. “Boo ni ban k’oshi da baccin ba fa, please ka mayar dani....â€? Tafad’a cikin yanayin zazzab’i da kuma kasalan da takejin ya sauk’ar mata. Sanyayyun Idanunsa ya d’an lumshe, tare dasa hannusa ahankali ya soma zagaye small lips d’inta, cikin muryarsa da tayi sanyi sosai yace. “I’m sorry kiyi sallah to saiki koma baccin kinji, tashi muje kiyi alwala.â€? Yanayin yanda ya k’are maganar yana me tallafota jikinsa ne, yasa ta narke masa tare dajin wani irin matsanancin soyayyarsa na k’ara shiga cikin zuciyarta. Shikuwa Maleek ahankali ya mik’ar da ita tsaye, tare da d’aukan towel ya daura mata ajikinta. Hannunta ya rik’e tare da soma d’an janta ahankali suka nufi toilet, duk da cewar kuma tana d’anjin zafi ak’asanta, but haka ta daure, saboda ta fahimci babu amfanin ci gaba da yi masa wani koke koke, domin tafi kowa sanin cewar kokad’an baya son kukanta. Koda suka shiga cikin toilet d’in kuwa, shida kansa ya taimaka mata tayi alwala, yana kuma rik’e da hannunta haka suka fito daga cikin toilet d’in. Ganin yanda take d’an ciccije baki ne kuma da yayi, yasashi zaunar da ita akan gado. Tare da k’arasawa ya bud’e murfin drawer, idanunsa ya zubawa tarin kayayyakin ta dake cikin drawer’n, wanda shi kansa bai isa zaman irga yawansu ba, hannunsa yasa ya zaro wata turkish abaya had’e da hijab. Karasowa inda Laylerh’n ke zaune yayi, hannunsa yasa ya warware towel d’in dake jikinta. Saurin rumtse idanunta tayi tare da sa hannayenta ta kare breast d’inta, saboda wani irin kunyansa takeji, musamman ayau daya gama gane mata duk wani sirrin jikinta, ciki kuwa harda inda ita kanta bata tab’a gani ba. Shikuwa Maleek idanunsa yad’an lumshe, lokaci guda kuma yaji tsikar jikinsa ta soma tashi, saboda sauk’e idanunsa da yayi, akan beautiful breast d’inta, da kyawunsu ke matuk’ar rikita shi, yayi imani komai na Laylerh’nsa mai kyaune, komai nata kuma daban yake dana kowa, ita ta musamman ce. Wani yawu daya tsaya masa amak’oshi ya had’iya, tare da d’an sunkuyowa ya zura mata doguwar rigar ajikinta, kana cikin danne new feeling d’in dake taso masa, ya mik’a mata Hijab d’in dake hannunsa. Da sauri kuwa ta karb’i hijab d’in ta saka, tare da mik’ewa tsaye tahau kan darduman dake shumfud’e agefen gadon, cikin nutsuwa kuma ta tada sallah’n. Shikuwa Maleek zama yayi agefen gadon, tare da k’urawa Laylerh’n idanu, har acikin ransa yana mejin sanyi da kuma samun gamsuwa da Laylerh’n ta zama matarsa, duk da cewar kuma akwai k’addara mai k’arfi da ta wahalar da rayuwarsu, amma kuma yau gashi, suna acikin inuwa d’aya, saidai kuma ayanzu babban tunanin dake yawo acikin kwakwalwarsa, shi ne yanda akayi Najeeb yabar masa Laylerh’n sa bai kusanceta ba. Idanunsa yad’an lumshe ahankali tare dasa hannunsa, ya shafi beard d’insa, Yayinda yakejin wani irin sanyi na sake game duk jikinsa. Daidai lokacin kuwa Laylerh’n ta idar da sallah, tare da kammala azkhar d’inta. Juyowa tayi tad’an kalli Yah M.jay d’innata daya lumshe idanunsa, hakanan ta samu kanta da kasa d’auke idanunta akansa, domin duk da cewar akwae d’an k’arancin haske acikin d’akin, amma hakan bai hanata ganin kyau da kuma haskensa ba, shid’in kyakkyawa ne tabbas, sannan akowani yanayi yake kyawunsa baya b’uya. Sam bata hango wata nakasa ko tawayayyar k’addara atattare dashi, domin ayanzu tasake gamsuwa cewar, lallai zata rayu dashi rayuwa kuma irin ta har abada, batare da fargaba ko kuma tsoron cewar zasu k’are rayuwarsu ahaka ba y’ay’a ba, komai Allah Ne ke tsarawa bawansa, rashi kuma bashi ke nuna cewar kazama kasashshe ba, haka zalika kuma rashi bashi ke nuna cewar, Allah Baya sonka ba, kowa da irin k’addararsa arayuwa, duk girman taka k’addarar kuwa idan zakayi dubi da wani, sai kafahimci cewa acikin munanan k’addarorin ma kai taka bata fiye muni ba, kuma asannu duk wani wanda yayi hak’uri ya kuma jure zaidace Insha Allah, abu mafi inganci akullum shine katsaya akan daidai, kada kuma kabari wata damuwa ta hanaka farinciki. Ajikinsa yaji cewar Ayshnoor d’in na kallonsa, hakanne kuwa yasashi d’an bud’e idanunsa ahankali, take kuwa suka fad’a acikin nata idanun. Murmushin daya sake bayyana kyawun fuskarsa yayi, tare da d’an ware hannayensa, cikin sanyin murya yace. “Zo.â€? Idanunta tad’an lumshe ahankali tare da sunkuyar da kanta k’asa, ahankali kuma ta mik’e tsaye, tare da soma taka k’afafunta dake d’an mata ciwo, ahaka harta k’araso inda yake zaune, durk’usa guiwowinta tayi ak’asa, tare da kama y’an yatsun hannunta ta shiga murzawa, cikin muryarta dake tafiya very slowly tace. “Good morning Yah M.Jay!â€? Hannayenta ya kamo tare da jawota jikinsa, ahankali ya had’e forehead d’insu, tare kuma da d’aura labb’ansa agefen bakinta. “Morning!!!â€? Yafad’a yana me sakar mata wani irin sassanyan kissing, d’in daya haifar mata da tashin duk wani tsikar jikinta. Hakanne kuwa ahankali ta lumshe Idanunta. Shikuwa Maleek hannunsa yasa ya zare mata hijab d’in dake jikinta, tare da d’aura hannunsa akan zip d’in dake gaban rigar ta, cikin yanayin nutsuwa kuma ya zuge gaba d’aya zip d’in. Ahankali ya d’ago idanunsa ya kalleta. Cikin wata irin kasalalliyar murya yace. “Daren jiya nayi hurting naki sosai ko? har yanzu kinajin zafi?â€? Kanta tad’an jinjina masa alaman “Eh.â€? Hannunta dake cikin nasa ya d’an murza, tare da fesar da iska ta bakinsa, still asanyaye yace. “I’m sorry Ayshnoor nah, i promised you bazan sake hurting naki ba, ki yafewa Maleek kinji, bansan ya abun yake ba shiyasa, amma yanzu I know idan zanyi bazanyi sosai ba promise!!â€? Ya k’are maganar yana me d’aura kansa akan shoulder d’inta, tare da shak’an daddad’an k’amshin daya kama fatar jikinta. Saidai kuma ganin yanda duk tayi laushi ne, yasashi kwantar da ita akan gado, tare kuma da kwantawa shima ya jawota jikinsa. Rigar dake jikinsa ya cire, had’e dajan blanket ya rufa musu. Ahankali ta sake shigewa cikin jikinsa, saboda bakad’anba take matuk’ar son k’amshinsa, domin k’amshin yana bata nutsuwa sosai. Cike da kasala kuma ta lumshe idanunta masu cike da bacci, alokacin da taji, sauk’an hannunsa akan bayanta yana shafata slowly, saboda dadin hakanne kuma yasa, cikin abunda bai wuce 10 minutes ba bacci ya d’auketa. Almost 15minutes kenan yanzu da kwanciyarsu, amma ya kasa d’auke idanunsa daga kallon kyakkyawar fuskarta. Wani irin yanayi na musamman yakeji akanta, hakika shikansa baisan cewar abunda yakeji akan Laylerh’n, ya zarce duk wani tunaninsa ba, sai ayanzu da tazama Halal d’insa. Haka yakejinta acikin kowani jijiya da jinin jikinsa, Tabbas yayarda duk wani feeling d’inta da yakeji ada, ba feeling bane matuk’ar za’a had’ashi da wanda yakeji ayanzu. Lallai kuma yayarda cewa itace cikon rayuwarsa, dole ne saida ita zaiyi rayuwa, Domin kuwa k’addara d’aya aka rubuta musu, wacce daga yanzu har abada zata ci gaba dayi musu yawo acikin jininsu, zuk’atansu guda ne, haka ma fata da burinsu duk abu d’ayane, K’AUNA’r junansu kuwa halittace dake rayuwa acikin jiki da zuk’atansu, har abada kuma wannan k’aunar ba zata tab’a gushewa ba. Idanunsa da suka ciko da k’walla ya lumshe ahankali, tare da d’aura bakinsa atsakiyar forehead d’inta. Yanayin yanda Laylerh’n ta sake cusa fuskarta acikin wuyansa ne kuma yasashi, soma sakin wani sassanyan numfashi ahaka har bacci ya d’aukesa. 9:30 am. Daidai vibrating d’in wayarsa dake aje akan bedside drawer ta tashe shi. Zare jikinsa daga na Laylerh’n yayi ahankali, tare da sauk’a akan gadon kaitsaye ya wuce toilet. Koda ya shiga cikin toilet d’in kuwa wanka yayi, bayan ya fito ne kuma ya sake kimtsa kansa cikin, wasu black T shirt and trouser. Sosai kayan suka bayyana haske da kuma annurin dake jikin fatarsa, domin ayanzu kallo d’aya kawai zakayi masa, ka fuskanci wani sauyi da kuma nagarta dake yawo akan fuskarsa, lallai Tabbas yana cikin farinciki, domin abune da kowa ya sani cewar samun Laylerh yafiye masa komai. Turarukansa na Oud ya shafa ajikinsa, tare kuma da d’aura babban agogo na company’n Gucci a hannunsa, cikin yanayin d’an hanzari ya saka wasu white sneaker shoe ak’afafunsa, bayan ya d’auki wayoyinsa da car key d’insa ne kuma, ya juyo ahankali ya k’araso inda Laylerh’n ke kwance tana bacci. Ganin yanda take d’an had’a gumi ne, kuma yasashi yaye mata blanket d’in dake jikinta, tare da sunkuyowa ya sunbaci beautiful lips d’inta. “I LOVE YOU Ayshnoor!!â€? Yafad’a ahankali tare da gyara mata kwanciyarta. Bayan ya k’ara mata gudun AC ne kuma, ya juya ya fice daga cikin d’akin, tare kuma da jawo mata k’ofar ya kulle. Koda ya fito falon kuwa, kaitsaye stairs d’in da zai sauk’ar dashi k’asa ya nufa. Bayan ya sauk’o falon k’asanne kuma ya tsaya yana k’arewa falon kallo, wanda shi kansa yasan bak’ananan millions su Abbou Jaheed suka kashe ba, wajen tsara had’uwa da kyawun faluka da kuma d’akunan gidan. Sanin kuma da yayi cewar sam bayason b’ata lokacinsa ne yasashi nufar k’ofar waje, domin so yake yaje inda zashi har ya dawo ba tare da Laylerh’n tatashi daga baccin da takeyi ba. Cikin takusan na nutsuwa ya gama fitowa daga cikin falon, inda ya samu kansa acikin babban compound d’in gidan. Kaitsaye wajen motarsa wanda Abdoul ya kawosa da ita daren jiya ya nufa, yana zuwa kuwa ya sawa motar key ya bud’e tare da shiga cikinta ya zauna. Kasancewar kuma su Abbou Jaheed sun turo masa maigadi ne, yasa tun kafunma ya tada motar, tuni maigadin ya wangale masa gate, atsanake ya cilla hancin motar tasa waje. Kaitsaye kuma hospital ya nufa, koda ya isa cikin hospital din kuwa, direct Office d’in Dr.Mouhammad ya nufa, yana zuwa kuwa aka bashi izinin shiga. Bayan kuma sun gaisa da Dr. d’inne Yayi masa bayanin cewar, yanaso ya rubutawa Laylerh magunguna ne saboda zazzab’in dake jikinta tun daren jiya. Sarai Dr. Mouhammad d’in ya gane abunda ya faru, saidai kuma bai tambayi Maleek d’in dalilin dayasa baizo da Laylerh’n ba, sanin irin cases d’inne kuma yasashi rubutawa Maleek d’in magungunan da ya kamata ace Laylerh’n tasha, ba ita kad’ai ba kuma harda Maleek d’in, saboda shima har yanzu akwai d’an zazzab’i kad’an ajikinsa. Gashi kuma tunda yayi sex d’in yakejin mararsa na rik’ewa, saidai kuma hakan bawani abun damuwa bane, domin hakan na faruwane ga wasu k’alilan daga cikin maza a lokacin da suka fara yin sex. Bayan ya k’arbi card d’in magungunan ne kuma yayiwa, Dr. Mouhammad d’in godiya, kana sukayi sallama, koda ya baro office d’in Dr din anan cikin pharmacy na hospital d’in ya saya magungunan. Bayan yafito daga hospital d’in kuwa kaitsaye hanyar gidansu ya nufa, Domin sosai yake da buk’atar ganin Oum Ayush musamman dan akwai wasu tambayoyin da yakeson yi mata, saboda abune da ke abayyane cewa, ita kad’ai ce zata iya bashi amsar tambayar da ke cikin zuciyarsa. *(Sorry kuyi manage bani da enough charging ne, sannan Insha Allah kafun Ramadhan zan gama Laylerh Maleek, because ma pages d’in da suka rage basu da yawa.)* *8:56 pm* 4/9/21, 6:43 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Note editing* *Chapter 79* Horn d’in motarsa ya danna adaidai lokacin daya iso gaban, tankamemen gate din gidannasu. Cikin abunda bai wuce 4minute ba kuwa maigadi ya wangale masa gate d’in, anutse ya tura hancin motar tasa cikin gidan. Saidai kuma sanin da yayi cewar bazae jima bane yasashi yin parking motar a tsakiyar compound din gidan, tare da bud’e murfin motar ya fito. Cikin yanayin nutsuwa ya soma takawa, saidai bai wuce taku biyar yayi ba, ya tsaya tare da juyowa ya sauk’e idanunsa, akan part d’in da Laylerh da kuma Najeeb d’in sukayi rayuwa. Idanunsa ya d’an lumshe ahankali, tare kuma da d’an cije jajayen labb’ansa, akaron farko kenan da yaji wani abu na rangwame acikin zuciyarsa. D’auke kansa daga kallon part d’innasu yayi, lokaci d’aya kuma direct ya nufi b’angaren Oum Ayush. Tsaye take agaban dinning table tana me harhad’a wasu had’add’un food flask acikin babban basket, k’aran knocking d’in falon da taji ne kuma yasa ta d’an dakatawa, tare da d’auko basket d’in ta rik’e ahannunta, dan a tunanin ta Abdoul ne, saboda tace masa yazo ya kaiwa su Laylerh’n kayan breakfast. K’arasowa jikin k’ofar tayi tare dasa hannu ta bud’e k’ofar. Idanu hud’u da sukayi da Maleek d’inne yasata dan bud’e baki, cikin kuma yanayin mamakin ganinsa tace. “Maleek kaine da safe haka ina kabaromin Laylerh’n?â€? Idanunsa ya d’an lumshe, batare kuma daya amsa mata tambayar da tayi masa d’inba, ya rab’a ta gefenta ya shige cikin falon. Ganin hakan da tayi d’inne kuma yasata d’an tab’e baki, tare da maida kofar ta rufe, saboda dama tasan dole idan dai zasu had’u to sai ya nuna mata halinnasa na shariya, wanda kuma idan da sabo ta riga da ta saba da hakan. “Good morning Oum Ayush.â€? Ya fad’a adaidai lokacin da ya k’arasa gaban, makeken fridge’n dake cikin falon, batare kuma daya jira amsawarta ba, ya bud’e murfin fridge’n ya d’auko bottle water maisanyi sosai. Dawowa tsakiyar falon yayi tare da zama akan d’aya daga cikin kujerun falon, ahankali ya b’alle murfin bottle water’n, tare da d’aura goran abakinsa. Only 8second kawai ya shanye rabin ruwan dake cikin goran, ahankali ya d’an janye kansa, tare da d’ago idanunsa ya kalli Oum Ayush da ta zuba masa ido. Nuni yayi mata da goran ruwan, tare dayi mata alama akan ko zata sha. “Bazan shaba, ko ce maka akayi ishin ruwa nakeji, da fari ka fara amsamin tambaya ta tukunna, ina kabaromin Laylerh, kodai barinta kayi awannan babban gidan ita d’aya?â€? Ta fad’i hakan tana me harararsa tare da ajiye basket d’in dake rik’e a hannunta, kana ta zauna akan kujerar dake facing d’inshi. Jin still Oum Ayush ta sake nanata masa tambayar ne kuma, yasashi d’an sake lumshe idanunsa, ahankali cikin kuma yanayin daya sabayin magana yace. “Bata da lafiya tana bacci.â€? “Bata da lafiya kuma Maleek? Meya sameta?â€? Oum Ayush d’in ta fad’a ad’an rud’e, Domin abunda ya fara zuwa ranta, shine wannan ciwon marar da Laylerh’n keyi. Kansa ya d’an sunkuyar kana cikin yanayin sanyin, dake bayyana tausayawarsa agareta yace. “No bawani babban ciwo bane, fever ne kawai, kuma na saya mata pain relievers a pharmacy.â€? Sassanyar ajiyar zuciya Oum Ayush d’in ta sauk’e, asakamakon jin abunda ya fad’a, lokaci d’aya kuma taji wani irin nutsuwa yazo mata, take kuma tunaninta ya bata cewar Lallai wani abu, ya faru atsakanin Laylerh da Maleek d’in, saboda haka kawai tasan cewa Laylerh’n bazata yi zazzab’i ba. “Allah Yabata lafiya, ga breakfast nan dama ku Abdoul zai kaiwa, amma yanzu tunda kazo saika tafi dashi.â€? Tafad’i hakan cikin kulawa, sannan ga kuma wani sahirtaccen murmushi da ya bayyana akan fuskarta. D’ago kai Maleek d’in yayi ya kalleta, tsawon minti d’aya kaman kuma zaice wani abu amma saiya fasa. Mik’ewa tsaye yayi, tare da k’arasowa inda Oum Ayush d’in ke zaune. Zama yayi agefenta tare kuma da juyowa ya fuskanceta, cikin yanayin daya tabbatar cewa zata fahimcesa yace. “Me yasa Najeeb ya saki Laylerh?â€? Oum Ayush kuwa saurin d’agowa tayi ta kalleshi, saboda jin tambayar nasa da tayi abazata. Ganin kuma da tayi cewar shid’inma kallonta yakeyi ne ya sata d’auke kanta, tare da sauk’e ajiyar zuciya, kana asanyaye tace. “Meyasa ka tambayeni hakan?â€? “Saboda inason sani.â€? Ya bata amsa atak’aice, had’e da janye idanunsa gefe. D’an Jim Oum Ayush d’in tayi acikin ranta tana me mamakin dalilin da yasa, Maleek d’in yayi mata wannan tambayar, saidai tasani koma meyene ayanzu bai kamata tak’i Gaya masa ba, saboda ta fahimci cewa ayanzu, shida Laylerh’n sun riga da sun zama abu d’aya, wanda kuma dama hakan shine burinsu gabaki d’aya. D’an gyara zamanta tayi, tare kuma da juyowa ta fuskanci Maleek din. Asanyaye tace. “Saboda ya baku dama kuyi rayuwa tare, Domin ya fahimci hakan shi ne samun saukin zuciyoyinku, zuciyoyin da kullum suke awahale, Tabbas Najeeb bai saki Laylerh dan baya sonta ba Maleek, ya saketa ne kawai don samun sauk’in zuciyar da take gab da tarwatsewa, kaima kasani Maleek abune da yake abayyane, wanda kuma kowa ya fahimta, Domin ko zaka iya b’oye abundake cikin zuciyarka, bazaka tab’a iya b’oye wanda ke rubuce akan fuska da kuma cikin idanunka ba, Najeeb ya saki Laylerh ne saboda ya gano cewar kuna yiwa junanku tsananin so kai da ita, sannan mafarki dama duk wani burin dake cikin zuciyoyinku ahad’e suke, Lallaine kuma Allah ya tsara cewar dole duka ku biyun zakuyi zaman aure da ita, da farko Allah ya tsara mata zama da Najeeb, saidai bai k’addara zaman nasu zaiyi tsawo ba, ayanzu kuma gashi tana zaune ak’arkashin inuwarka, shin tayaya kake tunanin zai iya jure zama da Laylerh’n, da akullum sunanka ne cike acikin bakinta? Koda acikin bacci sunanka take k’ira masa, duk wani ciwonka kuwa acikin jiki da zuciyarta takeji, koda sau d’aya fa Maleek Laylerh bata tab’a bashi kulawar aure ba, kuma duk asaboda kai, safe, rana, dare duk bata da wani aiki sai tunaninka, ta ya ya zai jurewa hakan? Tabbas akullum bamu iya sauya k’addarar mu Maleek, komai da Allah ya tsara mana, mai kyau ko marar kyau, bamu iya sanjawa ko guje masa, koda yaushe acikin k’addara da kuma jarrabawar Ubangiji muke rayuwa, saboda haka komai da ya faru rubutaccen al’amari ne, dan haka mu rungumeshi ayadda yazo mana, matuk’ar akwai Allah Kuma to kasani akwai zab’in alkhairi.â€? Idanunsa dake alumshe ya bud’e tare da sakin wani irin ajiyar zuciya. Tabbas kalaman Oum Ayush d’in sun shigesa, saidai kuma abun da zuciyarsa ke kokonto akai shine, dalilin dayasa Najeeb ya saki Laylerh batare da ya tab’a kusantarta ba. Ahankali ya kifa tafukan hannayensa akan fuskarsa, tare da fesar da wani sassanyan numfashi, akaron farko kenan da ya fara jin wani abu na rangwame na ratsa zuciyarsa adangane da Najeeb d’in, saboda ada wani mummunan kallo yakeyi masa, Kallon wanda ya rabasa da duk wani Fata da Muradinsa, Kallon wani na daban, wanda yayiwa rayuwarsa kutse. Jajayen idanunsa ya d’an ware, tare da mik’ewa tsaye ya zura duka hannayensa acikin aljihun wandon dake jikinsa. Ahankali ya d’an soma zagaye tsakiyar falon, tamkar wanda ke son nazartar wani abu. Ganin hakanne kuma yasa Oum Ayush ta zuba masa idanu, tare da shirin sauraran duk wani abu dazai fito daga bakinsa. Almost 6 minute kuwa acikinsu babu wanda ya sake cewa komai. Saima sunkuyawa da yayi ahankali ya d’auki basket d’in da Oum Ayush d’in ta ajiye atsakiyar falon, batare kuma daya sake kallonta ba yace. “Zan tafi, but please idan kinsamu time kizo ki duba Laylerh.â€? Kai ta jinjina masa alaman “To.â€? Juyawa yayi cikin nutsuwa kuma ya nufi hanyar fita daga cikin falon. Da kallo Oum Ayush ta bisa, ganin da tayi yakai bakin kofar fitane kuma yasa ahankali tace. “Please Maleek kakula da Laylerh sosai, duk da nasan cewar tana da mahimmaci sosai agareka, amma kada ka matsa mata domin kasancewar itad’in har yanzu yarinyace, zaku ma ta taso ne akan duk wani abu daka d’aurata.â€? Kansa ya jinjinawa Oum Ayush d’in, tare dayi mata alama akan cewar yaji duk abunda tace. Hannunsa dake kan handle d’in kofar ya murd’a, take kuwa k’ofar falon ta bud’e ya fice. Sassanyar ajiyar zuciya Oum Ayush ta sauk’e, tare da sakin murmushin jin dad’i, Lallai tayarda cewa akan komai Allah Ne ke ikonsa yanda yaso, domin duk da rashin sakewa irin ta Maleek d’in, hakan bai hanata hango zallan nutsuwa da kuma farinciki acikin k’wayoyin idanunsa ba. Daga wani sashi na zuciyarta kuwa, tausayin Laylerh ne yayi mata tsaye, saboda batasan wani irin aika aikane Maleek d’in yayi mata ba, duk da tana da yak’ini akan cewar Maleek bazae tab’a cutar da Laylerh’n ba, amma tasan dole baza’a rasa wani d’an wahala da Laylerh’n tasha ba, saidai koma meye tayi alk’awari cewa da yamma zataje ta duba Laylerh’n. Ab’angaren Maleek kuwa yana fitowa daga sashin Oum Ayush d’in, kaitsaye wajen motarsa ya nufa, bud’e bayan motar yayi ya saka babban basket d’in abincin dake hannunsa. Yana gama rufe motar kuwa Abbou Jaheed da kuma Abbou Khareem suka shigo cikin gidan. Ganin Maleek d’in da sukayine kuma yasasu fad’ad’a murmushi da kuma fari’ar dake kan fuskarsu. Maleek kuwa Kamar yanda yasaba gaishe da mahaifin nasa, haka yayi yau ma, d’an durk’usawa yayi ya gaishe dasu dukansu. Saidai gaba d’aya ya kashesu da mamakin ganin murmushi da sukayi kwance akan fuskarsa. Wani irin sanyi Abbou Jaheed yaji acikin zuciyarsa, tare kuma da samun gamsasshiyar nutsuwa, Tabbas akaron farko yaji ajikinsa cewa, yayi abunda ya dace, sannan ya samawa y’ay’ayen nasa nutsuwa da kuma farinciki na har abada. Haske da kuma annurin daya gani kwance akan fuskar Maleek, ya tabbatar masa da cewar zuciyar Maleek ta samu gamsuwa da kuma abunda takeso. Hakika ya sake tabbatarwa kansa cewar, zuciyar Maleek dana Laylerh’n ahad’e suke, sannan kuma farincikin kowannensu shine rayuwa tare da d’an uwansa. Sannan ada bawai ya nesanta Maleek da Laylerh’n saboda wani abu na daban bane, ya nesanta sune kawai saboda gujewa halin rayuwa da kuma biyewa zuciya. Saboda abune daya jima da sani cewar, akwai soyayya mai k’arfi atsakanin Maleek da Laylerh’n, wanda kuma k’arfi da tasirin soyayyar kan iya haifar da faruwar komai atsakaninsu, Domin abune da ke abayyane, matuk’ar k’arfi da tasirin soyayya tayi yawa, takan iya makantar da idanun masu yinsa, har ya Kaisu ga kasa iya jurewa lokaci, ahaka ne kuma za’a samu makancewar zuci, ta yanda zasu mallakawa juna gangar jikinsu, batare kuma da tunanin girman zunubin da suka aikata ba, haka koda yaushe zasu kasance tamkar abu d’aya. Wannan abun Abbou Jaheed yake matuk’ar gujewa, akullum shiyasa ada yake nesanta LaylerhMaleek d’in. Abbou Khareem da bakinsa ya kasa rufuwa saboda farinciki ne kuma ya kalli Maleek d’in, tare da cewa. “Maleek kaine haka da safe, to ina kabaromin y’artawa kuma?â€? Jajayen labb’ansa yad’an cije, tare da Kallon Abbou Khareem d’in, cikin yanayin dake bayyana, gajiyarsa da tambayar Abbou Khareem d’in yace. “Oum Ayush ma abunda ta tambaya kenan.â€? Murmushi dukansu sukayi, saboda dama sunsan halinsa bai cika yawan son tambaya ba. Kafad’ansa Abbou Jaheed yad’an bubbuga, cikin son dad’a basa k’arfin guiwa yace. “Kayi maza ka koma gida, Allah Ubangiji ya baku zaman lafiya mai d’orewa, Insha Allah Muma zamu zo gidan naku mu duba ku.â€? Idanunsa yad’an lumshe, tare kuma da jinjina kansa, hannun Abboun nasa ya kamo ahankali ya rik’e acikin nasa. Cikin wata irin muryar dake bayyana rauni da kuma sanyin zuciyarsa yace. “Thank you so much Abbou Jaheed!!â€? Ya k’are maganar murya atausashe tare kuma da d’an karyar da wuyansa gefe. Murmushin tsananin farinciki Abbou Jaheed d’in yayi, lokaci d’aya kuma yaji hawaye sun cika idanunsa, wanda suke bayyana tsananin tausayin Maleek d’in da yakeji. Ahankali ya jinjinawa Maleek d’in kai, tare dayi masa alama da idanu akan ya tafi gida. Hannunsa dake rik’e dana Abbou’n ya janye, tare kuma da bud’e murfin motarsa ya shiga. Bayan yayiwa motar tasa key ne kuma ya soma yin reverse, ganin hakanne kuma yasa mai gadi ya wangale masa gate d’in gidan ya fice. Da kallo su Abbou Jaheed sukabi motar tasa, kowannensu jin zuciyarsa yake tas, babu wani alama ko sauran damuwa. Domin yau sunga farinciki, da kuma nutsuwar da suke so da fatan gani akan fuskar Maleek tsawon shekaru. Kowannensu haka ya nufi sashinsa fuska d’auke da murmushi. Saidai kuma ak’asan zuciyar Abbou Jaheed damuwa ce, damuwa mai d’auke da Rauni, da kuma tsananin tausayin Maleek da Laylerh, wanda suka amincewa rayuwa ayadda tazo musu, suka kuma yi imani da k’addararsu. Tabbas ba’a tabbata acikin k’unci, Lallai watarana kowani mai damuwa damuwarsa zata yaye, farinciki zaizo koda kuwa acikin farincikin akwai nak’asu, hakan bazai tab’a hana zuciyar da ta wahala samun nutsuwa ba. Maleek Ahankali yake driving d’in motar tasa, Yayinda daga gidan nasu, kaitsaye juya akalar motar tasa yayi zuwa shoprite. Kasancewar kuma daga inda yake zuwa shoprite din babu wani tafiya sosai ne, yasa cikin mintuna kadan ya iso. Bayan ya gama daidaita Parking din motar tasa ne kuma, ya fito kaitsaye ya nufi cikin shoprite d’in. Saidai kuma koda ya shiga baiwani jima ba ya fito, saboda mafiyawancin abunda ya saya chocolates ne, shiyasa bai wani b’ata lokaci ba. Alokacin daya iso gaban tsararren gidannasa kuwa, horn d’aya kawai yayi maigadi ya bud’e masa gate. Bayan kuma ya gama daidaita parking d’in motar nasa ne, ya bud’e ya fito, tare da d’aukan babban ledan da yayi sayayya aciki, da kuma basket d’in abincin da Oum Ayush ta bashi. Ahankali ya tura k’ofar falon ya shiga, still kuma falon k’asan Yana nan kamar yanda ya barshi. Sama ya haura direct, a zuciyarsa yana mai fata da kuma addu’ar Allah Yasa Laylerh’n bata tashi daga bacci ba. Basket da kuma ledan dake hannunsa ya ajiye acikin falon, tare kuma da nufan bedroom d’innasu kai tsaye. Ahankali ya murd’a handle d’in k’ofar ya shiga. Sauk’e idanunsa da yayi akan gadonne kuma, yasa k’irjinsa wani irin bugawa... *(I’m sorry nayi azumi shiyasa na makara wajen typing, insha Allah amma gobe zan baku update)* *9:26 pm* 4/10/21, 7:32 AM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Note editing* *Chapter 80* Sauk’e idanunsa da yayi kuma akan gadonne yasa k’irjinsa wani irin bugawa. Saboda baiga Laylerh’n kwance akan gadon ba. Da sauri ya maida k’ofar d’akin ya rufe, tare da k’arasa shigowa cikin d’akin, fuskarsa d’auke da mamaki yake yawo da idanunsa akan gadon, kenan ina Laylerh’n tatafi, yaushe ma tatashi daga baccin? Zuciyarsa tayi masa tambayar da bashi da amsarta, hannayensa ya sanya ya kama waist d’insa, tare kuma da d’an juyowa ya zubawa k’ofar bathroom d’in dake cikin d’akin idanu. Ganin k’ofar da yayi ad’an bud’e ne kuma yasashi, d’an matsawa ahankali tare da k’arasawa jikin k’ofar ya tsaya. Daidai lokacinne kuma ta zuro k’afafunta k’asa ahankali, tare da fitowa daga cikin bathtub d’in wanka, taku biyu kawai tayi ta tsaya, tare da kuma da rumtse idanunta, kana ahankali ta d’an ciji labb’an bakinta, saboda wani irin zafi da kuma zogin da taji acikin jikinta. Ahankali cikin daurewa zafin da takeji d’in, ta mik’a hannu ta ciro wata light purpule bathrobe dake cikin wani cover na glass. Anutse ta saka bathrobe d’in ajikinta, tare da soma taka k’afafunta ahankali, cikin kuma sabon yanayin tafiyan da tasamu kanta aciki, ta nufi k’ofar fita daga cikin toilet d’in. Saurin janye jikinsa daga jikin kofar yayi, tare da sanya tafukan hannunsa ya dafe saman mararsa, da lokaci d’aya ya soma wani irin harbawa, lips d’insa ya cije dad’an k’arfi tare da soma sakin ajiyar zuciya akai akai. Tabbas ganin da yayiwa Laylerh’n naked ayanzu bak’aramin d’aga masa hankali yayi ba, lokaci d’aya yaji duk tsikar jikinsa na mimmik’ewa, Yayinda wani irin feeling d’inta ke game duk kan sassan jikinsa. Ahankali ta k’arasa bud’e k’ofar bathroom d’in, tare da sako kai zata fito, kasancewar kuma baiyi nisa da k’ofar bathroom d’in bane, yasa tana fitowa Idanunta suka sauk’a akansa. Saurin ja da baya tayi tare da sakin wata yar siririyar k’ara, dake bayyana tsoronta, saboda sam bata san cewar ya shigo cikin d’akin ba, ganinsa kuma da tayi yanzu abakin k’ofar bathroom d’inne yasa tayin tunanin cewar ko ya jima yana kallonta. Jin ihunnata ne kuma yasashi bud’e tsumammun idanunsa, ahankali ya sauk’e ganinsa akanta. Da sauri tayi k’asa da kanta, tare dasa hannayenta duka biyu akan k’irjinta, Cikin yanayin da yafi kama da shagwab’a tace. “I’m sorry naji tsoro, saboda bansan kana nan ba shiyasa.â€? Hot breath ya fesar, tare da takowa Ahankali ya k’araso gab da ita, hannunsa dake kan mararsa ya zare tare da kamo nata hannun ya rik’e acikin nasa. Rikitattun idanunsa da suke bayyana zallan feeling d’inta da yakeji ya sauk’e akan baby innocent face d’inta, dake d’auke da danshin ruwa, har kuma zuwa kan jajayen lips d’inta. Wani hawalallen yawu daya tsaya masa amak’oshi ya had’iya, tare da bud’e bakinsa, cikin sanyi yace. “Yaushe kika tashi?â€? Sanyi da kuma sautin amon muryartasa da suka ratsa cikin kunnuwanta ne, yasa ta d’an lumshe Idanunta, saboda wani irin abu da taji na musamman, ga kuma kusan cin dake tsakaninsu yasa duk taji Maleek d’in yayi mata kwarjini. Ahankali ta d’an d’ago kanta ta kalleshi, saidai kuma ganin wani irin kallo da yakeyi mata ne, yasa tayi saurin janye idanunta daga fuskarsa, ta dawo dasu kan faffad’an chest d’insa, cikin muryar dake fitar da zallan yarintarta tace. “Please ka ganni ahaka ne?.â€? “Eh.â€? Ya fad’a asanyaye still kuma yana me yawo da idanunsa akan bakinta. Jin yace “Eh.â€? ne kuma yasa ta rumtse Idanunta da k’arfi tare da juya masa baya, saboda wani irin nauyinsa da taji ya sauk’ar mata, duk da tasan cewar jiya yaga komai da komai nata, amma ba kamar yanzu ba, saboda jiyan kallon dare yayi mata, amma yanzu tasan kallon daya mata na sosai da sosai ne. Murmushi’n daya k’arawa fuskarsa kyau yayi, tare dasa hannunsa ahankali ya jawota zuwa cikin jikinsa, kansa ya d’aura akan shoulder d’inta, sassanyan k’amshin shower jel d’in da tayi wanka dashi, daya ratsa cikin hancinsa ne kuma yasa shi d’an lumshe idanunsa, tare da sauk’e ajiyar zuciya, saboda wani irin kasala da yaji na musamman na sauk’a ajikinsa. Itama jinta acikin jikin nasa ne yasata lumshe Idanunta, had’e da sake manne jikinta da nasa, saboda sosai duk wani abu daya shafesa keyi mata dad’i, musamman ma k’amshi da kuma laushin fatar jikinsa. Hannayensa dake kan waist d’inta ya d’an matsar gefe, tare da jan igiyan bathrobe d’in nata, wanda hakan yasa gaba d’aya rigar ta bud’e. Ahankali ya tura hannayensa cikin jikinta, tare da soma shafa saman shafaffen cikinta, slowly har zuwa kan mararta. Sake rumtse Idanunta tayi, tare dajan wani dogon numfashi saboda yanda taji sauk’an tafukan hannayensa akan soft skin d’inta ya masifar rikita ta, musamman da ayanzu taji yana cycling marar ta. Wani silent breath da yake fitarwa ahankali yana sauk’a acikin kunnenta ne, kuma yasa tsikar jikinta suka mimmik’e. “Uhummmm Yah M...Jay!!â€? Ta k’ira sunansa ahankali, cikin kuma yanayin shagwab’an dake nuna cewar tana enjoying duk wani abu da yake mata. Maleek kuwa da tab’a skin d’innata keyi masa dad’i sosai, jin tak’ira sunansa ne yasashi d’an bud’e idanunsa da suka k’ank’ance, kana kuma sukayi ja. Cikin muryarsa da tayi sanyi sosai yace. “Ummmmm Ayshnoor what happened?â€? Ya k’are maganar yana me juyo da ita,ya zamana suna fuskantar juna. Wanda hakanne kuma yasa idanunsu dake d’auke da matsanancin sha’awa had’ewa dana juna, wani irin kallo mai gigita tunani da Maleek d’in yayi matane kuma yasa ta d’an bud’e lips d’inta ahankali, tare da narkewa lokaci d’aya taji k’afafunta na rawa, ga kuma wani sanyi da takejin na ratsa cikin tafin k’afanta. Shikansa Maleek ayanzu feeling d’innasa k’aruwa yake, Domin har wani nauyi yakejin eyes d’insa sunyi masa, saidai yasani duk feeling d’insa ayanzu bai dace ya sakeyin sex da Laylerh’n ba, duk da cewar yana matuk’ar buk’atar ta, da kuma son sake jinsa acikin duniyarta ta musamman, amma yasan yin hakan tamkar sake hurting d’inta ne, alk’awari yayi kuma cewar bazae dake hurting nata ba, lallai dole zai daure zuwa dare, kafunnan yasan zata d’an daina jin zafi, musamman idan tasha pain relievers d’in daya kawo mata. Ahankali ya kamo hannunta tare da jawota, ya zaunar da ita agaban dressing mirror d’in dake gefensu, bathrobe d’in dake jikinnata ya d’an zare kad’an, tare da d’aukan wani body lotion ya soma shafa mata ajikinta. Ajiyar zuciya ta sauk’e ahankali tare da zubawa yatsun hannunsa ido, Domin duk da kasancewar mai yake shafa mata, amma ji take tamkar wani salon yake mata na daban, sam tarasa meyasa ko meye Boo d’in nata zaiyi mata, sai tajisa har cikin jikinta. Shikuwa Maleek atsanake ya gama shafa mata mai d’in, ga mamakinta kuma sai gani tayi ya d’auki powder tare da bud’e murfin powder’n, soson fowder’n ya d’auka tare da soma shafa mata akan fuskarta. Har ya gama kuwa bata bud’e idanunta ba, saboda wani irin dariyarsa ne ma ya kamata, because bata tab’a tunanin ya iya irin way’annan abubuwan ba. Ganin da yayi kuma cewar fowder’n ta gama shafuwa ne, yasa shi ajiye soson tare da zubawa fuskarta idanu, lokaci d’aya kuma Brain d’insa ta soma dawo masa da wasu moments d’in da suka jima da wucewa shekaru masu tsawo. Lallai har abada bazae tab’a iya manta rayuwar da yayi da Laylerh’n ashekarun baya ba, shine komai nata, idan tayi wanka shi yake shafa mata mai, sannan yayi mata kwalliya kamar yanda yaga sauran mata nayi, akanta ne ya fara sanin duk wani abu daya shafi Mace, akanta yake b’ata tsawon lokuta, akullum bashi da wani Uzuri sai nata, koda yaushe itace first acikin mine d’insa, tamkar kuma yanda jini ke gudana acikin jikin kowani d’an Adam mai rai, haka yakejinta acikin jikinsa, Yayinda akowani bugun zuciyarsa ita muradinta ne ke yawo, koda sau d’aya kuma numfashinsa bai tab’a fita da shiga ba, saida tunani da kuma burin kasancewa da ita akullum a kuma har abada. Hakika zuciyarsa ta jima tana yiwa Laylerh’n tsananin So, So kuma irin wanda har abada bazae tab’a misaltuwa ba. Hannayensa dake kan fuskarta ya d’an janye ahankali, tare da saurin kawar da kansa gefe, Cikin yanayin son kawar da damuwar dake shirin danne masa zuciya kuma ya nufi gaban babban wardrobe d’in da kayansa ke ciki. Bud’e murfin wardrobe d’in yayi tare dasa hannunsa ya zaro wata white t shirt d’insa, wanda agaban ta akayi rubutu da red paint, kasancewar kuma rigar tana da d’an fad’i ne yasa shi nufo Laylerh’n da ita. Mik’ar da ita tsaye yayi, batare da tayi tsammani ba kuwa taji ya zare bathrobe d’in dake jikinta, saidai ayanzun sam bai bari idanunsa sun sauk’a awajen da ganinsu yafi komai azabtar dashi ba. Rigar dake hannun nasa ya zura mata, take kuwa rigar ta sauk’o har kan cinyoyinta, maida ita yayi ya zaunar, tare da d’aukan comb ya gyara mata gashin kanta, bayan ya gama yi mata gyaran gashin ne kuma Ya shafa mata, turaren da yasan tana amfani dashi. Ganin yanda tayi masa kyaune kuma yasashi d’an lumshe idanunsa, kana asanyaye yace. “Ki k’irasa shiryawa inazuwa.â€? Kai ta jinjina masa, tare da bin bayansa da kallo har saida ya fice, kafun ta maida idanunta ga mirror, wani irin sassanyar murmushi ta sake tare dasa hannunta ahankali ta shafa gefen fuskarta, sam babu wani gyara kokad’an a shafa fowder’n da yayi mata. Kallonta ta mayar ga rigarsa dake jikinta, wanda tayi mata kyau sosai, kana ta kuma bayyana shatin breast da nipples d’inta. Hannunta tasa ta jawo hand bag dinta dake gefen mirror, wanda acikinsa ne Oum Ayush tace ta samata duk wasu k’ananan abubuwanta. Zuge zip d’in jakan tayi tare da zaro wani siririn gold anklet d’inta ta d’aura ak’afarta na dama, tanason anklets sosai saboda yana k’ara sawa kwalliyar mutum tayi kyau. Ab’angaren Maleek kuwa yana fita daga d’akin, direct kitchine ya nufa, plates spoons and cups ya d’auko, tare da dawowa cikin falon, rigar dake jikinsa ya zare Domin dama ba al’adarsa bace zama da riga. Kaitsaye d’akin ya nufa daidai lokacin daya shiga cikin d’akin kuwa Laylerh’n ta gama mak’ala mahad’in anklet d’in dake k’afarta. D’ago kan da tayi ne kuma yasa suka had’a ido, saidai ganinsa babu riga yasa tad’an sunkuyar da kanta. Shikuwa Maleek hannunta ya kamo suka fice daga cikin d’akin. Koda suka fito zama yayi akan lallausan turkish carpet d’in dake malale atsakiyar falon, tare da jawo hannun Laylerh’n ya zaunar da ita acikin jikinsa. Basket d’in abincin da Oum Ayush ta basa ya jawo, tare da ciro food flask d’in dake ciki. Duka food flask d’in dake d’auke da abinci kala kala ya bud’e, tare da kallon Laylerh’n da ta sake shigewa cikin jikinsa. “Ayshnoor nah me zakici, chips and ketchup?.â€? Yayi maganan yana me kama y’an yatsun hannunta. Kai ta jinjina masa alaman “Eh.â€? Murmushin daya k’arawa fuskarsa kyau yayi saboda dama yasan abunda takeso kenan. Chips and ketchup d’in ya zuba a plate, tare da soma d’auka da hannunsa yana bata, ahankali take tauna abincin, Yayinda kuma duk sanda yazo sa mata abaki sai ta had’a da yatsunsa ta tsotsa. Hakanne kuma yasa shi jin wani iri ajikinsa, har ya kaiga idanunsa sun d’an soma lumshewa. Almost 10mn yana bata abincin, kafun ahankali ta girgiza masa kai, tare dayi masa alaman cewar ta k’oshi. Idanunsa yad’an tsayar akanta tare dasa hannunsa ahankali ya shafa kan cikinta da har yanzu yake a lafe, da ace kuma baisan halinta ba, Tabbas da zai iya cewa bata koshi ba, saidai kuma sanin da yayi cewar bata cin abinci da yawane yasa shi k’yaleta. Ledan daya shigo dashi ya jawo tare da bud’ewa ya d’auko ledan chocolate biyu ya bata. Da sauri ta amshi chocolate d’in tare da kallonsa ta sakar masa murmushi, cikin kuma yanayin dake bayyana farincikinta tace. “Thanks so much Mah Boo.â€? Murmushi’n da tayi masa d’in ya mayar mata, tare da b’alle murfin hollandia milk d’in ya kafa abakinsa, saida kuma yasha fiye da rabi kafun ya jingina bayansa da jikin kujera, ahankali ya lumshe fitinannun idanunsa, da suka kasa dawowa daidai, saboda feeling d’in dake damunsa, musamman ayanzu da Laylerh’n take jikinsa sai yanajin kamar ana k’ara hura masa wutar feeling d’in. Laylerh kuwa ganin yanda yayi shiru ne, yasa ahankali ta sanya yatsan hannunta tare da soma zagaye tattoo din dake kirjinsa. Tamkar tafiyan hawainiya haka yakejin abunda Laylerh’n keyi masa, akasalance ya bud’e idanunsa tare da sanya hannayensa duka biyu ya rik’ota. Rikitattun idanunsa daya zuba mata ne kuma yasa ta soma d’an soma motsa labb’an bakinta. Ganin hakan da yayi ne kuma yasashi zaro harshensa, dake d’auke da sanyi da kuma gard’in madarar hollandia, ahankali ya tura mata acikin bakinta. Atake kuwa taja wani irin numfashi mai kama da groaning, tare da d’aura harshe da bakinta akan nasa tana tsotsan sanyi da kuma zak’in dake bakinsa. *9:18* 4/11/21, 8:48 AM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting by* fatymasardauna *Note editing* *Chapter 81* Wani irin numfashi me sanyi ya fesar,musamman alokacin da yaji yanda sugar lips d’in Laylerh’n ke tsotsan tongue d’insa. Yayinda daga gefe guda kuwa tsikar jikinsa ne ke wani irin tashi, lokaci d’aya komai ya soma k’ok’arin k’wace mai. Tabbas yasan idan aka k’ara wasu y’an minutes, zaikai wani stage da ba lallaine ya iya jurewa ba. Ahankali yad’an tallafo hab’arta tare da zare bakinsa daga cikin nata, ya k’urawa kyakkyawar fuskarta ido, hakan da yayi d’inne kuma yasa Laylerh’n lumshe Idanunta, tare da d’an fito da harshenta, tana lashe sauran saliva d’insa dake kwance akan lips d’inta. Ahankali ya jawo wata leda dake gefensa, tare da bud’eta ya ciro magungunan dake ciki, b’are iya adadin magungunan da yasan Laylerh’n zata sha yayi, daga jikin kowani sachet, kafun shima ya b’are nasa ya watsa acikin bakinsa, ba tare kuma da yasha ruwa ba haka ya had’iyesu. Pills d’in da Laylerh’n zata sha kuwa acikin tafin hannunsa ya zuba su, tare da d’ago kansa ya kalleta, cikin murya mai tafiya da sigar lallab’awa yace. “Zakisha magungunanki yanzu sai na k’ara miki chocolates koâ€? Jin abunda ya fad’a d’inne kuma yasa ta k’wab’e fuska, tare da d’ago kanta ta kalleshi. “No Yah M.Jay ni banason shan magani, saboda akwai d’aci sosai.â€? Tayi maganan cikin muryarta da yafi kama da zallan shagwab’a. Kansa yad’an girgiza mata ahankali kuma, cikin nuna tsananin kulawarsa agareta yace. “I know Ayshnoor amma please kisha kinji, banason kinajin pain, kuma I promise you idan kikasha zan baki duka ledan chocolates d’innan.â€? Idanunta tad’an zaro waje, saboda jin ya ambaci bata duka ledan chocolates yasa ta d’anji sanyi acikin ranta, murmushin daya bayyana white teeth d’inta tayi, cikin gamsuwa da maganar tasa kuma tace. “To zansha.â€? Shid’inma murmushi yayi mata, tare da d’aukan bootle water ya mik’a mata, bayan yasa ta bud’e bakinta ya zuba mata pills d’in. Duk da cewar kuma magungunan akwai d’aci sosai amma haka ta daure ta had’iyesu. Tana gama had’iyewa kuwa ya mik’o mata duka ledan da chocolates d’in ke ciki, wanda ciki kuwa harda babban kwalban Nutella, bud’e ledan tayi tana k’arewa chocolates d’in nata kallo, saidai kuma wani Leda na daban da tagani acikin chocolates d’inne yasata d’agowa ta kalleshi, kaman zatace masa wani abu kuma sai ta fasa, kaitsaye ya ciro ledan tare da bud’e wa. Abunda ta gani acikin ledanne kuma yasa ta sake kallonsa da sauri, had’e da ciro abun ta mik’a masa. Kansa yad’an girgiza mata, tare da nuna ta da hannunsa, cikin sanyi yace. “Naki ne ba nawa ba Ayshnoor.â€? Idanunta tad’an zaro waje,tare kuma dasa hannu ta dafe chest d’inta, cikin d’an yanayin mamaki tace. “iPhone 12promax wow!â€? Lokaci d’aya kuma ta saki Murmushi mai kama da dariya, tare da kamo hannunsa ahankali tace. “Thanks so much Boo.â€? Kansa ya d’an jinjina mata tare dasa hannunsa, ahankali ya shafi gefen fuskarta. Asanyaye cikin kuma muryar dake bayyana kasalan dake tattare dashi yace. “Ayshnoor please help me ki barni nad’anyi bacci ajikinki kinji, I’m tired duk jikina ciwo.â€? Murmushi tayi tare da jinjina masa kai alaman. “To.â€? saboda duk hankalinta naga sabuwar wayarta, da ayanzun take k’ok’arin b’areta daga kwali, sosai taji dad’i musamman da colourn wayan ta kasance milk. Maleek kuwa da gaba d’aya maganin da yasha, ya sauk’ar masa da kasala hannun Laylerh’n ya kama tare da mik’ar da ita tsaye, kana shima ya mik’e bayan ya matsar da kayan da sukayi breakfast d’in gefe. Still kuma yana rik’e da hannunta haka suka nufi d’aki. Suna shiga cikin d’akin kuwa ya rage duk wani haske dake ciki, tare kuma da k’ara gudun AC anutse ya jata zuwa kan gado. Rigar dake jikinta ya zare, tare da hayewa saman gadon ya jawota jikinsa. Atare suka sauk’e wani irin ajiyar zuciya mai k’arfi, saboda yanda d’umin jikin junansu ya ratsa su, musamman Maleek da d’umi da kuma taushin jikin Laylerh’n ya sashi jan dogon numfashi, tare da lumshe Idanunsa ya sake matseta k’am ajikinsa, Tabbas komai na Laylerh’n yayi masa hundred percent, kuma dama abune daya sani tuntuni cewa, Ayshnoor d’in nasa komai nata na dabanne. Tafukan hannayensa ya kifa akan naked skin d’in bayanta, tare da soma shafa jikin nata ahankali. Yanayin daya keyi mata d’inne kuma yasa ta lumshe Idanunta, had’e da sake shigewa cikin jikinsa, saidai kuma yanayin yanda breast d’inta ke gogan chest da kuma nipples d’insa ne yasa duk suka jisu acikin wani sabon yanayi na daban. Almost 17minutes suka kwance ahaka, batare da d’ayansu yaji yanayin ya ishesa ba, saidai ma k’ara samun kansu acikin shauk’in juna da sukayi. Yayinda daga b’angare guda kuwa tuni magungunan da Maleek d’in yasha sun soma aiki, ta hanyar sashi jin wani irin bacci, duk da cewar kuma magungunan daya shad’in pain relievers ne kawai amma suna saka bacci, shiyasa duk yaji jikinsa yayi weak sosai ga kuma idanunsa dake ta faman lumshewa. Yana acikin wannan yanayin ne kuma wani bacci mai k’arfi ya d’aukesa. D’umin numfashinsa da kuma sautin numfashin dake fita ahankali ne yasa Laylerh’n d’an d’ago kanta ta kalleshi, kyakkyawar fuskarsa dake cike da yalwataccen saje ta zubawa ido, bata ko k’yaftawa. Tabbas zata iya rantsuwa akan cewar bata tab’a ganin wani wanda yakai Yah M.Jay d’in nata kyau ba, komai nasa dabanne, musamman zara zaran eye lashes da kuma eyebrow d’insa dake ashirye tsab tsab, ga kuma shining red lips d’insa da yake k’arawa fuskar tasa kyau. Hannunta tasa ahankali ta shafi soft beard d’insa, da akullum shi yake d’auke mata hankali akan fuskarsa. “Yah M.Jay mai kyau ne!!!â€? Tafad’i hakan cikin yin k’asa da murya, tare kuma da sake mak’alewa acikin jikinsa. Difference feeling takeji sosai akansa, saboda feeling d’insa da takeji ayanzun, ba shine takeji da ba, wannan feeling d’in na musamman ne, ba kuma akan kowa ake jin irinsa ba, sai dai akan mutum na musamman, Kamar dai shi da ayanzu ya zamo Mijinta. K’warai takan ga kasantuwarta da Maleek d’in kamar amafarki, haka kuma zamantowanta mata agaresa tamkar al’amara, saidai kuma abune da yake abayyane cewa k’arfi da kuma ikon Ubangiji ya wuce komai, Allah Ne kad’ai keyin komai alokacin da yaso, ya hanaka alokacin da kake buk’ata, ya kuma baka alokacin da kafi tsananin buk’ata. Idanunta da suka ciko da hawaye ta d’an lumshe, tare da sake hugging d’in Maleek d’in sosai, ahankali kuma ta dawo da kanta dake kan k’irjinsa, daidai saitin inda zuciyarsa take, yanayin yanda taji zuciyar tasa na bugawa anutse ne kuma yasa akasalance ta saki murmushi, kasancewar itama maganin da tasha d’in ya somayi mata aiki, dan tuni ta farajin yanayin bacci na satarta, da yake kuma dama akwai gajiya ajikin ta, shiyasa ko mintuna 10 ba arufa ba itama bacci ya d’auketa. *** Aunty Aina’u dake zaune zugum akan sofa ne, tayi saurin d’ago da kanta ta kalli Momy wacce ita d’inma take zaune duk yanayinta babu dad’i. Gyara zama Aunty Aina’u tayi tare kuma da sake kallon Momy’n, cikin kuma nuna sak’ewar guiwanta akan abun tace. “Nikam gaskiya nagaji da way’annan abubuwan da suketa faruwa, yanzu fa almost 2years kenan da mukeson ganin bayan Captain Maleek da wannan shegiyar Laylerh’n amma abun ya kasa yiwuwa, duk wani plant d’in da muka tsara saiya warware, first kin tsara cewar Maleek zainemi Laylerh’n da aurenta amma bamu cimmawa hakan ba, har Najeeb ya saketa, fine naji plant dinki daya yayi aiki, wanda kikasa Najeeb yaje d’aya daga cikin gidajen Maleek ya ga sirrukan soyayyar Laylerh da yake ta b’oyewa tsawon shekaru, saboda haka nema yasa ya sauwak’e mata, bayan nan kuma kince zakisa Maleek ya maida Laylerh’n karuwarsa, amadadin hakan sai gashi ya maida ita matarsa ta sunnah, why duk way’annan abubuwan suke faruwa? hakan na nufin cewa kenan mu bamu da sa’a kwata kwata arayuwa, ga dukiya munaji muna gani amma mallakarta na nema ya zame mana bala’i, koda yake dama anfad’amin cewa har abada bazamu tab’a yin nasara akan LAYLERHMALEEK ba, amma nak’iji, To yanzu kam na tabbatar, kuma Insha Allah Zan cire hannuna akan wannan lamarin saboda yanzu duniya abun tsoroce, baka bi wani da sharri bama yaka k’are....â€? Harara Mom da ta cika tayi fam ta watsa mata tare da cije labb’anta, Tabbas ayanzu ita kad’ai tasan tafasar da zuciyarta keyi akan al’amarin, saboda kwata kwata ma yanzu Abbou Jaheed ya daina sata acikin duk wani al’amura nasa, ya daina fad’a mata komai daya shafesa, domin hatta auren Laylerh da Maleek d’in sai ana Gobe za’a d’aura ta sani, k’warai taji babu dad’i akan hakan, saidai yanzu babban abundake damun zuciyarta shine burinta da har yau yak’i cika, abu mafi tashin hankali kuma da take tsoron faruwarsa, itace ranar da Abbou Jaheed zai san gaskiyar abunda taji ma tana k’ullawa y’ay’ansa. Lallai tasan awannan ranar komai nata yazo k’arshe, saboda Abbou Jaheed bazae tab’a yarda yaci gaba da zama da ita ba, sannan kuma ba haihuwa tayi dashi ba balle tasa ka ran samun wani kaso daga cikin tarin dukiyarsa. Tabbas ayanzu mafita d’ayane ke gareta, kodai tayi regreting abunda ta aikata ko kuma ta sanja taku, saidai abu mafi sauk’i agareta shine yin regreting, Domin da hakan zuciyarta tafi aminta, abune kuma da tasani cewa Allah Yana jin k’an bayinsa masu tuba, matuk’ar kuma ta nemi yafiyan Maleek da Laylerh to tasan Allah Ma zai yafe mata, lallai wannan shine abu mafi sauk’i agareta, saboda tamkar ceton kanta tayi, matuk’ar ta share duk wani mummunan tunani da kuma k’udirin dake cikin zuciyarta, sannan ta kuma gamsu da duk abunda Aunty Aina’u ta fad’a, gaba d’aya duniya ba komai bace saidai idan kaine ka d’auketa wata abar girmamawa, nan kuma gaba d’aya rayuwarka zata k’are awahala da yawan buruka wanda har abada bazasu tab’a cika ba. Jikinta amatuk’ar sanyaye ta kalli Aunty Ayna’u, tare dasa hannu ta d’an matse hawayen dake cikin idanunta, saboda ayanzu ta sakejin gamsuwar cewar idan har ta cutar da Laylerh Maleek har abada Allah bazae tab’a barinta ba. Hannun y’ar uwarta Aina’u ta kamo, cikin muryarta da tayi sanyi sosai tace. “Insha Allah Aina’u bazan sake cutar da rayuwar Laylerh da Maleek ba, kamar yanda bazan sakeyi musu mummunan fata ba, zan kuma nemi yafiyarsu, amma kafunnan dole saina gyara tsakanina da Ubangijina da kuma Mijina, duk da cewar ya watsar dani ayanzu, amma bazan gajiya ba Insha Allah zanyi k’ok’ari wajen ganin na gyara kura kuran da nayi masa, tun ada bansan Meyasa na zamanto Mace mai tsananin son zuciya ba, idanuna sun rufe harta kai ga ina abu kaman ba Musulma ba, na manta cewar Allah Ne keyin yadda yaso, kana na manta cewar idan bai tsara abuba, har abada baya tab’a yiwuwa, lallai Tabbas zan gyara kuskurena, zanyi kokarin zama ta kwarai ko badan kowa ba, kodan saboda kaina da kuma karshena.â€? Rungume Mom d’in Aunty Aina’u tayi saboda, ita dama tuntuni zuciyarta ta jima da karyewa, saboda wani wa’azi da taji, kuma Insha Allah zata nemo wa’azin ta sakawa y’ar uwarta, wanda tayi imani hakan zai sake sawa zuciyar Momyn tayi sanyi, kuma dama tuncan sunsani cewar, duk wani abu da zakayi wanda zai cutar da d’an uwanka ba abu bane maikyau, kuma sannan Allah baya yafe laifin dake tsakanin bawa da bawa, saidai har idan har wanda ka zalunta d’in ne ya yafe maka, To Allah Ma zai yafe maka, duk sun san hakan amma son zuciya da dukiya suka rufe musu ido, sam suka kasa nazartar abunda zai amfanesu. *3:00pm* Daidai ya soma bud’e idanunsa da suka d’an k’ank’ance saboda baccin daya share sama da awanni yanayi. Jikinsa dake had’e dana Laylerh ya zare, tare da zuro k’afafunsa ya sauk’o daga kan gadon, agogon dake sak’ale ajikin bango ya kalla, ganin da yayi kuma lokaci ya d’anja har 3:2 pm ne yasashi mik’ewa tsaye, tare da d’an dafe kansa dake sarawa, sam baisan haka magungunan da suka sha d’in keda k’arfi sosai ba, saboda tun kwanciyarsu da k’yar ya iya tashi yayi sallah’n azahar, koda ya tashi Laylerh’n ma kukan shagwab’a ta saka masa, tare da cewa ita bacci bai isheta ba, haka dai ya lallab’ata tayi sallah’n, bayan ta idar da sallah’nne kuma suka sake komawa wani bacci’n, ba shi ne ya farka ba kuma sai yanzu da la’asar ta kusa. Still kuma ya tashi ne bawai dan baccin ya ishesa ba, saidan yunwan dake damun cikinsa, wanda ya kuma san cewar bashi kad’ai ne yakejin yunwan ba harda Laylerh’nsa. Hannunsa ya daura akan handle din kofar toilet d’in, tare kuma da tura k’ofar kana ya kutsa kansa ciki, kaitsaye gaban babban jakuzzie’n dake cikin toilet d’in ya nufa. Adaddafe ya had’a musu duk wani abu dayasan zasu buk’ata, tare kuma da juye wani turaren wanka mai dadin kamshi acikin ruwan jakuzzie’n. Bayan ya kammala komae ne kuma ya dawo cikin d’akin, tare da zare long jeans d’in dake jikinsa. Direct gaban gadon ya nufa, tare da bud’e hannayensa duka biyu ya d’auki Laylerh’n da har yanzu ke bacci, kaitsaye toilet d’in ya nufa da ita. Still kuma tana jikinsa, ya shiga cikin jakuzzie d’in, kwantar da ita yayi akan chest d’insa tare da lumshe idanunsa, yana mejin yanda ruwan ke ratsa duk jikinsu. Haka kuma d’umin ruwan daya ratsa cikin jikinsu d’inne yasa ta bud’e idanunta akasalance, ta sauk’e ganinta akansa. “Boo!!â€? Tak’ira sunansa ashagwab’e tare da sake manna kanta da jikinsa. “Ummm Shugarnoor!!!â€? Ya amsa mata, da wata irin muryar da dadinta yasata d’an lumshe Idanunta, tare da d’an lasan lips d’in bakinta, cikin yanayin dake nuna jin dad’in mood d’innasu ne kuma ta juyo ta fuskancesa. Idanunsa dake alumshe yad’an bud’e tare da yi mata wani irin kallo’n dayasa duk taji tsikar jikinta ya zuba, Daga cikin ruwan kuwa hannayensa yasa ahankali ya had’e waist d’insa da nata. Atare suka fitar da wani sexual eraction sound. Saboda wani irin abu da sukaji ya ratsa duk ilahirin jikinsu. Harshensa yad’an zaro waje tare da bud’e bakinsa, ahankali yace. *”I LOVE YOU Shugarnoor!!â€? * harshenta ta d’aura akan Lips d’insa daya d’an bud’e su tare, da lumshe idanunta, saboda yanda kalmar tasa ta shigeta sosai, cikin kuma muryarta dake shaking tace. *â€? I LOVE YOU too Boo!!!â€?* *(Love you all guys)* *10:20 pm* 4/12/21, 7:52 AM - Ummi Tandama: *82* Lumsassun idanunsa ya bud’e saboda yanda yaji amo da kuma sautin muryar nata, ya sake hautsuna tunaninsa tare dajin wani irin kasala na musamman. Tabbas yanayin maidad’ine agaresu, irin kuma dad’in da misalta shi keda wahala, saidai ga duk wanda ya kallesu, zai gane hakanne kawai ta yanda suke sake shigewa jikin juna. Sake rungumeta yayi sosai tare da d’aukan soap ya soma goga musu ajikinsu. Sannu ahankali cikin yanayi’n nutsuwa kuma, yayi musu wankan atare. Tare da d’aura towel akan waist d’insa ita kuma ya saka mata bathrobe a jikinta, kama hannunta yayi har zuwa gaban sink suka d’auro alwala. Still kuma yana rik’e da hannunta haka suka fito daga cikin toilet d’in. Yanzun ma shi da kansa ya shafa mata body lotion a jikinta, kamar dai yanda yayi mata da safe. Bayan ya gama shafa mata mai d’inne kuma da kansa ya bud’e wardrobe d’inta ya ciro mata wata net tight pencil gown marar nauyi, mik’a mata rigar yayi tare da yi mata alama akan tasa, kana ya juya shima ya soma kimtsa kansa. Laylerh kuwa ganin ya juya mata bayane yasa ta shirya kanta atsanake tare da zura rigar daya bata d’in a jikinta, saidai kuma kasancewar rigar ya kamata sosai ne yasa duk wani shape d’in jikinta bayyana. Dogon gashinta daya kwanta agadon bayanta ta d’aure, tare da neman waje ta zauna, Idanunta ta tsayar akan Maleek d’in daya gama shirya kansa cikin wasu had’add’un riga da wando. Kamar yanda kuma komai yasa ajikinsa yana yi masa kyau, haka wannan kayan d’in ma sun amshi jikinsa sosai. Juyowan da taga Yayine kuma yasata yin k’asa da kanta tare da kama y’an yatsun hannunta ta shiga murzawa. “Zo muyi sallah.â€? Ya fad’a adaidai lokacin daya gama daidaita tsayuwarsa akan darduma carpet d’in dake shimfud’e agefen gadonsu. Jin abunda ya fad’a d’inne kuma yasa ta mik’ewa tsaye, tare da k’arasawa gaban drawer ta d’auko hijab ta saka a jikinta. K’arasowa wajen da Maleek d’in ke zaune tayi, tare da d’an tsayawa abayansa, daidai lokacin kuwa ya tada sallah. Cikin nutsuwa ta bisa sukayi sallah’n, bayan sun idar da sallah’nne kuma ya kama hannunta suka fita falo. Ganin kuma yanda take ta hamma ne yasashi gane cewar ita d’inma yunwa takeji sosai. Akan d’aya daga cikin kujerun falon ya zaunar da ita, tare da k’arasawa gaban fridge ya d’auko musu, babban goran fresh yoghurt da kuma cups. Bayan ya zuba musu yoghurt d’in acikin cup ne kuma, ya zauna akusa da ita, tare da soma bata yoghurt d’in abaki tana sha ahankali. Saida kuma tasha fiye da rabin cup d’in kafun ta janye kanta ahankali, tare da karb’an cup d’in daga hannunsa, ahankali takai bakinsa kamar yanda yayi mata. Duk da cewar kuma baiso shan yoghurt d’inba, amma ganin da yayi cewar Laylerh’nne zata basa yoghurt d’in da kanta, ya sashi bud’e bakinsa anutse ya soma sha. Bai kuma janye kansa ba har saida duka yoghurt d’in dake cikin cup d’in ya k’are. “Ka k’oshi?.â€? Ta tayi masa tambayar alokacin da ta ke saka tissue ta goge masa bakinsa, da duk ya b’aci da yoghurt d’in. “Eh, kefa?.â€? Ya dawo mata da tambayar. “Nima.â€? Tafad’a asanyaye tare da ajiye cup d’in dake hannun nata, ta kwantar da kanta akan chest d’insa. Idanunta da har yanzu ke cike da bacci ta d’an lumshe, saboda kwata kwata sam baccin da tayi d’in bai isheta ba, Dan ji yake kamar ma yanzune maganin da tasha zai soma aiki. Shikuwa Maleek ganin yanda Laylerh’n ta lafe acikin jikinsa ne, yasashi soma shafa bayanta ahankali, saboda tun d’azu ya fahimci cewar bawai baccin da tayin ya isheta bane. Aikuwa shafata daya soma yid’inne yasa ta sake narkewa ajikinsa, cikin k’ank’anin lokaci kuwa ta sake maida baccinta. Shid’inma idanunsa ya d’an lumshe adaidai lokacin da yaji d’umin numfashinta na sauk’a acikin jikinsa. Wanda kuma hakan alamace dake nuna masa cewar Laylerh’n tayi bacci. “Ayshnoor!â€? Ya k’ira sunanta akasalance, jin bata amsa shi bane kuma yasa shi sake gyara mata kwanciyarta, tare da zaro waya da kuma earpiece d’insa dake cikin aljihun wandonsa, sak’ala earpiece d’in yayi acikin kunnensa, tare da kunna wak’ar Aligatie (Running on my mind) yana saurara. Yanayin yanda yayi da idanun nasa ne kuma, yasa duk wanda ya gansa zaiyi tunanin cewar bacci shid’in ma yakeyi kamar dai yanda Laylerh’n keyi. Ahankali Oum Ayush dake tsaye abakin k’ofar da zai sada ta da falon saman ta juyo ta kalli su Abbou Jaheed dake bayanta, wanda ayanzu sun share sama da 10minute suna tsaye abakin k’ofar suna ta doka sallama da knocking amma ba’a amsa musu ba. “Anya suna nan kuwa?.â€? Abbou Khareem ya tambaya, saboda yanda suka share tsawon mintuna suna knocking k’ofar batare da an bud’e musu ba. “Sunanan Oum Ayush bud’e mana k’ofar falon mushiga.â€? Abbou Jaheed ya fad’a atak’aice saboda ya gaji da tsayuwa awajen. Hannu Oum Ayush tasa ta murd’a handle d’in k’ofar ahankali, tare da tura kanta cikin falon kana su Abbou Jaheed dake tsaye suka rufa mata baya. Turus haka suka tsaya gaba d’ayansu, saboda tozali da idanuwansu sukayi musu da Maleek wanda ke zaune akan sofa ya lumshe idanunsa, Yayinda Laylerh’n ke jikinsa, da dukkan alama kuma dukansu bacci sukeyi. Wani irin murmushi mai d’auke da tsananin farinciki ne ya bayyana akan fuskar kowannensu, musamman ma Abbou Jaheed daya kasa d’auke idanu akansu, saboda yanda yaga sunyi matuk’ar dacewa da juna, wanda ayanzu ya sake tabbatarwa kansa cewar Lallaine Maleek da Laylerh ya dace, haka itama Laylerh’n da Maleek ta dace. Saidai kuma tuna irin tarin k’addarorin da suka fuskanta ne yasa shi jin idanunsa sun ciko da k’walla, Domin har yau ya kasa iya cire damuwar mummunan k’addarar da ta auku acikin rayuwar Maleek d’in, saidai kuma ya sani cewar Allah Baya tab’a d’aurawa bawansa abunda bazae iya ba, saboda haka yayi imani cewa komai yayi farko zaiyi k’arshe, idan kuwa k’addara ta dindince, to Allah Yakan sawa zuciyar bawa salama, tare kuma da k’arfin jure k’addarar da ta sameshi. Oum Ayush da fuskarta ke cike da yalwataccen murmushi ne, ta k’arasa shigowa cikin falon, tare kuma dasa hannunta ahankali tad’an tab’a kafad’ar Maleek d’in, saboda duk atunaninsu bacci yakeyi. Sab’anin gaskiyar lamarin daya kasance, idanunsa kawai ya lumshe amma bawai baccin gaske ya keyi ba, bai kuma ji knocking d’innasu bane saboda ya saka earpiece akunnensa, sannan ya kuma k’ure volume d’in wak’ar da yakeji. Jin da yayi antab’a kafad’ansa ne kuma yasashi ware idanunsa ahankali, tare da sauk’esu akan Oum Ayush dake tsaye tana sakar musu murmushi. Idanun nasa yad’an zaro waje tare da d’an saurin gyara zamansa. “Oum Ayush.â€? Yak’ira sunanta cikin yanayin dake bayyana mamakin ganinta. Oum Ayush kuwa hararan wasa ta watsa masa, tare dasa hannu ta d’an buge kanshi, cikin kuma nuna masa tsananin kulawa tace. “Wato dama ba bacci kakeyi ba, shine kanajin mu muna knocking nida su Abbou Jaheed amma kaki bud’ewa ko, to gamu mun shigo.â€? Murmushin daya d’an bayyana hak’waransa yayi, tare da juyawa ya kalli su Abbou Khareem da suka k’araso cikin falon suka zauna. Ahankali ya sakarwa Abboun nasa murmushi, tare da dawo da kallonsa ga Laylerh dake kwance ajikinsa tana bacci. Batare kuma da yaji kunyan su Abbou Jaheed dake cikin falon ba, ya d’aura bakinsa adaidai saitin kunnenta, cikin muryarsa dake fita slowly yak’ira sunanta, tare kuma da hura mata sassanyar iskan dake bakinsa. Ashagwab’e tad’an motsa tare da sanya hannayenta ta mak’alesa, Domin duk da kasancewar bacci takeyi amma hakan bai hanata jin sautin muryarsa acikin kunnuwanta ba. “Ayshnoor!â€? Ya sake k’iran sunanta akaro na biyu, tare dasa hannunsa ya tallafo hab’arta cikin muryar dake bayyana shauk’inta akansa yace. “Wakeup Ayshnoor nah Oum Ayush da Abbou Jaheed nefa suka zo.â€? Tamkar wacce aka zabura haka ta bud’e idanunta, tare da d’an d’agowa ta kalleshi. Da idanu yayi mata alama akan ta juya ta kalli su Abbou’n. Da atunaninta wasa Yah M.Jay d’in keyi mata, amma kuma ganin da gaske yakeyi ne yasa tayi saurin juyowa, ai kuwa atake ta sauk’e Idanunta akan su Oum Ayush d’in, da sauri ta diro daga jikinsa, tare da fad’awa jikin Oum Ayush d’in ta rungumeta k’am, cikin muryar dake bayyana zallar shagwab’a tace. “Nayi kewarku Oum Ayush nah.â€? Murmushi Oum Ayush tayi tare dasa hannunta tashafa kan Laylerh’n, murya d’auke da farinciki tace. “Nima nayi kewarki sosai Laylerh, amma kwana d’aya ne fa kawai tak, gashi kuma naga aure yayi dad’i har kinsaba da mijin naki.â€? Saurin sanya tafukan hannayenta tayi ta rufe fuskarta, tare da zame jikinta daga na Oum Ayush d’in ta zauna akusa dasu Abbou Jaheed, tare kuma da gaishesu akunyace, saboda sosai maganan da Oum d’in ta fad’a yasata jin kunya. Su Abbou Jaheed kuwa fuska asake duk suka amsa mata gaisuwan nata, tare da tambayarta jikinta, saboda kafun suzo Oum Ayush ta fad’a musu cewar batajin dadi. Akunyace duk ta amsa musu gaisuwar tasu, tare da mik’ewa ta kawo musu drinks da ruwa. Still dawowa tayi ta zauna akusa da Abbou’n, wanda suke d’an tab’a hira sama sama da Abbou Khareem. Bayan kuma sun d’ansha drinks din da takawo musu d’inne, Abbou Khareem ya d’anyi musu Nasiha, irin wanda iyaye keyiwa yayansu idan sunyi aure. tare da bawa Laylerh’n atm card d’in bank d’in daya sa mata sadakinta na aure aciki. Kasancewar kuma yammaci ya danyi ne yasa basu wani jima ba sukayi musu sallama, har waje kuwa Laylerh da Maleek d’in suka rakosu, gefe Oum Ayush ta jawo Laylerh’n tare da tambayarta batun ciwon mararta, da sauki ta bata amsa, saboda tun adaren jiya ta nemi ciwon marar nata ta rasa. wani abu me kaman chocolates Oum Ayush d’in ta bata, tare da tabbatar mata cewar kullum tasha guda d’aya, zai taimaka mata sosai. Godiya tayiwa Oum Ayush d’in, bayan kuma sun tafi ne Maleek ya kama hannunta suka koma cikin gida. Suna shiga cikin falon nasu kuwa wayar Maleek din ta soma ringing, ganin sunan Fou’ad akan screen din wayarne kuma yasashi saurin picking call din tare da kara wayar akan kunnensa. Daga b’angaren Fou’ad kuwa jin Maleek ya daga wayarne yasashi d’an gyara zamansa tare da shafa sumar kansa, cikin yanayin dake bayyana tsananin farincikinsa yace. “Kagama yangan angwancinka nima soon zan angwance malam, saboda na samu mata ajiya kawai har mun daidaita tsakaninmu Insha Allah zamuyi aure nan bada jimawa ba.â€? Murmushi Maleek d’in yayi, tare da d’an lumshe idanunsa ahankali yace. “Naji To Wacece matar?â€? “Aleeyah frnd din Laylerh mana, gaskiya babe din ta hadu, yanzu ma maganan da nake maka fa harna fadawa Abbana, yace nanda 3daya zaije gidansu, kai intak’aice maka dai Insha Allah nanda 2weeks Ina da mata, nima nagaji da zama hakaâ€? Murmushi Maleek d’in yayi, batare kuma da yace komai ba ya katse kiran, saboda yasan halin Fou’ad matuk’ar ya biye masa to zai ta damunsa da surutu ne, shikuwa ayanzun akwai abunda yakeson aiwatarwa. Kallon Laylerh dake gefensa yayi, tare da manna mata kiss a forehead dinta, asanyaye yace. “Bari naje wani waje Ina dawowa yanzu.â€? Kai ta jinjina masa alaman to, shikuwa Cikin hanzari ya juya ya fita, ganin kuma da tayi cewar zama waje Dayan zai takurata ne yasa ta jawo sabuwar wayarta tare da soma setting d’in abubuwa Domin ayau takeson fara amfani da ita. Ab’angaren Maleek kuwa yana fita daga cikin gidan, kai tsaye hotel ya nufa, saboda acanne yake da yakinin samun mutumin da yake nema. *(Yau nayi yping mai yawa amma ya goge😭 yanzu kuma wallahi bacci nakeji)* *10:06 pm* 4/13/21, 11:27 AM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK* *Writting by* fatymasardauna *Note editing* *CHAPTER 83* 8:30 pm daidai ya shigo cikin gidan, idanunsa ya zubawa Laylerh dake kwance akan sofa, Yayinda wayarta ke d’aure asaman chest d’inta, wanda da dukkan alama kuma amfani take da wayar bacci b’arawo ya d’auketa. Murmushi yayi tare da k’arasowa cikin falon ya ajiye ledodin dake hannunsa. “Ayshnoor!â€? Yak’ira sunanta ahankali tare dasa hannunsa yad’an bubbuga k’afarta. Kasancewar kuma baccin nata baiyi nisa sosai bane, yasa ta bud’e idanunta, ganinsa da tayi d’inne kuma ya sata d’an shagwab’e fuska, aksalance tace. “Shine katafi ka barni ko Boo!â€? Yanayin yanda ta k’are maganar tana me d’an karyar da wuyane kuma yasa shi, d’an lumshe idanunsa, tare da kamo hannunta ya tada ita zaune, cikin muryar dake bayyanar da kulawarsa agareta yace. “I’m very sorry Wifey, naje wani waje mai mahimmanci ne, bayan haka kuma na sayo miki ice cream.â€? Jin yace ya sayo mata ice cream ne kuma yasa tad’an sake fuskarta, saboda dama tayi missing ice cream sosai. D’aya daga cikin ledodin daya shigo dasu d’in ya mik’a mata, tare da shafa kanta, kana akasalance ya mik’e ya nufi hanyar bedroom. Da kallo ta bisa, saboda yanda taga yana tafiyan, da dukkan alamu agajiye yake, har saida ya shige cikin bedroom d’in nasu kuwa kafun ta d’auke kanta daga kallosa, tare da bud’e ledan daya bata ta ciro babban robar ice cream, atsanake ta soma sha, time to time takan maida idanunta ga tv, saboda kallon wrestling da takeyi. Ab’angaren Maleek kuwa yana shiga bedroom din kayan jikinsa ya rage, tare da wuce bathroom kaitsaye, ruwa ya sakarwa kansa tare da d’an lumshe idanunsa, lokaci d’aya kuma magangun da sukayi da Najeeb ya shiga dawowa cikin tunaninsa. Wani irin sassanyar murmushi yayi, tare dasa hannayensa ya dafe bango, Tabbas kamar yanda Najeeb d’in ya fad’a shine mutumin daya fi dacewa, da Laylerh, Domin ita d’in gaba d’aya rayuwarsa ce, itace komai nasa dama duk wani farincikinsa, shi kansa baisan wani irin so yakeyiwa Laylerh’n ba, saidai koma mene yayi imani cewar yana sonta fiye da yanda yakeson kansa, zai kuma iyayin rayuwa da ita ako wani irin yanayi, yana da kuma kyakkyawar gamsuwar cewa zasu rayu shida itad’in rayuwa ta har abada. Atsanake yayi wanka, bayan kuma ya fito daga cikin toilet dinne ya saka wani long trouser ajikinsa, tare da shafa turarensa mai dad’in k’amshi. Wayarsa dake kan gado ya dauka tare kuma da juyawa ya nufi falon. Har yanzu tana nan zaune akan kujerar daya barta, saidai zuwa yanzu ta shanye Ice cream dinnata, Yayinda takai sauran Roban ice cream din cikin fridge ta ajiye. K’arasowa cikin falon yayi, bayan ya zauna akan carpet ne, kuma yasa hannunsa ya jawo Laylerh’n jikinsa, tare da soma bubbud’e ledodin daya shigo dasu. Wanda cikinsu ke cike da kayan ciye ciye. Kamar kuma yanda ya sabawa Laylerh’n, yanzu ma shida kansa ya ciyar da ita, saida kuma ya tabbatar da ta koshi kafun ya kyaleta taje tayi wanka. Kasancewar kuma shima bai damu da cin abinci sosai bane, yasa sama sama yaci shawarma da kuma fresh milk din daya sayo. Ahankali ya d’aga kansa ya kalli agogon dake cikin falon, wanda ke nuna k’arfe 9:00 pm daidai. Har zuwa lokacin kuwa Laylerh’n bata dawo cikin falon ba. Mik’ewa tsaye yayi tare da k’arasawa ya kashe tv da kuma hasken dake cikin falon, bayan kuma yayi locked na k’ofar falonne ya nufi daki kai tsaye. Shigansa cikin dakin kuwa yayi daidai da fitowar Laylerh daga cikin toilet, wanda take daure da d’an karamin towel ajikinta. Hannayensa ya ware mata tare kum da d’an karyar da wuyansa gefe, cikin kuma muryar dake bayyana kasalan da yakeji yace. “Please Ayshnoor hug me!â€? Murmushi mai sanyi tayi tare da k’arasowa, ta fad’a jikinsa kamar yadda ya buk’ata. Jin jikinta mai d’auke da danshin ruwa acikin nasa jikinne kuma yasashi, maida hannayensa ya rufe, tare da d’aukanta ahannayensa ya nufi kan gado da ita. Kwantar da ita yayi tare da bin jikinta shima ya kwanta, yana me shak’an k’amshin dake fita ajikinta. “Ayshnoor!!â€? Ya k’ira sunanta asanyaye, tare kuma dasa hannunsa ya warware towel d’in dake jikinta. Jin muryarsa acikin kunnuwanta ne kuma yasa ta lumshe Idanunta, tare da jan wani dogon numfashi, adaidai lokacin da taji saukan hannunsa asaman mararta, yana shafawa slowly. Shid’inma numfashin ya shiga sauk’ewa akai akai, saboda yanda hannunsa ke yawo akan soft skin dinta, yasa shi jin wani sabon feeling na taso masa. Ahankali yad’an zame tare da jawota saman jikinsa, bayan ya zare gaba d’aya towel din dake jikinta. Hakan da yayi d’inne kuma ya bawa chest d’insu daman had’ewa, wanda take taushi da kuma laushin breast d’inta, ya sashi Jin kansa acikin wata duniya ta daban. Ahankali ya maida kansa k’asa tare da soma fitar da wani irin numfashi, mai kama da sexual eraction. Laylerh da ke kwance asaman jikin nasa kuwa, Jin irin numfashin da yake fitarwa ne, yasa ta d’aura hannunta akan zanen tattoo din dake jikinsa, tare dasa yatsarta d’aya ta soma zagaye rubutun dake kwance agefen cikinsa. “Ayshnoor!â€? Ta fad’i kalmar da taga anrubuta da tattoo din ajikinsa. Yanayin yanda tayi maganan murya ad’an sanyaye ne, kuma yasa shi bud’e fitinannun idanunsa masu cike da yanayin sha’awa. Ita kuwa Laylerh yalwataccen murmushi ne ya bayyana akan fuskarta. Take kuma ta sake aminta cewar Lallai soyayyar da Yah M.Jay din keyi mata, yakai soyayya tunda har zai iya rubuta sunanta ajikinsa. Dad’in ganin hakanne kuma yasa ta d’aura d’an karamin Bakinta, adaidai kan tattoo din, tare da sakar masa professional kiss din dayasa numfashinsa tsayawa na wucin gadi. Musamman saboda yanda yaji kiss din ya ratsa duk jikinshi. Take kuma yaji feeling d’in dake jikinsa ya sake k’aruwa, dan kuwa har wani har bawa yakejin jijiyoyin dake mararsa nayi. Ahankali ya d’ago kansa tare da sake d’an mirginawa ya kuma dawo da Laylerh’n k’asan sa. Bakinsu ya had’e waje d’aya tare da soma kissing dinta, saboda zuwa yanzun amatuk’ar buk’ace yake da ita. Laylerh kuwa Ganin yanda lokaci daya nutsuwarsa tabar jikinsa ne yasa itama ta soma mayar masa daduk wani salo da yake gwada mata. Wannan dalilin yasa cikin abunda bai wuce 13mn ba gaba d’aya suka fice acikin hayyacinsu. Yayinda ko wannensu ya fad’a cikin wata duniya ta daban. Aikuwa yauma Laylerh bata tashi shid’ewa ba, saida taji sauk’an harshe da kuma lips d’insa acikin jikinta, yana yi mata wani irin sucking na musamman. Da yasa numfashinta kusan d’aukewa. Saurin k’ank’amesa ajikinta tayi tare da sakin wani irin numfashin dake nuna cewar takai k’ololuwa acikin sabuwar duniyar da ya sakata. Wanda kuma ba ita kad’ai kejin kamar zata zauce ba harda shi. D’ago kansa yayi tare da kawo bakinsa daidai saitin kunnenta, cikin wata irin muryar dake bayyana zaucewa da kuma kaiwa kololuwa yace. “Please Ayshnoor ki sake trusting dina, nayi alkawari at this time bazanyi hurting naki sosai kaman jiya ba.....â€? Ya k’are maganar cikin harhad’ewar muryar dake bayyana halin da yake ciki. Itakuwa Laylerh Idanunta dake alumshe ta rumtse, tare da sanya hannayenta duka biyu ta lama shoulder d’insa. Tabbas tana jin tsoro da kuma farga ba, Domin har yanzu bata manta da radadin da taji daren jiya ba, saidai kuma amma tayaya zata hana shi abunda yake mallakinsa? Ita kanta ayau tana buk’atar kasancewa da Yah M.jay din nata. Har abada bakuma zata tab’a hanashi duk wani abu dake jikinta ba, koda kuwa zafin abun ya wuce tunani da hankalinta. Lallai zata jure akan komai dan kawai shi ya samu gansuwa. Kai tad’an jinjina alaman ta amince masa akan komai. Hakan da yagani dinne kuma yasashi hade bakinsu waje d’aya adaidai lokacin da yake shiga cikin jikinta. Gaba d’ayansu kusan zaucewa sukayi saboda wani irin sabon abu da sukaji ajikin junansu na musamman. Wanda har ya kaisu ga kasa jurewa. Musamman awajen Laylerh da abun yazo mata a wani yanayi na daban, wanda har hakan ya sata sakar masa kuka, tare da rungumesa acikin jikinta. Lallai awajen Maleek daren jiya dana yau din na musamman ne, Saboda sun sakashi manta duk wani abu, Duniyar da yakejin kansa aciki kuwa ta sakashi makancewa, saboda gaba daya idanunsa rufewa sukayi. Yayinda labb’an bakinsa kuwa suka kasa had’ewa waje guda. Kamar kuma yanda yake enjoying mood din haka ma Laylerh keyi, saboda zafin da takeji yaudin baikai na daren jiya ba, kuma sannan kamar yanda yace bazai yi hurting nata ba, baiyi d’in ba, wanda hakanne ma yasa ta jin wani irin feeling na musamman tare kuma da d’an soma enjoying mood d’innasu. After 49mn Ajiyar zuciya yake ta sauk’ewa akai akai, tare kuma dasa hannayensa duka biyu ya d’ago Laylerh’n, da ke kwance gaba d’aya jikinta yayi weak. Kaitsaye toilet ya wuce da ita tare da sata acikin bathtub, bayan kuma yayi mata duk wani abu daya dace ne ya taimaka mata tayi wanka. Saboda ya fahimci cewar ya habitat da ita sosai. Shid’inma wanka yayi, bayan sun fito daga cikin toilet dinne kuma, da kansa ya shiryata cikin wata doguwar rigar bacci. Tare da d’aukanta ya kwantar da ita akan gado. Bayan kuma ya rage hasken wutan dake cikin dakinne shima ya dawo ya kwanta ajikinta. Kasancewar kuma dukansu agajiye suke ne, yasa cikin abunda bai wuce 18mn ba duk bacci mai nauyi ya d’aukesu. Washegari. K’arfe 10 daidai suka tashi tun komawarsu bacci da sukayi bayan sunyi sallan asuba. Saidai kuma yaudin ita da kanta ta shiga kitchine tayi musu breakfast. Da misalin karfe 12 daidai kuwa Theemah da Aleeya suka zo, wanda kuma Fou’ad ne ya kawosu acikin motarsa. Zuwansu dinne kuma yasa Maleek tafiya yabar musu gidan, hakanne kuwa ya basu daman yiwa Laylerh’n tsiya yadda suke so. Bayan sun ci abinci ne kuma Laylerh’n ta d’ago ta kalli Teemah dake ta faman matsa wayarta. Hannun Teemah Laylerh’n ta kamo, tare da gyara zamanta asanyaye tace. “Teemah inason magana dake.â€? Jin hakanne kuma yasa Teemahn dakatawa da abunda takeyi, tare kuma da d’ago Kai ta kalli Laylerh’n. D’anjim Laylerh tayi na tsawon minti daya, saboda batasan ta yanda Teemah’n zata d’auki maganar ba, saidai kuma koma meye tana saka rai da fatan amincewar k’awartata. Hannun Teemah’n dake cikin nata ta rik’e da kyau, tare da d’an karyar da wuyanta, cikin sanyin murya tace. “Dan Allah Teemah kimin wata alfarma, wacce kuma nasan bazata tab’a ga gararki ba, nasan zaki iya Teemah saboda inajin hakan amatsayin alkhairi.â€? Idanu Teemah’n ta d’an zubawa laylerh’n cikin kuma yanayi nad’an mamaki tace. “Wace irin alfarmace Laylerh, ki fad’eta kawai kai tsaye.â€? “Inaso ki auri Najeeb Teemah, Domin ke kad’ai ce macen da na aminta cewar, zaki basa ingantaccen farinciki, nasan zaki goge masa duk wani damuwa dake cikin zuciyarsa, wallahi Teemah Najeeb bashi da makusa ko kad’an, sannan yana da kyau da nagarta, da kuma kyawawan halaye, shid’in Namiji ne kuma abunso ga kowacce mace, lallai tabbas nasan idan kika auresa zaku samawa juna farinciki, Insha Allah kuma zakuyi alfahari da kasancewarku atare, ina me rokonki kada kice aa Teemah, kada kuma kice wai dan ya tab’a aurena ke bazaki iya aurensa ba, kinsani babu abunda ya tab’a shiga tsakanina dashi, bai tab’a kusantata ba, kuma koda ma ace ya tab’a sanina amatsayin ya mace bana tunanin wannan zaisa ki ki aurensa, Domin nidake ba ya da kanwa bane, kuma koda ace har yau ina nan amatsayin matarsa, To aurenki dashi ba haramun bane halaltacce ne, dan Allah Teemah Kada kice aa.â€? Idanu Teemah’n tad’an zaro waje tare dasa hannu ta dafe kirjinta, cike kuma da mamakin abunda Laylerh’n ta fad’i ayanzun tace. “Anya kuwa Laylerh kinsan me kike fad’a? cewa fa kikayi ma auri Najeeb, tsohon mijinki, Chab gaskiya bazai yi wuba, bandamu ba koda akwai abunda ya shiga tsakaninku, nidai gaskiya bazan aureshi ba, bayan haka ma nifa sam banason second din Namiji sabo nakeso.â€? Tak’are maganan tana me d’an murgud’a bakinta. Wanda kuma hakanne yasa Laylerh da Aleeya sakin murmushi, saboda duk sun San halin Teemah’n tana da kafiya sosai. Again kafadun Teemah’n Laylerh ta dafa, tare da kwantar da muryarta yanda tasan Teemah’n zata fahimta, cikin sanyi tace. “Dan Allah Teemah ki amincewa auren Najeeb, ki kawar da duk wani tunanin dake cikin rai da zuciyarki, Insha Allah zakiyi farinciki da hakan, kinga Aleeya yanzu ta amince da Fou’ad za kuma ayi bikinsu nan bada jimawa ba, mun riga da mungama secondary school Teemah, kada ki manta ako da yaushe ke kike fad’amin cewa, idan dama ta sameka kada ka tab’ayin kuskuren wasa dashi, yanzu dama ta sameki Teemah why zakiyi watsi da ita? sannan awannan rayuwar tamu Kinsha fad’amin cewar, rufin asirin kowacce mace budurwa dake tasowa shine yin aure, saboda alokacin da tayi sake ta haurawa shekaru 20 batare da tayi aure ba, samun irin future husband d’in da take da muradi zaiyi mata wahalar samuwa, sam kada ki bari hakan ta kasance dake Teemah, ki mori k’uruciyarki ta hanyar yin aure yafi ki k’are k’uruciyarki awaje ba tare da aure ba, Tabbas aure lokaci ne amma idan naka lokacin yazo kada kayi wasa dashi, saboda watarana zaka so lokacin ya dawo, amma kuma yayi Nisan da juyowansa zaiyi wahala.â€? Idanu Teemah’n ta d’an lumshe tare da jinjina kanta, Tabbas tasan duk maganganun da Laylerh’n ta fad’i haka suke, za kuma taso ace itama tayi aure da yarintarta. Saidai kuma daga wani sashi na zuciyarta tanajin nauyin abun, kanta tad’an sunkuyar k’asa tare da murza yatsun hannunta cikin sanyi tace. “Na amince da maganganunki Laylerh but bansan tayaya Najeeb zai daukeni ba, saboda bani da tabbaci akan cewar yana sona ko a’a.â€? Murmushin tsananin jin dadi Laylerh’n tayi, tare dasa hannayenta duka biyu ta rungume Teemah’n, cikin kuma nuna tsananin farincikinta tace. “Nagode sosai Bestie Tee kuma Insha Allah Najeeb bazai tab’a kinki ba, saboda ke macece irin wanda kowani namiji zaiso samu, Insha Allah Kuma zakiyi farinciki da hakan.â€? Murmushi sukayi dukansu, cikin kuma farincikin da ya mamaye gaba d’aya zuciyarsu suka ci gaba da hira. Sunanan atare kuwa har 4 su suka taimakawa Laylerh’n tayi abinci, bayan ta fito daga wankane kuma suka sake zama wata hirar. Jin ana knocking kofar falonne kuma yasa Laylerh’n tashi taje ta bud’e, aikuwa tana bud’ewa idanunta sukayi tozali da Fou’ad, saidai kuma wanda ta gani abayan Fou’ad dinne yasata d’an zaro Idanunta waje, Cikin yanayin mamakin ganinsa tace. “Yah Najeeb.â€? “Na’am LaylerhMaleek.â€? Najeeb din ya amsa mata fuskarsa dauke da murmushi. Itadinma murmushin tayi tare Kuma da matsawa ta basu hanya suka wuce cikin falon. Ganinsu dinne kuma yasa Teemah saurin sadda kanta kasa. Itakuwa Laylerh direct ruwa da drinks ta tafi kawo musu. Adaidai lokacin da Najeeb din ke kokarin zama ne kuma idanunsa suka sauka akan Teemah, hakanan kuma at the first time daya samu kansa da kasa dauke idanunsa akanta, cikin yanayin tsokana ne kuma yace. “Teemah ba’a ji da ganinki sai awajen bestie’n ki ko.â€? Jin abunda ya fad’a dinne kuma yasa Teemah’n ta saki murmushi tare da gaishesa. Fuskansa asake ya amsa mata, daidai lokacin kuwa Laylerh ta cika musu gabansu da kayan drinks dana ciye ciye. Sake sabon gaisawa sukayi, cikin kuma yanayinta na shagwab’a tace. “Da fushi nakeyi dakai Yah Najeeb, but yanzu komai ya wuce.â€? Murmushi yayi tare da d’an shafa sumar kansa, k’asa k’asa kuma yake kallon Teemah. Ahaka dai suka dan sha drinks din da Laylerh’n ta kawo musu bayan Fou’ad ya sanarwa Laylerh’n cewa tun d’azu tare suke da Maleek, saidai jin zasu taho nan dinne yasashi wucewa wajen da yakeyin gym. Hira sukayi sosai dukansu, acikin hirar tasu ce kuma Laylerh take fadawa Najeeb cewar ta kama masa Teemah amatsayin mata. Ga mamakinsu kuma sai gani kawai sukayi Najeeb d’in yayi murmushi, tare da cewa. “To na amince Allah yasanya alkhairi.â€? Da “Ameen.â€? Suka amsa su dukansu, tare da d’an ci gaba da tab’a hira. Saidai kuma ganin yamma na dad’ayine yasa Najeeb yace su Teemah’n su tashi su sauk’esu agida. Hakan kuwa akayi har waje Laylerh’n ta rakosu, bayan taga tafiyarsu ne kuma ta juya ta koma gida. Acan b’angaren su Najeeb kuwa, tun acikin mota shida Teemah suka daidaita kansu, tare da yin exchanging phone number. Bayan sun sauke Teemah dinne kuma suka biya suka sauke Aleeya agida. Acan gidan Laylerh kuwa ana kiran sallan magriba Maleek ya dawo, haka Laylerh’n ta cika masa cikinsa da abincin da ta dafa, koda dare yayi kuwa yau dinma soyayyarsu suka sha, wanda dadinta yasa duk suka zautar da juna. Washegari kuwa suna zaune afalo sukaji ana musu knocking door, Maleek da kansa ya bud’e kofar saidai wacce ya gani dinne kuma yasashi hade fuskarshi. Momy da Aunty Aina’u dake tsaye kuwa gaba daya jinin jikinsu suka sha, duk da cewar dama sunsan zasu fuskanci hakan. Laylerh kuwa ganinsu Momyn da tayine yasata d’an fad’ad’a murmushi’nta, cikin nuna jindad’in zuwan nasu tayi musu iso, tare da kawo musu drinks. Akunyace haka dukansu sukasha drinks din, cikin kuma yin k’ank’an dakai Momy tashiga neman yafiyan Laylerh da Maleek d’in, tare da nuna musu cewar abubuwan da tayi abaya bata kyauta ba, musamman akan Laylerh, sannan kuma da bakinta ya fad’a musu cewar itace tayi sanadiyar da Najeeb ya saki Laylerh, saboda kiransa da tayi awaya, ta masa kwatancen gidan Maleek dake Asokoro inda yaje yaga duk wani sirri akan soyayyar Laylerh da Maleek d’in yake b’oyewa, sosai ta nuna musu cewar tayi nadama. Shidai Maleek kallonta kawai yakeyi batare da yace komai ba, saboda dama yawan magana ba al’adarsa bace. Laylerh kuwa ganin hawaye a idanun Mom dinne yasa ta cewa ta yafe mata, dama ita Momyn batayi mata komai ba, tunda bata tab’a yi mata wani babban abu na cutarwa gaba da gaba ba. Maleek kuwa duk yanda Momyn taso yace wani abu kincewa yayi, saidai acikin zuciyarsa ya raya cewa ya yafe mata. Haka Momy da Aunty Aina’un suka tashi suka tafi, saidai sun d’anji sanyi acikin zuciyarsu saboda Laylerh’n da sukafi zalunta tace ta yafe musu. A kuma ranar ne Alhaji Ahmad da Abbou Jaheed suka je suka nemawa NAJEEB auren Teemah, saboda kuma da mutumcinsu ne kuma yasa take mahaifin Teemah’n ya amince, Cikin aminci kuma suka nemi da asaka musu lokacin biki ba kuma sason lokacin yazo da tsawo, dayake kuma mahaifin Teemah’n attajirin gaske ne, take yace ya yanke biki nanda sati biyu. Godiya sosai su Abbou Jaheed sukayi masa, atake kuma suka bada kudin aure domin dama su already ashirye suke. Ahaka dai suka baro gidan su Teemah’n zuciyarsu babu ko digon damuwa. Kamar kuwa yanda aka tambayowa Najeeb din auren Teemah yau, haka aka tambayowa Fou’ad auren Aleeya kuma duk ayau d’in, inda nan ma aka yanke biki nanda sati biyu masu zuwa. Tun a washegarin ranar ne kuma grooms din suka soma Shirye shiryen biki. Yayinda ab’angaren Laylerh da Maleek kuwa wani irin sabo mai tsananin k’arfi da soyayya ne ta sake tsakaninsu, wanda kuma ayanzu har Laylerhn ta saba da yanayin feelings din Maleek dinnata, Domin ya koyar da ita kuma ta dauka, saboda hakanne ma kuma yasa akoda yaushe suke cikin feeling din junansu. Two weeks Tabbas rana bata k’arya kome akasa sai lokacinsa yazo, Domin yau ta kasance ranar Asabar kuma ayau d’inne aka d’aura auren Najeeb da amaryarsa Teemah, sai kuma Fou’ad da amaryarsa Aleeya inda dukkaninsu suka biya makud’an kud’ad’e amatsayin sadaki. Bayan an d’aura aurenne kuma akayi walimah, yamma nayi kuwa aka d’aiki kowacce amarya aka kaita gidanta. Inda aka kai Teemah had’add’en gidan Najeeb dake Wuse zone 2 sai kuma Aleeya inda aka kaita gidan Fou’ad dake asokoro. Koda dare yayi kuwa kowani groom ya shiga d’akin bride d’insa, tare da nuna mata irin nasa salon da kuma kaunar da yakeyi mata. Ab’angaren su LaylerhMaleek kuwa aranan suma amarcinsu suka ci, Domin kullum Maleek d’in sake jin Laylerh’n nasa yake sabuwa fil. *** *** *** After 2months. Acikin watanni biyun abubuwa da yawa sunfaru, wanda kuma yawancinsa zallan k’auna da soyayya ne dake gudana atsakanin Laylerh da Maleeek d’in. Acikin kuma watannin ne results dinta suka fito, wanda kuma duk acikin biyun babu wanda ta fad’i. Sosai tayi farinciki da hakan, inda a b’angaren Maleek kuwa tuni ya gama yi mata duk wani abu daya dace tare da sama musu visa, saboda so yake su koma London da zama, dan acan yakeson Laylerh’n ta k’arasa gaba d’aya karatunta. Wanda kuma yaune zasu tafi London d’in, Domin da k’arfe 4pm daidai jirginsu zai tashi. Tuni kuma ya gama had’a musu komai nasu da yasan zasu buk’ata, yanzun ma kuma shida kansa ya kai Laylerh gida, Dan yiwa su Oum Ayush bankwana, Domin yana da tabbacin idan suntafi suntafi kenan, ba abunda zaike kawosu Nigeria sai ziyara. Tunda sukaje gidan kuwa Laylerh’n keta zubawa su Abbou Jaheed shagwab’a, Domin gaba d’aya yanzu ta zama shagwab’abb’iya ta k’arshe, saboda Maleek ya riga daya gama shagwab’ata, Domin shi irin nasa salon rainon kenan, ahar kullum akan abu biyu ya daurata, daga sex sai shagwab’a, shiyasa ayanzu always take cikin shagwab’a. Kayayyakin ciye ciye kala kala Oum Ayush ta had’awa Laylerh’n, ciki kuwa harda wanda Momy ta kawo tace abawa Laylerh’n. Daga gidan su Oum Ayush d’in kuma, kaitsaye Laylerh’n gidansu Teemah ta nufa, wanda ayanzu Teemah da Aleeya dukansu suna da ciki, ita dinma Teemah kayan ciye ciye ta bawa bestien nata, tare da tabbatar mata cewar suma soon zasu taho London d’in. Daga gidan Teemah’n kuwa direct gidan Aleeya ta nufa, saboda yau d’in ita take driving da kanta. Bata wani jima sosai a gidan Aleeyan ba kuma ta tafi. Inda kaitsaye ta nufi gida. K’arfe uku da wasu mintuna na cika kuwa suka fara shirye shiryen su, kafun 4 kuma tuni sun isa airport inda suka samu rakiyar su Abbou Jaheed, da kuma Abbou Khareem sai Oum Ayush. Koda zasu shiga jirgi saida Laylerh’n tayi kuka, Domin tasan ba kad’anba zatayi missing Oum Ayush da kuma su Abbou Jaheed d’in, tanaji tana gani kuma haka Maleek ya rik’e hannunta, Yayinda d’ayan hannun nata ke d’auke da cat d’insa, haka suka shiga cikin jirgin. 4:00pm Daidai kuma jirginnasu ya d’aga zuwa sararin samaniya, sai alokacin kuma su Oum Ayush suka bar cikin airport din tare kuma da yiwa su Laylerh’n fatan sauk’a lafiya. Acan cikin jirgin kuwa Laylerhn kwanciya tayi lub ajikin Maleek, tare da lumshe Idanunta, sannu ahankali take shak’an daddad’an k’amshin dake fita ajikinsa, wanda akullum yake Samar mata nutsuwa. Suna ahakanne kuma jirginsu ya sauk’a acikin garin London. Kasancewar kuma abokan aikin Maleek din da kecan already sunsan da zuwansa ne shiyasa suna fitowa daga cikin jirgi suka samu an turo driver yazo d’aukarsu. Daga airport din kuwa direct masauk’insu suka nufa, sosai kuwa had’uwar masauk’innasu ya matuk’ar burge Laylerh, Domin kuwa irin wajennan ne da kai tsaye ake k’iransu da aljannar duniya, saboda tsabar kyau da had’uwar wajen kuwa, gaba d’aya glass ne shumfud’e ak’asan wajen, idan kana tafiya kuwa har sanja launin kala glass din keyi. Kaitsaye babban side dinsu suka nufa, koda suka shiga itakam Laylerh kasa rufe bakinta tayi saboda matsanancin kyau da side din kedashi. Bayan sun shiga bedroom dinsu ne kuma suka soma rage kayan jikinsu, kasancewar agajiye suke dukansu ne kuma yasa Maleek d’in da kansa yayiwa Laylerh’n wanka, tare da shiryata cikin wasu riga da wandon pencil crazy jeans, tare kuma da d’aura mata wata sweater mai gashin kuliya akan shigar tata, Bayan kuma shima ya shirya kansa ne, ya kama hannunta suka fice daga Cikin d’akin. Direct k’asan wajen suka sauk’a, inda suka tarar da wani k’aton cafe, yana rik’e da hannunta suka shiga cikin cafe d’in, bayan sun zauna ne kuma yayi musu order’n coffee da abinci irin wanda yasan Laylerh’n zata iyaci. Atak’aice dai kusan acikin cafe din suka k’arasa darensu. Bayan sun kammala duk abunda zasuyine kuma ya kama hannunta suka dawo gida, saboda ya fahimci yanda Layerh’n kejin bacci sosai ne kuma yasa shi kwantar da ita batare daya buk’aci komai daga gareta ba kuma ahaka sukayi bacci. Washegari kuwa tunda sukayi breakfast ya sake saka Laylerh’n ta shirya, the same irin shigan da tayi jiyan kuma tayi yau. Still yau dinma hannunsu na cikin na juna suka sauk’o k’asan, saboda yanayin hasken fatarsu ne kuma yasa gaba d’aya suka saje acikin turawan. Direct parking space ya nufa, inda ya ciro mota k’irar Mercedes wanda musamman abokanan aikinsa suka tanadar masa. Cikin motar suka shiga shida Laylerh’n kaitsaye OXPORD University suka nufa, wanda acanne Kuma ya samawa Laylerh’n gurbin ci gaba da karatu. Bayan sun shiga cikin school d’inne kuma yayi duk wani abunda ya dace, bai kuma bar cikin school dinba harsai da ya tabbatar da cewa Laylerh’n ta shiga aji ta zauna. Yau kuma kimanin sati guda kenan da zuwansu London din, a kuma cikin satin koda yaushe Laylerh sai taje university dinsu, Yayinda shi kuma Maleek din keyin aikinsa acikin camb dinsu dake nan London din. Ba laifi kuma tana gane salon karatun nata sosai. Yanzun ma zaune take akan wani Roma sofa, Yayinda ta nannad’e k’afafunta tare da maida hankalinta ga book d’in dake hannunta. Ahankali Maleek d’in daya share sama da 15mn atsaye yana kallonta ya sauk’e wata irin sassanyar ajiyar zuciya, tare da d’an lumshe idanunsa da suka cika da ruwan hawaye, kana kuma suke bayyana tsananin raunin da ke kwance acikin zuciyarsa. Takowa ya Shigayi ahankali tare da k’arasowa inda Laylerh’n ke zaune. Zama yayi ak’asa tare da mik’e k’afafunsa, ahankali kuma cikin muryarsa da tayi sanyi sosai ya k’ira sunan Ayshnoor d’innasa. Laylerhn dake zaune kuwa jin amo da kuma sautin fitar muryarsa ne, ya sata d’ago kai ahankali ta kalleshi tare da sakar masa wani irin sassanyar murmushi. Shid’inma Murmushi yayi mata, tare kuma da k’ura mata idanunsa, wani irin abu yakeji na musamman akanta, Yayinda abayan kowani minute tausayinta ke dukan zuciyarsa, abunda yake tambayar kansa kuma akullum shine. “Haka zasu k’are gaba d’aya dayuwarsu?.â€? Laylerh kuwa ganin wani irin kallon da yakeyi mata ne, yasa duk taji jikinta yayi sanyi, take kuma itama taji hawaye sun cika Idanunta, saboda abune dake yawo ajikinta akullum, matuk’ar Boo d’in nata yana cikin damuwa, lallai takanji yanayin ajikinta. Littafin dake hannunta ta ajiye tare da sauk’owa k’asa ta zauna akan k’afafunsa. Tafukan hannayenta tasa tad’an tallafo, hab’arsa tare da d’an shagwab’e masa fuskarsa. “Boo!!â€? Tak’ira sunansa asanyaye, tare kuma da sake matsowa kusa dashi. Shikuwa asanyaye ya janye idanunsa daga kanta, tare dasa hannunsa acikin aljihun wandonsa ya ciro wani dan madaidaicin box. Murfin box din ya bud’e tare da ciro waya yar gold chain dake cikin box d’in wanda agabanta, aka rubuta *L&M* da manyan bak’i, Yayinda kuma aka k’awata kan haruffan da wasu had’add’un sky blue din stones. Gold chain d’in ya mak’ala mata awuyanta, tare dasa hannunsa ahankali ya shafa gefen fuskarta cikin kuma muryar dake bayyana raunaninsa sosai yace. “Akullum inajin wani iri a zuciyata Ayshnoor , duk da nasan cewar kowani abu daya sameka arayuwa daga Ubangiji ne, amma nakanji ajikina k’addarata tayi tsauri, bansan Meyasa nake yawan jin faduwar gaba akan hakan ba, akowacce rana Rayuwarki nake dubawa Ayshnoor, har acikin zuciyata banason ace saboda son jurewa k’addarata Kin rasa madafa, nasani Ayshnoor nasani kowa aduniya yanason ganin jininsa, tambayar da nakeyiwa kaina akullum, shin ahaka zamu k’are rayuwarmu Ayshnoor? Banason nayi butulci ga Allah Amma kuma inajin rauni sosai azuciyata, taba heart d’ina kiji Ayshnoor kullum yana beating da fargaba inajin wani abu na daban, Domin hakan tamkar cutar da rayuwarki ne.....â€? Ya k’are maganar tasa yana me d’aura hannunta adaidai saitin heart d’insa, Yayinda kuma hawayen dake cikin idanunsa suka bayyana kansu. Wasu irin hawaye masu zafi ne suka gangaro daga cikin idanunta zuwa kan kyakkyawar fuskarta. Araunace take kallon Yah M.Jay d’innata, wanda sonsa yake dad’a k’aruwa acikin zuciyarsa akowani second. “Babu wata mummunan k’addara da zata tabbata arayuwa Yah M.Jay, akullum akuma koda yaushe banajin komai, saboda ni kaine GARKUWA ta, Tabbas babu wata damuwa da zata dameni matuk’ar akullum kana tare dani, kaine duk wani k’arfin guiwata, da soyayyarka kad’ai zan iya rayuwa mai dad’i, akullum akuma koda yaushe kaid’in kawai nakeso Yah Maleek, saboda haka ina da k’arfin guiwar da zan iya jurewa kowacce irin k’addararka, bazan tab’a damuwa akan hakan ba, Domin kowani bawa da irin k’addarar da Allah ke tsara masa, baizama lallai ace dan ya hanaka shine baya sonka ba..â€? Hannunsa ta kama ta rik’e acikin nata hannun, cikin kuma muryar kukan dake son k’wace mata tace. “Akwai millions din mutane acikin wannan duniyar da suke d’auke da k’addara irin taka, akwai kuma millions din da girman k’addarar su ta wuce taka, har akullum abunda Allah ya zab’a mana shine mafi kyau da alkhairi agaremu, saboda haka zan zauna dakai aduk yanda kake, zan rayu dakai rayuwa tahar abada, kaine akomai na, jininka ne yake gudana acikin jikina, har abada bazan tab’a barinka ba, Domin matuk’ar babu kai rayuwata bazata tab’a cika ba, alk’awari ne da bazai tab’a warwarewa ba, saboda haka sunan LaylerhMaleek ma bazai tab’a sanjawa ba, Domin akowanni bugun zuciyata Yah M.Jay ne, shid’inne ako yaushe, yanzu dama k’arshen rayuwata, zan kuma rayu da Yah M.jay na, batare da tunanin samun haihuwa ba, zan rayu dashi dakowani irin tabon k’addara, Domin kauna ta gaskiya babu ruwanta, da munin k’addara ko tabon da mutum yake d’auke dashi, zama dakai akowani irin yanayi shine fata da kuma burin rayuwata!!!â€? Takai k’arshen maganan nata adaidai lokacin da wasu hawaye masu zafi suka zubo daga cikin idanunsa. Hannayensa dake rawa yasa ya tallafo hab’arta tare da had’e foreheads dinsu waje d’aya. Tabbas Sosai kalaman Laylerh’n suka daki zuciyarsa, tare dasa shi jin kansa tamkar wani yaro k’aramin dake zaune agaban mahaifiyarsa. Lallai Tabbas Laylerh’n itace ta zame masa kowa, har abada kuma yayi imani babu wata mace da zata zo bayan ita. Labb’an Bakinsa dake d’an rawa ya bud’e ahankali, cikin wata sabuwar amon muryarsa dake shaking yace. “I can’t live without you Ayshnoor! Har abada rayuwata bazata tab’a cika ba idan babu ke, Tabbas zan rayu dake rayuwa ta har abada, Domin samunki yafiyemin komai, k’warai na yarda cewa ba kowani buri ne yake zama kammalalle ba, ba kuma komai da kakeso kake samu ba arayuwa, lallai tilas saika rasa wani abun kafun wani abun yake zuwa, abu mafi muhimmanci kuma shine samun k’arfin guiwa, da kuma nutsuwar zuciya.â€? D’an tsagaitawa da maganganun nasa yayi, saboda yanda muryarsa ke rawa. Ahankali cikin kuma yanayin dake bayyana amincewa da k’addararsa d’ari bisa d’ari yace. *”INASONKi Ayshnoor har abada kuma zamu rayu tare!!â€? * Idanunta tad’an lumshe tare da sake matse hannunta dake cikin nasa, murya araunace tace. *”INASONKA Yah Maleek kuma har abada zamu rayu tare, zamu kasance da juna acikin kowacce irin k’addara mai kyau ko akasintaâ€?* Tana gama fad’in hakan kuma ta d’aura bakinta akan nasa, tare da shigewa cikin jikinsa tayi hugging nasa sosai. Lallai Tabbas zata kasance da Maleek, kasantuwa kuma ta dindindin. Akullum akuma koda yaushe fata da burinsu d’aya ne, tamkar dai yanda zuciyoyinsu suke d’aya, har abada zasu ci gaba da kasancewa ahaka babu kuma wata k’addara da zasu bari damuwarta tayi tasiri acikin zuciyoyinsu. Tabbas *LAYLERH MALEEK* muradi da kuma fata ne adunk’ule awaje d’aya. Sunkuma amincewa k’addararsu, had’ari bisa d’ari saboda abu mai mahimmaci shine samun junansu, Allah Kuma ya cika musu burinsu, saboda haka daga yanzu har abada bazasu tab’a k’alubalantan Ubangiji akan k’addarorin daya sauk’ar musu ba. *Alhamdulillah!!! Rayuwa babu yanda bata zuwarwa bawa, abunda kayi tunani ya juye ya koma izuwa wanda baka tab’a tunani ba, Tabbas samun abunda kakeso babbar nasarace, amma kuma ba komai da kanema ne kake samu ba, akullum kuma k’addara takanzo ne a yanda Allah ya tsarawa bawa, babu kuma wanda ya isa sanjata, Lallai akoda yaushe abunda Allah ya tsara shiyake faruwa. Bai kuma zama lallai komai na rayuwarka ya zamanto hundred percent ba, Kamar dai rayuwar LAYLERH da MALEEK sun mallaki juna, duk da cewar akwai tawaya acikin rayuwarsu, amma hakan bawai shi yake nuna rashin kasancewar farincikinsu ba, ko babu zuri’a zasu rayu tare saboda ahaka tsarin k’addararsu tazo musu.* *(Insha Allah anan nakawo karshen littafin LAYLERH MALEEK Ina rok’on Allah Kuma daya bani ladan fad’akarwar dake ciki, ya kuma yafemin kurakuren dana aikata aciki, sannan masoya littafin Laylerh Maleek nagode kwarai da nuna kauna da kuma kulawarku agareni, Tabbas nasan kunyimin uzuri sosai, Allah ya saka da alkhairi, ina sake Mika godiyata agareku sosai, tare da addu’a da kuma fatan Allah yasa Muga Ramadan lafiya mukuma k’areta lafiya Allah Ubangiji ya yafe mana duk kurakurenmu ya kuma karb’i Ibadun mu, nasan wasu zasuyi tunanin ko katse labarin nayi, no ba katse labarin nayi ba, haka labarin yake ahaka yazo, unexpected ending gareshi, then duk wanda na b’atawa Dan Allah ya yafemin nima na yafewa kowa, ciki kuwa harda way’anda koda yaushe suke fitarmin da littafina waje, Inasonku dukanku Allah Ubangiji yabar k’auna, Insha Allah sai mun had’u a next book d’ina Ina ma kowa fatan alkhairi ayi ibada lafiya)* ********************** ? ************************** ********** Ai Hausa Novels **************** *************************? ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ? ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ? ************************** *12/4/2021* *9:14* *fatymasardauna* *Alhamdulillah #Ending*