[25/12, 13:21] Hassan Atk: 🤴🤴JININ SARAUTA🤴🤴 ********************** ? ************************** ********** Ai Hausa Novels **************** *************************? ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ? ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ? ************************** *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ *DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JINQAI* 1-5 Kallon mahaifinshi yake cike da murmushi yana girgiza kanshi "yanzu Abdul jalal kafison hakan? Kamar wanda magana take yiwa wahala ya bude bakinshi "Baffa kudin ne da yawa ga baki daya albarkar gonar nine nake amfani da ita kaga hakan be dace ba jalilah ma tana buqatar kudi tayi ilmi" Abdul jalal jalilah macece kaje kayi registration da kudin kuma banason musu kaji na gaya maka? Murmushi kawai yayi ya tashi ya fice Dakin mahaifiyarshi ya shiga ya zauna,, harara tayi mishi "jalal bazaka daina halin nan naka ba ko? Tashi ka fice ka bani wuri" sorry ummi nayi sallama bikiji bane" murmushi tayi mishi ya mayar mata "Ummi gobe zan tafi zaria baffa yace naje nayi registration" cike da farin ciki take kallonshi "idan zaka tafi zan baka saqo ka siyowa jalilah kayan kwalliya" kallon mamaki yayi mata Jalal ya zanyi da rikicin jalilah tace sajidah acen aka saya mata nata idan zaka tafi ka siyo mata dan Allah banason rikici,,,, kai kawai ya gyada mata Da waqa ta shigo tana ganinshi ta fara dariya "ya jalal alqawarina" kallonta kawai yake ta matsa kusa dashi tana qoqarin zama kan jikinshi ya dakatar da ita yana mata wani kallo,,, turo baki tayi cike da shagwaba Ya jalal toh me nayi kuma? Harara yayi mata Kuka ta fara yimishi yayi saurin dakatar da ita "meyasa kika gayama ummi ta saya miki kayan make up? Zama tayi kan jikinshi "kwalliya nakeso na koya irin na aunty jiddah" murmushi kawai yayi "kije ki gayama ummi bakyason kayan make up din kawai" ido ta zaro "ya jalal Allah inaso" aa kije ki gaya mata kinga ummi batada kudi idan naje zan saya miki da kudina" toh inga kudin naka? Hannu yasa cikin aljihu ya fito da naira dubu uku ya nuna mata Dariya tayi "harda tulare ka siyomin dan Allah" toh naji je ki gaya mata kin fasa" Da gudu ta shiga dakin ummi " ummi na dawo daga islamiyya" sai akace kada kiyi sallama? Sorry my mom, ni so nake kada ki sayamin kayan make up banaso" murmushi kawai tayi Rakiya tayi mishi zai tafi yana riqe da hannunta "ya jalal bani ashirin dan Allah" kallonta yayi "me zakiyi da ashirin? Sadaka zanyi maka Allah ya tsareka" sosai ta bashi dariya "Jalilah madarar kuka zaki saya" dariya tayi har saeda beauty point dinta ya fito sosai Hamsin ya dauko ya bata cike da murna ta juya ya janyota "ke meye haka? Bana hanaki gudu ba? Toh ai banason ta qarene? Kiyi tafiya banason gudu kinji ko? Kai ta gyada ta juya ya tsayar da mashin ya hau ya nufi tasha Yana sauka yayima ummi waya ya sanar da ita ya sauka,,, jalal kaci abinci sosai banason wannan zama da yunwa da kakeyi kuma a riqayin ibada akan lokaci" murmushi kawai yayi "jalilah fa? Tana wurin baffan jalal" murmushi yayi kawai ya katse wayan Baffan ya kira cike da murmushi baffa ya daga wayan "abdul jalal ina fatan ka sauna lafia? Lafia qalau baffa jalilah fa? Wayan baffa ya bata ta karba "Yaya jalal kyaun alwawari cikawa" ba ya hanya sai zancen kayan make up jalilah? Dariya tayi Yaya nasan ka sauka lafia ai" hmmm toh naji ki tabbatar kinje islamiya" ya jalal ai yanzu daga wurin baffa cen zan tafi" Toh kiyi karatu sosai kinji? Ta amsa da toh sukayi sallama Tsaye yake cikin school din duk ya gaji gashi yaso ya koma kafancen amma ba yanda xeyi sai ya kwana Da dare ya shirya ya nufi wani store yana tunanin ta ina zai fara sayen kayan make up din Cike da fargaba ya kwashi kayan make up dinda yake tunanin basuda tsada Wurin da ake biya yaje akayi mishi bill ajiyan zuciya yayi yana murmushi ya ciro kudin ya biya Kallonshi take kamar tanason tayi mishi magana amma sam ba alaman faraa a tare dashi har ya fice tana kallonshi tana mamakin wannan baqon al amari....... [25/12, 13:21] Hassan Atk: 🤴🤴JININ SARAUTA🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 6-10 Cike da murna taje ta taryeshi "ya jalal oyoyo" murmushi ya sakar mata suka qarasa ciki direct wurin baffa ya nufa ya gaidashi "abdul jalal sannu da hanya" yauwa baffa ya gajiya? Alhamdulillah Murmushi ta sakar mishi ya maida mata "Ummi sannu da gida" jalal ya hanya? Lafia qalau Ciki ya shiga yana riqe da hannun jalilah "ya jalal ka siyomin kayan make up din? Harara yayi mata Ke bakisan idan mutum yayi tafia yana buqatar hutu bane? Toh ka huta sai ka bani,,, murmushi kawai yayi ta juya ta fice ya bita da kallo Zaune yake dakin ummi tana kallonsu ahida jalilah sunacin abinci har ya kammala yabar jalilah dan duk da kasan cewarta qarama ta fishi cikin abinci Tashi yayi ya nufi dakinshi ya dauko saqon jalilah ya bata cike da farin ciki ta tashi taje tayi wanka ta dawo ta zauna ta fara kwalliya Kallonta ummi take ciki da mamaki yanda take tsara kwalliya har sai da ta kammala ta dago ta ware ma jalal idanuta saida tasashi dariya "ya jalal meye abin dariya banyi kyau bane? Allah kinyi kyau sosai jalilah dariya tayi ta tashi taje ta sanya kaya ta fito "ya jalal dauremin gashina" ya kama gashin ya daure mata ya daura dan kwalli duk ummi na kwallonta tana mamaki yanda jalilah ta iya kwalliya "Jalah wai nawa ka kashe ka kayan kwalliyar nan? Kamar beji me tace ba "jalal bakaji ina magana bane? Toh ummi me zance? Ai nasan bakada abin cewa tunda ka kashe kudi masu yawa" Tashi yayi yana murmushi ya fice zuwa dakinshi dan yana buqatar yayi bacci ********************************* Zaune yake a gaban mai marata ba duk ranshi a bace yake cikin qasaita ya kira sunanshi "abdul jabbar arayuwa mutum baya sanya sabon Allah gaba kaji tsoron Allah a gaba kaji tsoron Allah shine kawai zan gaya maka mutuwa tana biye dakai aduk inda kake kuma baza ta gaya maka zuwanta ba sai dai ta risqeka dan haka kayiwa kanka tanadi mai kyau" yana kaiwa nan ya gyara kwanciyarshi cike da girmamawa yayi godiya ya tashi ya fice Dakinshi ya nufa ya shiqa zuqar sigari "ya dai cool A J? Busar da hayaqin bakinshi yayi "AK bansan meke damun abba ba nifa gaskiya dolene nabar qasar nan dan bazan iya wannan takurawa ba can you imagine wai wannan imran din ne ya gayama abba wai shaye shaye nakeyi kuma wai zance aure fa mami takemin duka yaushe na gama secondary school wai zan lalace idan baayimin aure ba? Dariya AK yayi toh kai kaje ka nemi mata acikin matan da suke sonka mana Haba AK I can't do that kai bari kaji nifa I wish to finish my life single Dariya AK yayi harda riqe ciki dan yana mamakin hali iri na abokinshi shi sam mata basu dameshi ba kawai yasha gida da sauran kayan maye yayi wanka ya shiga gari ya kashe kudi kawai yayi bacci Haka suka ci gaba da shan kayan mayensu har sukayi bacci ********************************* Cike dajin kewar su yake tafiya cikin mota ba abinda ummi bata hada mishi ba haka baffa ya bashi kudi sam beyi tunanin baffa ya tara wannan kudin ba *8:45pm* abdul jalal yana zaune cikin dakinsu ga baki dayansu sabbin zuwa ne ba wanda yake magana da wani,,,,, wayanshi ya dauko ya kira ummi cike da sanyi take mishi magana "Ummi kin fara bacci ne? Murmushi tayi,,, jalal kewarka ce ke damuna,,, dan murmushi yayi "Ummina ga jalilah bazata debe miki kewa ba? Hmmm toh ina fatan ba wani damuwa ko? Ummi ba wani damuwa komi lafia qalau Toh adai kiyaye dokokin Allah banason ayi wasa kaji ko? Dan murmushi yayi ba tare da yace da ita komi ba tasan ba magana yake ba shiyasa ta kawar da zancen zuwa zancen ya riqa cin abinci haka sukayi sallama Washe gari ya shirya ya nufi wurin lectures cike da natsuwa yake sauraren lectures din bashi ya fito ba sai 2pm ya nufi masjid Kallonshi yayi yana murmushi shima ya mayar mishi tare da tashi ya fita daga masjid din ya nufi hostel Zaune yake bayan ya kammala cin abinci yana bida jotting dinda yayi ya shigo da sallama ya amsa mishi "na fito daga masjid ban sameka ba ashe ka dawo hostel" murmushi kawai jalal yayi mishi ba tare da yace dashi komi ba "Gashi muna room daya saida bansan sunanka ba,,, duo jalal ji yake an takurashi "Abdu jalal" ya bashi amsa a takaice "nice to meet you abdul jalal am mubarak muhmud" kai ya gyada mishi sorry abdul from which department? Ahankali ya dago yana kallonshi kafin ya bashi amsa "Information technology" dariya mubarak yayi "nima fa information technology suka bani, wow am so happy gaskiya pls can we be a friends? Ya fada tare da tsareshi da ido, murmushi jalal yayi tare da gyada mishi kai cike dajin dadi mubarak ya zauna kusa dashi ya fito da wayanshi mai tsada ya kira mami dinshi "mami kinga na samu friend kuma yanada kirki" dariya jalal yaga mubarak yayi shi ga baki daya mamaki ya cikashi Wayan mubarak ya bashi karbi Ku gaisa da mami ba musu ya karba Sallama yayi mata cike da girmamawa ya gaidata ta amsa sosai taji ya burgeta "ya sunanka? Abdul jalal, masha Allah toh kayi karatu banda wasa "in shaa Allah" tace da ita ya bawa mubarak waya sukaci gaba da magana da ita Kallonshi mubarak yayi "abdul anjima zamuje muyi karatu a tare ko? Kai kawai ya gyada mishi yaci gaba da karatunshi ga baki daya mubarak ya takurashi *8:30pm* mubarak ne tsaye yana jiran abdul jalal su fita shi sam hakan be mishi dadi ba haka ya haqura ya shirya suka fice sai faman janshi da surutu mubarak yakeyi amma sam baya kulashi har suka qarasa lecture hall din suka nemi wuri suka zauna Tunda suka fara karatu mubarak be qara yiwa jalal magana ba har suka gaji suka nufi hostel Chin chin jalal ya fito dashi daga cikin kayanshi kafin yayi magana mubarak har ya fara ci,,, kallon shi mubarak yayi "amma fa chin chin din ya hadu wa yayi mana shi? "Ummi" ya bashi amsa kirata nayi mata godiya pls "tayi bacci" okay kawai tace yaci gaba dacin chin chin din kuma yaci sosai ya tashi ya fita ya dawo musu coke mai sanyi ya ba jalal "no thanks" harara yayi mishi ya kawar da kanshi "Allah sai kasha,,, ya karba yasha kadan yayi kwanciyarshi ********************************** Kallonta kawai yake tana zuba mishi fada kamar zata cinyeshi "Allah kayima kanka fada kafin mai martaba ya yanke maka hukunci da zai baka mamaki kasan dai baya wasa gara kaje kayi registration ka koma school ya fiye maka Mami amma kin janye zancen auren ko? Kai ta gyada mishi cike da farin ciki ya tashi ya fice direct sai school ya kammla komi nashi yayi shirin fara lectures Zaune yake cikin mota na zuqar shigari yana shan waqa Juwairiya kinga maras kirkin nan ya dawo zo mu sanja hanya, tsaki tayi "ina ruwanki dashi dan Allah muje kinga ni yunwa nakeji" sam AJ be kulasu ba har suka fice dan shi takaicin mata ma yakeyi shi sam bass gabanshi "Abdul kayi sauri kada mu makara pls" saida ya kammala shirinshi ya dago yana kallonshi ya sakar mishi harara "Allah ka iya wulaqanci sai nayita faman magana kana wani shareni nima fa JININ SARAUTA ne" sosai yaba jalal dariya dan shi bayada alaqa da sarauta yanayi ne kawai Haka suka qarasa lecture hall din har 1suna ciki koda suka fito kowane yunwa yake ji,,,, kallonshi mubarak yayi "muje eatery yunwa nakeji" wani kallo jalal ya watsa mishi ya juya ya nufi hostel mubarak ma yabi bayanshi cike da takaici suka qarasa sai faman fada mubarak yake jalal be kulashi ba ya dora ruwan zafi saida suka tafasa ya dauko garin kunu ya dama ya zuba a flask din da ummi ta bashi ya dauko farin dan wake ya hada mubarak sai kallonshi yake har ya gama ya tashi ya fita be wani jimawa ba ya dawo da crete na egg da coke da ruwa ya dafa egg din ya yankashi cikin dan waken ya zuba yaji da mai kafin yayi magana har mubarak ya fara ci shikam kunu yasha yaje masjid yayi sallah ya dawo yayi kwanciyarshi saida akayi laasar mubarak ya tadashi sukaje masjid sukayi sallah Kallon mubarak yake ya bude jakanshi ya bedo chinchi yazo ya zuba kunu a cup ya fara sha har ya kammala jalal be kulashi ba "Abdul me zaka girka mana anjima? Ko kallonshi beyi ba bale ya kulashi "cool jalal ko baza muci komi bane? Sai a lokacin ya kalleshi kamar me nazari dariya yayi "Allah ni kana bani mamaki kai haka kake rayuwa ba magana? Sunkuyar da kanshi yayi kawai yaci gaba matsa wayanshi "assalamu alaikum" a dayan bangaren kuma baffa ne ya amsa "baffa bacci nake koda ka kira" jalilah ce keson magana dakai murmushi kawai yayi baffa ya bata waya "ya jalal dan Allah ka qaromin foundation idan zaka dawo " meye hakan? Wanda ake shafawa kafin a shafa powder" jalilah banfa gane ki bari dai zan bincika, toh amma fa kuma irin wannan nakeso, toh bayada wani suna ne? Ailin liquid foundation murmushi yayi "toh naji hope kinje school yau? Eh naje, islamiya fa? Ya jalal kasan banawasa fa, murmushi yayi toh ki haifa ummi ta amsa ta bawa baffa wayan "Abdul jalal karatu da sauki ko? Eh baffa ba wani wahala Allah ya taimaka a riqe ibada sosai kaji? Kai ya gyada kamar yana ganinshi sukayi sallama ya ajiye waya........... [25/12, 13:21] Hassan Atk: 🤴🤴JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 11-15 Kallon shi mubarak yayi "amma kai asalin bahaushe ne wallahi" kallon shi yayi da alamar tambaya, harara yayi mishi "ai ni dana kira mamina na baka kun gaisa at least ko qanwarka ka bani mu gaisa mana amma kaqi" murmushi kawai jalal yayi ya zuba dan wake a plate ya fara ci *********************************** Tsaye yake bakin hall din da zeyi lecture yana zuqar shigari yana matsan wayanshi hankalinshi a kwance gashi yasha wanka ya hade iya haduwa Prof dan asabe ne ya biyo yana sauri zeyi musu lecture cike da mamaki yake kallonshi ko ajikinshi sai da ya kammala shan sigari kafin ya nufi cikin hall din Dakatar dashi prof yayi "abdul jabbar pls get out" cikin black spectacle dinshi yayi mishi kallon raini, ahankali ya taka yaje kusa dashi "atarihi ka tabajin an kori zaki daga dawa? Cike da takaici prof yake kallonshi sam besan hali irin abddul jabbar ba kodan yana ganin shi dan sarki ne? Murmushin takaici yayi ya juya yaci gaba da bawa yara lecture abdul jabbar kuma ya juya ya fice ya hau saman motanshi ya kunna sigari ya shiga aikinshi A J how far? As usual "ya kafita? Dan tsaki yayi "nifa daman ba lectures din nakeso ba kasani amma wai wannan dan asaben ya zanyi dashi ne zan sa adan mishi bulala ne ko ayi mishi na yaren Igbo da yoruba? Aiko A K yace me zeyi inba dariya ba "A J man din nan fa ba yaro bane me zaisa kayi mishi bulala? Kawai naga ya fiye rashin ji ne" amm ya zancen imran? Kawai nasashi ya hada kayanshi ya koma hostel kuma na gaya mishi idan yayi exam ya wuce gidan ubanshi" sosai A K yayi dariya "cool A J kana shaaninka fa" saukowa yayi daga kan mota dan bayason surutun A K In zaka? Cikin motan ya shiga ya dauko giya kawai ya fara sha "cool A J ba anan ya dace kasha giya ba fa kasan ni ba yanzu zan koma gida ba" harara yayi mishi yasha iya shanshi ya tada mota kawai cike tashin hankali AK yake kallonshi saida yaje ya samu wuri inda yake da itatuwa acikin school din ya kwabe sit ya shiga baccinshi Juwairiya kinga mutumen naki fa,,, salma Allah zamu bata dake" dariya salma tayi,,, bari kiji Allah nafison baqin kumurci akan wannan guy din shi sam besan darajar mace ba Bikiga yanda sukayi da fatima muktar ba kawai ya tureta ba tare da ya juyoba yayi mata sannun ba ya wuce abinshi ta sameshi kinsan itama ba sauki ne da ita ba taje tayi mishi masifa kawai ya kira wani wai zan biyaka ko nawa kakeso kayi mata bulala cike da mamaki ta tsaya tana kallonshi sam batayi tunanin rashin kirki irin na cool A J yakai hakan ba Manta da zancenshi ni banida lokacinshi Fira suke har suka qarasa hostel Zaune suke shida mubakar suna karatu wayanshi tayi ringing ya daga kallonshi juwairiya tayi yana magana da ummi har ya kammala ya ajiye wayan ba tare da ya kalli mubarak ba dan bayason qorafi Salma kinga wani ikon Allah? Salma kam baki ta bude tana kallon jalal yana karatu Kallon mubarak yayi "ka gaji ne? Murmushi kawai yayi mishi "toh muje mana" ya tashi suka fice Amma they are related ko? Anya? Haba wannan kamar tayi yawa har voice dinsu fa Ke kyaleni da zancen nan banaso Dariya Salma tayi sukaci gaba da karatu Cikin parlour ya sami mai martaba zaune cike da girmamawa ya gaidashi ya amsa "abdul jabbar da gaske ne ka koma makaranta? Abba na koma" murmushin qasaita yayi Allah ya taimaka "ameen abba" ya tashi ya fice............ [25/12, 13:21] Hassan Atk: 🤴🤴JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 16-20 Wanka yaje yayi ya shirya cikin qanana kayan ya zuwa rings dinshi na gold guda biyu yasa agogonshi na Rolex ya dauki mota ya nufi cikin school yana tafe yana shan waqa har ya qarasa ciki ya bude motan ya fito ya haye saman motan yabar motan bude waqa yana tashi ahankali Cike da yanga ta biyo wani tsaki yaja "wai macece zata fito tana wari har take ganin ta hadu tana yanga Iya bacin rai juwairiya tajishi amma ta danne zuciyanta ta shareshi kawai ta wuce abinta dan ita tasan bata wari dan Arabian sultan take amfani dashi Har ta qarasa A G T (Agric theater) ranta a bace ta nemi wuri ta zauna ta zuba tagumi tana tunanin wulaqancin da zata yiwa cool A J Dariya mubarak yake lokacin da suke qarasowa cikin AGT din jalal sai faman murmushi yake dan ba kadan shima mubarak din ya bashi dariya Cool jalal zanso ganin ranar da zakayi tadi gaskiya,,, bata ranshi yayi ya nemi wuri ya zauna sam ba wani nisa ne suke da da juwairiya ba Abdul jalal wai kai wannan shurun baya damunka? Kallonshi abdul jalal yayi amma sam bayajin zai iya magana kuma badan bayada abinda zai gaya mishi ba " kayi magana mana ka tsareni da ido haka gashi ni wannan idanun naka bawai so nake kana riqa dorasu akaina ba dan sai naji kamar nayi laifi an tsareni" kawar da kanshi yayi yana murmushi Wayanshi ce tayi ringing yaga ummi ce ya daga Cike da hanzari mubarak ya karbe wayan yayi mata sallama ta amsa ya gaidata "Ummi sunanan mubarak nima yaronki" murmushi tayi saboda ya bata dariya "sannu mubarak ya karatu? Lafia ummi sai dai matsala na daya abdul sam bayason yimin magana eh aa ne kawai tsakanina dashi" mubarak haka yake ko a gida idan kaji yayi magana toh jalilah ce ta sanyashi magana" Ummi jalilah tana ina? Ai gata kusa dani, ummi bata mu gaisa" Sallama tayi ya amsa "ya jalal baka manta da alwarina ba ko? Kuma ka siyomin abaya dan Allah inaso na riqa shigan larabawa kuma kada ka manta ka qaromin tulare na kusa qarasa wannan" dariya yayi "wannan ya mubarak ne ba ya jalal ba kuma zan saya miki saboda ni kika gayama" kai waye? Nima yayanki ne Toh ya jalal kuma fa? Gashi,, ya bashi wayan ya karba "Ya jalal wannan waye? "Bana hanaki yawan surutu ba? Yaya jalal ai nayi tunanin kaine kasan bana magana da wanda bansani ba Toh anjima zan kira Ummi sai muyi magana ki gaida ummi kuma ki tabbatar kinje kinyi kitso "Yaya jalal ba wanda zai rakani" aa kiyi haquri kije kinji? Dariya tayi ta amsa mishi ya katse wayan "Ya jalal jalilah zatakai shekara nawa? Kamar beji me mubarak din yake fada ba "jalal fa? Kallonshi yayi cike da nazari "bazan iya ganewa ba" kamar ya? Ba qanwarka bace? Murmushi yayi yaci gaba da karatunshi "Kaji dashi cen" cewar mubarak tare da matsawa kusa da jalal din Kallonshi juwairiya takeyi koda baa fada ba tasan ba wani hali ne dasu ba saboda yanayin kayan jikinshi da wayanshi kadai ya tabbatar mata da hakan Haka suka qaraci karatunsu suka nufi hostel _after a weeks_ Mubarak yana kwance yana bacci jalal ya hada kayanshi da basu set uku ba ya rubuta mishi short note "Zan tafi weekend" Ya ajiye ya tafi kawai, mubarak yana tashi sosai gaji beji dadin hakan ba at least ya rubuta contact dinshi ya ajiye mishi mana gashi bemasan daga ina jalal din yake ba, haka ya qaraci zamanshi na week end cikin kadaici da kewar jalal Zaune yake cikin room dinsu abdul jalal yayi sallama ya amsa ba tare da ya kalleshi ba yasan fushine mubarak din yakeyi Wanka yaje yayi ya dawo ya shirya,, magana yakeso yayi mishi amma besan same sai fara ba "Muje class" wani kallo mubarak yayi mishi yayi murmushi tare da kawar da kanshi "me kace? Mubarak ya tambayeshi Shuru be bashi amsa ba "abdul jalal ina takuraka ne? Kallonshi yayi da alaman tambaya "eh abinda nake nufi kenan saboda na fahinci kai ba bakason muaamala dani banason shiga rayuwanka idan ina takuraka ka gayamin zan kyaleka" Murmushi kawai yayi danshi ba mubarak din ne matsalanshi ba kawai dai yana mamakin yanda mubarak ya gagara fahintar halinshi ne hakan Kai nake sauraro,,, ahankali ya bude Bali yace "sorry" kallonshi mubarak din yayi ya kawar da kanshi yanaso yayi dariya Dariya mubarak yayi "gaskiya baka kyautamin ba za kaje week end ae sae ka gayamin da wuri gashi saqon jaililah ma bakajemin dashi ba kuma dan wulaqanci ko contact dinka baka ajiyemin ba kawai ka tafi abinka" Hmmm muje Bazani ba dan yunwa nakeji,,, kallonshi yayi ya juya ya ajiye hand out dinshi ya fice, be wani jimawa ba ya dawo da coke a hannunshi ya bude jakan da yazo da ita ya ciro naman kaza da Ummi ta bashi ya miqa mishi ya karba Sosai yaji naman saboda yayi mishi dadi Bayan ya kammla ya boye sauran abdul jalal yana kallonshi ya wanke hannunshi suka fice Kallonshi mubarak yayi "cool jalal waya soya naman dan Allah? " Ummi" ya bashi amsa ba tare da ya kalleshi ba Allah na matsu na koma na qaracinshi, ko kallonshi jalal beyi ba yaci gaba da karatunshi _After a weeks_ Exam sukeyi ba wanda yake wasa da karatu acikinshi Tafiya suke ya biyo da mota da gudu ya watsa musu ruwa duk yanda mai karatu yake tunanin baci ran jalal ya wuce hakan sosai ya bawa mubarak mamaki ganin yanda ya wani hade rai ba tare da yayi magana ba, haka suka nufi hostel jalal sai faman cin magani yake Yaune ranar da suka kammala exam mubarak zai wuce garin Kaduna jalal yace shi sai gobe zai tafi dan bayason mubarak ya bada komi a kawai jalilah Okay gayamin shekarun jalilah,,, banza yayi dashi "Wai jalal meyasa kakeji dadin kyaluwa ne? Murmushi yayi ya tashi ya fice Zaune mubarak yake hanata faman jiranshi amma shuru ba wani labari kusan 1h kafin ya dawo Kallon kayan hannunshi yake ya ajiye ya kwanta Ledan mubarak ya diba yaga abayane da cosmetics Sam jalal be kula da kallon da mubarak yake mishi ba Tashi yayi ya hada kayanshi ba tare da tace dashi komi ba yaja akwatinshi ya fice ya dawo ya dauki wayanshi ba tare da tace dashi komi ba ya wuce abinshi cike da takaici Murmushi kawai jalal yayi ya tashi ya hada kayanshi ya fito Cike da mamaki ya kalli mubarak zaune yana amsa waya danshi a tunaninshi mubarak ya tafi kenan Murmushin dole yayiwa mubarak yaje kusa dashi ya tsaya "Baka tafi ba kenan? Harara yayi mishi "malam meye damuwarka dani? Rana ta farko da mubarak yaga jalal yayi dariya tare da juyawa sosai ya burge mubarak "sorry na sanja shawara ne zan tafi yanzu" Murmushi yayi tare da girgiza kai "bari driver yazo mu tafi" ido jalal ya zare "ina? Kafancen mana" dariya ya qarayi cike da qasa ita kamar wani jinin sarauta Sorry baza muje tare ba gaskiya "meyasa? Nazarin ya shigayi "toh me zakayi kafancen wai kawai saboda tsaban son wahalar da kai? Kallonshi mubarak yayi "Allah ka gama duo wani tunani da zakayi sai munje tare murmushi kawai yayi ya nemi wuri ya zauna Driver din ne yazo "ganshi inji hajiya tace na Baka wannan ya karba suka shiga ciki driver yaja suka dauki hanya Da gudu ta fito "ya jalal oyoyo oyoyo" murmushi kawai yayi tayi hugging dinshi sam bata kula da mubarak har suka shiga ciki sai zuba mishi surutu take Gaban baffa ya zube cike da girmamwa ya gaidashi "abdul jalal haka makarata ya maidamin dakai? Murmushi yayi baffa ya gaisa da mubarak tare da Santa musu albarka ta fatan alkhairi Dakin Ummi suka nufa cike da murna ta tarbi mubarak suka zauna Kallonshi jalilah tayi "ya jalal wannan ne mukayi waya dashi ko? Kai ya gyada mata Umurni ummi tayi musu suje suyi wanka suzo suci abinci........... [25/12, 13:21] Hassan Atk: 🤴🤴 JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 21-25 Zaune suke a dakin ummi ta zuba musu dambu da taha musu zobo mubarak kam sai faman ci yake Jalal ne ya fara kammalawa ya tashi ya koma kan kujera ya zauna Da gudu ta shigo ta zauna kan jikinshi tadan kwantar da kanta "ya jalal me kakeyi? Be amsa mata ba yaci gaba da matsa wayanshi tana kallon abinda yakeyi Kallonsu kawai mubakar yakeyi yana murmushi "ya jalal inzo ka gyaramin kaina sai muje wurin kitso? Kallonta yayi "yanzun ne za muje ke bikisan ina tare da gajiya bane? Turo baki tayi alaman fushi "toh ai gobe akwai school kuma banaso na tafi ba kitso" kidaizo in yi miki kalaba idan kinaso sai ki bari week end muje kitson" Mamakin yanda yake magana mubarak yake daman Ummi ta gaya mishi jalilah ce kawai take sanyashi magana "Ya jalal in kwanta? Aa ki zauna a qasa yanda za muyi sauri" bata ranta tayi tare da turo baki "Allah ni nafiso a kwance Be kulata ba ta kwanta ta dora kanta saman lap dinshi ya fara yi mata Dariya mubarak yayi "lallai cool jalal babba kake, wai da gaske ka iya? Dariya ummi tayi "ai har kunshi yi mata yake dan ni bazan iya rigimar jalilah ba ga baki daya ya batata da son jiki da fitina ga rikici akan abinda ba nata ba" dariya mubarak yayi yaci gaba da kallon jalal da yake faman yima jalilah kalaba har ya kammla tas kai baxakace jalal ne yayi ba ya hada wuri daya yasa mata ribbon "tashi kije kiyi wanka" ya wari nakeyi? Aa ban fada ba" aiko mubarak ya shiga dariya "jalilah kitsonki yayi kyau gaskiya" ai ya jalal din ne ma yau beso yimin mai kyauba da ka ganni kamar wata balarabiya " ta qarasa magana tana dariya aiko mubarak ya shiga dariya taje tayi wanka ta dawo Kayan make up dinta ta kwaso ta zauna kusa da jalal "ya jalal ka banisu daya bayan daya ina shafawa kaji? Kai kawai ya gyada mata Daya bayan daya ya riqa batasu tana shafawa har ta kammala kwalliya gashi tayi kyau sosai Taje tasa kaya ta fito "ya jalal dauramin dan kwalina" ba musu ya karba ya daura mata Cool kace kai na mace ne kawai,,, dariya sukayi shida ummi Mubarak ai dolene ya koyi komi na mata dan shi ya dauka ma kanshi yanzu wa zaice jalilah jss 2 take? Ido mubarak ya zare dan shi Sam bega alaman hakan ba "Amma ummi shekarunta nawa? 11 yeas "ummi yanzu fa 12 nakeda ko ya jalal? Kai ya gyada mata "toh kaji amma ko yaushe tana jikin jalal kamar mage Dariya mubarak yayi Duk yanda juwairiya taso ta qyale cool A J ta gagara saboda ruwan da ya watsa mata kuma ya kirata da sunan jahilah Cike da takaici ta qaraso wurinshi tadaga hannu ta wankeshi da mari Ranata farko da cool A J ya qare mata kallo ba tare da yace komi ba kawai ya bude motanshi ya dauko wayanshi yayi snapping dinta ya shige motanshi Sam bata kawo komi aranta ba da dare ta shirya ta nufi class dan akwai assignment din da takeso tayi Haskata akayi da fitila sai tayi murmushi " Salma Allah ki daina" haka har ta qaraso wurin da Salma take Cikin zafin nama suka turata cikin motan sai zuba ihu take suka rufe suka tafi da ita Sam bata fahinci idan suka nufa da ita ba kawai dai ta ganta a wani dan qaramin gida sun turata cikin wani daki suka rufe Ba irin kukan da bata sha ba amma sukaqi budeta har gari ya waye Cikin takunshi na isa yazo ya bude qofan ya shiga Ahankali ta dago tana kallonshi idanunta duk sun kubura Tsaye ta miqe da sauri tana nunashi Ya nemi wuri zauna sam ba alaman wasa a tare dashi "Allah ya isa tsakanuna dakai mugu kawai kuma wallahi idan har ka bari na fita gidan nan sai kayi Dana San in abinda ka aikata zakasan nu juwairiya ba kanwar kasa bace kuma danasan Kaine kasa aka kawoni nan da ban bata hawayena ba nayi kuka " Murmushi yayi ya kira AK a waya ya shigo "kaida ka damu da mata ga wannan idan zaka iya hada jiki da wannan qazantar Dariya AK yayi "gaskiya yau zan more" kada ka yarda tayi mana taurin kai idan kuma tayi zan turo wadan da zasu daure maka ita" dariya AK yayi Cool AJ karma damu ai ba wani yawa ne da ita ba zan iya tafiyar da ita Tashi yayi ya fice AK ya matso kusa da ita tayi murmushi "na roqi Allah tsari da sharrunka dan haka kasa ka bata likacinka dan bazaka iya yimin komi gara kawai kaje abinka" kallinta yayi ba tare da yaji yana iya dogon motsi ba ta juya ta nufi Inda take tunanin toilet ne Cikin sanyi AK ya juya ya nufi inda cool A J yake Cool AJ kabarta ta tafi kawai "eh zata tafi na kira wanda zai yanka hannun da ta mareni dashi tace yana kan hanya" ido AK ya zare ganin da gaske cool A J yake yanka hannunta zeyi Cool A J ta cancanci wannan hukuncin amma ka yafeta No ka daina wannan zancen bazai yuyu ta zauna da wannan hannun ba dan ba nata bane,,, kallonshi kawai A K yakeyi Cool A J amma ka tausaya mata mana "tsaki yayi kawai ya tashi ya dauki wuqan da yake kusa dashi Cool A J!!! AK ya kirashi da qarfi "kada ka aikata hakan kasan mai martaba bazai taba kyalekaba zeyi maka hukunci fiye da hakan kada ka soma Tsaki yayi "wait, kai zaa yima hukunci? Kai ya girgiza amma kasan duk abinda ya shafeka ya shafeni ko? Dakin ya nufa ya sameta ta kammala sallah Kusa da ita yaje ya zare wuqan ya janyo hannunta cike da zafi tayi wani ihu Suka shiga kokawa tana ihu har ta kaisu ga faduwa qasa Iya karfi cool A J ya danneta tare da janyo hannunta ya fara yankawa Cikin wahala ta furta "pls A J have mercy on me for God sake" cak ya tsaya yana kallonta duk ta jigata ga wani zazzafan hawaye da yake zuba a idonta Rana ta farko da mace ta bashi tausayi Kallonta yake cikin yanayin tausayi idanunta na rufe ga azaba ga nauyin A J Ahankali ya tashi daga kanta tare da dagota Hawayene suka qara zubo mata saboda yanda cool A J............ [25/12, 13:21] Hassan Atk: 🤴🤴JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 26-30 Hawayene suka zubo mata sakamakon yanda cool A J ya janyo hannunta, haka ya riqa janta har suka fito wurin da yayi parking,,, cike da tanshi hankali AK yake kallonshi ya turata cikin mota ya rufe Direct sai hospital ya kira family doctor dinsu ya gaya mishi yanason ganinshi Zaune yake saman kujera Dr. Labaran yana kallonshi cike da alaman tambaya "Stitching zakayi mata" ya fada tare da ci gaba da matsa wayanshi "Meya sameta ne? Ni na yanka hannun saboda ta mareni dashi" kallon mamaki yayi mishi "abdul baka tunanin abinda zai biyo baya? Wanikallo ya watsa mishi "kayi mata abinda nace kafin na daina jin tausayinta dan wallahi burina na cire hannun ga baki daya" murmushi Dr labaran yayi ya fara yi mata stitching "Ke tashi muje" ba musu tabi bayanshi suka fice direct sai cikin school ya nufa da ita ya nemi wuri yayi parking "Ki gode Allah yaune rana ta farko Dana fara jin tausayin mace da wallahi keda hannu saedae ki gani a wurin wasu" kallonshi kawai take tana mamakin qarfin hali irin na A J Kudi ya ciro ya miqa mata kallonshi kawai take ba tare da ta karba ba, murmushi ya sakar mata tare da zube mata kudin a jikinta "out" Ahankali ta bude motan ta fice Tsaki yaja tare da tada motan da qarfi ya fice daga cikin school din ya nufi gida direct sai dakin mami ya zube Kallonshi "abdul daga ina haka? Mami wallahi school nake duk na gaji" murmushi tayi mishi "toh kaje ka huta ko? Murmushi yayi ya tashi ya nufi part dinshi ya zube wayoyinshi ya kunna sigari ya fara sha yana kurba giya har ya samu yin bacci *********************************** Zaune suke shida mubarak sai faman surutu jalillah take zuba musu wani zancen ya kualata wani kuma yayi kamar beji ba sai dai mubarak din ya kulata "Ya jalal kaga yanda gonar baffa yayi? Allah kadan ya rage na cire wani rake sai naji baffa yace jalilah muje gida yamma tayi,,, sai na cije yatsana nasan da kana nan Allah zakasa qarfi ka ciremin ko? Kai kawai ya gyada mata Ya jalal ko za muje ne? Aa bazani ba,, turo baki tayi "Allah ni sai munje" ke wane irin fitinane kika qaro haka? Kuka taxa mishi ya aika mata da saqon harara ya aika mata ta tashi taje kan jikinshi ta zauna "ya jalal muje" wai ke kenan idan kinaso abu sai kinyi fitina? "Toh muje" tsaki yayi "je ki sanya hijab kizo" aa ya jalal bari nasa abayana" kai ya gyada mata tayi mishi dariya ya sakar mata murmushi Kallonshi mubarak yayi "gaskiya kanaji da jalilah sosai fa" murmushi yayi "toh ai banida kowa sai ita" dariya mubarak yayi "har gara kai ni ni kadai mami ta haifa abba ya rasu bata qara yin wani auren ba bale na samu wani ko qanwa" murmushi yayi mishi Kallonta mubarak yake har ta qaraso wurinsu taje jikin jalal ta zauna "ya jalal ummi tace a dawo da wuri" kai ya gyada mata suka tashi suka fice "Yaya jalal kawo kudin madarar kuka, ya mubarak kaima zakasha ko? Eh zansha mana kawai ya bamu kudin mu siyo" dariya tayi tana kallon jalal ya dauko naira dari ya bata "toh Ku jirani anan kunji" dariya mubarak yayi tare da gyada mata kai Sosai mubarak yayi mamakin gonakin da su jalal suke da komi yayi sosai gonar ta burgeshi suka shiga zaga gonakin "Ashhh" da sauri suka juyo "menene? Bansan meye na taka ba, sunkuyawa yayi ya cire mata "sannu ya furta ahankali tare da shafa face dinta, kallon da mubarak yayi mishi ya sashi jin kunya ya juya yana murmushi yana juyo suka hada ido da mubakar ba shiri yayi dariya Allah cool Jalal Kannada abin dariya,,, ai kai kake sanyani dariya Allah Wannan irin so haka anya zaka iya bada auren jalilah ko? Kallonta yayi tayi dariya " toh kasan sae dolene tayi auren so pls zancen ya wuce" yayi gaba ya barshi shida jalilah Zaune suke mubarak da jalilah suna shan rake jalal kuma yacin abinci "Yaya mubarak bani labarin school dinku" kallonta jalal yayi tana shan raken Jalilah ai ina gaya miki school tafi rake dadi" ido ta zare "school kayi bulala school fa akwai wahala amma rake akwai dadi idan fa ina shan rake har ni yake iska tana daukana Tashi jalal yayi yana murmushi ya shige dakin ummi aiko mubarak ya shiga dariya harda riqe ciki "Jalilah muje wurin ummi" suka tashi suka nufi dakin ummi "Malam saboda Ku fa na dawo nan" wurin ummi fa mukazo Kallonsu Ummi tayi tana murmushi " Ummi gobe nakeso na tafi" kallonshi jalal yayi suna hada ido ya kawar da kanshi yana murmushi "Toh mubarak Allah ya kaimu goben" ameen ya amsa Washegari driver yazo dauka mubarak su jalal sunyi miahi rakiya ummi ta hada mishi chin chin ta soya mishi zaki ta bashi ya tafi dasu Kallonshi jalal yayi ya rufe idanunshi ahankali yana murmushi ya bude suna hada ido ya kawar da kanshi yana dariya cike da qasa ita shima mubarak din dariya yayi tare da daga mishi hannu suka fice sosai jalal yaji kewar mubarak haka mubarak din yakeji kamar yabar wani rabin jikinshi ne Zaune take duk abin duniya ya isheta ga baki daya ba yanda Salma batayi da juwairiya ta gaya mata ina ta kwana kuma me ya sameta amma taqi da qarshe ma bacci ta shiga yi................. [25/12, 13:21] Hassan Atk: 🤴🤴JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 31-35 Bayan ta tashi daga bacci tayi wanka suka nufi class ita da salma dan gobe za suyi exam na qarshe su wuce gida "Juwairiya ga mutumenki nan fa" ahankali ta dago suka hada ido da cool A J tayi saurin kawar da kanta taci gaba da karatun da take Sigari ya shiga zuqa yana matsa wayanshi har ya gaji ya nufi gida Bayan juwairiya ta gama exam ta hada kayanta suka nufi katsina ita da salma Haka sukaci gaba da rayuwa har hutu ya qare kowa yayi shirin dawowa school Tsaf ya sami dakin da alama jalal ya qaraso kenan, murmushi yayi cike dajin dadi ya sauke kayanshi ya nufi toilet yayi wanka Tsaye yake yana kallon jalal wanda kallo daya yayi mishi ya kawar da kanshi yana murmushi " kai baka ganni bane? Ya fada yana qara hade face, dariya jalal yayi "toh ai ko kaine malam ibrahim bazaka wuce haka ba" dariya mubarak yayi ya sa kaya yazo ya zauna Ina saqona? Kallonshi yayi da alaman tambaya "eh abinda ummi ta baka ka kawomin nake nufi" tashi yayi zai fita mubarak ya riqeshi " malam yunwa fa nake ji" kamar ba zeyi magana ba ya tsaya yana kallon mubarak " na gaya maka banason wannan kallon" murmushi yayi "2mnts pls" ya janye hannunshi daga na mubarak ya fice, be wani jimawa ba ya dawo mishi da coke ya bashi ya fitar mishi da naman kaji ya miqa mishi ya zauna ya faraci shi kuma jalal kwanciya yayi abinshi yana kwallon mubarak har ya kammala ya tashi ya wanke hannunshi ya dawo Malam tashi dan Allah bacci zanyi,, sam jalal yayi kamar beji me mubarak yake fada ba ya shareshi "Allah nima fa na iya shariya gara kawai ka bini ahankali" kallonshi jalal yayi ya kawar da kanshi " malam zaka tashi kosai na tureka? Kallonshi jalal yayi da kyau sai kuma yayi dariya dan yasan mubarak bayada qarfin da zai tureshi "kalleni da kyau ba makusa ajikina" dariya yayi ya tashi ya koma gadon mubarak din ya kwanta ************************************ Mami dan Allah kada kice sai ya dawo gidan nan yana takurani ne,,, abdul wai me imran din yake mana ne? Ni ki barshi a gidansu kawai" tsaki tayi tare da girgiza kai ya tashi ya nufi fada Gaisuwa ya miqawa sarki fadawa suka fara "an gaisheka magajin sarki" wani harara yayi musu ya nemi wuri ya zauna Cikin muryar nan ta qasaita sarki mahmud ya fara magana "abdul jabbar munada baqi wadan da kaine zaka shige musu gaba a madadina har su kammala abinda sukazo yi su tafi" cike da girmamawa ya amsa tare da yiwa sarkin fatan yawancin rai ya tashi ya fice Jakanshi ya janyo ya bude ya shiga fitar da kaya ko wace set biyu ne a hade wuri daya haka yayita fitar dashi tun daga manyan kayan har izuwa qananan kaya set goma sha biyar kuma duka iri daya haka ya fitar da shoe set goma sha biyu ko wane biyu iri daya ne sam jalal be kula da abinda mubarak yakeyi ba saboda hankalinshi yana kan waya Mubarak ya kwashi set goma sha biyar da na shoe 6 yakai ya zuba acikin locker din jalal ya juya ya dauko system sabuwa ya zauna yayi connecting da nashi ya shiga copying abubuwa masu amfani Kallonshi kawai jalal yake har ya kammala, kallon jalal yayi yana murmushi ya tura mishi system din "nasan koda na Santa mana films zaka gogesu ne shiyasa banyi ba mami ce tace a baka" wani kallo yayi mishi "amma na gaya mana banason irin wannan kallon ko? Kawar da kanshi yayi amma Sam ba alaman faraa a tare dashi,, kallo mubarak ya bishi dashi yana qoqarin sanja kaya alaman fita zeyi "Jalal ina zaka? Ya tambayeshi,, be kulashi ba kawai ya fice Kusan 1hr be dawo ba mubarak ya kirashi a waya yaqi dagawa shuru mubarak yayi yana nazari "toh ko kyautan ne ya bata ran jalal? Toh meye laifinshi dan yanason su kasan ce 'yan uwan juna" Kwance yake kamar me bacci yaji shigowan jalal, ahankali ya bude idanunshi yana kallonshi yana qoqarin rage kayan jikinshi "Jalal" ya kirashi ya juyo yana kallonshi "meyasa baka daga wayana ba? Shuru jalal be bashi amsa ba, tashi yayi ya nufi wurin da jalal din yake tsaye "Nasan ba kowa yake jure hakan ba amma mami ta dauke kamar dan da ta haifa ni kuma haka nake jinka kamar wani bari na jikina sam banyi tunanin kyautar mami a wurinka zata sanya ka daina yimin magana amma kayi haquri ka karba saida ni inajin kunyar na maidawa mami kayan nace bazaka karba amma zan gaya mata ta kiyaye gaba" Kallonshi kawai jalal yakeyi har ya qarasa zancenshi yaje ya dauki wayanshi ya fice Kiran mami yayi a waya ta daga ya gaidata "befi 1hr ba da jalal ya kirani yana godiyan kayan nace kasa na qarajin godiya daga gareshi shine fa yayi shuru nace koda abinda yake buqata ne da sauri yace aa" ta qarasa maganan tana dariya "amma ai zaku samu week end kuzo Kaduna ko? Murmushi yayi "mami kinsan tunda na bashi kayan yake fushi na zata kayan ne suka bata mishi" dariya sukayi "toh kaida jalal din ne ai bazan shiga tsakaninku ba" haka sukayi sallama ya koma ciki Kallonshi jalal yayi yanaso yayi dariya amma ya gimtse ya juya kawai yana matsala wayanshi, kusa dashi mubarak yaje "Allah bakada kirki jalal amma bari baji Allah bazan qara daukan miskilancinka ba saboda nine kawai kake yiwa" murmushi yayi yana qoqarin tashi "me kuma nayi? Tsaki mubarak yayi ya nemi wuri ya zauna "pls jalal ka rage wannan rashin maganar pls kaga fa ni dan uwanka ne dan Allah ka daina" kallonshi jalal yayi yana murmushi " mubarak bazan iya yawan magana yanda kake tunani" amma kakeyi da jalilah? Kawar da kanshi yayi yana murmushi ya tashi yayi shirin yin girki Cool jalal kayi mana irin wannan jolof din da kayi ranar da mukayi csc,,, harara yayi mishi yaci gaba shirin girkinshi "sai fa kayi mana" Girki yayi ya kammala "cool jalal ka dama mana kunu" tsaki jalal yayi ya Dora ruwan zafi ya cika flacks da ya ajiye mishi yaje yayi wanka ya dawo ya sami mubarak zaune ya cika plate da abinci ya cika cup da kunu sai faman ci yake,, ko kallonshi beyi ba ya shirya cikin irin kayanda suke jikin mubarak soaai mubarak yaji dadin hakan ya tashi suka fice Kallonsu take har suka qaraso kusa da ita taji mubarak yace "Cool jalal Allah dan kawai banayi ne amma kasan na cika iya girki........ [25/12, 13:21] Hassan Atk: 🤴🤴JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 36-40 Tsayawa jalal yayi yana kallon mubarak yanaso yayi dariya "meye? Sai a lokacin yayi dariya kadan yaci gaba da tafiya Kayi magana mana "no I don't hv anything to say" I know, mubarak ya fada tare dayin gaba abinshi "Toh wai wannan waye? Anya sun taba haduwa ko? Murmushi tayi ta tashi tabi bayansu,, sallama tayi mubarak ya amsa jalal kam ko juyowa beyiba yayi gaba abinshi " amm bawan Allah dakai nakeson muyi magana kuma ka tafi" juyowa yayi ya tsareta da ido ba tare da yayi magana ba "Amm daman inaso nasan sunanka ne saboda kanamin kama da wani" kallon mubarak yayi aiko mubarak ya shiga dariya dan yasan koda sama zata hade jalal bazai gaya mata sunanshi ba "Kinga malam sunanshi Abdul jalal ibrahim" ya juya yabi bayan jalal dan har ya fara tafia Tabbas bazasu rasa alaqa ba Sanye yake da manya kaya farar shadda yayi kyau sosai aciki akeje aka taryo baqin masarautar sarki mahmud sosai suka yaba da hali irin na abdul jabbar basusan tsoron hukuncin mai martaba ne yasa yayi hakan ba dan yasan kowa sai yaji abinda ya aikata wa masarauta Cikin girmamawa yq zube gaban sarki ya kwashi gaisuwa "an gaisheka magajin sarki" Cike da natsuwa ya shiga jera bayani game da baqin da tayasu godiya akan abinda masarauta tayi musu kuma suna tafan alkhairi ga wannan masarauta Sosai sarki Mahmud yaji dadin abinda abdul jabbar yayi dan ba kadan ya burge ba Akayiwa baqi rakiya cool A J ya dawo part dinshi ya sami A K zaune yana jiranshi A K gaskiya dole na dauki mataki "name kenan? Mami zan lallaba ta nemo maganin da zata haihu Allah bazan yarda da wannan aikin sarauta ba kai kaji yanda zuciyana yake kadan ya rage nayi zagi a fada yau" aiko A K yace me zeyi inba dariya ba Wai meke faruwa ne? Tsaki yayi ya shege toilet yayi wanka ya fito ya sanyawa dakin key ya kashe wayanshi suka shiga shaye shaye har sukayi bacci Haka rayuwa taci gaba da tafiya har yakai su jalal ana first semester UG 3 dashi da mubakar ko yaushe zaka gansu da kaya iri daya abdul jabbar da juwairiya kuma suna UG 4 sam ba wani abu da yake shiga tsakanin juwairiya da abdul jabbar saboda ta daina ko kallonshi shi kuma ba damuwa yayi da mata ba Tafiya suke jalal sai faman fushi yake da mubarak wanda ya sanya mubarak dariya saboda ya nuna mishi wata yace sun dace ya aureta shine sanadin fadan har abdul jalal yayi fushi Suka kawowa kusa da motan cool A J kawai ya bude mota wanda sanadin hakan ya sanya ya buge mubarak kuma yayi hakan da gangan saboda ya hango su suna zuwa ta kusa da motanshi "Ashhhh" mubarak ya fada tare da sunkuyawa qasa da sauri jalal ya dawo kusa dashi Mubarak kaji ciyo ne? Kai ya gyada mishi, ya juya yana kallon motan yaga bayada alaman fitowa bale ya bashi haquri kawai ya tashi da sauri juyawa jalal yayi mubarak yayi sauri ya riqeshi "kyaleshi kawai" fisge hannunshi yayi kawai yaje ya janyoshi daga cikin motan ya wankeshi da mari.............. Kallon mamaki cool A J yake mishi wanda sam be hango wannan ba "what's d fillings? Ka buge mutu kuma u can't tell him sorry, who r you and who d you think you are!!!? Ya fada da qarfi Kallonshi A K cike da mamaki Sam cool A J beji me yake fada ba saida tsananin mamakin kamarsu da yake gani ansha gaya mishi akwai wani mai kama dashi amma ya nuna bayason zancen saboda ba gaskiya bane sai ganshi ya gani da kanshi Tureshi jalal yayi ya nufi mubarak ya taimaka mishi ya tashi suka nufi hostel yana riqe da hannun mubarak sai furzar da wani zazzafan iska yake Kallonshi mubarak yayi "jalal kaga abinda na gani ko? Cire kayanshi kawai yayi ya nufi toilet yayi wanka ya dawo Ta bangaren A J kuma mamaki ya hanashi yayi magana sai AK ne yayi magana. "Cool AJ kaga abinda na gani ko? Har voice dinku irin daya ne fa? Ga baki daya cool A J ya rasa me zeyi dan gani yake kamar a mafalki ne "AK r u sure munada kama sosai ko nine nake ganin hakan? Cool AJ Allah bakuda babbanci amma waye wannan?.......... [25/12, 13:21] Hassan Atk: 🤴🤴JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 41-45 Waya ya sameshi yanayi da mami "mami I saw what amazing me wlh Allah I was so surprised da na ganshi yana wannan fadan kuma shi sam be kula da yanda sukayi kama ba fa" murmushi tayi "hope dai ba Inda yake maka ciyo yanzu? "Aa mami saidai kawai inajin tsoron kada su tabashi? Baza suyi mishi komi ka kwantar da hankalinka" toh mami sai munzo week end "Kai kenan komi sai ka fada ko? Bazaka iya shuru da bakinka ba ko? Meyasa kakeson ka zama parrot? Eh na fada ka dakeni idan kaji zafi,,, murmushi kawai yayi sosai masifar mubarak take bashi dariya kamar wani qaramin yaro idan yana magana Zama yayi kusa dashi ya janyo abinci ya fara zubawa a plate sai da ya gama zubawa mubarak ya dauke ya faraci, be kulashi ba kawai yayi kwanciyarshi har saida mubarak ya kammala ya dauka ya faracin ragowar ************************************ Cike da murmushi take kallonshi "abdul kasan dai bakada yaya ko qani ko? Toh kama ce kawai" mami Allah akwai alaqa dan wannan kamar tayi yawa" hmmm meye sunanshi? Mami nifa kawai ya mareni ne yaci gaba da fadanshi ina kallonshi" mari fa kace? Kai ya gyada mata "toh waye wannan? Dan a iya saninta abdul bayada sauki amma gashi har wani ya mareshi be dauki mataki ba "Kaje ka binciko asalinshi" Zaune suke cikin hall suna karatu sai ummi ta kirashi ya daga suka gaisa "jalal meke faruwa dakai ne? Ummi ba komi me mubarak ya gaya miki ne? Aa kawai dai nayi wani mafalki ne dakai,, ba komi Ummi, toh ka yawaita addua kaji? In shaa Allah Kallon mubarak yayi "wai kai bazakayi aski bane? Eh ya bashi amsa,, murmushi yayi ya janye handout dinda yake gaban mubarak "sai fa kayi" dariya mubarak yayi dan yasan koyonshi ne jalal yake "dan Allah ka bani Allah zanje inyi idan na tashi daga nan" aa tashi muje kayi" tsaki yayi "matsala na dakai kenan wallahi" ya tashi ya fice jalal yabi bayanshi Cak mubarak ya tsaya yana kallon cool A J cikin shiga ta alfarma ga baki daya haka ya ganshi kamar jalal din Kallo daya jalal yayi mishi yaji gabanshi ya fadi dan beyi tunanin kamar tasu takai hakan ba amma yayi saurin kawar da kanshi ya qarasa wurin mubarak yaja hannunshi "Malam muje kada mu bata lokaci" kallonshi mubarak yake shima kallonsu yake yana mamakin jalal "AK how r we going to do? Mu bisu kawai,,, no banason raini ya shigo tsakanina dasu Amma kasan da alama ba wanda zai gaya mana komi game dasu saboda duk wanda na tambaya zaice haka ya gansu su biyu kuma basa magana da kowa" Ajiyan zuciya cool AJ yayi "Muje kawai zansa a kawominsu" murmushi AK yayi dan yasan yafi komi sauki a wurin cool AJ Aski aka gamawa mubarak suka fito "cool jalal muje hostel yunwa nakeji" harara yayi mishi "kai kenan da an fara karatu ka fara jin yunwa" eh naji yunwa" dariya yayi "Bari na samo mana snacks kaci amma bazamu je hostel ba yanzu gaskiya" tsaki mubarak yayi yayi gaba ya barshi yana dariya Juyawa yayi dan zuwa siyo mishi snacks din Cike da natsuwa yake tafiya Parking sukayi kusa dashi kawai suka fito suka turashi cikin motan suka fice Kallon juna suke da jalal duk yanda yake tunanin zafin jalal yafi hakan dan yana hangoshi ba irin abinda baa yimishi ba amma amma bayada alaman magana ga wayanshi yana ringing amma sun hanashi ya daga kuma yasan mubarak ne Tunanin halin da mubarak din ze shiga ya sanyashi suke ajiyan zuciya Ahankali ya furta "Abdul jalal" ido cool AJ ya zare "From where? Daya daga cikinsu ya tambayeshi,, ahankali ya dago yana kallonsu daya bayan daya "kafancen" mamaki ne ya cika cool AJ ba alaman qarya a tare dashi amma toh shi iya saninshi basuda alaqa da kafancen asaluma basuda kowa acen toh ya haka? Umurni yayi musu dasu maidashi makaranta Cike da takaici ya siyo snacks ya nufi hall din be sami mubarak ba ya kirashi a waya "jalal kana ina ne dan Allah? Hall kawai ya bashi amsa ya kashe wayan Kallonshi yake cike da tashin hankali "jalal meya sameka? "Mota ta kadeni" ya bashi amsa kawai Sosai mubarak yaji hankalinshi ya tashi "jalal muje clinic a dibaka " harara yayi mishi kaci abinci ba Inda zani" kallonshi kawai mubarak yake yaci gaba da karatunshi Zama yayi kusa dashi "jalal wannan guy din ne yasa aka dakeka ko? Harara yayi mishi "amma kasan banason surutu idan ina karatu ko? Yaci gaba da karatunshi Zaune yake gaban mami yana mata bayanin yanda sukayi da jalal Ikon Allah toh yanzu ya zaayi in ganshi? Mami nifa harda tsoro nakeji "tsoron me? Ai gara na ganshi mami zansa a kawo miki shi" kasa kayi haka kyaleshi Zaune suke a premises na school din "mubarak muje mana bacci fa nakeso nayi" Kallonshi ya maida wurin da mubarak yake kallo Tsaye yake yana kallonsu ya jingina da jikin mota Tsaki jalal yayi wai dama wannan bastard din ne kake kallo? Dariya mubarak yayi jalal yaja hannunshi suka fice Zaune take a gaban mai martaba tana sanar dashi abinda ke faruwa Ya sunan yaron? "Abdul jalal" zaune ya tashi cike da tashin hankali "da gaske kike? Kai ta gyada mishi" Shuru na tsawon lokaci ya shiga tsakaninsu kafin yayi mata izinin tafia Tsawon lokaci yana tunanin wasu abubuwa Zaune yake gaban mai martaba yana mishi cikakken bayani game da abdul jalal,, Umurni yayi da akawo mishi jalal din Ga baki daya mamaki ya cika mami mai martaba kam ya shiga tashin hankali ta wani bangaren kuma ya cika da farin ciki Cike da qasaita ya shiga yi mishi tambayoyi Kamar wanda akayiwa dole duk da hakan ce akayi mishi "Sunana abdul jalal Ibrahim ina zaune a farin kafancen" yana kaiwa nan yayi shuru tare da Sara hade face "A wurin iyayenka kake? Wani kallo ya aikowa mai martaba tare da kawar da kanshi "murmushi mai martaba yayi Aje dashi kafancen nazo da iyayenshi............... [25/12, 13:21] Hassan Atk: 🤴🤴JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 46-50 Kallonsu suna hada ido da mami ya sunkuyar da kanshi tare da ciro wayanshi Mubarak ya kira ya da cike hanzari yake tambayarshi lafia? " ka kwantar da hankalinka zan dawo amma yanzu kafancen zamu tafi wai zaa zo dasu baffa da ummi" lafia dai? Oho maybe suna ganin ba gaskiya na fada ba kawai dai ka kwantar da hankalinka zan dawo kuma kaci abinci yana nan na girka maka" jalal ko inzo muje ne? Murmushi yayi wanda ya qara tabbatarwa da mai Martaba abinda yake zargi "karka damu zan kiraka back" ya kashe wayan tare da qara hade face dinshi Tafia suke cike da gudu har suka qarasa kanfance Jalilah ya hango tana tafia cike da natsuwa murmushi yayi ya nuna musu gida suka shiga baffa na zaune ya tashi da sauri "abdul jalal lafia? Baffa ka kwantar da hankalinka ba komi bane kazo muje ina ummi? Murmushi ya sakar mata lokacin da take fitowa? "Jalal lafia? Be bata amsa ba jalilah ta qaraso da sauri tayi hugging dinshi "ya jalal lafia? Ba komi je ki sanja kayan zamu tafi zaria ne ana buqatar ganin family nane? Wai wa yake buqatar ganinmu? Baffa a masarautarsu ne ake buqatar ganinku muje kada mu bata lokaci mubarak yanacen hankalinshi baa kwance yake ba Da ummi har baffa hankalinsu a tashe yake ba wanda baya addua acikinsu har suka qarasa Parlour'n baqi aka ajiyesu suka zauna Kallon juna suke shida mai martaba cike da tashin hankali baffa yake kallonshi "Dan Allah kada ka tarwatsa rayuwar jalal Alhaji ka barshi yaci gaba da rayuwa cikin natsuwa wallahi bamu karya alqawarin da mukayi ba" Kallonshi jalal yayi "baffa meke faruwa ne? Mai martaba ne ya bashi amsa "ba komi abdul jalal ku tashi ku tafi a maidasu garinsu" "baffa dan Allah meke faruwa ne kada ka boyemin rashin fadamin shine zai tarwatsa rayuwana ummi dan Allah ki gayamin menene? Kallonshi ummi tayi "baffan jalal bayada wani amfani boye mishi ahalin yanzu kayi haquri mu rungumi qaddara mu sanar dashi wannan sirrin kodan kwanciyar hankalinshi" Haba Aisha me kikeso ki gayamin kin karya alqawarin da kika yimishi kenan? Ba haka bane wallahi banason abinda zai sanyashi damuwana ne kwanciyar hankalinshi nake nema Kallonsu mami tayi "wai meke faruwa ne? Ai gara a fada musan koma menene? Cike da girmamawa cool A J yake kallon mai martaba "abba dan Allah ka bari a fada ko muma hankalinmu zai kwanta Tashi jalal yayi "jalal ina zaka? Ummi zan shigo da mubarak ne" ya juya ya fita sai gashi ya shigo tare da mubarak Kallonshi mai martaba yayi "mubarak mustapha azare" kallon mai martaba yayi cike da mamaki yanda yasan sunanshi "Tashi ka ficemin daga gida kada na qara ganinka cikin gidan nan kuma ka gayawa maryam ni sarki mahmud nace ba kai ba abdul jalal idan kuma na qara ganinka cikin gidan nan zakayi dana sani" Kallon mamaki suke mishi mami ce tayi magana "kana nufin yaron maryam ne? Kai ya gyada mata "gaskiya bazai fita ba tunda Allah yasa mun ganeta bazamu bari ta qara bace mana ba" Mami wai me kuke magana dakai ne dan Allah? Wannan da kake gani dan qanwar mahaifinka ne matsala suka samu akan mubarak din tayi fushi tabar yayanta Kallon juna suke shida abdul jabbar "mami jalal fa? Shine nakeso nasan meye alaqarshi da gidan Kallonsu mai martaba yayi Labari ne mai tsayi hafsa amma ya zama dole na gaya muku kuma na nmi gafararki Duk da inada damar yin haka *ASALIN LABARN* Sunana Mahmud Adam ni haifaffen farin zaria ne kuma cikin masarautar zaria iyayenmu Mu biyu kadai suka haifa ni da maryam qanwata wacce nafisonta da komi a rayuwa Lokaci mai tsayi Allah baci kawowa maryam mijin aure ba kasancewar ta zurfafa cikin karatu Sam bata damu da aure ba Lokacin aurena ya gabato lokacin mahaifina yana kan karagar mulki Bayanda mahaifinmu beyi da maryam amma taki amincewa da zancen aurenta da dan gidan sarkin mijittafa haka ya haqura ya kyaleta da yake mutum ne mai saukin kai Na auro hafsat acikin farin zariya saboda na yaba da natsuwarta sai dai duk lokacin da hafsat zata samu ciki zai zube wanda sanadiyar hakan yasa matan mahaifina suka tsaneta kasan cewar mahaifiyarmu bata raye Ba irin wahalar da hafsat Natasha a wurinsu ba saboda wannan matsalar Wata rana hafsat ta samu ciki wanda ya kasan ce shine na bakwai ajikinta sam na hana idanuna bacci ko yaushe ina roqon Allah yasa ta haifa wannan cikin lafia Wata rana hafsat ta tashi da ciyon na quda na dauketa myka nufi asibiti da ita cikin ikon Allah hafsat ta haifa tagwaye Na fito zan tafi masjid na hadu da wasu bayin Allah sai faman kuka matar take mijinta yana bata haquri na riqinshi ya sauwaqe mata Nayi musu sallama suka amsa "bawan Allah lafia? Sunanan malam Ibrahim sunan matata Aisha muna zaune lafia da ita saidai duk lokacin da zata haihu abin baya zuwa da rai shine mahaifiyata tace mayyace ita ke cinye jikokinta wannan shine na bakwai kuma Allah yayi mishi rasuwa shine Mike tunanin baqincikin da zamu fuskanta har take roqona Dana sauwaqe mata ni kuma inason matana na yarda da qadda Cike da tausayi nake kallonsu wanda nake hango baqin cikin da yake cikin zuciyansu saboda nima acikin irinshi na fito Dakin da hafsat take ciki na koma na dauko wanda yake hassan din na fito dashi ba tare da sun ganni ba kasan cewar hafsat tana bacci na fito na samesu "Zan baku Dana bisa amana kuma Ku bashi tarbiya inaso ka sanyashi yayi ilmi kuma kasa ku taba sanar dashi wannan sirrin ka Santa mishi suna abdul jalal Cike da farin ciki suke yi mishi godiya Wannan ba komi bane saidai inaso Ku bani wanda yake naku dan na mayarwa matan dashi saboda Mu sallaceshi a matsayin Santa da ya mutu Gawar suka bani na sanja mishi zani zuwa cikin na abdul jalal na maidashi wurin hafsat Tun daga wannan lokaci ban qara San in halinda suke ciki ba saboda taimako nayi kuma dan Allah nayi shiyasa ban taba nemasu ba kuma ban taba bawa kowa wannan labarinba *matsalata da Maryam* Abdul jabbar yanada wata Biyar a duniya Maryam ta shigo gidan yayanta "Yaya ina wuni? Lafia qalau maryama "Yaya dama mijin da zan aura ne na kawo maka" cike fa farin ciki nayi mata umurnin ta shiga dashi muka gaisa sosai na yaba da halinshi akayi shirin aure ba tare da bata lokaci ba aka aurar da maryama Ranar da maryama ta cika wata goma a gidanta aranar Allah yayiwa mahaifinmu rasuwa tashin hankalin da maryama ta shiga ya sanyata haihuwa ta haifa da namiji haka mukayi faman zaman taaziya wanda farin Zaria ba wanda beji mutuwar ba ajikinshi Yaron Maryam yaci suna mubarak Lokaci kadan aka dauka aka dorani akan karagar mulki Wata rana maryam tazo tana kuka akan mijinta ya saketa wai ta zagi mahaifiyarshi wanda sam jikina be yarda da hakan ba na tura aka kiraminshi yazo na tambayeshi dalilin sakin "Wallahi ko gobe na dawo mahaifiyata ta gayamin tayimata rashin kunya bazata zauna gidana ba Cike da Bacin rai nake kallonshi Nayi mishi umurni da ya kawomin takardan sakina Maryam "Yaya ya zaayi da mubarak so kake ya tashi ba uba? Kallon mamaki nayi mata da takaici " toh ki sani ba Inda zaki bazaki koma gidanshi ba "Yaya gaskiya banson mubarak ya tashi ba tare da mahaifinshi dan bansan wa zai kalla yaji dadi ba "Maryam kuna nufin ban isa ga mubarak din ba? Ka isa Yaya amma ai mahaifi mafine kuma baza samu kamarshi ba "Hakane gaskiya amma kisa ni muddin kika bishi bani bake" Tashi tayi ina kallonta tabi mijinta saboda danta mubarak Run daga wannan lokacin ban qarajin tarihim maryama ba wannan mubarak din da zakuga mahaifinshi zakusan cewa wannan jimin mustapha azarene................ [25/12, 14:04] Hassan Atk: 🤴🤴JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 51-55 Jalal lafia? Ummi bacci zatayi ajina nasani kuma tafia zakuyi" kallonshi baffa yayi yana murmushi "abdul jalal kuzo ku tafi kuyi karatunku kada jalilah ta bata muku lokaci kuma mu anan zamu kwana mai martaba ne yayi umurnin hakan" Kallon ummi yayi ta sakar mishi murmushi shima ya mayar mata "mubarak tashi ku tafi ko? Cike da girmamawa ya qarasa gaban mai martaba "abba dan Allah ka yafewa mami tabbas batayi biyayya a gareka ba kuma tayi maka rashin kunya, abba ka yafeta dan Allah nasan mami rayuwa kawai take ba tare dajin dadi ba saboda abinda ta aikata kuma nasan gudun zuciyanka ne yasa bata dawo ba kuma tunda mahaifina ya rasu ka yafe mishi laifinda yayi maka,,, "mubarak kana nufin mahaifinka ya rasu? Abba ni bansanshi ba saboda inada shekara biyu ya rasu daga wannan lokacin mami ta dawo Kaduna da zama" "Inna lillahi wa inna ilaihin raju'un" abinda mai martaba ya samu damar furtawa kenan daganan ya tashi ya nufi dakinshi ba wanda ya yiwa magana acikinsu Kallon mubarak jalal yayi "muje ko? Murmushi mubarak yayi rana ta farko da jalal yaga tsantsar damuwa a tare da mubarak din dan sam baya sanya abu aranshi Hannunshi mubarak ya riqe sukayiwa su ummi sallama Sam jalal be kalli inda mami take ba haka be kalli cool A J ba Kallon jalilah yayi "gobe kafin ki wuce zan saya miki kayan" dariya tayi "ya jalal wannan wayon fa? Ai bazan hanaka tafia ba" murmushi yayi suka juya "Mami let me drop them" no thanks,,, cewar jalal Mamakine ya cukasu shida mami yaja hannun mubarak suka fice,, kallonshi jalilah tayi tana daria "Allah ya jalal bayada gwani gara ma kada ka sanya kanka cikinsu kaga ai ko ya mubarak yanda yake fama dashi" sosai cool AJ yaji zafin abinda jalal yayi mishi ko ba komi ai shi twins brother dinshi ne sufa jini daya ne Tafia suke yana tsokanar mubarak har suka sami a daidaita sahu suka qarasa cikin school Bayan sunyi wanka mubarak ya kalli jalal "jalal sai dai akwai abinda kayi wanda baka kyauta ba dolene muyi haquri abdul jabbar dan uwanmu ne ba yanda za muyi fa abinda kayi gaskiya baka kyauta ba" Kallon wulaqanci jalal yayi mishi "Allah kada ka qara yimin irin wannan kallon" Murmushi yayi ya kawar da kanshi "jalal pls kada ka qara yi mishi haka" mubarak Allah sai ranar da ya karbi kuskurenshi ya baka haquri zan kalleshi a matsayin mutum" ido mubarak ya zare "wai kai wane irin mutum ne mai kafiya? Kwanciya yayi dan ya gaji da surutun da mubarak yake sanyashi Waya yake da mami yana sanar da ita duk abinda ya faru "mubarak yanzu kana nufin jalal din yaron Yaya mahmud ne? Ikon Allah "Mami ki shirya kizo ki nemi gafara a wurin yayanki dan Allah" murmushi tayi "mubarak gobe zanyi sammako in shaa Allah Yauwa mami sai ki taho mana sinasir kinsan jalal yana sonshi sosai Murmushi tayi aranta tanajin dadin yanda mubarak da jalal din suke son junansu duk da jalal din ba wani magana yake da ba Washe gari da sassafe mami ta kira jalal tana shaida mishi tana cikin school din Sauri yayi ya shirya "jalal ina zaka? Be kulashi ba yayi sauri ya fice Cike da girmamawa ya gaidata "jalal mubarak din fa? Sunkuyar da kanshi yayi "baka gaya mishi nazo bane? Yanajin bacci ne shiyasa bn gaya mishi ba Murmushi tayi "ai ya fito dan gidan yaya mahmud zamu tafi" kiranshi yayi a waya ya sanar dashi zuwan mami Gaidata yayi tare da yi mata sannu da zuwa "Mami ke kikayi driving da Kanki? Eh muje ko? Bata suka shiga ga baki dayansu taja suka tafi Cike da sallama ta shiga ciki sai faman miqa gaisuwa barorin gidan suke saboda akwai wadan da suka santa acikinsu Kallon juna suke itada mami "maryama" da sauri ta qarasa wurinta "aunty hafsa ina yaya" hannunta taja suka nufi dakinshi sukayi nocking yayi musu izinin shiga da sauri ta qarasa gabanshi ta fashe da kuka "Yaya dan Allah ka yafeni nasan na saba maka banyi mana biyayya ba" Zama yayi ta zube a gabanshi "maryama ban riqe ki da komi ba kuma kafin ki roqeni gafara na Riga na yafe miki Kusa dashi ta matsa "Yaya da gaske ne labarin da mubarak ya bani? Murmushi kawai yayi tasan me hakan yake nufi Zaune suke cikin parlour din ya kira Ummi ya sanar da ita suna gidan Zaune suke suna gaisawa dasu ummi Mai martaba yayi gyaran murya suka qaraso shida mamin mubarak da kuma hajiya hafsa Gaisawa akayi da juna wanda mai martaba yana Kyle da jalal shi kadaine be gaida kowa ba sam be daga kai ya kallesu ba Cool AJ ne ya shigo yaje ya kwashi gaisuwa duk wanda yake dakin ba wanda be gaida ba ya nemi wuri ya zauna "Ikon Allah, aunty hafsa wadan nan tagwayen mazan duk ke suka kwaso Amma dai voice din kam nawane dan tun a jalal na gane hakan sai kuma ga abdul naji shima duk daya ne Sallama mai martaba yayi dasu saboda zai shiga fadasukayi mishi fatan alkhairi "Mami za muje school saboda munada lectures" kai nifa bazani ba,,, kallonshi jalal yayi "lectures din ne baza kayi ba? Eh,,, dariya jalillah tayi "ya mubarak sai kayi tayin abu kamar yaro qarami Allah" kawar da kanshi yayi "mami ni zan tafi" mubarak tashi kuje mana,, Ummi Allah ba wani lectures bane kawai shi idan yana kusa baa missing lectures ne" murmushi baffa yayi "mubarak tashi Ku tafi mana" Tashi yayi yana qunaquni ya fice kadan jalal yayi dariya wanda ya fito da kamanninshi da mahaifiyarshi yabi bayan mubarak din Kai mami ta girgiza "mubarak Allah ya shiryeka dan ni bansan irin wannan halin naka ba" Mami ya jalal ne ya takurashi ai,,, jalilah meye laifin wanda yace kaje Neman ilimi? Dariya kawai tayi "Mami zan tafi school inada lectures nima" shine ka bari 'yan uwanka suka tafi? Cewar mamin mubarak Kallon maminshi yayi "mami ya jalal fa bayason tafiya dashi jiyama haka yayi mishi" kamar ya? Ai wannan shashanci ne ta kirasu a waya suka dawo "Mami gani" meyasa Baja kula dan uwanka? Kallon mubarak yayi ya dawo da kallonshi gun mami Au bazakayi magana ba? Sunkuyar da kanshi yayi "Mami Allah nayi mishi magana amm biki amsar da ya bani ba? "Jalal d u want us to fight? Kai ya girgiza "toh ka sanja" kai ya gyada mata "Mami rantsuwa fa yayi akan bazai kalleshi a matsayin mutum ba har sai ya bani haquri akan bigeni da yayi Fada Ummi ta fara yima jalal "yaushe ka zama haka shi din an gaya mana as on ranshi yayi ne? Dan Allah ummi kiyi haquri,,, naji amma banason wannan fadan kaji na gaya maka? Kai ya gyada kuma Ku tafi tare nan ma amsar daya ce Kusa ummi cool AJ yaje ummi sai mun dawo Mubarak da cool AJ ne a gaba jalal yana bata suka qarasa cikin school din Kallon mubarak yayi tare da sakar mishi murmushi "am very sorry mubarak" kai ya gyada mishi suka fice shida jalal yana hangosu suna dariya saboda tsokanar jalal da mubarak yayi sai abin ya basu dariya Wani tunani ya zowa mai martaba ya umurci su Ummi dasuyi sati daya a cikin masarautar wanda hakan sam beyiwa jalal dadi ba Zaune suke shida mubarak suna sanye da kaya iri daya Da gudu ya shigo da mota yayi parking ya fito ya haye saman motan ya shiga zuqar sigari kallon juna sukayi wanda sam cool AJ be gansu ba Jalal kaga me abdul yakeyi? Tsaki yayi "toh meye damuwarka? Dariya yayi Cike da yanga take tafia tana waya har ta qaraso kusa da cool AJ "mummy dan Allah ki bani" cak ta tsaya dan bata kula dashi ba Tsaki taji yayi ya kawar da kanshi daga kallonta "Jalal gafa qawarka cen" sam be kallesu ba ya tashi mubarak yabi bayanshi yana dariya Kusa da cool AJ suka so sam basuyi tunanin zeyi musu magana ba "Hi bros" "morning,,, Cewar mubarak "hey bros jalal excuse me pls Juyowa yayi yana kallonshi "ka bude wayanka mana Ummi zatayi magana dakai Juyawa kawai yayi yaci gaba da tafia............ [25/12, 14:04] Hassan Atk: 🤴🤴JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 56-60 Kallonsu juwairiya tayi cike da mamaki daman 'yan uwane amma suke haka? Duk yanda akayi tagwayene Sam cool AJ be qara kallonshi ba yaci gana dashan sigarinshi ************************************ Zaune yake cikin school tare da jalilah da mubarak Jalilah kije mubarak ya maidaki gidan anjima zamu shiga lecture,,, aa bazani ba Kallonta mubarak yana dariya "zo muje in badaki ajiya kafin mu qarasa lectures din" Sallama yayiwa juwairiya suka gaisa "amm nace kinada lectures ne? Aa lafia dai? Dan Allah ga qanwana ajiya zan shiga lecture ne" Murmushi tayima halillah "zo ki zauna" godiya yayi mata ya juya "ya mubarak" ya juyo yana kallonta "hhhhh karku dade fa kuma kazomin 😉 " aiko ya shiga dariya tare da girgiza kai ya tafi Kallon ta juwairiya tayi cike da murmushi "ya sunanki? Jalilah? Wow nice name,, amma brothers dinki twins ne? Dariya tayi "ya jalal da abdul ne twins ya mubarak qaninsu ne amma maminshi itace qanwar mai martaba" okay kice ke gimbiyace Aa fa ni qanwar ya jalal ce,,, kenan ke gimbiyace ni ba 'yar sarki bace fa,,, Toh ke wacece? Cike da quruciya jalilah ta bawa juwairiya labarin komi har dariya juwairiya take saboda yanda jalilah ke magana "Muje hostel kici abinci ba yanzu zasu fito ba" Zaune suke jalilah taci abinci har ta qoshi suka shiga fira da juwairiya "Bari na danyi bacci kafin su fito ko? Kai ta gyada mata Sosai ran mubarak ya baci dan ba inda basuje nemanta ba amma basuga juwairiya ba kuma ba jalilah "Jalal ka dauki abinnan da wasa fa? Tsaki yayi "kafi kowa sanin halin jalilah fa maybe itace ta janyeta sukayi wani gu daban" Tafe suke sai faman dariya jalilah take daga nesa ta hangosu ta qaraso wurinsu da sauri "ya jalal kun fito? Tsaki mubarak yayi "ina kika je? Hostel nayi bacci Meyasa? Meyasa nace!!!! Ke bakida hankali ne? Ko bikisan zamu nemeki ba? Kallon mamaki juwairiya take mishi "ya mubarak ba budurwarka bace? Shut up pls!!!! Yayi exclaiming da qarfi "Pls come down" jalal ya fada a cen qasa "Kallon juwairiya yayi "sannu ko? Kai ta gyada mishi tare da juyawa ta wuce kawai "Haba mubarak at least ka bari har yariyar nan ta tafi sai kayi fadan mana, gaskiya baka kyauta ba" ita mahaukaciyace da zata tafi da ita? Ya isa haka Kallonshi kawai jalilah take ya juwa ya tafi Dariya jalal yayi "muje jalilah" ni bazani ba ta juya ta nemi wuri ta zauna Sauri yayi ya cimma mubarak "wai kai meye haka? Kai kayi fushi ita tayi fushi Allah zan kyaleku" juyawa yayi ya hangota ta sunkuyar da kanta da alama kuka take Juyawa yayi yaje wurin da take,, dagowa tayi a tunaninta jalal ne tana ganinshine ta qara kuka Dariya ta bashi "jalilah kinga yanda kika daga hankalin jalal ko? Kinga bansan yarinyaar ba nayi tunanin ta gudu da qanwanane shiyasa nayi miki fada sorry tashi muje" toh ka bata haquri tanada kirki sosai Toh naji muje na maidaki kinsan gone zaku tafi " muje mu bata haquri toh Kallonta kawai yake "muje toh,, dole yabi bayanta ya nemi wuri ya zauna ta shiga ciki ta kirata "Ya mubarak gata nan ka bata haquri" kallon jalilah yayi "Yaya ka bata haquri sai Mu tafi" ahankali ya furta sorry ba tare da ya kalleta ba Aa yaya bata haka ake bada haquri ba idan mutum yayi laifi zeyi kalan nadama ne sai ya bada haquri Kallonshi ya mayar gun juwairiya tare da furta sorry ya wani kwanta da kai gefe daya, dariya ya bata "is okay ta juya kawai tana cikin tafia tajiyo dariyansu Kallonsu jalal yake har suka qaraso kusa dashi duo ya wani hade face yayi ya juya Manta dashi muje na maidaki Kallonsu cool AJ yayi har suka qaraso "hey where to? Zan maidata gidane? Kallonta yayi farace sosai ba laifi "muje" aa kuje kawai Pls ya mubarak kuzo da wurin anjima kuma ka zomin da ice cream,, kai ya gyada mata tare da yi mata murmushi *********************************** Juwairiya kada ki fita da Alama akwai hadari fa,, salma Allah bazan dade ba zan dawo Tafiya take ta qarasa wani store ta ciko leda da kayan zaqi tana tafiya tana waya Iskane ya fara tasowa duk mai adaidaita sahu ko taxi idan juwairiya ta tsayar dashi bata tsayawa Sauri take iska ya qara tasowa Duk hankalinta ya tashi aka fara ruwa sosai juwairiya ta jiqe har ta soma kuka ta shiga cikin school Ruwan ya dake juwairiya na tafia take ahankali duk material dinta ya kwanta ajikinta komi nata a bayyane yake Kallonta yake har ta qaraso kusa dashi duk kunya ta kamata cike da rashin kuzari ta biyo ta gabanshi ta wuce Kallonta yake tana tafia duk jikinta a bayyane yake har tausayi ta bashi Ahankali taji ya kira sunanta ta tsaya cak,,, motanshi ya shiga yaja kusa da ita ya tsaya ya bude mata ahankali ta zaga ta shiga Driving yake ahankali har ya qarasa bakin hostel da ita Kallonta yayi duk taji ta tsargu ganin yanda yake kallonta "out" ya furta ba tare da ya kalleta ba ta bude tq fice sum sum ta shiga hostel............ [25/12, 14:04] Hassan Atk: 🤴🤴JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 61-65 Kallonta salma tayi ta shiga dariya "daman wanda beji bari" harara tayi mata ta nufi room dinsu ta sanja kaya ta nemi wuri ta kwanta sosai ta shiga bacci Zaune suke a parlour mami da ummi suna fira jalal da mubarak suna sauraren labarin jalilah "Ya jalal kamin kunshi mana" ido ya zare "ke wai meyasa kike dauko abinda kikasan bazai yuyu ba? Ya jalal kunshin ne bazai yuyu ba? Dan Allah kamin "Jalilah dan Allah ki ajiye zancen kunshin nan Allah banida lafia juriya ce kawai nake" meke damunka? Headache,, Hannunta ta dora saman kanshi sosai ko taji da zafi,, kallonshi tayi cike dajin ba dadi "ya jalal kasha magani? Kai ya gyada mata "toh kaje ka kwanta ka huta mana Murmushi yayi ya tashi yaje kusa da Ummi "Ummi zamu tafi kaina yana ciyo" cike da damuwa take kallonshi "kasha magani? Kai ya gyada mata "toh shikenan Allah ya qara sauki" ya amsa da ameen "amma ummi gobe bazamu hadu ba saboda munada text kuma da alama mubarak ba wani karatu yayi ba zamu tsaya dan ya samu yayi karatun Kai ta gyada mishi "Allah ya kiyaye hanya" ta amsa da ameen ya tashi ba tare da ya kalli mami ba "mubarak muje ko? Tashi yayi yayi sallama dasu ummi suka fice A harabar gidan suka hadu da cool AJ da AK sam jalal be kallesu ba yana riqe da hannun mubarak Daka ganshi kasan yana cikin damuwa shima be wani kula dasu ba saboda yanayin da yake ciki AK kaje kawai gobe za muyi magana ya juya ya nufi part dinshi ************************************ Rikici sukeyi sosai acikin class din amma sam bakajin muryan jalal sai na mubarak "Wallahi a kaduna za muyi hutu gara kawai kasa aranka cen zamu tafi" sam jalal be kulashi ba "tashi muje mu hada kaya" "bafa inda zani na gaya maka a kafancen zanyi hutu" why? Its where I belong" tsaki mubarak yayi "kaci gaba da nacin zance mana Allah wannan nacin naka na yau sai na karyashi Ya tashi kawai ya nufi hostel Dariya jalal yayi "kaji dashi cen ba inda zani" Cike da natsuwa yaje kusa dashi ya zauna, kallo daya jalal yayi mishi ya kawar da kanshi "Bros jalal bros mubarak fa? Kamar bazeyi magana ba cen qasa ya amsa mishi "he is in d hostel" okay can I ask you something? Kai kawai ya gyada ba tare da ya kalleshi ba "Pls did I upset you? Kallonshi jalal yayi shima din ya tsareshi da idanu kawar da kanshi yayi kafin ya bashi amsa "no" okay to meyasa bakason ganina? Idan akan mubarak ne ai na bashi haquri ko? I'm your twins brother so pls tell me if am did something that make you fell bad and you can't tolerate? Tsawon lokaci kafin jalal yace mishi "ba komi" no jalal there is something in your mind just tell me" "I have something to do" ya tashi kawai da sauri cool AJ ya riqo hannunshi "jalal why all this? Saboda kaga na damu dakai? Kallon juna suka tsaya yi "jalal ne ya fara kawar da idanunshi daga kallon da suke yiwa juna Juyo da face dinshi AJ yayi "did I upset you? Kai ya girgiza,,, then why all this? Sam jalal besan me zece dashi ba "pls jalal say something I know you have something to say, so pls just say it "Abdul I don't have anything to say" murmushi yayi AJ yayi "Me zakayi yanzu? Kallonshi yayi badan yaso ba yayi murmushi "gobe zan tafi kafancen" Murmushin yayi shima tare da sake mishi hannunshi ya zauna "meyasa baza kayi hutu anan ba? Ko kallonshi beyi ba dan besan me zai gaya mishi ba Juwairiya ce ta shigo tare da salma ,, lokaci daya jalal da AJ suka kawar da kansu daga wurin da suke AJ harda Jan tsaki ya tashi kawai ya fice Kallonshi jalal yake har ya daina hangoshi ya dauki wayanshi ya nufi hostel......... [25/12, 14:04] Hassan Atk: 🤴🤴 JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 66-70 Kallon juna sukayi itada Salma "juwairiya wannan fadan harda dan uwanshi kike yinshi? Salma dan Allah banason yawan surutu mu jira zuwanshi ki gama abinda kike mu tafi,,, Tsaki salma tayi "Allah juwairiya banason guy dinnan" toh ya zakiyi? Mahaifinki ya zaba miki fa Zaman jiran zuwan anas sukayi wanda ze auri salma har yazo sukayi magana da salma ya tafi abinshi Jalal banda kallon mubarak ba abinda yake har ya kammala ya fito musu da kayan bowel fari "tashi ka shirya zamu fita" banza yayi dashi "amma kaji me nace ko? Tsaki yayi "wai ina zamuje ne? Ka tashi mu tafi Shiryawa sukayi suka fito sosai sukayi kyau cikin kayan mubarak ya tsayar da taxi ya gaya miahi inda zai kaisu Takaici ne ya cika jalal lokacin da ya fahinci gidan mai martaba ne zasu tafi Ko kallonshi mubarak beyi ba yana riqe da hannunshi suka shiga ciki Sai faman miqa musu gaisuwa ake ba wanda yake amsawa cikinsu har suka qarasa ciki Zaune take cikin shiga ta alfarma tana karatun al Qur'ani sukayi sallama suka shiga ciki Saida ta kammala ta dago cike da murmushi tana kallonsu, cike da girmamawa mubarak ya gaidata ta amsa jalal kam kanshi na sunkuye qasa mubarak ne yake magana "Mami gobe zamu tafi ne shiyasa mukazo mu gaidaku" murmushi tayi ta tashi ta nufi part din mai martaba bata jimaba ta dawo tayi musu umurni da su biyota Zaune yake cikin parlour yana kallon labarai sukayi sallama ya amsa musu suka shiga ciki Cike da girmamawa mubarak ya gaidashi amma jalal kanshi yana sunkuye qasa "Mubarak ya karatu? Alhamdulillah abba,,, dama gobe zamu tafi kaduna ne muyi kwana biyu sai mu tafi kafancen saboda taya baffa aikin gona" murmushi mai martaba yayi sosai kuma zancen na mubarak ya bashi dariya Zaune suke shuru ba wanda yake magana saiga cool AJ ya shigo da sallama suka amsa ya nemi wuri ya zauna ya kwashi gaisuwa "Abba mu zamu tafi" oh bros mubarak da wuri haka? Murmushi yayi "jalal yanada wurin da zai tafi ne" Ahankali jalal ya dago ya kalli mubarak ya sakar mishi harara murmushi yayi tare da kawar da kanshi Murmushi mami tayi da suka hada ido da mubarak Basusan ko meye acikin envelope din da mai martaba ya basu ba mubarak ya amsa yayi godiya "Zaku koma school ne? Matse hannun mubarak jalal yayi suka dago suka kalli juna "bros jalal nafa ganka" murmushi yayi suka fito tare da cool AJ Tsaye sukayi mubarak ya fara fada "Allah bakada kirki kai kenan komi sai anyi maka gyara Allah baka kyautawa kuma zan gayama ummi Allah" kallonshi yayi ya kawar da kanshi ganin mubarak ya harareshi qara juyowa yayi suna hada ido yayi dariya badan yaso ba Sauke labulen mami tayi tana murmushi tare da mamakin halin jalal din sam be taba gaidata ba kuma atunaninta harda mai martaba be taba gaidashi ba AK ne ya shigo suka gaisa "Cool jalal muje ko? Kasan fa akwai saqon jalilah" kallon juna sukayi "cool jalal and cool AJ" that is nice,,, cewar AK murmushi mubarak yayi suka juya Kallonsu AK yake har suka fice yayi murmushi kawai suka nufi dakinsu Duk yanda mai karatu yake tunanin Bacon ran jala yafi hakan a lokacin da baffanshi yake sanar dashi yanda sukayi da mai martaba "baffa wai meyasa yakeso ya shiga rayuwarmu ne? Gaskiya bazamu koma cikin wannan masarautar da zama ba meye alaqanmu da ita? Kuma zancen masu yi mana aikin gona gaskiya bama so dan ba gazawa mukayi ba" Murmushi baffan yayi "jalal nima banso hakan ba amma banida zabi saboda wani dalili kuma banaso hakan ya sanyaka damuwa kaji,,, shuru yayi ummi ta karbi wayan taci gaba da kwantar mishi da hankali Dariya mubarak yayi ya Santa kayan cikin mota suka nufi Kaduna Sosai mami tayi hidima dasu Zaune suke a parlour mubarak yana buga game jalal yana aiki da system dinshi Mami ce ta shiga ta zauna kusa da jalal "dadina ya yoron nan yasan computer" dariya mubarak yayi jalal kam kunya ma yaji Three days sukayi a Kaduna suka nufi zariya kasancewar su ummi sunzo kuma zuwan ga baki daya ne Kowa yana farin cikin ganin wani jalal yana zaune kusa da baffa sai faman magana suke qasa qasa ba wanda yake jiyo abinda suke tattaunawa akai Gyaran murya yayi ya shigo kowa ya shiga miqa gaisuwa ya nemo wuri ya zauna kowa yayi shuru yana saurarenshi "Malam Ibrahim bana nuna mulki bane akanka said an ganin hakan ba wani abu bane a wurina kuma nasan ka fahinceni,,,, abdul jalal dawowarka anan bayana nufin mune iyayenka ba nasan zakayi wani tunani aranka wanda ba haka bane dan haka inaso kowa ya cire wani kwankwanto acikin zuciyanshi" ya qara da cewa maryama zama ba aure ba naki bane nasan koda ban fada ba kinsman dalilin wannan maganar dan haka inaso ki shirya ranar jumaa zan daura aurenki da alhaji sadiq wafa Murmushi kawai tayi ga baki daya dariya ta cika mubarak Mai martaba ya tashi ya fice sukayi mishi fatan alkhairi Kallonta mubarak yayi "Allah ranka zai baci" aiko ba ahiri yayi dariya " mami me kuma nayi? Cool jalal ne ya sanyani dariya fa" bata qara kulashi ba su ummi suka nufi part din da aka basu "ya jalal ai zakamin kunshi yau ko? Kai ya gyada mata "amma banason black red kawai zaamin" nan ma duk amsar daya ce Duk wani abu da suke buqata ba wanda babu komi an tanadar musu *8:30pm* jalal yana zaune yana Yuma jalilah kanshi mamin mubarak ga baki daya mamaki ya cikata ganin yanda jalal ya tsara kunshin kai bazakace namiji ne yayi ba haka mubarak din yake kallon ikon Allah "Ummin jalal wai dagaske ne abinda nake gani? Hmmm jalal kam yafi hakan indai jalilah zaayiwa Allah mai iko Toh yaushe zaa yimin nawa? Dariya mubarak yayi "cool jalal zaka iya na amare ko? Duka taki mishi ya goce yana dariya "mubarak wallahi ka kiyayeni........... [25/12, 14:04] Hassan Atk: 🤴🤴 JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 71-75 Ummi ma dariya tayi "mubarak Allah zamu bata idan baka daina ba" mami na daina basai mun bata ba Zaune yake gaban mai martaba cike da girmamawa "abdul jabbar yanzu ka kusa kammala karatu inaso ka nemi matan da zaka aura kafin kaje service zaayi auren in yaso duk garinda aka turaka sai kaje da iyalinka " Sosai yakejin zuciyanshi yana bugawa yayi godiya ya tashi har jiri yakeji Tafiya yake jiri na dibanshi shi sam bayaso mace ta shigo cikin rayuwarshi ya tsani abinda zai hadashi da bace ya fison ya qare rayuwarshi ba tare da yayi aure ba" Kallonshi jalal yake yana tafiya kamar wanda zai fadi ya matsa kusa dashi kamar bayaso yaji me yake cewa "Are you sick? Kai ya griza mishi "bros I need your advice but not yet,,, why? Am not in the mood" kallonshi yayi yanayinshi ga baki daya ya sanja kai kawai ya gyada mishi ya juya ya fice Sosai yasha giya a wannan ranar amma duk da haka be samu yin bacci ba saboda sanin halin mai martaba yasan idan ya fada toh sai ya cika koda be kawo wacce zai auraba toh zai nema mishi da kanshi Tsawon kwana biyu kenan jalal yana kule da yanayinda abdul jabbar yake ciki amma sam beyi yunqurin tambayarshi ba dan a tunaninshi ba huruminshi bane tunda ba mubarak bane Su mubarak sun shirya sun koma school kasancewar jalal yace shi sam bazai zauna a gidan ba school zai koma Zaune yake cikin mota idan yasha sigari ya kurba giya ya dan kwantar da sit dinshi Kallon mamaki mubarak yake mishi dan beyi tunanin shaye shayen sun kaishi ga shan giya ba Jalal ne ya qaraso kusa da mubarak yaga hankalin mubarak baya kanshi ya mayar da hankalinshi kan Abdul din Lokaci daya yanayinshi ya sanja ganin a rubuta gulder Duk yanda yaso kyaleshi dan bayason shiga harqallarshi amma yaji bazai iya ba cike da zafi ya janyoshi cikin motan ya karbi sigari da giyan ga baki daya ya jefar dashi ya hadashi da mota sai faman huci yake "kai me kake nufi ne? Saboda kanada sai ka riqa sabawa Allah? Toh bari kaji wallahi kana gab da mutuwar qasqanci inhar baka gyara tsakaninka da Allah ba dan zakasha wannan kayan mayen ka dauki mota ka fita kayi mummunan hatsari wanda zai kaika ga mutuwar qasqanci" yana kaiwa nan ya wani tureshi yaja hannun mubarak iyaka qarfinshi yake Jan mubarak har suka qarasa hostel Kallonshi kawai mubarak yake idanunshi sun kada sunyi jajir sam mubarak beyi yunqurin yi mishi magana ba ganin yanayin da yake ciki Tunda suka fice yake tsaye ya rasa wane irin tunani zeyi ga baki daya jin jikinshi yake kamar bashi ba ya haqura ya bude motanshi ya shiga ya kwantar da sit ya shiga baccinshi Tsawon kolaci cool AJ yana bacci cikin mota ba tareda damuwa ba haka yayita faman bacci tsawon 3hrs Dan tsaki yayi yaja motanshi ya nufi gida direct part dinshi ya nufa ya shiga toilet yayi wanka ya sanja kaya yayi sallah ya nufi part din maminshi Ahankali take mishi magana "abdul ka sanja rayuwanka wanda ba haka nasanka ba gayamin damuwarka? Shuru yayi kafin ya fara magana "Mami wallahi koda mafarki nayi da mace a wunin ranar zan wuni zuciyana yanamin zafi wanda dalilin ne banason muaamala da mace Akwai waya juwairiya mami aranar Dana taimaka mata zuciyana nayi tunanin zata FASA qirji nane kuma ganshi mai martaba yace na fitar da matan da zan aura, mami wallahi ni kadai nasan me nakeji idan naga mace wannan jalilar din ma ita ke hanani gaida su ummi" Sosai mami taji hankalinta ya tashi amma bata nuna mishi ba Saboda bakason aure shine ka tsani mace? Kai ya shiga girgizawa Tashi ka tafi Tashi tayi ta shiga zaga dakin ahankali tana tunanin ko aljanace ta auremin yaro? "Inna lillahi wa inna ilahin rajiun" haka ta shiga nanatawa tsawon lokaci Daya daga cikin bayin tasa ta kira mata ummi sai gasu sun shiga a tare Zama tayi suna fuskantar juna "ummin jalal nasan zakiyi mamakin wannan kiran da nayi miki toh ba wani abu bane face wata matsala da nakeso muyi shawara ni dake saboda yanzu kece 'yar uwata ta kusa" Kai Ummi ta gyada mata ta shiga bawa ummi labarin halinda cool AJ yake ciki Kwantar mata da hankali ummi ta farayi daga bata ta nuna mata wannan ba wata matsala bace jalal ma zai iya taimaka mishi basai zancen yakai ga baffan jalal ba Murmushi tayi "toh taya jalal din zai taimaka mishi? Zan turoshi sai kiyi mishi bayanin komi" murmushi tayi tare da girgiza mata kai Idan kikayi mishi bayani ma ya wadatar Murmushi ummi tayi dan ta fahinci da jalal din da ita kowa bayason mu'amala da wani Waya ta daga ta kira jalal ta gaya mishi idan ya samu time yazo tana nemanshi "Zanzo yanzo in shaa Allah" Kalllon mubarak yayi da yake bacci kawai ya yake shawarar ya tafi shi kadai Part din mami ta nufa dashi "Ummi me za muyi acen din" jalal banason shashanci Shuru be qara magana ba suka nufi dakinta tare da yi mata sallama Sanin halin Ummi ne yasa ya gaida ta cen qasa kamar bayaso taji Murmushi kawai tayi dan ita rana ta farko da ya gaidata kuma tanada yaqinin akan Ummi ne ya gaidata "Jalal matsala ce ta task wacce ta shafi dan uwanka" cike da tashin hankali yake kallonta "Ummi wallahi be gayamin kinsan halin mubarak ya fiye wasa" Kallonshi suke ga baki dayansu "Ummi Allah be gayamin ba amma zan tamabayeshi" Jalal mubarak ne kadai dan uwanka? Shuru yayi ba tare da ya amsa mata ba "ka amsamin? Kai ya girgiza Tashi ka tafi,,, ummi dan Allah kiyi haquri nayi tunanin mubarak din kike nufi" tashi ka tafi nace Ummi dan Allah ki yafeni,,, yayi magana a raunane "Jalal me abdul jabbar din yayi maka ne ka tsaneshi haka? Ummi Allah ban tsaneshi ba kawai dai nashi raayin daban ne da nawa" shine kuma bazaka yi qoqarin ganar dashi ba? Shuru yayi tare da sunkuyar da kanshi qasa Dan tsaki tayi kafin ta fara yi mishi bayani akan matsalar abdul din Nasan zaka iya basai baffanku ya Sani ba shiyasa na kiraka ana kasa yazo yaji muna zancen Kai ya gyada mata "yau zaka dawo? Yana gidane? Bari abincika aji Kiranshi mami tayi ya gaya mata gashi nan zuwa Tunaninshi qara jalal ya kawoshi yanashan giya ya nemi wuri ya zauna Kallonshi jalal yayi "ummi bani miski " Tashi tayi taje ta dauko mishi ta kawo Dawo nan ka zauna Ba musu yaje kusa dashi Duk wani joint nashi jalal saida ya sanya mishi miski Kallonshi kawai suke Kunnenshi daya jalal yasa yatsanshi ciki sosai ya fara yi mishi karatu acikin daya Mami kallon ikon Allah kawai take da sauraren qiraa mai shiga zuciya Tsawon lokaci yana mishi karatu har yayi bacci jalal be daina ba Kallon ummi yayi tare da kwantar dashi da kyau "gobe zanje kafancen" Allah ya kaimu, tashi kawai yayi ya fice Kallo mami tabishi dashi tare da yima Allah godiya........ [25/12, 14:04] Hassan Atk: 🤴🤴 JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 76-80 Tsawon lokaci ya dauka yana bacci kafin ya samu tashi daga bacci Kallonshi ummi tayi ta sakar mishi murmushi ya tashi ji yake kamar yayi wani aikin gajiya "Tashi kaje kayi wanka" ba musu ya tashi har mamakin lokaci yayi Washe gari jalal yasa mubarak yayi mishi rakiya zuwa kafancen sukaje Kallonshi kawai yake yana yana diba sayyun itatuwa Wai me zakayi dasu ne? Ummi ta sani nemansu mana Haka suka gama abinda suke suka dauko hanya suka dawo zariya Kallonshi mubarak yake yana hada sayun ya gama ya hada man shafawa Sayyun itatuwa da zaitun da habbatus sauda Zanje wurin ummi,,, harara yayi mishi ya tashi shima ya sanja kaya zuwa irin na jalal din Cike da girmamawa suka gaida ummi "jalal ka gama hada maganin? Eh kawai yace "toh muje ko? Part din mami suka nufa harda mubarak din Suka sameta kishingide ta tashi zaune suka gaidata Ummin jalal dazu ko na tura a kiraki akace bacci kike Ciyon kaine ya sani bacci Toh da sauki dai ko? Alhamdulillah gaskiya Abdul din fa? Bari na kirashi yanzu ya bar nan ta daga waya ta kirashi ya shigo da sallama "Ummi wannan zai riqa shane wannan kuma zai riqa shafawa ne idan ze kwanta" Toh meye matsalan? Sai bayan kwana uku zan gaya miki "Bros jalal na menene? Ko kallonshi beyi ba bale ya bashi amsa Bakaji me yake cewa bane? Kallon mubarak din yayi ya aiko mishi da saqon harara Murmushin dole yayi tare da kawar da kanshi Ummi zamu koma school Ummi kin soya nama? Mubarak jalilah ce ta cinye sauran saidai kazo anjima ko gobe Wannan yarinyar ta fiye kwadayi wallahi Kallonshi jalal yayi "toh meye damuwarka? Ba shiri jalal yayi dariya dan yanayin yanda mubarak din yayi magana ba kadan ya bashi dariya ba "Wai jalal idan ba mubarak ba ba wanda yake sanyaka dariya ne kome? Ummi dan Allah ki daina yanzu zaice saboda nayi mahaukaci dashi ne Dariya sukayi lokaci daya mubarak da jalal suka tashi har sun kusa fita daga dakin jalal ya juyo yana kallonshi alama yayi mishi da yazo Wuri ya nema suka zauna mubarak kam tashi yayi ya matsa yana amsa waya Kallonshi jalal yayi cikin ido "Ka riqa addua kafin ka kwanta ka daina sauraren waqoqi nan da kake saurare basu da amfani ga rayuwarka" CD plate ya bashi "ka sanyashi acikin motanka ka zubar da wadan nan" kai ya gyada mishi yana murmushi "Giya illa ce ga rayuwarka ka daina shanta kafin kayi dana sani" nan ma kai kawai ya gyada mishi Jalal ne ya fara tashi yana kallon mubarak "malam wayan nan ya isa haka mana" Kashe wayan yayi "jalal Allah yunwa nakeji" dariya yayi tare da kawar da kanshi daga kallon mubarak din "Toh muje" wai ka dafa wani abune da zakace muje,, part din ummi mubarak ya nufa Binciken food flacks din ya fara "yauwa ai da sauran naman" Jalilah ce ta shigo da alama daga school take ko kallon jalal batayi ba shige kawai Bayanta yabi ya sameta tsaye kusa da mubarak sai shagwaba take zuba mishi Tana ganin jalal kawai tayi ciki yabi bayanta Hijab dinta ya cire ya qaraso kusa dashi "jalilah fushi kike dani? Kyaleshi tayi "bazakimin magana ba? Ya qaraso kusa da ita har suna juyo numfashin juna "gayamin me kike yima fushi? Ba komi Amma kike fushi? Ya fada a raunane "toh meyasa jiya kazo na hangoka ina sauri kawai ka fice dan kada ka ganni" murmushi yayi "sorry ummi ce ta aikeni shiyasa kikaga ban tsaya ba" juyawa tayi da sauri ya juyo da ita "bazaki daina fushin ba? Toh zaka sayamin ice cream? Dariya yayi cike da qasa ita Zan saya miki,, dariya tayi ta fada jikinshi rabata yayi da jikinshi bari naga ko mubarak ya gama zamu tafi ne "ya jalal" juyowa yayi yana kallonta "hhhhhh yau kunyi kyau" murmushi kawai yayi ya fice daga dakin Zaune ta samesu ta zauna kusa dashi "ya jalal na samu qawa tanada kirki sosai" kinsan banason wannan shirmen ko? Maza ki rabu da ita Kwantar da kanta tayi ajikishi "ya jalal kayi haquri Allah tanada kirki sosai" Murmushi mubarak yayi ganin yanda suka kafe juna da ido gashi ta wani shigewa jikinshi kamar wata mage "Ya jalal kayi haquri? Kai ya gyada mata har lokacin tana jikinshi Ummi ce ta shiga kallonsu tayi ba wanda ya kula da ita cikinsu jalilah hankalinta yanaga chatting din da jalal yakeyi "jalal meye haka? Ummi menene? Harara tayi musu "ko yaushe sai fadan da nake maka bazai shiga kunneka ba ko? Jalilah Allah na qara ganinki jikin jalal rankin zai baci" kallon juna sukayi Tsawa ummi ta daka mata da sauri ta tashi ta nufi dakai tana kuka Tashi yabi bayanta ya sameta kwance tana kuka Dariya yayi "jalilah tashi kiji" ba musu ta tashi Share hawayenki kiji,,, Ta share hawayenta "banason kina yawan kuka kinsan banason wannan kukan ko? Toh me nayi takemin fada? Ya isa banason irin wannan surutun Jikinshi taje ta kwantar da kanta "yaushe zaka kawomin ice cream din? Tashi yayi "anjima zan kawo miki amma ki tabbatar kinje islamiyya Kai ta gyada ya fice ya sami mubarak sukayiwa ummi sallama suka fice.............. [25/12, 14:04] Hassan Atk: 🤴🤴JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 81-85 Sai mami tayi da gaske kafin cool AJ yasha maganin sai yace ba dadi tsawon kwana uku kenan ummi ta kira jalal "jalal ba yaune zakazo ba? Ummi muna hanya ai" Zaune suke a parlour'n mami ta kira cool AJ yazo suka gaisa Kallonshi jalal yayi da kyau "zo nan" ba musu yaje amma gaskiya ji yake kamar zuciyanshi zata fashe ga baki daya ji yake ya tsani jalal din "Mubarak zo ka gani" ba musu ya matsa kusa dashi "riqemin babban yatsanshi" haka ko akayi kallonsu kawai mami da ummi suke Wani magani ya fitar ya fara shafa mishi acikin kanshi ko ina kafin ya shafa mishi a face dinshi Hade face yayi yana yiwa jalal mugun kallo "wai me kakeyi ne haka? "Mubarak sakeshi kawai Karatu jalal ya fara yi ba tare da ya riqeshi ba da sauri ya tashi ya shiga zaga dakin jalal ko kallonshi beyi ba yaci gaba da karanto ayoyin al Quran Tsawon lokaci yana karanto ayoyin masu ratsa zuciya cool AJ sai faman zaga dakin yake Cike da razana suke dafe kunnayensu sakamakon qarar da yayi ya fadi Kusa dashi jalal ya matsa yaci gaba da karatun ahankali bakinshi ya fara motsawa Shuru jalal yayi yana kallonshi " 'yata ke sonshi ni kuma ba abinda zata nema na bari ta rasashi" A iya tunaninki akwai aure tsakaninsu? Wannan ba damuwata bace Idan na qonaki nayi laifi? Kada kayi haka Meyasa kika bata rayuwanshi? Bani bace,,, "qarya kike" dan murmushi yayi "Idan har banyi hakan ba duk mace ta gari zata soshi daga baya na gane hakan ba mafita bace sai na sanya tsanar mata acikin zuciyanshi" "Abu mai sauki ne na qonaki amma zanyi miki adalci" Kada kayi tunanin zan rabu dashi dan 'yata ko yaushe tana ganinshi tana kasancewa cikin farin ciki ni kuma bazan rabu dashi ba" Kinsan a ina 'yarki take yanzu? "Ka daureta acikin jikinka" Kinsan dalilin yin hakan? Aa Jikina tamkar garwashi yake a wurinta zan azabtar da ita kafin in qonata ne kamar yanda zan qonaki Amma kasan sauran 'ya'yana bazasu barka ba? Murmushi jalal yayi "ba abinda zasu iya dani dan ke kanki biki iya aikata komi ba" Kana ganin idan kayi hakan zaka zauna lafia? Murmushi yayi ya fara karanto wasu addu'o'i Nan take ta fara ihu "Zan barshi basai ka qonani ba" sam jalal be saurara mata yaci gaba da qonata Tsawon lokaci tana ihu har tazo ta daina ga baki daya Shuru yayi yana kallon cool AJ Sanyayar ajiyan zuciya ya sauke Dafe zuciyanshi yayi "ummi bani ruwa" da sauri mubarak ya miqa mishi yasha Duk idanunshi sun sanja zuwa ja kallonshi kawai suke "Jalal lafia? Kai ya girgiza sai faman gumi yake Lokaci daya kuma ya fara kakkarwa "jalal wai lafia? Ummi ta riqeshi "Mubarak tashi ka fita" Lafia? Tashi nace Tashi yayi yana tafia yana waige "Ummi dan Allah ki yafeni ba lallai bane na rayuwa kuma nayi hakan ne saboda abdul jabbar ya samu lafia nasan zasu ilkatani amma nayi miki alqawarin zan qonasu kafin nabar duniya, ummi dan Allah kada ki bari mubarak ya shiga wani hali akan rashina" Jalal meyasa kayi haka? Cewar mami duk hankalinta ya tashi "Ummi bani ruwa " karatu ya shigayi yana tofawa a ruwan tsawon lokaci kamar numfashinshi zai dauke Zubawa yayi ajikinshi wani zafi yaji duk ya fita hayya cinshi Daqyar yake numfashi Ahankali har ya fara samun natsuwa mami ga baki daya hankalinta atashe yake sai faman jera addua take Ahankali ya dago yana kallon ummi "ummi zai dauki tsawon kwana uku yana baccin nan a nemo wadan da zasu sanja mishi wurin kwanciya "Jalal kai kuma fa? Kallonta yayi "Ummi jinin da yake jikina kadan ya rage bazai wadaceni na rayu ba" nan take ummi ta gane matsalar saboda ta taba faruwa da baffa Da sauri ta kira mubarak "muje a kaishi asibiti da wuri a qara mishi jini kafin ya mutu" Jinin mubarak aka fara gwadawa cikin sauri aka fara qara mishi jinin Duk wannan abinda da ake mai martaba be sani ba haka baffan jajal Mami kam hankalinta be kwanta ba ta kira mai martaba ta gaya mishi halinda ake ciki Da sauri suka nufi hospital din har ya fara bacci mubarak kam har idanunshi sun kumbura saboda kukan da yake A&E ga baki daya cike take saboda zuwan sarki Mahmud Kallonshi baffa yayi yayi murmushi "Aisha yaron nan naki bayada jarumta fa" haba baffan jalal na'ima saida aka qara mana jini" toh meye abin roqon gafara? Murmushi mai martaba yayi "Allah ya bashi lafia" suka amsa da ameen Kallon mubarak yayi ya sakar mishi murmushi Zaune suke tare da baffan jalal "wannan shine na farko da yayi shiyasa kuma bata bayn gida yazo musu ba saboda zuciyanshi ta riga ta kawo kawai ya tunkaresu Murmushi mai martaba yayi Zaune suke gaban AJ sai faman bacci yake Kallon mai martaba baffa yayi "sun cutar da yaron nan ba kadan ba kuma matsalan basu zauna ajikinshi ba bale a gane da wuri" jinjina lamarin mai martaba yayi Washe gari jalal yana kwance ya juya yana kallon mubarak murmushi sukayi juna Mamin mubarak ce ta shigo suka gaidata tayi musu ja jiki Abinci ta zuba musu sai faman hararan jalal mubarak yake "malam lafia? Meye damuwarka dani? Kawar da kanshi yayi yana murmushi ********************************** Da salati ya bude bakinshi ahankali ya fara bude idanunshi ya qarewa dakin kallo Sannu mami tayi mishi jin zuciyanshi yake kamar an dake mishi dotse akanta Kallonta yayi "mami jalal fa? Murmushi tayi mishi Je kayi wanka kazo ka rama sallar kwana uku Ido ya zare "mami kwana uku fa? Kai ta gyada mishi Tashi yayi ya nufi part dinshi yayi wanka ya shiga reja sallolin da make binshi Ba yanda ummi batayi ba akan jalal yazo su tafi gida yace shi school ze tafi dole mubarak ya haqura yabishi suka tafi............ [25/12, 14:04] Hassan Atk: 🤴🤴 JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 86-90 _Allah ya gafarta miki aunty amina yasa aljannah ce makomarki_ *ameen* Kwance suke bayan sunyi wanka kowa da abinda yake tunani aranshi, wayan jalal ce tayi ringing ya diba yaga new number ne ya daga tare da kwarara sallama Ta dayan bangaren kuma cool AK ne ya amsa "bros jalal where r u? Shuru yayi kamar bezeyi magana ba "Hello" sai a lokacin yayi magana "am in d hostel" okay which room you guys r? "7" okay ya katse wayan Kallonshi mubarak yayi "waye? Abdul" Ni dan Allah ka hadamin kunu Allah shi nakeso nasha "Kai bazaka iya bane? Eh bazan iya ba Ko kallonshi jalal beyi ba bale ya tashi Sallama yayi suka amsa mubarak ne kawai ya tashi amma jalal sam bayada alaman tashi suka gaisa "Bros jalal jikin ne? Kai ya girgiza mishi alaman aa Murmushi yayi ya zauna kusa da mubarak suka dan fara taba fira "Jalal amma kasan inajin yunwa ko? Tsaki yayi ya sauko ya dora ruwan zafi ya dama mishi kunu ya zuba a cup saura kuma ya juye a flacks Qin dauka mubarak yayi "Allah idan yayi sanyi kamin magana zakasha mamaki" toh ka bani ne? Ya fada yana hararan jalal din Murmushi cool AJ yayi "you guys r very funny" Kwanciya jalal yayi abinshi mubarak yaqi daukan kunun tsaf jalal yasan mubarak ba dauka zeyi ba ya sauko ya dauka ya bashi "sai ka zubamin ajiki ne? Eh ya bashi amsa "Bros mubarak wai haka kuke fada? Bakasan waye cool jalal ba ai wallahi hurt jalal yafi dacewa dashi Aiko jalal saida yayi dariya dan mubarak din ya fiye rikici Haka mubarak da cool AJ suka sha fira abinda mubarak ya fahinta kusan halinsu daya kawai dai abdul din yafi jalal yawan magana Lokacin sallah ne yayi mubarak yace ba inda zashi a ciki zeyi sallah "Allah baka isa ba sai kaje" sai kamin dole "sai fa kaje" tsaki kawai yayi jalal yazo yayi tsaye gabanshi suka shiga kallon juna Jalal kasan dai baa wasa da sallah ko? Sai fa kaje masjid din Tsaki yayi ya janyo kaya irin na jalal din ya sanya yayi gaba jalal yabi bayanshi yana dariya Sosai cool AJ yaji sun burgeshi shida jalal ne a baya mubarak yana gaba suka qarasa cikin masjid din jalal yaje kusa dashi ya tsaya Sosai ya basu dariya ganin ya sanja wuri Jalal da AJ ne suka daidaita suka fara yin sallah AJ yan bin jalal har suka kammala Mubarak ya rigasu fita ya nufi hostel Lokaci daya suka dago dan satar kallon juna aiko suka hada ido jalal yayi sauri ya kawar da kanshi murmushi AJ yayi "Amm rakani mana" kallonshi yayi "akwai wanda nakeson gani" juyawa sukayi Kowa ya gansu baya buqatar tambaya yasan jini daya ne Wuri ya nema ya zauna yana jiranshi ya gama magana da AK ya juyo yana kallonshi tare da sakar mishi murmushi ya tashi kawai suka fara tafia Kallonta yake yana nazarin wasu abubuwa kallonshi ya maida ga hannunta ba alaman jin ciyo har ta kawo kusa dasu ba tare da kallesu ba ahankali ya sauke ajiyan zuciya wanda ya sanya jalal ya kalleshi Hanya jalal ya sanja yaje ya siyo coke guda biyu suka nufi hostel Kallon coke din mubarak yayi jalal yayi mishi harara ya cire kayan jikinshi Supergetti da kifi jalal ya dora sosai ya bawa abdul dariya ganin yanda yake girkin kamar mace ya kammala ya juye a food flacks ya tashi ya fita Be jimaba ya dawo da qanqara a hannunshi ya fasa ya ya zuba a cups ya dauko plate ya ajiye musu kawai ya nufi toilet yayi wanka AJ tunanin yanda zeci abincin yake dan ganin yake bazaiyi dadi ba haka ya zuba abincin yakai spoon daya a baki Sosai yayi mamaki test din abincin Kallon mubarak yyi yaga shi sam hankalinshi baya kanshi ci kawai yake Ba wanda ya kalla daga cikinsu ya sanja kaya da alama fita zeyi "Malam ina zaka? Meye damuwarka? Bafa inda zaka Tsaki kawai yayi ya mayar da kayan ya dauki ragowar abincin mubarak yaci kadan yayi kwanciyarshi Haka suka wuni a hostel din AJ sai faman dariya yake ganin fadane kawai tsakanin jalal da mubarak kuma ba wanda yake tsallake zancen wani Sun gama sallah isha cool AJ ya kallesu cike da murmushi "bros zan tafi bacci nakeji" dariya mubarak yayi toh muje muyi maka rakiya ko? Tafiya suke sai mubarak ne kawai yake zuba surutu Wurin da yayi parking suka tsaya ya bude motanshi ya shiga ya tada motan "bros abdul ka sayamin ice cream wa jalilah dan Allah" cewar mubarak Kallonshi yayi yana murmushi tare da gyda mishi kai sukayi sallama dashi suka juya Kallonsu yake suna tafia da alama jalal magana yake yiwa mubarak kuma serious magana ce Waya take har ta qaraso ta wurin da cool AJ yake Kallo daya tayi mishi ta kawar da kanta tayi taci gaba da tafia kamar ya tsayar da ita kuma yaji sam bazai iya yi mata magana ba har ya daina hangota Gida ya nufa cike da tunani a zuciyanshi Tsawo sati daya cool AJ ko yaushe a hostel yake wuni idan sunada lectures su tafi su barshi haka shima idan yanada zai tafi ya barsu Yau ta kama sunday jalal ya kalli mubarak "malam ya dace kayi aski fa" tsaki yayi Bros abdul muje dan Allah tunda ya fara zancen askin nan sai nayishi gara na tafi kafin ya batamin Dariya jalal yayi ya sanja kaya suka fito Duk yanda abdul AJ yaso su tafi a mota sam jalal yaqi haka suka taka da qafa suna tafia Tafe suke itada salma sai faman dariya salma take mata Tunda ya hangosu yanayinshi ya sanja tafia kawai yake Duk yanayin da yake ciki jalal yana kule dashi haka mubarak amma ba wanda ya nuna mishi Aski akeyiwa mubarak jalal yace acire gashin ga baki daya wani kallo yayiwa jalal "Allah baka isa ba" sai fa an cireshi duka Tsaki yayi yana kallon mai shagon "malam dan Allah cire duka sauri nake" dariya jalal yayi "kada ka cire duka yi mishi wanda ka saba yi mishi" kallonsu kawai cool AJ yake amma hankalinshi baya wurinsu har suka kammala suka nufi hostel Kwanciya yayi yana tunanin juwairiya shin dagaskene ya yanka mata hannu ko mafarkin hakan ne yayi? Wa zai amsamin? Tashi yayi ya dauki wayanshi ba tare da yayi musu magana ba ya fita ba wanda yayi mishi magana daga cikinsu Duk inda yake tunanin zai ganta ya diba ba alamanta har ya haqura ya nemo wuri ya zauna Tun kafin su qaraso ya ganeta yayi saurin tashi ya nufesu Sosai juwairiya taji zuciyanta ta buga dan tasan ba kirki ne da cool AJ ba Cak ta tsaya suka zubawa juna ido,,, cike da qarfin Hali ta fara yi mishi magana "malam lafia? Salma kam gaba tayi tana murmushi Tsaki taja tabi gefenshi zata wuce Cike da mamaki Salma take kallon ikon Allah ganin yanda cool AJ ya janyo juwairiya ya hanata da qirjinshi ahankali ya furta mata "am very sorry pls" Janye jikinta tayi da sauri tana hararanshi Da sauri ta nufi wurin salma Kallonta Salma take taja hannun Salma suka nufi hostel Kallonta salma take duk tayi wani iri "juwairiya kinga fa guy din nan ya cika da rainin hankali kamata yayi kasan abin yi tun da wuri" Kwanciya kawai tayi lokaci kadan tayi bacci har mamaki salma take Hostel ya nufa kallo daya jalal yayi mishi ya fahinci akwai abinda yake damunshi Sam AJ yace bazaici abinci ba wani kallo jalal yayi mishi Key dinshi kawai ya dauka ya nufi hanyar fita "abdul" jalal ya kirashi ya juyo yana kallonshi Something bothering you and your keeping it to yourself, right? Murmushi kawai yayi ya juya ya fice Kwanciya jalal yayi yaci gaba da aiki da system dinshi Kallonshi mami take tana nazarinshi "abdul meke damunka ne? Kamar zeyi kuka yake kallonta "mami kamar a mafalki na yake hannunta fa amma fushi nake dani kuma ni sonta nake" kai ta girgiza tana murmumshi Ya gaji da zaman da yake ya tashi ya fita sai faman fushi yake "Ya abdul fita zakayi? School zan tafi" jirani dan Allah zan bika Da sauri ta nufi part din ummi ta sanja kaya suka nufi school din "Bros jalal suna lecture fa" ba wurinshi zan tafi ba wurin sis juwairiya" da sauri ya juyo yana kallonta "jalillah kinsanta ne? Ya mubarak ne yake sonta " sosai yaji zuciyanshi ta buga wani tashin hankaline ya ziyarceshi............... [25/12, 14:04] Hassan Atk: 🤴🤴 JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 91-95 Kallon juna suke shida ita ganin tayi duk ya fita hayyacinshi har ya fara zufa "ya abdul lafia? Girgiza kanshi yayi "by 2 zan gama abinda nake sai ki fito" Sam AJ beyi attending lecture ko daya ba saboda baya cikin hayyacinshi Kasancewar mubarak yanajin yunwa ya sa jalal ya fito shi kadai yaje sayen kayan da suke buqata Kallonshi ya tsaya yi sam baya tare da natsuwa Kusa dashi yaje ya dafashi Kallon juna suke na tsawo lokaci kafin AJ ya sauke ajiyan zuciya "Meke damunka? Murmushi ya qaqalo wanda ya sanya jalal qara hade face dinshi "Gayamin meke damunka? Bros jalal abubuwa sunata zuwanmin kamar a mafalki ne kawai" tsaki yaja "Wai atunaninka bansan damuwarka bane? Juwairiya right? "No na haqura da wannan yarinyar kabar zancenta" meyasa? Amma kasan mubarak ne yake sonta ko? Dariya jalal yayi yana kallonshi "mubarak din ne ya gaya maka hakan? No jalilah ce tare ma mukazo da ita tana wurin juwairiya din" Sosai yake kallon jalal yana dariya "abdul meye abin dauka acikin zancen jalilah? Toh ba gaskiya bane dan baya soyayya idan kana sonta kaje ka gaya mata kawai "Bazata saurareni ba" why? Bayanin abinda ya faru yayiwa jalal Ka bata haquri kuma? Kai ya gyada mishi Tashi ka rakani Tafia suke jalal yanajanshi da fira ahankali yake amsa mishi jalal kam mamaki yake yanda soyayya take mayar da mutum haka Harara mubarak yayi musu "kawai daga zuwa sayen tulare sai kayi zamanka" meyasa bakaje nemana ba? Kai waramin yarone da zanje nemanka? Tsaki jalal yayi mubarak ya matsa kusa dashi "Bawan Allah ai yau zaka yi mana dan wake ko? Kakan wake zanyi" sai a lokacin AJ yayi dariya "sai fa kayi mana" Duk yanda yake cikin damuwa idan jalal da mubarak suka fara rikici dole ne yayi dariya "Bros jalal nifa zanci" sai ku girka,,, kwanciya AJ yayi tare fito da wayanshi ya bude email dinshi Zama jalal yayi ya janyo system dinshi ya shiga aikin gabanshi "Bros jalal wai bazaka yi mana ba? So kake yunwa ta illatamu ne? Tsaki yayi ya kashe system din ya dora ruwa suka shiga dariya Allah za kuyi girkin nan da kanku Ba wanda ya qara yin magana daga cikinsu sai faman dariya suke qasa qasa Zuba musu yayi a plate yaje yayi wanka ya dawo ya sami AJ sai faman sauri yake ya kammala "Ba kyau fa" jalilah jirana take kada tayi gaba" wallahi yafi komi sauki indai jalilah ce " Rakiya mubarak yayi mishi "kaga bari na koma banason fitina ka gaida su mami" Kallonsu yake har suka qarasa kusa dashi sai faman fira suke suna dariya "Ya abdul sis juwairiya tayimin dan wake" murmushi yayi "muje" Kallon juwairiya tayi "sai nazo muje wurin ummi ko? Kai ta gyada mata tana murmushi Ta shiga motan yaja jalilah na daga mata hannu *9:30pm* duk mubarak yayi bacci jalal ya shirya tsaf ya fita sai zuba qanshi yake ya nufi wurin da yasan zaiga juwairiya Cikin saa ya ganta ita kadai zaune tana rubutun project dinta yayi mata sallama ta amsa ya nemi wuri ya zauna Kallonta yayi tayi saurin sunkuyar da kanta "juwairiya right? Kai ta gyada mishi Murmushi yayi yana kallon system dinta "project kike typing? Zan turawa supervisor dina ne a email dinshi Karba yayi yana kallo tare da murmushi "Sorry zan iya yi miki correction? Kai ta gyada Janyo system din yayi ya shiga typing yana gyara mata cike da mamaki take kallonshi har ya kammala tanada yaqinin da itace ko rabi batayi ba Kallonta yayi cike da natsuwa "juwairiya nasan kinajin zafin abinda abdul yayi miki wanda nasan hakan ba dadi amma inaso ki fahinci abdul mutum ne mai kirki saidai matsalan rayuwa da ya samu nasan ke kanki kinsan ya sanja yanzu,, cike da natsuwa yayi mata bayanin abinda ya faru da cool AJ ba abinda ya boye mata ,,, "juwairiya abdul yana sonkine bawai da wasa pls ki bawa zuciyanki haquri for God sake" sam juwairiya batayi tunanin abinda jalal yazo mata dashi kenan ba Kallonta yake yana jiran yaji me zatace "pls say something" ahankali ta fara magana "kayi haquri ni inda wanda zan aura" kallon cikin idanunta yayi ta kawar da kanta "Qarya bata kamaceki ba idan bakyasonshi ki fadamin gskiya" Bazan iya aurenshi ba saboda bayada imani acikin zuciyanshi,,, "Juwairiya banajin na taba furta Kalmar da take qarya kodan ceto rayuwata bale nayi miki qarya ki yarda da abinda na gaya miki da zuciya daya" Kallonshi tayi. Tabbas bayada alaman qarya dan ko abdul tasan bata qarya koda zakasheshi ne "Zanyi shawara" murmushi yayi "jalilah tazo wurinki dazu ko? Kai ta gyada tana murmushi sai kuma tayi dariya "Lafia? Da gaske kai kakeyi mata kisto da kuma qunshi? Kai ya gyada mata tare da tashi "atashi lafia" ya juya kawai Tafia yake yana tunanin taya shi ze nemi mata gashi wannan duk ta sanyashi surutu akan simple issue Dan tsaki yayi duk yaji haushin juwairiya _After a week_ Jalilah sai murna take zata kawo juwairiya ummi ta ganta AJ ne ya daukosu juwairiya tana baya ya shigo ya nemi wuri yayi parking Gaisuwa ce barorin gidan suke ta zubawa ba wanda ya kalla bale ya amsa ya nufi part dinshi su kuma suka nufi part din ummi Cike da murna ummi ta tarbeta jalal yana zaune yana kallo murmushi sukayiwa juna suka gaisa Fira suke da ummi Sama Sama baffa ya shigo suka gaisa ya nufi dakinshi Ina zuwa juwairiya ummi ta fada Kusa da ita jalal ya matsa yana murmushi "zan iya introducing dinki wurin mami as her inlow? Sunkuyar da kanta qasa tayi tana murmushi Tashi muje,,, ba musu tabi bayanshi suka nufi part din mami Zaune take tana karatun Qur'an sukayi sallama ta amsa tana kallonsu ya nemi wuri ya zauna "Jalal lafia? Juwairiya ce na kawo ta gaidaki" dan tsaki tayi "ina ummin taka ne? Abdul ne ze aureta,,,, murmushi tayi "shine ka wani shigowa gaba? Murmushi yayi ya tashi ya fice Tashi mami tayi ta sanja wurin zama ta kira AJ tana son ganinshi Shigowa yayi yaje kusa da ita ya zauna ba tare da ya kula da juwairiya ba "Mami gani? Lafia? Mami ba komi ya yi magana cike da shagwaba "Hmm toh tashi daga kan jikina juwairiya zata yi maka dariya" mami dan Allah ki daina Naji tashi ka zauna Ba musu ya tashi aiko suka hada ido da juwairiya da sauri ya juyo yana kallon mami murmushi tayi "jala ne ya kawota" Kallonta yayi ta sunkuyar da kanta duk kunya ta kamata Kaga ni bani wuri mai martaba yana jiranmu zasu gaisa Hannun juwairiya mami ta riqe suka nui part din mai martaba Sosai mai martaba ya yaba da hankalinta ya sanya mata albarka Kyauta ta musamman mai martaba yayi mata sabuwar mota ce qirar vibe haka mami ta zuba mata gwala gwalai suka nufi part din ummi "Au ashe tana wurinki? Toh sirikatace fa" murmushi ummi tayi "yanzu jalal yake gayama baffan jalal toh Allah ya Sanya alkairi Jalal ne ya shiga "ummi zan koma school" toh kuma lafia kake wannan bata face din? Ummi ai naga biki soyawa mubarak naman bane Ni na gaya maka hakan? Ummi ai biki bani ba Murmushi kawai mami take ya karbi naman yayima ummi sallama ya fice.......... [25/12, 14:04] Hassan Atk: 🤴🤴 JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ Lace guda biyu da atamfofi ummi ta bata suka dawo part din mami Kallonta ummi tayi tana murmushi "juwairiya nifa ba sirikarki bace ki daina jin kunya na" murmushi tayi AJ ne ya shigo "mami zata koma school" tun yanzu? Eh zan tafi school din ne bros jalal nakeso ya tayani wani aiki kuma bazan dawo da wuri ba "Toh shikenan ai zaka kawota idan maryam tazo ko? Murmushi kawai yayi Barorin gidan mami tasa sukayi mata rakiya har mota Tada motan yayi yana sanye da farin yadi ya sanya driving lens dinshi sai faman zuba qamshi yake Gate din gidan aka bude mishi kafin yakai ga main gate din wayanshi yayi ringing yaga sunan ummi Hello jalilah ya akayi? Ya abdul adalci kenan? Nifa nazo da ita Sorry zan dawo muyi magana ya katse wayan Kallonta yayi ta sakar mishi harara ya kawar da kanshi yana murmushi yaja suka nufi school din A kusa da hostel din yayi parking ya juyo yana kallonta ta wani hade face "ya dai? Bansani ba kawai ka hana jalilah tamin rakiya kamar gunka naje" murmushi yayi "am sorry" kallonshi tayi daga still face dinshi dauke yake da murmushi tasa hannu zata bude motan ta fita yayi saurin dakatar da ita Kafeshi tayi idanunta farare tas dasu wani murmushi ya sakar mata "meye abin fushi kinfison jalilah akaina kenan? Harara tayi mishi "zaka hada kanka da jalilah ne? Kai ya girgiza yana murmushi tare da kawar da kanshi Kallonshi take a tunaninta baya ganinta ba tare da saninta ba ta saki wani sanyayyar murmushi kawai taga yayi dariya Juyowa yayi tayi saurin kawar da kanta "bafa hanaki kallona zanyi ba kici gaba kawai" hannu tasa ta rufe face dinta ya shiga yi mata dariya "Pls can I ask you? Kai ta gyada mishi "me bros jalal ya gaya miki har kika bawa zuciyanki haquri kika yafeni? Kallonshi tayi tana murmushi "komi be gayamin ba kawai nayi zuciyan muslunci ne na yafeka" girgiza kanshi yayi yana murmushi "kinga yanda qarya tayi miki kyau ko? Ga baki dayansu dariya sukayi "Hmmm bros jalal he is very kind and jovial" kai ya gyada mata yana murmushi Bari naje kasa salma tayi tunanin na bata "oh zaki tafi ki barni kenan? Bafa mami bace wannan Dariya yayi ya fita yaje ya bude mata ya fito mata da kayanda aka bata ta dauka yana kallonta har ta shiga hostel din murmushi yayi yaja ya nufi male hostel Kallonshi sukayi daka ganshi kasan yana cikin farin ciki "Bros jalal typing nakeso kamin dan Allah" Bacci nakeji "saifa kamin zakayi bacci" Tsaki yayi "sai kamin dole" "Bros jalal kaine babba dolene kayi haquri fa" sam be kula AJ ba ya shiga baccinshi sosai AJ yayi fushi yasan da mubarak ne jalal bazeyi bacci sai yayi mishi 2days su jalal basuga AJ ba kuma be kira ko daya a waya ba basusan cool AJ soyayya tayi dadi ya manta dasu fa amma kuma yana fushi jalal din Zaune suke shida juwairiya tana sanye da wani material ya qara fito da kyauta sosai sai faman zuba soyayya suke Jalal da mubarak ne suka shigo yana ganinsu ya wani bata rai Kusa dasu suka qarasa "bros jalal shuru haka ba labari? Murmushi kawai yayi Kallon AJ yayi ya zuba mishi harara aiko ba shiri yayi dariya ya matsa ta kusa dashi "meye na hararana? Kyaleshi yayi "bazakamin maagana ba? Eh "sai fa kayi" sai kamin dole Wai wannan fushin na menene bros? Ai nasan kanku a hade yake "Sweet muje" dariya jalal yayi "sorry idan inajin bacci bana iya typing ne shiyasa" Harara yayi mishi "sis juwairiya kawo na tayaki aikinki kisa bros abdul zae daina fushi damu" bataso" Dariya mubarak yayi "ka iya fitina wallahi" kallon mubarak jalal yayi wai mubarak yake cewa wani ya iya fitina? Hmmm lallai Malam daina kallona,,, dariya jalal da AJ sukayi ganin yanda ya hade face kamar dukan jalal zeyi idan be dena ba Juyawa jalal yayi AJ yayi saurin riqeshi "saifa ka tayani aikin nan ai ba fushi nayi ba" dariya jalal yayi ya karbi system din juwairiya ya qarasa typing dinda ta fara Saida ya kammala ya miqa mata suka nufi wurin da zasu zauna Cike da sallama tazo kusa dasu jalal sam jalal be daga kai ya kalleta ba "Jalala Ibrahim............ [25/12, 14:04] Hassan Atk: 🤴🤴JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ _Afuwa gareku masoyana na samun tsaiko da nayi ba tare da nayi posting ba kasan cewar wani sha'ani da na shiga sai kuma ban haquri a bisa kuskuren da nayi_. _Page 96-100 bayada page number sai a gafarceni_ 101-105 Ahankali ya dago yana kallonta ba tare da ya sake face dinshi ba, ga baki daya sai taji ta muzanta Mubarak ne yayi mata magana "boyar Allah lafia? Amm dama inaso muyi magana da jalal ne,,, toh ki fadi abinda yake tafe dake Kallon jalal din tayi wanda tuni ya daina kallonta "Jalal dan Allah idan bazaka damu ba zanso ka bani contact dinka idan na koma hostel zan kiraka sai muyi magana saboda naga kamar yanzu bakada time" "Malama dan Allah zo ki tafi bama son surutu" amma jalal nace bakai ba ko? Wani tsawa jalal ya daka mata wanda ya sanyata fita hayyacinta ta juya da sauri Murmushi mubarak yayi "hurt jalal me yasa kayi mata haka? Tsaki yayi ya tashi mubarak yabi bayanshi yana dariya Kallonsu kawai cool AJ yake yana dariya har suka fice Kallon juwairiya yayi face dinshi dauke da murmushi "bros jalal akwai zafi idan kikayi bincike mubarak ta taba duk shine ya janyo mata wannan" dariya juwairiya tayi Lafia? Kaine ka bani dariya Allah" toh me nayi? Kai kake cewa bros jalal yanada zafi? Murmushi kawai yayi dan bayason tuna baya "Hubbi na manta ban gaya maka ba gobe zan tafi katsina" wani kallo ya watsa mata Menene? Meyasa biki gayamin ba? Sorry mantawa nayi fa,,, kawar da kanshi daga kallonta yayi "fushi kakeyi dani? Mummy zanje in diba fa" juyowa yayi yana kallonta "me ya sami mummyn? Ahankali take mishi magana "kawai nayi missing dinta ne harda mafalkinta nayi shine nakeso nake naje na ganta" murmushi ya sakar mata "Idan mukayi aure kenan kikaji kinyi missing dinta banida kwanciyar hankali har sai munje katsina? Dariya tayi Nafa dade ban ganta ba,,, murmushi yayi suka shiga firan katsina Washe gari AJ ya shirya ya gayawa mami zai tafi katsina kuma ze dawo gobe tayi mishi fatan alkhairi Mamakin sammakonshi tayi cike da murmushi ta qaraso wurinshi "hubbi wannan sammakon fa? Hmm ai banaso ki tafi ki barni ne shiyasa Dariya tayi "hubby shine kayi wannan sammakon? Murmushi yayi Ga driver dinda zai tafi da motanki ni kuma zmuje a nawa ni da ke,,, murmushi kawai tayi mishi ta koma cikin hostel ta qarasa shiri suka dauki hanya "Pls hubby ka rage wannan gudun katsina za muje fa" murmushi yayi ba tare da yayi mata magana ba ahaka har suka qarasa ta shiga bashi direction na gidansu Sosai tsarin gidan ya burge AJ tun kafin su qarasa Mai gadi ne ya bude muau gate suka shiga ya nemi wuri yayi parking tare da sauke ajiyan zuciya Kallonshi tayi "hubby ka gaji ko? Kai ya girgiza mata yana murmushi bayan a agjiye yakejin kanshi dan be taba driving mai wahala ba irin wannan Cike da tsari irin na manyan mutane ta fito da alama fita zatayi "La hubby ga mummy ta fito" da sauri ta bude motan harda hadawa da gudu taje tayi hugging dinta "Juwairiya tafiya haka ba sanarwa? Mummy kawai nayi missing dinki ne fa shine nazo" Waye wancen? Oh na manta da baqo nake fa,,, harara tayi mata ta juya ta nufi ciki Da sauri aka bude mishi parlour'n da yake waje aka saukeshi mummy sai faman fada takewa juwairiya Mummy mantawa fa nayi,,, idan abbanki yazo sai ki gaya mishi mantawa kikayi Mummy dan Allah ki rufamin asiri kice kece kika manta bani ba Harara tayi mata aka hada abinci da snacks da juice aka kaiwa AJ Zaune suke bayan laasar juwairiya sai faman roqon mummy take akan tyi haquri amma taqi suka nufi parlour'n abban yana yiwa juwairiya kallon mamaki Juwairiya yaushe kika zo? Abba dan Allah kada kamin fada" murmushi yayi mummy ta tashi ta fita bata wani jimawa ba ta dawo tare da AJ cike da girmamawa ya gaida abban "Halima wannan waye? Tamabayi juwairiya kaji" turo baki tayi "mummy dan Allah fa nace" Au so kike nayi qarya? Baqon juwairiya ne kuma tare sukazo amma koni bata gayamin tare sukazo ba bale a tanadar mishi wani abu sai dan abinda muke da ya tarar" Kallonta abban yayi "meyasa kikayi haka? Abba mantawa fa nayi" kai ya gyda suka qara gaisawa da cool AJ "A garin nan kake? Kai ya girgiza ba tare da yayi magana ba Kallon mummy abba yayi da mamaki a face dinshi Daga wane gari kake? Ahankali ya furta zaria Okay toh sannu ko Allah yayi mana albarka Murmushi kawai yayiwa abban tare da sunkuyar da kanshi Kai asalin dan zaria ne? Sai a lokacin ya amsa da eh shima cen qasa yayi magana Ya sunan mahaifinka? Ahankali ya dago yana kallon juwairiya Kallonshi ya mayar gun abba "Alhaji Mahmud Yusuf" A wane wuri kuke zaune acikin zaria? Sunkuyar da kanshi yayi dan bazai iya fadan shi dan sarki bane Kallon juwairiya abba yayi da alaman tambaya "Abba dan sarki Mahmud ne shine ma da naje gaidashi ya bani wannan vibe din da kagani a parking space" Kallonshi abban yayi ya qara sunkuyar da kanshi Mummy kam aranta cewa tayi ba banza ba wannan rashin maganar Ahankali ya dago suna hada ido da abba ya sunkuyar da kanshi Ya sunanka? "Abdul jabbar" Murmushi abban yayi "masha Allah, Allah yayi muku albarka ya sanya alkhairi" mummy ce kawai ta amsa a bayyane Shuru ba wanda yake magana sai abba ne ya katse shurun "juwairiya sai ki rakashi ya samu ya huta ko? Tashi tayi mummy tayi mata harara "oh mummy me nayi kuma daga zuwana kuma fa saboda ke nazo" Da gudu ta shiga ta fada kan jikin mummy "Jawahir lafia? Mummy na gaji ne" murmushi tayi toh tashi ki gaida yayanki "La aunty juwairiya yaushe kika zo? Dan Allah ni bansani ba kawai daga zuwa kitso shine kikayi zamanki" Qawatace fa tazo mukaje tare kinga bazan tafi in barta ba Murmushi tayi mata sukayi hugging din juna Jawahir ga mijin juwairiya nan fa Juyowa tayi suka hada ido da AJ "Wow aunty juwairiya wallahi you are lucky, kin samo mai kyau saura ni na samo wanda ya fishi" Tashi abban yayi ya nufi dakinshi yana murmushi Alama juwairiya tayi mishi da su tafi Zaune suke a parlour'n da aka saukeshi sai faman kallon jawahir yake tana zuba................... [25/12, 14:04] Hassan Atk: 🤴🤴JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 106-110 Jawahir ki barshi ya huta mana,,, aunty juwairiya wulaqanci zakimin? No ba wulaqanci bane a gajiye yake kinga yana buqatan hutu" Okay naji amma zan tambayeshi kafin in tafi nima zanyi wani aiki ne,,, Murmushi yayi mata "pls kanada qanwa mace? Kai ya gyada mata Ya sunanata? "Jalilah" ya bata amsa a takaice "okay yaya fa? Kai ya girgiza mata Sorry lissafin ku nawane saboda anan gidan kaga ni da aunty juwairiya ne kawai Dan murmushi yayi "ni da jalilah ne kawai" dariya tayi kace kawai we are equal Tashi tayi "bros abdul zan baka saqo ka kaiwa jalilah dan nasan zamu zama qawaye idan kukayi aure amma yaushe zaka tafi? "Tomorrow" kai ta gyada ta fice Kallonshi ya mayar gun juwairiya "sweet meyasa kika korarmin qanwana? Habibi bakasan jawarib bane yanzu ba gajiya zatayi ba koda cewa akayi ta kwana anan tana maka questions bazata rasa abin cewa ba Murmushi yayi suka ajiye zancen jawahir suka nemo nasu daga inda suka tsaya ********************************** *8:30pm* jalal da mubarak ne a dakin ummi sai faman fada sukeyi ba wanda ummi ta kula daga cikinsu jalilah sai faman kallonsu take "Allah baka isa ka hanani rawan gaban hantsi ba anan zan kwana bazan koma school ba, kai kenan mutum ko yaushe sai yayita faman hawa kan raayinka toh yau ba inda zani" Kawar da kanshi yayi daga kallon mubarak din ya mayar gun ummi "ummi zan tafi" kai kawai ta gyada mishi ya tashi ba wanda ya kalli wani daga cikinsu "Ya mubarak kayi haquri kuje mana" harara yayi mata tayi dariya "ya jalal muje nayi maka rakiya yau fitina ya mubarak yakeji" tare suka fito shida jalilah wani sanyayar iska ne yake kadasu Cike da murmushi take kallonshi "ya jalal fushi kakeyi har yanzu? Ko kallonta beyi ba "ya jalal fa? Ta fada kamar zatayi kuka Juyowa yayi yana kallonta "wai ke bazaki daina wannan shagwabar ba ko? Toh meye abin kuka anan? Kawai saboda kinyi magana na kyaleki sai ya zama abin shagwaba? Aiko tasa mishi kuka Tsaye kawai yayi yana kallonta sai faman kukan shagwaba take mishi so kawai take ya lallabata shi kuma ya zuba mata ido Ganin ba gajiya zatayi ba ya sanya jalal fara magana badan yana raayin maganar ba "jalilah rakiyan nan yamin tsada dan Allah ki koma banason wannan kukan" Kusa dashi ta qara matsawa "kawai dan na tambayeka shine zaka shareni? "Sorry, ba fushi nakeyi ba kawai dai na fahinci lectures din gobene bayaso yayi attending" turo baki tayi "toh muje ni sanyinnan bayamin dadi Murmushi yayi sukaci gaba da tafia Kallonshi yayi ya kawar da kanshi da sauri Jalilah ce ta janyo hannunshi "ya jalal mai martaba muje mu gaidashi" taja hannunshi da sauri Ba yanda jalal ya iya suka qarasa gaban mai martaba Har qasa taje dole jalal yabi bayanta "sannu da zuwa abba" murmushi yayi "jalilah ina zuwa haka? "Ya jalal ne zai tafi shine zanyi mishi rakiya" kallonshi yayi ya sunkuyar da kanshi Murmushi yayi ya gyada mata kai suka tashi tana riqe da hannunshi sukaci gaba da tafia Kinga rakiyan ya wadatar ki koma,, ya jalal gobe zaka so? Jalilah sai na gama exam gaskiya" ido ta zare Ya jalal Allah yayi nisa, murmushi yayi "zanzo before exam din "yafi gaskiya" murmushi yayi ya zame hannunshi daga nata ya juya Hannu ta daga mishi yayi mata murmushi kawai *main gate* Jeep ce black tana dauke da tambarin masarautar Da sauri ya qaraso kusa dashi "Allah ya taimaki magajin sarki, umurni daga maimartaba zaa saukeka a makaranta" Kallon jeep din yayi wanda yasan sarkine kawai yake shiganta Ba musu ya shiga aka rufe direct sai school Kwance yake shi kadai ga baki daya duk rashin mubarak a dakin ya sanyashi jin wani iri Call ne ya shiga wayanshi yaga new number kuma number din ba wani wahalan dauka akai Cike da natsuwa ya daga tare da kwarara sallama Shuru yayi jin voice din mai martaba "JALAL" ya kira sunanshi cikin wani yanayi kamar na cikin damuwa "Naam" "Duk da ban taba daukanka a matsayin dan da na haifa ba na cancanci girmamawa a wurinka, jalal ban bayar dakai ba saboda bana sonka saidan kyauta da abinda kafiso, Kaine na farko da aka fara haifamin a lokacin da nake cikin tsananin neman ganin jinina wannan ne yasanya na badaka saida hakan ya sanya mana tsanata acikin zuciyarka wanda har ya shafi hafsa da ba hannunta aciki,, jalal zan baka zabi acikin tsarina babu cutarwa inaso ka zabi rayuwar da kafiso ni kuma zan baka wannan rayuwar koda hakan zai rabani da komi nawa harda rayuwata" Duk wannan jawabin na maimartaba ba abinda ya Sanya jalal face zubar da hawaye Cikin rawar murya ya fara magana "abba dan Allah ka yafeni wallahi ni sam ba wannan ne araina ba, abba kunya nakeji nayi muamala daku saboda ko kasan banason su baffa suji wani abu aransu wanda ni a wurina sam ba haka bane Abba na samu yata da tarbiya wanda nasan ba kowa zeyi dace da iyaye na gari irin nawa ba ban tabajin hakan araina a matsayin cutarwa ba sai bata da kayiwa rayuwata ka badani ga iyaye na gari,,, abba dan Allah kayafeni zan gyara kuskurena abba ka yafeni dan Allah" Sosai mai martaba yayi mamakin zancen jalal dan sam beyi tunanin hankalin jalal din yakai hakan ba sosai yayiwa Allah godiya ganin jalal sam bai kasan ce cikin masu butulci ba "Allah ya albarkaci rayuwarka abdul jalal" "Ameen" ya furta ahankali "abba ka yafeni din? Murmushi cike dajin dadi a ranshi "sam bakayi laifi ba jalal haka akeson da nahalat ya kasance " ajiyan zuciya ya sauke sukayi sallama ya ajiye wayan...... [25/12, 14:04] Hassan Atk: 🤴🤴JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 111-115 Shuru yayi na tsawon lokaci yana tunanin toh idan har abba yaji hakan aranshi mami fa? Ya zataji aranta? Shuru yayi yana tunani har yayi bacci Washe gari ya nufi lecture hall bashi ya fito ba sai 2 ya nufi hostel yayi wanka ya shirya ya nufi cikin gari Tsaye ya sami mubarak yana waya sam be kalleshi ba ya nufi part din mami Sallama yayi ta amsa tare da zuba mishi ido Kusa da ita yaje ya zauna ya sunkuyar da kanshi "Jalal lafia? Kallonta yake kamar zeyi kuka "Mami dan Allah ki yafeni nasan banyi dai dai ba dan Allah ki yafeni wallahi injin kunyar ummi taga nayi miki kallon mahaifi sai nake ganin kamar na saka da sharri akan alkhairi ne" Murmushi tayi aranta tace "tabbas jalal yafi abdul jabbar shagwaba" a zahiri kuma cewa tayi "jalal hakan da kayi shine dai dai ban dauki hakan a matsayin komi ba koda a hannunmu ka tashi ai bazaka wuce hakan ba dan ko yanzu ba abinda abdul jabbar zai nuna mana dan har ka fishi da ilmin addini" Sunkuyar da kanshi yayi tare da sauke ajiyan zuciya Shuru na tsawon lokaci ba wanda yayi magana daga cikinsu "Jalal kana buqatar wani abu ne? Kai ya girgiza mata "murmushi tayi "toh ai sai ka tashi kaje ko? "Mami korana kike yi? Kallonshi tayi sai kuma ya bata dariya "jalal ai yanzu ummin jalal zatazo nemanka gara kaje ko? Tashi yayi da alaman fushi Har ya kusa fita ta kirashi ya dawo "Jalal yanzu fa ka gayamin kanajin kunyar taga kayimin kallon mahaifiya shine dan nace ka tafi kake fushi? Mami ai naga bakya yiwa abdul haka Abdul din ai nawa ne kai kuma fa? Murmushi yayi ya tashi kawai ya fice Zaune ya sameshi a dakin ummi sai faman cin abinci yake yaje ya gaida ummi "Ummi baffa ya fita ne? Eh ya tafi kafancen "Ummi wurin me? Wurin aikin da yake gabanshi mana Kusa dashi mubarak yaje ya zauna Amma ai ka ganni ko? Ko kallonshi jalal beyi ba ya zauna ya fara cin abinci kawai har ya kammala baya magana da kowa "Ummi zan tafi school" "Mubarak tashi ku tafi" ba musu ya tashi suka fice amma jalal baya mishi magana koda ya mishi magana *Main gate* Kamar jiya suna qara sowa aka bude jalal ya shiga kawai haka mubarak ya shiga shima sai hostel aka saukesu Zaune suke ba yanda mubarak beyiwa jalal magana ba amma yaqi kulashi har mubarak din shima yayi fushi ya kyaleshi Har dare ba wanda yake yiwa dan uwanshi magana Girki jalal ya kammala yaje ya siyo coke yazo ya zuba a plate ya turawa mubarak aiko ya ture abincin har ya zube "Bazan ci dolene nima ka kyaleni" Ya tashi kawai ya fice sosai ya bawa jalal dariya Tashi yayi yabi bayanshi ya sameshi zaune sai faman fushi yake Dariya yakeso yayi amma ya jure "Meyasa zaka zubar da abincin idan bazakaci ba? Ko kallonshi mubarak beyi ba "tashi mu tafi" bazani ba Sai fa kaje "ai sai kamin dole" Janyo hannunshi jalal yayi da qarfi aiko yasa qara Kallonshi jalal yayi "wai kai meye haka? Ni da na kwana ni kadai banyi fushi sai kai dan kamin magana naqi kulaka? Harara yayi mishi "sai fa kaje kaci abincin nan" tsaki yayi ya nufi cikin block din nasu Sai faman cin magani yake jalal ya tasashi gaba da abinci "dolene sai naci abinci? Murmushi jalal yayi "idan bakaci ba meye amfanin wahalan da nasha kafin nayi girkin? Ko a naka tunanin saboda inajin yunwa ne nayi girkin? *kuyi haquri ban samu nayi typing da yawa ba* *written by mum haneef* [25/12, 14:04] Hassan Atk: 🤴🤴JININ SARAUTA 🤴🤴 *written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 116-120 Harara yayiwa jalal ya kawar da kanshi ya tashi ya zuba mishi wani abincin ya bashi Sam mubarak be wani cin abincin ba yace ya qoshi "wai mubarak me kakeyi haka ne? Wannan abincin ne bazaka iya cinyewa ba? Harara ya aikowa jalal Tashi jalal yayi da alama fushi yayi ya fice Tsawon lokaci mubarak bega jalal ya dawo ya kirashi a waya yayi rejecting Tashi yayi ya shiga nemanshi amma ba labarin jalal Wuri ya neman ya zauna yana tunanin ko jalal ya tafi gida ne Haka yayita faman nemanshi amma ba labari dole ya haqura ya koma ciki Kallon mamaki yayiwa jalal dake zaune yana karatu "Amma kaga calls dina ko? Banza yayi dashi yaje ya karbe handout din da yake hannun jalal "Allah sai ka gayamin ina kaje" Dan tsaki yayi ya kawar da kanshi "sai fa ka gayamin" "Mubarak wai meyasa kake jin dadin fitina ne? Toh gayamin ina kaje? Ba inda naje kawai naje waje dan banason fitina,,, meyasa baka daga wayana ba? Murmushi jalal yayi "mubarak dan Allah ka barni haka banason wannan surutun" Tsaki mubarak yayi ya janyo chinchin ya faraci Wai abincin kuma fa? Bazanci ba Jalala be qara magana ba ya karbi handout dinshi ya ci gaba da karatunshi "Jalal wai bros abdul bazai dawo bane? Eh ya bashi amsa Kaji dashi cen ya tashi yaje ya kwanta Jalal ya gama karatunshi yaje ya dauro alwala yayi addua ya kwanta Kai tashi kayi addua,,, jalal Allah nayi fa Dariya jalal yayi ya gyara kwanciyarshi Washe gari cool AJ yayi musu sammako saboda a wurinsu ma yayi break Kallon jalal yayi "Allah jiya akan hanya azumin magana nayi saboda na hadu da parrot a gidansu juwairiya" murmushi yayi "Wa yafi surutu itada mubarak" wani kallo mubarak ya aiko mishi wanda ya sanya su dariya "Bros jalal bani a zancen nan gaskiya" yayi kwanciyarshi Haka sukaci gaba da rayuwa har su cool AJ suka kammala suka bar jalal da mubarak ********************************** ********************** ? ************************** ********** Ai Hausa Novels **************** *************************? ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ? ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ? ************************** Mubarak ne yake driving jalal yana gefenshi yana aiki da system dinshi har suka qarasa cikin yayi parking Kallonshi yayi "jalal meye mafita kasan dai ni da kai ba wanda yake da wacce yakeso kuma kasan wannan kallon da baffa yake mana da alama shawara ne shida mai martaba da abba Sadiq" "Mubarak kaje ka nema kawai amma ni idan sun gaji su nemamin dan bazan iya neman aure ba gaskiya dan bansan me zan gayawa mace ba" Dariya mubarak yayi dan shi kawai be samu wacce yakeso bane shiyasa Cikin suka shiga kowa ya zube kayan hannunshi Mamin mubarak ce zaune tana zuba musu fada "jalal auren ne bakuso ko me? Mami bafa haka bane,, kai na tambaya? Allah ya baki haquri Murmushi jalal yayi Duk yanda jalal yaso mami ta fahinceshi abu ya faskara dole ya haqura yayi shuru sai faman masifa take mishi Haka suka tashi suka fice Result juwairiya tazo karba sosai AJ yake cikin farin ciki zaiga juwairiya Part din mami suka nufa shida juwairiya da jawahir sai faman surutu take zuba mishi yana murmushi Sosai mami tayi farin cikin ganinsu suka gaidata "Bros AJ qawata fa? Harara juwairiya tayi mata ta rama ta mayar da kallonta ga cool AJ Murmushi mami tayi ta nemi daya dagacin kuyanci ta tura ta kira mata jalilah Cikin fushi ta shigo "mami gani" nuna mata jawahir tayi Murmushi tayi "shine ba ko sanarwa? Dariya jawahir tayi Jalilah ta zauna kusa da ita Sai ga mubarak ya shigo yana dariya aiko jalilah ta hade face "mami kin ganshi ko? Allah zan hadaka da abba sadiq" Kusa da AJ ya zauna "bros shine yau naga kayi sammakon fita ashe yau ba wasa Murmushi kawai sukayi "Waike meye na hararana? Cool jalal ne ya bata miki kayan fa" Ai kai kace zaka biyani ko? Toh ai zan biya "pls ya mubarak dan Allah ka biyani" Dariya jawahir tayi "bros AJ wannan fa? Sosa kanshi yayi dan yasan shida jalilah kawai ya gaya mata "He is my friend" qarya ba kyau ya abdul jawahir muje wurin ummi Taja hannunta suka fice Cike da mamaki take kallonshi "sis wannan fa? Ya jalal ne mana twins brother din ya abdul" Sam jalal be daga kai ba bale ya kallesu suka shiga ciki "Sis amma kinsan be gayamin ba kawai yace ku biyu ne" hhhhhhhh bikinsansu bane ai ya mubarak ne kawai yake magana acikinsu kuma fa gara ya abdul da ya jalal Okay mubarak din shima yayanki ne? Dariya tayi kinga manta da ya abdul surutun ne bayaso shiyasa Haka sukaci gaba da fira na tsawon lokaci "Sis jawa muje mu zaga gari" Da sauri ta tashi jalilah ta sanja kaya suka fito Kusa da jalal taje ta zauna "ya jalal zamu fita" kai ya girgiza mata Kwantar da kanta tayi kan jikinshi "ya jalal Allah bazamu dade ba" I said no and I mean it,,, Kuka tasa mishi "ya jalal jawahir bazataji dadi ba fa" Ko kulata beyi ba aiko ta qara sa mishi kuka Kallonta yayi "ya jalal pls" Kai ya gyada mata tayi dariya tayi mishi peck ta tashi da sauri taja hannun jawahir Part din mami suka nufa ta zauna da mubarak "ya mubarak muje ka zaga gari damu" Bacci zanyi gaskiya, kukan shagwaba ta fara yimishi Tsaki yayi "bros sai mun dawo" ya tashi suka fice Sosai rayuwarsu take burge jawahir da sunada namiji a gidansu itama haka Zara riqa yi musu "Ya mubarak tsaya tsaya" kallonta yayi menene "ice cream zamu sha mana Wuri ya nema yayi parking suka nufi wurin Zama sukayi ya karbo musu yaje kusa da jalilah ya zauna Jefar da ice cream din tayi ta tashi da gudu taje ta tareshi ya fado jikinta suka fadi qasa Da sauri jalilah ta nufeta ta tadasu Sannu menene halam? Bata bata amsa ba kasancewar taji ciyo Zama sukayi sai a lokacin mubarak ya kalleta dan bega yanda face dinta ba tunda sukazo be kalleta ba Sis menene? Xikin yanayin jin zafi ta fara magna "Kinga yaron ya hau kan gini ne shine yake qoqarin sauka naga zai fadi shine naje na tareshi kasa yaji ciyo" Eyya sannu bari na karbo miki wani ice cream din ta tashi Kallonshi tayi ahankali ya furta "good Samaritan" yana murmushi Murmushin tayi tare da Ciro wayanta daga cikin jaka "Hello mummy ina wuni? Jawahir juwairiya fa? Mummy bana tare da ita mun fita ni da qawata" katse wayan mummy tayi Ice cream din ta bata ta karba taxi gaba dashi sai faman satar kallonta mubarak yake Ya mubarak muje gida jawahir fa da alama wurin yana mata zafi Tashi yayi suka nufi wurin da sukayi parking direct suka wuce gida Kallonta yake har suka shiga part din ummi Ahankali ya furta "my angel"............. [25/12, 14:04] Hassan Atk: 🤴🤴 JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 121-125 Murmushi yayi yabi bayansu dan ganin halin da suke ciki dan yau yayi gamo da angel Zaune ya samesu jalilah sai faman yi mata sannu take "Karbo mata pain reliever a wurin mami tasha" Da sauri jalilah ta tashi dama so yake ya koreta Kallon da yake mata ne ya sanyata jin kunya ta sunkuyar da kanta Gabanta yaje ya sunkuya yana kallonta Ahankali ta dago suna hada ido da sauri mubarak yace "I love you angel" Ido ta zare ya sauke mata lallausan murmushi tayi saurin sunkuyar da kanta Ga baki daya mubarak ta qara birkitashi "pls say you love me" Jalal da yake zaune ga baki daya mamaki ya cikashi ganin yanda ake fadan ina sonki kai tsaye Jin motsin jalilah ne ya sanyashi tashi yana murmushi ya juya Saida ya danji zuciyanshi ta buga dan be san jalal yana ciki ba a tunaninshi ya fita Harara ya aika mishi shi kam jalal badan jawahir ba da yayi dariya "Dama akan gulma zaka qare ya fice jalal yabi bayanshi Be kula jalal ba har suka qarasa part din mami Zama yayi kusa da mubarak yana dariya Kallonsu mami tayi "lafia? Mami wallahi jalal ya fiye gulma Murmushi tayi bata qara kulasu ba "Allah zamu bata idan baka daina ba" "Sorry angel" sai a lokacin mubarak yayi dariya "Cool jalal kai ka fiye gulma Allah kawai ka batamin tsari" Murmushi yayi yana kallonshi "muje school pls" Kaima kasan anan zan tare Ido jalal ya zare "saboda angel? Yes, any problem? Kai ya girgiza yana murmushi "ka gayama ummi na tafi sai Wednesday zan shigo" har Wednesday? Next week kenan fa? Eh akwai abinda yake gabana Toh nidai ka dora daga inda na tsaya Wai dan Allah research nawa nakeyi ne? 2 ya bashi amsa ba tare da ya kalleshi ba Kallon mami yayi ta aiko mishi da hararan wasa ya wani bata rai ya fice Zaune yake cikin hostel sai faman typing din research din mubarak yake Call din mami ne ya shigo wayanshi ya daga "Jalal bakaji na kiraka bane dazu? Aa Saboda kayi fushi shine na kiraka ka kyaleni? "Mami toh me nake miki ne dan Allah, bakya yiwa abdul hakan mubarak ma bakya yimishi hakan toh ni me nake miki kika tsaneni? Shuru tayi tana saurarenshi har ya gama qorafinshi "jalal wa yake da gatan da kake da acikinsu? Kai kadai kake da iyaye har uku Sam abdul bazaiyi bugun gaba da ummin jalal ba mamin mubarak ma kai kadai kake da gata a wurinta toh meye na fitina aciki? Shuru yayi "bazakayi magana ba? Toh mami ni me nake miki ne? "Baasan magajin sarki da shagwaba fa da jarumta aka sanshi" mami dan Allah ki daina Allah banason sunan Murmushi tayi "toh yaron ummi baya shagwaba da jarumta aka sanshi" Murmushi yayi suka dan taba fira daga bisani sukayi sallama Pic dinta ya bude a system din mubarak ya zubata manyan idanunshi akanta cike da nazari Murmushi yake lokacin da yake kallon pic din ummi "My mum My world My life My soul" ya furta yana murmushi Washe gari su juwairiya sunyi shirin tafia sosai suka sha tsaraba Kallon jawahir mubarak yayi duk ya wani kalan tausayi "my angel sai yaushe kenan? Kallon mamaki juwairiya da cool AJ sukayi mishi Murmushi tayi mishi "sai kazo gaida abbana" "Inzo gobe? Dariya "you are welcome" wani sanyi yaji aranshi ya juyo yana kallon su cool AJ "Malam lafia? Gulma kawai kun wani tsareni da ido ya juya tare da daga mata hannu "My angel naga abba Sadiq bari naje Neman izinin tafia kafin ya tafi" dariya tayi wacce ta qara fito da sak kamaninta da juwairiya "Jawa me kikeyi ne? Aunty juwai abinda kukeyi ne fa Dariya cool AJ yayi "Jawah Juwai" dariya sukayi ga baki dayansu "Habibi bari muje kada muyi rana a hanya" kai ya gyada mata "Am going to miss you habibi" murmushi yayi dan gani yake nata wasa ne Dariya jawahir tayi "bazaka iya magana ba kenan saboda naka yayi yawa" dariya sukayi juwairiya taja mota suka fice ************************************ Bayan dawowar mubarak daga katsina mai martaba ya tura akayi Neman izinin aurensu tare da sanya musu rana aurensu Zaune yake a gaban mai martaba da mamin mubarak alhaji Sadiq da kuma ummi da baffa Mami ce ta shigo ta nemi wuri ta zauna Baffa ne ya fara magna "abdul jalal meye matsalanka da ka gagara fitar da wacce zaka aura? Shuru yayi dan began wacce zai iya aura ba "Jalal baza kayi magana ba? "Ummi Allah ni bazan iya kallonsu ba bale nace ina son wata" Ga baki dayansu ba wanda jalal be bawa dariya ba "A haka zaka zauna kenan? "Dan Allah ummi ki fahinceni Allah ni bazan iya kallonsu ba" "Jalal tashi kaje" cewar baffa Sosai yaji sanyi aranshi ya fito yana murmushi ganin kallon da mami tayi mishi Duk wani shirin biki da akeyi an kammala sam mai martaba yace ba wani bidia da zaayi aka shirya akaje aka daura aure katsina ABDUL JABBAR MAHMUD & JUWAIRIYA HAMEED MUBARAK MUSTAPHA AZARE & JAWAHIR HAMEED Ana kammala wa suka dauko hanya sai sharra gudu suke Cike fadar mai martaba sarki Mahmud take abin baa magana Fatiha sukaji ana karantowa Sai faman tsokanar mubarak jalal yake da mijin angel "Alhamdulillah an daura auren ABDUL JALAL IBRAHIM da JALILAH IBRAHIM.......... [25/12, 14:04] Hassan Atk: 🤴🤴 JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 126-130 Kallon juna sukayi da mubarak zuciyanshi sai bugawa yakeyi, lokaci daya suka juya suka nufi wurin da su baffa suke Alhaji Sadiq ne ya tareshi "jalal zo ganinan" cikin rawar murya ya fara magana "Ab.. Abba daurin auren wa akayi? Alaman yayi shuru yayi mishi yaja hannunshi ya shiga dashi cikin gidan har zufa yake suka shiga parlour ya nemi wuri ya zaunar dashi "jirani anan" Ga baki daya jalal ya fita hayyacinshi sai zufa yake Da sallama mai martaba ya shigo shida baffa da alhaji Sadiq suka nemi wuri suka zauna Gyaran murya alhaji sadiq yayi "abdul jalal ni na daura aurenka da 'yar uwarka jalilah wanda na samu goyon baya daga wurin baffanka na biya sadaki kamar yanda addini ya tanadar ina fatan zaka riqeta amana" Daqyar jalal ya samu qarfin daga kanshi alaman eh,,, Tashi kaje Allah yayi maka albarka Tashi yayi ya fito ya rasa ina zaije kawai ya nufi part din mami Zaune take tare da hadimanta tana ganinshi tayi musu umurni dasu fita Sai a lokacin jalal ya samu damar yin kuka "Mami dan Allah ki tausayawa rayuwata ki fahintar dasu abba sadiq bazan iya rayuwar aure da jalilah ba" "Jalal kasan me kake fada ko? "Mami jalilah fa? Haba mami kada ki goyi bayan wannan auren dan Allah ki tausayawa rayuwata" "Jalal tun aranar da na fara ganinka kafin nasan cewa nice na haifeka nake alfahari da rayuwanka, tun daga lokacin da nasan kai dana ne nake qara yiwa Allah godiya, kasan cewarka dan halat yasa ko yaushe idan na tuna dakai nakajin wasu abubuwa da suka gabata sun wanke a zuciyana, Jalal anya kasan babbancin alkhairi da sharri ko? Shuru yayi yana mai jin zafi a zuciyanshi Jalal ya kake tunanin baffanka da ummin jalal za suji idan sukaga ka guji gudan jininsu? Jalal kayi tunanin rayuwarka ta baya da abinda kake shirin aikatawa yanzu,,, nikam sam banyi tunanin jalal zai guji hada zuria da jalilah ba" Mami dan Allah kada ki fassarani wallahi ba butulci nake shirin aikatawa ba kawai bansan ta yanda zan kalli jalilah a matsayin matana ba Murmushi tayi "jalal kana tunanin akwai wanda zai ci gaba da bawa jalilah tarbiya da kulawa sama dakai ne? Kaine komi na jalilah fa kuma ba ko wane namiji ne zai riqa yiwa jalilah wadan nan abubuwan ba Jalal kanaso jalilah tasha wahalan rayuwa ne? Kai ya girgiza Toh kaje ka ci gaba da riqonta bisa da amana nasan kaine mutum na farko da za muyi alfahari a aurar dashi a zuriar nan Kai ya gyada ya tashi ta kirashi ya dawo ya zauna "haka zakaje wurin ummin naka cike da damuwa? Murmushi yayi ya dauki ruwan da yake gabanta yasha badan yaji sanyi a zuciyanshi ba saidan bushewar da throat dinshi yayi Dakin ummi ya nufa tana zaune sai faman rarrashin jalilah take tana sauke ajiyan zuciya Ganin jalal ne ya sanyata tashi ta shige ciki Kallon ummi yayi tare da sakar mata murmushi ta mayar mishi "Uwace kawai zata iya fahintar halin da danta yake ciki" Kusa da ita yaje ya zauna "sannu da gida ummi" Ya fada voice dinshi a disashe "Jalal banso ganin ranar da zan ganka cikin damuwa ba amma sai gashi kana cikin damuwa banida abinda zanyi maka maganinta,, jalal kayi haquri da hukuncin iyayenka a wurinka ni......... Saurin dakatar da ita yayi "Ummi su waye iyayen nawa? Murmushi tayi "jalal bansan da wannan auren baffanka da alhaji sadiq suka qullah ba sai bayan an daura auren Ajiyan zuciya ya sauke "ummi sam bana tare da damuwa akan hukuncinsu akaina tausayin jalilah ne kawai a tare dani bansan wane irin hali zuciyanta take ciki ba" Murmushi tayi ya kwantar da kanshi a lap dinta shi kadai yasan yanda yakejin zuciyanshi Baffane ya shigo sosai yaji tausayin jalal din Ahankali jalal yayi mishi sannu da zuwa ya amsa mishi "Jalal mubarak yana waje yana nemanka kasan cewar be samu wayanka ba" Tashi yayi jiki a sanyaye "ummi sai na dawo" murmushi kawai tayi mishi Tsaye ya sami mubarak da cool AJ Murmushi ya sakar musu "angel ta qaraso ne? Murmushi kawai mubarak yayi yasan jalal yanaso ne kawai ya boye damuwanshi Kallonshi cool AJ yayi "bros muje ciki ko? Ba musu ya bisu suka shiga ciki Zaune suke a part din da juwairiya zata zauna an zagayeshi an gyarashi sosai Kallonshi suke ya nemi wuri ya zauna "abdul kaida juwairiya wa yafi wani son abunda yake purple? Murmushi kawai yayi dan yasan zancen da yakeso yayi ne jalal yakeso ya kawar "Bros jalal dan Allah ka qara bawa zuciyanka haquri ka zauna da jalilah a matsayin mata" murmushi yayi kawai danshi ko zancen bayaso Kallon mubarak yayi "zan fita akwai wanda nakeson gani sai na dawo sai muyi magana ko? Kai ya gyada mishi Ga baki dayansu tausayin jalal din sukeji School ya nufa yaci gaba da gudanar da shirye shiryen seminar presentation da yake gabanshi a wannan satin Ba irin nemanshi da baayi ba amma shuru ba labari Haka suka haqura sunsan duk inda yaje zai dawo Washe gari cool AJ da juwairiya sukaje gaida ummi bayan sun dawo daga wurin mami Kwance suka sameta ta rufe idanunta amma ba bacci take ba tanajin su ta tashi tare da sakar musu murmushi "morning my sis" murmushi tayi "ya abdul barka da safia" Komi nata a sanyaye yake "Jalilah kin tashi lafia? Kawar da kanta tayi tana murmushi "bari na kira ummi tana ciki Tausayinta yaji ya fito da wayanshi ya turawa jalal text ya maida Tsawon kwana hudu ba wanda yaga jalal haka ba wanda ya nemeshi mubarak ne kawai suke haduwa a school din Gobene ranar da jalal zeyi presentation ya shirya ya nufi gida Ahankali yayi sallama kamar mai rada Kallonta yake ta zabga tagumi tana tunani ga Baku daya sai yaga tayi rama Sallama ya qarayi sai a lokacin ta juyo Kallonshi tayi ta sunkuyar da kanta "ina wuni? Lafia qalau ya amsa tare da shigewa ciki "Ummi ina wuni? Murmushi tayi ta tashi "jalal duk karatu ne haka? Murmushi yayi ya zauna kusa da ita Ummi yunwa nakeji Jalilah ta kira "ummi gani" kawoma jalal abinci Ta juya ta fice Bayan ya kammala cin abinci ya kalli ummi "ummi gobe zanyi presentation dan Allah ki tayani da addua" Jalal Allah yasa ayi akan nasara Shuru ba wanda yake magana acikinsu "jalal kaje ka gaida mamin abdul tana fama da mura Tashi yayi ya nufi part din mami Harara ta aiko mishi tare da kawar da kanta........... [25/12, 14:04] Hassan Atk: 🤴🤴 JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* 136-140 Kallonta yayi na wani dan lokaci ya kawar da kanshi suna saurarenta har ta gama waya da amira ta ajiye wayan taci gaba da sha fruit dinta "Jalilah bikiga yayanki bane? "Ai na gaidashi" ta fada a takaice taci gaba da sha fruit dinta ba tare da ta kallesu ba Mamaki ne kome ya cika jalal ganin jalilah tayi qarya karo na farko kenan kuma ga wani basarwa da take Tana kammalawa ta tashi zata fita "ina zaki haka? Cewar ummi "Gum mami" ta fada ta fice kawai Murmushi ummi tayi tasan duk wannan jalal ake yiwa sai kuma abin ya bata dariya Kallon ta mami tayi cike da murmushi ga qanshin nan ga baki daya ya cika dakin mami "jalilah yau ba school ko? Murmushi tayi "eh shine nakeso anjima zan tafi wurin kunshi" au jalal din kuma fa? Turo baki tayi "ni banason nashi" murmushi mami tayi "toh ai sai kije ayi miki wanda kikeso" tayi dariya Fira suka dan taba ta koma wurin ummi ta sameshi shi kadai a parlour ta wuce ba tare da tayi mishi magana Sanye da wani lace ta fito pitch yayi kyau sosai da jikinta ta shiga wurin ummi ta gaya mata ta tafi wurin kunshi kai kawai ta gyada mata ta fito Ko kallon arziqi jalal be samu daga gareta ba ta fice yana jiyo fitanta da mota ya sauke ajiyan zuciya Gidansu amirah taje sukaje wurin mai kunshi sosai akayiwa jalilah kunshi aka gyara mata kanta ta fito fes da ita "Amirah Allah duk da ya jalal be kyauta ba abinda yayimin amma fa banason yaga nayi mishi rashin kunya kinga harda qarya nayi mishi a gabanshi kuma nasan yayi mamakin hakan kar ya shiga damuwa" Damuwar nakeso ya shiga ai Ido jalila ta zare "Allah ni banaso" idan be shiga damuwa ba ai bakikai mace ba kenan kinga zo ki tafi banason qorafi kuma kada ki daga mishi qafa ta juya kawai dariya jalilah tayi taja mota tayi gida Mubarak ne tsaye shida cool AJ da jalal taje nesa dasu tayi parking Qafarta daya ta fara fitarwa wacce tasha zane abu ga farar fata tayi kyau sosai Tsawon lokaci suna jiran ta fito ita kuma bada wani nufin ba kawai ta tsaya wayane da jawahir "Kinga yanzu nake dawowa kinaso ki kasheni da dariya zan bawa ya mubarak zam zam din ya kawo miki" ta kashe wayan ta janyo jakanta ta fito Kallon mamaki suke mata ta biyo kusa dasu batayiwa kowa magana ba saida ta wucesu kadan "ya mubakar akwai saqon sis a hannuna kazo ka karba" Duk yanda sukaso su boye mamakinsu ba wanda ya iya daga cikinsu sosai ta burge cool AJ yasan dole jalal yaji ta burgeshi Dariya mubarak yayi "bros bari naga mami sai inzo muje ga baki daya ko? Kai ya gyada yana murmushi Sauri sauri tayi wanka ta fito tayi kwalliya ta shirya ta zuba tularenta ta fito da ice cream daga cikin fride ta nufi part din mami Sanyayar qamshi ne ya ziyarcesu a lokacin da suke qoqarin ficewa lokaci daya suka juya Tafia take tanasha ice cream ko kallon batayi kamar batasan suna wurin ba ta wuce abinta Dariya mubarak yayi "bros wannan fa neman magana jalilah take" ka barshi kawai ai tamin dai dai Jalal ne ya fito cike da qasaita yana sanye da baqin wando da riga dark blue ya sanya glass dinshi sosai yayi kyau "Mami nason ganinka fa" kallonshi yayi da mamaki ya juya kawai ya nufi part din mami "Amma kasan qarya ba kyau ko? Banason yayi missing wannan wanka ne shiyasa na turashi Murmushi kawai AJ yayi Sallama yayi cike da girmamawa ta amsa mishi "mami gani" Kallonshi tayi "lafia? Mubarak ne yace kinason ganina" Kallonshi tayi cike da zargi sai kuma tayi murmushi "na bawa abdul saqon kaje kawai" Ko kallonshi jalilah batayi sai faman game takeyi.............. [25/12, 14:04] Hassan Atk: 🤴🤴 JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 131-135 Murmushi yayi ya nemi wuri ya zauna "mami ya mura? "Sai zakamin ya jiki? Murmushi yayi tare da kawar da kanshi "Mami kimin addua gobe zanyi seminar presentation" "Allah yasa ayi akan nasara" ameen ya amsa tare da tashi Wurin ummi ya koma suka dan taba fira na tsakanin uwa da da ya gaya mata zai koma school Tun daga wannan lokacin ba wanda yayiwa jalal zancen tarewar jalilah haka shima beyiwa kowa ba kuma ba wanda ya nuna mishi komi har suka kammala karatunsu shida mubarak Zaune yake jalilah tazo ta sameshi "ya jalal ina wuni? Kai ya gyada ba tare da ya kalleta ba "Ya jalal dan Allah so nake ka barni nayi karatu koda diploma ne" Kai ya gyada mata tayi mishi godiya ta fita tana murna direct taje ta shirya tazo ta sameshi "Ya jalal zanje gidan ya mubarak" kai ya gyada mata tayiwa ummi sallama ta fita Daya daga cikin motocin gidan aka dauketa da ita kasan cewar mubarak yana gidan da alhaji Sadiq ya bashi mijin mamin munarak kenan Cike da farin ciki suke zuba fira har mubarak ya shigo "Mrs jalal ce haka? Bata rai tayi "Allah ya mubarak zamu bata" dariya yayi ya zauna "cool jalal fa? Na barshi gida mana" dariya yayi "Ya mubarak ya jalal fa yace inje inyi karatu shine fa nazo wurinka dan ka samomin admission" Jalal din kuma fa? Toh meye babbancin ka da ya jalal din? "Aa kije ya nemo miki mana" sai fa ka nemomin" Dariya jawahir tayi "sis jalilah kin fiye rikici Allah" hhhhh wallahi ban kai ya mubarak ba" Dariya sukayi ga baki dayansu "Ya mubarak diploma zanyi yafi wannan zaman banzan da nakeyi" Ki kawo credentials dinki gobe sai ayi amfani da stamp din mai martaba mana Ai dasu nazo,, ya karba sai ki shirya dan next week nasan zaa fara lectures sai kije" "Ni kuma fa? "Angel sai kin haihu" dariya sukayi ga baki dayansu Sai kusan magrib jalilah ta koma gida *********************************** Cike da murna ta sami jalal da admission letter dinta ta nuna mishi be karba kawai ya gyada kai ta tashi ta fice Sam wannan auren be yiwa jalilah dadi ba dan gashi jalal din ya daina yi mata komi ko magana tayi mishi baya kulata Mubarak ne yaje ya biya kudin registration dinta yayi mata komi kuma yayiwa cool AJ magana da yayi haquri juwairiya ta riqa koyawa jalal driving yanda zaifi sauki gareta Haka akayi ko sam jalal be damu da kulawar da 'yan uwanshi ke bawa jalilah ba komi na buqata su suke mata kuma ba wanda ya nuna mishi komi Hangosu yayi ita da juwairiya zasu fita,,, kallon mamaki yake mata ganin yanda taja mota hankalinta kwance suka fita Tsawon kwanaki yana kule jalilah ita ke kai kanta school kuma besan waye ya bata motan ba dan sabuwa ce Cike da sallama ta shigo yana zaune yana cin abinci ta gaidashi sam be kalleta ba bale ya amsa Kusa dashi taje "ya jalal bakaji na gaidaka bane? Kai kawai ya gyada mata "Toh ae baka amsa ba" tsaki yaja ya tashi ta bishi da kallo cike da mamaki Tashi tayi ta nufi dakinta wunin ranan ga baki daya ranta baya mata dadi Zaune take cikin school ta shigo tayi parking inda ta saba yin parking din Sallama tayi jalilah ta amsa "ai nayi tunanin yau biki shigo ba" murmushi jalilah tayi kasan cewar ranta a bace yake batason yawan magana "Jalilah bakida lafia ne? Lafia qalau amira Sam bata qara tambayanta ba sukaci gaba da fira sosai amira take mamakin yanda jalilah yau bata yawan magana Haka suka nufi class din sukayi lectures suka fito Kallonshi take yana magana da wani sosai ya gansu itada amira yana gamawa yabi ta gabansu ya wuce ta bishi da kallon mamaki "Jalilah lafia? Kai ta girgiza ta shige mota kawai taja tayi gida Washe gari ba yanda jalilah bata yiwa amira magana ba amma ta kyaleta "Amiira wai fushin me kikeyi ne haka? Kallonta tayi "haba jalilah meyasa bazanyi fushi ba, kin manta farkon haduwar mu ne? Na dauki yarda da amana na baki duk wani matsala nawa saida na gaya miki amma ke sam ba haka bane a wurinki" "Amira ba haka bane wallahi kawai bansan me zan gaya miki bane" "Waye wannan? Murmushi tayi "mijina ne" ido amira ta zare "jalilah dama kina da aure? Haquri jalilah ta bata kafin ta fara bata labarin rayuwarta "Amira ba auren ne damuwana ba irin wulaqancin ya jalal, ko gaidashi nayi bata amsawa kuma ba haka ya sabamin ba "Hmmm jalilah kenan ai ke bakida matsala wallahi kinsan me nakeso dake? Kai ta girgiza "kada ki qara gaidashi duk wurin da yake kada ki qara kallon wurin duk da kasan cewar ba gida daban kuke ba dole ki kasan ce ko yaushe cikin yin kwalliya kuma zan hadaki da mai kunshi ko yaushe zaki riqayi kuma zaki sanja tulare ba wannan da yasanki dashi ba" Dariya jalilah tayi "wai saboda ya soni ko me? Harara amira tayi mata "kinsan dai wannan auren naku ba na rabuwa bane dole ku so juna wata rana gara kawai ki koya mishi sonki kafin ke ki fara sonshi" Murmushi kawai tayi amira tace ta tashi su tafi Kallon amira take sai faman kwasar kaya take ta bude jakanta ta biya kudi suka fito Saukeni a school sai na dauki Montana Zaune suke a motan jalilah amira nayi mata bayani "Kinga wannan tularen da wannan shi nakeso ki riqa hadawa kuma kada ki gayawa kowa wannan sirrin shiyasa ma zan zubeshi anan saboda 'yan leqon asiri ko ummi kada ki gayawa bale ta bawa sirikarta juwairiya sirrin" dariya sukayi ga baki dayansu Tsaye yake yana waya da mubarak tayi parking ko kallonshi batayi tabar kayanta cikin mota ta fice Sam be damu da rashin gaidashi da tayi ba Sai da tabbatar ya fita taje ta kashe kayanta daga cikin motan ta nufi dakinta ta bude ta shiga gwadawa tana murmushi Yau ta kama sunday su jalilah ba school tayi wanka ta matse cikin wasu riqa da wando da amira ta saya mata ta zuba tularen ta gyara gashinta tayi parking dinshi ya zubo a gefenta kai kace wata 'yar qasar hindu ce Voice dinshi taji yana magana da ummi ta daga waya ta kira amira Fira suke da amira ta fito Kallonta sukayi dan ita kanta ummi bata tabajin qanshin da yayi mata dadi irin wanan ba Fridge ta bude ta dauko fruit salad din da ta hada ta zauna tana facing dinsu tayi crossing legs nata ta fara shan fruit din tana mai ci gaba da waya da amirah........... [25/12, 14:04] Hassan Atk: 🤴🤴JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 146-150 Kallonta jalilah tayi "jalilah aurenki da ya jalal ba abune wanda zance zaa raba ba saidai idan dayane yabar duniya dan haka zan baki zabi biyu" Shuru jalilah tayi tana saurarenta "Na farko ko kici gaba da nemawa kanki 'yanci a wurin jalal din har ya nemi sulhu a tsakaninku ko kuma ki zubar da qimarki ta 'ya mace ki sallama kuma ki jure duk wani wulaqanci da zeyi miki" Shuru tayi "wane kika zaba daga cikinsu? Ajiyan zuciya ta sauke "amirah banaso na rasa qimata amma kinsan ko waye ya jalal a wurina wallahi bazan jure yana shiga damuwa ba zuciyana bazata iya haquri ba pls ki bani wani shawara kawai wanda ba rashin kunya aciki" Murmushi amirah tayi "karki damu ba rashin kunya bane zai fahinceki kinji? Kai ta gyada tare da share hawayenta suka sanja fira Tsawon kwana uku ba wanda ya qara ganin wani tsakaninsu Yau jalilah ta shirya zata tafi school tana tunanin da wane mota zata tafi? Sallama yayi taqi amsa mishi ta zubawa TV ido kamar da gaske kallon take Sallama amirah tayi cike da farin cike ta taryeta "jalilah mu tafi kada mu bata lokaci" Tashi tayi ta shiga ciki yabi bayanta "kiyi mata umurnin tafia saboda ba inda zakije" ya juya ya fice Tsaki tayi "Allah ni sai na tafi Mamaki ne ya cikashi ganin jalilah da amirah sun fice ya koma dakinshi yana tunanin mafita Tashi yayi ya nufi part din ummi ranshi bace ya nufi dakinta ya shiga hada kayanta ummi kam kallonshi kawai take Kuyangi ne suka shigo suka kwashe kayanta ga baki daya suka maida part dinshi ya dawo ya zauna kusa da ummi "Ummi jalilah zata koma part dinta yau" kallonshi tayi da alaman tambaya Cike da shagwaba ya fara yi mata magana "ummi kawai dan taga na kyaleta shine zata riqa gallafiri a gari da aurena" Jalal wani laifin ne tayi? Ummi ko yau fa saida nace bazata fitaba shine ta fice abinda kuma rashin kunya takemin dan kawai taga bana kulata" Murmushi ummi tayi "ka kira baffan jalal ka sanar dashi" kai ya gyada ya tashi ya fice ummi kam dariya tasa Hangosu yayi itada amirah sunyi parking sai faman dariya suke Sallama tayiwa amirah ta nufi part din ummi Mamakin yanda aka hargitsa mata daki take sai gashi ya shigo "ke zo nan" Ba musu tabi bayanshi suka nufi part dinshi Kulle parlour'n yayi ya juyo yana mata wani kallo daya razanata "Me kika maidani? Me kika maidani nace!!!!!!!!!! Tsorone ya kamata "y...... ya..... ya jalal me nayi? Belt ya cire ta zare idanu "ya jalal Allah lectures kawai mukayi ai ta amidani" Kusa da ita ya qaraso tayi sauri ta rufe idanunta "ya jalal am sorry Allah bazan qara yi maka rashin kunya ba" Kallonta yake na tsawon kafin ya fara mata magana "Bazaki qara fita daga part din nan idan kuma kina ganin kamar da wasa nake zan baki key sai ki fita" "Ya jalal dan Allah yaushe ka zama mugune? Wani kallo ya aiko mata tayi saurin kawar da kanta tana turo baki Ciki ya shige ya barta nan ta tashi tabi bayanshi direct toilet ya shige tayi wanka ta fito daure da towel Sam jalal be daga kai ya kalleta ba har ta kammala goge jikinta "ya jalal kayana fa? Kije dayan dakin zaki gansu" fita tayi ta shiga dakin da yake kusa da nashi Dakinshi ta koma ta zauna "ya jalal zanje wurin ummi yunwa nakeji" kamar beji me take cewa ba "ya jalal fa" "Kije kitchen kiyi girki" ido ta zare "ya jalal yunwa fa nakeji "kije kiyi girki" kuka tasa mishi "saboda nace kiyi girki shine kike kuka? Ya jalal yunwa fa nakeji" tsaki yayi ya tashi yaja hannunta suka nufi kitchen din Girki yake tana kuka har ya qarasa ya zuba mata a plate ta dauka ta fice Zaune ya sameta sai faman cin abincin take ya nufi dakinshi yayi wanka ya fito ya zauna parlour "Ya jalal inje wurin ummi? Ko kallon wurin da take beyi ba bale ya kulata "yajalal dan Allah wai me yasa kake son kyaluwa ne? Banza yayi da ita ta tashi taje kusa dashi "ya jalal Allah yanzu mugunta kawai kakeji dan Allah ni kabarni inje wurin ummi" kallonta yayi cike da nazari sai kuma taga yayi murmushi ya tashi ya koma dakinshi Da sauri jalilah tabi bayanshi Kwance ta sameshi tq zauna kusa dashi ta fara yi mishi kuka kallonta kawai yake "Ya jalal dan Allah kabarni naje" tsaki yayi "wai ke me kika maida kuka ne? Abu mai sauki ko? "Toh ni me nake maka ne? Auren nan nima ai dole akamun nima banason.... Saukan mari taji wanda ya sanyata fita daga hankalinta Wani zafi taji zuciyanshi nayi ya janyota zuwa jikinshi yana fitar da zazzafan numfashi Karo na farko da jalilah taga tsantsar bacin rai a tare da jalal "wallahi jalilah idan har kika ware furta mummunar kalma akan auren sai kinyi dana sani maras misaltuwa, an gaya miki aure yana cikin tsarina ne? Amma wannan auren shine abu mafi tasiri a rayuwata idan har kikayi qoqarin furta mummunar kalma akan abinda iyayena suka daukeshi a matsayin gata da nuna soyayya a gareni wallahi zaki raina kanki" Yana kaiwa nan ya tureta ya tashi ya fita Wayanshi ta dauka ta kira amirah sam amiran bata gane ba sai daga bata "Jalukah lafia kike kuka haka? Jalilah ta gaya mata yanda sukayi da jalal "Kwantar da hankalinki zanyi miki maganinshi" haka ta lallabata har ta daina kuka sukayi sallama Tun daga wannan lokacin jalilah ta shiga fushi da jalal gashi ya hanata fita ga school Bayan kwana uku jalilah na zaune akayi nocking taje ta bude ihu tayi ta janyota suka shiga ciki "Amirah kinga muguntar da ya jalal yakemin ko? 3days kenan banje ko wurin ummi ba fa? Kwantar da hankalinki wannan tularen da kike gani zai sanya yaji tausayinki ya riqa bari kina fita kinsan sunanshi? Kai ta girgiza "Kaji tausayina" dariya sukayi ga baki dayansu (Ni dai nace anya ba wayo amirah tayiwa jalilah ba) Jalilah zan tafi ya amir yana jirana "hmmm toh asha soyayya lafia" dariya tayi amira ta fice ta bata........... [25/12, 15:52] Hassan Atk: 🤴🤴 JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 141-145 Fitowa yayi ya samesu a tsaye "a tabbatar qayen nan sun samu ruwa acikin sati biyu" Harara mubarak yayi mishi "wata daya mai martaba yace" "haka na shirya nawa tsarin" Juyawa yayi ya koma part dinshi yayi kwanciyarshi Kallon raini abdul ya bishi dashi "bros ka manta da cool jalal akwai damuwa a tare dashi" Tsawon lokaci jalilah bataji bata gani sai faman shige da fice take wurin dauka shiri na fitar hankali har suka kammala ND 1 itada amirah sam amirah bata bata daman dainawa ba sai qara fitowa da salo kala kala Zaune take a part din juwairiya suna fira "jalilah sai yaushe zaki tare ne? Dariya tayi "sai yaushe zan kashe auren dai, ai bazan zauna da ya jalal ba" murmushi kawai juwairiya tayi dan tasan qaryane Cike da murna masarautar sarki Mahmud take saka makon haifa mata jika da akayi sai faman murna cool AJ yake ranar suna aka sanyawa yaro sunan kakanshi mahmud Bayan wata daya da haihuwar juwairiya jawahir ta samu yaronta namiji shima yaci sunan kakanshi mustapha Ranar sunan jawahir amirah tazo sukasha fira da jalilah sai da yamma jalilah tayi mata rakiya Zaune yake sai fama yake da ciyon kai har idanunshi sun kada sunyi sam jalilah bata kalleshi ba ya tashi ya nufi part dinshi Tsawon wuni ummi bata ganshi ta nufi part dinda yake Sosai ta shiga rudu ganin halinda yake ciki "jalal bakada lafia shine bazaka fada ba? Wannan wane irin abune? Tashi kaje jalilah tayi maka rakiya zuwa hospital Fita tayi sai ga Dr labaran yazo ya dibashi ya bashi magani tare da shawara 5days jalal yayi be fito ba harda mai martaba ya shiga ya dibashi baffa ko yaushe yana tare dashi jalilah kam kamar bata gidan itada mami Wanka yayi ya shirya dan yanaso ya fita ya gaji da kwanciyar sosai yaga yayi rama sai farin da ya qara gashi sajenshi ya qara fitowa ya kwanta luf Qanshin da yaji ne ya tabbatar da jalilah ce ke wurin haka itama qanshin da taji ya tabbatar mata jalal ne ya fito Kallonta ya tsaya cike da mamaki Sanye take da 3 quarter ta juya baya tana waya da amirah sai faman dariya take Juyowa tayi suna hada ido taja tsaki tayi ciki Mamaki ne ya cika jalal yau shi jalilah zata yiwa tsaki saboda tana ganin ta girma Part din ya nufa sam be sameta parlour ya nufi wurin ummi ya gaidata tayi mishi ya jiki ya amsa "Jalal kaje ka gaida mamin abdul" kai ya gyada ya tashi ya fice Sallama yayi ta juyo ba tare da ta amsa ba ta tsaya tana kallonshi ya nemi wuri ya zauna "sannu da gida mami" Zama tayi tare da gyada mishi kai "ya saukin jikin naka? Da sauki ya amsa mata Kallonshi tayi ga baki daya tausayinshi taji da alama ba ciyon kawai ke damunshi ba yana damuwa "Jalal ka kira mubarak ya kawomin mustapha in gani" murmushi yayi mata ya tashi kawai ya fice Zaune suke shida mubarak a part dinshi mubarak ya kalleshi da kyau "cool jalal meke damunka ne? Kallonshi yayi da alaman tambaya "wannan ba ciyo kadai bane kanada damuwa kuma kasan na fahinci hakan Murmushi yayi dan bazai iya boyewa mubarak damuwanshi ba Duk yanda naso jin me jalal yake gayawa mubarak abin ya faskara kasan cewar jalal ba wani daga voice dinshi yake ba mubarak kuma yaje ya zauna kusa dashi kamar masu rada Shuru mubarak yayi yana kallonshi "jalal meyasa ka aikata hakan? Rayuwa fa ba abin wasa bace, ka tashi mu nemi mafita kawai" Mubarak dan Allah kadan bani lokaci na qara samun sauki pls Mumushi yayi "bazan jure ganinka cikin damuwa ba kasani pls ka cire damuwa arnka" murmushi yayi tare da gyada mishi kai Sukaci gaba da fira Washe gari jalal da mubarak ne tsaye suna magana akan zuwansu juwairiya katsina cool AJ da yake zaune yana amfani da wayanshi yana murmushi ya tashi tsaye Nifa bazaka wahalmin da matana ba gaskiya wane irin aje yau a dawo gobe Ba wani kawai kace kanaso ta matsa ka huta Murmushi jalal yayi tare da kawar da kanshi Jalilah ce ta fito tana waya "ya amir pls am sorry on my way" ta fada a shagwabe Cike da zafi jalal y janyota ya wanketa da mari ya karbe wayan ya watsar da ita, tas kakjeji ya karbe key din hannunta yaje ya shiga motan yaja yayo kanta da sauri tayi bayan cool AJ yaje yayi wani parking da ko wanensu tunanin yake taya zai iya Santa mota a haka ba ya kashe motan ya fito ya nufi part dinshi kamar zai tashi sama Kuka tasa da gudu tabi bayanshi zuwa part dinshi Lokaci daya cool AJ da mubarak suka sa dariya Tsaye ta sameshi tayi kanshi kamar wacce zata dakeshi "Ya jalal me nayi maka zakamin haka? Kawai saboda mugunta saika fasamin waya" Cike da tsawa ya dakatar da ita "wa kuka maida saanki? Ni? Saboda kinga na kyaleki sai ki dauki aurena kina gallafiri dashi acikin gari? Tunda ya fara fadan take ja baya yana biyanta "Kina tunanin dan kin girma ne ko kuma kin taka wani matsayine da bazan iya hukuntaki ba? Janyota yayi da qarfi ya hadata da jikinshi "Har yanzu kinanan a matsayinki na jalilah Ibrahim kafancen, wallahi zan saita wannan mummunar aqidar da kika dauko acikin qanqanin lokaci, zakisan ni jalal Ibrahim ba saanki ba ne" Tureta yayi ya shige cikin dakinshi ya rufe Da kuka ta fito ta wuce ta wurinsu ta nufi wurin ummi Ke lafia Cikin kuka ta gaya mata yanda sukayi da jalal Tashi ummi tayi dan sosai abin ya bata dariya Bayan kwana biyu da fadansu amirah tazo gidan suka shiga daki jalilah ta gaya mata abinda ya faru Ihu tayi "muna kan hanya kenan" tsaki jalilah tayi bazaki gane zafin da yake cikin zuciyana bane wallahi ya jalal da gaske yamin wannan marin Dariya amirah tayi "kisa wannan tularen kije karbo key dinki kice zaki bawa amirah ne motan amiran ne yaqi tashi "Allah idan ya mareni zan sauke akanki" agreed Sukasa dariya jalilah ta tashi ta fice Shida mubarak ne a parlour ko sallama batayi ba shiga "ya jalal key dina zan bawa amirah motan ne" Dariya mubarak yayi ya tashi ya fice dan bayason ganin me zai faru "Ya jalal fa" tashi yayi bako tsoro a tare da ita tasha gabanshi "bakaji me nace bane? Kallon juna suke natsawon lokaci Kawar da kanta tayi ya saki wani lallausan murmushi Hannunta yaja ya zaunar da ita "meye dalilinki na rainani? Turo baki tayi ba tare da tayi magana ba "Meyasa kike wasa da haqqinda yake Kanki? "Amma dai bazakace bana sallah ba ko? "Ki daina tunanin zan kyaleki ki aikata ba dai dai ba bazan bada key ba tashi fice" Murguda mishi baki tayi ta tashi Mamaki ne ya cikashi ga wani sanyayan qanshi daya daki hancinshi Dariya suke itada amirah "Amirah ya jalal ne fa? Banida wanda ya fishi bana jure ganinshi cikin damuwa akan nayi mishi rashin kunya" murmushi amirah tayi Zan baki zabi jalilah sai ki zabi wanda kike ganin mafita a wurinki.............. [25/12, 15:52] Hassan Atk: 🤴🤴 JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 151-155 Sam jalilah ta manta da tularen da amirah ta bata har dare tayi girki sukaci itada jalal System dinshi ya bude yana wasu lamuran gabanshi "ya jalal inje wurin ummi? Kai ya girgiza alaman aa Tashi tayi ta nufi daki ta kwanta tana tunanin abin yi Tularen ta tuna tayi dariya ta tashi ta shafa tularen ta fito Da sauri jalal ya dago yana kallonta ta nufi fridge tasha ruwa taje kusa dashi "Ya jalal pls ka barni na tafi mana dan Allah" kallonta yayi tare da lumshe idanunshi "pls ya jalal" kai ya gyada mata tayi sauri tashi ta fice Sosai take dariya "Allah zaka riqa shan mamaki dan zance amira ta sayamin da yawa dan na riqa kamaka cikin sauki Tsawon lokaci jalal yana kwance daqyar ya qarasa dakinshi ya kwanta sam besam lokacin da jalilah ta dawo ba Washe gari jalilah taga shuru jalal be fito ba ta shiga dakinshi Kwance yake a dunqunqune taje kusa dashi "ya jalal lafia? Shuru ba magana Ahankali ta janye blanket din ta hau gadon Cike da wahala ya bude idanunshi "ya jalal meke damunka? Rufe idanunshi yayi "ya jalal bari na kira ummi" da sauri ya riqe hannunta ba tare da ya bude idanunshi ba "Ya jalal dan Allah meke damunka? Ga baki daya jalilah taga jalal ya qara rikice mata sai gumu yake kuma ya riqe hannunta sosai sai faman mayar da numfashi yake "Ya jalal dan Allah ka bari ko ya mubarak ne na sanar dashi" cike da wahala yake magana "Kada ki gayawa kowa pls" ya jalal zaka zauna da ciyo ne? Da qarfi ya fitar da wani numfashi cike da wahala saida hankalinta ya tashi "Ya jalal sannu" harda kwalla a idanunta Ahankali bacci yayi gaba dashi Kallonshi take ga baki daya ya bata tausayi Tsawon lokaci yana bacci kafin ya samu tashi Wanka yayi ya fito kamar wanda beyi ciyo ba yaje yayi break fast ya nemi wuri ya zauna cike da tunani Jalilah ce ta fito ta sameshi zaune taje kusa dashi "ya jalal ya saukin jikin? Kai ya gyada mata "Allah ya qara afuwa" Ga baki daya yanayin jalal ya sanja ya qara rashin magana Yau jalilah ta shirya zata tafi school ta shafa tularenta tayi dariya ta fito tana murmushi ta nufi dakinshi Zuba mata ido yayi taje kusa dashi ta zauna "ya jalal inaso in tafi school" Sam jalal yaji bazai barta ta fita ba "Kiyi haquri ba yau ba" turo baki tayi "ya jalal plssssss" Da qarfi ya janyota jikinshi yayi hugging dinta sai faman mayar da numfashi yake Jalilah kamar tsoro ya kamata duk tunaninta mugunta jalal yake mata kasan cewar matseta da yayi sosai Daqyar jalilah ta samu ta qwaci kanta tasa mishi kuka "ya jalal idan bazaka barni na tafi ba ai ba sai kamin mugunta ba" shuru yayi ba tareda ya daga kai ya kalleta ba Kusa dashi taje tana kukan shagwaba wanda jalal jinshi yake kamar tana Sara zugashi ne Ahankali ya dago yana kallonta "pls jalilah kefa qanwatace meyasa za kiyi haka? Kwantawa tayi kan jikinshi "ya jalal am sorry bazan qara yi maka rashin kunya ba" (Hhhhhhhhh oh my goodness) Hannunshi ya dora saman jikinta tare da jan numfashi "Ya jalal lafia? Idanunshi da suka kada sukayi ja ya bude suka zubawa juna ido Ahankali ya janye nashi idanunshi "Am very sorry jalilah" ya fada tare da juyar da ita ya dawo kanta Wasa wasa jalilah daga jalal sai faman kissing dinta yake bako sauki kamar zai cinyeta Duk ta cika da tsoro ganin yanda yake mata duk ya hargitsata Zip din riganta ya bude sai qoqarin tashi take amma ta gagara saboda qarfinda yake nuna mata ga baki daya jalal ya rabata da kayanta sai faman kuka take tana bashi haquri amma kamar turashi take ya aikata abinda yake niya ************************************ Sosai jalilah take kuka jalal kam ya shiga duniyar tunani abinda ya faru ahankali ya tashi ya nufi toilet yayi wanka ya fito ya sameta har tayi bacci ya shirya ya fice direct sai gidan mubarak Kallonshi yayi yata kamar ba dai dai jalal din yake ba ya jashi suka nufi gadding suka zauna "Meke damunka? Ajiyan zuciya ya sauke "mubarak bana cikin hankalina koda na aikata hakan kuma jalilah ce sila" Me ka aikata? Ya tambayeshi hankalinshi a tashe "Mubarak wani tulare ne jalilah take amfani dashi wanda yake sanyani cikin wani yanayi kuma ba ko yaushe take amfani dashi ba wannan tularen ya sanyani na kusanceta mubarak kasan bazan taba yiwa jalilah hakan ba" Murmushi mubarak tare da dafashi "jalal kaifa mijinta ne kuma ba haramci acikin abinda ka aikata ka kwantar da hankalinka pls ba komi bane jalilah ta ilmantu da ilmin addini tasan baka shiga haqqin addinka ba kuma sunnar annabi kayi kada ka sanya damuwa aranka kaje ka kula da ita kawai" Murmushi jalal yayi "jirani muje zan gaida ummi suka fice jalilah ce zaune bayan tayi wanka ta gasa jikinta sai faman fushi take Sam beyi tunanin ae sameta parlour ba gashi tare da mubarak suka shigo Kawar da kanta tayi "sis jalilah yau ba school ne? Kyaleshi tayi ya nemi wuri ya zauna haka jalal shima ya nemi wuri ya zauna "Ya jalal inaso inje wurin ummi" kai ya gyada ta tashi kai bazakace wani abu ya faru da ita ba Dariya mubarak yayi jalal ya bata ranshi "Allah zamu bata" kaga muje dan Allah Zaune suke itada ummi sam ummi bata fahinci komi ba su jalal suka shiga suka gaidata ta amsa "Ummi bani chinchin din saboda zan wucene idan na gaida mami" Rakiya jalal yayi mishi ya dawo ya nufi part dinshi ya kwanta kan 3 sitter tare da lumshe idanunshi "Ya jalal".................. [25/12, 15:52] Hassan Atk: 🤴🤴 JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 156-160 Ahankali ya bude idanunshi ya zubasu kanta sosai zuciyanshi take bugawa "kamin izini na tafi school za muyi test ne" kai ya gyada tare da rufe idanunshi Tsaf ta shirya ta nufi part din mami ta karbi key din wani mota ta fice tana sanye da abaya Zaune suke itada amirah suna fira "jalilah wai meke damunki ne? Shuru jalilah tayi "bazaki gayamin ba? Kallonta jalilah tayi cike da damuwa "amirah tularen da kika bani na menene? Dariya amirah tayi "meke faruwa ne? "Amirah meyasa kika yiwa ya jalal haka? Kinsan yanda yake jin zuciyanshi? Kin watsar da farin cikinshi ga baki daya amirah kinsa ya aikata abinda sam be taba tunanin aikawata ba,, amirah danasan abinda kika shirya kenan dana barki wallahi, a rayuwa ba abinda na tsana kamar ganin ya jalal cikin damuwa kin sanya damuwa acikin zuciyanshi kin bata farin cikinshi kin sanya damuwa acikin zuciyan ya jalal" Murmushi amirah tayi tare da dafa jalilah wacce idanunta suka ciko da kwalla "Jalilah sam banji zafin maganarki ba saidai inaso ki saurari abinda zan gaya miki Kece zaki sanya duk wadan nan acikin zuciyan ya jalal, iya sanina ku musulmaine kuma kunsan meye aure hakan sam ba sabawa Allah bane bale ya zame maku baqin ciki ko abin kunya Jalilah aurenku ba zancen rayuwa kuma bana tunanin ya jalal din zai qara aure kuma dole wata rana yaji yana shaawar kusantar mace saboda shima mutum ne kuma lafiyayye shin jalilah kinaso ya jalal ya fada cikin halaka ya shiga cikin fushin ubangiji kuma ya kwasowa kanshi cutar zamani? Jalilah ina sonki banason abinda zai shige miki duhu shiyasa na baki wannan tularen dan ki riqa amfani dashi wurin ceto ya jalal daga halaka Inada yaqinin duk ranar da ya jalal ya shiga cikin wata matsala kece ta farko da zata fara shafa Jalilah duk imaninka wata rana sai shaidan yayi qoqarin ganin ka sabawa ubangijinka bakya tunanin wata rana shaidan zai qawata ya jalal surar wata 'ya mace har ya aikata ba daidai ba? Jalilah hakan ya faru da aunty na har yayi dalilin da yasa suka rasa rayukansu Jalilah ina tsoron hakan ta faru dake shiyasa nayi hakan badan na sanya baqin ciki acikin zuciyan yayanki ba saidan qoqarin ganin rayuwarshi ta zama ingantacciya kun kasance cikin farin ciki har qarshen rayuwarku Jalilah ki yafeni banyi dan cutar daku ba saidan son ganinku cikin farin ciki" Tana kawai nan ta tashi da sauri jalilah ta janyota ta zauna "Amirah dan Allah kiyi haquri sam banyi tunanin akwai masu sona haka ba nagode sosai" Murmushi tayi mata "jalilah ki rungumi mijinki kada wata tayi miki illa ga rayuwa ki kyautata mishi ki mayar dashi naki nasan zaki iya jalilah saboda kinada abinda ko wane namiji yakeso ki dage wurin ganin kin koyar dashi sonki kin zama wacce yakejin in ba ita ba zai iya rayuwa ba" murmushi jalilah tayi tare da gyada mata kai "Promise? Kai ta gyada sukayi dariya ga baki dayansu Anan jalilah ta sameshi kwance inda ta barshi murmushi kawai tayi da ta tuna wani zancen na amirah Kusa dashi taje "ya jalal" ta kirashi cikin wani yanayi Ahankali ya bude idanunshi da suka sanja sukayi ja sosai Ido ta zare tare zubewa kusa dashi "ya jalal meke damunka? Ahankali ya rufe idanunshi Hannu takai ta tabashi da sauri ya bude idanunshi kasan cewar wani shock da yaji "ya jalal dan Allah meke damunka? Kai ya girgiza mata alaman ba komi "ya jalal kada kace haka dan Allah ka gayamin" rufe idanunshi yayi aiko ta sanya mishi kuka Ga baki daya jalal jin kukan yake har cikin zuciyanshi gashi sai qara kukan take Ahankali ya tashi "ya jalal bazaka gayamin ba? "Ba komi" ya furta kamar bayason magana tashi tayi ta nufi dakinta tana qara kuka Tashi yayi yabi bayanta Kwance ya sameta tana kuka ya zauna kusa da ita "jalilah" Juyowa tayi tana mai qara kuka "ni ka kyaleni in bazaka gayamin ba" "Jalilah kukan ya isa tashi kiji" Tashi tayi ta zana kusa dashi ba tare da ta daina kuka ba "Gayamin inji" kawar da kanshi yayi daga kallonta Cike da mamaki jalal yake kallon jalilah kan jikinshi sai faman kukan take "jalilah kukan ya isa haka" Toh gayamin inji Hugging dinta yayi tare da rufe idanunshi "jalilah bansan meyasa nayi miki hakan ba am sorry am very sorry" Ajiyan zuciya tayi ta fara yi mishi magana ahankali "Ya jalal banji zafin hakan ba kai mijinane kuma bana sabawa Allah ba ka daina tunanin ka aikata ba dai dai ba ka cire damuwa aranka banson ganinka cikin damuwa ya jalal" Sanyayyan ajiyan zuciya jalal yayi Shuru na dan lokaci suna hakan kowa da abinda yake tunani acikin zuciyanshi Ahankali ta zame jikinta daga nashi ta dago tana kallonshi "ya jalal muje kaci abinci da alama ko break fast bakayi ba" Murmushi yayi suka nufi parlour Zaune suke kan dinning yanacin abinci kamar ba jalal ba ga baki daya shi kunyar jalilah ma yake ni Har ya kammala suka koma parlour suka zauna suna fira Jalilah ta fahinci jalal kamar kunyar ta yake sai abin ya bata dariya Haka suka wuni suna fira sallah kawai ke tadasu *10:30pm* jalal yana zaune shi kadai a parlour mubarak ya kirashi "cool jalal bros AJ fa ba lafia" meke damunshi? Nima bansani ba kawai ya kirani ne yana gayamin kuma da alama hakane saboda voice dinshi ma sanja sosai Okay bari in dibashi ya tashi ya fice Nocking yayi juwairiya ta bude suka gaisa "cool AJ fa" Bro jalal kaga yaqi shan magani yaqi bari a kira Dr labaran" Murmushi yayi muje Kwance yake da alama sanyi yakeji "Cool meke damunka? Murmushi yayi "headache ne wallahi" harara yayi mishi "kai yaushe zaka zama namiji wai? Murmushi yayi Hannu ya dora saman kanshi ya fara karanto addua Kallin juwairiya yayi ki bashi ruwa yasha kawai rakine dashi Doka cool AJ yakai mishi ya goce "saboda ka samu sauki ko? Tashi yayi da sauri jalal ya juya suka shiga dariya "Malam tsaya ba komi zanyi maka ba" juyowa yayi yana hararanshi "wannan hannun daga ne wanda yayi aiki a gona banajin kana iya dauka dukanshi" Dariya sukayi ya juya tare da yi musu saida safe Kallonshi juwairiya tayi "da gaske wai bakajin komi yanzu? Hugging dinta yyi yana murmushi "sweet ba abinda nakeji yanzu sai ke" Dariya tayi suka nufi dakinshi Sam jalal beyi tunanin jalilah zata nemeshi ba Da sauri ta qaraso wurinshi "ya jalal ina kaje? Murmushi yayi "ba inda naje" Harara tayi mishi "shine naje har wurin ummi ban ganka ba" Ido ya zare " cool AJ ne fa ba lafia naje ganinshi" ajiyan zuciya ta sauke Dariya yayi "meye na dariya kuma? Ba komi kinyi tunanin na bata ne? Murmushi tayi "nayi tunanin kaje wurin waya ne" Ga baki daya mamaki ya cika jalal amma sai ya boye yayi murmushi kawai "Eh toh ai cool AJ ma na mace ne" dariya tayi Ai ba shine ya mubarak ba Dariya yayi shima tare da girgiza kai ya dauki wayanshi ya nufi dakinshi tabi bayanshi Wanka yayi ya fito ya shirya ya kwanta taje kusa dashi ta zauna "Ya jalal dan Allah ka bani waya na riqa community da amirah" Murmushi yayi aranshi yace "zaki qara jefani ruwa kenan" Ya jalal ruwan me? Ido ya zare dan beyi tunanin ya fada taji ba Ya jalal ruwan me? Aa ba komi "Allah sai ka gayamin" Tayo kanshi da sauri ya tashi aiko jalilah tabishi sai faman zaga dakin suke ta gaji tasa mishi kuka da sauri ya qaraso wurinta "Bafa komi nake nufi ba" Allah ni sai ka gayamin Janyota yayi jikinshi ya rada mata akunne "kinaso na qara baki wahala ne kamar yanda kukasha da safe?............ [25/12, 15:52] Hassan Atk: 🤴🤴 JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 166-170 Sauri sauri gudu gudu haka jalal yayi ya qarasa dan yasan qaramin aikin jalilah ne ta sanyashi jin kunya a gaban mutane Tsaye ta sameshi cikin parlour yana jiran qarasowarta kuka tasa mishi yayi saurin kama kunnenshi aiko jalilah ta shiga dariya "Ya jalal kasan bazaka goyeni meyasa kamin haka? Zama yayi taje ta zauna kusa dashi "bikiga su baffa bane? Toh ni meye damuwana ai sunsan fiye da goyo ma zaka iya yimin Murmushi yayi "meyasa kika dade? "Lectures" ta bashi amsa tana qoqarin kwantawa a jikinshi "Kayi tunanin na bata ne? Kai ya girgiza "toh me kayi tunani? Kawai naga har kusan 4 sai naga diploma din yamin tsada Dariya tayi "ya jalal Allah ya mubarak ya koyar dakai yawan magana" murmushi yayi "Ki daina zargin mubarak fa" shima yasan da hakan ai "Hmm muje kiyi wanka ki rage gajiya " zaka tayani? Dariya yayi yana girgiza kanshi "Toh bazani ba" sai fa kinje" ayimin dole" Cak jalal ya dagata ya nufi dakinshi da ita be tsaya da ita ko ina ba sai kan gadonshi "Ya jalal Allah zan iya basai anyimin dole ba" dariya ta bashi Rake mata kayan jikinta ya fara tana qoqarin tureshi "ya jalal meye haka dan Allah nace zan iya fa" Sam be kulata ba saida ya rabata da kayan jikinta ga baki daya ta wani bata rai Ahankali ya fara shafa jikinta yana kissing dinta Duk da gajiyan da ke tare da jalilah be hanata biyewa jalal ba suka shiga romancing din juna Tsawon lokaci jalilah na jiran jalal ya kyaleta shiru ba labari nipple dinta har yayi ja ga zafin da yake mata Shi kanshi jalal din a gajiye yake amma ya kasa samun natsuwa yabar jikin jalilah Ahankali ya zame boobs dinta cikin bakinshi tare da dora mata nauyinshi ga baki daya yana mayar da numfashi sam beji ya samu natsuwa ba amma yasan zai takura jalilah ne kawai gajiyan zata yi mata yawa Ya jalal dan Allah dagani haka mana so kake wai ka qarasani ne ga baki daya? Dariya ta bashi ya dago yana kallonta da idanunshi da sukayi kamar mejin bacci "Me kuma nayi? Ni dagani haka dan Allah naje nayi wanka" Zan tayaki "banaso" dariya yayi ya tashi daga kan jikinta da sauri ta janyoshi ya dawo "Menene? Kayana fa? Akwai wanda ze ganki ne? Harara tayi mishi tasa hannu ta janyo dan kwalinta ta tureshi Kasan cewar dan kwalin babbane haka ta daurashi ta nufi toilet Murmushi jalal yayi yabi bayanta "Ya jalal amma na gaya maka banaso ko? "Ni inaso" Janyo towel tayi ta daura "sai kazo kayi" Ta nufi qofar yayi sauri ya janyota "Ya jalal wai meyasa kakeyin haka ne? "Sorry" ya fada tare da kwance towel din Mamakin jalal jalilah take ta gagara gane wane irin mutum ne har a toilet din bazai barta ba Sai faman kissing dinta yake yana wasa da boobs dinta ga baki dayansu ko wane yanada buqatar wani Daqyar jalal ya qarasa da jalilah kan gadonshi sukaci gaba da kissing din juna Hannunshi ya dora saman company dinta da yake cike taf sai faman nishi take yana wasa da boobs dinta da dayan hannunshi Duk da zafin da takeji be hanata jin dadin yanda jalal yake shiganta ba ga baki daya sun fita hayyacinsu Jalal na hango kwance yana mayar da numfashi jalilah kai kace ba rai a tare da ita Daqyar jalal ya nufi toilet yayi wanka ya fito ya taimakawa jalilah suka nufi toilet din sam bata hanashi ba dan batada qarfin yiwa kanta wannan hidimar Bayan sallar magrib jalal ya shigo ya sameta kwance kan supper kamar me bacci Kusa da ita ya kwanta tana jinshi ta kyaleshi Har tausayi ta bashi ya tashi ya nufi kitchen be jimaba ya dawo ya ajiye plate dinda yake hannunshi ya tadata "Pls ya jalal bacci nakeji Allah" Sorry kici abinci sai kiyi sallah zakifi jin dadin baccin Kallon abincin tayi sosai kam tanajin yunwa amma bacci yayi mata yawa haka ta haqura ta fara cin abincin sosai kuma tafi ya kwashe kayan ya mayar Sallah ya sameta ta fara ya juya ya nufi masjid dan gabatar sallah Jalilah ko addua batayi ba ta haye gado ta fara bacci Mamaki ne ya cika jalal ganin da gaske baccin jalilah take ya juya kawai ya fice dan yanason ganin mubarak Karao sukayi da mami a parking space "sannu mami" murmushi tayi mishi "Ina zaka? Mami zanga mubarak ne" murmushi tayi karbi wannan mijin da yayi min rakiya yayi bacci Murmushi yayi ganin junior yana bacci a mota ya dakeshi ya nufi part din AJ dashi Juwairiya ya Sama a parlour ya bata ta karba ya juya ya nufi gidan mubarak............ [25/12, 15:52] Hassan Atk: 🤴🤴 JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 161-165 Tureshi tayi tana murmushi ta juya zata fice ya janyo hannunta "tambaya fa nayi? "Oh ya jalal yaushe ka zama haka? Murmushi yayi ya saketa ya nufi gadonshi ya kwanta "Good night" ta fada taji shuru be karba mata ba "ya jalal fa" still be juyo ba bale ya karba mata Gadon tahau da sauri ya janyota yasa hannu kawai ya kashe light din dakin tare da janyo blanket ya rufesu "Ya jalal meye haka dan Allah" addua taji yana karantowa ahankali "Ya jalal wai me kakeyi hakane dan Allah ka barni na tafi mana" sam jalal be kulata ba ba irin maganar da jalilah bata yi mishi ba amma ya kyaleta kamar baya cikin dakin Qoqarin tashi take amma ga baki daya jalal ya hanata dogon motsi ta gaji dan kanta ta nemi sulhu "Ya jalal toh dan Allah taya zanyi bacci a haka ga baki daya zance akan jikina kake taya zanyi bacci a haka" Sam ba wanda yake ganin face din wani daga cikinsu amma sosai jalilah ta bashi dariya dan har ya hango yanda face dinta yake a lokacin da take wannan maganar "Ya jalal toh yi haquri kadan ragemin wannan nauyin naka Allah daqyar nake numfashi" Ahankali ya matsa daga kan jikinta amma be sauka ga baki daya ba "Ya jalal dama kana jina ka kyaleni? Sam yaqi amsa mata haka ta haqura ta fara bacci Saida ya tabbatar tayi nisa da baccin ya tashi ya rage kayan jikinshi ya kwanta kusa da ita Tunani kala2 suke shigo jalal wani abin har mamaki yake bashi musamman da ya juya ya kalli face din jalilah Haka yayi ta fama har yayi bacci Da asuba ya riga jalilah tashi yaje yayi alwala yazo ya tadata "jalilah" ya kirata sunanta "Jalilah ki tashi kiyi alwala lokacin sallah ya kusa fa" tashi tayi ta nufi toilet ya bita da kallo kawai Masjid ya wuce sukayi sallah Bayan sun kammala mai martaba ya kirashi suka nufi part din mai martaba "Abdul jalal" naam abba barka da asuba" barka ka tashi lafia? Lafia qalau "Toh ya iyalinka? Sunkuyar da kanshi yayi cike da jin kunya Murmushi mai martaba yayi "abdul jalal meye matakin karatunka na addini? Kallonshi yayi cike da tambaya Inaso inji littafan da ka karanta ne da kuma abinda kake iya magancewa ta hanyar addini "Abbana na karanta littafai da yawa a wurin fa kafin na qare secondary school na kammala karatun fiqqihul muyassir na kuma kammala zadul ma'ad" Nakan fitar da jinni nakan qonashi Zan iya hada maganin cutuka kamar haka Heart disease, ulcer, hypertension, diabetes kidney disease harma da abinda ya shafi wasu abubuwan da suke cikin cikin dan adam Na kan hada wasu da itatuwa wasu kuma zuma da ayoyin al Qur'ani Murmushi mai martaba yayi "Allah ya sanya maka albarka acikin al'amarinka" Ameen abba Tashi kaje Ba musu ya tashi ya nufi part din ummi suka gaisa "Ummi baffa be shigo bane? Baffa ya fara bacci yace bazai fita da wuri ba Murmushi yayi suka shiga fira tsakanin uwa da da *7:3am* jalal yabar ummi dan ta samu hutu ya nufi part dinshi Jalilah kam har ta kammala hada break fast saboda tanaso taje school ta shige dakinta dan tayi wanka ta shirya Dakinshi ya nufa yayi wanka Zaune ta sameshi ta shirya tsaf da alaman fita zatayi "Ya jalal zan tafi school" Kallonta yayi tun daga sama har qasa ya kawar da kanshi "Ya jalal amma dai ba hanani zuwa zakayi ba ko? Murmushi yayi tare da girgiza mata kai "Zo kiji" ba musu taje kusa dashi ta zauna Gyalen jikinta ya fara cirewa ya zame dan kwalinta "Ya jalal lecture nake da yanzu fa" "I know" then why are you removed m.... Toh my menene take nufi Bakin jalal na hango cikin na jalilah sai faman kissing dinta yake hungrily Daqyar ya kyaleta tare da sanya hannu ya kwantar da ita ya zuba mata 👀 shi yana murmushi Kwantawa yayi kan jikinta ya shiga shafa ko ina na jikinta duk ya birkita jalilah saboda irin mutannan ne masu tsananin sha'awa Ga baki daya sun sauka akan layi sai faman kissing din juna suke ya rabata da kayan jikinta Duk yanda jalilah taso kwace kanta ta garara saboda zafin da take ji sai faman gumi take daqyar jalal ya qyaleta Da sauri ta tashi ta qarasa toilet tayi wanka ta gasa jikinta ta fito Ko kallonshi batayi ba ta wuce dakinta da sauri ta shiga shiri ta kammala ta fito Karo sukayi da jalal yayi saurin riqeta "sorry" harara tayi mishi "dan Allah ni bari na tafi kasa nayi missing lecture dina kawai" Kawar da kanshi yayi yana dariya "muje" bazani dakai ba fa " saifa kinje dani" dariya tayi ta tureshi ta fice da sauri "kayi break fast pls" Murmushi ya bita dashi taje ta dauki motanshi wacce shi da mai Martaba kadai keda irinta Tafia take ana bata hanya kasan cewar tinted galss ne sunyi tunanin mai martaba ne Har ta qarasa cikin school Harara amira tayi mata "amirah Allah na shirya da wurin ya jalal ne ya batamin lokaci" Naji nidai muje kafin sarkin masifar nan yazo Suka shige class Har kusan 4 ba labarin jalilah ga Baki daya jalal takaicin rashin bata waya ya cikashi haka ya haqura Suna qarasa sallah ya hango motarshi murmushi kawai yayi yana dagowa suka hada ido da mai martaba yayi sauri kawar da kanshi Ciki ta wuce taje tayi parking shuru taqi fitowa Takawa yayi zuwa wurin har ya qarasa bata fito ba Bude motan yayi ta juyo da sauri Ajiyan zuciya ta sauke "me kikeyi ne? Allah ya jalal na gaji ne" Murmushi yayi "sauko muje" ai na gajine shiyasa" Kawar da kanshi yayi yana murmushi "Zaka goyani ne? Ba shiri yayi dariya ganin ga hadiman gidan gasu baffa kawai a ganshi ya goyeta "Su baffa suna kusa fa" turo baki tayi "meye damuwana ni" "Okay sauko na gayaki din" Da sauri ta sauko ta rufe motan ai koda ta juyo jalal yayi nisa Ganin su baffa ne ya hanata binshi da gudu........... [25/12, 15:52] Hassan Atk: 🤴🤴JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 171-176 Zaune suke a parlour'n gidan suna fira "cool jalal jalilah tana zuwa school ko? Kai ya gyada Amma nayi mamaki fa sabida idan zan fita zan ganta a hanya ta wuce amma yanzu na daina ganinta "yau ma sai after 4 ta dawo" okay Menene? So kake in barta tayi wasa da karantun? Kai ya girgiza yana murmushi "Allah akwai wani abu dan wannan murmushin naka nasan da magana a qasa" Kasan dai bazan hanata ba ko? Harara yayi mishi "yafi komi sauki a wurinka" ni din? Eh, wannan kishin naka da ka gagara biyewa shi kadai ya isa ka hanata zuwa school din" kawar da kanshi yayi yana dariya "wai me ka maidani ne? "Wanda zuciyanshi ta cika da tsananin so da kishin jalilah tun tana qarama" Duka jalal yakai mishi ya goce yana dariya "Malam kasan fa nayi zaman kafancen nima naga meke tafia" "Amma kasan kawai ina kulawa da itane badan nasan matsayina a wurinsu ba ko? Wannan yaren naka bana fahintarshi Ai nasan bazaka fahinta "Cool jalal kaga tun jalilah na primary kuke soyayya fa" Aurenta nayi a lokacin ai Dariya mubarak yayi "taya zaace ummi data haifeka bata samun mafanarka baffa ma haka nima haka amma jalilah har fira kake mata kuma qanwarka" Zancen ya isa haka,,, sai fa mun tuna baya Sai kayi "tare za muyi" wai meye haka Allah zan tafi" Idan ka tafi nasan jalilah ce ta hanaka sakat shiyasa kakeso kaje ka ganta kuma bazan haka ba soyayya gaskiya ce "Tsaki jalal yayi ya tashi mubarak ma ya tashi "ka gaida jalilah" Be kulashi ba yayi fice mubarak yabi bayanshi yana dariya har wurin da yayi parking "Baza muyi sallama ba? Eh "Wai me yasa? Dan Allah banason surutu saida safe" Murmushi mubarak yayi dan ya fahinci fushi ne jalal din yayi "Fushi kakeyi dani kenan? Be kulashi ba ya bude motan kawai ya shiga Qofan mubarak ya riqe "Allah ba inda zaka sai ka amsamin" fushi kakeyi dani? Dariya jalal yayi "kai ka fiye matsala wallahi meye abinshi anan zanyi fushi da wanda nafiso ne? Duka mubarak ya kai mishi "Allah ka daina dukana a qirji dan zaka iya fasamin zuciya" dariya sukayi ga baki dayansu sukayi sallama Mubarak yana tsaye har saida ya daina hango cool jalal yayi murmushi kawai ya shige ciki A parking space ya hadu da cool AJ "daga ina haka? Harara yayi mishi "nawa da sauki dan ban dade da fita ba ai" Dariya cool AJ yayi "rakani dan Allah nayiwa ummi laifi" Kaje ka bata haquri mana saina rakaka? Cool jalal kasan fa da kayi magana ta haqura pls muje dan Allah Murmushi yayi suka nufi part din ummi Kallonsu tayi tasan meyasa jalal din yazo dan taga kallon da yayiwa cool AJ "Sannu ummi" kai ta gyada mishi kawai "Ummi na tuba ki yafeni" Ummi karki yafeshi ason ranshi yayi Harara cool AJ yayi mishi "ummi dan Allah kada yayi mana dariya laifin juwairiya ne fa Juwairiya baza tazo ta dauke yaron nan ba kai kazo ka daukeshi Ummi itace ta aikoni fa Dariya ummi tayi "abdul baka rabo da abin dariya wallahi naji Ku tashi Ku tafi saida safe" Suna fitowa cool jalal yayi dariya "Allah zamu bata" "Rakiya fa nayi maka? Eh naji ai da mubarak bazaka ziga ummi ba saidai ka tayashi bata haquri Murmushi jalal yayi yana mamakin yanda cool AJ yakejin zafin kusancinsu da mubarak "Kana tunanin nafi sonshi dakai? Eh hakane Murmushi kawai yayi ya juya ya nufi part dinshi dan besan me zece da cool AJ ba Sosai take bacci ya nufi dakinshi yayi wanka ya shirya ya nufi dakinta Cikin bacci jalilah taji kamar ana tabata ta farka Bata rai tayi "lafia? Murmushi yayi "bacci zanyi" shine sai ka tadani? Ta fada cike da shagwaba Qara hadata yayi da jikinshi yana shaqar qamshin jikinta "Ya jalal dan Allah ka barni nayi bacci mana" Shi kasanshi jalal din ta bashi tausayi ya rasa meke damunshi ko yaushe cikin tsananin shawarta yake "Ya jalal fa? Sam be saurareta ba yasa hannu ciki boobs dinta yana wasa dasu Kamar tayi kuka takejin dan tasan idan yaci gaba da abinda yake mata zata biye mishi kuma batajin tanada wani qarfi a jikinta "Ya jalal dan Allah ka daina mana" tayi magana cikin wani yanayi da ya qara birkita jalal Kamar qara bashi kwarin gwiwa take idan tana yi mishi magana sai faman romancing dinta yake Abinda jalilah take gudu shine dai ya faru da ita Nidai kam na tausaya musu dan shi kanshi jalal din a gajiye yake *12:30am* na hango jalal ya fito daga wanka shida jalilah ga baki daka gansu kasan a agajiye suke Kwanciya suka cikin qanqanin lokaci sukayi bacci Dakyar jalal ya samu ta tashi tayi wanka tayi sallah Lafian gadon tabi ya gama abinda yake yaje kusa da ita ya kwanta "Ya jalal dan Allah kai mutum ne? Dariya yayi ya janye hannunshi dakai kan boobs dinta Tana jinshi saita fara bacci sai ya fara shafa jikinta sai abin nashi ya bata dariya "ya jalal Allah jarabarka tayi yawa" Dariya yayi "nifa ba komi nake miki ba kiyi baccinki" hannunshi da yake cikin riganta ta kalla "Me hannunka yake acikin rigana? Dariya ta bashi "Tambayeshi kiji" ya fada tare da matsa mata boobs dinta Qara tayi cike da shagwaba "ya jalal Allah nipple dina har zafi yakemin ka daina dan Allah" "Sorry bari naga yanda yayi" harara tayi mishi "saida na gani" Rigan ya zame ya tsurwa boobs dinta ido yana murmushi Iska ya hura mata ta tureshi tana dariya shima dariyan yake "Ya jalal Allah ya yaye maka" ba ameen ba" Ya wani hade rai "ya jalal dan Allah ka barni nayi bacci Allah zan hadaka da ummi" Dariya yayi ya gyara mata riganta "ayi bacci lafia" "Allah yasa zaka barni" murmushi yayi ya kwanta Bacci suke sosai ba wanda ya samu tashi daga cikinsu har 10 Jalilah ce ta fara tashi taje tayi wanka ta hada break har lokacin bacci jalal yake taje ta qara gasa jikinta ta fito ta shirya Kasa dashi taje sai kuma wani tunanin yazo mata "gara kayita baccin ai na huta nima.................... [25/12, 15:52] Hassan Atk: 🤴🤴 JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 177-180 Juyawa tayi kawai ya janyo hannunta ta fado kan jikinshi yasa hands dinshi ya zagayeta yana shaqar qamshin jikinta "ya jalal ka tashi mana kasan meye time ko? Hannu yasa ya bude zip dinta tayi sauri ya tashi ya qara janyota still idanunshi a rufe suke yana murmushi "Ya jalal ko machine ne kai saika barni yanzu kam" Sosai suka shiga dariya ta samu da gudu zuwa part din mami Fira suke saiga cool AJ da mubarak sun shigo da murna sun karbo appointment latter dinsu harda na jalal a company din alhaji sadiq "Ya mubarak Allah ya sanya alkhairi" ni kuma kimin mummunar addua kinji? Dariya sukayi "ya abdul meye abin fushi ai naga ba ya mubarak kadai nayiwa ba" Banza yayi da ita suka shiga fira Sallama yayi kasan cewar yaje part din ummi be ganta ba "Mami barka da yau" kai ta gyada mishi mubarak ya bashi appointment letter dinshi Murmushi sukayiwa ahankali jalal ya furta "congratulation na angel" murmushi mubarak yayi "thanks na...." Dariya sukayi Tsaki cool AJ yayi ya fice mubarak ya bishi da kallo "cool jalal ka taba bros ne ko? Murmushi kawai jalal yayi ya nemi wuri ya zauna Tsam jalilah ta tashi ta fice ya bita da kallo kawai ya juyo ya fara magana da mami "Mami bansan meke damun cool AJ ba kawai yana fushi dani wai nafison mubarak akanshi" Murmushi tayi "ai kuna nuna mishi qabilanci ne" haba mami kawai kice yaronki kike tarewa nida mubarak fa ba wanda yake nuna mishi kawai rikici ne irin nashi ni da mubarak fa ko yaushe cikin fada muke shine kuma yake wani qorafi" Yanzu da kayiwa mubarak congratulation kayiwa abdul din? Mami kinga fa tsaywa beyi ba ya fice "Dole ya fice dan yaga bakwa sonshi" Mami ya kike magana haka dan Allah? Toh ai gaskiya ne Fushi yayi ya tashi "jalal zo nan" yaje kusa da ita ya zauna "Jalal kaine babba nasan kunfi shaquwa da mubarak akan abdul kuma hakan ba damuwa bane a wurina ka qara haquri dasu fushi ba naka bane sai ka jure kuma ka fahintar da abdul din hakan kai da mubarak kunfi shaquwa ne amma bawai kafi son mubarak din bane" Kai ya gyada mata ya tashi ya fice Tunaninshi mubarak yana tare da abdul amma sam be ganshi ba abdul kawai ya sama "mubarak fa? Tsaki yayi ya wuce part dinshi ga baki daya jalal yaji hankalinshi be kwanta ba kar dai abdul ya gayawa mubarak abinda yake ranshi Da sauri yabi bayan cool AJ ya sameshi a parlour "Me ka gayawa mubarak din ne? Harara yayi mishi "meye damuwarka da abinda na gaya mishi? Ajiyan zuciya ya sauke "abdul me yasa kake haka ne? Mubarak fa dan uwanmu ne meyasa zakayi haka? Zama yayi ya shiga matsa wayanshi "abdul ka gayamin me ka gaya mishi" "Banason surutu pls kaje ka tambayeshi" Ajiyan zuciya ya sauke "abdul dan Allah ka daina wannan tunanin pls kaida mubarak duk dayane a wurina kada ka manta fa mubarak ya sadaukar da ranshi saboda mu,,, ummi, baffa, mami, abba kai har jalilah ba wanda yayi yunqurin bani jininshi lokacin da nake qoqarin bari duniya,,,, saurin dakatar dashi cool AJ yayi "ka sadaukar da ranka akaina shi kuma ya sadaukar da nashi akanka right? Na fahinceka ya juya da sauri jalal ya janyoshi "Abdul meke damunka ne? Ya kake magana haka? Kai kenan ko yaushe da kalan fitinar da kake yi? Eh ai zakace haka amma ai shi mubarak din ba kalan fitina da umurnin da baya baka baka taba complain ba sai ni da bana damuwa da abinda kake yi" Ajiyan zuciya jalal yayi "so kake nabar mubarak din ko me kake so? Yanayin yanda yayi magana sai kuma ya bawa AJ tausayi ya tabbatar jalal bayason fitina "Kana nufin duk yanda nace kayi zakayi? Kai ya gyada mishi Murmushi "yaje ya bude fridge ya zuba mishi ruwa ya bashi ya karba kawai "kasha mana" ba musu yasha Ya dago yana kallonshi "pls abdul banason fitina dan Allah ka sanja wannan tunanin na nafison mubarak akanka mubarak ya fiye fitina ne shiyasa nake binshi saboda a zauna lafia kuma kaima kasan da hakan" Murmushi yayi tare da gyada mishi kai shima murmushin yayi "Gayamin meyasa mubarak ya tafi? Jawahir ta kirashi mamin mubarak tana nemanshi" ajiyan zuciya ya sauke "Bari naje nayi break fast" ya tashi ya fice Murmushi cool AJ yayi aranshi yanajin tausayin jalal yasan sun sanyashi tsakiya dan mubarak ma gwanine wurin fitina Zaune ya sameta sai faman qoqarin hada waya take "Ina kuka samu waya? Ya mubarak ne ya sayamun Ta bashi amsa ba tare da ta kalleshi ba Kusa da ita ya zauna "yunwa nakeji" kaje kaci abinci mana Ke an gaya miki haka akewa miji? Dariya tayi "ya jalal dan Allah kai kenan da kalan fitina da kake zuwa ko yaushe" Murmushi yayi ya karbe wayan yaja hannunta suka nufi dinning Kallonshi tayi lokacin da ya kammala cin abinci "ya jalal yunwar kenan? So kike naci da yawa har na kasa aiwatar da komi? "Allah ya jalal ga baki daya ka sanja bansan meke damunka ba" dariya yayi ya jata suka koma parlour Fira suke gwanin shaawa sai kasan 2 jalilah ta tashi taje ta shirya ta fito "lafia? Ya jalal lectures nake da har 6 fa,,,, amma tare zamuje ko? Aa ya jalal kayi mana girki mana Dariya yayi "saifa kinje dani" muje ai nasan dolene sai ka bini Kallonshi tayi cikin farin bowel dinshi ya qara gyara kanshi ya kafa hula ya Sanya baqin glass dinshi Murmushi tayi mishi suka fice Driving yake cikin natsuwa suna fira har suka qarasa Bari na jiraki anan ko? Ya jalal girki kuma fa? Me kakeso muci dan Allah? "Mu cinye kanmu mana" dariya tayi "saina fito" kai ya gyada mata yana murmushi tayi mishi peck ta fice Kallonta yake har ta fice yana murmushi Kusan 4 ya hangosu itada amirah sai faman cin magani take har suka qaraso Bude bayan tayi amirah ta shiga ta bude gaba ta shiga Kallonta yayi cike da murmushi "wayatabaki ne? "Ya jalal Allah duk laifinka ne" Dariya amirah tayi "yanzu kuma ya tashi daga laifina ya dawo kan ya jalal? Murmushi yayi "gayamin meye laifi na? Test fa nayi yanzu saboda ban shiga da wuri ba "Toh menene? Ya mubarak fa yace ba ruwanshi da nayi aure zai iya dukana idan na bata mishi kudi a banza dan ya fahinci diz dayz ina wasa sosai kuma duk laifinka ne Allah" Murmushi yayi "sorry zan kiyaye" muje masjid pls" Motan ya tada suka nufi masjid sukayi sallah Sai 6 fa zamu fito,,, murmushi yayi tare da lumshe idanunshi tayi saurin kawar da kanta saboda komi na jalal yana sanyata shiga wani yanayi Sosai jalal ya fahinceta dariya yayi "lafia? Sai mun fito ta juya "bikiji ba" ta dawo tana kallonshi alama yayi mata da tazo ba musu taje Kallon amirah yayi yaga hankalinta baya wurin Hannunshi yakai kan boobs dinta yadan matsasu tare da lumshe ido saurin janyewa tayi ta juwa da sauri yana mata dariya Zaune suke amirah ta kalleta sai kuma tayi dariya "lafia kike dariya "jalilah wallahi kin more miji" murmushi kawai jalilah tayi ta mayar da hankalinta gun lecture din *6:05pm* jalal ya hangosu sun fito direct wurin wani mota suka wuce sun dade tsaye suna magana kafin suyi sallama ta juyo ta nufi wurin da jalal yake Ajiyan zuciya sukayi lokaci daya tare da sakawar juna murmushi Tafiya suke ta juyo tana kallonshi "ya jalal ko za muje gidan ya mubarak ne? Kai ya girgiza mata "Ai nasan baza muje ba kafison muje gida ka takurani" murmushi yayi ba tare da yace da ita komi ba Suna qarasawa kowa ya nufi dakinshi Kitchenta nufa ta hada cuscus ta fito ta nufi dakinta Zaune ta sameshi ya sakar mata murmushi Da sauri ta shige toilet ta rufe dariya kawai yayi Daure da towel ta fito bata sameshi ba tasan masjid ya tafi tayi sauri ta shirya ta gabatar da sallah *8:30* jalal ya shigo direct dining ya nufa jalilah tabi bayanshi sukaci abinci Janyota yayi ahankali ya kwantar da ita kan dining yana murmushi "ya jalal yau kuma akan dining za muyi? Kai ya gyada mata lumshe ido Kayan da suke jikinta ya fara ragewa saida ya rabata dasu ga Baki daya Kallonta yake yana murmushi ya fara kissing din company dinta sai faman fitar da numfashi take kamar zata shide Ahankali ya fara shigatan ta qanqameshi suka shiga raya sunnah Dagota yayi yana suka sakarwa juna murmushi ya mayar mata da kayanta Wani kallo tayi mishi ya shiga dariya "i'm jalal Ibrahim kafancen" tureshi tayi tana dariya "ai nasan jalal Ibrahim kafancen ne kuma jarabbabe" ai taimaka miki nakeyi dan kin fini jaraba" au haka zakace? Eh ya bata amsa murmushi kawai yayi ta tashi ta nufi dakinta ya shiga dariya Kusan 1hr jalal ya nufi dakinta ya sameta tayi shirin kwanciya yaje kan gadon ya zauna ta kammala abinda take ta nufi qofa "ina zaki? Zanje dayan dakin kasan ni jarababbiyace kada na takuraka" Dariya yayi ta juya kawai ta fice yabi bayanta Kwance take kan 3sitter ta juya mishi bata Kallon shape dinta yake yana murmushi yaje kusa da ita yayi kneel down yana shafa kanta Juyowa tayi ta aiko mishi harara "Allah nine jarababbe kawai na fada ne" ka kyakeni da jarabana" dariya yayi "am very sorry" haka ake bada haquri? "Aa" ya fada da sauri ya janyota zuwa jikinshi Bakinshi ya hada da nata suka shiga kissing din juna............ [25/12, 15:52] Hassan Atk: 🤴🤴JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TI _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 181-185 Ga baki dayansu ba wanda baya mayar da numfashi jalilah ce ta fara tashi haka jalal din ya tashi suka nufi dakinshi "Ya jalal dan Allah ka barni nayi bacci pls" dariya yayi "Ai nima baccin zanyi" suka haye gadon suka kwanta Ji yake idan baya tabata ba baya iya bacci "jalilah" "uhmm" am sorry ba komi zan miki ba kinji" "Ya jalal ko rantsuwa nayi bazanyi kaffara ba kai ba mazinaci bane dan Allah ya kake controlling kanka ne dan ni wannan jarabar mamaki take bani" Murmushi yayi "jalilah bansan meke damuna ba kawai ko yaushe banajin zan iya gajiya dake" shuru tayi saboda koda yake maganan hannunshi yana cikin riganta yana wasa da boobs dinta haka ta haqura har ta samu yayi bacci ta zame hannunshi ta juyo tana kallonshi tana murmushi sosai takejin sonshi a ranta ta sanya hannu ta shafa face dinshi tare da yi mishi peck ta qara shigewa jikinshi tana shaqar qamshin jikinshi har bacci yayi awon gaba da ita Lokacin sallah ne ya gabato ahankali jalal ya bude idanunshi yana kallonta Murmushi yayi ya zame jikinshi ya nufi toilet Ahankali ya shiga tadata "jalilah tashi time yana tafia" hamma tayi tare miqa tana karanto addua Masjid ya wuce bayan sun gama sallah ya wuce wurin ummi suka shiga fira shida ummi da baffa "Abdul jalal sai yaushe zaka fara zuwa aiki? Sai Monday baffa" toh Allah ya qara rufa asiri ameen baffa "Wai jalilah lafia take? "Lafia" ya bashi amsa tare da miqewa tsaye "Ummi a wuni lafia" ya fice kawai Murmushi baffa ya bishi dashi tare da tausaya masa "Aisha ina tausayin jalal gashi an sanya qiyayya tsakaninshi da jalilah kuma ya gagara aure" baffan jalal kayi mishi izini yayi auren dan Allah" kar ki damu Aisha zanyi mishi magana akan yayi auren Tsawon wata biyu da wannan firan na ummi da baffa Kwance jalilah take a dakin ummi kasan Cewar batajin dadin jikinta ganshi yau fushi take da jalal saboda ya hanata shan madaran kuka Baffa ne ya shigo shida jalal ta gaida baffa ta aikawa jalal da harara Zama baffa yayi jalal ya zauna kusa dashi "Sannu baffan jalal" yauwa ummin jalal Murmushi tayi ta zauna suka gaisa da jalal Kallonshi baffa yayi ya sunkuyar da kanshi "Jalal daman inaso muyi magana dakai,,, jalal banaso rayuwarka ta qare a haka inaso kaje ka nemi wacce kakeso kazo zan nema maka aurenta" Zumbur jalilah ta miqe "Allah ni kuma bazan zauna dakai ba kuma zanje a ciremin cikin nan,,, kawai sai ka wani nunawa baffa kanaso kayi aure toh meye ne bana maka da zaka wani qara aure? Toh wallahi bari kaji saina zubar da cikin nan saidai wacce zaka aura ta haifa maka yara kawai sai kani cewa zaka qara aure toh kaje kayi auren ni bana sonka" Ga baki daya kunya ta kama jalal ji yake kamar ya shige cikin qasa Kallon mamaki su baffa suke musu "Wane cikin ne zaki zubar? "Allah ummi bazan zauna dashi ba inhar ya qara wani auren" Wai wane cikin ne kike magana akai? Ummi Allah bana rageshi da komi kawai auren ne yakeso ni kuma bazan zauna dashi kuma saina cire wannan cikin" Kallonshi ummi tayi "jalal da gaske juna biyu ne da ita? Sunkuyar da kanshi yayi yana shafa face dinshi Kallon juna sukayi itada baffa jalilah kam tashi tayi ta wuce part dinsu tana kuka Ahankali ya dago yana kallon ummi ta aiko mishi da harara "ummi dan Allah ki yafeni" tashi ka bani wuri Da sauri ya miqe ya fice "Baffan jalal kaji wani labari" dariya yayi "ga baki daya yaran nan sun raina mana da hankali" murmushi yayi "Allah ya qara basu zaman lafia Sosai ya sameta tana kuka yaje kusa da ita ya janyota jikinshi "jalilah nifa bana ce zan qara aure kawai baffa ne kyma bazan qara Auren ba ai" ba wani nan ai na fahinceka Me kika fahinta? "Baka sona" "jalilah ya kike magana haka? Bana sonki fa? Eh ta janye jikinta da sauri ya janyota "ni ka kyaleni nima bana sonka" sosai yaji zafin hakan "Saboda me zakice haka? Kusa dashi ta zauna idanunta sun ciko da kwallah "ya jalal katajin kana sona a zuciyanka bayan kasancewana qanwarka? Idan har ka tabaji toh meyasa baka taba furta hakanna gareni ba? Murmushi tayi tare da share hawayen da suka zubo mata "Kaje ka nemi wacce kakeso ya jalal nima zan tayaka sonta" janyota yayi jikinshi yana bubbuga bayanta "Jalilah banida wani farin ciki face kasan cewa tare dake ke kadaice farin cikina ke kadai nakeso ki daina cewa bana sonki wallahi ke kadai nakeso" Ajiyan zuciya ta suke ga Baki daya jalilah ji take kamar zaa kwace mata jalal din ta qanqamehi tana mayar da numfashi "pls ya jalal say you love me" Murmushi yayi yana shafa cikinta "I love you so Much" Murmushi tayi ta qara shigewa jikinshi "I love you more" sun Dade a haka daga bisani ya dago da face dinta yana murmushi "ki kulamin da bros mubarak pls" dariya tayi "Amma fa ya abdul zayi fitina" murmushi yayi ya dagata "muje ki ragemin gajiyana pls" ya jalal aikin me kayi dan Allah? Kin manta zafin da kika hada min a gaban su ummi? Murmushi tayi suka nufi dakinshi............... [25/12, 15:52] Hassan Atk: 🤴🤴JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 186-190 Ya jajal dan Allah kada ka dade idan ba so kake ya mubarak din yasha gajiya ba shima,,, murmushi yayi "idan jarabarki ta barki bazan dade ba amma idan naga biki rabu da ita ba bazan barki ba gaskiya dan banaso na tauye haqqinki" Dariya tayi "nice ma jarababbiya? Eh "toh naji na haqura a barni da jarabana" Ni kuma nayi ya da nawa? Naka me? Jaraban da kuka koyamin mana" dariya sukayi ga baki dayansu suka shiga raba juna da kaya suka tare kan gado Tsawon kwana uku jalal ya shiga wasan boyo da baffa sam baya bari su haddu ummi ma sai ya shigo yana sauri yaje zai tafi wurin aiki ne har dariya yake bata Zaune take a part din ummi tanasha madaran kuka jalal ya shigo da sauri ta boye tana mishi wani kallo Dariya yayi "ai ba hanaki zanyi ba" kama isa ka hanani? Toh meyasa kika boye da kika ganni? Saboda kada ka aranka zan iya baka "Ni da nake da pure madara me zanyi da madaran kuka" duka ta kai mishi suka shiga dariya "Ummi fa? Tana kitchen" ya tashi ya nufi kitchen din "Sannu da aiki ummi" yauwa ya aiki? Lafia qalau "Ummi baffa ya fita ne? Baffa ya kirani dazun yana shaidamin ya tafi kafancen kuma sai gobe zai dawo" Ummi lafia? Aikinshi yajeyi mana" wuri ya nema ya zauna "Lafia kayi zaune anan? Ummi firan zan tayaki fa" ka gama guduna kenan? Sosa kanshi yayi yana murmushi "Jalal wai wane irin mutum ne kai? Kai kenan komi naka yana acikinka? Ummi dan Allah me nayi? Bakayi komi ba,,,, ummi dan Allah kawai sai nayita fada jalilah nada juna biyu? Kallon mamaki tayi mishi "au idan ka fadamin ne wani abu? Aa ummu ba haka nake nufi ni Allah bazan iya fadawa kowa ba" toh ai ita ta fada kuma aure ba fashi sai kayi Leqawa yayi yaga ko jalilah na kusa "ummi dan Allah ki ajiye wannan zancen Allah ni jalilah kawai ta isheni Dariya ya bawa ummi "toh naji tashi kaje ni zaka hanani aikina" murmushi yayi yaci gaba da kallonta Wayanshi ce tayi ringing yaga sunan mai martaba ya daga cike da girmamawa ya gaidashi "Zanzo yanzu abba" ya ajiye wayan "ummi abba yana nemana" toh kaje mana Zaune yake gaban mai martaba "abdul jalal aiki nakeso kaje kayimin acikin yankina akwai qauyen da nakeso ka bincikamin damuwarsu meye suke buqata" Shuru yayi yana tunanin yanda zeyi da wannan aikin "Jalal akwai matsala ne? Kai ya girgiza ya tashi ya fice Shiryawa yayi cikin rantsatstsiyar shadda ya nufi part din ummi kusa da jalilah ya zauna "jalilah zan tafi wani qauye abba ya sanyani aiki" aiki fa? Kai ya gyada mata "amma yau zaka dawo ko? Murmushi acen zan kwana,,, ido ta zare "kuma kai kadai zaka tafi? Kai ya gyda mata yana murmushi Kukan shagwaba ta fara mishi "Allah da wasa nake yau kuma bazan dade ba" turo baki tayi tadan kwanta jikinshi "Kinaso na dade ne? Aa banaso "toh ki barni naje yanda zan dawo da wuri" Peck yayi mata ya fice yana sauri Sosai jalal yasha wahala wurin zaga garin kafin ya dawo duk wani kudi da ya fita dasu saida ya kyautar dasu ga mabuqata sosai yaji tausayinsu Masjid din qauyen ya nufa yayi sallah magrib ya fito Wayanshi ya dauko yaga missed calls na jalilah ba iyaka Dana ummi Kiran ummi yayi "jalal lafianka? Ummi wayan yana silent wallahi " yaushe zaka dawo? Ummi yanzu zan taso Allah ya kawoka lafia Kiran jalilah yayi kamar Kira take "ya jalal dan Allah meya sameka? Murmushi yayi "wayan yana silent sai faman aiki nake" shine ka manta dani ka manta baby'n ka? Dariya yayi "na manta dake amma baby na yana raina" Ido ta zare kamar yana kusa "ya jalal ni ko? A da wasa nake kasa ki batamin hawayenki pls" toh yaushe zaka dawo? Shuru yayi kamar mai nazari "ya jalal fa? "Jalilah ban kammala aikin saidai zuwa gobe" aiko tasa kuka "Allah da wasa nake yanzu zan taso pls kukan ya isa haka kinji" "pls ya jalal kada ka dade" "Bazan dade ba jarababbiya" Dariya sukayi ga baki dayansu ya ajiye wayan *9:45pm* jalal yayi sallama a parlour'n mai martaba ya gaidashi "abba suna buqatar taimako sosai gaskiya" murmushi yayi Kaje gobe kazo muyi magana godiya yayi ya tashi ya nufi wurin ummi Baffa ya fara haduwa dashi suka gaisa ya nufi dakai wurin ummi "Jalal ka dawo? Eh ummi "toh sannu da hanya" murmushi yayi "yanzu jalilah tabar nan tana kuka wai ta kiraka bata sameka ba" kanshi ya sosa ya tashi kawai ya fice "Kwance ya sameta kan 3 sitter yayi sauri ya qarasa wurinta ya Dora hannunshi saman cikinta ta bude idanunta dariya yayi "kinje wurin ummi kina kuka saboda jaraba har wurin sirika ake zuwa ana kuka miji be dawo ba" "Ya jalal Allah ka daina" dariya yayi ya janyota jikinshi "na daina kada a hanani wannan precious company" dariya tayi suka fara kissing din juna har jalilah ta gaji ta tureshi "Allah kai ba'a maka bismillah" dariya yayi ya jata suka nufi dakinshi Wanka yayi suka fito suka nufi dinning Cin abinci suke yana tsokanarta sai zuba mishi shagwaba take yana dariya "dama ummi ta fada ni zanfi kowa shan wahala tunda na shagwabaki" Dariya tayi "ya jalal dan Allah yaushe zamuje kafancen? Murmushi yayi "sai weekend" Sosai jalilah taji dadi ta shiga murna "ai za muje gonar baffa ko? "Kije ki debo rake kiyita faman zubamin surutu ko? Hhhhhhh "ya jalal ai shuru zanyi sai dadin ya kasheni kawai" "Me kikace? Dariya tayi "bazan qara fada yi haquri" Murmushi yayi suka kammala suka nufi daki Washe gari bayan jalal ya dawo daga aiki cool AJ ya tareshi "pls zakamin rakiya anjima? Kai ya gyada yana murmushi kowa yayi gabanshi *8:30pm* zaune suke shida jalilaha part din mami sam mami bata fahinci akwai jituwa tsakanin jalal da jalilah ba saboda sam ba wanda yake kula wani daga cikinsu Mubarak ne ya shigo "cool jalal kamin rakiya dan Allah" ba musu ya tashi saiga cool AJ ya shigo "cool jalal muje ko" Kallonsu yayi kawai ya fara dariya "lafia? "Kaga abdul yace na rakashi fa" Kana nufin ka manta? "Kaga nifa sai ka rakani" Allah ni zai yima rakiya Tsam jalilah ta miqe taja hannun jalal " Muje ya jalal kowa yaje shi kadai dan bazasu sanyaka tsaka suna maka fitina" bayanta yabi yana dariya suka fice Kallon juna sukayi sai kuma sukasa dariya mami ma murmushi tayi dan sun bata mamaki Kallonta jalal yayi cike da dariya "Allah ba ruwana idan kuka hadu da mubarak" dariya tayi "ai naga karasa abin yi ne shiyasa nayi hakan nasan bazasu ga laifinka ba" dariya yayi Ba waninan kinsman zamu Dade ne kuma bazaki iya jurewa ba "eh naji ai kaine kake sanyani jaraban" Dariya suka shigayi suka nemi wuri suka zauna suka shiga firansu................ [25/12, 15:52] Hassan Atk: 🤴🤴 JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 191-195 Ya jalal bacci nakeji,,,,, cak ya dagata suka nufi dakinshi ya sauketa kan gadonshi ya nufi dakinta Wani rigane wanda da sashi da rashin sashi duk dayane jalal ya daukowa jalilah Kallonshi tayi tana murmushi ya taimaka mata ta sanja Murmushi yayi "precious sai qara cikowa kike fa" duk aikin baby'n ka ne ai Gaskiya ya kyautamin Dariya tayi "ya jalal baka rabo da abin dariya" Hannunta yaja suka koma kan gadon "Ya jalal kaga tsaya kaji ranar naji mami tana yiwa ya abdul fada akan ya daina takura sis juwairiya saboda tanada juna biyu hakan zai iya taba baby'n" ido ya zare "da gaske? Kai ta gyada mishi "Kinga banda irin wannan baby'n manta da wannan zancen" Allah da gaske nake" shafa cikin yayi "dan Allah ka rufamin asiri ai zan iya mutuwa na barka a maraye kaga kayi haquri kasa ka samu matsala saboda zan shiga damuwa ni kuma zan riqayi ahankali ba tare da na takuraka ba" Tureshi tayi tana dariya "ya jalal dan Allah na rana daya ka dagamin qafa mana" dariya yayi "duk ranar da kika haihu promise you zan daga miki qafa" Dariya suka shigayi ya janyota jikinshi yana shaqar qamshin jikinta ahankali ta shiga shafa jikinshi tare da lumshe idanunta tana shafashi ahankali Sannu2 jalilah ta shiga wasa da machine dinshi tana shafawa ahankali sai faman jan numfashin shi yake kamar ze shide Zamewa tayi daga jikinshi wanda sam jalal bayada karfin da ze riqeta tayi qasa kadan ta fara yi mishi socking sai famar mayar da numfashi saida ta tabbatar ya samu natsuwa ta dawo kan jikinshi ta kwanta tana murmushi "Bazaka qara bawa baby na wahala ba" murmushi yayi cike da farin ciki "Jalilah kin zama daya tamkar dubu banajin akwai namijin da ya kaini sa'a a duniya,,,, bansan dame zan sakawa su ummi ba,,, suka raineni suka bani tarbiya da ilmi suka zabamin mace ta gari,,,, Allah ne kadai zai iya biyanku" Murmushi tayi tare da shafa face dinshi "ya jalal kai ka fada ni kuma nace me? Duk abinda su baffa sukamin ba wanda yafi tasiri arayuwa face mijin da suka auramin wanda nasan burin ko wace 'ya mace ta samu irinshi" Murmushi suka sakarwa juna "Allah ya saka maka da alkhairi baffa da ka auramin jarababbiyar mace" Duka ta kai mishi a qirji "yanzu waye jarabarshi ta bayyana? Dariya yayi tare da qara hugging dinta ahaka har bacci yayi awon gaba dasu Washe gari kowa ya shirya zuwa wurin da yafi iyawa jalal yaje ya fitar da motan jalilah cikin qanqanin lokaci aka wanketa suka fito "Wai waya baki wannan motan? Dariya tayi "bazan fada ba sai yanzu zaka tambayeni? Sorry gayamin dan Allah "Hmmm wa kake tunanin zai bani wannan motan in ba ya mubarak ba" murmushi yayi aranshi yana tunanin ko mutuwa yayi yasan mubarak bazai taba bari wani abu ya shigewa family dinshi ba Saida ya shiga ya tada mata motan ya bata taja ta fice kafin yaja nashi motan yayi gaba *After a months* Jalilah ta dawo daga school tana murna yau dai ta kammala ga cikinta har ya tsufa haihuwa yau ko gobe" Zaune take part din ummi jalal ya shigo ya zauna kusa da ita "ummi bacci take? Kai ta gyada mishi "Gani" kamar ya gaka? Ai naga kin kirani ne,,, a waya? Ta tambayeshi,,,, kai ya gyada mata Ni ban kiraka ba gaskiya,,,,, kallon ummi yayi yaga bacci take ya juyo yana kallonta "Saboda jarabanki har wayanki kika koyawa jaraban kirana? Dariya tayi "eh na koyar da ita kuma ummi tace bazan koma part dina ba saboda any time ina iya haihuwa kuma tafison akwai wani kusa dani wanda zai kula "Biki gaya mata jarababben miji kike da bane? Ya jalal tashi Mu tafi kar ummi ta falka taji kana wannan zancen" dariya yayi ya taimaka mata ta tashi suka nufi part dinsu Dariya ummi tayi "wannan zamanin da muke ciki Allah ka tsaremu yanzu wa zaice jalal zai iya wannan zancen dan Allah" Jalal kam besan me ummi takeyi ba yayi gaba abinshi *some hours ago* Kwance suke jalilah duk ji take maranta na mata ciyo ta kalleshi "ya jalal taimakin nayi wanka dan Allah" Tun jalilah na dauriya kada jalal ya fahinta har abin yazo yafi qarfinta sai faman zufa take "Jalilah lafia? Duk yanda taso tayi mishi magana abu ya gagara ga baki daya hankalin jalal ya tashi da sauri ya nufi part din ummi ya sanar da ita Cak jalal ya dauketa suka nufi part din ummi "jalal kaje ka kiramin assibi "ummi me zatayi? Banason fitina kaje ka gaya mata kuma dagacen kayi wurin sabgoginka kaji na gaya maka? Sam jalal bata iya musu da ummi ya tashi ya fice ga baki daya bata cikin natsuwa Masjid ya shige yana ta faman gayawa Allah damuwanshi Kiran mubarak yayi ya gaya mishi halinda ake ciki sam be bata lokaci ba yashigo gidan suka hadu Sosai ya shiga kwantarwa jalal da hankali har ummi ta kirashi ta sanar dashi jalulah ta sauka "ummi jalilah fa? Lafia qalau suke da sauri ya kashe wayan suka nufi part din ummi shida mubarak Mamaki ne ya cikasu ganin yara guda biyu wanda su daya suka sani kuma duka maza "Wow cool jalal wannan job din naka yayi kyau wallahi" ya daga waya ya kira mai martaba ya sanar dashi ga baki daya kowa murna yake harda mai martaba yaje ganin yaran amma mami kam bata leqa ba Ummi ce ta shirya taje wurinta "mamin abdul da nice naqi zuwa ganin jikanki da ya zama abin magana amma shuru ban ganki ba" Murmushi yayi "ban samu time bane" murmushi ummi tayi "toh a samu time aje aga jikokina" kai ta gyada sukayi sallama ta fice............ [25/12, 15:52] Hassan Atk: 🤴🤴 JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 196-200 Harara ummi ta aiko mishi ganinshi kwance kusa da jalilah "tashi ka fita" ummi dan Allah ina kikeso naje? Bazaka tashi ba sakina saba maka" "Ummi dan Allah ki barshi mana bayada wurin da zashi fa" jalilah Allah zan bata miki" Tashi yayi ya fice ya nufi part din mami ya nemi wuri ya kwanta "Jalal lafia? "Ummi ce ta koreni" sosai ya bata dariya "Kaje ka hanasu jego ko? Mami Allah ba abinda nayi kawai tace saina fita" "Wai zai shiga tsakaninka da umminka yayi kunya" "Jalal wane suka ka tanadarwa yaran? Mami mubarak yace wai sam sunan beyi mishi ba shine na barshi ya sanya wanda yayi mishi" Murmushi tayi ai duk dayane sai ku jira kuji sunan da zai sanya musu Yau ta kama ranar suna mai martaba yace ayi suna a masjid bayason wannan taron kallon mubarak baffa yayi yana murmushi "mubarak ya sunan da ka tanada musu? "Baffa hassan din shine Ibrahim khaleel husain din kuma shine Abubakar Sadiq" toh Allah ya raya mana su akan sunnah ya amsa da ameen Harara jalal ya aikawa mubarak shima ya maida mishi Murmushi mai martaba yayi sosai mubarak da jalal suke burgeshi Sosai kayi walima yara kam sunsha kyaututuka sai dare jalal ya shigo part din ummi "Me kazo yi? Ummi dan Allah wai me nayi ne da bakyason ganina? Au bakasan me kayi ba? Juyar da kanshi yayi yana kallon jalilah ta aiko mishi da sanyayyan murmushi "Ya jalal kaci abinci ko? Yaje wurin juwairiya yaci abinci banason yawan surutu" Haba ummi wa zaice ya jalal yana surutu kawai dai yanzu kin samu jikokine kin daina sonshi "Jalilah zo kibishi kuje cen harda yaran" ummi toh me yake miki ne dan Allah? Tunda na haihu sai faman fushi kike dashi ni bazan ma qara haihuwan ba" ta tashi tabar yaran ta shige ciki Kallon yaran yayi ya juya kawai ya fice Kune masu dawowa ku daukesu ai Mubarak ne ya shigo "ummi jalilah fa? Tana ciki Shine zata bar yara ta koma ciki? Idan wani abu ya samesu fa? "Gaskiya ne gara ta kula dasu" murmushi yayi "ummi dan Allah me cool jalal yayine yace kin tsaneshi ga baki daya ya daga hankalinshi" Mubarak fitina kawai yakeji bazai bari su gama jego ba idan suka koma part dinsu ya cinyesu ai ba wanda zai hanashi "Ummi dan Allah ki kyaleshi kinsan fa jalal baya jure kina fushi dashi ki daina dan Allah ummi" mubarak ai ba fushi nake dashi ba Amma bazaki qara hanashi ganin yaran ba ko? Murmushi tayi ganin mubarak yayi magana kamar zeyi kuka "Mubarak da yara hudu amma baka daina ahagwaba ba" dariya yayi "ummi idan ina gabanku aimantawa nake dasu Dariya tayi "toh Allah ya raya mana Ku" amin ummina" ya tashi ya fice Zaune ya sami jalal "cool muje walid yana yiwa mami fitina Mu maidashi dan Allah murmushi yayi yaje ya karbo walid din suka nufi gidan mubarak Tun daga wannan lokacin shiga part din ummi saboda fushi yake baffa ma a masjid suke haduwa Yau jalilah ta cika 50days a part din ummi sam ba wani ganin jalal take ba hakan yana damunta shima jalal haquri kawai yake Baffa ne ya tambayi ummi yaushe jalilah zata koma part dinta? Baffan jalal ka barni da jalal kawai fushi yake dani shine nakeso naga qaryan fushin" Keda jalal din naki kuma Aisha? Ka barshi kawai sai yazo ya sameni Bayan sallan isha jalal ya shiga part din ummi ya gaidata ta amsa "ummi gobe zanyi tafia" "toh" kawai tace dashi taci gaba da lazimi Ahankali ya dago yana kallonta "ummi dan Allah ki daina fushi dani koda zan samu ci gaba a rayuwana" Ni nace ina fushi dakai? "Ummi toh me nayi kika daina yimin addua? Kallonshi tayi dakyau ga baki daya dariya yake bata "jalal wa nakeda Sama da kai da zan daina yimaka addua? Toh ummi meye laifin da nayi miki? Murmushi tayi "bakamin laifin komi ba jalal saidai banason wannan damuwar da kake ciki" murmushi yayi ya dora kanshi saman qafanta ya kwanta "Ummi su khalil fa? Nace su sarkin tsotso dai ai wannan badan sunan baffan jalal yake da ba da nace na fasan auren khalifa ne dai ba ruwanshi da nono saidai ko yaushe idan ba hannun jalilah yajishi ba ba zaman lafia" murmushi yayi "Ya kwaso fitinar jalilah kenan? Ai Kaine ka bata jalilah dan ba wani damuwa tayi dani ba saboda kai Dariya yayi daya tuna yanda suke rayuwa kafin aurenshi da jalilah Fitowa tayi dauke da khalifa sai faman tsala kuka yake jalal yayi sauri ya karbeshi ya dorashi saman qirjinshi yana shafa bayanshi be wani jimawa ba yayi bacci Sarkin tsotso bacci ake ne? "Hmmm ummi wallahi wannan idan banyi da gaske ba sai ya shanyeni ga baki daya" Dariya jalal yayi "Allah ki daina yiwa baffana sharri" Ya jalal baya qoshi fa,,, toh menene? Dama a tagwaye zaka tarar hassan yafi rikici Harara ya aika mata wanda sam ita ba nufinta ta tsokani jalal ba Dariya ummi tayi "ai zaman jalal da mubarak ne ya sanya jalal ya fara magana" Allah ummi kamar kin sani haka nayita fama dashi a school Haka suka sha fira sosai jalilah taji dadin ganin jalal "Ummi gobe da wurin zan tafi kuma 2days zanyi" "Ya jalal ina zaka? Dan tsaki yayi kafin ya fara magana "abba ne ya sanyani wani aiki kuma a qauye ne" Ya jalal shine zaka zauna har tsowon 2days? Jalilah aikin yanada yawa fa,,, kukan shagwaba ta fara yi mishi "Jalilah bafa ko yaushe kike ganina bale yanzu kiyi fitina inaga kusan 5days ban shigo nan ba toh me akayi 2days" Dakin ummi ta nufa tana kuka ya bita da kallo har ta shige ciki Kallonshi ya mayar gun ummi "ai na gaya mana kai zakafi kowa shan wahalar jalilah saboda kai ka batata" Tashi yayi yabi bayanta yana dauke da khalifa Zaune ya sameta tana bawa khalil nono ya zauna kusa da ita ta juya mishi baya Murmushi yayi "precious bikiyi missing dina bane? Juyowa tayi tana kallonshi "ya jalal dan Allah kada ka kwana pls" Jalilah meye abin damuwa aciki tunda biki koma ba Ya jalal Allah zan koma yau Dariya yayi "yi haquri aikin bana wuni daya bane" kai ta gyada mishi Kallon khalil yayi wanda yake ta faman shan mono ya kafe jalilah da ido Dariya yayi "khalil wannan wayon naka yayi yawa gaskiya" Cire mishi nonon tayi a bakinshi aiko yasa kuka da sauri jalal ya maida mishi yana dariya "Baffana gaskiya ka daina yiwa khalifa wayo kana shanye ga baki daya shi kuma sai faman bacci yake Dariya jalilah tayi "ya jalal mami tace haka tayi fama da ya abdul har fada sukeyi da abba idan ta hanashi Murmushi yayi yaci gaba da matsa mishi nonon "Ya jalal haka ai sai ka sanya ya qware" wannan ai idan yafi haka bazai qware ba Ya jalal tsaya ka gani ta zame mishi nonon ya shiga kuka ta fara lallabashi sai faman kuka yake Kallonshi kawai jalal yake "precious yi haquri ki qara mishi kinji? Ya jalal Allah baya qoshi "Yi haquri precious qara mishi kadan" Ci gaba da bashi tayi yana sha daqyar yayi bacci Dariya jalal yayi "sannu da qoqari Murmushi tayi ta karbi khalifa ta kwantar dashi ta juyo tana kallonshi "ya jalal yaushe zamu koma part din mu? Yaushe kike so? Dariya tayi "yau nakeso" kai ya gyada mata.......... [25/12, 16:10] Hassan Atk: 🤴🤴 JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 201-205 Ya jalal da gaske fa nake Allah na gaji da wannan rashin ganin naka "ba wani rashin ganina ki dai fadi abinda yake ranki" Ya jalal idan har zaka riqa zuwa ko yaushe ina ganinka ka barmu anan kawai Dariya yayi dan shi bega abi fushi anan ba "fushi kikayi? Dariya tayi "ya jalal Allah kai sai kayita faman fassara mutum" naji muje ki hadamin kayan da zan tafi dasu" ya jalal wai da gaske kake 2days zakayi? Murmushi yayi aranshi yace 1week ma zanyi wallah,,,,, "Jalilah kinga idan banje ba zaiyi tunanin kawai dan ba aikin baffa bane" murmushi tayi "Allah ya taimaka" *8:30pm* jalal ya shigo wurin ummi suka gaisa yq nemi wuri ya zauna "ummi dan Allah ki bari jalilah tq koma part dinta yau" Kallonshi tayi da kyau "jalal ba tafia zakayi ba? "Ummi dan Allah ki barta ta koma" "jalal naga tafia zakayi idan ka dawo sai ta koma ko? Shuru yayi kawai ya daina kallonta "Jalal tashi ku tafi sauki ne na nema muku nima ai bason zaman naku nakeyi ba" "Aa bari kawai ayi yanda kika tsara" au fushi kayi kenan? "Ummi ba fushi nayi ba kawai dai na sanja raayine" Idan har ba fushi kayi ba ka hada iyalinka ku barni wurina nasha iska" Kai ya gyada zuciyanshi cike da farin ciki dan yasan idan ba haka yayi ba ummi zatace sai ya dawo daga tafia Tashi yayi ya nufi dakin da jalilah take ya sameta kwance direct kan jikinta yaje ya kwanta "Ya jalal ina ka shigene haka? Wurin ummi mana "Kinga tashi mu tafi dan Allah" ya jalal ka gayama ummi ne? Harda fushi saida nayi kafin ta amince Dariya jalilah tayi "ya jalal Allah yanzu ya dace ka ajiye shagwaba ka girma fa yanzu " Wane girma ne nayi? Yara nawa kake da? Mahmud da Mustapha" Amma kuma kake shagwaba? Dariya yayi "Allah bari kiji koda jikoki nake da idan ummi na kusa bazan daina jin kaina yaro ba" Dariya tayi "ni dai yanzu na girma gaskiya tunda har aisam ya zama saurayi" dariya sukayi naga yanda kika girma ai Ai tashi daga kan jikinta ya daga "dauko khalifa sai muje" Mamaki yake me mai martaba yakeyi tsaye kuma shi kadai Wurinshi suka nufa "sannu abba" murmushi yayi ya karbi khalifa da yake hannun jalilah "wannan waye? "Abba sadiq ne" murmushi yayi "masha Allah, aminina ka girma sosai fa" murmushi sukayi ya bata ya karbi khalil "Malam Ibrahim bacci yake gashi sak kamar malam Ibrahim din" Ya bawa jalal shi "abdul jalal sammako zakayi gobe? Kai ya gyada "Allah ya taimaka" ameen suka amsa tare da juyawa suka nufi part dinsu Kallo ya bisu dashi yana murmushi sai faman murmushi jalal yakeyi jalilah nayi mishi magana har suka shige ciki Ajiyan zuciya mai martaba yayi yaci gaba da zaga gidan Washe gari jalilah ta zubawa jalal ido taga ya kwanshi kaya da yawa "ya jalal wai har kwana nawa zakayi wannan uban kayan ai sunyi yawa" Murmushi yayi "kinsan halin abba yana iya qaramin kwanaki kuma yana iya ragemin gara naje da shiri" Ba wani qara maka da zeyi saidai ya rage maka "Haka nake fata ai" Rakiya tayi mishi yana dauke da yaran ga baki daya Suka nufi parking space Kallonshi cool AJ yayi yasa dariya sosai jalal ya hade rai "Ya abdul lafia? Kusa dasu yaje ya karbi yaran "cool jalal wai da gaske 1week zakayi acen? Kanshi ya dafe "1month zanyi" "Ya jalal amma fa 2days kace zakayi" "jalilah 1week abba yace ni kuma na shirya aikin cikin 2days zan gamashi" Kai ta gyada tana murmushi Cool AJ kam dariya kawai yake dan yasan 1week jalal zeyi Sallama sukayi cool AJ ya nufi part din mami da yaran Kallonta yayi "wai ahaka zan tafi? Dariya tayi taje tayi hugging dinshi tare da hada lips dinsu suka shiga kissing din juna Daqyar jalilah ta samu ya barta ya tafi Part din ummi ta nufa Kallon yaran mami tayi cike da murmushi "abdul ina zaka da yara haka da sassafe? "A hannun cool jalal na karbosu kinsan yau ne zeyi tafian toh na hadu dasu ne a parking space" Murmushi kawai tayi aranta tayi mishi addua Call din ummi ne ya shigo wayanshi ya daga "ummina kin tashi lafia? Murmushi tayi mishi "Tafia ba sallama? Ummi na shiga naga kina bacci shiyasa Dana shirya na wuce dan banaso na tadaki" "Allah ya tsaremin kai kuma kayi a hankali a kiyaye dokokin Allah" "In shaa Allah ummi" Sukayi sallama ya kira baffa "Abdul jalal kana hanya ne? Eh baffa ya kafancen din? Lafia qalau abdul jalal Allah ya kiyaye hanya ka kula sosai kaji? In shaa Allah baffa zan kula Sukayi sallama ya ajiye wayanshi Cikin 3hrs ya isa qauyen da mai martaba ya turanshi Kallonsu jalal yake cike da tausayawa yanda suke rayuwa haka yaci gaba da zaga garin yana ganin abinda ke faruwa harda kwalla a idanunshi Zama yayi acikin mota ya shiga lissafin kudin da yaga kamar suna buqata da kuma abinda mai martqba ya bashi Call din mubarak ne ya shigo wayanshi ya daga cike da murmushi "Amma kasan da nine bazanyi maka hakan ba ko? Cike da dariya yake magana "me kuma nayi? At least idan bazaka samu damar zuwa ba sai kamin waya inje mana dan Allah yanzu idan ka dawo ka tarar na mutu kuma fa? Shikenan na tafi ba tare da munyi sallama ba? Murmushi jalal yayi "sorry ba haka bane ka daina zancen mutuwa akanka pls" Toh meyasa kayi haka? "Mubarak wallahi hankalina yakan mutanen nan ga baki daya tunda abba ya gaya mana halin da suke ciki duk da ba qarqashin masarautar abban bane hankalina a tashe yake wallahi" "Eh daman nasan bazaka rasa abin fada ba abdul jalal mai imani" Dariya yayi "mubarak rayuwar mutanen nake dibawa rayuwa ba ruwa ba abinci ai akwai tausayawa" "Ka tausaya musu ni kuma ai ka jefani cikin halin jin yunwa dan bazanci abinci ba sai ka dawo" "Allah ko jawahir ce tayi tafia bazaka qi cin abinci ba bake ni" Dariya sukayi ga baki dayansu mubarak yayi mishi fatan alkhairi sukayi sallama ya ajiye wayan yaci gaba da aikinshi Duk yanda jalal yake tunanin aikin sai yaga yafi hakan ga engineers suna qoqarin fara nasu aikin Call din jalilah ne ya shigo ya daga "my heart desire" dariya tayi "ya jalal duk aiki ne haka? Murmushi yayi "aiki yanzu na fara wallahi" zaa gajiyarmin dakai kenan? Murmushi yayi "bazan bari hakan ta faru ba ai" Haka sukaci gaba da fira yana kallon yanda ake gudanar da aikin Tsawon kwana 3 jalal ya samar da ruwa a qauyen gashi sai fama yake da rigiman jalilah akan ya dawo Cikin tsari jalal ya bawa kowa hannun jari akan su nemi Sana'a yafi ya zube musu abinci idan ya ware kuma shikenan Yau jalal ya cika kwana shida sai murna mutanen qauyen suke da abinda yayi musu ya shirya ya dawo cikin zaria Kwance take Khalil yayi bacci khalifa kuma mubarak ya tafi dashi part din cool AJ Ahankali ya shiga cikin dakin Qamshin tularenshi taji ahankali ta rufe idanunta tana murmushi Kwanciya yayi bayanta da sauri ta juyo tayi hugging dinshi "oyoyo ya jalal" dariya yayi ya qara hugging dinta ya fara kissing dinta................ [25/12, 16:10] Hassan Atk: 🤴🤴JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 206-210 Sai faman dariya take shi kuma ga baki daya yaji jikinshi ya amsa saqon da jikin jalilah yake aika mishi _some hours ago_ Zaune suke a parlour mubarak yayi sallama ya shigo ya nemi wuri ya zauna,,, kallonshi jalal yake cike da murmushi "na angel fushin ne har yanzu? Kai ya girgiza yana murmushi "Meke faruwa ne? Ba komi ya bashi amsa Kallonshi jalal yayi cike da nazari yayi saurin kawar da kanshi ya maida kan yaran da suke kusa da jalal din yana murmushi "Mubarak" jalal ya kirashi Kallonshi kawai yayi ba tare da yayi magana ba "gayamin abinda yake damunka" Kusa dashi mubarak yaje ya zauna "ba abinda yake damuna kawai gajiya ne" Kai jalal ya gyada yaci gaba da kallonshi sam ba wanda yake magana da wani daga cikinsu Tsawon lokaci mubarak ya tashi kawai yana kallon jalal "zan tafi" kai ya gyada mishi kawai ya juya ya tafi jalal ya bishi da kallo Zaune yake a gaban mai martaba ya bayanin aikin da yayi a qauyen sosai mai martaba ya sanya mishi albarka ya tashi ya nufi gidan mamin mubarak "Jalal lafia naga kayi zaune ba magana? Mami dan Allah taimako nakeso kimin,, me kake so jalal? "Mami a rayuwa ba abinda yake sanya mubarak damuwa face abinda ya shafeki ko kuma mahaifinshi dan Allah ki sanar dani damuwarshi" "Jalal yanaso yaje wurin dangin mahaifinshi ni kuma nace baxashi ba saboda basu damu dashi ba kuma basa sonshi dan ba wanda ya nemimu tunda mahaifinshi ya rasu" "Mami dan Allah kiyi haquri yaje tunda sunzo ranshi yanason ya gansu kinga ya shiga damuwa sosai wallahi" Jalal sam bazaije ba gaskiya gara ya haqura kawai Mami dan Allah kada kiyi haka kiyi haquri kinga zai samu lada kuma baasan halin da suke ciki ba dan Allah mami kiyi haquri kada ya shiga wani hali "Jalal banason nacin zance nace bazashi ba ko? Sunkuyar da kanshi yayi qasa tsawon lokaci yana zaune a gabanta "Jalal kana buqatar wani abune? Kai ya girgiza mata Toh ai ka koma ya fiye maka wannan zaman Ta tashi ta shige ciki ya bita da kallo Kusan 10mnts tayi aciki ta fito ta sameshi murmushi kawai tayi "Jalal wannan nacin naka ko mubarak din beyishi ba" Mami dan Allah kiyi haquri ki barshi yaje Address din gidan su alhaji Mustapha azare ta bawa jalal "wannan shine address din gidansu mahaifinshi yaje Allah ya kiyaye hanya Cike da farin ciki jalal yayi mata godiya ya fito ya nufi gidan mubarak Kwance yake kan 3sitter ya rufe idanunshi jalal yayi sallama ya tashi zaune yana murmushi "Daga ina haka? Jawahir fa? Murmushi yayi ya tashi ya kirata "Cool jalal nake gani haka? Murmushi yayi "kawai kinje kin sanya yaro a daki kina koya mishi lalaci bayan shi jarumi ne" Amma kasan nima ai raguwa bace Eh hakane gaskiya shiyasa ko yaushe kina a kwance Dariya tayi suka gaisa tayi mishi ya gajiyar zuwa qauye "Ni zan koma dama naje karbo wani saqo ne kawai" Rakiya mubarak yayi sam ba wannan wasan da yake tsakaninsu har jalal ya shiga ciki mota yana mamakin mubarak Kallonshi "ajiyemin wannan ya bashi kawai yaja motanshi ya fice Mamaki ne ya cika mubarak ya koma ciki ya kira maminshi ta gaya mishi yanda sukayi da jalal din Shiryawa yayi ya nufi gidan mai martaba Kallonshi jalal yayi ya kawar da kanshi yaje kusa dashi ya zauna yana murmushi Tashi jalal yayi da sauri ya rikeeshi "ka tsaya muyi magana mana" fizge hannunshi yayi da sauri mubarak ya tashi ya riqeshi Dariya jalilah tayi "ya mubarak daman wannan fushin da dakeshi Kaine ka janyoshi har ya shafeni? "Jalal bansan me zan gaya maka bane shiyasa" fizge hannunshi yayi kawai ya nufi dakinshi "Ya mubarak Allah nifa mamaki kuke bani" murmushi kawai yayi yabi bayanshi Wuri ya nema ya zauna jalal ya tashi ya fito yaje kusa da jalilah ya zauna "ya jalal kayi haquri mana" Yatsanshi ya dora saman lips dinta yana murmushi Tsaye yayi kusa dashi "jalal meyasa bazaka saurareni ba kawai sai kayita faman fushi dani? Tashi yayi ya kalleahi da kyau "me zaka gayamin? Ni dan uwanka ne kuma friend indeed amma ba in need ba ko? Toh kasa ka bata lokacinka nasan da hakan "Jalal ya kake magana haka" me kakeso ka gayamin yanzu wanda bansani ba? Murmushi mubarak yayi "haquri nakeso kayi" "Mubarak kaje dan Allah" "jalal hamma kasan ni bana mana hakan ko? Cike da zafi jalal yake mishi magana "me kake nufi ne? Me kuma kakeso ka gayamin? Tsawon lokacin da na hadu da kai ban taba gayama ummi damuwana kaine mutum na farko da yake fara sanin duk wani abu da ya shafeni bana boye maka komi har nida family dina ba abinda nake boye maka amma kai sam ba haka bane a wurinka me kakeso yanzu ka gayamin? Kallonshi yayi cike da rauni "jalal abinda nazo kenan in gaya maka sai kuma naga alaman akwai gajiya tare dakai shiyasa kawai ban gaya maka ba dan sanan zaka shiryane kace zakaje ka sami mami" Banzan kallo jalal ya aika mishi "ka ajiye wannan tarihin kuma kasa aranka ko a wurin wani bazaka qarajin damuwa na ba" "Jalal wai kai kenan ko yaushe cikin doramin laifi meyasa bazaka fahinceni ba " "Dan Allah kaje a gajiye nake inaso na huta" Tsaki yayi kawai ya fice jalal ya bishi da kallo yana murmushi Kallonshi ya mayar ga jalilah "jalilah gobe zamuje Neman family din mubarak a bauchi "Ya jalal yanzu duk wannan gajiyan sai kuma ka qara debo wani? "Jalilah mubarak ne fa? Murmushi tayi tadan kwanta ajikinshi "adawo lafia" Wayanshi ya dauka ya kira cool AJ "Abdul pls ka shirya gone za muje bauchi wurin family din mubarak "Wa zeyi driving? Dariya jalal yayi "amma ai zaka tausayamin ko? Mubarak din fa? Ka manta dashi fushi ma yake dani dan na gaya mishi gaskiya Dariya cool AJ yayi " kuma ahakan za muyi tafia? Ka barshi kawai Idan ya gaji zai daina "Idan kun gaji zakace air na'ima nasan fushin yana damunka" dariya sukayi ga baki dayansu jalal ya gaya mishi sammako za suyi Kallonshi jalilah tayi "ya jalal fadanku da mubarak Allah dariya yake bani " jalilah ni kaina mubarak din dariya yake bani kawai nayi mishi hakan ne dan ya sanja wani halin Murmushi tayi "bari naje na hada maka kayan ko? Kai ya gyada yana murmushi tq tashi ta shige ciki................. [25/12, 16:10] Hassan Atk: 🤴🤴JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMUNA ALHASSAN_ 211-215 Part din ummi ya nufa ya shaida musu zasuyi tafi tayi musu fata na gari ya nufi part din mai martaba acen ya sami cool AJ yaje sanar dasu mai martaba Wuri ya nema ya zauna "jalal toh me kuka shirya kai musu? "Abba ai bamusan halin da suke ciki ba bale musan me suke buqata" Murmushi mami tayi "Abdul zan baka saqo cikin garin Idan kunje" Kallonta jalal yayi "meyasa ni bazaki bani ba? Harara ta aiko mishi "bazan baka ba din" Murmushi mai martaba yayi ganin kallon da jalal yayi mata "Mami meye saqon dan bana tunanin zamu shigo da safe wucewa za muyi" "Acikin FGC azare nakeso kaje quarters dinsu duk wanda ka tambaya gidan hajiya Fatima 'yar azare zai nuna maka idan kaje duk abinda kaga ya dace sai ka bata" murmushi yayi sukayi sallama suka fice Tsaye suke parking space na gidan mubarak jalal ya kalleshi "kirashi ya fito muje" Kiranshi yayi ya daga suka gaisa "muna parking space muna jiranka" bazani ba kuje kawai" ya katse wayan Dariya cool AJ yayi "cool jalal kuna fada da mubarak ne? "Yace bazashi bane? Kai ya gyada yana dariya "Muje ciki" suka shiga Zaune yake kan kujera yana wasa da aisam "Mallam tashi ka shirya muje" Jawahir ce ta fito suka gaisa "Bazaka tashi ba? Ko kallonsu beyi ba Kusa dashi jawahir taje "abban khaleel yi haquri kuje mana kaga fa kai kadai suke jira" "Angel suje kawai bazani ba" "Kaga ka daina bata mana lokaci ka tashi ka shirya mu tafi" Cike da tsiwa yake mishi magana "nace bazani ba kuje ko dolene sai naje" ya tashi ya nufi upstair din Kallo jalal ya bishi dashi cool AJ kam dariya ya shigayi yana girgiza kai "Cool jalal ka lallabashi muje dan Allah kasan fa so yake kawai ka lallabashi ka yarda kaine bakada gaskiya" "Abdul kasan me yayi min ne? Koma menene yanzu kaga yanada bata mana lokaci ne" Upstair din ya nufa ya shiga dakinshi ya sameshi kwance, kallo daya yayima jalal ya kawar da kanshi yaje kusa dashi ya zauna "Ka tashi ka shirya muje" tsaki yayi ya tashi zai fita jalal ya janyoshi "wai mubarak me kakeyi haka? Meye amfanin zuwanmu ba tare da kai ba? Saboda nayi magana akan abinda yake damunka shine ya kawo wannan fushin? "Kaga kai kaje ka nemo izinin tafi toh ga address din sai kaje ni bazani ba" Sosai jalal ya dau zafi dashi kawai ya juya ya fice ba wanda ya kalla daga cikinsu ya fice "Tsaki cool AJ yayi ya nufi mubarak din daqyar ya lallabashi ya shirya jawahir ta hada mishi kayanshi kawai ta fice zuwa dakinta Acen ya sameta yaga sai faman fushi takeyi dashi "angel me kuma nayi? "Dan Allah me yasa kakeyin haka? Kaida bros jalal har sai wani yaji kanku sai kayita faman fushi dashi kuma kazo daga baya abin ya riqa damunka" Murmushi yayi "angel kinga jalal ya nuna shi yake sona ni bana sonshi shiyasa nake fushi dashi" Dariya abin ya bata "kai da bros jalal na kasa gane kanku walkahi" Murmushi yayi ya mata peck "kije ki dibamin su khaleel pls" kai ta gyada mishi tayi mishi rakiya Motan jalal ce wacce take irin ta mai martaba tana dauke da tambarin masarautar Fatan alkhairi jawahir tayi musu suka shiga ciki Cool AJ da mubarak ne a gaba jalal yana baya Suka dauki hanya sai cool AJ ne yake dan kawo fira hamma jalal baya kulasu sai faman gudu cool AJ yake "Cool jalal na gaji fa" ya nemi wuri yayi parking Fitowa jalal yayi ya karbi key din da sauri mubarak ya fito ya koma baya sosai cool AJ ya shiga dariya,,, kallo kawai jalal ya bishi dashi ya zaga ya shiga wurin da mubarak din ya fita "Cool jalal meya kawo muku wannan fadan? Sam jalal be kulasu ba yaja kawai sukaci gaba da tafia sosai jalal yake gudu fiye da cool AJ dan yasan mubarak bayason hakan "Malam ka tafi a hankali yara hudu nakeda ban shirya barinsu a matsayin marayu ba" Dariya cool AJ yake yana qoqarin daga wayan mai martaba "Eh abba mun kusa gaskiya saboda cool jalal ne yake driving yanzu" Harara jalal yayi mishi sukayi sallama da mai martaba Tsawon lokaci jalal ya shiga cikin garin azare ya shiga neman bayanin gidansu alhaji Mustapha azare besha wahala ba ya gane gidan yaje yayi parking ya nemi yaro ya tura ayi mishi sallama da wani daga cikin gidan Kallonshi yake sak mubarak saidai shi ba yaro bane suka gaisa "daga zaria muke mu 'ya'yan Maryam ne matar marigayi alhaji Mustapha azare" cike da tashin hankali yake kallonshi "kaine dana mubarak? Kai ya girgiza mishi "hamma Kaine Mustapha azare? Aa yayana ne ya dade da rasuwa ina mubarak din yake? Magana yayima cool AJ suka fito sosai mutumen ya shiga zubar da hawaye "mubarak ina Maryam ta yafemin na cutar da ita na cinye dukiyarka gashi yau duniya tayi mishi zafi ga ciyon shuga ya kamani na sayar da wannan gidan gobe ma zamu tashi ni kadai na rage hajiya ta rasu matata ta gujeni saini da yara kawai mubarak ku yafemin" Kallonshi kawai sukeyi ahankali jalal ya sauke ajiyan zuciya "abba ka daina wannan kukan bayada wani amfani zai iya tada ciyonka dan nasan bazaka rasa hawan jini ba" Dolene nayi kuka ba abinda Yaya Mustapha bayamin amma kaga bayan ranshi na cuci zuriarshi "ka daina cewa haka abba mu shiga ciki sai muyi magana Kallon yaran yake ga baki daya ba wanda bayada kama da mubarak din da ka gansu kasan sunajin yunwa "Abba wannan waye? Murmushi yayi "mustapha wannan yayanka ne" kallon mubarak yayi "yaya ka bamu hamsin mu siyo gari da sikari kaga maryam sai faman kuka take har tayi bacci "kawu Mustapha abba yace mu riqa kiranta da mummy fa kai bakaji ko? Toh batada kunya ne shiyasa nima ai bata girmama sunana" Murmushi jalal yayi ya juya ya fice su cool AJ suka nemi wuri suka zauna Restaurant ya nema cikin farin ya saya musu abinci akayi mishi take away ya biya kudin ya kai musu "Amm kaje ka kira mummy sai taci abinci ko? Yaya kyaleta batada kunya ta riga tayi bacci" Yaya mustapha bata fada da Maryam kaima ka daina "Abba dazu fa dukana tayi ta gudu dan kawai nasha farin da adda bilkisu ta bata Murmushi jalal yayi aranshi yace "wannan halinsu daya da mubarak" "Abba muje waje za muyi magana dakai" ba musu yabi jalal suka fice "Muje wurin wanda ka sayarwa gidan" ba musu ya shiga mota sukaje Sam jalal besha wahala wurin amincewarshi da zai bar mishi gidan shi yakeso ya saya saboda family house dinsu ne Kai tsaye jalal ya biya kudin suka shiga masjid sukayi sallah jalal ya koma dashi gidan Harara mubarak ya aika mishi sam be kulashi ba "Abba za muje Mu nemi wurin da zamu sauka saidai gobe zamu dawo" Godiya yayi musu tare da yi musu rakiya jalal yaja suka fice............. [25/12, 17:18] Hassan Atk: 🤴🤴 JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 216-220 Hotel jalal ya kama musu suka sauka cool AJ ya shiga nashi dakin yabar kayanshi haka mubarak ya tafi ya barshi da kaya ya dauki nashi ya fice kawai Bude dakinshi mubarak yayi ya juyo yana kallonshi "bani key zan dauki kayana" Key din ya bashi ya fice Waya yake da jalilah mubarak ya shigo ya nemi wuri ya zauna har ya kammala waya "malam yunwa nakeji" tashi yayi ya dauki key din ya fice kallonshi mubarak yayi yana murmushi be jimaba ya dawo suka shigo tare da cool AJ suka nemi wuri suka zauna Cin abincin suke jalal yana zaune yana kallonsu har suka kammala "cool jalal bazakaci abinci ba? Kai ya gyada mishi ba tare da ya kalleshi Tashi cool AJ yayi "ni zan kwanta bacci nakeji" ya fice kallon shi mubarak yayi ya tashi ya koma kusa dashi ya zauna "ina kukaje dazu? Sam jalal be kulashi ba "bakaji me nace bane? Kallon mubarak yayi "ka tambayeshi kaji mana "ai na ganshi na tambayeka" "Bazaka yimin magana ba? Mubarak me kakeso na gaya maka? Abinda na tamyeka" "Mun maidawa wanda ya sayi gidan kudinshi ne" meyasa kayi haka? Saboda yana family house ne bakyau a sayar dashi" Murmushi yayi "meyasa bazakaci abinci ba? Banajin yunwa ne Ba gaskiya bane kawai saboda kana jin haushi nane shiyasa Kallonshi kawai jalal yayi ba tare da yayi mishi magana ba "Jalal dan Allah ka riqa fahinta na meyasa kake tunanin na boye maka matsalana amma kai kanq gaya min baka damuwan kaga hakan yana nuna kai kake da zuciya daya ni kuma ba haka bane" "Ai ba qarya na fada ba haka ne mana me kake tunanin zanji a raina kai damuwana nakane amma naka kai kadai ya shafa" jalal bafa haka bane ka gaji sosai kuma abinda naje na gaya maka kenan sai naga kawai zan takuraka ne" "Ban tabaji a raina na taba takuraka ba amma kai har kanajin hakan aranaka saboda ni banaida matsayinda zan sha wahala akanka? Dariya mubarak yayi"nifa ba haka nake nufi ba kaine kayi wannan fassarar" harara jalal ya aika mishi "Pls ka daina wannan fushin Allah ni fushin nan yana takurani" ni nake fushi dakai? Kai ya gyada mishi,, kawar da kanshi kawai yayi "kaci abinci ni zan tafi in kwanta ya tashi kawai ya fice Washe gari jalal ya tashi da matsanancin headache idanunshi kamar wanda yakejin bacci suka nufi gidansu mubarak din Suna shiga ciki Mustapha yayi dariya wacce ta qara fito da kamarshi da mubarak "Jiya ka tafi baka gayamin sunanka ba" murmushi jalal yayi yaja hannunshi suka shiga ciki suka gaida abban "Abba muje waje za muyi magana" ya tashi suka fice Kusa 2hrs su cool AJ na jiranshi basu dawo ba suka kirashi a waya ya daga "cool jalal kana inane? Cikin sanyi yake magana saboda headache dinda ke damunshi "abdul yanzu zamu dawo" Tare suka shiga da wata mata sukayi sallama da gudu sukaje wurinta "umma oyoyo" suka rungumeta Sai faman murna suke ta nemi wuri ta zauna kallo daya tayima mubarak ta ganshi "Mubarak ina yaya Maryam? Tana zaria Kai ta gyada suka gaisa dasu cool AJ "Amma abba yanzu zama haka beze yi ba kamata yayi ka nemi wani business ka fara tunda ga iyali" "Toh abdul jalal wane Sana'a zanyi yanzu? Shafa kanshi yayi saboda tsananin ciyon da yake mishi "abba ka nemi wanda zaka iya sai ka sanar dani" Kallonshi mubarak yayi da kyau "are you sick? Kawar da kanshi yayi daga kallon mubarak "Abba zamu koma ga wannan dubu dari ukune sai kaje ka siyo abinci da zasu daya da sauran abin buqata umma kiyi manage da wannan kafin muga abinda yafi dacewa kiyi dan zaman beze yiyu haka ba" godiya sukayi tare da sanya musu albarka suka tashi abba mudassir harda kuka yake suke fice Abdul ka maidamu pls "Wai meke damunka? Murmushi kawai yayi ya buds bayan ya shiga suka nufi hotel din Kwance yake ya rufe idanunshi ko wane daga cikinsu ya zuba mishi ido kamar ma ba mubarak ba da yakeji kamar ace shine yake ciyon "Cool jalal wai meke damunka ne? Ahankali ya bude idanunshi "bacci ne kawai" "Wane irin bacci,, wannan cumin da kakeyi kuma fa? Murmushi yayi ya buqaci su bashi ruwa Addua yayi a ruwa yasha ya zuba a kanshi Shuru ba wanda yayi magana daga cikinsu mubarak sai faman kallonshi duk ya wani susucewa kallonshi jalal yayi ya sakar mishi murmushi ya tashi ya nufi toilet yayi wanka ya fito ya sanja kaya "muje ko" Ido mubarak ya zare "Allah ba inda zaka garama ka kwanta ka huta" yunwa fa nakeji" harara yayi mishi ya tashi ya fice yaje ya kawo mishi abinci Kadan yaci ya kwanta ya shiga bacci sai a likacin hankalinsu ya kwanta kowa ya nufi dakinshi Sai kusan azahar ya tashi yayi wanka yaje ya sami su mubarak suka nufi masjid Zaune suke dakin jalal "abdul duk abundant za muyi yaune yafi dacewa Mu kammalashi gobe sammako za muyi" "Wannan hajiya Fatima kadai zamu nema yanzu" Ba inda zani kuma baza aje da motana ba Wai saboda me? Ta aikeni ne? Dariya cool AJ yayi ya kira mami a waya yana shaida mata yanda sukayi da jalal Wayan ya bawa jalal ya karba "jalal Aiken nawane baza ajeba? Ni banace baza aje ba nine kawai bazanje ba Motan kuma fa? Mami meyasa bezo da motanshi ba saboda saqonki "Jalal banason shirme Idan ba zaka ba ka bada Mota suje Murmushi kawai yayi ya bawa cool AJ wayan Neman gidan matar sukayi har suka qarasa Sosai tayi farin cikun ganinsu cool AJ ya kira mami ya bata sukasha fira Kudine masu yawa jalal ya ajiye mata sai faman Santa musu albrka take suka fice Dariya taji sunayi qasa qasa yayi kamar beji ba dan yasan shi akeyiwa dariya............. [25/12, 17:18] Hassan Atk: 🤴🤴JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 221-225 Cool jalal wai kai aljihunka baya gajiya ne? Sam be kulasu ba yayi gaba suka sameshi cikin mota direct family house dinsu mubarak suka nufa ya dade zaune cikin mota yana lissafi Kallonshi kawai mubarak yake "malam daina kallona" Murmushi kawai yayi Fita yayi yaje ya dauko wani jaka ya dawo kallon kudin suke ba wanda yayi mishi magana "Abdul wane business kaga ya dace abba yayi wanda at least kullum zai lissafa shima" Dariya sukayi "bros abdul kasan me? Guy din nan asalin bahaushe ne wallahi idan yayi maka wani hausan sam bazakace shine ba" "Ya hada hausan kafacen yazo ya hada dana zazzau" yanzu harda na azare ya dauka ai" Mere baki yayi "kanku akeji" Pls abdul gayamin inji mana "Nawane kudin da zaka bashi? Naga kaga ya dace? Ni inaga kamata yayi ka bashi kudin kawai ya nemi wanda yaga zai iya yafi "Idan kuma ya kashe kudin fa? Dariya jalal yasa "mubarak dan Allah me ka maida abbane? Taya zai kashe kudin zancen abdul shine daidai gaskiya Amma nawane zaka bashi? "2 million" ido mubarak ya zare "Kai wallahi kayi hauka, Allah zaka wayi gari wannan motar bakada kudin da zaka sanya mata fuel" Murmushi yayi "Allah ne zai bani ba kai ba ka gane ko? Ya bude motan kawai ya fice Gaida abban sukayi jalal ya kira maryam yana murmushi "mamina bakya zuwa school ne? Kai ta gyada mishi "meyasa? Ba school fees ne" murmushi yayi toh ki shirya gobe sai kije school kinji? Kai ta gyada tana murmushi Mustapha ne ya shigo yana kuka jalal ya kirashi "abbana meya sameka? Adda bilkisu ce ta dakeni" Cike da girmamawa ta gaidasu "adda bilkisu meyasa kika dakeshi? Yana neman magane kuma na gaya mishi ba kyau yaje islamiya firdausi da farid sun tafi amma shi sai neman magana yake a unguwa" Murmushi jalal yayi "zaka bini muje zaria? Eh zan huta da wannan maryam din" murmushi jalal yayi Amm abba gobe sammako za muyi Mu koma saboda wurin aiki" ba damuwa jalal Allah ya kareku ya albarkaci rayuwarku Murmushi sukayi ga baki dayansu "Ya jalal zan bika fa" kai ya gyada mishi yana murmushi Abba ga wannan sai ka nemi abinyi dashi wannan kuma sai a maidasu school umma wannan kenan kiyi sanaa kada ki zauna a ahaka" godiya suka shigayi jalal kam tashi yayi ya fice yabar su mubarak Ciki abban ya shiga ya fito da wani jaka ya bawa mubarak "idan kaje saika diba ka gani kai ya gayda "abba Mu zamu tafi" Da kawu mustaphan zaku tafi? Kai ya gyada Sai faman murna yake yayi sauri yayi wanka ya sanja kaya suka fice Zaune suke a dakin da jalal yake mustapha har yayi bacci mubarak ya bude jakan ya fara dibawa Kallon jalal yayi yaga hankalinshi baya kanshi yayi murmushi ya qara fito da wani pic aiko ya shiga dariya "Cool jalal pay and see something" murmushi yayi ba tare da ya kalleshi ba Pic din abbanshi ne yana yaro ya tara suma a kanshi sosai ya tsaya jikin wani mota Duka jalal yakai mishi ya goce yana dariya "bros abdul kaga wani wanka da abba yasha? Ga baki dayansu dariya suka shigayi Pics ne masu yawa harda na Auden mamin mubarak "cool amaryar nan fa ta hade" dukanshi suka shigayi yana ihu "Zasu kasheni dan kawai banida twins brother" dariya suka shiga yi "Zaka qara dariyan mami? Allah na tuba bazan qara ba" Cool jalal kaifa mugune wallahi ya fada yana qoqarin tashi Da qarfi suka maidashi ya kwanta "cool jalal kaifa magajin sarki ne" wani bata rai jalal yayi "Allah za muyi fadan da bazamu shirya ba Idan ka qara kirana da wannan sunan" ya dakeshi yaje ya kwanta Dariya suka shigayi "ai duk wanda aka hada Allah beyi ba qarshe da fushi zai qare" dukanku sai kun gaji sarkin Yana gama fada ya fita da sauri yana dariya Kai cool AJ ya girgiza yabi bayanshi Washe gari sukayi sammako suka dauki hanya zuwa garin sarki mahmud Cike da gajiya jalal ya qarasa dasu gidan mubarak "dan Allah kada nace sai gone zaka fito ka sameni anjima" Kai ya gyada suka fice Part din Ummi ya ajiye Mustapha ya fice ba tare da yaga jalilah ba Kaya ya sayawa ya saya mishi ya bawa Ummi ya fice zuwa part dinshi Tsalle jalilah tayi tayi hugging dinshi Ajiyan zuciya ya suke ya qara hugging dinta tana dariya "Ya jalal hamma kasha gajiya gaskiya" murmushi yayi mata idanunshi suna a rufe kissing din lips dinshi tayi ya bude idanunshi da sauri lokaci daya sukayi dariya ya bata suka nufi daki *9:30pm* cool AJ da mubarak suka shigo parlour'n jalal yana kwance sukayi sallama ya amsa musu daga kwancen "Cool jalal duk gajiya ne haka? Murmushi yayi ya tashi yaje sanja kaya suka nufi gidan main mubarak Kallo daya tayiwa Mustapha tasan dan uwan mubarak din ne "Jalal wannan waye? "Sunana Mustapha" murmushi jalal yayi Kallonshi mami tayi da alaman tambaya "Abba name lokacin da aka haifeni yayi mafalkin abba Mustapha shine ya sanyamin sunanshi hamma dan rashin kirki irin da Maryam bata kirana da uncle mustapha" Dariya jalal yayi dan haka yake ganinshi kamar mubarak din "Jalal da gaske yake? Kai ya gyada mata Murmushi tayi anan mubarak ya shiga gaya mata abinda jalal din yayi "Jalal meyasa ka kashe kudinka haka? Mami air ba kashewa nayi ba na basu ne saboda su zauna lafia" dariya cool AJ yayi jalal ya aika mishi da harara "Allah yayi albarka ai ko albarkacin abban mubarak zaa iya taimaka musu,,,, jalal hamma wannan anan zai zauna ko? Sosa kanshi yayi "mami na Riga na bawa ummi" jalal ni kadai fa nake zaune a gidanan Mami zan baki aisam da khaleefa Idan suka qara girma Aa banaso dan a gidan nan mubarak zai tare Murmushi yayi suka dan taba fira sukayi mata sallama suka fice kowa yayi gabanshi jalal ya maidawa Ummi uncle qarami............. 🤴🤴JININ SARAUTA 🤴🤴 *Written by Hafsat MN* IN DEDICATION TO _AUNTY AMINA ALHASSAN_ 226-230 _Some years ago_ Sallama sukayi suka shigo aisam ne a gaba su khaleel na bayanshi "Abba sanu da gida" aisam daga ina haka? Abba mubarak mukayiwa rakiya shine mukazo gaidaka" murmushi yayi "Ummina fa? Taje batason ganin mummy jalilah"murmushi yayi Khaleefa wai school ne ya maidaka haka? Abba fada sukayi da junior" fada kuma? Abba shine yakemin rashin kunya kuma abba ya gaya mishi nine babba ya daina" Kai ka fiye zafine shiyasa,,, aisam dama nasan bazaka bani gaskiya ba amma ai lina ce shaida "Tsaki khaleel yayi "wai kai kenan komi lina ce shaida" khaleel na gayama Idan ka qara yimin tsaki zamu bata dakai Mubarak ne ya shigo shida aisha qaramar 'yar juwairiya sai kuma maryam lina wacce itace qaramar 'yar jalilah sai kuma mudassir asrim na qaramin jawahir "Wai fadan ne bazai qareba? Abba mun daina "ai bazan qara fita daku ba" Abba laifin ya khaleefa ne shi yake mishi rashin kunya "Na tambayeki? Abba wai meyasa kafison ya khaleefa ne akan ya aisam? Dariya jalal yayi "Lina su mufida da mufid fa? Dariya tayi "ummin abban jalal tace a wurinta zasu zauna yau Rana daya jalilah da juwairiya suka haihu aka sanya musu mufida da mufid jalilace keda mufid Daqyar mubarak ya hada kansu ya sasu a gaba zai wuce dasu jalal har tausayin mubarak yakeji ga baki daya ya kwashe yaran ya maida wurinshi sai faman hidima dasu yake Zaune suke a gaban mai martaba ga baki daya ya tarasu yanason magana dasu "Nasan za kuyi mamakin wannan taron dana shirya toh ba komi bane inaso na shaida muku zanyi murabus ne sabida wasu dalilai Na farko lafiana na biyu kuma shekaruna sunja banaso na Gaza da mutanen da suke qarqashin mulkina dan hakan zan sauka na samu hutu nima Shuru ba wanda yayi magana "kaka toh ka bawa abba jalal mana sai ya zama sarki" cewar aisam Harara jalal ya aika mishi "Alhaji Mustapha ai abba jalal ba jinin sarauta bane" murmushi jalal yayi yana kallon cool AJ wanda bakine dauke yake da addua akan Allah yasa a bawa jalal sarautan "Haba yaya wane irin shi ba jinin sarauta bane" toh Maryam kinsan dai jalal akan dole yake zaune damu abdul jabbar ne zai gaji sarautar zazzau Dariya ce ta subucewa jalal da mubarak ganin yanda cool AJ ya hade face Murmushi mai martaba yayi "Wannan shine dalilina kuma abdul jabbar Kaine zaka gaji wannan karagar ni kuma zan dawo gida saidai abinda ya shige maka duhu acikin shanin masarautar zaka iya zuwa ka sameni "Abba da wane ilmin ne zanyi sarauta? Murmushi abban yayi ya tashi kawai ya fice Harara mamin abdul ta aikawa jalal Na angel ni zan dan fita da jalilah zatace gidan qawarta amirah "Dan Allah Idan kaga uncle qarami ka turashi ya karbo saqon" kai ya gyada mishi ya fice Ba wanda ya qarajin voice din cool AJ ya tashi kawai ya fice mubarak ya shiga dariya "Mubarak Allah zamu bata" mami na daina ya tashi ya hada kan yaran ya fice Murmushi mamin abdul tayi "mubarak abban yara" dariya mamin mubarak tayi "ai jawahir ce da qoqari "Uncle qarami daga ina haka? Kanshi ya sosa yana dariya "ya jalal birthday din wani friend dina naje" Murmushi yayi "toh ai zaka karbomin saqon mubarak ko? Eh amma banida fuel wanda zai wadaceni Kai jalal ya girgiza yana murmushi "kaje wurin Ummi ka karba" ya jalal batada kudi gaskiya Kallonshi "yq akayi kasani? Ummina ce fa? Dariya jalal yayi Uncle wannan case din sai ka dawo muje wurin ummi zanji wa yakeda Ummi tsakanin jalal da uncle qarami Dariya sukayi kowa yayi gabanshi Kyau ta kama Friday sarki yayi murabus busa zai Dora danshi Mubarak da jalal sai faman kallon cool AJ suke duk ya wani hade ranshi aka kammala jabawani da tarihin masarautar a Idan aka gabatar da Abdul Jalal a matsayin sarkin zazzau Kallon abban jalal yayi ya juya yana kallon baffanshi murmushi yayi mishi Kasan ya rage cool AJ yayi dariya dan yanayin jalal din b ba mai fassaruwa bane Cike da tashin hankali yake zaune aka nadashi a matsayin sarkin zazzau Hamdala abbansu yayi saboda cikar burinshi Ba jalal ya samu dawowa gaida ba sai qarfe daya na dare direct part din mai martaba yaje Kallonshi yayi tare da sakar mishi murmushi "Abdul jalal an sallami mutane ne? Zama yayi nesa da mai martaba "abba meyasa ka zabamin wannan rayuwar? Hakan ya nuna kenan ni ba dan malam Ibrahim bane ni danka ne" "Abdul jalal sam ban doraka akan wannan mulkin ba saida amincewar iyayenka" Ajiyan zuciya ya suke "Kayi haquri jalal haka rayuwa take zuwa inaso mutqnen zazzau su kasan ce qarqashin ahugaba na gari kamar yanda suka saba ahiyasa na doraka akan mulkinsu, jalal kai kadaine zakayi musu adalci kai kadaine zaka tausaya musu ka riqesu tamkar yanda uwa take riqon yaronda ta haifa ka kuma yi adalci a tsakaninsu Jalal saboda masarautar nan da kuma ci gaban alumma ya sanyani doraka akan wannan karagar mulkin badan na shiga rayuwarka ba kuma inaso kayi adalci kamar yanda nasan, kai mutum ne mai adalci mai jin tausayin mutane inaso ka riqe wannan jalal kuma har yanzu kai abdul jalal ibrahim ne ba abdul jalal mahmud ba" Ajiyan zuciya ya suke sarki yayi mishi fatan alkhairi ya tashi ya nufi part dinshi Zaune ya sami jalilah ya sakar mata murmushi yaje kusa da ita ya zauna "Ya jalal ka dawo? Kai ya gyada mata "Yq mubarak ma be Dade da ficewaba tare yake dasu aisam dasu junior harda su uncle qarami Murmushi yayi "jalilah muje ni tayani nayi wanka na gaji sosai Kwance yake kan jikin jalulah yayi shuru sai faman tunanin yake "Ya jalal ka cire damuwa aranka haka rayuwa take zuwa nasan mulki abune mai wahala hamma ahaka zakayi haquri ka kuma jure kayi" Murmushi yayi "ba damuwa nakeda ba kawai ina tunanin wane nauyine yafi ko wane acikin masarautar nan inaso na dorashi akan mubarak ne" Dariya tayi "ya jalal ka tausaya mishi jifa yanda yake fama da yaran nan yara nine kuma ka Dora mishi mulki" Ki barshi kawai nafison hakan ai Haka suka sha fira har sukayi bacci Bayan sun kammala sallah sarki jalal ya koma ciki yaci gaba da baccinshi lokacin zuwa aiki yayi ya shirya ya fito Kallon mamaki mai martaba yayi mishi yayi mishi alama da yaje suka nufi part din abban "Jalal fada kuma fa kasan dai bazaka samu Hutu ba sai ka Dade sai ka gama shirts komi kafi ka samu Hutu kuma ka riqa sammakon fita maza tashi kaje ka Sanja kayan ana jiranka a fada Jiki a sanyaye jalal ya koma sosai ya bawa mai martaba dariya.............. ********************** ? ************************** ********** Ai Hausa Novels **************** *************************? ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ? ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ? **************************